0% found this document useful (0 votes)
824 views1,522 pages

Sakayyah-Aysha Aliyu Garkuwa

Uploaded by

eshraty3
Copyright
© © All Rights Reserved
We take content rights seriously. If you suspect this is your content, claim it here.
Available Formats
Download as DOCX, PDF, TXT or read online on Scribd
0% found this document useful (0 votes)
824 views1,522 pages

Sakayyah-Aysha Aliyu Garkuwa

Uploaded by

eshraty3
Copyright
© © All Rights Reserved
We take content rights seriously. If you suspect this is your content, claim it here.
Available Formats
Download as DOCX, PDF, TXT or read online on Scribd
You are on page 1/ 1522

❤️❤️❤️

‫بسم لله الر حمن الر حيم‬...

2:03 Pm.

Friday 4 February 2022.

*SAKAYYAH*

*GARKUWA SABON SALO*

Book One, page 1

NA

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*FREE PAGE*

*Komai na rayuwa sai Allah ya nufa, kugafa Time and Date din da na fara rubata littafin nan amman sai
Allah ya bani ikon fara sakinshi.*

Wannan littafin nawa mai suna FATTANAH kirkirerren labarine, Amman akwai wasu abubuwan dama da
sun faru da gasken gaske, banyi da wata ko waniba, Hakkin mallakarsa nawane AYSHA ALIYU GARKUWA,
ban aminceba! ban lamunceba!! ban yardaba!!! ayimin amfani da labarin littafina tako wacce sigaba, har
sai in an nemi izinina an samu sahalewata, sabida haka ga number ta 09097853276 kafin ayi komai a
nemi sahalewata, komai yafi daɗi cikin mutuntaka zama lfy yafi zama ɗan Sarki!!!..
*Yah Allah ka bani ikon rubuta al'khairai da abinda zai amfani al'ummar fiyeyyen halinta, Ya Allah kayi
riƙo da hannayena, tunanina, idona, yatsuna, nazarina, ka hanani samun damar rubuta duk wani abin ƙi
da zai zamewa al'ummar musulman masifa ko ƙazanta ko bata tarbiyya, ya Allah ka bani ikon tunasarwa
da jan kunne da jan hankali ih zuwa ga nasarar mai tawakkali da imani da riƙo da ibada, Ya Allah ka nuna
min ƙarshen littafin nan lfy kamar yadda ka nuna min forkonsa Lfy dani da iyayena ƴaƴana, yayuna,
ƙannena, da maƙota makaranta na masu biyana kafin su karanta da masu karanta na sata da dukkan
musulmai ya Allah ka nuna mana forkonsa da ƙarshensa lfy kayiwa rayuwarmu data ƴaƴan mu al'barka
ka shirya mana ahlinmu ka bawa yayanmu mata maza na gari, mazan ka basu mata na gari, aurarru ka
basu zaman lfy da zuri'a ta gari ka tsare mana tarbiyar yaranmu bisa tafarkin dai-dai. Ya Allah kayi mana
rufin asiri duniya da ƙiyama, ya rabbil izzati ka dubi bayinka masu buƙatan haihuwa da aure da idanunka
masu rahama ka basu masu albarka, marasa lfy Allah ka basu lfy masu juna biyu Rabbi ka sauƙesu lfy
masu fama da matsar babu da bashi ya Allah ka yalwata masu ka basu arziƙi mai albarka la basu ikon
biyan bashi, Ya Allah ƴaƴan musulmai da tatbiyarsu ke a gurɓace Allah ka shiryesu. Ya Allah ka kawo
mana sauƙin wannan zadar rayuwar, ka magance mana fitintinun dake damun ƙasarmu, mahajjatsnmu
kasa sunyi hajji Mabruk. al'farmar Annabi da al'ƙur'ani, ya Ubangijin talikai ka jiƙanmu ka yafe mana
kurarenmu kayi mana Kekkyawar ƙarshe kasa mucika da kalmar shahada yayin barinmu duniya ka
sadamu da mala'ikun rahama masu zaran rai salamun salaman. Yah hayyu ya ƙayyum birahamatika
astaƙisu ka jiƙan mahaifiyata Fatima (Deddena) ka sanyaya mata makwanci ta ka haskaka mata ƙabarinta
ka yelwata matashi ya Allah kasa tana cikin dausayin jannatul firdausi ya ubangijin kasa can yafi mata
nan, ya Allah ka bamu haƙurin da juriyan rashinta. Ya Allah kai mata rahama al'farmar Annabi da
al'ƙur'ani😭😭😭*

~Aisha Alto, Mom Bobo, kune wanɗa nake ganin kamar kunsan ciwon da nakeji a raina a duk sanda na
tuna banda mahaifiya, domin kusan lokaci daya muka rasa iyayenmu. Allah yayi musu rahama yasa sun
huta, ina tunawa a lokacin nafi son yin mgn daku fiye da kowa a social media, domin gani nake kun san
yadda nakeji a zuciyata, Aisha Alto addu'o'in da kikeyi min dani da mahaifiyata yasa nakejin ke ta
dabance mom bobo kuwa munsha kokawa tare, mu rasa mai lallashi wani tsakaninmu~

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine 1k ne kacal wannan Free page, yar uwata ki biya ki karanta abinki cikin
Salamah 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP
09097853276. In baki da account zaki iya bada a P.O.S ki Basu 100 na su turo 900 wasuma 50 suke amsa,
ko kuma ki sayi katin Mtn sai ki copy number's ɗin katin ki turo min ta WHATSAPP. Banda V.T.U. dan
Allah.*
A hankali ta turo ƙofar ɗakin nata, cike da jin nitsuwa da salamar, sanin ta yanke baccinta ne ta tashi
cikin talatainin daren, domin neman aminci da yardar ubangijinta daya halincceta ya bata rai da lfy, cikin
rashin tsoron da ko yaushe in ta tashi tsakiyar dare, Allah ke yaye matashi, duk da kasancewar makaken
gidane bila haddin wanda ke kewaye da tsirrai, kana ga wutsiyar kogin Gembulan na jihar Taraba da
yayiwa gidan zanen harafi C, yayinda kuwa su biyu ne rak suke rayuwa a cikin ƙaton gidan.

Koda yake tazarar dake tsakanin ɗakinta da sade ɗin jikanta Modibbo tazarace mai yawan gaske, sai dai
suna raya gidan da Ambaton Allah a koda yaushe, shiyasa ubangiji yake saukar musu da cikekkiyar
nitsuwa salama.

Numfashin ta fesar a hankali tare da gyara ɗaurin zaninta, kana ta gyara riƙon da tayiwa yar butar dake
hannunta.

Ido ta lumshe tare da buɗe su a hankali, sabida wani irin sassayan iska mai masifar daɗi da ratsa jiki da
taji yana ratsata da sakar mata wani irin nitsuwa, salama, da farin ciki.

Juyowa tayi ta kalli yamma sabida ganin wata ta faɗi alamun dare ya tsala, domin watan tayi kwana
goma sha ɗaya ne, faɗawanta ke nuni da biyun dare ko ɗaya da rabine.

Kai ta ɗan juyo gabas ta kalli ƙofar safe ɗin Moddibo wanda yake can nesa da ita sosai, yayinda wasu
sassayan fulawowi yayiwa ko ina na gidan ƙawanya.

Tsarin ginin gidan tsarine, wanda ko a ƙasashen turawa na musamman ne,

Ƙaton gidane mai yalwar fili.

Daga can bakin gate ɗin gidan filine mai girma wanda zai iya ɗaukar motoci shida ba tare da wata ta gogi
wata ba, ko matsi wataba, ɗakine mai ɗan girma a bakin gate ɗin wanda ke haɗe da bayi a ciki, da yar
baranda alamun ɗakin mai gadi, saidai babu kowa a ciki.

Daga gefe kuwa watsu tsala-tsalan bishiyoyin na mijin gwanɗa ne masu masifar tsawo da ganye mai
duhu a can sama sune suke jere reras a jikin katangar gidan baki ɗaya, daga ƙasansu kuma, wasu tsirran
fulawowi ne masu masifar kyau da sanyi masu collor's blue, red, and yellow.

Tsakanin farfajiyar gidan da can cikin gidan kuma, akwai wani katanga a tsakiyar da kuma ɗan
madaidacin gate shima ɗin mota zai iya wucewa ta nan,

Cikin katangar shima zagaye yake da bishiyoyin dabino ta wajen ta cikin kuma in bishiyoyin mangoro ne
guda biyu sai daya gefen kuma na goiba, ne da kuma cabɓulle (Tsada) akwai fili ta gefen hagu, inda
motoci biyu zasu iya tsayawa a wurin.
Sai gefen dama kuma, wani ɗan siririn hanya ne, wanda fulawowi ne yazama kamar katangar wurin,
tafiya kaɗan zakayi ka riski part din Moddibo, irin ginin nanne mai tudu, duk da bawai bene bane amman
ginin a sama sosai yake, forko daga wurin baranɗace mai girma, da tudu wacce ke malale da tayis mai
masifar sheƙi, a bakin barandar anyi wasu steps guda bakwai masu faɗi, kafin hawa barandar,

A gefen dama da hagunsa kuwa wasu fararen ƙarafun silver ne masu kyau sukayiwa barandar garkuwa, a
ƙasansu kuwa, wasu. Tukwanen ƙasane masu tsirran fulawowi masu masifar kyau da ƙamshi, kana a kan
ko wanne step akwai tukanen a gefen hagu da daman a jere, guda bakwai-bakwai kenan.

In ka gama haurawa saman barandar kuwa ka juyo ka kalli bayanka ras zaka hango tekun Gembilan
kwance a can, da tsirran bakin Kogin.

A can bayan Part ɗin nashi kuwa wani tamfatsetsen garding ne mai masifar kyau da ƙamshi, sai wani
tabkin wanka mai kyau kujeru guda bibbiyu a kusurwowin alƙibila, sai kuma gado a gefen dama da
hagunsa,

Cikin Part ɗin nasa kuwa, wani tamfatsetsen parlour ne mai kyan tsarin ƙasaitattun kujeru da labulaye da
kayan wuta, komai na ciki farine tas,

tambarin shaidar tsananin tsabtar ma-mallakin wurin kenan, sai ɗan ratsin sky blue, wanda hakan yasa
in ka shiga falo sai kayi zaton a sararin samaniya kake shawagi.

Sai dinning area, da kuma kitchen, sai wani yalwataccen corridor'n wanda ke gefen dama da hagu ko
wanne bedroom ɗaya ne a ciki, sai can mashigar falon nanma akwai wani ɗan madaidaicin bedroom.

Hatta cikin falon kuwa kewaye yake da fulawowi, shaidar ma-mallakin wurin masoyin sirraine da sanyi da
kamshi window palon irin manyan nanne har kusan ƙasa, haka yasa yana iya hango bakin tekun daga
cikin palonshi.

Daga Part ɗin nashi kuwa gefen hagu akwai wata hanyar mai kewaye da tsirrai, wacce ke sadashi da can
cikin gidan.

inda ɗaki ɗaya ne rak, na kakarsa Innayi wacce tace ya isheta rayuwar duniya.

Sai kuma kitchen nata a gefe mai tsarin gargajiya, kana da bayan gidanta can gefe, domin sam taƙi yarda
ayi mata bathroom a cikin ɗaki, acewarta kada santsin tayis ya ƙaryata, dole haka Modibbo ya haƙura da
tsarinta komai na gargajiya, hatta gadonta taƙi a sauya mata.

Sai dai ta amince da tsarinsa na zageyesu da tsirran shuke-shukensa da zuba mata tattausan Turkey
carpet mai masifar taushi, tsarin dakin nata komai ya fito kamar na gidan sarakai shuke-shiku kuwa ba
dama.
Daga can gefen hagun side nashi, wani wurine mai ɗan tudu wanda akayiwa rumfa irin ta gargajiya
rumfar bunu, gefenta zagaye, da tsirran, cikinta kuwa wasu tsala-tsalan kujerune masu masifar kyau
guda hudu da table a tsakiyar su, sai ɗan dandamali na al'adar mutanen Gembilan wanda suke hura
wuta a ciki sabida rage tsananin sanyin da ake tsula musu.

ALLAH kuma ya yelwata hannunsa da al'barka duk abinda ya shuka sai ya tsiro a yalwace.

(Moddibo kenan)

Numfashi Innayin ta sauƙe lokacin da ta gama ƙarewa farfajiyar gidan da lukkunan gidan kallo,

duk da ba hasken farin wata, babu kuma na taurari sosai, sakamakon hadarin gajumaren da yayiwa
sararin samaniya ƙawanya.

Juyawa tayi ta nufi, ɗan bayan gidanta dake, nan gefenta kaɗan, tana maiyin taku cikin yanayin tsufar da
ya cinmata, tare kuma da taka tsantsan gudun kada santsin simintin dake malale a farfajiyar sashin nata
ya kadata.

A bakin ƙofar bayin ta ɗan tsaya tare da yin, addu'a shiga bayin.

“Allahumma inni'aauzubika minal kuɓsi wal kaba ihsi”.

Kamar yadda Moddibo ke nusar da ita mahimmancin addu'a ako wanne lokacin.

Bayan ta fito ne, da addu'a a bakinta, ta zauna bisa, wani dutse mai kyau dake bakin barandar ɗakinta, ta
fuskanci gabas.

Tare da fara al'wala.

A can side ɗin Moddibo kuwa, kwance yake, harshensa jiƙe da ambaton Allah, duk da cikin bacci yake.

Saidai baccin, ba baccine kamar na kowa ba, domin bacci yake cikin wani irin yanayin daya gaza
tantancewa, shi ba bacci ba, kuma ba ido biyu ba, ba kuma mafarkiba ba kuma zahiri ba, ba kuma a
sumeba wasu abubuwan da lokuta da dama yana riskarsu cikin bancinsa yake fuskantar su.
Ita kuwa Innayi a hankali ta gyara zamanta, tare da juyowa ta kalli bayanta, da sauri sabida wani irin
haske da taga ya gilmawa ganinta, sai kuma tayi saurin juyowa gabanta ta, kalli gabas saitin ɗakin
Moddibo domin a zatonta ko an dawo da wutar nepa ne.

Ga mamakinta kuwa, babu alamun hasken wutan nefan sai wani irin sanyi mai ratsa jiki.

Haka nan taji wani yanayi na rufeta,

wanda yafi kama da tsoro abinda bata taɓa fuskarta sa acikin gidanba duk duhun dare.

Hakan yasa tayi saurin sunkuyar da kanta taci, gaba da yin al'wa'ar, hannunta ta wonken, kana ta ciko
tafin hannunta na dama da ruwa, zata kai bakinta domin kuskuran baki kenan.

Wani irin saurin ɗago kanta tayi ta kalli gabanta, sabida ganin wani irin masifeffen haske mai firgitarwa
da taga ya haska illahirin duniyar har hasken yana haska cikin ruwan dake tafin hannunta.

Cike da tsoro ta zubda ruwan tare, da juyawa ta kalli.

Gabas da yamma Kudu da Arewa.

Babu mutun ba dalilinsa, babu kuma alamun ta inda hasken ke fitowa.

Kana kuma ga kuma hasken dake tsananta.

Da wata sassayan iska mai ratsa jiki da sanyaya zuciya.

Wacce tasa Moddibo gyara kwanciyarsa tare da ci gaba da wani irin bacci mai mayataccen daɗi da yaji ya
dannesa da kuma shigo masa da wasu sabbin ababen gani a idanniyansa, yayinda harshensa kuwa ke
nanata addu'o'in masu tarin yawa.

Yayinda ita kuwa Innayi, wani irin tsuma jikinta ya farayi lokacin da taga gaba ɗaya duniyar ta ɗauki wani
irin mashahurin haske mai kyan gani.

Wanda ta rasa ta ina yake fitowa.

“Innalillahi wa innailaihi raji'un hasbunallahiwani'imanwakil”.

Ta fara maimaita cikin firgici lokacin da ta ɗago kanta, ta kalli sararin samaniya.

Wani irin kerma da makerketa mai cike da tsananin tashin hankali, firgici, tsoro, da karkarwa jikinta ya
farayi, sabida yadda taga ubangijin talikai, yana wanzar da ikonsa da buwayarsa a sararin samaniya.
Wasu irin masifaffun hawaye masu zafi wanda irinsu kan tsinkowa ɗan Adam lokacin da yaga tsananin
abin tsoro da shiga firgici da ƙudurar Allah.

Kar-kar haka jikinta yake rawa, ganin yadda taurari.

Suke fizgowa sunayin wani irin haske mai kashe idanun ɗan adam, wanda sune take ganin duk sun cika
sararin samaniya da haske tamkar rana.

“Ya hayyu ya ƙayyum birahamatika astaƙisu, ya Salam, innalillahi wa innailaihi raji'un, la haulawa ƙuwta
illabillahil aliyul azeem”.

Sune tasbihai da furucan da ubangijin ya bata ikon furtawa, lokacin da ta fara ganin taurarin sunayin
ƙasa tamkar zasu faɗo, ƙasa domin gani take kamar sai sunzo har ƙasa sosai kamar zasu taɓo rufin
kwanon ɗakin Modibbo, sai kuma taga ubangijin ya janyesu sun koma sama da azaban sauri tare da
tartsatsin haske mai kyan gani.

Fadin halin tsoro ko tashin hankali ko firgici da ɗimuwar da take ciki ya zarta zaton mai zato, ya wuce
tunanin mai tunani ya shallake nazarin mai nazari, wasu irin wahaye ne ke kwaranyo mata.

Yayinda ta koma baya ta jingina bayanta da jikin filan barandar ɗakinta dake bayanta, ta jingina kanta
tana kallon sama.

Tare da fara nanata kalmar shahada.

Domin ta gama sallamarwa cewa, lokacin ta yayi, ma'ana mutuwa zatayi.

“La hailahaillahu Muhammadu Rasulullahi sallahu alaihi Wasallama”.

Shi ta fara maimaitawa can ƙasan maƙoshinta domin.

Komai na jikinta ya fara tsayawa, sabida azabebben tsoron daya rufeta da cikekken imanin kaɗaita
rabbissamawati wal ardi zuwa yanzu tama fara ɗimautan shin anyama kuwa a raye take?.

A ƙalla 30 minute ubangijin talikai na wanzar da ikonsa! Da kuma, buwayarsa!! Can kuma sai ta fara
ganin gaba ɗaya duhu na meye hasken.

Duhu mai cike da sassayan iska.

Wani irin tsorone ya kuma rufeta wanda ya diro mata da zazzafan zazzaɓi mai haɗe da masifeffen ciwon
kai.

Wanda ya tilasta mata kife kanta bisa guiwowinta tare da rumtse idanunta tamkar zata liƙesu da juna.
A can cikin masarautar Gembilan kuwa, Gimbiya Dadu ce, ke kwance bisa tsakiyar gadon ta, wani irin
masifeffen mafarki mai tada hankali takeyi.

Wanda yasata ihun neman ceto, wanda bata saninba har ya fito fili.

Fitarsan ne, yasa hadimarta saurin shigowa tare, da tadata. Ai kuwa cikin tsananin firgici da tsoro ta
farka tana mai karkarwa, lokaci guda kuma zazzafan zazzaɓi ya rufeta.

A nan gidansu Moddibo kuwa.

A hankali ya fara buɗe idanunsa tare da ambaton Allah.

Hannunsa yasa bisa bed side drawer ya jawo wayarsa.

Gefen wayar ya ɗan taɓa da yatsarsa manuniya, wanda hakan yasata kawo haske har ya haska
Kekkyawar fuskarsa mai cike da yalwataccen saje mai sulɓi da ɗan madaidaicin gemun da bazai uwace
kamu ɗaya ba yayiwa siraran jajjayen leɓɓansa masu sheƙi ƙawanya.

A hankali ya ziro ƙafafunsa ƙasa, sabida ganin, ƙarfe huɗu saura kwata.

Bathroom ɗinsa ya nufa.

Yana shiga yayi brush da wonka tare da yin al'wala, kana ya fito.

Durowarsa ya buɗe yayinda yake amfani da wayar hannunsa wurin haska abin nemansa domin har
yanzu babu wuta kasan cewar yanayin garin Gembilan garin mai masifar sanyi mai daɗi, yasa basu cika
damuwa da rashin wutar da ƙasartamu ke fama dashi ba.

Wata tattausar jallabiya fara ya zira kan ƙananan kayan dake cikinsa, tare da jawo farin hula taɓa kaji
hadis a kansa, turaren Oud bakhur mai masifar ƙamshi ya fesa, tare da sa hannunsa na dama, ya zaro
carbinsa kana ya fito, falonsa, tare da sassarfa ya buɗe ƙofar falon ya fito.

Can cikin gidan ya nufa kamar kullum domin tabbatar da cewa kakartasa ta tashi daga bacci duda yasan
kullum bisa sallaya zai sameta to amman hakan baya hanasa zuwa.

Ɗan tsayawa yayi tare da kallon inda Innayi ke zaune har yanzu, yadda kanta ke kife bisa guiwarta sai
yayi kamar tana sunkuyene irin zata wonke fuskartan nan.
Da ɗan sauri ya juya ya nufi bakin gate nasu yana mai tasbihi.

Ƙarami ƙofar dake manne jikin gate ɗin ya tura ya fita asalin farfajiyar babban gate din nasu,

A hankali yake motsa laɓɓan bakinsa, yana taibihai, tare da shaƙar sassayar iskar,

A hankali ya kuma buɗe ƙaramar kafar kana ya nufi masallacin jumma'a dake layin nasu wanda yana
kallo tamfatsetsen gate din gidan tsohon gidan Alhaji Abubakar Mafindi mahaifi ga Amininsa M Jamil
kenan.

Ita kuwa Innayi ƙamshin turarensa ne, da kuma motsinsa ya tabbatar mata shine, so take ta ɗago kanta
amman ta gaza, sabida wani irin sarawa da kanta yakeyi.

Har yanzu sunan Allah take kira, a ƙalla mintuna 20 da fitarsan kafin Allah ya bata ikon motsawa,

Cikin ƙarfin hali ta ɗago kan nata, lokacin da taji sautin murya Jamil yana kiran assalatu.

Wasu irin zafafan hawaye ne suka tsilalo mata wanda tsananin ciwon kan ne ya jaza mata su,

Cikin ƙarfin hali tayi, al'wala tare da yunƙurawa ta mike tsaye tana mai dafe kanta, ta koma, cikin
ɗakinta, dai-dai lokacin kuma aka dawo da wuta, yayinda ko ina ya gauraye da haske, sallaya ta shimfiɗa
kana ta zira hijabinta, ta fara nafila, jiki na rawan zazzaɓi da kyarman tsoro tanayi tana mamakin shin wai
ashe a raye take?...

Ƙarfe bakwai dai-dai na safe.

Ya shigo gidan, maida ƙofar yayi ya rufe, tare da ɗan tsayawa, tsakiyar gidan, yana mai kallon ƙofar
kitchen ɗin, Innayi yana mai nufar cikin gidan.

Agogon hannunsa ya kalla, tare da ɗan jinjina kai sai kuma ya juya, ya nufi, side ɗinsa, yana shiga
bathroom ya wuce, ƙofar ya maida, ya rufe, tare dasa hannunsa ya jawo, tattausan towel, ya ɗaurasa a
ƙugunsa bayan ya zare, jallabiyar, da vest, yana ɗauke da towel, sassayan numfashin ya fesar kana ya
shiga cikin jaccuzie ɗin.

Cikin nitsuwa yayi wonka fes, ya fito.


Yana wani irin masifeffen ƙamshi yayinda gargasan jikinsa ya kwanta lib a tattausar farar fatarsa da
damshin ruwa,

Wani towel ɗin ya jawo ya ɗaura, kana ya zare na ƙasan, matseshi yayi tare da shanyasa.

Sannan ya fito yana mai tsane tattausan sumar kansa da ƙaramin towel ɗin.

Gaban dreesin meeror'nsa ya tsaya, ya fara kimtsawa, cikin yanayin nitsuwarsa da rashin yin abu da
gaggawa...

Bayan ya gamane ya fito fes yana baza ƙamshi mai masifar daɗin shaƙa, sai wani irin kyalli sajensa keyi,
yayinda jajayen lips ɗinsa suke wani irin sheƙi tamkar dai irin yadda lips ɗin jarirai yake sheƙi in sun ɗan
laso lips ɗin.

Wata tattausar jallabiya blue color mai ɗan karen taushi da kyau ne, a jikinsa, tayi cib-cib da ɗan
madaidaicin jikinsa, sai kuma fararen takalma half cover masu taushi da ya zira tattausan sawayensa da
suke farare ƙal, yayinda dun-duniyar sawun nasa ke sarari.

Farin hirami ya naɗa a kansa, irin naɗin nan na zamani wanda matasan larabawa keyi,

Sai wayarshi daya zira a ajihun gaban jallabiyar tasa, wani irin sassayan ƙamshi mai ɗan karen daɗin
shaƙa yake zubawa,

Taku yakeyi cike da kamala, yayinda hannunsa na dama ke riƙe da jakar system nasa.

Cikin yanayinsa na nitsuwa ya ƙara so bakin kitchen ɗin.

Siraran Idanunsa ya ɗan jujjuya ya kalli tsakiyar gidan baki ɗaya, sai ya kuma ɗan leƙa cikin kitchen din,
nan ma babu alamun Innayi.

Cikin nitsuwa ya kuma juyowa ya nufi ɗakin nata, ganin takalmanta a bakin ƙofar.

“Assalamu alaikum”. Yayi sallama cikin wata iriyar sassayar muryar mai cike da haiba nitsuwa da kamala.

Sai kuma yayi saurin shigowa cikin ɗakin.

Ganin Innayi na kwance bisa sallaya babu ko pillown ga kuma karkarwa da jikinta keyi.
A hankali ya rusuna tare da takwara ƙafarsa ta dama ya zauna kanta ta hagu kuma ya tsaidata, cikin
kulawa da tarin so tausayi, ya motsa lips ɗinshi a hankali yace.

“Yah Salam.

Innayi! Innayi!! Innayi!!!”. Ya kirata sau uku, ganin bata amsa bane, yasashi manna tafin hannunsa kan
goshinta, wanda hakan ne yasata buɗe kwayar idanunta da sukayi ja.

Sai kuma ta medasu ta rufesu, sai ga wasu hawayen masu zafi sun kwaranyo mata.

Jiki na rawa tasa hannunta, ta kamo hannunsa, murya a raunace tace.

“Aliyu”. Da sauri ya zuba mata idanun tare da tsareta dasu, domin zai iya cewa, wannan shine karo na
biyu a rayuwarsa da yaji ta kirasa da asalin sunansa na yanka.

A hankali yace.

“Na'am Innayi meke damunki? Meyasa baki kirani kin gaya min baki da lfy ba? Tashi mu tafi asibiti”.

Ya ƙare mgnar yana mai tallabota ya zaunar da ita.

Wani dogon numfashi Innayin taja cikin rawan murya tace.

“Aliyu ka zauna, kaji abinda zan gaya maka”.

cikin yanayin kulawa a sanyaye yace.

“A'a muje asibiti tukuna, sai mun dawo”.

Cikin ɗan ɗaga murya tace.

“Aliyu ka bari kaji abinda baka saniba.

Bana son in mutu in barka a nahiyar maraici, bana son in mutu da abinda ni kaɗaice na sani kuma
nakeda dama da ikon sanar da kai, idan na mutu a haka ban sanar da kai abinda ke bibiye da muba, nayi
maka cuta mafi muni a rayuwarka.

Aliyu ka bari in sanar da kai abinda Allah ya nuna min a daren jiya”.

A hankali ya fesar da nannauyan numfashi, sai kuma ya juyo ya kalli ƙofar ɗakin, jiyo Muryar Amininsa
mafi ɗan uwa, wato M Jamil yanayin sallama, a hankali yace.

“Wa alaikassalam J”.

Ya ƙira Aminin nasa da sunan da duk duniya shi kadai ke kiransa da hakan,

Ido ya zubawa M Jamil ɗin a hankali tare dayi masa alamun ya shigo da kwayar idanunsa,

Cikin yanayin sauƙin kai sakin fuska faram-faram Jamil ya sako kansa cikin ɗakin yana mai cewa.
“Iya innare yau me kika dafa mana ne, dan tun jiya da na dawo ƙasar nan banci komai ba, nace sai
abincinki zanci ko na Ummina”.

Sai kuma yayi shiru tare da matsowa kusa da ita...

Cikin Masarautar Gembilan kuwa.

Wata Kekkyawar matace yar duma-duma mai kyan shiga da haiba, ke zaune bisa kujera, yayinda System
ke gabanta bisa ɗan madaidaicin stool yayinda fuskarta ke manne da wani ɗan farin glass siriri.

Da alamu typing takeyi.

Kai ta ɗan jinjina tare da juyowa ta kalli dinning area inda hayaniyar yaranta ke tashi.

Kai ta ɗan jinjina tare da kallon wata yar narkekkiyar matashiya da bazata wuce 14 year's ba.

Ido ta zuba mata ganin ta nufota da sauri.

Hannunta ɗaya.

Riƙe da school bag da takalmin sinika da kuma ɗan madaidacin hijabin Uniform ɗin ta.

Da sauri ta rusuna gaban Matar tare da juya mata baya tana cewa.

“Ayya Momy tubke min kaina, nayi-nayi yaƙi sai na ƙulleshi sai ya sule”.

Kwaffa tayi tare da cewa.

“To wai ke kam Khausar yaushe ne zaki iya, tubke gashin kanki”.

Ta ƙare mgnar tana tattaro suman Khausar din yana mai zamewa,

Sai kuma ta ɗago kanta ta kalli Ɗan matashin yaron da yanzu ya fito cikin Uniform ɗinsa. Wanda yake iri
ɗaya dana jikin wacce aka kira da Khausar.

Da alamun ya gama shirinsa tsab.

Cikin tsuke fuska ya watsawa Khausar din harara tare da cewa.

“Gsky ni zan tafi Ramadan Raudat zomu tafi, kullum ita ke jaza mana yin letting muje aita zanemu kamar
bayi.
Ni wlh da zan samu a rabamun hanya da ita inaso, muna shiga school kamar wasu shaidanu zakaji an
fara cewa.

FATTANAH kuka biyewa ko, duk sai an gama shiga aji kafin ku iso.”

Cikin yanayin tsiwa da son girma ta miƙe tsaye tana ɗaure ɗan kwalinta harara ta watsa mishi tare da
cewa.

“Wallahi ka shiga hankalinka dani Haydar in baka dena cemin FATTANAH ba zan fasa maka baki”.

Dogon tsaki yaja tare da juyawa ya nufi ƙofar falon, yana gyara zaman net ɗin sa. Tare da cewa.

“Sai ki gayawa wanda yasa miki sunan, ko kuma ki nitsu ki dena rashin kunya da rawan kai”.

Cikin ɗan ɗaga murya Momyn nasu tace.

“Gsky Babana bana son wannan sunan da aka liƙawa Mamana sam bafana son sunan”.

Da sauri yace.

“Toh Momy ai ita ta jawa kanta fitinenneyar ce ta gasken gaske, in dai kinji faɗa to da ita a ciki, in kuma
babu ita to zakiji ance ai gulma akayi ta maidawa maishi, wai ita ba'a gulma da ita, itafa tana iya zuwa
zuwa ta samu ana faɗa ta shiga tayi kane-kane sai an gama tace wai me dalilin faɗan”.

Ya ƙare mgnar yana fita.

Ita kuwa Khausar zama tayi gefen Momynsu tana sa takalmanta da ɗan sassarfa domin yau din ranace ta
musamman a wurinta tana cike da ɗokin zuwa makaranta kasancewar yau suka dawo hutu, kuma
hutune na canjaza aji da JSS zata tafi SS 1 wanda takega matakin samun encinta ne kenan zata taka,
tunda yanzu zata koma aji da matan aure, a islamiyar safe, sai kuma na bokone tacan anan ne babu enci
sai randa ta gama sa takalmin ta saka, tana sakin yelwataccen murmushi.

Yayinda Ramadan da Raudat suke tsaye gefenta.

Hannu tasa ta kama hannun Raudat tare da cewa.

“Mu tafi”.

Da sauri ta juyo ta kalli Momyn nasu tare da kwaɓe fuska jin tana cewa.

“Ku biya sashin Gimbiya Dadu ku gaidata, bata da lfy”.

Cikin kwaɓe fuska tace.

“Momy zamuyi letti muje wannan mai sunan baban naki ya samu damar sawa a azabtar dani”.

Ta ƙare mgnar cikin son zillewa zuwa sashin Gimbiya Duda, ita kuwa Momy tsuke fuska tayi tare da
cewa.
“Ku biya ku gaisheta da jiki nace ko”.

Cikin bin umarnin mahaifiyar tata badon tasowa tace.

“Toh Momy”.

Daga nan ta kada kan ƙannen nata Duk suka fito.

Sai kuma tayi sauri ta juyo tare da cewa.

“Momy mun tafi”.

Murmushi tayi sanin manufar ta yasa cikin lumshe idanu tace.

“Allah ya kaiku lfy ya baku Sa'a Allah yasa ki shiga SS 1 da ƙafar dama, Allah ya shirya min ku”.

Cike da jin daɗi tace.

“Amin Ya Allah”.

Kana suka fita.

Suna fitowa suka samu duk sauran yaran gidanma sun fito.

Kamar haɗin baki kab ɗin su sashin Gimbiya Dadu suka nufa.

Kai tsaye suka wuce har bedroom ɗin ta domin bata falon.

Su Asiya ce, a gaba ita da sauran ƙannenta, sai kuma su Khausar din.

Zaune suka sameta bisa tsakiyar gadon mulkinta, mai martaba Lamido Gembilan yana zaune ƙasa bisa
carpet, yana haɗa mata tea,

Cikin tarin biyayya, da sauri suka rusuna baki ɗayansu, kusa haɗa baki sukayi wurin cewa.

(“Allah saine Abba, noi nɓanɗu Dadu?) Allah ya faranta maka Abba ya jikin Dadu?”.

Cikin son ahlin nasa ya jinjina masu kai tare da cewa.

(“Yettore Allah nwodi dama) an godewa Allah da sauƙi”.

“Allah ntokkin dama”.

Suka faɗa a tare, cikin tankwashe sawunsa yace.


“Allah jabu”.

Amin suka faɗi baki ɗayansu,

Yayinda Khausar kuma taketa jan hijabinta, tana mai sunkuyar da kanta ƙasa,

Allah ya sani bata ƙaunar abinda zai kawo ta gaban Gimbiya Dadu,

Domin jikinta da nitsuwarta duk rasasu takeyi, sabida wani irin mayataccen kallo mai bada tsoro da
tsohuwar ke Binta dashi.

Kamar koda yaushe kuma hakane, duk da bata da lafiya, amman wani irin masifeffen kallo ta tsare
Khausar ɗin dashi har bata jin gaisuwar da jikokin nata keyi mata,

Cikin taɓe baki Asiya tace.

“Dadu wannan wanne irin kallo ne? muna gaidaki kinyi shiru?”.

Jin hakanne yasa Khausar ɗan ɗago kanta,

Ai kuwa ido cikin ido sukayi da Dadu.

Da sauri ta motsa lips ɗin ta a hankali tare da cewa.

“Innalillahi wa innailaihi raji'un”.

Sabida wani irin tashi da tsikar jikinta ya farayi, yam-yam.

Ita kuwa Dadu har lau bata cire idanunta a kantaba,

Haydar ne ya ɗan miƙa tsaye tare da kamo hannun Ramadan da Raudat yace.

“Dadu Allah ya sauwaƙa, zamu tafi school kada muyi letti Raudat muje”.

Abin mamaki har lau Dadu batama san anayi mata mgna ba, bare ta amsa musu, gaba ɗaya nitsuwarta
da kallonta yana kan Khausar....!

Lamido kuwa ido ya zubawa maifiyar tasa, cike da mamakin lamarinta, ya zama ana kallon kalo, ita tana
kallon Khausar data kasa koda ƙwaƙƙwaran motsi shi kuwa yana kallonta.

Asiya kuwa itama miƙeqa tayi tare da kaɗa kan ƙannenta tayi gaba Amina ce ƙanwar Asiya mai binta ta
ɗan miƙa tare da cewa,

“Uhum”. ta fice

Ya zama daga Dadu sai Lamido sai Khausar.


Cikin wani irin yanayi da Khausar din keji ta kuma kallon Dadu, wacce zuwa yanzu ta saki laɓen bakinta
na ƙasa, wani irin yawu mai cike da mayataccen kwaɗayi ne ya tsinko mata, har yana ɗan sauƙowa kan
lips ɗin ta.

Cikin sauri Khausar ta miƙe jin Lamido yana cewa.

“Mamana tashi ku tafi”.

Ai kafin ma ya rufe bakinsa, tuni ta fita tana mai cewa.

“Toh Abba”.

Ita kuwa Dadu wani nannauyan numfashin ta sauƙe tare da juyowa takalli ɗan nata, dake miƙa mata cup
ɗin tea.

Cikin diriricewa tace.

“A'a bana buƙatar abin zaƙi, a kawo min abu mai yaji-yaji”.

Cike da biyayya yace.

“Toh”.

Kana ya miƙe ya fita.

Tuni su Khausar kuwa sun shiga school bos ɗinsu,

Amina ce ƙanwar Asiya mai binta ta kalli Ramadan dake cewa.

“Kalli fa 8:13 na tabbatar yauma zamu zanu”.

Cikin sanyi tace.

“Mu dai Allah ya rufa mana asiri daga SS 2 akwai matan aure da yawa a ciki, so ba batun duka a side ɗin
mu.

Kuma ma duk bama saɓa doka cikin nitsuwa da tarbiyyar mu muke, ko nayi litting nasan za'ayi min uzuri.

Cike da jin daɗi, Khausar tace.

“Nima dai Allah ya yaye min masifa da cin zalin su Moddibo tunda yau dai zan tafi Ss 1 ɗin, da ba duka
ba zagi, wlh inci karena babu babbaka”.

Taɓe baki Haydar yayi tare da cewa.


“Mu gefen maza, babu manya, duk yarane, manyan da dare suke zuwa, shiyasa babu roggomi”.

Asiya ce ta kalli Khausar cikin yanayin son yarinyar tare da cewa.

“Ai wlh ke dai in baki nitsuwa ba ko jami'a kikaje in dai Moddibo na cikin malamanku, na tabbatar zai san
matakin da zai ɗauka a kanki.

Sannan ma da kike batun kin tafi Ss1 akwai matan aure, kin mance cewa, na safene, na islami.

Akwai na rana zuwa biyar bokone, kuma kuna tare da moddibo.”

Kwaffa tayi tare da cewa.

“Kai na shiga ukuna wlh”..

Anan gefen su Modibbo ku, fir innayi taki aje asibitin. Su kuna su kasa fahimtar ta, gani suke zafin
zazzaɓin maleria ne yake son sata surutai shiyasa suke hanata mgn sukayi ta mata addu'o'i hardai ta ɗan
fara samun nitsuwa har bacci ya ɗan sureta.

Gani ta ɗan rumtsane yasa suka tafi wurin Ummin M Jameel suka ɗauko Ummin dan tazo ta ɗan kula da
ita.

Suna isa bakin gate, ba tare da sun shigaba, Ummin ta kalli M Jamil da yayi saurin fitowa bayan yayi
parking marfin motar ya buɗe, mata cikin tsananin son mahaifiyar tasa, yace.

“Bismillah Ummi fito ki shiga wurin Innayinki, domin mu dai yau mun gaza gane kanta, da alamun Ita dai
dare ɗaya gigin tsufa ya sauƙo mata”.

Ɗan buge ƙeyarsa tayi tare da ciwa.

“Tsufa kan zai cimma taka uwar mafa, kawai dai inaga zafin zazzaɓine kusan wasu lokutan yanasa yara
surutai, to ita kuma girma yazo dole in ciwon yayi zafi zatayi kamar na yara”.

Juyowa tayi ta kalli Moddibo daya jingina kansa jikin kujerar gaban motar gefen mai zaman banza,

Cikin sanyin murya yace.

“Uhmmmm Ummi waifa cewa tai taga taurari suna sauƙowa ƙasa har kamar zasu taɓa rufin side nan,
anya kuwa Ummi wannan zazzaɓi ne?”.

Sai kuma ya ɗan fesar da numfashi tare da lumshe idanunsa cikin alamun nazari yace.

“Ina tsoron kada fa matsalar ƙwaƙwalwa ce, nayi nayi muje asibiti kuma taƙi.”
Ya dire mgn tare haɗa kan yatsun hannunsa.

Jamil ne yaci gaba da cewa.

“Saida fa Moddibo yayi ta mata tofi kafin muka samu tayi bacci har muka fito ɗin.”

Cikin kulawa Ummi tace.

“In sha Allah babu komai, bari in shiga, ku kuje”.

To Jamil yace kana ya shiga mota, ita kuma tayi cikin gidan.

A hankali ya miƙa dalleliyar motarsa ƙirar BMW kan shimfiɗeɗen titin,

Yana tafiyar hawainiya, murmushin yayi ganin kallon da Moddibo yake masa.

“Sanin yau za'a dawo makaranta ne, yasa nayi ƙoƙarin dawowa baro Marrocco, duk da akwai ayyukan da
ban gama dasu a company'nba,”.

Cewar M Jamil shi kuwa Moddibo kai ya jinjina alamun yana jinsa, shi kuwa M Jamil gudu ya ɗan ƙara
tare da ci gaba da mgn dan yasan ba lallai ne Moddibo ya amsa mishi da bakiba, inda sabo ya saba, kuma
shi yasan cewa body language al'adane ko ɗabi'a koma yace halittar Moddibo ne.

Juyowa yayi ya kalleshi tare da cewa.

“Na zaƙu muje makarantar nan, dan nasan zaiyi kyau sosai a tsarin gyarashi da akayi”.

Cikin ɗan ƙwaɓe fuska yace.

“In an gama gyaran ba”.

Da sauri M Jamil yace.

“Kamar yaya za'a gama mana”.

Juyowa yayi ya ɗan kalli M Jamil ta gefen ido kana a takaice yace.

“Toh ba'a gaman ba”.

Cikin sauri M Jamil yace.

“A.S da gaske ba'a gama ba?”.

A.S shine sunan da yake kiran Moddibo dashi kuma su biyu kaɗai suka san ma'anar sai kuma abokan
karatunsu.

Shi kuwa Modibbo littafin dake gaban motar ya ɗauka tare da buɗe wa kana yace.
“Dama tun lokacin da za'a bada hutun na faɗa bazai isa a gama gyaran school ɗin ba, musamman da ya
zama an ƙara yawan class, kana ga gina hall din da akace za'ayi, kuma dole aikin bazaiyi guduba sabida
Ramadan, tun lokacin nace a ƙara kwanakin hutun, sabida samun isasshen lokacin, wannan Ba fulatanin
yaƙi”.

Murmushin M Jamil yayi tare da cewa.

“Toh kai meyasa baka ƙara hutunba, ai da sai ka sanar”.

Juyowa yayi ya kalleshi bayan hannunsa yasa ya shafa tattausan sajensa tare da cewa.

“Uhmmmm”.

Ya san me wannan Uhmmm ɗin take nufi, kai ya jinjina tare da cewa, “Mu dai yan kallone,".

Da sauri yace.

“Nima haka, dan na gaji ko yaushe sai ya kwaɓa abu yazo yana cemin ina mafita”.

Dai-dai lokacin aka buɗe musu gate din makarantar, Ya Salam.

Wani irin tsarine da zubi makarantar yake dashi, tsari mai burgewa, yayinda shima makarantar Moddibo
ya ƙawatata da tsirrai na kyautata muhalli.

Tabbas gyara kam da saura ba'a gama shi ba.

Domin daga woje dai kam an kammala komai amman daga ciki, duk cikin ajujuwan a hargitse yake.

M Jamil nayin parking, wani kekkyawan dattijo bafulatani ya nufo matar tasu da sauri, bisa alamu dai
shine shugaban makarantar domin duk malaman na miƙa gaisuwar garesa cikin mutuntawa.

“Moddibo! Moddibo!! Moddibo!!!.”

Jamil ne ya fito yana murmushin tare da cewa.

“Allah rene,”.

Da sauri yace.

“Ina Moddibo”.

Cikin motar Jamil ya nuna masa, da sauri ya sunkuyo,

Yayinda shi kuwa Moddibo meda bayansa yayi ya jingina tare da lumshe idanunsa, murmushi Dattijon
yayi tare da cewa.

“Ga ɗalibai duk sun dawo makaranta ta cika maƙil ga sabbin ɗauka, kuma aiki baifi rabi ba, ya zamuyi?”.

Cikin taɓe baki yace.


“Allahu a'lamu!”.

Jamil ne ya juyo ya kalli Malam Ahmad da Malam Habibullah da suma fitowar su kenan daga can cikin
makarantar.

Shi kuwa Malam Arɗo Umaru mamallakin makarantar kuma .

Kai ya ɗan dafe tare da cewa.

“Dan Allah ka fito Moddibo kasan bayanin da zakayi musu, kana ka kara musu kwanakin hutun, tsawon
lokacin da kakega za'a iya gama gyaran”.

Yadda ya dire mgnar da karya wuyane yasa Moddibo fitowa.

Murmushin sauran malaman sukayi, domin sosai tsufa ya fara cimma Mala Arɗo, zuwa yanzu ya kamata
ragamar makarantar ya zama a hannun yara, domin badon Allah yasa Moddibo ke tsara komai na
jadawalin abubuwan ciki da wajen makarantar ba, da tuni ta durƙushe, to amman sabida shi da sauran
haziƙan malamai da suke da tsananin kula da tarbiyyar yara da sukeyi yasa har yau makarantar bata da
na biyu a faɗin birnin Gembila.

Kusan a tare suka rakaya cikin makarantar.

Yayinda hayanin ɗalibai manya da yara maza da mata, ke tashi.

Juyowa yayi ya kalli Jamil tare da cewa.

“J kaje masallaci kayi mgn duk mu su haɗu a tsohon halla ɗin mu na sama.”.

To Jamil yace yana tunanin to me zaice musu,

Masallacin ya wuce tare da yin sanarwan.

Nan take kuwa, duk ɗaliban suka haura sama, suka shiga cikin babban hall ɗin nasu wanda yake ƙato sai
dai duk da haka yanzu ya musu ƙaramin,.

A gafen mazama suma duk sun haɗu a halla nasu.

Shi kuwa Moddibo office nasa ya wuce.

Jim kaɗan ya fito, da Lapel Microphone a hannunsa yana saƙalasa a wuyan tattausan jallabiyar jikinsa
Malam Ahmad ne ya matso kusa dashi tare da cewa.
“Zamu jirane ko an ƙara mana hutu”.

Ɗan murmushin gefen baki yayi tare da cewa.

“Hutu kuwa sosai ma har na tsawon mako uku za'a ƙara”.

Cike da murmushi yace.

“Mu tafi kenan”.

Kai ya gyaɗa masa tare da cewa.

“Suma duk yanzu zan kaɗa kansu ko wacce tai gida sai dai muma muna da zama na musamman”.

Ai kuwa jin haka yasa duk malam suka zauna jiran.

Shi kuwa ya haura saman yana mgn da M Jamil a waya.

“Su maza basu da hayaniya, kawai J ka ɗanyi musu nasiha, kana kace sai bayan mako uku zasu dawo
kafin nan an gama gyara,

Sai dai masu zuwa hadda suci gaba da zuwa."

Cike da gamsuwa M Jamil yace to.

Kana sukayi sallama.

Dai-dai lokacin kuma su Khausar suka shiga cikin makarantar,

Da in ka gani kace a ƙasashen ƙetarene, domin makaranta ce mai zaman kanta, mai cike da haziƙan
malamai, duk da sunyi makarar mintuna 20, an bar motarsu ta shiga ne, sabida magiyar da sukayi tayi da
kuma girman gidan da suka fito, da bada uzurin motar ta ɗan lalacemusu a hanyane kana da kuma ganin
ma yau ba karatun za'ayi ba, hutun za'a kuma ruɓanyawa.

Suna shiga kuwa, ga mamaki su aka barsu suka shige ba hukuncin komai.

Kana ko wa ya nufi sashin da ajinsa yake.


Da sauri duk suka tsaya jin Malam Habibullah na cewa.

“Fattanah uwar yan letti yau makarar har ta 20 minute duk da yau aka dawo, duk kuyi sama ana taro a
hall”.

Cikin ɗan tura baki tace.

“Toh Malam”.

Yayinda tuni su Asiya kam sun haura har sun shiga hall ɗin.

Da ɗan sassarfa ta fara take steps ɗin da zai sasanta, da hall da yake a sama ganin ita kaɗai ta rage.

Daga corridor'n steps ɗin, ta ɗan lumshe idanu ta, tare da gyara saƙala school bag ɗinta a kafaɗar dama.

Sabida ƙamshin turarensa ya shaida mata, tabbas tuni ya shiga hall ɗin.

A hankali ta sauƙe numfashin ta tare, da nemo dukkan nitsuwarta.

Lokacin da ta gama haurowa, sama, da sauri ta tsaya, jikin window dake gab da bakin ƙofar shiga, ido ta
lumshe tare da buɗewa a hankali kana ta kutsa kai cikin hall din da a kalla mutane ciki sun kai ɗari da
hamsin, duk da tasan bai taɓa barinta, ta shiga ajiba, muddin ya rigata shiga, to amman kullum sai ta
gwada sa'anta musamman yau da yake a hall ne.

Taku ɗaya tayi ana biyu, ta tsaya, sabida, ganin ya ɗaga mata, tafin hannunsa.

Cikin yin mui-mui da bakinta tace.

“Afwan ya mu'allim sayyara...”.

Da sauri ta ɗan ja da baya ta koma jikin window ganin ya juya baya tare, da gyara ɗan masaƙalin Lapel
Microphone dayake saƙale a wuyan jallabiyar jikinsa, sabida tsananin sanyin sautin muryarsa yasa dole
sai dashi yake amfani a cikin class, domin ɗalibansa su samu damar jinsa sautinsa ras domin sam baya iya
kware muryarsa yayi mgna da ƙarfi haka Allah ya haliccesa da nitsestsiyar sauti to bare a irin taron maƙil
da hall ɗin yayi yau.

Cikin tattausar muryar sa mai cike da sanyi yace.

“Makfut?”. Cike da jin daɗin nasihar da yakeyi musu suka amsa da “Na'am”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Ɗeyib!”.
Sai kuma ya ɗan juyo ya fuskancesu, hakan ya zama, ya ɗan bawa Khausar baya, tattausan sumar
ƙeyansa dake kwance lib-lib ta zubawa harara.

Numfashi mai sanyi taja tare da shaƙa daddaɗan ƙamshin turarensa mai sawa ɗan adam salama.

Sai kuma tayi ƙasa da kwayar idanunta dugadigin sawunsa, ta zubawa idanu tana ganin yadda sukeyin ja
in ya taka sawun, in kuma ya ɗaga sai suyi fari, baki ta ɗan tura sama ta da liƙa ƙeyarshi wani sabon
hararan.

Shi kuwa Moddibo a hankali yake taku a gaban ɗaliban nasa, masu biyayya da girmamawa a garesa, cikin
tattausan lafazi yace.

“Falalar zikirai da karatun Alqur'ani , nakeso son in tunasar mana, sabida kididdigar manazarta, ta nuna
mana Al'ummar wannan ƙarnin sun samu naƙasun zikiri da karatun Alqur'ani mai girma, sun maida
hankali akan sashin yanar Gizo-gizo fiye da yadda ya kamata, mu maida hankali kan Al'ƙurani littafin
Allah da hadisan Manzon Allah, mu samman a wannan taki da muke ciki, na shuɗewar Ramadan wanda
zaka samu da yawa mutane sun fuskanci aikin al'khairai da bautar ubangiji a cikin watan, da zaran watan
ta gabata sai a koma gidan jiya aita sharholiyar duniya.”

Sai kuma yayi shiru, tare da fesar da numfashi a hankali, kana ya juyo a hankali yace.

“Mutane da yawa sun mance koma ince wasu basu san me Allah maɗaukakin sarki yace ba A cikin
Suratul Baqara, ayata 152.

Allah maɗaukakin sarki yace.


‫َأ‬
‫َفاْذُكُر وِني ْذُكْر ُكْم َواْش ُكُر وا ِلي َواَل َتْكُفُر وِن‬.

Ma'ana:

Ku ambaceni zan ambaceku, ku godemin kada ku butulcemin.”.

Ya ƙare mgnar da rumtse tafin hannunsa alamun ƙarfafa mgnar, wanda kuma wannan ɗabi'arsace ko ace
halittar sace.

Duk mgnar da yakeyi yana kamantata ko suffantata da tafukan hannunsa like dai yadda manyan
sarakuna keyin mgn turawa kuma suka cewa hakan body language, Wanda mafi akasari ɗabi'ar yan
jarida ne, in suna mgn.

Shiru hall ɗin yayi alamun suna fahimta sosai.

Shi kuwa Moddibo cikin girmama zancen Allah madaukakin sarki yaci gaba da cewa.

“A dai wannan ƙarni da muke ciki da yawa, suna butulcewa faɗin Allah madaukakin sarki, daga barin
ambatonsa, gaba ɗaya shagala tayiwa al'ummar mu ƙawanya, shafukan sada zumunta na yanar Gizo-gizo
ya maiye gurbin da yake muhallin Qura'ani ne a wurin wasu musul manmu, sai a wuni a kwana musulmi
bai ɗauki Qura'an ya karanta ya duba kyan baƙin da yake haɗawaba, amman sai ka sameshi awa 14 na
awannin 24 na rana yana rungume da wayarsa, ana charting, a Facebook a koma whatsApp, daga nan a
tafi Instagram, sai kuma a murgina a koma twitter sai kuma a rarrafawa zuwa wannan lalataccen kuma
kazamin dandalin Tiktok, ayi ta raye-raye da waƙe-waƙe, anaiwa juna cin zarafi, wasu su koma yiwa
malamai isgilanci ana yaɗa fasadi da fajirci ana meda ashariya kamar ruwan sha.”

Ya dire ayar mgnar tare da haɗe kan yatsun hannunsa gaba ɗayansu wuri ɗaya alamun ya dunƙule
mgnar kenan bawai ya gamata bane zai tafi sashi mafi muhimmanci ne.

A jikin window a waje kuwa, cikin jujjuya ido Khausar ta raɓa jikin window tare da maida hankalinta baki
daya cikin.

Shi kuwa Moddibo a hankali ya ɗan juyo gefen damansa, jin inda sautin surutu yake ɗan tashi kaɗan.

Ganin yana kallon sune kuwa yasa,

Samira Sani yin shiru.

Cikin nitsu ya kuma cewa.

“A wata ayar kuwa a cikin suratul Ahzab ayata 41, me Allah maɗaukakin sarki yace mana!???”.

Ya ƙare mgnar da alamun ayar tambaya, hakan na nufin su ja mishi baƙi yake so, sanin mafiya akasarinsu
yan haddansa ne,

Ji kakeyi, hall din sit kowacce tayi ƙasa da kai, gudun kada ya nuna ta kaɗan daga cikinsu kuma bawai
basu sani bane diricewa ne da kwarjininsa ke sasu yin ƙasa da kai.

Cikin sanyi yace.

“Na'am Samira Sani”. Da sauri tace.

“Malam ni?”. Fuskarsa ya tsuke tare da juyowa ya kalli Asma'u Ahmad dayi mata alama da hannu, tsilli-
tsilli tayi da idanu.

Samira Sani kuwa ganin ya cire ido a kanta ne yasa tayi saurin buɗe Qura'an ɗin ta.

Dan dubo ayar,

sai kuma duk suka ɗago kansu suka zuwa Khausar dake jikin window idanu,

jin ta uzi shaitan tare da yin basmalla kana taja numfashinta tare da lumshe idanu murya cike da tajwed
ta fara jan ayar.

Surah Al-Ahzab aya ta 41:


‫َيا َأُّيَها اَّلِذيَن آَمُنوا اْذُكُر وا الَّلَه ِذْكًر ا َكِثيًر ا‬

Murmushin mai cike da jin dadin Asma'u Ahmad tayi tare da sauƙe numfashin, FATTANAH ta ɗauki
belinsu kamar yadda aka saba, domin in dai batun jane na ƙwaƙwalwa to kwanyar Khausar ta
musamman ce.

Mata da yawa kuma cikin manyan mata kallonta sukeyi cike da sha'awa da jin daɗin zazzaƙar muryarta
na kuma ratsa musu kunnuwa.

Shi kuwa Moddibo ba tare da ya juyo ya kalle taba.

Ya fara kawo musu fassarar ayar.

“Allah madaukakin sarki yana cewa:

Yaku waɗanda suka yi imani, ku ambaci Allah ambato mai yawa.

Ammato kuma na haƙiƙa bawai kawai kije kiyi karatun Qura'an kara zube ko gatsa-gatsa ba, kuyi karatu
kwatankwacin yadda tayi inma kunce juyawa ih zuwa irin nawa da wuya.”

Cikin sanyi Asma'u Ahmad tace.

“Malam ai karatun Khausar irin nakane, ba banbanci kawai dai, ita muryar mata kai muryar maza muna
son mu koya irin ƙira'ar sosai.”

Kai ya ɗan juya ya ɗan basu baya tare cewa.

“In sha Allah zaku iya”.

Samira Sani kuwa, tattausar sajensa ta zubawa idanu cikin wani irin salo dake cikin jiki da zuciyarta.

Shi kuwa Moddibo a hankali ya kuma yin gyaran murya tare da cewa.

“A wata ayar kuwa cikin suratul A'araf aya ta 205. Allah maɗaukakin sarki na cewa...

Sai kuma yayi musu alamun suja ƙira'arar.

Cikin kauda kai Khausar ta lumshe idanu ganin wani irin masifeffen kallon daya watsa mata, wanda saida
taji hantar cikinta ta kaɗa.

Cike da dagiya a fagen neman ilinta dan bata wasa kuma bata barin tsoronsa ya hanata fahimta, cikin
nitsuwar da take samu in zatayi karatu tayi bismilla tare da fara jan ayar.

“Surah Al-Araf, aya ta 205:


‫َواْذُكر َّر َّبَك ِفي َنْفِس َك َتَضُّر ًعا َوِخيَفًة َوُدوَن اْلَج ْهِر ِمَن اْلَقْوِل ِباْلُغُدِّو َواآْل َصاِل َواَل َتُكن ِّمَن اْلَغاِفِليَن‬

Ta dire ayar da sauƙe nannauyan numfashi sabida tagib da taja, wanda dole ta ɗan riƙe numfashinta na
kusan second 32.

Samira kuwa, wani irin malolon bakin cikine, ya tokare mata maƙoshi, sabida masifar kishi da takaicin
yadda ko yaushe Khausar ke gaba dasu.

Asma'u kuwa sai murmushi takeyi,

Yayinda da yawa suke fatan Allah ya buɗa musu kwakwalensu kamar na Khausar.

Shi kuwa Moddibo a hankali ya fara fassara musu ayar.

“Abinda Allah madaukakin sarki yake cewa.

(Kuma ka ambaci Ubangijinka, a cikin zuciyarka, kana mai ƙanƙan da kai, da tsoro, ba da ɗaukaka murya
a, tsaka-tsaki tsakanin asirtawa da bayyanawa da safe da kuma maraici, kuma kada ka zamo cikin falaki,.

A wata ayar kuwa, Allah madaukakin sarki na cewa.

(Da masu ambaton Allah, maza, da masu ambaton sa mata, Allah ya tanadar musu gafara da lada mai
girma)”.

Sai ya kuma ɗan tsagaita wa tare da kallonsu yana cewa.

“Makfut?”.

“Na'am”. Suka amsa baki ɗaya,

“Ɗayyit”. Yace tare da kallon agogon hannunsa, ganin saura 9 minute lokacin da ya kamata ya sallamesu
yacika ne, yasashi ci gaba da cewa

“Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace:

(Misalin wanda yake ambaton Allah da wanda baya ambaton Ubangijinsa kamar misalin rayayya ne da
matacce.

A wani wurin kuma yace.

(Shin bana baku labarin mafi al'khairin ayyuka ba, kuma mafi tsarkinsu a wajen Sarkin da yake
mallakarku, kuma mafi ɗaukakarsu, ga darajojinku, kuma mafi al'khairi gareku daga ciyar da zinariya da
azurfa, kuma mafi al'khairi gareku daku haɗu da abokan gabanku ku riƙe dukkan wuyoyinsu kuna dukan
wuyoyin suba?)

Duba Sahihul Bukhari, tare da sharhinsa Fathul Bari (11/208) Muslim ya ruwaito da lafazin:

Misalin gidan da ake ambaton Allah a cikinsa da wanda ba'a ambaton Allah a cikinsa kamar misalin
rayayya ne da matacce, (1/539)

Sai Sahabbai Sukace ka bamu labari.

Sai yace musu.

(Ambaton Allah madaukaki sarki)

Kuma yace:

Allah madaukaki yana cewa:

(Ni ina tare da zaton bawana dani,

Kuma ina tare dashi idan ya ambaceni, cikin ransa, zan ambaceshi a cikin raina,

Idan kuma ya ambaceni a cikin jama'a zan ambaceshi a cikin jama'ar da ta fisu al'khairi, in ya kusanceni
taƙi ɗaya, zan kusancesa kamu guda, in ya kusanceni kamu guda, zan kusancesa tsawon gaɓa guda, in
yazo min yana tafiya zan zo masa ina gaggawa)”.

Sai kuma ya fesar da sassayan numfashi a hankali tare dasa tafin hannunsa ya shafa tattausan sajensa,
yana mai lumshe idanunsa alamun cikekkiyar nitsuwarsa buɗe idanun yayi a hankali tare da cewa.

Tirmizi (5/459). da Ibn Majah, (2/1245). duba Sahih Ibn Majah (2/316). da kuma Sahihul Tirmizi (3/139).
Bukhari (8/171). Da Muslim (4/2061) lafazin riwayar na Bukhari ne.

Cikin nitsuwa ya kuma juyowa ya fuskacesu, murya cike da kamala, da tashin lafazi yace....!

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma na dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi Gumbar Ukku
al'khairi, Dukansu garukan da gumbunan akan dubu uku uku ne sai gumbar Riɗi da uku khairi su dubu
biyar biyar ne ! Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace ta koma tamkar budurwa 7k, kana masin
Daɗi har Maɗigan mai masifar kyau da kwaranyo da ni'ina 5k

Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima
yanada abubuwa masu kyau haɗinsa 8k, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa
jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi duka a dubu uku-uku ne
ƙananan robobinfa, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi
sadidan, set dinsa dubu goma in kuma komai rabi-razi zan sa miki 5k ne butar sirri da dai sauransu...Se
kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce
mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya
zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma
shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin
Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai duba littafin (Garkuwa) sirrin hakan na tare da
Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma
Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta
rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi
number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan
Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci ga kuma account
no 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, kina iya tura kuɗinki kafin ma ke min mgn duk abinda
na irga akwaisu Available...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️
*SAKAYYAH*

Page 2

NA

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*FREE PAGE*

*LITTAFIN SAKAYYAH NA KUDINE, WANNAN FREE PAGE NE, ƳAR UWA KI BIYA KI KARANTA CIKIB AMINCI
BA HAƘƘIN WANI GABA GAREKI 1k ne kacal kuɗin littafin duk da yawa shi. 0661110170 GTBank AISHA
ALIYU GARKUWA, ta nan zaku biya, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. In kuma
baki da account ko matsalar Network ZAKI IYA SAYAN KATIN MTN sai ki copy number's ɗin katin ki turo
min ta WHATSAPP. 09097853276. Kada ki kirani in kin san ba kayan Ɗa'a kike soba. In dai littafine kiyi
min mgn a whatsapp ɗin.*

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun da zuƙatan mazajensu
Uwar gida,Amarya,Tsakar gida, kai har ma da tan kaɗen gida Shararru kuma ƙasaitattun magungunan
matan dans saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata daga hannun. *AYSHA
ALIYU GARKUWA* Garkuwar Ma'aurats ayau ma na dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu
kyau da inganci domin gyara kanki, ko ƙanwarki, ko ƴarki, ko a miniyarli, damake kanki ki zamto
tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin
maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Dukansu ƙananan robobin akan dubu uku
uku ne kacal Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, koriyar gumba, gumbar madara, Gumbar kolli mai kellin
al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, dukansu a kan dubu uku uku ne ƙananan
robobin, sai ta kwalli da ridi da Uku al'khairi da 3 in 1 su dubu biyar biyar ne. Masin Maliƙi mai masifar
ƙarfi da matse mace, ta dawo da sabon budurci shi ƴar mitsilar robar 7k ne kana ga masin Daɗi har
Maɗigan 5k ne kacal Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da
inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, 8k ne Zumar goron tula mai masifar kyau,
tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi,
su duka dubu uku uku ne, haɗin Cida kaza, kala biyu ne akwai na 18k shi yanada su tsumi da kwai da
rubutu, sai kuma ɗaya haɗin shi 13k ne Ciccibi Abodi, shi 19k ne Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, duk 3k ne
kana akwai maganin sanyi sadidan, wanda bani da haufi a kansu set ɗin 10k ne, rabinshi kuma 5k. Ko mai
ciki zata shashi baida matsala, infection ko na cikin mahaifane yana magninsa da uzin Allah. Sai su butar
sirri, audugar babbar mace, da dai sauransu...

Sai kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko
wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci
ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da
kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin
Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276.
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci idan kuna ga account no da zaku tura
kuɗinku ta ciki masu son kayan Ɗa'an 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min
shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

Cikin fesa sassayyan numfashi, Modibbo ya ci gaba da faɗin.

“Kuji falalar Allahu rabbil samawati garemu, ubangiji yana sonmu yana tausayin mu, yana kuma
jinkanmu."

Ya dire mgnar yana ɗan sauƙe wani numfashi dan Allah ya sani ya fara jin bakinshi ya gaji da mgna. Cikin
tattausan muryarsa yaci gaba da cewa.
Daga Abdullahi ibn Busr, Allah ya yarda dashi, yace:

(Ya ma'akin Allah! Shari'o'in Musulunci sunyi yawa a gareni, saboda haka ka nuna mini wani abu da
zanyi riƙon da shi.

Sai Manzon Allah (S.A.W) yace masa.

(Kar harshenka ya gushe yana ɗanye daga ambaton Allah.

Kuma mai tsira da amincin Allah yace:

(Wanda ya karanta harafi ɗaya daga littafin Allah yana da ladan kekkyawan aiki ɗaya, shi kuma
kekkyawan aiki ɗaya yana da ladan misalin goma.

Ba ina nufin Alif lam Mim harafi bane,

A'a. Alif harafi ne, Lam harafi ne, kana shima Mim harafi ne.”.

Wani irin mayataccen kallo Samira ke bin lips ɗin Moddibo dashi, tana mai kallon dukkan yadda yake
motsasu, da yadda tattausan sajensa ke zuba ƙyalli ƙawarta Ikilima Ibrahim ce ta ɗan taɓata da kafa
alamun wannan wanne irin kallo ne.

Yayinda gefen damansu kuwa, wata madaidaciyar macece, Hadiza Muhammad Yahaya, wacce take cikin
sabbin dalibai.

Kallon da Samira Sani keyiwa Moddibo ne ke bata mamaki.

Shi kuwa Moddibo a hankali yaci gaba da cewa.

Kuma daga Ukbatu Ibn Amir Allah ya yarda dashi yace:

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.

Ya fito alhalin muna cikin rumfa sai yace:

(Wannene daga cikinku zai so ya fita kullum da safe zuwa ƙoramar Buɗhan ko Aƙiƙ ya dawo da taguwa
biyu masu manyan tozuna ba tare da yayi wani laifi ba ko yanke zumunta ba?

Mukace masa muna son haka.

Yace:

(Ɗayanku yaje Masallaci ya nemi sani, ko ko ya karanta ayoyi biyu daga cikin littafin Allah, mabuwayi mai
ɗaukana, yafi masa taguwa uku ayoyi huɗu sun fi masa taguwa huɗu da kwatankwacin adadinsu na
raƙuma.)
Kunga ashe muna ɓarar da damarmakinmu riƙe da waya ba tare da mun samu mun ribaci ilimin da
iyayenmu da malanmu suka bamu ba.

Kuma mai tsira da Amincin Allah yace:

(Wanda ya zauna a wani waje, bai ambaci Allah a wajenba, wannan zai zamanto masa abin bibiya a
wajen Allah, wanda ya kwanta a makwanci bai ambaci Allah a wajenba shima zai zamanto masa abin
bibiya a wajen ALLAH.

Kuma mai tsira da amincin Allah yace:

(Babu wasu mutane da zasu zauna a majalisi da basu ambaci Allah a cikinsa ba, kuma basu yi salati ga
annabinsu ba, face ya zamo musu abin bibiya, in Allah yaso yayi musu azaba, in yaso kuma sai ya gafarta
musu.”

Jujjuya idanunsa yayi fuskarsa cike da shauƙin son Mahaikin Allah Muhammadu Rasulullah, da
sahabbansa,

Wani irin sassayan numfashi ya fesar tare da lumshe idanunsa, wanda yakan shiga wannan yanayi a duk
lokacin da yakeyiwa ɗalibansa nuni da al'khairan dake cikin ammaton Allah da bin sunnar manzonmu
abinkoyinmu abinsonmu da sahabbansa masu daraja.

Ita kuwa Khausar ƙasa tai da idanunta.

Sai kuma ta ɗan ɗago ta kalleshi jin tattausar muryarsa yaci gaba da cewa.

“Kuma mai tsira da amincin Allah yace:

Babu wasu mutane da zasu tashi daga wani majalisi da basu ambaci Allah a cikinsa ba, face sun zama
kamar sun tashi daga kan *mushen jaki ne* kuma zai zamanto musu abin dana sani)”....

Ya ƙare mgnar da haɗe kan yatsunsa duka, kana sai ya buɗasu a tare da ware tafin hannunsa kamar ya
sake abu,

alamun ya dasa babbab ɗamba, ya gama da wannan yankin.

Gaba ɗaya hankalinsu tunaninsu duk yana kansa, domin suna matuƙar jin dadin yadda wasu lokutan idan
ya shiga aji yake tunasar dasu mahimman abubuwan da suka cancanci musulmi ya lizamcesu.

Yayinda wasu kuwa da sam baya shiga ajujuwansu cike da son salon sa suke sauraronsa, kasan cewar
makarantar nada yalwar malamai kuma shi aiyuka sun mai yawa shisa ba dukkan class da suke dashi
yake shigaba.
Shi kuwa Moddibo cikin alamun gajiya da yawan motsa lips nasa da yayi yaci gaba da cewa a gaggauce.

“Mu farka mu ribaci wannan shekarar dukanta kada muce dan wannan wata na Ramadan daya shuɗe,
zamu bar wasu ayyukan ibada, mu jure mu zamo dasu ɗabi'armu a kullum domin shi ubangiji ka
gafartawa bayinsa, a duk sanda yaso ya ainta wasu daga azaba zuwa rahmarsa madaumiya, mu wasar
da wayoyin nan mu ruggumi Alqur'ani mai girma da tasbihai ya zama dai ita wayar nan sai time to time
zamu riƙe ya ke mai karatu dake nake."

Ya faɗi hakan yana nuna gefensu Samira dake buɗe da littafi a gabansu.

Sai kuma ya ɗan gyara saƙale Lapel Microphone din a wuyar jallabiyar jikinsa dan yaji muryarsa tana ƙasa
sosai alum yadan zame kaɗan, da ɗan sauri yace.

“Zaku iya duba Muslim (1/554) Abu Dawud (4/264) da waninsa duba Sahihul Jam'i, (5/342). Tirmizi duba
Sahihul Tirmizi (3/140) Abu Dawud (4/264) da Ahmad (2/389) duba Sahihul Jami (5/176) Allah shine mafi
sani... Abinda nace dai-dai Allah ya haɗamu a mizanin ladan abinda nai kuskure Allah ya gafartamin.”

Ya rufe mgnar da addu'a tare da juyawa ya fita.

Sukuwa gaba ɗaya numfashi suka sassauƙe, yana fitowa Malam Jamil na isowa wurin, dan shi zai shiga ya
shaida musu kwanakin da aka ƙara.

Kai Modibbo ya kauda gefe, jin Aminin nashi na cewa.

“Fattanah maza yi gudu ki shiga aji kada in rigagi, shiga, dan in na rigaki nima yau gadin aji zansa kiyi
mana”.

Da sauri Khausar din ta juyo tare da kallon shi cikin alamun yanai musu barkwanci tace.

“Malam ko ta window ma zan shiga”.

Murmushin yayi tare da cewa.

“Har yanzu baki girmi shiga ta window ba FATTANAH”.

Da sauri tace.

“Toh ai banyi jikiba, ka gani”.

Kawai sai ta kama jikin window alamun zata zauna ta wajen sai ta juya ta ciki.

Cikin yamutsa fuska Moddibo yace.


“Ke bar nan,”.

Ai da sauri ta diro tare, da nufar ƙofa, tana tura baki.

Shi kuwa Malam Jamil cikin tsananin son yarinyar sabida ƙwazonta da jan da kwanyarta keyi kana da
ƙawancenta da ƙanwarsa Asma'u Ahmad ya bita da ido.

Rungume Moddibo yayi tare da yin mgn murya can ƙasa.

“Tuba mukeyi Moddibo ai mana tsawan a hankali ka mance baka cire Lapel Microphone ɗinba, har nima
tsawar ta razanani”.

Wani irin nannauyan numfashin Moddibo ya sauƙe tare lumshe idanunsa.

Shi kuwa M Jamil murmushin yayi kana kuma ya sake shi yace.

“Lokaci na tafiya sai na fito na sallami maza kam”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da sauƙa ƙasa.

Goma dai-dai aka tashi islamiyan gaba ɗaya duk ɗaliban suka koma gida bayan M Jamil ya musu bayanin
dalilin ƙarin hutun, wanda kuma suma sunga hakan.

Ƙarfe ɗaya dai-dai suka tashi daga taron tattaunawa da malaman nasu baki ɗaya.

Bayan sunyi sallan azahar ne, kana duk suka tafi, ma'aikata sukaci gaba da aikinsu.

A gidansu Khausar kuwa.

Khausar ce kwance bisa 3 str daga ita sai yar doguwar rigar material mai taushi a jikinta, Pink collor, sai
hular sanyi data sa a kanta, yayinda himilin gashinta yayi tub-tub a ciki.

Da alamun bacci take sonyi.

Cikin sanyi ta buɗe ido ta tare da juyowa ta kalli Momynta dake fitowa daga kitchen ɗinta, hannunta riƙe
da plate da yankakkun fruits a ciki masu sanyi, gefen ta ta zauna bisa 1 str ta ɗaura plate ɗin kan
cinyarta tare kallon Khausar ɗin data miƙa mata hannu alamun ta bata.

“Tashi kije ki ɗebo Uniform ɗin ku, nasan yanzu ya bushe kizo ki goge muku kafin a kira magriba”.
Numfashi mai ɗan sanyi Khausar ɗin ta fesar tare da miƙewa zaune, ita kuwa Momy tafin sawun ɗiyar
Tata take kallo cike da ganin kamannin sawunta dana ahlinta.

Hannu tasa ta ɗauki inabi guda uku. Kana ta miƙe tsaye tare da juyawa ta fita.

Ita kuwa Momy da idanu ta rakata.

Tana fita a barandar ta tsaya tare da ɗan sa hannunta na dama ta riƙe ƙugunta.

Amina ce ta fito daga side din Gimbiya Bunayya, mahaifiyarsu kenan, uwar gidan Lamido,

Wacce daga itana sai Maman su Khausar wacce itace amaryarsa.

Wani irin kallo Amina tayiwa Khausar tare da cewa.

“Hamshaƙiya, cin abu a tsaye ba koyarwar musulunci bane”.

Fuska Khausar ɗin ta ɗan yamutsa tare da cewa.

“Ngd”. Sai kuma ta miƙawa Aminu ƙanin Amina wanda yake gefenta.

Da sauri Amina ta kwaɓe hannun yaron da bazai gaza shekara goma sha ɗaya ba tare da cewa.

“Makwaɗaicin baza, in zakaci akwai a fridge kaje a baka”.

Ido Khausar ɗin ta zuba mata, sai kuma ta sauƙe numfashi dan batayi mmkin hakanba, cikin alamun
kasalan da baccin da takeji ya sakar mata, ta nufi wurin shanyan nasu, a hankali take tafiya, dan ganin
shanyan nasu yana can har bayan Part ɗin Hajia Bunayya Umma.

“Wannan daga gani ma aikin Ramadan ne, shine zai zo yayi mana shanya har nan, zaice waɗan can
igiyoyin tsawonsa bazai kaiba”.

Ta ƙare mgnar tana nufar can.

A hankali ta fara janye shanyan, har ta isa dai-dai window Hajia Bunayya, cikin mamaki ta ɗan tsaya jin
yadda Umman ke mgn da faɗa-faɗa.

“Kada in damufa kake cewa.

Kasan kuwa irin tashin hankali da nake ciki duk sanda na buɗi idanuna na kalli Haiydar a matsayin ɗan
Lamido Yariman Gembila kuwa, ko ka mance shine ɗan sa na miji babba, shin baka ganin iyakata da
mulki sai dai gani sai hange tunda shine ɗa babba akan Aminu na.

Kai bakaga yadda komai zai juye min ba a gaba, ina gani sarauta zata koma ɗakin Aysha ƴaƴanta ne zasu
mulki masarautarmun”.
Sai kuma tayi shiru alamun tana sauraron abin da ake cewa a ɗaya sashin.

Ita kuwa Khausar cike da tsoron halin irin na Umma, gashi dai abinda taji, amman koda zata kwana
gayawa mahaifiyarsu bazata taɓa yardaba, domin Umma bata taɓa nuna kishinta a kanta, shiyasa ta
ɗauki dukkan yarda ta bata.

Cikin tsananin tsoro Khausar ɗin ta zaro ido ta tare dasa tafin hannunta ta dafe ƙahon zuciyarta, jin Hajia
Bunayya na cewa.

“Wallahi tallahi billahil azeem zanyi komai dan ganin bayan Aysha da yaranta, zanyi duk abinda ya kama
domin in kauda Haiydar a matsayin yarima mai jiran gado, dan wlh Allah zan iya kasheshi kowama ya
huta!...”.

Cikin tsananin kaɗuwa Khausar ta juya da sassarfa ta koma sade ɗin Maminta, tana isa kawai sai ta
watsar da kayan bisa kujera.

Da sauri ta kamo hannun mahaifiyar tata tare da cewa.

“Momy! Momy dan Allah ki biyoni zo kiji wani abu”.

Ta ƙare mgnar a matuƙar kiɗime, wanda hakan yasa dole Hajia Aysha ta bita a baya.

Ita kuwa da sauri take jenta, har zuwa bayan window Hajia Bunayya.

Cirko-cirko suka tsaya,

Ita kam Khausar cike da firfito da ido waje take sauraron abinda Hajia Bunayya ke faɗi.

Momy kuwa wani irin...!

A hankali M Jamil yayi parking a bakin gate ɗin gidansu Moddibo juyowa yayi ya kalli Moddibo dake
gefensa yana lallatsa system nasa.

“Toh wazai fita ya buɗe mana gate ne kam?”.


Ba tare da ya ɗago ya kalleshiba ya ɗaga kafaɗarsa ɗaya tare buɗe tafin hannunsa alamun

Oho.

Kai M Jamil ya jujjuya tare da cewa,

“To bari ni buɗe”.

Kai ya kuma gyaɗa masa alamun.

“Toh”.

Murmushin M Jamil yayi tare da fita ya buɗe gate ɗin, kana ya dawo yaja motar suka shiga ciki.

Parking yayi kana suka fito suka nufi cikin gidan,

Kai tsaye sashin Innayin suka wuce.

Wani irin yalwataccen murmushin M Jamil yayi tare dayin saurin ya haura kan barandar zama yayi daɓas
bisa tattausan carpert ɗin dake shimfiɗe a barandar.

Innayi na kwance yayinda Ummin Jamil kuwa ke gefenta tana ɓare mata banana.

Itama yalwataccen murmushin tayi tare da miƙawa Moddibo ayaban data ɓaren.

Amsa yayi tare da juyowa ya ɗan kalli M Jamil da ya zame ya kwanta bisa carpet ɗin tare da ɗaura kansa
bisa cinyarta, cike da so, ƙauna, shaƙuwa, tausayawa, yace.

“Ummina kin san irin farin cikin da nakeji a raina kuwa in na ganki?”.

Murmushin kawai tayi dan ita bazata iya cewa komaiba a gaban Innayi sabida Jamil shine ɗan ta na fari,
kuma su nan Gembila sashine na cikakkun Fulani.

Kawai dai abinda ta sani a baɗini tasan ta fishi farin ciki.

Shi kuwa Moddibo gefen Innayi dake kwance da alamun har yanzu nitsuwarta bai ida dawowa jikintaba,
hannunta ya riƙe tare da kallon M Jamil.

“Kai dan Allah ɗagata kada ka karya mana cinyarta da katon kankan nan”.

Ya ƙare mgnar yana gutsuran banana.


Shi kuwa Jamil da sauri ya tashi zaune jin Umminshi na ture kanshi tana cewa.

“Ai kam gskyarka Moddibo”.

Tashin nasa ne, yasa ta miƙe ta nufi kitchen, trayn data shirya kulolin abincinsu ta kawo musu.

Ta ajiye a tsakiyar su,

Shi kuwa Modibbo a hankali ya kamo hannun Innayin tare da tallabota alamun so yake ya ganta a zaune.

Sai kuma duk suka kalli Innayi data buɗe kwayar idanunta jin yana tallabota.

Zaunar da ita yayi cikin kulawa yace.

“Yanzu me yake miki ciwo?”.

Cikin sanyi tace.

“Nima kaina ban saniba, kawai dai zuciyata ke a tsinke tsoro nakeji Moddibo”.

Da sauri Jamil yace.

“Toh Innayi tsoron me kuma kikeji?”.

Cikin sanyi tace.

“Tsoron kada mutuwa tai mini zuwan ba zata”.

Wani irin masifeffen tsinkewan zuciya ne ya riski Moddibo jin Jamil ya ɗan yi yar dariya tare da cewa.

“Kada ki damu Innayi ki dena jin tsoron mutuwa, domin ita wajibinmu ne ita.

Kuma tsufa ba shine hanyar mutuwaba, ba abin mamaki bane ki rayu ni nan Jamilu in mutu in barki, in
bar Ummina da rashina, in bar Aminina Moddibo da rashin Aboki kamata, tabbas a al'amarin ubangiji
zan mutu in barku a raye da kuma ƙunar rashina”.

Da sauri Moddibo yace.

“Yah Salam wai kai J meyasa ne wasu lokutan kalamanka a baibaisuke? Dan Allah kasan abinda zakana
cewa”.

Murmushin mai sauti Jamil yayi tare da cewa.

“Zanfa mutu kam, dole zan mutu to kai dama a gani kake a haka zamu tabbata ne?”.

Da hannu Moddibo ya nuna masa Umminsa da haka kawai taji wasu irin zafafan hawaye sun zubo mata.

Da sauri Jamil yasa tafin hannunsa ya sharce mata hawayen tare da cewa.
“Kada kiyimin kuka kodama na mutu kada ki damu Ummina kinga aminina Aliyu ko to shi zai zame miki
madadina”.

Da sauri tayi mishi dakuwa.

Sai kuma yayi dariya mai sauti tare dace.

“Oh su Ummi ana son ɗan fari wato irin bakya son Jamilunki ya mutun nan ko”. Ya ƙare mgnar cikin
tsigar wasa kamar dai kakarsa ce,

Hakanne yasasu yin murmushin ganin zata kai mishi duka ya ɗan zille yana cewa.

“Haka kawai wai kunya wai ni ɗan fari bazakice kina sonaba, toh ni kam ina sonki ina sonki ina sonki
Ummina”.

Ƙeyarsa ta ɗan buge, kana ta tura musu plate ɗin dake cike da fruits sai kuma ta mimmiƙa musu fork,

Innayi kuma yar wannan hirar da sukayi yasa ta ɗan sake kaɗan, duk da har yanzu in ta rufe idanunta
tana ganin abinda Allah ya nuna mata daren jiya.

Jamil ne ya kalli Innayin tare da cewa.

“Dr Jamila tazo ta dubaki ko, dan da safe kafin mu wuce makaranta na kirata tazo”.

Kai Ummi ta gyaɗa alamun eh tazo.

Frutis ɗin kawai suka ci kana suka miƙe suka nufu part ɗin Moddibo.

Suna shiga falon,

Cikin sanyi Jamil ya zauna bisa kujera tare da riƙo yatsar Moddibo manuniya, cikin wata iriyar sassayar
muryar yace.

“Moddibo kasan ina jin farin ciki na musamman in naga Ummina ko?”.

Sunkuyar da kai Moddibo yayi tare da zuwa aminin nasa idanu cikin sanyi yace.

“J nasani! Na sani dan farin cikin baya ɓuya a fuskarka”.

Cikin Muryar da tafi ta ɗazu rauni ido na ciko da hawaye yace.


“Amman kuma fa farin cikina raggene, duk daɗin da nakeji in na tuna cewa Ummina ba a gidan Dadyna
takeba, inajin ciwo mai yawa a raina, inajin takaicin Kasan cewar mahaifiyata bata gidan mahaifina tana
can a wani gidan.

Bayan ita tasha wahalar zama dashi cikin talauci, saida yayi kuɗi dai-dai sanda zataji dadin rayuwa ya
saketa, gashi yan uwanta ba masu haliba, mijin da Allah ya ƙaddara ta aura shima rayuwar ba daɗi
sabida baida ƙarfi”.

A hankali Moddibo ya zauna kusa dashi cikin ƙarfafa mishi guiwa yace.

“J wanne dadine na kuɗi ya rage wanda bakayiwa Ummi ka tunafa, duk abinda kace kanaso Daddy yana
baka, duk kuɗin da zaka nema zai baka, a haka har Makka ka kai Ummi yaranta ka sasu a makaranta mai
kyau sanadin su kaƙi kayi aiki a ko ina kace zakayi karantarwa a makarantarsu dan ka tayata basu
tarbiyya. Kana kuma yi tunda gashi yanzu sun kusa gamawa, tunda ko Asma'u nanda shekara uku dai
zasu gama, secondary School, kace kuma suna gamawa zaka aurar da Asma'u kana ka ɗauki nauyin
karatunta, ta na gaba tana gidan mijinta, shi kuwa Bashir na mijine kuma kace in ya gama so kake ya
samu jami'atul Madina, in ya tafi can sannan kayi aure kace kuma kana aure zaka ɗauke Ummi da ita da
mijinta Malam Ahmad zaka riƙe su, Jamil to meya rage na jin daɗi da baka samawa Ummi ba, ka gyara
mata gidan da take, ka gyara mata ɗakinta”.

Wani murmushin mai sanyi yayi tare da cewa.

“To wai Moddibo da kake cewa haka, rainafa mallakin ubangijine a duk sanda yaga dama zai ɗaukeni
daga wannan duniyar, ko ban gama cikace burukana ba, in babuni a raye wa zai maiye musu gurbina?”.

Cikin tsuke fuska Moddibo yace.

“To dama wa yake da tabbacin rayuwa, yanzu ni in dai naci zan lizanci irin tunaninka Innayi fa bata da
kowa a duniya saini.

J ni zaka gayawa mutuwa? Ni Aliyu zaka gayawa mutuwa?”.

Sai kuma duk sukayi shiru suka zubawa juna ido.

Numfashi mai nauyi Moddibo ya fesar kana a hankali yace.

“J ka kalleni mana! In zame maka madubi, gwara kaifa,

kasan su Ummi kana ganin ta gafa Daddy”.

Da sauri M Jamil ya ri ƙa gyaɗa mishi kai tare da tuno maraicin aminin nasa.

Shi bai san iyayensu ba ranar da mahaifisa ya rasu, firgicin abin ne ya tadawa mahaifiyarsa naƙudansa,
ta haifeshi kana itama tabi bayansa kamar yadda Innayi ke basu labari.
Da sauri M Jamil ya kalleshi jin yana mgn a hankali.

“Ba uwa ba uba ba wa ba ƙani ko ƙanwa ba Baffa ba kawu ba goggo ba Yafendo, yanzu ashe bazaka dubi
maraicina ba, sai kai ka godewa Allah ba J kaga ni kuwa idan na tuna duk rashin da nayi in naji ƙunci da
ciwo sai in tuna.

Allah ya azurtani da rayuwa da lafiya kana yayi min ni'imar kasan cewa Musulmi, ya bani hankali ya ƙara
min da haddar izu settin, da littattafai masu tarin yawa wanda masu iyaye da dama basu samuba, ya bani
sa'a a dukkan karatuna mukayi digire har master's har zuwa P.H.D a makaranta mafi daraja a duniya
Jami'atul Madina, kana muka samu gurɓin aiki kuma a can.

Wanda ko yau muka koma can da aikinmu a hannu, amman kai ga uzurin daya tsareka, nima kuma da
uzurin daya tsareni”.

Da sauri M Jamil yace.

“Astagfurullah! Astagfurullah!! Astagfurullah!!! Alhamdulillah aboki na gari rahama ne, ai kam ni ga


uzurin daya tsareni to amman kaifa Moddibo uzurin menene ya tsareka duk da bana son mu rabu
Amman zaso kaje can kayi aikinka da al'bashinka mai daraja”.

Kai Moddibo ya kauda tare da cewa.

“Uzurina ai a fili yake J Innayi na tana son kulawata”.

Da sauri M Jamil yace.

“Ba gsky bane Moddibo karo na forko kenan a rayuwarmu daka ɓoye min abinda ke ranka kaƙi ka gaya
min me dalilin ka na zama a ƙasar nan bayan saudia na buƙatar ka, kuma harda daman zama da
iyalanmu fa muke dashi a can”.

Kai ya jujjuya tare da cewa.

“J yaushe na zama makaryacin da har mgnata bazata samu karɓuwa a wurinka ba?”.

Da sauri M Jamil yace.

“No wlh ni mai shaidar ka ne har gaban abadan kai ba makaryaci bane, kawai dai ban gamsu da hujjar
bane”.

Kanshi ya jujjuya kana ya nufi bedroom ɗinsa,

Shi kuwa M Jamil ɗayan ya shiga.

A can cikin masarautar Gembila kuwa,


Cike da kaɗuwa Khausar ta...

Ta juyo ta kalli mahaifiyarta sabida jin kalaman da Hajia Bunayya ke faɗi.

“Eh Sulaiman a kawo min mashin ɗin lipan mai kyau wanda zaiyi dai-dai da Haiydar,

A kawo fari dan yafi son komai nasa fari”.

Sai kuma ta ɗan yi jim, alamun tana sauraran abinda ake faɗi a ɗaya sashi,

dariya mai cike da sakewar zuciya tayi tare da cewa.

“Ai kaima kasan shi na musamman ne, Yarima ne fa, mai jiran gado, kuma gashi sunan Babanmu gareshi,
in banji dashi ba da waye zanji”.

Ita kam Khausar cike da mmki take kallon yadda mahaifiyar ke sakin wani murmushi mai cike da yarda da
jin daɗin kawaici da ihsanin uwar gidan tata,

Yayinda ita kuwa Khausar take kallon abun da idanun basira, tana tuna kalaman da taji ɗazu da wanda
Umman keyi a yanzu, a sanyaye tace.

“Marching kuma?”.

Daga ciki kuwa sai suka tsinkayo muryar Asiya na cewa.

“Ehye Haiydar ɗan gatan Umma da Lamido, yaron nan kunaji dashi,”.

Murmushin mai cike da manufa tayi tare da kallon inuwar Khausar da Mami ta jikin window nata, cikin
ɗan daga sauti tace.

“Kema ai ɗan lelenki ne,”.

Miƙewa tsaye Asiya tayi tare da cewa.

“Yauwa dan Allah Umma ni zanyi masa albishir”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Amman ba yauba sai marching ɗin ya iso”.

Numfashi mai sanyi Momy ta fesar tare da kamo hannun Khausar suka juya suka tafi.
Ganin tafiyar sune yasa Hajia Bunayya yin kwaffa tare da cewa.

“Uhum zanyi mgnin kine, shegiyar yarinya mai masifar wayon tsiya da sa ido, tama fi mahaifiyar tata
wayo da fahimtar manufar mutum”.

Su kuwa, suna shiga falon Khausar ta juyo a hankali tace.

“Dan Allah Momy kada ku bari Haiydar yaja marching yayi ƙarami dudu du fa shekarunsa sha 13 ne
kawai dan yanada saurin girma”.

Da sauri ta juyo ta kalli Haiydar da yanzu shigowarsa, kanshi ya nuna da yatsarsa manuniya tare da cewa.

“Ni ne ma yaron? To da shekaru nawa kika fini dabino uwar tsufa, ba shekara ɗaya rak kike bani”.

Yes tabbas kam shekarunsa 13 ne, amman in ka ganshi zakayi zaton yaje 16, domin yanada girman jiki,
kuma irin masu wayo da halin girman nanne shiyasa sam bazaka tantance shekarunsa ba, ya fita jiki da
tsawo sosai.

Dan in ka gansu zakayi zaton shine babban irin ya bata shekara ukun nannan ne”.

Kai ta jujjuya tare da rumtse tafin hannunta, kana cikin sanyi tace.

“Dan Allah Momy kada ki bari dan Allah a wannan karon dai ki yarda dani”.

Kai Hajia Aysha ta gyaɗa mata tare da cewa.

“Zan duba."

Cikin kwaɓe fuska Haiydar ya turo baki gaba tare da cewa.

“Plesse Momy kada kibi ta kan mgnar ta”.

Still kai ta gyaɗa masa shima tare da cewa.

“Toh zan duba”.

Cirko-cirko sukayi a gabanta.

Dan dama da haka take yanke musu taƙaddama.

Idanu ta ɗan lumshe jin an kira sallan magrib cikin fesar da sassayan numfashi tace.

“Lokacin salla yayi, maza muje muyi salla”.

Ba musu duk suka juya, shi Haiydar waje ya fita yana cewa.

“Ramadan zomu tafi masallaci”.


Ita kuwa Khausar ɗakinsu ta nufa tana cewa.

“Raudat zomuje muyi salla."

Da sauri kuwa sukabi bayansu.

A can gidansu Moddibo kuwa,

M Jamil ne, ya kalli dun-duniyar sawun Moddibo lokacin da suka fito kan barandar da alamun al'wala
sukayi.

A hankali yake taku cikin nitsuwa, yayinda yake motsa laɓɓan bakinsa yana taibihi.

Sai kuma ya maida kallonsa kan sumar ƙeyarsa dake kwance lip-lip tayi irin naɗin nan mai kamar
taburma.

Kusan a tare suka sauƙo,

Hango Ummi da Innayi zaune bisa sallayunsu, da kaskon rushi a tsakiyar su ne, ya sasu juyawa suka nufi
waje, sabida tafiya masallaci.

A hankali Moddibo ya zira tafukan hannunsa cikin aljuhun jallabiyar jikinsa, sabida wani irin masifeffen
sanyi dake fesowa, duk da rigunan sanyin da suka ɗaura kan jallabiyoyin bai tsare musu sanyi irin na
garin Gembila ba, musamman ma, a lokacin da magrib ta ƙarato, wanda lokacin sanire ke sauƙa.

Kasan cewar masallaci babu nisa da gidan ne, yasa suka, tafi da sawu.

A hankali M Jamil ya lumshe idanunsa sabida yadda yake jiyo sautin muryar Moddibo can ƙasa yana
zikirin tafiya masallaci.

Shi kuwa Moddibo cikin yanayin sanyin da yakeji yake motsa laɓɓan sa a hankali cikin dadɗan sauti can
ƙasa-ƙasa yake cewa.

‫ َو ِمْن‬،‫ َوِمْن ََفْوِقي ُنورًا‬،‫ َوِفي َبَصِرِي ُنوًر ا‬،‫ َوِفي َسْمِعي ُنورًا‬،‫ َوِفي ِلَس ـاِني ُنورًا‬،‫الَّلُهـَّم اْجَعـْل ِفي َقْلِبـي ُنورًا‬
،‫ َواْجَعْل ِفي َنْفِس ي ُنورًا‬،‫َوِمْن َخ ْلِفي ُنورًا‬,،‫ َوِمْن َٔامَاِمي ُنورًا‬،‫ وَعْن ِش َماِلي ُنورًا‬،‫ َو َعْن َيِميِني ُنورَا‬،‫َتْح ِتي ُنورًا‬
،‫ َواْجَعْل ِفي َعَصِبي ُنورًا‬،‫ ٔاَلَّلُهَّم َٔاْعِطِني ُنورًا‬،‫ واْجَعْلِني ُنورًا‬،‫ َواْجَعْل ِلي ُنورًا‬،‫ َوَعِِّظْم ِلي ُنورًا‬،‫ؤََاْعِظْم ِلي ُنورًا‬
‫ َو ُنورَا‬...‫ َٔالَّلُهَّم اِج َعْل ِلي ُنورًا ِفي َّقْبِري‬،‫ وِفي َبَش ِري ُنورًا‬،‫ َوِفي َش ْعِري ُنورًا‬،‫ َوِفي َدِمي ُنورًا‬،‫َوِفي َلْحِمي ُنورًا‬
‫ َوَهْب ِلي ُنورًا َعَلى ُنورًا‬،‫ َوِزْدِني ُنورًا‬،‫ َوِزْدِني ُنورَا‬،‫ َوِزْدِني ُنورًا‬،‫ِفي ِعظَاِمي‬

Dai-dai lokacin da yazo ƙarshen addu'ar suka isa bakin masallacin.

Kusan a tare suka haɗa baki wurin yin addu'ar shiga Masallaci.

” ‫ ِبْس ـِم الّلِه َوالَّصاَل ُة َوالَّس الُم‬،‫ ِمَن الَّش ْيـَطاِن الَّرِج ـيِم‬،‫ َوِبَوْج ِهـِه الَكِريـِم َوُس ْلطَـاِنه الَقِديـِم‬،‫َٔاعوُذ ِبالّلِه الَعِظيـِم‬
‫ َالَّلُهـَّم اْفَتـْح ِلي َٔاْبَواَب َر ْح َمتِـَك‬،‫“َعَلى َر ُس وِل الّلِه‬

Kana a nitse suka shiga cikin masallacin.

Shi Moddibo gefen daman sahun forko ya zauna, yayinda shi kuma M Jamil ya nufi wurin kiran salla...

Kasan cewar M Jamil ke ladancin masallacin Moddibo kuma limancin...

Bayan an idar da sallane, Khausar ta juyo ta kalli Raudat tare, da miƙa mata littafin Dua azkar, amsa tayi
kana ta buɗe daga shafin forko ta fara cikin sassayan sautin yarinta.

Ita kuwa Khausar Alqur'anin ta, ta ɗauka tare da fara, rero karatun Alqur'ani cikin zazzaƙar muryarta take
biya suratul Nisa'i.

A haka har aka kira isha sukayi kana, suka fito.

A falon suka zauna baki ɗayansu suna cin abinci.

Misalin ƙarfe tara da rabi, Ummi ce zaune gefen Innayi da hijabi a hannunta alamun ta gama shirin
tafiya.

Cikin kulawa da martabawa tace.

“Toh Innayi Allah Ubangijin talikai ya baki lfy yasa zakkan jikine, in Sha Allah gobe koda dare zan zo in
kuma dubaki da jiki”.

Kai ta gyaɗa cike da jin daɗin kulawar Ummin Jamil cikin ƙarfin guiwar da ta ɗan samu tace.

“Amin ya rabbil izzati Fatima ngd matuƙa Allah ya raya miki ahlinki yasa suyi miki fiye da abinda kikeyi
min”.
Cike da jin daɗin addu'ar tace.

“Amin ya Allah”.

Moddibo kuwa, kai ya tankwara gefe yana kallon kakartasa, sosai ta rame a dare ɗaya da wuni ɗaya.

Haka dai sukayi sallama Jamil ya ɗauke ta suka tafi.

Har bakin gate Modibbo ya rakasu.

Kai ya ɗan juya ya kalli wata motar dake gefen damansa ƙirar BMW irin dai wacca M Jamil yaja sukaje
makaranta, sai dai wacce baƙace wannan kuma farace ƙal mai masifar kyau.

Murmushin M Jamil yayi sabida ya fahimci kallon da yayiwa motar ma magana ce.

kanshi ya juya tare da cewa.

“Lafiyarta ƙalau kawai na barta a nanne sabida nan ya dace da ita, tunda ba gida ɗaya mukeba, Allah ya
kiyaye wani uzurin zai iya tashi da dare, kaga kamar jiya da kasan Innayi ba lafiya kawai ɗaukarta zakayi
ku tafi hospital ko Ummi?”.

Ya dire ayar mgnar yana kallon Umminsa da shima Moddibo ita yake kallon.

Cikin gamsuwa Ummin tace.

“Sosai ma kuwa”.

Cikin yin ƙasa da kai Moddibo yace.

“Ummi har kema haka zakice, kamar baki san me ake faɗi a cikin gariba, ba cikin gari, bama har cikin
gidansu fa, ganin kaskas akemin wasuma ɗaukar abotarmu ta tun yarinta sukeyi a matsayin na maida J
saniyar tatsa."

Cikin sanyi Ummin tace.

“To Moddibo ai shi ɗan adam ba'a biye masa”.

Da sauri Jamil yace.

“Yauwa Ummi gaya masa dai kam”.

Cikin tsare M Jamil din da ido yace.

“Motace dai ta hannunka ta ishemu, kuma ga waccar ma, kasan in bawai baka nanba always muna tare”.
Da sauri Jamil ya jujjuya mishi kai tare da jan motar ya tafi.

Sashin Innayin ya nufa, cike da zurfin nazari.

Tv ya kunnamata tashar Sunna, inda aka sa sautin karatun Alqur'ani mai girma.

Ido Innayi ta lumshe jin nitsuwa da salama na diro mata,

Saida safe yayi mata kana juya ya fita zuwa Part ɗin sa.

Washe gari ranar Alhamis ne, yau babu makaranta ko yan haddan bazasu jeba, shiyasa su Khausar suna
gida,

Bayan sallan la'asar Asma'u Ahmad ta shigo falon Momy cikin sakin fuska tayi sallama.

Da sauri Khausar ta fito daga ɗakin Momy tana cewa.

“Wa alaikissalam Giɗaɗo".

Murmushin Asma'u Ahmad Giɗaɗo tayi, ƙanwar M Jamil kenan da suka haɗa uwa.

Cikin sakin fuska tace.

“Jauro”.

Fuska Khausar ta kwaɓe tare da cewa.

“Wai jauro gsky ni an cuceni”.

Murmushin sukayi baki ɗaya sabida daƙuwar da Mamy tayi musu.

Cikin kunya Asma'u ta ɗan rusuna, tare da cewa.

“Barka da yamma Mamy”.

“Barka dai Asma'u ya Umminki?”.

“Tana lfy tace in gaidaki”.

“Masha Allah Ina amsawa”.


Da sauri ta miƙe tsaye jin Khausar ta kamo hannunta.

Ɗakinta suka nufa, suna shiga suka zauna bisa gado.

Raudat dake kwance kan gadon riƙe da wayan Mamy tana game ne ta miƙe da sauri ta faɗa kan Asma'u.

Ruggumi yarinyar tayi tare da cewa.

“Autan Mamy tsifa ake yi ne”.

Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.

“Eh kuma gashi har yanzu Adda Khausi bata gama minba, tsifanta zafi”.

Hararanta kausar ta ɗanyi tare da cewa.

“Da Allah tashi daga nan, nawama da yaya nake tsifan, kin samu ma inayi miki”.

Ta ƙare mgnar tana fita daga ɗakin.

Jim kaɗan ta shigo riƙe da filas da kofuna guda biyu bisa tray da kuma kayan tea, kan bed side drower ta
ajiye tiran kana ta haɗa musu tea mai zafi, sabida rage sanyin da suke rayuwa cikinsa, yasa tea ya zame
musu tamkar ruwa, madadin in kaje baƙunta a baka abin sha mai ɗan sanyi, sai a tarbeka da zazzafan
shayi.

“Gidado bar tsifan nan ga tea".

Khausar ta faɗa tana zama gefenta tare da miƙa mata, kofin.

Amsa tayi tare da kallon Raudat da ta fice da gudu sabida jin Abbansu ya shigo yana kiranta.

Riƙe cup ɗin tayi ba tare da tasha ba,

Ido Khausar ta ɗan zuba mata kana tace.

“Ya dai Giɗaɗo lfy kuwa?".

Numfashi mai nauyi Asma'u ta fesar kana cikin sanyi tace.

“Kamar zan biya ɗazu ki rakani”.

Ajiye cup ɗin hannunta tayi tare da cewa.

“Ina?”.
Murmushin Asma'u tayi tare da cewa.

“Gidan su Moddibo”.

Fuska ta kwaɓe tare da cewa.

“Allah ya kiyasheni, me zai kaini gidansu wannan mugun, mutumin da duk duniya bana da maƙiyi sama
dashi, duk abin da nai laifine, ni zanje gidansu yace na kai musu fitsara ya dakani a banza”.

Murmushin Asma'u tayi tare da cewa.

“Yoh ai shiyasa ma ban biyaba dan nasan bazaki taɓa yarda kijeba, kuma dai don shine sarkin masifa da
mugunta kawai daga zuwa gidansu sai ya kama dukanki”.

Baki ta taɓe tare da cewa.

“Yoh ai bazanma jeba ma”.

Kai Asma'u ta jinjina a ranta tana raya wata rana zatayiwa Khausar tsiya, ta kwasheta ta kaita.

Ajiye kofin tea ɗin tayi tare da cewa.

“A'a dubiyar mara lfy cefa Innayinsa ce ba".

“Can musu”.

Ta faɗa tana kwaɓe fuska

Murmushin Asma'u tayi tare da cewa.

“Toh naji”.

Daga nan sukaci gaba da hira.

Washe gari ranar jumma'a, misalin ƙarfe biyar dai-dai Khausar da ta shigo cikin gidan riƙe da hannun
Raudat da alamun kitso ta kaita.

A bakin mashigar gidan nasu tayi kiciɓis da Amina da Samira sani,

Sun iso bakin ƙofar a tare, dole sai ɗaya ya kaucewa ɗaya kafin a samu wurin wuce.

Wani masiyacin kallo Samira ta cillawa Khausar tare da jan tsaki.


Ita kuwa Khausar tsuke fuska tayi cikin rashin shakka ko tsoro ta goga kafaɗarta da na Samira duk da
kuwa Samira ta girmeta ainun.

Cikin izza Samira tace.

“Ke karere ki nitsu kisan da waye kikeyi”.

Ba tare da ta cire idanunta cikin nataba tace.

“Toh dodon gori”.

Cikin fahimtar caguben baƙar mgnar da Khausar ɗin ta yaɓa mata wanda yafi abinda ta gaya mata ciwo,
tace.

“Ke nifa uwarki zanci”.

Wani bauɗeɗɗen harara da dogon tsaki Khausar taja tare da cewa.

“Raudat mu tafi, kada mu tsaya muji, kukan tsuntsaye marasa tushe da gurbatacciyar tarbiya”.

Daga nan, ta juya tayi gaba.

Samira sani kuwa wani irin masifeffen kallo mai cike da tsana take Binta dashi.

Cikin takaici tace.

“Wallahi na tsani wannan yarinyar sam bana son ganinta, domin ta zame min madakatar nasarata".

Kwaffa Amina tayi tare da cewa.

“Bar shegiyar yarinya zanyi mgninta”.

Cikin tarin tsana Samira tace.

“Kune ma kuka bata dama ai, tana agola sai iyayi take muku, an wani dai-dai ta komai naku da nata, wai
hatta makarantarku ɗaya da ita, ni wlh da nice ke sai na zuga Umma ta zuga Lamido tasa an cireta a
wannan makarantar, shegiyar yarinya mai kama da ƴan ruwa.”

Kwaffa Amina tayi tare da cewa.

“Bar hegiyar yarinya, zanyi maganinta”.


Ita kuwa Khausar a falo suka samu Mamynsu kishingiɗe bisa carpet saƙale da wayarta a kunne, da alamu
waya takeyi, ido ta zuba mata jin tana cewa.

“Eh Hajja Nana in Sha Allah, zata zo, don dama cikin azumi suna hutu to kuma rashin lfyar ne ya hanata
zuwa, amman yau suka koma makaranta, kuma an ƙara musu hutun mako uku guda, sabida gyaran da
akeyi a makarantar in Sha Allah zata zo, a satin nan,".

Sai kuma ta ɗan yi shiru, na wasu ƴan daƙiƙu, cikin sanyi da girmamawa tace.

“Eh gata nan ma”.

Tayi mgnar tana miƙawa Khausar wayar, cikin kwaɓe fuska kamar zatayi kuka ta amshi wayar tare da
karawa a kunne murya ciki-ciki tace.

“Njam ɓanɗu.

Ina yini?".

Daga can kuwa cikin irin isa da kasaita ta tsofi masu iko Hajia Nana tace.

“Lafiyata lau, ki shirya kuna gama jarrabawar jarabar taku ta bokoko a wutan zakizo nan Jauro yaya
inada buƙatar ganinki”.

Cikin sauri da alamun akwai zaunanniyar tsama a tsakaninsu tace.

“Toh ai muna da hadda yanzuma da aka ƙara mana hutun, kuma zamuna zuwa leson”.

A faɗace tace.

“Leso mato nace leso mato, ita haddar mu nan ɗin ce miki akayi garin kafuraine, kizo liman Sadu zai baki
duk ilimin da kikeso in dai na addinine, na kafurcine dai bamu dashi”.

Cikin takaici tace.

“Nifa ki dena kafurta mana ilimin mu".

Cike da mamaki da al'ajabi Hajja Nana tayi wani dogon salati, tare da sanar da Ubangiji wai itace tana
mgn ana bata amsa, ita da mgnar ta take tamkar wahayi a cikin rugarsu kasancewarta itace babba.

Da sauri ta katse kiran tare dasa wayar a Airplane mode, ta kifeta gefenta sabida kada Mamynta ta
gane.

Cikin yin rau-rau da ido tace.

“Mamy dan Allah kice mata tayi haƙuri sai ran babban sallah zanje muyi kwana biyu kafin a koma
makaranta”.
Da sauri Momy ta fara jujjuya mata kai tare da cewa.

“Ban isaba Khausar ni dai kam bani da bakin yin taƙaddama da umarni Hajja Nana, ki kwana da sanin can
zakije kiyi hutun nan, da kika samu ma bakije kinyi azumi a canba, tun tsawon shekaru takebi tana son
hakan kuma bai samuba sabida uzurin da ita kanta ke fadarsa na zuwan ta Umara, bana kuma tace,
saboda ke, bazata je Umrar ba, saboda tana so kije ki daɗe kisan yan uwanki su sanki.”

Cikin jan dogon numfashi tace.

“Mamy ni dai kin san ba shiri nakeyi da ita ba, ko zuwa nan tayi a wuni ɗaya sai tayi min masifa da sharri
sama da sau biyar”.

Cikin haɗe fuska Mamy tace.

“Kuma dole kan umarnin ta da izininta mizanin muhallin zamanki yake, ki fara shiri kawai ma in Allah ya
kaimu gobe zan gayawa Abbanku, zuwa ranar jumma'a mai zuwa sai ki bisu in sunzo cin kasuwa kije
RUGAR JAURO YAYAH tabbas d....!

Littafin SAKAYYAH na kuɗine biya ki karanta cikin Salamah yar uwa.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_Page 3_

_NA_

_AYSHA ALIYU GARKUWA_

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*FREE PAGE*
*Littafin SAKAYYAH na kuɗine 1k ne kacal ƴar ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki
0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP
09097853276*

*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son
k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman
lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun
matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa
ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran su dawo aiki
tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones
dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da
tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da
ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda
ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya
wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka
kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki
da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp
in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta,
muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina
nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a
ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.

0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta
wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk jihar da kike kayana zaije
gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida. Set ɗina akwai manya
akwai ƙananan set akwai kuma na tsakiya, ƙananan set ɗin daga 40k 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙara
ɗan cukulan haɗiba bana haɗin kasa da 10k sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar mace shi 8k set ɗin
tsakiyan su da 50k 60k 70k 80k 90k ne manyan kuma daga 100k ne zuwa yadda zaki iya Hajia ta*

GARKUWAR MA'AURATA

Cikin sanyin jiki Khausar ta miƙe tsaye tare da juyawa a hankali ta bar falon Mommy ta wuce ɗakinsu.

Ɗakin mai girmane wanda ke ɗauke da matsakaici gado ƙiran Italian bed sai durowarsa dake gefe wanda
ke ɗauke da ƙofa shida, daga kusurwan gabas babban TV plasma ne da DStv sai tattausan canis carpet
pinch color dake shimfiɗe Atsakiyar ɗakin wanda shi ke ɗan rage musu masifeffen sayin tayis ɗin,

komai na ɗakin pinch colour ne sai ɗan ratsin fari.

Cikin jagulewar zuciya ta kwanta bisa gadon tare da lumshe manyan Idanunta dake cike da ruwan
hawaye.

Allah ya sani sam bata ƙaunar zuwa Jauro Yaya ko kaɗan, ya zame mata dole ta newa kanta mafita.

Ɗan gajeren tsaki taja tare da mirginawa ta juya tsakiyar gadon, kana ta lumshe idanunta, da wannan
tunani bacci ya ɗauke ta...

Cikin nutsuwarsa da kuma sanyinsa kamar koda yaushe yake tuƙa motar, yayin da M Jameel ke gefen
hagunsa kamar wanda akace ya dubi madubin dake gefensa se kuma yayi saurin kallon Moddibo dake
Driving cike da mamaki yace.

“Kai A.J kaga kamar binmu akeyi fa ko?”.

Kai Moddibo ya jinjina tare da ɗan yamutsa fuska anitse yace.

“Eh binmu akeyi sai munje gidan Ummi zan tsaya”.

Cikin sauri M Jameel ya juyo gareshi tare da ɗan ware idonsa yace.

“Kama san ana binmu kuma shine ka ƙi tsayawa? Idan kuma wanda zasu cutar da mune fa A.J?”.
Kai Moddibo ya girgiza yana mai cigaba da tuƙinsa tare da buɗe lips inshi a sanyaye yace.

“Ai nasan wanda ke binmu fa Alhaji Bashir ne”.

Da sauri M Jameel yace. “Waye Alh Bashir?”.

Ɗan juyow Moddibo yayi tare da ɗan kallonshi kafin yace.

“Babban yaron Malam Arɗo ne”.

Cikin sauƙe Numfashi M Jameel yace.

“Ok to Meyesa ba zaka tsaya ba?”.

Ba tare da ya juyo ba yace.

“Nasan magana ce mai yawa yazo dashi, koda na tsaya ma, ba zamu gama ba kuma kaga agefen titi
muke baya ga hakama na masa signal ya fahimta”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare da faɗin.

“Ok shikenan”.

Daga nan sukaci gaba da tafi.

Suna isa ƙofar gidan Ummi M Jameel ya buɗe ƙofa ya fita dai-dai lokacin da Alh Bashir ya ƙara so
fuskarsa ɗauke da murmushi ya miƙa wa Alh Bashir hannu sukayi musabaha cikin sakin fuska Alh Bashir
yace.

“M Jameel Ko?”.

Kai M Jameel ya gyaɗa mishi tare da cewa.

“Ya gida ya iyalai ya kuma Baba Arɗo?”.

Cikkn sakin fuska Alhj Bashi yace.

“Duk Suna lafiya”.

Murfin motar M Jameel ya buɗewa Alh Bashir tare da cewa.

“Bismillah kashiga”,

Sannan ya zagaya gefen da moddibo yake wanda har zuwa lokacin bai fito ba yace.

"Bari nashiga ciki sai ka shigo”.


Kai Moddibo ya gyaɗa cikin yanayin sanyin magarsa yace.

“Nima Ina Shigowa yanzu”.

“To sai ka shigo”.

Ya fadi tare da juyawa ya nufi cikin gida yashiga bakinsa ɗauke da sallama.

Ba lefi madedecin gida ne mai kyau daga farkon gidan ze iya ɗaukan motoci biyu se tank na ruwa dake
can gefe tsakar gidan shimfiɗe yake da interlock sai babban sashe guda ɗaya cikin gidan zagaye yake da
fulawa wi masu kyau wanda keda alaƙa da Moddibo dan duk inda yake da dama sai ya ƙawatasa da
fulawowi, sabida suna samishi farin ciki.

Tsarin ginin yayi matuƙar kyau duk da cewa ba babba bane amma komai fess dashi haka zalika
madedecin falon nasu da befiye girma ba yayi matuƙar kyau falon na ɗauke da manyan setin kujeru kalar
ash da baƙi cai Centre table dake tsakiya da kuma ƙaton TV dake maƙale abango daga gabar da TV akwai
ƙaton fanka bayan AC dake maƙale da bango daga yamma da TV zagaye yake da wasu flowes masu kyau
da ɗaukar hankali sai tattausan carpet mai ɗan kare kyau dake malale a tsakiyar falon...

Cike da so kulawa ƙauna irin ta uwa Ummi ta kalli Jameel dake shigowa tare da sakar masa da
murmushin da bata san ya subce mata ba,

bayan ta amsa sallama.

Cike da farin ciki Asma'u ta miƙe tare da gyara wuyan abaya ɗan baby himar dake zage da fuskarta da
ɗauke da murmushi cike da jin daɗi ta rungume M Jameel da faɗin.

“Oyoyo Yaya Jameel na Ina yini”.

Kanta ya shafa cike da son yar uwar tasa yace.

“Lafiya lau my blood ya karatu?”.

Cikin murmushin ta amsa da.

“Alhamdulillah”.

kana ta zauna daga ƙasa kusa da ƙafafunsa,

Ummu kuwa miƙewa tayi tana ɗan leƙan bayansa.

Murmushi M Jameel yayi domin ya fahimci Moddibo take leƙawa ganin basu shigo tare ba.

Cikin yanayin fara'arsa yace.


“Kai Ummina ki bari mugaisa kafin ki tambayi 'yan biyun nawa??”.

Ka ta girgiza tare da cewa.

“A'a gwara in tambaya naji, domin shi yace na muku dambun couscous shiya keso kaga kuwa ai bazan ji
daɗi ba in ban ganshi ba”.

Murmushi M Jameel yayi yana mai jin daɗin yadda mahaifiyarsa ke nunawa amininsa ƙauna tamkar ita
ta haifeshi, yana murmushi jin dadi yace.

“To yana mota”.

Da sauri ta sake dubansa tare da cewa.

“To me yakeyi amota da bai shigo ba?”.

Ashagwaɓe yace.

“To Ummina mu gaisa mana”.

Dawowa tayi ta zauna bisa kujera 2 str,

shi kuwa M Jameel zamewa ƙasa yayi zauna daɓas bisa carpet kana ya ɗaura kansa acinyarta murya a
sanyaye yace.

“Ummina daga shigowa ko gaisawa ba muyiba sannan baki samin albarka ba kika tsareni da tambayar
Moddibo”.

Hannunta ta ɗauka bisa tsakiyar kasan tare da shafa kansa tana mai cewa.

“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwarku! Allah ya dafa muku acikin dukkan lamuranku!!

Ubangiji ya tsareku daga sharrin abinƙi tsakanin mutum da aljan!!!

Allah ya baku 'ya'ya masu biyayya tamkar yadda kuke mana kaida Amininka”.

Cike da tsananin jin dadi da sassayan salama yace.

“Ameen thumma Ameen Yah Ummi”.

Hannunta ta ɗan janye daga kansa tare da sake tambayar sa.

“Ina Moddibo?”.

Ƴar dariya mai sauti yayi tare da miƙewa ya zauna akusa da ita kasancewa kujeran 2sitter ne.

gyara zamansa yayi yana fuskantar ta yace.

“Moddibo zai shigo amma ba yanzu ba”.


Da sauri tace.

“Meyasa?”.

Cikin saurin shima yace.

“Bari dai in miki bayani hankalinki ya kwanta.

Muna tahowa ne Alh Bashir babban yaron Malam Arɗo ya biyo mu to suna mota suna tattaunawa.

Nasan bazai wuce ƙorafi ya kawo akan mahaifinsu ba”.

Tsaresa da ido Ummi tayi kana tace.

“ƙorafi akan Babansu kuma?”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

"Eh Ummi saboda Malam Arɗo wani irin mutum ne wanda zamuce mai dukiyar lukudi gashi dai Allah ya
bashi dukiya na ban mamaki amma babu wanda ya isa yaci wannan kuɗin kamar abin masifa”.

Gyara zama Ummin tayi tare da cewa.

“Ikon Allah to sabi da me?”.

Numfashin M Jameel ya ɗan fesar tare da cewa.

“Tun bayan rasuwar mahaifinsa abubuwan suka ƙazanta.

Domin baya sauraron shawarar kowa koda kuwa ƙannensa ne domin shine babba acikinsu dan haka
babu mai tanƙwarashi.

To fa saidai Allah ya ɗaura masa son Moddibo a zuciyarsa duk abinda Moddibo yace ko kuma ya kawo
shawara akai to zaiyi koda kuwa ransa baya so.

Duk da wani lokaci zakiji yana yiwa Moddibon ma faɗa akan cewa zaisa shi kashe kuɗi amma koda ya
gama surutun daga baya zakiga yayi abin da ya fadan.”

Gyara zama M Jameel yayu tare daci gaba da cewa.

“To fa wannan dalilin ne yasa muddin 'ya'yansa suna buƙatar wani abu saidai su biyo ta hannunsa
Moddibo”.

Ka saƙe Ummi tayi tana kallon Jameel din kana cikin sanyin murya tace.

“To kada fa hakan yasa yayi baƙin jini awajen 'ya'yansa kasan ɗan adam”.
Dariya M Jameel yayi kana yace.

“Ummi me Moddibo zai buƙata awajen Malam Arɗo me zeyi da dukiyarsu? Mutumin da baiwa yayansa
Bama me zai bawa Moddibo wanda baida shi".

Kai Ummi ta gyaɗa tare fesar da numfashi a sanyaye tace.

“Hakane kam al'amarin Moddibo da Innayi akwai al'ajabi, domin ko nasan baza su taɓa buƙatar wani
abu awajensa ba, duk da kuwa anayi musu kallon basu da wani cikekken jigo acikin rayuwarsu.

Amma kuma yanda suke tafiyar da rayuwarsu cikin tsari da hikima da wadata yana bani makaki”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cewa.

“Kinga Koda motar da Malam Arɗo ke hawa tsohuwa ce aƙalla zata kai shekaru ashirin da biyar ko ashirin
da takwas amma har zuwa yau ya kasa can zawa, anyi-anyi dashi yaƙi duk yanda akayi dashi ya sauya
wata yaƙi kuma kullum ciki bashi ciwon kai takeyi.

har kyautar Mota ɗansa Alh Bashir ya bashi amma yaƙi amsa domin atunaninsa daga baya zai fanshe
kuɗin sa.

Ko gidansa da kike gani yanzu ga gini dai yayi mai kyau amma ɗakunan matansa kamar zauren haka suke
babu kujeru bare wani abu shi Tv.

Yanzu haka kwanan ake gyaran makarantarsa wanda da taimakon Moddibo akeyinsa kuma adalilinsa ne
yake biyan Malamai albashi mai tsoka inba haka ba baki ɗaya makarantar ta koɗe sannan babu albashin
kirki saboda Moddibo yanzu aka rushe makarantar ake gyarawa yanzu hutun da aka kara ma gani yake
kamar za'a yi masa asara shiryasa yace adawo ko ba'a gama gininba to bayan an dawo yanzu dole aka
sake komawa hutu saboda ba'a gama gyaranba yanzu ma cewa yayi dole kada a wuce wata ɗaya da ƙyar
Moddibo ya lallaɓasa aka tafi hutun kafin adawo angama gini da kuma tsare tsare sa duk ya buwaye mu
da cewa Moddibo na sashi kashe kudinsa”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa.

“Masha Allah shiko wannan wani irin mutum ne?”.

Murmushi M Jameel yayi tare da cewa.

“Ummi haka 'ya'yansa ke fama dashi, kin san ku fulani”.

Murmushi Ummi tayi tare dayi masa daƙuwa.

Aɓangaren Moddibo kuwa.


Zaune suke da Alh Bashir bayan sun gama gaisawa shiru na wasu daƙiƙu ya wanzu atsakaninsu kafin.

Cikin kulawa Moddibo ya ɗan juyo ya kalli Alh Bashir cikin kulawa yace.

“Alh ya akayi?”.

Numfashin mai nauyi Alh Bashir ya sauƙe kana a hankali yace.

“Mitsss Moddibo Agaskiya al'amarin Babanmu yana matuƙar ɗaure mana kai?”.

Lumshe idanunsa yayi kafin yace.

“Meya faru!?”.

Kai ya girgiza cikin yanayin damuwa yace.

“Modobbo wallahi Mahaifiyata bata da lafiya, ance sai anfitar da ita waje, gashi duk cikin mu babu
wanda yake da halin biya afita da itan.

Kasan halin Babanmu kuma, duk iyakar iyawata yaƙi amincewa.

Ni kuma bani dashi”.

Cikin sanyi Moddibo yace.

“Alh baka dashi kuma”.

Kwaffa Alh Bashir yayi tare da cewa.

“Wallahi Allah Moddibo wasu lokuta idan akace min Alh Bashir ba ƙaramin ɓaci raina yake ba domin
bafa mahaifina ne yabiya min Makka ba.

Sannan ba nine na biyawa kaina ba dukiyata bace yasa naje ba.

Dalilin Surukina naje wato mahaifin Matata fa ya biya min na samu naje duk wani abu da nake buƙata
sai dai Inje wajensa wanda kuma hakan da kunya da kuma zubar da girma.

amma mahaifina Allah ya hore masa fiye dana surkina amman bazai taimaka manaba ayanzu ga jinyar
mahaifiyarmu dole sai anfitar da ita waje an mata dashen ƙoda.

shi kansa yana ɓuƙatar canjin mota lokuta da dama yana tafiya Atsakiyar titi zakaga ta lalace, idan shi
baya damuwa da zaginsa da akeyi a gari da rayuwarsa to mu muna buƙatarsa ba mason wani abu ya
sameshi kuma bama jin dadin habaice-habaicen da akeyi mana.

Shiyasa nazo wajen ka.

Dan Allah da Manzonsa kayi masa magana ya kai mahaifiyarmu asibiti. Sannan ya canza motarsa bayan
wannan akwai kannen mu mata da suka gama secondary akwai buƙatar su tafi jami'a amma yaƙi sasu
domin aganinsa za'a cajesa kuɗi masu yawo dan Allah katemaka kayi masa magana akan waɗan nan
abuvuwan”.

Ya dire ayar mgnar da haɗe tafin hannunsa alamun roƙo da neman al'farma.

Moddibo kuwa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da buɗe idanunsa dake lumshe kana a hankali yace.

"Insha Allah zanyi masa magana, amma ayanzu da ƙyar zai amince domin da mun zauna zance ɗaya yake
nanata min wai na sashi kashe kuɗi amakaranta wai zan talautashi”.

Murmushi mai ciwo Alh Bashir yayi tare da cewa.

“Muma ko agida haka muke shan complain Koda kudin cefene da sauran abubuwa aka tambayesa zaice
Ni bani da kudi wannan yaron Moddibo duk yasa na kashe kuɗaɗenna aginin makaranta”.

Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙara fitar da ainihin kyawunsa cikin sanyi yace.

“Uhufm Malam Arɗo kenan.

Ba matsala Insha Allah zanyi magana dashi duk yadda mukayi dashi zakaji”.

Ya kare mgnar yana shafa tattausan sajensa.

Godiya Alh Bashir ya masa sannan su kayi sallama Moddibo yashiga cikin gida.

Shi kuma ya juya ya tafi.

Tattausan murmushi Ummi tayi ganin Moddibo cikin kulawa tace.

“Babana na kaina sannu da zuwa”.

Kasancewar sunan mahaifinta garesa.

Cike da ladabi ya zauna yana cewa.

“Ummi fatan mun same ku lafiya ya yara?”.

Da murmushi afuskarta tace.

“Duk muna lafiya ya jikin Innayi?”.

“Alhamdulillah Ummi jiki kam da sauƙi sosai ma".


Ya kare mgnar yana mayar da kallonsa ga Asma'u data fito daga Bedroom da alama muryarsa taji ta fito,
har ƙasa ta tsugunna tare da cewa.

“Yah Moddibo ina yini”.

“Lafiya Asma'u ya karatu da hadda?”.

“Alhamdulillah”.

Kai Ya jinjina tare da faɗin.

“Meyesa yau bakije hadda ba?”.

Kanta aƙasa tace.

“Yah Moddibo bani da lafiya ne zazzaɓi ke damuna”.

Kallonta yayi na daƙiƙu uku, kana yace.

“Asmau kadafa ki biyewa wannan mashiririciyar ƙawar taki, ki dena harƙa da ita sam banason alaƙarta
dake tsakaninku.

Domin yarinyar bata ji kona misƙala zarratin, bana son ganinki tare da ita dan gaba ɗaya sunanta ya
zagaye makarantar saboda rashinjinta sam bata da nutsuwar da za'ayi abota da ita.”

Ita dai Asma'u kai take jinjina mishi.

M Jameel kuwa ido ya zuba mishi yayinda Ummu kuwa ke murmushi.

Shi kuwa Moddibo gyara zamansa yayi tare daci gaba da cewa.

“Domin shin abota anaso ayi da na gari, bi ma'ana idan za kayi abota kayi da mutum na gari domin
kamar dai misalin:

meyin abota da me saida turarene koda ba azata masa ƙamshi ba to baza azata masa wari ba, sannan
misalin: mai abota dame zuga-zugi koda yana da haske to ba za'ayi masa zaton haske ba".

Ɗan kishingiɗan M Jameel yayu tare da lumshe idanunsa.

Shi kuwa Moddibo cikin nitsuwa yaci gaba da cewa.

“Manzon Allah (S.A.W) ya kwaɗaitar damu da yin abota da mutanen ƙwarai domin abokin ƙwarai yana
daga cikin wanda Allah yayi alƙawarin zai sasu acikin inuwar alarshinsa ranar tashin ƙiyama, amma kuma
duk abotar da ba'agina sa saboda Allah da manzo ba to ƙarshensa nadama ce sam wannan FATTANAH
bata dace da zama abokiya a garekiba”.
Itade Asma'u kanta na ƙasa batare data ɗago ba tace.

“Toh Yah Moddibo”.

M Jameel dake kishin giɗe idanunsa lumshe kuwa a hankali ya miƙe tare da buɗe idanunsa akan
Moddibo dake cigaba da yiwa Asma'u nasiyya akan tarabu da Khausar cikin tsareshi da ido yace.

“Wai dan Allah A.S meye haka? kana tayiwa Asma'u huɗubar watsar da aminiyarta shin ita Khausar ɗin
sheɗan ka ɗauketa ko kuwa dujjal?”.

Ɗago kai Moddibo yayi tare da tsuke fuska yana kallon M Jameel yace.

“Kusan haka domin sam yarinyar bata da ɗabi'un kirki”.

Kai M Jameel ya girgizi kana yace.

“Haba Moddibo yarinyar nan tana fahimtar karatu duk wasu abubuwa da ake koyarwa tana ganewa fiye
da duk yan ajinka,

kawai rawan kai da ƙuruciya ke damunta, da zaran ta mallaki hankalinta zata dena, amma ka zauna kana
ƙoƙarin cusa ƙiyayyarta azuciyar Aminiyarta sam hakan ba dai-dai bane yoh ba ita cema ke taimakawa
ƙanwar taka da kake zugawarba ita me take ganewa ma tana nan kai kamar na kifi”.

Itade Asma'u kanta na ƙasa tana wasa da yatsun hannunta.

Wani kallo mai cike da manufofi Moddibo yayiwa M Jameel tare da taɓe baki kana yace.

“Ina ruwanka? bansa bakinka ba da Asma'u ƙanwata nake magana”

Kana ya juyo ya kalli Asma'u da har zuwa lokacin kanta ke sunkuye yace.

“Maganata kika ɗauka zakiyi amfani dashi ko nasa?”.

Da sauri tace.

“Naka Yah Moddibo”.

Murmushi yayi da faɗin.

“Ɗayyit Allah ya miki albarka”.

Ɗago kai M Jameel yayi dai-dai lokacin Asma'u ta ɗago kanta,

ido yakashe mata ita kuma murmushi ta sakar masa.


Ummi dake sauraronsu kuwa sai yanzu tace.

“Yawwa Moddibo ka cigaba da samun Ido akan yaran nan dan yaran saida sa ido”.

Moddibo kuwa ido ya lumshe tare da gyaɗa kai kana yace.

“Insha Allah Ummi na lura J da wannan fitinanniyar yarinyar kusan halinsu ɗaya shima kullum fama nake
dashi ya nutsu yaƙi nitsuwa”.

Wara ido M Jameel yayi tare da cewa.

“Nine bani da nutsuwar A.S?”.

duk dariya suka sanya banda Moddibo da yayi murmushi.

Abinci Ummi ta bawa Asma'u umarnin ta kawo musu fita tayi ba daɗewa ta dawo hannunta ɗauke da
warmers ta ajiye musu M Jameel ne ya buɗe murmushi Moddibo ya saki yana kallon yanda dambun yayi
kyau sai tashin ƙamshi albasa da kuma ƙamshin man shanu.

Ummi da kanta ta zuba musu tare da mimmiƙa musu plate ɗin.

Bismillah sukaui kafin suka fara ci suna kammala ci sukayi wa Ummi sallama sannan suka tafi.

Washe gari. Tun wuri Khausar ta tashi amma taƙi shiryawa da wuri seda kowa ya gama shiri ya rage
saura ita kaɗai, dan Allah ya sani ita ta tsani ta gama shiri ta tsaya jiran wasu.

Ahankali take shan comflakes dake hannunta kamar ba jiranta akeyi ba yayin da Raudat ke zaune
gefenta, Cikin fushi Amina ta banko labulen ɗakin cikin kumfar baki tace.

“Wallahi Khausar zamu tafi in banda raini da samun waje tuntuni muke jiranki amma kin tsaya feleƙe
dan kin san in mun tafi mun barki Abba zaiyi faɗa”.

Anutse ta ɗago manyan Idanunta dake lumshe ta watsawa Amina wani kallo kafin ta taɓe bakinta kamar
zata ce wani abu sai kuma ta fasa ta miƙe ta riƙo hannu Raudat suka fita bayan ta gama shanye
Comflakes ɗin.

Ajiyar zuciya Amina ta sauƙe cike da takaici tabi bayan Khausar da haramta, duk sanda tazo da niyyan
ciwa yarinyar mutunci da zaran sun haɗa ido zata nemi duk wani karsashinta ta rasa koda suka shiga
motar Amina bata tanka taba ita da Raudat keta faman surutu har suka isa cikin sa'a Moddibo beshiga
ba zamansu ba daɗewa yashigo as usual cikin shigar jallabiya Onion color da yasha guga kansa sanye da
hula malam taɓani kaji ruwan hadith yayin da ya naɗe da hirami jikinsa na fitar da ƙamashin daddaɗan
tularensa,
cike da ladabi suka shiga gaishesa Amsawa yayi kamar ko yaushe a saman laɓɓan sa.

Taɓe baki Khausar tayi aranta tace.

“Akwi madaran ƙasaita ana mutun kamar sarki”.

Batare daya kallesu ba yace.

“Su kawo hadda wiƙiƙi da ido Amina tashiga yi kasancewar itace afarko kuma bata iya ba ya dubi Samira
sani yace ta karanta hadda still itama bata iyaba kallon Abeeda Sa'idu yayi yace ta karanta wacce ƙawar
Samira Sani ce da ƙyar ta karanta aya biyar aciki sumunin da zasu karanta koda yazo kan Khausar cikin
nutsuwa da ƙwarewa ta karato sumuni ɗaya na farkon Suratul Taubah.

Kanshi ya jinjina tare da juyowa ya kalli Asma'u Ahmad.

Cikin yanayin tsoro ta kawo suminin amman yayi mata gyara biyu.

Da ɓacin rai Moddibo ya fitar da wanda basu karanta ba ya basu punishment.

Khausar kuwa tasa su gaba ta riƙa dariya baƙin ciki ya cika musu zuciya kamar su mutu ahaka Malam
Ahmad dake malamin Tajweed ne shima ya zuwa wurin addar.

Har yayi ya gama basu dawo ba seda aka tashi kafin aka ƙyalesu akan punishment ɗin...

Da dare.

Mamy ce tsaye cikin ƙasaitacciyar shiga, tana zuwa wani irin ƙamshin kulaccar sirri da ta saya wurin
Aysha Aliyu Garkuwa.

Baki ta ɗan taɓe tana kallon yada Khausar ke shishita sabida uban yajin da ta zambadawa indomei
wanda yaji nama da.

Kai kawai ta jijjiga sannan tayi musu sallama ta wuce turakar mijinta.

Tanaci tana kurɓar ruwan sanyi, tana bawa Raudat har suka gama ɗaukar Raudat tayi suka shiga ɗaki kai
tsaye toilet suka wuce brush tayi sannan tayiwa Raudat kana suka ɗaura alwala suka fito.

Jikin window Khausar ta nufa da niyyan rufewa Idanunta suka sauka akan Haiydar dake ɗauke da
Ramadan zasu shiga sashen Hajiya Bunayya,

fasa rufe window tayi cikin ɗan ɗaga murya tace.

“Haiydar ina zakuje?”. shima cikin ɗaga murya yanda zataji yace.
“inda kika aikemu”.

Cikin takaici ta rumtse idonta kafin tace.

“Wai Haiydar meyesa karai nani ba dama in maka magana, ko in baka umarni saika riƙa bani amsa kai
tsaye”.

Bakinshi ya taɓe tare sa fadin.

“Acikin gida ma saiki riƙa tambayar ina zanje! Me zanyi? Me zanci? fisabilillah ni bani da ikon da zanyi
abu da kaina koda Mamy bata Matsamin irin yanda kike min gsky na gaji”.

Bai jira jin amsartaba ya wuce yashiga sashen Hajiya Bunayya,

Aseeya yayar Amina na ganinsa ta saki murmushi tace.

“Umma ga babanki yazo”.

Cikin sauri Hajiya Bunayya ta fito hannunta ɗauke da glass cup na madara tana jujjugawa fuskarta da
murmushi tace.

“Gashi babana madaran shanu ne mai ɗumi”.

Amsa yayi yana murmushi saboda yanayin sanyin dake garin yace.

“Nagode Umma”.

Jujjuya Glass Cup ɗin yayi kafin ya kai bakinsa da faɗin

"Bismillahi”.

Khausar kuwa jingina bayanta da jikin bango tayi kafin ta ɗaga hannunta sama cikin raunin murya tace.

"(Ya wadud³,Ya zul'arshil makin,ya fa'alillima yurid,As'aluka bi izzatil lati la yura,wa mulki kallazi la
yuda)ya Allah katsare min ɗan uwana kada Hajiya Bunayya taci galaba wajen cutar dashi”.

Kafin ta shafa ta kwanta lamo agado....

A can side din kuma cikin mugun sauri Hajiya Bunayya ta riƙe hannunsa domin bokan daya basu maganin
ya tabbatar musu da zaran anyi Bismillah laƙanin maganin ya karye,ta anshi Glass Cup ɗin da faɗin.

“Bari mugani kode da zafi ne kada ka ƙone bakinka”.


Kai ya girgizi tare da faɗin.

“Ba zafi Umma”.

miƙa masa ta sake yi amsa yayi ya sake kaiwa bakinsa da faɗin.

“Bismillah”, saurin karɓa ta kuma yi tare da cewa.

“Mugani kode sugar bai jibane”.

Kai ya girgizi yace.

“Kin san ba damu da zaƙiba Umma”.

yaƙe tayi da faɗin.

“bari dai na ƙaro maka sugar”.

Ta faɗa tare da shigewa Bedroom duk aƙoƙarinta na ganin ta mantar dashi Bismillah ba jimawa ta fito ta
sake miƙa masa tana jujjuyawa aranta tana addu'ar Allah yasa ya manta da Bismillah. Aseeya kuwa ikon
Allah kawai take gani wajen mahaifiyarta ita kuwa Amina tasan komai domin ita ta karɓo maganin wurin
boka Karƙuzu.

Karɓan Glass Cup ɗin yayi yakai bakinsa kana yayi Bismillah yasha kallon Ramadan yayi yace.

“Zaka sha?”.

Kai Ramadan ya girgiza alamar a'a...

Hajiya Bunayya kam ji tayi kamar ta haɗiye zuciya ta mutu ganin maganin data kashe maƙudan kuɗi
wajen amsarsu aranta tace.

“Shegen yaro mai ta ammalli da addu'a duk uwarsu ta koya musu yin addu'a akan ko wani irin abu afili
kuwa murmushi tayi tace.

“Babana sugan yayi?”.

Kai ya gyaɗa mata sannan ya shanye bayan sun sake taɓa hirane ya mata seda safe ya fice...

Washe gari da safe Ummi ta nufi gidansu Moddibo domin duba jikin Innayi bakinta ɗauke da sallama
tashiga cikin gidan atsakar gida taci karo da Innayi dake faman gasa nama irin wanda ake yiwa masu
jegon.

Cikin sakin fuska Innayi ta mata sannu da zuwa, Murmushi Ummi tayi tare da zama ta gaisheta cike da
ladabi tare da tambayarta ya jiki kana ta kama mata aikin suka gama.
Bayan sun gama ne Moddibo da M Jameel suka dawo zama sukayi tare da gaisawa Ashagwaɓe M Jameel
ya dubi Ummi yace.

“Ummi bacci nakeji”.

bai jira cewarta ba ya zame ya kwanta tare da ɗaura akansa a cinyarta

Moddibo kuwa Hararansa yayi yace.

“Kaidai ba zaka taɓa girma”.

Tura baki M Jameel yayi amma baice komaiba saboda baccin dake cinsa kwanciyarsa ba jimawa bacci ya
ɗaukesa ganin lokaci na tafiya yasa Ummi tace. “Moddibo bani filo ka gani”.

miƙewa yayi ba daɗewa ya fito hannunsa riƙe da pillow Ummi ta karɓa ta ɗaura kan M Jameel akai
sannan ta yiwa innayi Sallama.

Moddibo ya tafi mai data bayan sun hau kwalta Moddibo ya dubi Ummi cikin sanyin murya yace.

"Dan Allah Ummi ki riƙa yiwa Asma'u faɗa ta daina ƙawance da wannan yarinyar sam bata da nutsuwa
zata ɓata Asma'u da halayyarta na rashin nutsuwa yarinya nada naci in ba da gaske mukayi ba bazamu ci
nasara ba da na lura ta shiga ranta koda na yiwa Asma'u magana kan tarabu da ita.

Kuma naga kamar ba zata yiba anma idan ya zamana mu biyune muke mata faɗa zata ɗauka”.

Kai Ummi ta jinjina tare da cewa.

“Insha Allahu zan riƙa yi mata”.

Ahaka suka isa gida ya ajiyeta sannan ya koma...

Washe gari. Ya kama Juma'a misalin ƙarfe uku Khausar na zune kan 2sitter Raudat na gefenta tana yanke
mata ƙumba yayin da Mamy ke riƙe da hisnul Muslim tana Azkhar Asma'u tashigo bakinta ɗauke da
sallama miƙewa Khausar tayi tare da rungumeta tace.

"Oyoyo Ƙawar arziƙi”, Murmushi Asma'u tayi cikin sigar zolaya tace.

“Fattanah kina son karya ni ko?”.

Saketa Khausar tayi tare da tura ƙaramin bakinta tace.

“Kina so mu ɓata ko?”, Murmushi Asma'u tayi tare da tsugunnawa har ƙasa ta gaisheda Momy cikin
sakin fuska Momy ta amsa tana tambayarta Umminta ta bata amsa da.

“Tana lafiya, Momy tace ma in gaidaki”.


Cikin sakin fuska Momy tace.

“Ina amsawa”.

Ita kuwa Asma'u cikin girmamawa tace.

“Ayyah Momy in ba abinda Khausar zatayi miki ta rakani mana Ummi ta aikeni kuma banason zuwa ni
kaɗai”.

Sanin Asma'u yarinya ce me tarbiya da nutsuwa uwa uba kamun kai yasa Momy amincewa.

Kai ta gyada mata tare da cewa.

“Toh kada dai ku daɗe ku kuma kula da kanku banda kula maza”.

Cikin jin dadi Asma'u tace.

“In sha Allah kuwa Momy”.

Ita kuwa Khausar murmushi tayi tare da cewa.

“To ni baki nemi izinina ba”.

Ta ƙare mgnar tana

Shiga Bedroom ɗin ta, murmushin Asma'u tayi tare da bin bayanta kana ta langwaɓar da kai tace.

“Ayimin afuwa ƙawar arziƙi”.

Hira suka ɗan fara taɓa sannan Asma'u ke sanarwa mata zata raka unguwar Teku ta kai saƙo Ummi ta
aiko cikin zumuɗi da son fita ta miƙe tare da ɗaukan dogon hijab maroon colour tasa akan riga da
wondon dake jikinta ba tare data tambayi inda zata jeba tace su tafi dan kawai tana masifar son
unguwar Teku...

Aɓangaren Moddibo kuwa bayan ya dawo daga sallar la''asar,

Side ɗinsa ya wuce,

Ruwa ya watsa tare da sauya kayan jikinsa, wani tattausan riga da wondo nevy blue mai taushi ya zira,
tare da fesa turarensa oud jannah mai masifar ƙamshi,

System ɗinsa da wayarsa ya ɗauka kana ya fito, a hankali ya lumshe idanunsa jin yadda sassanyar iskar
ke ratsa cikin tattausan sumar kansa da yana iya kwana biyu bai cire hulaba.

A hankali yake taka steps din yana sauƙowa ƙasa wani irin masifeffen kyau yayi collor kayan jikinsa yayi
matuƙar amsarsa farar fatarsa ta ƙara bayyana, yayinda tattausan sajensa yayi lib-lib gwanin burgewa
jajayen lips ɗinsa dake cikin zagayen sajensa da kota million ɗinsa sai sheƙi sukeyi, a hankali yake taka
tattausan silifas dake sawunsa.

ya nufi can gefen yamma inda wasu kyawawan bukoki na zamani da yake wajen hutuwansa,

Wurine mai kyau da ban sha'awa a hankali ya zauna bisa ɗaya daga kujerin dake cikin bukkar da tafi
sauran ƙawayuwa da flawers.

A hankali yake motsa lips ɗinsa alamun yana tasbihi yalwataccen sumar kansa kamar na larabawa na
sheƙi da ɗaukar ido idanunsa na lumshe yana motsa bakinsa a hankali.

Cikin nutsuwa Asma'u da Khausar suka fito duk da rawan kai irin na Khausar komai nata anitse takeyi
cikin nutsuwa suke tafiya yayinda hijabansu yarufe har takalmansu adedeta suka tara tare da sanar dasu
inda ze kaisu.

Tafiyar Mintuna ashirin da biyar sukayi suka isa aƙofar gidan.

A gaban gate ɗin adedeta ya ajiyesu.

Asma'u ce agaba tasa hannunta da babu komai ta tura ƙofan gate ɗin yayin da ɗaya hannu ke riƙe da
Kula wanda Ummi ta yiwa Innayi dambun naman kaza.

Cikin wani irin shauƙi Khausar ke bin ilahirin gidan da kallo ganin yanda flowes da shuke shuken kayan
marmari suka zagaye gidan tamkar garden,

Da sauri ta juyo da kallonta kan Asma'u tare da cewa.

“Wooow masha Allah.

Kai Asma'u wannan gidan waye haka? gaskiya yayi kyau sosai”.

ta ƙare mgnar tana lumshe idanunta tare da shaƙar sassayan iskar dake haɗe da ƙamshi flawers da kuma
turare jikin Moddibo.

Kana ta riƙa bin fulawowin tana shafa duk wanda hannunta ya sauƙa akai saita tsinke takai hancinta kana
taja dogon numfashi tare da lumshe ido.

Shi kuwa Moddibo tun ƙarar buɗe gate ɗin da yayi ya ɗago kansa yana kallon wajen.

Cikin mamaki yace


“Khausar Usman Lelelwal a gidan nan”.

Hannunsa yasa ya tallabe habarsa tare tsuke fuskarsa.

Ita kuwa Khausar cike da shauki ta buɗe hannunta tare da jujjuyawa har hijabinta na buɗuwa cikin ɗan
ɗaga sauti tace.

“Agaski Asma'u gidan nan ya min komai na ciki sun burgeni gawani irin ƙamshi da suke, ji yanda ilahirin
gidan ke fitar da wani ni'imantaccen ƙamshi.

Gaskiya gidan nan shine aljannar duniya da alamu kuma mutanen ciki maƙurane wajen tsabta ina son
komai na gidan nan”.

Asma'u Kam dariyar dake cinta take ƙunshewa ta tabbata da Khausar tasan cewa gidansu Moddibo ne
babu dalilin dazai kawota sannan ta tabbata yau juma'a ya irin wannan lokacin Moddibo na gida babu
inda zeje.

Ita kuwa Khausar juyi ta cigaba da yi tare da sauri ta nufi side din Moddibo steps din ta fara tattaunawa
tana shafa furannin dake jere a kan.

Saida ta hau har tsakiyar barandar kana ta juyo ta fuskanci yama.

“Wooww Masha Allah Asma'u zo ki hau ki gani wlh ina hango bakin Teku kinga yadda ruwa da tsuntsaye
keyi!".

Ita dai Asma'u hannunta tasa ta rufe bakinta tana murmushi.

Yayinda tun shigowarsu Moddibo ya zuba musu idanu saidai sam su basu lura dashi ba,da gudu Khausar
ta juya ta fara taka steps din tana sauƙa ta nufi sashen da Moddibo ke zaune tana faɗin.

“Wowww gaskiya wannan gidan yayi mugun yimin kyau da ace zan rayu a ciki da wanda raina zaiso zan
meda mishi gidan tamkar dausayin farin cikin duniya”.

Cikin danne dariya Asmau tace.

“Khausar zomu tafi mana”.

kai Khausar ta girgiza tace.

“A'a ki tafi ni wlh saina cire inabin can da Appel kije kawai”.

Ahankali Asma'u tace.


“Kizo muje mugaida Innayi sai mu gaya mata kafin ki cire”.

dan tasan a irin wannan lokacin tabbas Moddibo na nan shiyasa take mgn a hankali wai dan kar ya jisu.

Kai Asma'u ta dafe tare da cewa.

“Idan masu gidan kuma suka zo suka sameki fa?”.

Taɓe baki Khausar tayi tace.

“Gida kamar wannan masushi bazasuyi rowa ba, kuma ai nan kamar babu kowa babu wanda zaizo”.

ta faɗa tana komawa inda inabi yake tasa hannu ta fara tsinka tana tsalle jin hijabinta zai takurata ne
yasa ta zare hijabin tare da ajiyeshi kan kujerar dake ƙasan bishiyar.

Middibo kuwa dafe kunci yayi yana ganin ikon Allah Aransa yace.

“Yarinya kamar ba mace ba dubi yanda take tsalle kamar biri wannan ba budurciba abinda yafi
budurcima zata watsar domin yasan illar hawa bishiya yakan buɗa mace duk da cewa ita ba hawan tayi
ba.

Tunaninsa ne yakatse asanda ta nufi bishiyar Appel tsalle tayi da niyyar tsinkowa dan bishiyar Appel irin
yan masaƙaitan nanne,

tsalle ta kuma yi amman ta kasa ga dai hannunta na taɓawa sede baza ta iya tsinka ba.

tattare gashinta tayi tare da dan mai dashi bayan wuyanta kana ta nannaɗe ƙafar wandonta,

tsalle tayi tare da kamo rashen da yafi kusa,

sai kuma ta hango wasu a can sama haka yasa ta fara taka jikin bishiyar har ta hau bisa rashen duk da ba
wani tsowone da shiba,

Cal sai gata akan bishiyar.

Cikin tsananin takaici da sassarfa ya mike tare da nufar wajen, yasan koda yace zeyi mata tsawa
muryarsa baze fita ba saboda bashida da amo mai karfi sannan yasan dai baya cikin tarbiyya mai.kyau ƴa
mace tai ta hawe-haween bishi yana isa bakin bishiyar ya tsaya tare da harɗe hannayensa aƙirji kafin
yayi magana ta juyo da niyyar kai hannu zata tsinki appel sukayi ido huɗu dashi ido cikin ido sukayi
kamar yadda damisa kan iya tsare kenwa da ido haka yayi mata.

Cikin tsananin firgici da tsoro da kaduwa tace.

“Hasbunallahu wani'imal wakin,


Aizubillahi Minal shaiɗanirrajim, innahu min sulaimanu wa innahu Bismillahir rahmanir rahim”.

Cikin tsananin tsoro take jera addu'o'in domin gani take shin fatalwane ko kuma aljan yazo mata
asuffarsa cikin kiɗima da firgici ta rikito tayi ƙasa ta faɗo gababsa yayin da hannayenta suka sauƙa
akan.....!

Kada dai ku shagala wannan duk garaɓasar FREE PAGE. Labarin sashi-sashi gareshi. Ko wacce kusufa da
darasin dake ƙunshe a ciki. Al'amarin babbane fa babu abinda babu cikin lbrin

Inada lbri na musamman

Wanda nake son in rubuta in Allah yaso ya yarda ya bani aron rai da lfy da dama.

In na gama TUBALI.

Zafin labarin kan sani inji Tamkar in aje TUBALI na fara wancan ɗin

*SAKAYYAH*

lbri ne mai cike da abubuwa na musamman masu tarin rikitarwa al'ajami matsalar kasarmu kalubale
masautu.

Taraddadin rayuwa, tsaka mai wuya, tsubucewar dama da samunta,

Nesanta da kusanta, tausayi, kuka, dariya, barkwamci, iko, isa, mallaka, kasaita, kekkyawan ilimin addini,
da aiki dashi, fasadi, zalumci, shirka da sakamonta, kalubalen dalibai ga Malami, matsalar , yadda ya
kamata gomnati da jami'an tsaro da masarautun gargajiya su juyo kam lamarin bindiga Dadi Zazzafar
soyayya mai kekkyawan tubalin raino a ɓoye!!!.

Ya Salam Labarin ya rusa min tunanin da nake cewa bazan sake wani littafi Mai kamar GARKUWA ba sai
gashi in second's Allah ya buda min tunanin na harhaɗo Labarin *SAKAYYAH. FATTANAH kenan.*

Amman sai dai kuwa kusan wani Abu!??!


In kuna son sani ku biya 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar
biyanki ta WHATSAPP 09097853276. In kin biya kikuma bibiyeni zakusha al'ajab.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_Page 4_

*NA*

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*Free page*

*KADA DAI KU MANTA WANNAN FREE PAGE NE, KI KI BIYA KI KARANTA CIKIB AMINCI BA HAƘƘIN WANI
GABA GAREKI SAKAYYAH 1k ne kacal ƴar uwa. 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo
min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*

*Al'bishirunku Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku


ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA Ɗiyar ALIYU GARKUWA.


Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce,
akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna
uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin
yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace
ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa
bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore
ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaici, ta kuma dorar da mijinta kan turbar
gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san
hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa
tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan
mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina
mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka
yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke
taimakawa (sex hormones 😍) dinki.

Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin
soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?

Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da
ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa
domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.

Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?

Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar
amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin
mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar
mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,

Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ji zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke
mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan set ɗin 10k ne kacal wlh koda sanyin
mahaifane in sha Allah zakiji saukin.

Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta
akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.

Akwai ɗaya bangaren wato *KAMSHI*


Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne
masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na
daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka
ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar
da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, kana da
kulaccar sirri sayan na gari maida kuɗi gida, banda harkar karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276
domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA
ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba
Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA


😘

*(GARKUWAR MA'AURATA)*

Tana dirowa hannunta dake dungule da Appel suka sauƙa kan ƙafarsa.

Yayinda yatsun hannunta dake ɗauke da zoban azurfa na kusa da da ƙaramin yatsa da kuma ƙaramin
suka sauƙa akan faratun yatsun sa,

atake yatsun hannunta suka bada sautin ƙash! yayin da shi ma Moddibo yatsun ƙafansa suka bada sautin
ƙas-ƙas!, Idanshi ya rumtse da sauri, sabida wani irin masifaffen zogi da yaji ya ratsa sa cikin sauri ya
tsugunna da niyyan matsasu tuni ɗanƙwalin ta ya zame yalwataccen sumar kanta baƙi daya sauƙa zuwa
kafarɗarta ya zubo yana fitar da wani sihirtaccen ƙamshi...

Khausar kuwa jin zafin daya ratsa ƙafarta data malkoɗe ne yasa ta furta.

“Wayyyo Allah ƙafata!”. ta faɗa da ƙarfi tare da ɗago kanta yayin da yalwataccen sumar kanta ya rufe
mata fuska da sauri tasa hannu ta janye ta ɗago kanta.

Idanunta ne suka sauƙa akan Moddibo dake durƙushe, cikin ruɗewa da tsanananin tsoronsa ta ɗauki
ɗan kwalinta kana ta miƙe da gudu tana cewa.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n dan Allah kayi haƙuri wallahi Allah bansani ba”.
Ta faɗa tana ƙoƙarin fita daga gate ɗin.

Asma'u kuwa fitowarta daga gate ɗin da zai sadaka da cikin farfajiyar Innayi kenan ta hango Khausar na
shirin fita babu ɗan kwali akanta.

Cikin Sassarfa tabi bayanta tana faɗin.

“Khausar! Khausar!! Khausar!!!”.

ta kira sunanta har sau uku Kafin ta sake cewa.

“Dan Allah kada ki fita ahaka Khausar ki tsaya”.

Moddibo kuwa cikin yanayin nutsuwarsa da kuma sanyinsa ya kira sunanta da faɗin.

“Asma'u”.

Saidai akwai alamun ɓacin rai acikin sautin Muryansa.

Atsorace Asma'u ta juya Idanunta cike da tsoro tace.

“Na'am Yah Moddibo”.

Tsayuwarsa ya gyara tare da lumshe idanunsa masu ƙwarjini da haiba kana ya buɗe su ya dubi Asma'u
da har yanzu take tsaye da tsoro a idanunta yace.

“Meyesa zaki ɗauko Biri ki kawo mana gida!?”.

Ya ƙare mgnar da bin Khausar da ido wacce tuni ta kai bakin gate.

Asma'u kuwa saurin ɗagowa tayi ta dubesa jin ya kira Khausar da Biri saidai bata yarda sun haɗa ido ba.

Shi kuwa cike da takaici

ya cigaba da cewa.

“Koda wasa kada ki sake zuwa da wannan yarinyar gidan nan, tunda ita bata da hankali da kuma
nutsuwa da kamun kai”.

Ya ƙarashe mgnar yana mai lumshe idanunsa dake cike da ƙwarjini har zuwa sannan yatsun ƙafar na
masa rawa tamkar alokacin ta buga masa yatsunsa.
Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe ganin tuni Khausar ta fice kanta a ƙasa tace.

“Dan Allah kayi haƙuri Insha Allah hakan bazai sake faruwa ba”.

Moddibo kuwa baice da ita Komai ba saima lumshe idanunsa da yayi yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi
yaci gaba da yi.

Ita kuwa Asma'u jin baice komai ba yasa ta juya cikin sassarfa ta nufi gate dan bin bayan Khausar...

M Jameel dake zaune cikin falon Moddibo kuwa wanda ya tsirawa window idanu yana ganin duk abinda
ya faru ya saki lallausan murmushi tare da miƙewa yana gyara zaman Farin t-shirt da blue jeans dake
jikinsa kana ya sanya hannu ya buɗe ƙofan falon ya fito fuskarsa ɗauke da ƙayataccen murmushi cikin
yanayin sa na ƙaunar Amininsa yace.

“Ba sa ido ba?,ka fita sabgar yarinya ka ƙi yanzu inba sa'a ba kasa taji ciwo dan naga lokacin da take gudu
tana ɗin gishi”.

Moddibo kuwa buɗe idanunsa dake lumshe yayi tare da zab gawa M Jameel Harara cikin yanayin
nutsuwarsa daya zame masa jiki yace.

“Dama karyewa tayi da shi yafi yarinya bataji bata da hankali ko kaɗan”.

Da gudu Asma'u ke bin Khausar tana cewa.

“Khausar ki jira ni mana”.

Ƙin tanka mata Khausar tayi tana cigaba da sassarfa yayin da ko wani gaɓa na jikinta ke rawa kana tana
cigaba da ɗaure gashinta daya baje kasancewar unguwa ce da babu hayaniyar mutane yayin da take
yarfe hannunta dake masifar zugi kana tana me ɗingisa ƙafarta.

Ganin da gaske Khausar ba zata tsaya ba yasa Asma'u ta ƙara gudunta har ta isa inda take tana sauƙe
numfashi saboda gudun da tayi tace.

“Ayyah Khausar ki tsaya mana ga hijabinki saka”.

Hannunta tasa ta amshi hijabin nata tare da zirashi a jikinta kana taci gaba da tafi.

“Ayyah Khausar ki tsaya mana”.

Asma'u ta kuma faɗa tare da shan gabanta,


a raunane tace.

“Bazan tsaya ba Asma'u meyesa zaki min haka Asma'u? banyi tsammanin zaki yimin haka ba gidansu
Moddibo kika kawoni mutumin da kin san baya ko son ganina.

Gashi yanzu kinsa na buga masa yatsuna masu zobe aƙafa naji masa ciwo,yanzu bansan wani irin
hukunci zai ɗauka akaina ba”.

Tsoron Khausar ɗaya kada Moddibo yace zai zaneta duk irin rashin ji da ƙiriniyarta tana matuƙar tsoron
bulala kana tasan duk hukuncin da Moddibo zai ɗauka bazai wuce yasa Malam Bello ya zaneta idan taje
Hadda.

Cikin sanyin murya Asma'u tace.

“Ayyah Khausar kiyi haƙuri, amman kuma ai da kinji mgnata da haka bai faruba. kece bakya ji sannan ba
kyaso ataɓa lafiyar jikinki”.

Kallonta Khausar tayi da Idanunta dake cike da tsoro da kuma fargaba tace.

“Meyesa zaki ce haka Asma'u kawai naga Appel da inabin ne ya ban sha'awa shiyasa na cira”.

Kai Asma'u ta girgiza tace.

“Inabi Khausar? na tabbata duk wannan abubuwan da kika gani akwai su a gidanku ku fiye ma da
hakan”.

Sake Marerece fuska Khausar tayi tace.

“Na ganine ya bani sha'awa laifi ne dan na cire!?”.

Murmushi Asma'u tayi ganin har zuwa lokacin Atsorace Khausar take sai kuma tace.

“Kema dai baki jira kanki ba daga zuwa gidan mutane sai ki fara cire musu abu batare da neman izini ba”.

Ita kuwa khausar jin abinda Asma'u tace yasa ta watsa mata Harara cike da tsiwa tace
“Tun da kinsan gidan masu baƙin hali zaki je Meyesa zaki ɗaukeni ki kaini?, Kisa aranki daga yau babu
inda zan sake rakaki tunda haka kikayi min”.

Wara ido Asma'u tayi sai kuma ta langwaɓar da kai tace.

“Kiyi haƙuri Khausar bansan haka zai faru ba ni kawai da niyyar mu gaida Innayi nace ki raka ni amma
kada kice baza ki sake raka niba na tuba”.

Kallonta kawai Khausar tayi amma ba tace komai ba, sake langwaɓar da kai Asma'u tayi cike da
tausayinta tace.

“Ki zauna awancan dakalin se inja miki ƙafar!”

Kai Khausar ta girgiza tana rintse Idanunta tace.

“Basai kin ja minba kawai sama mana adedeta mu hau”.

Kai Asma'u ta jinjina tare da riƙe hannunta suka ɗan tsaya bakin titi cikin sa'a tsayuwar su babu daɗewa
suka samu adedeta hawa sukayi tare da yimasa kwatancen inda ze kaisu...

Aƙofar gida me Adedeta ya sauƙe su bayan sun isa Asma'u ce ta ciro kuɗi ta basa kana ta riƙe hannun
Khausar suka nufi gate Khausar ce tasa hannu ta tura gate ɗin cikin rashin sani suka buge juna da Samira
Sani wacce ke ƙoƙarin fita Amina na biye da ita.

Saurin ɗago kai Khausar tayi jin Samira Sani na cewa.

Ke 'yar uban waye da zaki haɗa kafaɗa dani shin dame kike taƙama!?”.

Kamar Khausar za tace wani abu sai kuma ta fasa taja siririn tsaki tare da jan hannu Asma'u suka bar
wajen tana me cigaba da ɗingisa ƙafarta.

Ƙwafa Samira Sani tayi cikin kumfar baki tare da tsanan Khausar aranta tace da Amina.

“Wallahi na tsani wannan shegiyar yarinyar me kama da sadaka yalla Idan ban sabautata ba bazan taɓa
samun nutsuwa ba!”.

Tsaki Amina taja tana kallon Samira tace.

“Allah ne kaɗai yasan irin abinda zan mata”.


Kafin su ƙarasa shiga falon Khausar ta janye hannunta dake cikin na Asma'u kana ta gyara tsayuwar tare
da dai-dai ta tafiyarta tana me rintse Idanunta sam bataso Momy ta fahimci abinda ya sameta.

Asma'u kuwa kallon ta tayi cike da tausayinta amma batace komai ba Ƙofan falon suka tura

suka shiga tare da haɗa baki wajen cewa.

“Assalamu Alaikum”.

Momy dake zaune kan kujera ta ɗaura ɗaya kan ɗaya ce ta faɗaɗa Murmushin fuskarta tace.

“Wa'alaikum salam har kun dawo?”.

Zama suka yi daga gefen ƙafarta aƙasan chanis capet Asma'u tace.

“Eh Momy”.

“Masha Allah ya jikin Innayin?”.

Cewar Mommy.

Khausar na ƙoƙarin miƙewa tace.

“Da sauƙi Momy” Sannan ta nufi Bedroom ɗin ta da sauri Asma'u ta miƙe tabi bayanta.

Bakinta ɗauke da sallama tashiga ɗakin nata kana tayi saurin ɗin gisa ƙafarta se kuma ta kwanta agefen
gadonta dake shimfiɗe da white bedsheet tana sakin ajiyar zuciya akai-akai alamar har yanzu akwai tsoro
atare da ita.

Zama Asma'u tayi agefenta ganin yanda ƙafan Khausar ke rawa yasa tace.

“Bari na ɗebo ruwan ɗumi na matsa miki”.

Kai Khausar ta girgiza da faɗin.

“A'a ga can man zafi agaban mirrow ki ɗauka min na shafa”.

Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta ɗauko man zafin ta ɓude kana ta kama ƙafar Khausar tana mulka
mata.
Khausar kuwa rintse Idanunta tayi tanajin zafin man na ratsa jikinta yayin da aƙasan zuciyarta tsakanin
tsoro da firgicin hukuncin da Moddibo ze ɗauka akan tane.

Asma'u kuwa hira ta riƙa yiwa Khausar na ɗebe kewa kana daga bisani ta miƙe ganin yamma tayi seda ta
biya ta kichen ta sake yiwa Momy Sallama kana ta tafi.

Khausar kuwa yanayin zogin da ƙafarta da kuma hannunta ke mata yasa bayan tafiyar Asma'u ba jimawa
bacci ya ɗauke ta...

Ita kuwa Momy ganin har maghariba tayi bata jiyo motsin Khausar kuma bata nemi Raudat suyi salla ba
se abin ya bata mamaki bayan ta idar da Sallah ta fito daga Bedroom ɗinta Kai tsaye Bedroom ɗin
Khausar ta nufa,

bakinta ɗauke da sallama ganin Khausar na bacci yasa ta ƙarasa bakin gadon tare da taɓa fuskarta da
hannunta dake da damshin ruwa ruwa tana kiran sunanta da faɗin.

“Khausar! Khausar!! Khausar tashi kiyi Sallah maghariba tayi”.

Momy ke faɗa tana me sake shafa fuskarta da hannunta dake da damshin ruwa.

jin muryan Momy da kuma damshin hannunta da take shafa fuskarta yasa ta buɗe Idanunta ahankali
tace.

“Na tashi Momy”.

Juyawa Momy tayi ta fita ita kuwa khausar miƙewa tayi tare da furta.

“Alhamdulillah”,Jin babu ciwo da Zugin da ƙafar ke mata se kuma hannun data ji ya sake baki ɗaya
tamkar ba ajikinta yake ba.

Ta lumshe lumsassun idanunta kana ta miƙe ta nufi toilet tana me furta.

“Allahumma Inni Auzubika Minal khubsi wal khaba'is”.

Kana tashiga cikin toilet ɗin da komai ke akimtse yana fitar da wani irin ƙamshi Anutse tashiga yin
alwalan har ta ida kana ta fito bayan ta furta.

“Gufra naka”.
Bayan ta gabatar da Salla tayi adduo'i ta miƙe tare da naɗe darduman se kuma ta juya ta fice tana me
buɗe hannunta da rufewa koda ze dawo dai-dai...

Zaune ta samu Momy kan kujera hannunta riƙe da hisnul Muslim tana Azkharul Masa,Yayin da Raudat ke
gefenta daga ƙasa tana bin bakinta zama Khausar tayi daga gefen Raudat kanta aƙasa tace.

“Momy gobe zan tafi JAURO YAYAH”.

Da mamaki Momy ta zuba mata ido jin mgnar a bakatatam cike da mmki tace.

“Zaki tafi Jauro yaya kuma Khausar?”.

Ataƙaice Khausar tace.

“Eh”.

tana mai cigaba da jan yatsun hannunta.

Momy ta sake duban ta da mamaki akaro na biyu tace.

“Anma babu yanda banyi dake ba jiya kan cewa kishirya yau kutafi tunda mutanen garinsu na zuwa
sallan jumma'a sosai ku tafi tare, kika ce ba zaki tafi dasu ba kuna hadda, sannan kun kusa zuwa ƙarshen
surar idan kika tafi karatun ki ze koma baya sannan na yarda na barki kan cewa se sati me zuwa yanzu
kuma kice zaki tafi gobe”.

Murmushi ta ƙaƙalo tare da faɗin.

“A'a Momy babu damuwa munyi magana da Asma'u tace koda awaya zan iya ƙarawa da kaina batare da
anwuce Ni ba”.

Dubanta Momy tayi tare da cewa.

“Kin tabbata Khausar har cikin ranki kikeson zuwa Jauro Yaya!?”.

Kai ta gyaɗa tace.

“Eh”.

Aranta kuwa cewa tayi ba gwara masifar wancan tsohuwar ba dan ko yaya bazan tsaya ta dake niba
amma wannan mutumin ya riƙa tsareka da firgitattun idanunsa masu saka tsoro da fargaba, baya ga
haka in banyi sa'a ba duka na zai sa ayi banyi masa lefi bama idan yasamu sarari sawa yake aci zalina
bare kuma nayi masa laifi...

Muryan Momy dake cewa.

“Toh shikenan nima nafi so ki tafi Kinga idan hutun ku ya ƙare sannan anƙarasa muku gyaran makaranta
seki dawo”.

Ya dawo da ita daga duniyar data lula.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Shikenan Momy”, Sannan ta miƙe ta shiga Bedroom ɗin ta.

Momy kuwa Hisnul Muslim ta ɗauka ta cigaba da Azkhar yayin da Raudat ta miƙe tabi bayan Khausar.

Ita kuwa khausar na shiga ɗaki ta hau kan stoll ta janyo trolley ɗin ta sannan tashiga haɗa kaya Raudat
dake kallonta tace.

”Dani Zaki tafi Addah Khausi?”.

Girgiza mata kai Khausar tayi alamar a'a.

Kuka Raudat ta fashe dashi tana cewa.

“Ni zan biki”.

Zama Khausar tayi ta riƙe hannunta tare da langwaɓar da kai tace.

“Raudat garin bashi da daɗi fa, ga tsohuwar garin ta fiye masifa, kana yi mata kuskure kaɗan zata zane
Mutum”.

Jin haka yasa Raudat ta girgiza kai tace.

“Nide ba zanje ba idan haka ne”.

Aɓangaren Momy kuwa bayan tashiga turakar Lamiɗo sunyi shirin kwanciya ta dubesa fuskarta ɗauke da
murmushi me sanyi tace.
“Uhum wai ɗazu Khausar ke cemin idan Allah yakaimu gobe tana son zuwa Rugar Jauro Yaya”.

Zamanshi ya gyara tare da faɗaɗa Murmushin dake fuskarsa kana yace.

“Allah ya kaimu hakan nada kyau idan yaso tunda gobe weekend ne zamuje dukan mu kema sai ku gaisa
tunda kinyi shekaru baki jeba”.

Kai ta jinjina kafin tace.

“Kai naji dadi Allah ya kaimu”.

Amin yace kana sukaci gaba da hirarsu.

Washe gari Ya kama asabar da wuri Khausar ta tashi ta gyara ɗakinta sannan ta nufi ɗakin Momy ta
gyara kana ta share har zuwa falo da kuma duk sashen saida ta gyara ko wani lungu da saƙo.

Bayan ta gama ta dawo ta shiga kichen ta zuba musu Breakfast soyayyan cheaps da tea ita da Raudat ke
ciki.

Bayan sun kammala ta miƙe tana ƙoƙarin tattare wajen Momy tashigo Idanunta akan Khausar.

fuska ta ɗan tsuke tare da faɗin.

“Maza kije yanzu Aunty Jamila tayi Miki kitso”.

Aunty Jamila matar ƙani Lamiɗo ne sannan Momy tasan inba tayiwa Khausar dagaske to baza taje ba
domin bata ƙaunar kitso.

Ganin fuskar Momy babu walwala yasa Khausar gyaɗa kai tare da shiga Bedroom ta ɗauko dogon
hijabinta fari Nevy blue daya sha ninkin guga ta ɗaura akan riga da wandon dake jikinta kana ta fice ta
nufi gidan Aunty Jamila tana zumɓura baki da kuma kifiya da kum a hannunta.

Bakinta ɗauke da sallama tashiga gidan, Aunty Jamila dake zaune ta amsa Sallamar tana faɗaɗa fara'ar
dake fuskarta tace.

“A'a Khausar kece?, sannu da zuwa”.

Sake fuska Khausar ta ɗanyi tace.

“Eh nice Aunty wai kitso nazo kiyi min zanje Jauro Yaya”.
Murmushi Aunty Jamila tayi tare da cewa

“Masha Allah kice zakije ziyara?”.

Kai Khausar ta gyaɗa tana murmushi.

Cikin sakin fuska Aunty Jamila tace.

“Allah Ya kaiku lafiya".

“Amin ya rabbil izzati”.

Cewar Khausar.

“Kinga kuwa kinyi sa'a duk na gama aiyuka na”.

Da sauri tace.

“Aunty Jamila manya fa zakiyi shida ko takwas”.

Murmushi Aunty Jamila tayi.

Kana ta miƙe ta shiga ɗaƙi tare da kwantar da yaronta kana ta fito,

Akan kujeran roba Khausar ta zauna ita kuma ta tsaya ta fara yi mata kitson suna cikin kitson ne suka jiyo
Sallamar Gimbiya Dadu.

Anutse Aunty Jamila ta ɗago kanta fuskarta ɗauke da murmushi tace.

“Sannu da zuwa Mama”.

Asaman laɓɓa Gimbiya Dadu ta Amsawa Aunty Jamila baki ɗaya nutsuwarta da hankalinta suna kan
Khausar.

Miƙewa Aunty Jamila tayi tashiga ɗaki dan ɗaukowa Gimbiya Dadu Darduman zama.

Ita kuwa khausar ahankali ta ɗago kanta caraf Idanunta suka sauƙa akan Gimbiya Dadu data tsareta da
ido ita kuwa khausar cikin hanzari tayi ƙasa da idanunta tana mai karanto duk wata addu'ar da tazo
bakinta kamar minti ɗaya Khausar ta sake ɗago kanta akaro na uku still Idanun Gimbiya Dadu na kanta.

Ita kuwa khausar kasa jurewa tayi ta tsayar da Idanunta akan Gimbiya Dadu cikin dakiya tace.

“Wai dan Allah Gimbiya Dadu Meyesa kike kallona haka?”.


Wani murmushi mai cike da ma'anoni Gimbiya Dadu tayi tare da cewa.

“Uhum yaro man kaza,

ai tunda kika bar cikin Awaki 'yan uwanki kika dawo cikin Kuraye ai dole akalleki! In kalleki in kuma”.

jin abinda Gimbiya Dadu tace yasa ta miƙe cikin rawan jiki da alamar tsoro aƙwayar Idanunta ta sanya
hijabinta ta fita batare data jira Aunty Jamila ta fito ta ƙarasa yi mata kitson ba...

Sauri-sauri gudu-gudu take tafiya har ta isa bakin gate dinsu da sassarfa ta shigo coumpund ɗin su har
yanzu jikinta be daina ɓari ba tana gyara zaman hijabin kanta Momy ta fito,Kallonta Momy tayi tare da
cewa.

“Har angama kitson ne".

Ka ta gyaɗa mata ba tare da tace komai ba.

“Dama yanzu zan aika Haiydar ya kira ki kizo mu tafi”.

Murmushin karfin hali ts ƙirƙira kana tace.

“Eh mun gama”.

Wuce ta Momy tayi taje tashiga gaban mota Ita kuwa khausar kallon Raudat, Ramadan, da kuma Haiydar
dake tsaye tayi tare da ɗaga musu hannu suma hannu suka ɗaga mata ahankali ta juya ta nufi wajen
motar tana isa tasa hannu ta buɗe tashiga gidan baya Haiydar da Ramadan na cigaba da ɗaga mata
hannun.

Babban gate mai gadin ya buɗe musu kana Lamiɗo ya cilla hancin motarsa.

Khausar kuwa jingina bayanta ajikin motar tayi tare da lumshe Idanunta zuciyarta na bugawa da mugun
sauri abu biyu ne suka yiwa zuciyarta ƙawanya na farko hukuncin da Moddibo zai ɗauka akanta na biyu
kalaman Gimbiya Dadu wanda suke ƙara tabbatar mata da zantuka dake yawo a gari cewa matar nan
mayyace...

Anutse Momy ta dubi Moddibo dake sharara gudu akan Lafiyayyan titin nasu tace.

“Abban Haiydar gudun nan baiyi yawa ba”.

Kanshi ya ɗan jujjuya mata,

Ita kuwa cikin sanyi tace.


“Gsky dai ka rage gudun kamar yayi yawa”.

Juyowa yayi ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace.

“Lokaci na tafiya kinga yanzu goma tayi gwara mu isa da wuri kada rana tayi mana mu samu mu juyo da
wuri”.

Kai ta gyaɗa kafin tace.

“Amma duk da haka arage gudun".

Tattausan murmushin ya sakar mata tare da gyaɗa kai...

Sunyi tafiya mai tsawo kafin suka fara hango garin Atake suka fara tabbatar da sanyin da ake acikin
Gembila wasa ne.

Domin tun kafin su shiga garin suka hango tamkar hayaƙi ke tashi saboda masifaffen sanyin da ake
tsugawa acikin Jauro yaya suna shiga cikin garin suka fara ratsa bishiyoyi masu korayen ganye suna
rangaji tare da fitar da sanyayyan Iska kasancewar hantsi ne duk makiyaya sun tafi se kuma,

'yan dalo da aka ɗaɗɗaure masu kyan launi ga kuma kukan tsuntsaye dana zabbi da ke tashi suna ajiye
ƙwai.

Suna shiga tsakiyar Rugar Jauro,

kai tsaye ƙofar gidan dake kusa da babbar fadan Rugar suka nufa anan sukayi parking motar tare da
fitowa.

Wasu dattawa dake zaune aƙofan masallacin dake kusa da babbar fadan suka taso baki ɗaya idanun su
akan Khausar data fito daga mota tana gyara zaman hijabinta suna faɗin.

“Audiii Barka da zuwa kece?”.

ɗaya daga cikin dattijon ne ya taso wanda ya kasance shine Jauron garin ya riƙe hannun Khausar.

Fuskarsa ɗauke da murmushi yake faɗin.

”Addah, Addah, Addah, kizo ga Khausar”.

sauran ma bin bayansu sukayi zuwa cikin gidan suna masuyiwa Momy da Lamido Barka da zuwa.
Biyu daga cikine suka ce da Momy da kuma Lamiɗo.

“Sannunku da zuwa ya kuka tsaya ku shigo daga ciki”.

Kai Momy ta gyaɗa kana suka yi musu godiya bisa jagoranci suka nufi cikin gidan.

Jauro kuwa yana riƙe da hannun Khausar yana mata wasa da faɗin.

“Iyeee girman falo ji jiki kamar auduga,

bakisan riƙe sandar kiwo ba sannan baki san ta tsar nono ba girman burodi wayon shayi kawai”.

Ita kuwa khausar hannu ta wara da faɗin.

“Ban iya ba kam”.

Murmushi yayi kana yace.

“Zamu koya muki ai”.

maƙale kafaɗa tayi tace.

“Bana so ba kace min girman bread wayon tea ba”.

Murmushi yay i tare da cewa.

“To girman fura da nono”.

Akuma dai-dai lokacin suka shiga ɗakin tsohuwar wanda yake ginin gargajiya shatin kobo.

Suna shiga Jauro yace. “Addah ga 'yar Usman tazo”.

Ya mutse fuska Hajja Nana tayi tare da kallon Khausar tace.

“Shegiyar kaya me wuyar ɗauka se yau kika ga damar zuwa??”.

Murmushi Jauro yayi still hannunsa na cikin na Khausar yace.

“Tazo da mahaifiyarta da kuma Mahaifinta”.

Wani kallo Hajja Nana ta masa tare da cewa.

“Kai Jauro ka gyara kalamanka,


badai mahaifinta ba mahaifin riƙo dai ko? ka manta mahaifinta da kai aka binnesa shekaru goma sha
biyar da suka wuce?”.

Kai ya jinjina alamar hakane amma bece komai ba ita kuwa miƙewa tayi ta ɗauko taburma ta shimfida
tare da ɗauko darduman kilisa ta shimfiɗa.

A kuma lokacin Momy da Lamiɗo suka shigo cikin sakin fuska tashiga yi musu lale marhaba.

zama Momy da Lamiɗo sukayi akan shimfiɗar data musu kana ita kuma ta zauna awajen zamanta na
farko yayin da duka ƙannenta maza suka zauna daga bayanta se ta zamto tamkar sarauniya acikinsu ko
wannensu fuskarsa ɗauke da murmushi yake faɗin.

“Addah yau kam ga Khausar tazo”.

Haka yasa ta juyu.

Ta dubi Khausar da alamun farin cikin ganinta afuskarta saidai yanayin zafinta bazai sa ka fahimta ba.

Ta dubi Khausar da tayi kicin-kicin da fuska tace.

“Menene kike wani kumbura fuska? gwara ma ki saki ranki fa”.

Zumɓura baki Khausar tayi saidai ba tace komaiba.

Hajja Nana kuwa sake kallon Khausar tayi akaro na barkatai tace.

“Ki tashi ki kawo ma baƙi abin taɓawa”.

Lumshe idanu tayi kafin tace.

“Nice zan kawo abin taɓa wa?,Nima ai baƙuwa ce akawo mana dai”.

“Ina magana kina magana!?”.

Hajja Nana ta fadi a faɗace.

Cikin tura baki tace.

“Ai gaskiyane”.

Danƙolo Momy ta yiwa Khausar hakan yasa ta tsuke bakinta.


Ɗaya daga cikin ƙannen Hajja Nana wanda ya kasance shine ƙaramin su (Autah)ya miƙe da faɗin.

“To bari na kawo musu”.

Sannan ya shige uwar ɗakan Hajja Nana ba daɗewa ya fito hannunsa riƙe da Akwashi ya ajiye agabansu
sannan ya koma ya ɗauko goran zuma kana ya koma ya sake ɗauko wani Akwashin.

Hajja Nana ta dubi Momy tare da cewa.

“Ayyah wallahi ban san da zuwanku ba”.

Kai Momy ta gyaɗa tare da cewa.

“Ai inata gwada kiran layin ki baya shiga”.

Murmushi Hajja Nana tayi kana tace.

“Kinsan Rugar tamu bamu da network se kaje bishiyar ƙare zancenka in kaje bishiyar ma seka hau sama
ni kuma ban cika son zuwa ba da girmana Inje in hau bishiya na faɗo”.

Khausar kuwa taɓe baki tayi tace.

“Hmmm ba network kuma har sai anje wani bishiya?”.

Harara Hajja Nana ta watsa mata ta cigaba da cewa.

“Wallahi bansan da zuwan kuba dana shirya muku abin taɓa wa”.

Murmushi Momy tayi batace Komai ba.

Akwashin da aka shigo dashi ne Autansu Hajja Nana ta buɗe Nono ne me zafi yana tururi ga kuma goran
zuma dake gefe ɗayan kuma daya buɗe ɗumamen danɗerun zabbi ne suna tururi.

Sauran mazan dake kewaye da Hajja Nana ce suka shiga Gaisawa dasu Lamiɗo.

Muskutawa Hajja Nana tayi tare da gyara zamanta ta kalli Lamiɗo dake zaune ya tanƙwashe ƙafafunsa
tace.

Wa'annan daka ke kallo duka ƙannena ne mu goma ne acikin mahaifiyarmu gaba ɗayansu Mazane ni
Kaɗai ce mace kuma nice 'yar Fari.
Jinjina kai Lamiɗo yayi yana sauraronta da duka nutsuwarsa duk da yasa abinda take faɗa kishin. tunda
ba yaune zuwansa na firkoba.

Ita ko Hajja Nana nuna wanda ke gefenta tayi tare da cewa.

“Ga mai bina Jauro, Sannan kuma sai Sadu, Sannan se Abubakar, Sai kuma Garga, sannan sai Aliyu liman,
Sannan kuma sai Dumau ,Sai Salmanu, Sannan kuma Isa sai kuma Umaru”.

Lamiɗo kuwa kallon su yake yana sake tabbatar da abinda ta faɗa saboda kamannin dake tsakanin su.

Hajja Nana tayi murmushi tace.

“Duk ƙanne nane sannan kuma duk da matansu”.

Ta nuna Jauro tace.

“Matan sa biyu,Garga ma Matansa biyu, Sannan Sadu ma matansa biyu, sai kuma Liman shima Matansa
biyu”.

Ta sake nuna Jauro, Sadu, Garga, da kuma Liman tace.

Jauro da Sadu 'ya'yansu maza biyu sunyi aure kuma 'ya'yan Liman da Garga suka Aura ma'ana Auran
dangi sukayi”.

Lamiɗo kuwa murmushi yayi alamar yana fahimtar abinda take faɗa masa.

Ita kuwa Hajja Nana cigaba tayi da cewa.

“Duk garinmu babu bare mu ya mune, sannan kuma babu maye mu garinmu atsarkake yake kushigo
hankalin ku kwance ku fita lafiya,

Salamun Ƙaulan Min rabbil Raheem”.

Momy kuwa sunkuyar da kai ƙasa tayi Saboda tasan ana zargin Mahaifiyar Lamiɗo da Maita.

Shima Lamiɗo sun kuyar da kansa ƙasa yayi dan yasan zargin da ake yiwa Mahaifiyar sa kenan
kasancewar sa mutum me haƙuri da kuma dattako saiya ɗago kansa fuskarsa ɗauke da murmushi yace.

“Masha Allah yayi kyau zuri'a tayi albarka Allah yaƙara rufa asiri”.

Murmushi Hajja Nana tayi tace.

“Ameen ya Allah”.
Domin Hajja Nana 'yar takife ce bata tsoro inma tsoron wani abu ake itace ke isar dashi.

Miƙewa Sauran sukayi suna kallon Lamiɗo suka ce bari mu barku kuci abinci sannan suka fice.

Itama Hajja Nana miƙewa tayi tace.

“Khausar zo mu shiga ciki kici naki”.

Girgizi kai Khausar tayi tace.

“A'a zanci anan”.

Ta juyi ta dubi Khausar da kyau tace.

“Kizo mu tafi nace”.

Shi kuwa Lamiɗo cike da ladabi yace.

“Da kin barta munci anan ɗin babu matsala”.

Juyawa Hajja Nana tayi kafin tace.

“Toh shikenan”.

Miƙewa Khausar tayi tabi bayanta ta karɓo ƙananan akwashi aka zuba mata sannan suma suka
zuba,Yanayin sanyin da ake tsugawa agarin yasa mazauna garin ke bukatar abu me ɗumi,Suna cin zabbin
suna ɗaurawa da Nono me ɗumi bayan sun gama Khausar ta miƙe ta tattara akushin ta mayar.

Ganin ta mayar ne yasa Hajja Nana fitowa suka zauna.

Atake sega yara suna ta shigowa a jere a jere angama abincin rana suna kawowa duk gida Jen garin
Hajja Nana tana da kwanonta acan suna kawo mata abinci domin ita bata girki abinci safe ne kawai bata
Yarda akawo mata ita take dafa wanda zata ci,Duk ƙannenta taran nan sai ankawo kwanuka tara an ajiye
mata ga kuma na 'ya'yansu da sukayi Aure tana da ƙore goma sha uku.

Ga yaran garin ƙanana kyawawa dasu farare soll kamar irin yaran ƙauyen larabawa.

Lamiɗo da kansa da yaga yaran na shigowa sun basa sha'awa,Ko wacce idan tashigo zata ce.

“Goggo Hajja! Goggo Hajja!! Aɗonna”.


Ƙannenta da Addah Nana suke kiranta 'Ya'yan ƙannenta kuma Goggo Goggo Hajja idan kuma jikoki
zasuce mata Hajja Nana.

Duk Wacce ta kawo mata abinci zata ce nice,daga gidan Sadu,Nice daga gidan Garga,saboda yawansu
kowa ke gabatar da kansa.

Duk wanda yazo ya ajiye zata ce.

“Angode masu nomawa Allah ya basu ƙarfi da lafiyar nomawa masu girkawa ma Allah yabasu ƙarfin
girkawa”.

Sannan ga yanayin tsarin yaran garin babu alamar ƙazanta ajikinsu ko wanne tsaf dashi ga kuma tarbiyya
duk wanda suka zo sai sun tsugunna sun gaida Lamiɗo da Momy da fulatanci kasancewar basu iya Hausa
Sosai ba.

Ɗaya daga ciki data zone ta ajiye kwanon Idanunta akan Khausar tace.

“Goggo Hajja Khausar naa” .

Murmushi Hajja Nana tayi tace.

“Eh”.

Murmushi yarinyar tayi ta matso kusa da Khausar tace.

“Sunana Dija”.

Murmushi Khausar tayi tace.

“Yayi kyau Dija”.

Dija ta kuma murmushi tace.

“Kullum Goggo Hajja na bamu labarin ki rabonki da nan tun kina ƙarama yanzu ya kai shekara shidafa
ake cewa”.

Kai Khausar ta jinjina da faɗin.

“Eh”.

Hannunta Dija ta riƙe tace.

“Kizo muje gidanmu ku gaisa da Mamana”.

Ta ƙare mgnar tare da jan hannu Khausar suka fice...


Kiran sallan Azahar yasa Lamiɗo ya miƙe ya tafi masallaci tare da Ƙannen Hajja Nana ita kuma Momy tayi
alwala tare da gabatar da sallah bayan sun idar da Sallah Hajiya Aysha ta ɓude jakan da tazo dashi ta fito
da turaman zannuwa da Sabulai ta miƙawa Hajja Nana.

Murmushi Hajja Nana tayi tace.

“Hadda ɗawainiya haka?,To angode Allah yayi albarka”.

“Ameen”, Momy ta amsa kafin tace.

“Hajja ga Khausar nan na kawo tayi hutu amma mako uku ne hutun nasu”.

Murmushi Hajja Nana tayi tace.

“Toh Nagode”.

Ita ko Momy tana gyara mayafinta tace.

“Sati uku ne hutun nasu”.

Faska Hajja Nana ta tsuke tare da cewa.

“Sai kin sake Jaddada min ne?”.

Da sauri Momy ta girgiza mata kai.

Cikin isa tace.

“Toh sai sanda naga dama zata dawo kinyi naki saura nawa”.

Ƙasa da kai Momy tayi tare da faɗin.

“Shikenan Hajja duk yanda kikace yayi mukan zamu tafi”.

Miƙewa Hajja Nana tayi tace.

“Bari akira muku Khausar kuyi sallama”.

Cike da ladabi Momy tace.

“A'a Hajja base ankira taba”.


Dan tasan muddin aka kirata sai tayi kuka kafin su rabu.

Sallama suka sake yi musu kafin suka fice suka tafi...

Acan Gembila kuwa Washe gari.

Asabar Moddibo ya shirya kamar ko yaushe cikin Jallabiya Sky blue Kansa sanye da hula da kuma hirami
cikin nutsuwarsa kamar ko yaushe ya shiga cikin makarantar yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi da
hannu kawai yake amsa gaisuwar da ɗaliban haddar ke masa kai tsaye Ajin haddarsu Khausar ya nufa
yayin da Aransa yayi ƙudurin sawa Malam Bello ya casa masa ita saboda gaba ta kiyaye domin ya lura
ganganci da sakalci ke damunta.

Cikin rashin sa'a yana shiga ajin ya samu bata nan.

Asma'u ya kira.

Cike da ladabi ta fito tare da tsugunnawa agabansa tace.

“Gani Yah Moddibo”.

Tsayuwar sa ya gyara cikin yanayin sanyin Muryansa yace.

“Ina wannan Birin?”.

Asma'u kuwa kanta aƙasa tace.

“Nima yau da nazo ban ganta ba sai nake tambayar Amina ina take shine tace wai taje garin
Kakanninta”.

Ƙwafa yayi yace.

“Shikenan yayi kyau”.

Kana ya juya ya bar waje....

Acan mota kuwa Momy ta dubi mijinta tace.

“Kayi hakuri da Hajja Nana yanayin tsufa ne”.

Murmushi yayi still Idanunsa ahanya yace.

“Ai bakomai ba gamu da Gimbiya Dadu ba ai haka take”.


Acan Rugar Jauro yaya kuwa bayan Khausar ta dawo gida ta tar da Momy ta sun tafi ta tsare Hajja Nana
da ido tace.

“Meyesa ba ki kirani ba kafin su tafi?”.

Salati Hajja Nana ta sanya tace.

“Tuhuma ta kikeyi? Ko kuma me?”.

baki ta cinna sama tare da cewa.

“Ai gaskiyane abinda ya dace na faɗa”.

Salati Hajja Nana ta sanya tare da faɗin.

“Ohhh ni Shatu Allah ya nuna min 'yar Usmanu yarinya kamar ruwan aski sai rashin ta ido”.

Ta ƙare mgnar tana kallon Khausar dake tsaye fuska akumbure cikin tsawa tace.

“Bari kiji in faɗa miki ni agarin nan idan nayi magana kamar yankan wuƙa yake babu me bani Amsa ko
musu ko jayayya dani!”.

Ita kuwa Khausar wani irin juya Ido sama tayi tare kana tace.

“Uhummm to gwara ma ki sani.

Idan maganarki yankan wuƙa ne to kin samu me yankan rez”......!

Littafin SAKAYYAH na kuɗine biya ki karanta 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_Page 5_
*NA*

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*FREE PAGE*

*LITTAFIN SAKAYYAH NA KUDINE, 1K NE KACAL ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki.
0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP
09097853276.*

Zare Ido Hajja Nana tayi cikin faɗa da fushi tace.

“Ke! Ke!! Ke!!!.Faɗimatu ki kiyayi kanki dani fa zan tsige Miki fuka-fukinki!”.

Ita kuwa khausar fuska ta haɗe Idanunta tsaye akan Hajja Nana tace.

“Nifa ba tsuntsuwa bace da zaki tsige min fuka-fuki, ai gaskiyane tsakani da Allah da Annabi mahaifiyata
zata tafi kinsa ankawo ni aise ki kirani muyi sallama na musu Allah ya tsare”.

Ta ƙare mgnar tare da juyawa ta kalli Dija tace.

“Fisabillilhi ba haka ya kamata ba Dija?”.

Dija kuwa tuni ta sunkuyar da kanta yayin da jikinta ya shiga ɓari tsananin tsoro ya bayyana afuskarta
sanin halin Hajja Nana babu wanda ya isa tana magana yana mayar mata da martani!.

Cikin rawan jiki da tsoro daya bayyana amuryanta tace.

“Khausar kidena kar ki sake bata amsa ki bata haƙuri”.


Tana ida maganar ta tsugunna gaban Hajja Nana tace.

“Goggo Hajja Waɗɗu munyal”.

Hajja Nana kuwa kwaffa tayi kana tace.

“Aaaa Dija matsa kusa da ita inzo na same ta ai ke ba ruwanki”.

Ita kuwa khausar batare da tsoro ba tace.

“Toh kizo mana kawai dan mutum ya faɗi gaskiya don dai ba'a son gaskiya da zaman lafiya ai yakata dai
akirani muyi sallama da Momyna tunda dai ansa an kawoni wataƙila ma sai nayi sati biyu ko uku bangan
taba aida se akirani muyi sallama ince agaida mutanen gida sannan nayi musu fatan isa gida lafiya”.

Ita kuwa Hajja Nana afusace tace.

“To idan kece zaki kaisu gida lafiya kada Allah yasa ki kaisu shegiyar yarinya mara ji Ɓee Usmanu La'ilaha
illallahu ohoho gabtarel”.

Tuni Baffa Jauro da Baffa Sadu suka shigo idanun su akan yayar tasu suka ce.

“Lafiya Addah Hajja?”.

Kai ta girgiza tare da nuna Khausar dake cika tana ba tsarewa tace.

“Ɓeee Usmanu,Nikam ban taɓa ganin fitsararriyar yarinya kamar 'yar Usmanu ba”.

Itade Khausar na jingine jikin bango tana tura ƙaramin bakinta dake ƙarawa fuskarta kyau.

Kallon ta Hajja Nana tayi cikin harara tace.

“Nikam Usamanu na Kam ba haka yake ba, haka zalika Mahaifiyarki ko surukata ce bazan mata ƙazafi ba
macece mao mutunci amma ke kam waya fitsare miki Ido? Kodan zama tsakiyan Mayun gidan kune yasa
kika zama haka!?”.

Khausar dake jingine da bango ta ɗago kanta kana ta wara manyan Idanunta masu kyau da tsari tace.

“Nikam de kar kice min Mayya idan su Mayu ne toni ba Mayya bace idan kince ni Mayyace sede idan
awajenki na gada!”.
Baffa Jauro da Baffa Sadu suka dubi juna alokaci ɗaya cikin ƙasa da murya yanda Hajja Nana ba zata jiba
Baffa Jauro yace.

“Lalle akwai rigima anan? Addah Hajja ba abata amsa idan tayi magana amma ga 'yar Usmanu daga
zuwa tana bata amsa gatse-gatse jika kenan mafi akasari duk zafin mutum jikoki bazasuji tsoronka sosai
ba”.

Murmushi Sadu yayi yana jinjina kai.

Baffa Jauro kuwa kan Khausar ya ɗan buga yace.

“Kay Hausajo kidena mu ba'a rashin kunya agarin nan!”.

Ita kuwa khausar inda ya ɗan bugeta tasa hannu ta riƙe tana sosawa duk da cewa bawai zafi ya mata ba
ta tura ƙaramin bakinta tace.

“To ai muma ba rashin kunya bane wannan kam”.

Dan ƙolo ya mata yace.

“Dije jata ku tafi”.

Kai Dije ta gyaɗa wacce se alokacin ta samu kuzarin miƙewa tace.

“Khausar kizo mu tafi“, Sannan taja hannunta suka fita.

Suna fita Khausar kuwa hannunta dake cikin na Dije ta janye tace.

“Yanzu ina zamuje?”.

Murmushi Dije ta sakar mata tace.

Rafi zamuje”.

Murmushi mai sanyi Khausar ta sakar mata wanda ke ƙarawa fuskarta kyau tace.

“Toh mu tafi”.

Dan sosai weather garin yake abin burgewa da sha'awa.

Cikin nutsuwa suka nufi Rafin suna hira.


Da sauri Dije ta riƙon hannun Khausar tare da nunawa mata gefen damansu, masu wasa da birine ke
tafiya kana yaran rugagen dake gefe dasu na biye dashi, bisa alamun yanzu kuma rugarsu zasu shiga.

wani ƙaton Biri yake ta kolongoiso yara nata ja da baya.

Cike da nishaɗi Khausar tace.

“Muje muma mu gani”.

Kai Dije ta gyaɗa mata , kana suka nufi wajen me wasa da Biri suna ganin yanda Birin ke duk abinda aka
sashi.

Cike da farin ciki Khausar ta kalli mai wasa da Birin tana ƙara kusawa cikin yara matan tace.

“Mai Biri yanzu duk abinda na sashi zai min?”.

Kai mai wasa da Birin ya jinjina yace.

“Idan kuma baki yarda ba ki gwada ki gani”.

Kusa da Birin Khausar ta matsa tana murmushi tace.

“Yauwa yaya salon mugun Malami yake idan zai daki ɗalibansa?”.

Da sauri ta ware idanunta ganin.

Birin ya wani ja baya tare da harɗe hannunsa aƙirji kana ya ɓata fuska tare da harɗe sawunsa sai kuma
ya ɗauki wani sanda ya riƙe yana nuna Khausar da Dije.

Hannu Khausar tasa ta dafa kafaɗar Dije tare da tintsirewa da dariya mai cike da sautin shauƙi yayin da
ɗaya hannun kuma ta ɗaura saman shafefen cikinta tana mai cigaba da dariyar.

Domin kuwa babu wanda ya faɗo mata arai lokacin da Birin ke gwadawa face Moddibo duk da
kasancewarsa ba mutum ne mai Fara'a ba amma duk sanda zaisa a zaneta a makarantar Islamiyya seya
sake tamke fuskarsa..

Dariya sosai takeyi wanda da yawa cikin yaran tayata sukeyi.

Ganin bata da niyyar daina dariyar ne yasa Dije jan hannunta cikin dariya tace.

“Khausar Mu tafi,Dariyar me kuma kike haka!?”.


Tsagaita Dariyar Khausar tayi sai kuma lokaci ɗaya jikinta yayi sanyi tuna wa da tayi Moddibo zai iya jira
duk lokacin da tawo ya yanke mata hukunci ahankali tace.

“Kawai na tuna da wani Malamin mune”.

Murmushi Dije tayi tace.

“Allah sarki shike zaneki kena”.

Kai ta jujjuya tare da cewa.

“Wancan da shegen madarar ƙasaita sawa yake a zaneni dai yana nan jiki kamar auduga ai shi dukan ma
aikine a wurinsa”.

Murmushi Dija tayi tare da cewa.

“Da Goggo Hajja zataji haka sai ta sa mishi al'barka”.

Baki ta tura ba tare da tace komai ba sukaci gaba da tafiya.

Suna shiga Rafin idanun Khausar ya sauƙa akan Bishiyoyin Piya, Caɓɓulle, Mangoro, Ayaba, Gwanda,
Gwaba, Lemo, da sauran kayan itatuwa duk sun yiwa wajen ƙawanya.

Sake wara Ido Khausar tayi ganin bishiyoyin Inabi guda uku a jere,

Cikin farin ciki ta dubi Dije tace.

“Harda Inabi Laha'Ila Ha'illalhu Masha Allah zan kuwa ci”.

Ta ida maganar tare da nufar jikin Bishiyar zata hau.

Saurin riƙe hannunta Dije tayi tace.

“Kada ki hau Khausar Baffa Liman ya hanamu yace ba shida amfani 'ya'ya mata su riƙa hawa bishiya ba
tarbiyya bace mai kyau”.

Ita kuwa khausar janye hannunta dake cikin na Dije tayi tace.

“Ke rabu dashi da ƙa'idojinsa hawa za muyi mu cire abinmu, ai kuma ba har can sama zamu hauba”.

Langwaɓar da kai Dije tayi kafin tayi magana suka hango wani farin saurayi kyakkyawa daga ɗaya gefen.

Hannu Dije ta ɗaga masa da faɗim.

“Yawwa Sadik dan Allah zoka cire mana Inabi wai zata ci”.
Ƙara sowa Sadik yayi idanunsa akan Khausar yace.

“Dije wannan yarinyar wa kika samo?”.

Murmushi Dije tayi tace.

“Yarinyar Marigayi Baffa Usmanu cefa yaron Goggo Hajja”.

Murmushin fuskarsa ya faɗaɗa yace.

“Allah sarki itace wacce take Birni ko?”.

Kai Dije ta gyaɗa tace.

“Eh itace”.

Ita dai Khausar ba tace komai ba.

Raɓar bishiyar yayi ya ciro musu Inabi kana ya koma bishiyar Ayaba shima ya ciro yasa musu aƙaramin
kwandon dake hannunsa irin na saƙar kaba na gargajiya miƙawa Dije yayi.

Sai asannan Khausar tace.

“Mungode”.

Murmushi kawai yayi ba tare da yace komai ba,

suka fara tafiya cikin rafin akai-akai Khausar ke lumshe idanunta tana wasa da yatsun hannunta sosai
weather garin ya mata daɗi.

Juyowa tayi ta kalli Dije tare da cewa.

“Garinku yayi min daɗi”.

Cikin sauri Sadik yace.

“Garinmu de kin cire kanki ne a ciki? Ko kin manta nanne tushenki kuma asalinki nanfa cibiyarki take
abinne”.

Dariya tayi kafin tace.

“Hmmm Shiyasa ma naji daɗin garin inba haka bama masifar wannan tsohuwar yasa bana sha'awar
zuwa garin nan”.

Zare ido Sadik yayi yace.


“Wacece masifaffiyar!?”.

Asanyaye Dije za tace.

“Wai Goggo Hajja take cewa masifaffiya”.

Sake zare ido Sadik yayi se kuma yace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”,Ya dubi Dije yace.

“Meye sunanta ma kika ce?”.

“Khausar”

Dija tace.

Ya maida kallonsa kan Khausar da hankalinta yabi shuke-shuken da kallo yace.

“Khausar kiyi Istigfari”.

Khausar kuwa kallon mamaki tayi masa kafin tace.

“Saɓon Allah nayi da zanyi Istigfari?”.

Habarsa ya riƙe still Fuskarsa ɗauke da Mamaki yace.

“Goggo Hajjan kike cewa Masifaffiya”.

Baki ta taɓe tace.

“Yo ba masifaffiyar bace daga zuwa na fa kawai takama yimin bala'i”.

Kai ya jinjina kafin yace.

“Toh kar ki sake wallahi in Goggo Hajja taji abinfa baze miki daɗi ba”.

Cikin sanyin murya Dije tace.

“Allah de ya kyauta anma wannan baƙunta ai akwai kallo aciki”.

Ba wanda ya sake magana har suka fito daga cikin Rafin.


Gani tayi Sadik ya ɗauki wani babban kwando da sunyi ta fiya kaɗan sai ratsa cikin ciyawa ya buɗe ya ɗibi
ƙwan Zabbi ya saka acikin kwando.

“Me kakeyi haka?”.

Khausar ta tambayesa tana kallon wajen da ciyayi masu kyau da tsari suka lulluɓe wajen.

Murmushi yayi yace.

“Ƙwan Zabbi nake tattarawa”.

Cikin lumshe ido tace.

“Ohhhh lalle kam Masha Allah abamu naci”.

Murmushi yayi tare da faɗin.

“Toh babu damuwa”.

Haka suka riƙa tafiya suna hira jefi-jefi sun kusa fita daga cikin Rafin ne Khausar ta jiyo hayaniya na tashi
kamar kasuwa anata surutu da dariya jujjuya wa tashiga yi amma bata ga inda sautin surutun ke tashi
ba.Ta dubi Sadik da Dije tace.

“mene nake tajin hayaniya da surutun nan kam a cikin daji?”.

Sadik ne yace.

“Mutanen Bishiyar ƙare zancen kane”.

Da sauri ta sake duban sa tare da cewa.

“Bishiyar ƙare zancen ka?,Wai mene ma'anar Bishiyar ƙare zan cenka?”.

Dije ce tace.

“Ai mu garin nan bamu da service, Service ɗinmu waje ɗaya ne inde mutum yana so yaje yayi waya seya
je ya hau bishiyar ƙare zencen ka anan ne ake samun network idan kina wajen zaki iya kira sannan za'a
iya kiranki kina sauƙa daga bishiyar ko kuma kina Matsawa daga wajen bishiyar toh shikenan Service ya
yanke ba zaki samu kiyi magana ba kuma shima sai in layin MTN ne ko Zain”.

Cike da Mamaki Khausar tace.


“Ikon Allah wannan wani irin ruga ne?. Dama ashe har yanzu akwai irin wuraren nan daya rage
aduniya?”.

Murmushi Dije tayi tace.

“Sosai ma”.

Ahankali Khausar ta ɗaga kanta nan ta hango manyan tsaunika da bishiyoyi Kallonta ta mayar kan Dije
tace.

“Haba ko wannan manyan tsaunuka da bishiyoyin ai sa tare muku service da network”.

Kai Dije ta gyaɗa tace.

“Lalle kam da alama shi ya tare”.

Ta dubi Sadik dake tsintar ƙwai tace.

“Muje inga wajen”.

Kai ya gyaɗa sannan yashiga gaba ita da Dije na biye dashi ta cikin wata siririyar hanya Sadik na cigaba da
tsintar ƙwo'yin suna fita asirin hanyar Khausar ta hango wani ƙaton bishiyar ɗaurawa dake ɗauke da
rassan bishiya masu taren yawa saura daga sama saura kuma sun zuba yayin da ƙasansa bishiyar
duwatsu ne baƙaƙe masu sheƙi ke zube wanda suke kamar kujeru.

Juyawa tayi ta maida Idanunta kan dandazon mutanen dake wajen mafi yawa Matasane sai kuma
Dattijai tana ɗaga kanta sama ta hango Baffa Jauro yana waya.

Dariya ta ƙyalƙyale dashi tace.

“Baka tsoron ka faɗo ko tsohon nan?".

Dije ce ta ɗan bigi ƙeyarta tare da yi mata hararan wasa tace.

“Baban nawa ne tsoho?”.

Murmushi Khausar tayi tace.

“Toh baya tsoro ne kiga ya hau kan bishiya ya ɗane kamar birin can”.

Tsayuwa Dije ta gyara tare da mata hararar wasa tace.


“Ai shikam dole seya zo nan yayi waya tunda shine Jauron garin nan akwai ɓuƙatar magana da Jauro da
sauran Jaurorin garirruwa”.

Khausar kuwa kai ta gyaɗa tace.

“Ikon Allah lalle de kam irin wannan gari haka”.

Tayi maganar tana kallon matasan dake sanye da kayan Fulani kowa na amsa wayar, Idanunta ne suka
sauƙa akan wata tsohuwa dake waya.

Ta maida kallonta kan Dije tace.

“Wannan kuma fa?”.

Dije tace.

“Tafff!, Wannan ƙawar Hajja Nana ce”.

Kallonta Khausar ta sake yi tace.

“Ƙawar Masifa de zaki ce”.

Sadik dake gyara kwandon ƙwai yace.

“Ki bari fa”.

Ta kallesa da manyan Idanunta dake lumshe tace.

“Ai da gskene Hajja Nana in ba masifa ba meta iya!?”.

Duk mutanen wajen juyawa sukayi tare da zuba mata idanu jin tana kiran Hajja Nana Masifa,Wasu daga
cikin mutanen ne suka ce Dije ina kika samu wannan yarinyar.

Dije kuwa tayi murmushi tace.

“ 'Yar Baffa Usmanu ne”.

Jin Abinda Dije tace yasa sauran mutane dake saman bishiyar kashe wayansu suka sauƙo.

Wani kyakkyawan Matashi fari ne ya nufosu kallo ɗaya zaka masa kasan akwai wayewa atare dashi yace.

“Wannan itace 'yar Baffa Usmanu itace ƙanwar Nenne ko Masha Allah?”.
Kai Dije ta gyaɗa tare da nunawa Khausar matashin tace.

“Kinga wannan?”.

Kai Khausar ta gyaɗa.

Dije tace.

“Yaron Baffa Liman ne acikin Birni yake karatun sa”.

Murmushi Khausar tayi tace.

“Ayyah Allah Sarki yayi kyau".

Ya dubi Khausar da murmushi afuskarsa yace.

“Hi Sister how are you?”.

Ta mayar masa da martanin Murmushin tace.

“Am fine how's everyone?”.

“Fine Long time?".

“Thank God”.

Dije ta wani ɓata fuska Idanunta akan Khausar tace.

“Kuyi magana da yaren da zanji”.

Murmushi Khausar tayi tace.

“Ba wani magana muka yiba kawai gaisawa ne fa”.

“Toh”.

Dije tace sai kuma ta maida kallonta kan Matashin saurayin tace.

“Ayyah Yaya Abba nima ka koya min turancin”.

Murmushi yayi yace.

“Ba matsala zan koya miki Kinga ga wata ma zata koya miki”.
Hira suka cigaba dayi yayin da Sadik ya cigaba da tsintar ƙwoyaye wasu ma da yawa nata tsintar ƙwoyin
ko wannensu da alama akwai inda ƙwan Zabbinsa ke tsayawa akwai waya da ake sakawa atsakanin
waje-jen...

Baffa Jauro daya gama waya ya sauƙo tare da zuwa inda Khausar take ya riƙe hannunta suka fara tafiya
sai kuma ya fara matsa hannun, Janye hannun tayi tace.

“Wallahi tsohon nan ka iya mugunta inka riƙe hannun mutum kaita matsewa da faratu ni banaso”.

Murmushi Baffa Jauro yayi tare da sake matse hannun!.

Ashagwaɓe tace.

“Wayyo na tuba ka sake”.

Sake mata hannun yayi yana dariya yace.

“Ohhh in dai baki daina yiwa Adda Nana rashin jiba, toh fa hakan zanyi ta matse mata ke, ga jiki ba ƙwari
ba'ason wahala”.

Sai kuma ya juya ya dubi Dije yace.

“Dije”.

“Na'am Baba”.

Yace.

“Kishirya Gobe idan Allah ya kaimu da sassafe zaki ɗauke ta kuje kuyi tsar Nono tare”.

Kai Dije ta gyaɗa kana tace.

“Insha Allah zan ɗauke ta muje tare”.

Kallonsa Khausar tayi still hannunta na cikin nasa tace.

“Nide inda wuya bazan yiba”.

Dije tace.

“Ba wuya ai zamu baki man shanu ki shafawa yatsunki yanda zai yi santsi.

Kai ta gyaɗa tace.

“Toh shikenan ba damuwa zanje”.


Kallon Dije Sadik yayi tare da bata kwandon Ƙwan Zabbin yace.

“Ki tafi dashi".

Sannan ya juya ya cigaba da tafiya.

“Khausar kuwa murya ta ɗan ɗaga tace.

“Kaifa baza ka bimu bane”.

Girgiza Kai yayi yace.

“A'a ban ƙarasa ɗiba ba”.

Kai ta gyaɗa tace.

“Toh inde kazo ka kawo min nawa”.

“Toh”,Yace sannan suka juya suka tafi.

Suna shiga rugar suka nufi hanyar gidan Hajja Nana kasancewar duk gidan da zaka je seka wuce ta
ƙofanta,sannan duk lokacin da taji motsi seta tambaya waye.

Sallama Dija tayi cikin ladani kana suka shiga, Hajja Nana dake cikin uwar ɗaka tace.

“Waye”.

Cike da ladabi Dije tace.

“Dije ce".

Haɓa Khausar ta riƙe tare da cewa.

“Ikon Allah duk mai wucewa saita tambayesa waye sai kace wata Traffick light?”.

Ƙasa da murya Dije tayi tace.

“Aaa ki bari Khausar kiyi ahankali kar taji”.

Khausar kuwa baki ta taɓe tace.

“Ai wannan abu yayi yawa wannan mulkin mallaka haka ake yi muku agarin nan”.
Daga ciki Hajja Nana tace.

“Dije keda waye naji kamar ana magana ƙasa-ƙasa?”.

Dije tace.

“Nida Khausar ce zamuje gida kai saƙo ne ƙwoyi muka kawo”.

Ita kuwa Hajja Nana cewa tayi.

“Toh shikenan”.

Ajiyar zuciya Dije ta sauƙe sannan suka fice.

Lokacin da suka fita makiyaya sun fara dawowa daga kiwo sannan sanyin magriba na sake sauƙa sanyin
ya fara yawa ahaka suka isa gidansu Dije Khausar sai lumahe ido take.

Suna isa suka ajiye Ƙwoyin.

Dije na ƙoƙarin shiga ɗaki Khausar da Idanunta suka sake lumshewa tace.

“Dije muje ki rakani ɗaukan Sweater na sanyi nake ji sosai”.

Kai Dije ta gyaɗa sannan suka fice kallon garin Khausar tayi ko ina baƙi ba alamar hasken wutar lantarki
ta dubi Khausar tace.

“Wai kam garin nan baku da wuta ne?,tun da nazo banga ƙyallin wuta ko sau ɗaya ba?”.

Kai Khausar ta gyaɗa tace.

“Eh babu amma ana tada Generator”.

Khausar kuwa hankalin tane ya tashi jin babu wuta garin!.

Ganin yanda tayi yasa Dije sakin murmushi tace.

“Kada ki damu kinga Yaya Abba shike tada Generator sannan yake sa kawa mutane Caji kuma aƙofar
gidan Hajja Generator yake akwai ɗan haske kaɗan koda ba farin wata, bare kuma in akwai farin wata
rana zakiga garin”.

Sai asannan Khausar ta ɗan saki ajiyar zuciya dan Allah ya sani tana tsoron duhu.
Bakinsu ɗauke da sallama suka shiga gidan shigarsu yayi dai-dai da kiran Sallar Magriba da akayi.

A tsakar gida suka samu Hajja Nana na alwala, kallonsu tayi tace.

“Kuzo kuyi alwala kuyi Sallah”.

Kallon ta Khausar tayi tace.

“Ni gaskiya sanyi nake ji yanzu ma rigar sanyi na nazo ɗauko kuma asamar min ruwan zafi dashi zanyi
alwala”.

Harara Hajja Nana ta watsa mata kafin tace.

“Wa zai samar miki ruwan zafi?,Kina yarinya ƙarama yau har wani sanyi kirki akeyi! da har zaki nemi
ruwan zafi”.

Bakinta ta tura amma ba tace komaiba.

Dije ce tace.

“Muje gidanmu akwai ruwan zafi sai kiyi acan”.

Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.

“Toh shikenan”

Sannan tashiga ɗakin Hajja Nana kasancewar akwai hasken lanta da aka kunna inda trolley ta yake ta
nufa ta buɗe tare da ɗaukar Sweater ta sannan ta rufe trolley juyawar da za tayi Idanunta suka sauƙa
akan kuliya (Mage) dake kwance akan ɗaya daga cikin gadon Hajja Nana kasancewar gado biyu ne aɗakin
sai kuma ɗan shirge-shigen ta na Tsoffin ruga.

Cikin matsananci tashin hankali da ruɗu mara misaltuwa daya bayyana afuskarta take faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!!,Hasbunallahu!!!, wani'imal wakin Astagfirullah wa'atubu ilaik!!!”.

Aruɗe Dije ta shiga ɗakin tana cewa.

“Lafiya Khausar meye faru?”.


Aruɗe Khausar ke yarfe hannunta takamar wacce ta ƙone duk jikinta na rawa takasa furta komai
numfashinta na wani irin fusga na tsananin tsoro da tashin hankali, da ƙyar ta iya furta.

“Kuliya”.

Sai asannan Dije ta lura da kuliyar da har zuwa lokacin ke kwance akan gadon Hajja Nana.

Ita kuwa Hajja Nana wani dogon numfashi taja.

Dan da kusan mutuwar zaune tayi dan jin irin karajin da Khausar ɗin tayi.

Ita kuwa Dija hannu tasa tashiga koran kuliyar.

Daga can waje Hajja Nana ke cewa.

“Kuliyar take wa wannan Ihun? zata kasheni tun kwanana bai ƙareba”.

Ina ita kam Khausar bata san sunayi ba, har zuwa yanzu tsalle takeyi a tsakiyar ɗakin tana yarfa
hannunta tare da furta duk addu'ar da tazo bakin, istagfari takeyi ba ƙaƙƙautawa.

A gigice Dije ta fitar da kuliyar tana mai cewa.

“Khausar ki nitsu ya fita, na koreshi, kuliyar Goggo Hajja cefa.

Cikin tsananin tsoro da rawar jiki cike da gigita,

Ta fito cikin ɗakin Hajja Nana ta nufi gidan Baffa Jauro tana cigaba da faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n

Ya Allah na tuba ka yafe min”.

Yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa na tsananin tsoratan da tayi.

Jin shiganta Aruɗe yasa Goggo Nanne fitowa daga ɗaki wato Mahaifiyar Dije.
Matsawa kusa da Khausar tayi ta riƙe Hannunta tace.

“Lafiya”.

Asanyaye Dije tace.

“Kuliya take tsoro taga kuliyar Goggo

Hajjs ce take haka”.

Cike da tausayinta Goggo Nanne tace.

“Ayyah Subhanallah ki kwantar da hankalinki nan babu kuliya kar ki damu Khausar ki kwantar da
hankalinki ki nutsu kinji?”.

Kasa furta komai Khausar tayi sai Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n da take yi aƙasan ranta.

Addu'a Goggo Nanne tashiga tofa mata kafin ta samu hankalinta ya dawo jikinta.

Jauro daya fito daga banɗaki yana alwala yace.

“Yau kuliya ce haka kamar wanda taga kura haka?”.

Ya faɗa yana kallon yanda tsananin razana ya bayyana afuskarta.

Juyawa yayi yana kallon Goggo Nanne yace.

“Lalle wannan baƙunta akwai saɓani a cikinsa. Ita Addah Hajja ba zata iya rayuwa babu kuliya ba ita
kuma wannan ga tsoron kuliya”.

Tana sakin ajiyar zuciya tace.

“Nide bazan sake shiga ɗakinta ba shegen ɗaki ga tarukuce ga duhu sannan ga kuliya wannan ɗakin har
macizai za asamu acikinsa bazan sake shiga ɗakinta ba”.

Murmushi Goggo Nanne tayi tace.

“Ki kwantar da hankalinki kada ki damu tashi kiyi alwala ga ruwan zafi abuta”.

Batace komai ba ta miƙe ta ɗauki butar ta zaga bayi sannan ta fito tayi alwala ɗakin Goggo Nanne suka
shiga da Dije cikin ɗakin duhu.
Araunane Khausar tace.

“Daƙin duhu ni gani nake ma ko ina akwai kuliya”.

Dafa kafaɗar ta Dije tayi tace.

“ki kwantar da hankalinki nan babu kuliya”.

Ta ƙare mgnar tana kunna lantansu mai ɗan karen haske,

Kai kawai ta jinjina tare da sauƙe ajiyar zuciya ganin hasken, sannan ta tada sallah suka idar da Sallah
maghariba Khausar kuwa jingina bayanta da jikin bango tayi ta fara addu'a.

Dije kuwa miƙewa tayi zata fita, Kallon ta Khausar tayi tace.

“Ina kuma zaki je?”.

Juyawa Dije tayi ta fuskance ta tace.

“Zanje in dafa mana ƙwoyin da kika ce kina so ne”.

“A'a kibari ba da fawa zamuyi ba soyawa zamuyi ina akwai attaruhu da albasa da kuma maggi?”.

Kai Dije ta gyaɗa tace.

“Eh akwai”.

“Ok to kibari sai munyi Azkhar”.

“Toh”,Dije tace.Sannan ta dawo ta zauna suka cigaba da yin Azkhar ɗin Khausar nayi da ƙarfi Dije na
binta wani ta iya wani kuma bata iya ba sai Khausar ta tsaya ta gyara mata suna zaune har akira Isha'i
suka Idar...

GEMBILA

Anutse Momy ta gama shirin baccinta bayan tayi addu'a sai kuma ta lumshe Idanunta ahankali ta sake
buɗesu ta juya kwanciyar ta daga hagu zuwa dama sai kuma ta tashi ta zauna baki ɗaya kewan Khausar
ɗin ta ke damunta acikin yini ɗaya da bata kusa da ita se taji kamar wata tayi ba tare da ita ba gashi basu
da network bare ta kira taji muryanta.

Jin ƙaran Knowking ɗin ƙofa yasa Momy gyara zamanta kana ta bada izinin shiga,Anutse Haiydar ya shigo
bakinsa ɗauke da Sallama kana ya zauna kusa da Momy.
Murmushi Mommy tayi tace.

“Haiydar lafiya ko kana bukatar wani abu?”.

Kai ya girgiza yace.

“Momy wallahi yau gidan nan ba daɗi da Addah Khausi bata nan”.

Murmushi Momy tayi cike da ƙaunar 'ya'yan nata da kuma yanda suke nunawa juna kulawa tace.

“Yau kuma?,Ko da yake dama haka kuke bakwa shiri sannan bakwa san rabuwa da juna”.

Fuska ya Marerece kafin yace.

“Allah yau gidan babu daɗi yau tunda gari Ya waye babu wanda yace min Haiydar kar kayi kaza, Haiydar
zo in aikeka, Haiydar bakaji, Haiydar karenani, Haiydar kada fa kaci komai wurinsu Umma, Haiydar ban
girme ka bane kam wai da in na saka abu bazakayi ba, Yau duk babu wanda ya faɗa min haka nayi
missing ɗinta! Sosai wlh Momy Ina son Adda Khausi”.

Murmushi mai cike da shauƙi Momy tayi tare da zuba musu ido.

Raudat da shigowarta kenan ta Shagwaɓe fuska tace.

“Wallahi nima nayi kewarta Mommy yaukam tare zamu kwana ko?”.

Janyo hannunta Momy tayi tace.

“Autanah ba dole ba yau In kwana dake tunda Addah Khausar bata nan”.

Haiydar ne ya sake kallon Momy cikin yanayin kewar 'yar uwarsa yace.

“Momy dan Allah ki kira kice ta dawo munyi missing ɗin ta”.

Ramadan da Raudat suma sukayi saurin cewa.

“Please Momy ki kira”.

Kai Momy ta girgiza tace.

“Basu da network sai dai idan sunje wajen bishiyar ƙare magarka sun kira”.

Ramadan yace.

“Toh yanzu Mommy Gobe wa zai Miki shara?,da wanke-wanke da kuma gyaran falo?”.
Murmushi Momy tayi tana shafa kansa tace.

“Zanyi ƙoƙari nayi da kaina”.

Zare Ido Ramadan yayi yace.

“To wallahi Momy aɗauko Miki Addah Khausi yafi Miki gidan babu daɗi idan bata nan”.

Murmushi tayi tace.

“Toh”,Da haka hiran yazo ƙarshe Haiydar ya miƙe kana ya ɗauki Ramadan suka tafi ɗakinsu wanda zai ka
fita falon Momy ƙofar nasu na jere da ƙofar falonta,

ita kuma Raudat gadon ta hau ta kwanta gefen Momyn.

Acan ɓangaren su Moddibo kuwa.

Zaune yake Atsarerren falonsa da yagaji da tsaruwa kana yana fitar da sihirtaccen ƙamshi mai masifar
daɗin shaƙa.

Yayin da M Jameel ke kwance akan 3sitter da waya maƙale akunnensa, Anutse Moddibo ya juya ya zuba
masa Idanunsa tare tsarasa da su, still wayan yake Amsawa ɗauke kansa yayi ya cigaba da operating
system ɗin sa kana ahankali ya sake maida Kallonsa kan M Jameel still wayar ne maƙale akunnensa.

Cikin ga jiyawa da wayar da yake yi Moddibo ya zuba masa idanunsa tare da motsa laɓɓansa da suka
sake yin pinch kana suka tattare saboda tsananin sanyi da akeyi yace.

“Wai kai da wa kake yin wayar?”.

Gyaɗa masa kai M Jameel yayi tare da juya hannunsa alamar ya kusa gamawa.

Ganin haka yasa Moddibo maida hankalinsa kan system ɗin sa yana cigaba da duba muhimman saƙonnin
da suke shigo masa.

Wayarsa dake gefen Centre table ne yayi ƙara hannu yasa ya ɗaga nan yaga sunan Abba na yawo a
screen ɗin wato Abban M Jameel.

Cikin han zari yayi picking call ɗin kana yace.

“Assalamu alaikum Abba Barka da dare”.


Daga ɓangaren Abba yace.

“Barka dai Moddibo ya gida ya kuma ɗalibai?”.

“Lafiya lau Alhamdulillah Abba”.

“Masha Allah kana tare da Hassan ɗinna ka ne?”.

Murmushi Moddibo yayi wanda ke sake fitar da ainihin kyawun fuskarsa yace.

“Eh Abba muna tare waya yake tun ɗazu nayi zaton ma da kai yake yin wayar”.

Abba yace.

“Aina kira wayarsa naji Line busy shiyasa nace bari na kira ka naga dare yayi bai dawo ba za'a rufe ƙofar
gida”.

Murmushi Moddibo yayi yace.

“Ayyah Abba yau kam abarshi mu kwana tare gashi naga alamun Agajiye yake bacci ma yake ji”.

Kai Abba ya gyaɗa yace.

“Toh shikenan Moddibo ayi bacci lafiya Allah ya tashe mu lafiya amma gobe da safe kuzo ina son ganin
ku”.

Kai Moddibo ya gyaɗa cike da mutuntaka yace.

“Toh insha Allah Abbah”.

Kana ya katse kiran.

kallon M Jameel yayi sai kuma ya ajiye System dake kan ƙafarsa ya miƙe ya isa inda M Jameel yake yasa
hannu ya cire wayar daga kunnensa ya duba screen ɗin sai yaga number ba suna saidai aƙasan Number
ansa Bahrain wato ƙasan Bahrain.
Kallon M Jameel yayi yace.

“Ooo kaida Jalaludeen ne dama?”.

Kai M Jameel ya gyaɗa yace.

“Eh shi ya hana ince da kai dashi nake waya”.

Murmushi M Jameel yayi yace.

“Yayi kyau”.

Jalaludeen abokinsa ne tare sukayi karatu a Jami'atul Madina asalin Balarabe Bahrain ne...

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe yace.

“Abba ya kira yace baka koma ba har dare yayi sai nace zamu kwana tare yace gobe yana son ganinmu”.

Kai M Jameel ya gyaɗa da faɗin.

“Allah ya kaimu”.

“Ameen”.

Moddibo ya amsa tare da kallon M Jameel yace.

Bacci na keji zanje nayi wanka”.

Zare Ido M Jameel yayi yana kallon Moddibo yace.

“Wallahi inba cikin kashi na faɗa yanzu ba ba zanyi wanka ba yanda ake tsuga wannan sanyi agarin nan.

Kai Moddibo ya girgiza ba tare da yace komai ba ya wuce Bedroom.

wanka yayi da ruwa mai ɗumi, kana yayi shirin bacci.

Washe gari, da safe bayan sun dawo daga masallaci sashen Innayi suka nufa lokacin da suka shiga tana
zaune kan darduma tana lazimi M Jameel ya zauna kusa da ita tare da riƙo tafin hannunta yace.

“Barka da safiya tsohuwa mai ran ƙarfe!”.


Murmushin fuskarta ta faɗaɗa tare da damƙe hannunsa dake cikin nata tace.

“Jameel Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwarku”.

Ya amsa da.

”Ameen Innayi”.

Shi kuwa Moddibo kusa da ita ya matsa ya ɗaura kansa akafaɗarta yana mai lumshe idanunsa ahankali
yace.

“Barka da safiya Innayi”.

Hannunta tasa ta shafa fuskarsa tare da cewa.

“Fatan ka tashi lafiya ya ƙoƙari?”.

Ya amsa da. “Alhamdulillah” sai kuma ya miƙe tare da kallon M Jameel da still hannunsa ke cikin na
Innayi yace.

“Mu je ko”.

Bai jira cewarsa ba ya fice daga sashen nata kana ya nufi nasa yana shiga kai tsaye Bedroom ya wuce ya
cire naɗin Hiramin dake wuyan sa da kuma jallabiyar.

Kai ya shiga bathroom Masha Allah Komai na cikin toilet wanka ya fesa kana ya fito bakinsa ɗauke da
addu'a

“Gufra naka”.Alokacin daya ziro ƙafarsa ta dama zuwa cikin Bedroom ɗin ya fito M Jameel kuwa jin
ƙamshin sabulun wankan da kuma tularensa yasa ya ɗago kai sai kuma ya miƙe ya shiga toilet ɗin.

Shi kuwa Moddibo zama yayi agaban dressing mirrow ya shafa mayukan sa tare da taje yalwataccen
sumarsa kana ya miƙe ya buɗe durowarsa

Masha Allah kayane aciki masu uban yawa fannin jallabiya da ban fannin yaduka da ban haka zalika
fannin ƙananun kaya daban duk da cewa bai fiye amfani dasu ba yana tsaye awajen har M Jameel ya fito
daga wanka bai ɗauki komai ba.

Murmushi m Jameel yayi tare da nufar jikin durowar yana cewa.

“Nasan koda zaka kwana nan ba zaka taɓa cire kayan da zamu sanya ba kai de inba jallabiya ba baka
ganewa ko wani irin kaya”.

Moddibo kuwa murmushi yayi Aransa yana jinjinawa M Jameel yanda yake iya fahimtar komai nasa koda
kuwa ƙwaƙa-ƙwaran motsi yayi yasan me yake nufi...
M Jameel kuwa Wani boyel Sky blue mai gidan dara-dara ya ciro musu tare da boxer da kuma singlet Fari
ƙal.

Kallon Moddibo yayi tare da miƙa masa.

Murmushi Moddibo yayi tare da karɓa yana kallon kayan amma bai ce komai ba sai ya juya ya kimtsa.

Masha Allah wani irin kyau na musamman Moddibo yayi acikin kayan kalar shigar sai ta kasance tamkar
kalar sararin samaniya ƙirjinsa na ƙiran jarumtaka ya bayyana acikin rigar kana yalwataccen sumar kansa
ya kwanta luf yana sheƙi,Anutse ya juya wajen M Jameel dake miƙo masa takalmi da hula kalar sky blue
Masha Allah m Jameel ma sosai Yayi kyau acikin kayan sai suka kasance tamkar tagwaye masu tsananin
ƙaunar junansu.

Atare suka fice sashen Innayi suka nufa tun daga farfajiyar tsakar gidan Moddibo ya lumshe idanunsa
yana jinjinawa tsaftar Kakar tasa har sanda suka isa ƙofanta inda sanyayyan ƙamshi turaren wuta ke
tashi.

Ganinsu atare yasa ta sakar musu da murmushi atare suka shiga ɗakin suka zauna.

Ta dubesu cikin ƙaunarsu tace.

“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ku Allah yasanya farin ciki acikin rayuwarku Ubangiji ya tsareku da
dukkan sharrin mai sharri”.

Cikin jin daɗin addu'ar da take musu ako yaushe suka amsa da.

“Ameen Innayi”.

Innayi kuwa miƙewa tayi ta haɗo musu tea mai zafin gaske saboda sanyin da akeyi sosai amsa sukayi.

A hankali Modibbo ya ɗan zuƙan tea ɗin ahankali har ya Ida shanyewa zuwa lokacin tuni M Jameel ya
shanye nasa.

Yana ƙoƙarin ajiye Mug ɗin yaga M Jameel ya tsaresa da ido Harara Moddibo ya watsa masa shikuma
saiya sakar masa da murmushi.

Kallon Innayi Moddibo yayi yace.

“Zamu je gaida Abba”.


Jinjina kai Innayi tayi tace.

“Idan kunje ku gaishe min dashi”.

Moddibo na miƙewa yace.

“Zaiji insha Allah”.

Sannan suka fice.

Suna fita suka nufi inda mota ke ajiye M Jameel ne ya buɗe gefen Driver ya shiga yayin da Moddibo ya
shiga mazaunin mai zaman banza ahankali M Jameel yayiwa motar key suna isa gate ɗin Moddibo ya
fita ya buɗe musu gate sannan M Jameel ya cinna hancin motar yafita saida Moddibo ya sake rufe gate
ɗin kafin ya koma cikin motar M Jameel ya tayar suka bar unguwar.

Anutse M Jameel ya dubi Moddibo da idanunsa ke lumshe yace.

“Anma aikin makarantar nan zai yi kyau domin masu aikin sun san makamar aikinsu”.

Shi kuwa Moddibo kai ya gyaɗa da faɗin.

“Sosai Insha Allah”.

Tafiyar Mintuna Kaɗan sukayi suka isa gidansu M Jameel Hon yayi mai gadin ya taho da sauri ya buɗe
musu tamfatsetsen gate din.

Wow Masha Allah babban gida ne wanda yake ɗauke da Sashe huɗu sai kuma BQ da kuma wajen ajiye
motoci kamar takwas zuwa goma sai ɗakin mai gadi cikin gidan akwai shuke-shuke saida basu da yawa
sosai bayan sunyi parking sun fito ajere suke cikin tafiyar nutsuwarsu da tazame musu jiki kai tsaye
sashen mahaifin M Jameel ya nufa dasu.

Adai-dai ƙofar da zai sa dasu da falon Mahaifin M Jameel suka haɗu da Hajiya Karima kallon Jameel tayi
kana ta kawar da kanta wani irin tsuke fuska tayi ganin Moddibo abayan M Jameel.

Cike da ladabi M Jameel yace.

“Ina kwana Aunty Karima”.

Fuska ta sake tace.

“Lafiya lau ɗana ya gida ya kuma ƙoƙari??”.


“Alhsmsulillah ya amsa”.

Yana mai shafa sajensa

Shi kuwa Moddibo cikin tsuke fuska alamun ba wargi ataƙaice yace.

“Ina kwana”.

Wani irin kallo ta watsa masa kafin tace.

“Kaska raɓi mai jini anzo kenan?”.

Shiru Moddibo yayi tare da kauda kansa kamar bai jitaba.

Sai ma Murmushi da yayi tare da kallon gefen dama inda Aunty Larai Amaryar Aunty Karima ke tare da
ce mata.

“Yau barka dai”.yayi mgnar yana mai tsare fuskarsa da ido alamun yana nazartar ta,

Ita kuwa Aunty Larai cikin sakin fuska tace.

“A'a to Moddibo ya kuka tsaya nan ku shigo daga ciki man Jameel”.

Ta ƙare mgnar tana kallon Jameel tare da juyawa ta nufi cikin falon Daddyn Jameel din.

Cikin jin yanayin ɓacin ran da kalaman Aunty Karima suka sa mishi yace.

“Gamu nan shigowa Aunty Larai”.

Ya kare mgnar tare da

ɓata fuska cikin rashin jin daɗin abinda ta yiwa amininsa yace.

“Aunty!Aunty!!, Meyesa!!?, Meyesa!!!?”.

Cikin taune lips inta dubesa tace.

“Jameel gaskiya ne ai, amma ba zaka gane ba, ba zaka yarda ba sabida ya fika wayo.

Kawai dai ya zama dole in faɗa maka”.

Shiru M Jameel yayi tare da juyawa wajen Moddibo wanda har zuwa lokacin yake tsaye hannunsa M
Jameel ya riƙe yace.

“Dan Allah kayi haƙuri inda sabo yaci kasaba da halin Aunty na roƙeƙa Kayi haƙuri mushiga daga ciki”.
Murmushi Moddibo ya sakar masa ahankali ya furta.

“Bakomai me zatayi ya dameni sam babushi tunda tana son aminina”. Yayi mgnar da iya gskyarsakan

suka shiga cikin falon.

Ita kuwa Aunty Karima tsaki taja tare da barin wajen tana maijin tsanar Moddibo.

Zaune suka samu Alh Bashir Mafindi Shahararren mai kuɗi daya sharahara aƙasa da kuma faɗin Afirca
baki ɗaya mutum mai tsananin tausayin al'umma da jin ƙai.

Hannu ya buɗe musu cikin nutsuwarsu suka ƙarasa Moddibo ya nufi gefen damansa yayin da M Jameel
ya nufi gefen hagunsa ya rungumesu tare da buga kafaɗar su.

Cike da so yace.

‘Yan ta gwayena Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ku ina jin dadin ganinku atare kunyi kyau tamkar
matasan Larabawa Allah Ubangiji ya nuna min aurenku”.

Moddibo kuwa murmushi yayi shikam sai ya zo wajen Abban Jameel ake masa maganar aure sai yaji abin
banbara ƙwai duk da yasa ba duk lokacin da yazo wajen Abba saiya masa Maganar amman kullum a
baƙuwa yake jin kalmar a cikin kunnuwansa.

Cike da ladabi da kuma girmamawa suka gaishesa cike da ƙaunarsu ya amsa da.

“Lafiya”.

Kana ya tambaye su ya ɗalibai?.

Suka haɗa baki wajen faɗin.

“Lafiya lau Alhamdulillih”.

Zama Abba yayi bisa kujera.

Kana su kuma suka zauna a ƙasa bisa tattausan carpet ɗin, cikin kula Abba ya ɗan sunkuyo ya kalli M
Jameel kana yace.
“Yanzu kaga damuna ta kusa sauƙo za'a fara shuke-shuke to inason bana zan shuka Auduga mai yawa
saboda ina son zan habaƙa Company dake Marrocco muna buƙatar Auduga mai yawa domin mun samu
haɗin guwar da wani ɗan Saudia wurin sufurin Sallayoyi da zannuwan gadaje da kuma Abayoyin na
mata”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cewa.

“Eh Abba hakan yayi Allah ya sanya alkhairi”.

Shima Moddibo yayi Murmushi da faɗin.

“Allah yabada sa'a”.

Cikin jin dadi Abban yace.

“Ameen. Yauwa sai kuma noma shinkafa da zamuyi mai yawa da alkama, dan Company kayan masarufin
dake Ɓadamaya yana buƙatar ninkin abinda yake sarrafa a shekara, domin samun haɗin guiwa da shi'ar
ƙasar Niger”.

Kai suka jinjina alamun gamsuwa kana cikin kula Abban yace.

“Na sani kuma na fahimta, cewa akan su Asma'u ne ka nacewa karantarwa da kai da amininka. To
Alhamdulillah na baku dama, amman ku sani suna gama secondary School, dole ku bar karantar wannan
Moddibo ina buƙar taimakonku a Company's ɗin tunda Allah yayi kun karanci Business ɗin nan kafin ma
ku tafi Jami'atul Madina.

Babana yanzu girma ya cinmini abubuwa sunayi min yawa dole ina bukatar tai makonku”.

Ya kare mgnar yana dafa kaɗan Jameel.

Cikin sanyi Jameel ya ɗago kansa ya kalli mahaifin nasa kana cikin sashi farin ciki yace.

“Allah ya kaimu lokacin Daddy in Sha Allah zanyi maka dukkan abinda kake so, muddin ina raye”.

Cikin jin dadi yace.

“Kaifa Moddibo baƙace komai ba?”.

Murmushi gefen baki yayi tare da cewa.

“Daddy duk inda J yake to in sha Allah ina nan”.

Cike da jin daɗin Alh Bashir

Mafindi ya shafa kansu tare da cewa.

“Allah yayi muku al'barka".


Cike da jin daɗin sukace. “Amin Ya Allah Allah ya ƙara nisan kwana da lfy”.

“Amin Ya Allah”.

Abba ya amsa tare da nuna musu dinning area da hannunsa, inda Aunty Larai ke shirya dinning ɗin tama
mai murmushin jin tattaunawarsu.

Sai kuma ya kalli Moddibo kana yace.

“Bismillah kuje kuyi Breakfast”.

Moddibo kuwa kai ya girgiza a hankali yace.

“Daddy na ƙoshi”.

Kallonsa Daddy yayi cikin kulawa yace.

“Meyesa haka ne Moddibo gsky ni bana son yadda kake in kazo gidan nan kaci abinci sai kaƙi ci”.

M Jameel ne ya amshi zancen da cewa.

“Rabu dashi Daddy in baici ba sai muyi masa ɗure”.

Murmushi Daddg yayi tare da faɗin.

“Aikam".

Moddibo kuwa harara ya wurgawa M Jameel.

Adam ƙanin M Jameel yaron Aunty Karima ne yashigo ganin M Jameel yasa ya faɗaɗa Murmushin sa
yace.

“Yaya Jameel Ina kwana?”.

Cikin murmushi M Jameel ya mayar masa da.

“Lafiya lai alhamdulillah Adam ya school”.

Adam kuwa kallon tsana ya watsawa Moddibo ba tare daya gaishe saba dan gani suke yana amfani da M
Jameel ne wajen cin dukiyar mahaifinsu ko kaɗan M Jameel baiji daɗin abinda Adam yayi wa Moddibo
ba, haka yasa ya haɗawa yaron fuska.
Acan Rugar Jauro yaya kuwa Washe gari.

Bayan Khausar sunyi Sallar asbah tare da Azkharul sabah ɗakin Goggo Nanne suka shiga ita da Dije suka
gaisheta,

Ta amsa fuska asake Idanunta akan Khausar tace.

“Ya kwanar baƙunta da kuma tsoron kuliya?”.

Murmushi Khausar tayi tana wasa da yatsun hannunta har yanzu Atsorace take idan akwai abinda tafi
tsoro acikin dabbobin duniya to kuliya ce da ƙadaggare.

Dije ce ta miƙe tace.

“Mun tafi gidan Hajja Nana”.

“Toh adawo lafiya".

Miƙewa sukayi suka fita ahanya Khausar ta dubi Dije cikin sanyin murya tace.

“Idan munje Kar mu daɗe tsoron gidan nake".

Kai Dije ta gyaɗa suka cigaba da tafiya bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga Hajja Nana dake hakimce
akan kujeranta ta amsa Khausar kuwa kusa da ƙafafun Hajja Nana ta zauna tace.

“Ina kwana Hajja Nana”.

Ta dubeta fuska asake ta amsa tana jin ƙaunar ta aranta.

Dije ma gaisheta tayi ta amsa fuska asake.

Miƙewa Khausar tayi tace.

“Mu tafi”.

Kallonta Hajja Nana tayi tace.

“Ki zauna mutanen garin zasu zo gaisheni zan gabatar dasu awajenki”.

Khausar kuwa narai-narai da idanu tayi har cikin ranta take tsoron gidan Hajja Nana Allah ya sani tana
masifar tsorob kuliya, jiki asaɓule ta zauna tare da riƙe Dije suka zauna tare.

Suna zaune Baffa Jauro yazo cike da girmamawa da kuma ladabi yace.
“Addah Hajja ina kwana”.

“Lafiya ta amsa”,tare da kallon Khausar dake takure tace.

“wannan shine ƙanina dake bina”

Murmushi Khausar tayi tare da gyaɗa kai tace.

“Baffa ina kwana”.

Dariya yayi yace.

“Lafiya Audiii ya fargaban kuliya!?”.

Baki ta ɗan tura amma batace Komai.

Can sai ga Goggo Nanne

Kusa da Khausar ta zauna tace.

“Addah Nana ina kwana”.

Ta amsa da lafiya tare da kallon Khausar tace.

“Wannan itace matar Jauro wacce kuka kwana agidanta sunanta Nanne ita ce kuma takwaran marigayi
yayarki”.

Kai Khausar ta gyaɗa tana sake damƙe hannun Dije dake cikin nata.

Can sai ga Garga yazo idanun sa akan Khausar ya mata murmushi hannunta ya riƙe yace.

“Addah Nana ina kwana ya kwanan baƙuwa?”.

Hajja Nana kuwa taɓe baki tayi tace.

“Ga tanan matsoraciya saboda kuliya taƙi kwana anan".

Murmushi Garga yayi yace.

“Audii ki zama jaruma Mahaifinki fa ba rago bane babban jarumi ne”.

Murmushi tayi amma batace Komai ba.

Hajja Nanan ce tace.

“Wannan shine Garga shike bin Jauro.


Can sai ga wata mata tazo itama ta gaida Hajja Nana.

Hajja Nana ta dubeta tace.

Wannan itace Dijarro matar Garga”.

Cikin sanyin murya Khausar ta gaisheta,

Cikin sakin fuska Dijjaro ta amsa.

Ba daɗewa saiga Liman yazo sanye cikin Alkyabba kansa naɗe da hirami kusa da ƙafafun Hajja Nana ya
zaune cike da ladabi da kuma dattako yace.

“Addah Hajja ina kwana”.

Ta amsa da.

“Lafiya”.Sannan ta dubi Khausar tace.

Wannan shine Aliyu Limamin garin nan Uwarmu ɗaya Ubanmu ɗaya mutum ne mai tarin Ilimin addini”.

Cike da ladabi Khausar tace.

“Ina kwana”.

“Lafiya lau ya kwanan baƙunta?”.

Ta amsa da

“Alhamdulillah”.

Bayan tafiyarsa sai ga matansa biyu Rabi da Loddo,Kai kawai Khausar ke gyaɗawa.

Ita de Khausar ta kasa sakewa,Ahaka suka riƙa zuwa duk wanda yazo Hajja Nana zata gabatar wa da
Khausar shi.

Can saiga Yaya Abba yazo Hajja Nana tace.

“Wannan shine Abba ɗan ƙanina ne liman shi aka tura karatu birni yana karatun arnanci irin wanda kike
yi”.

Abba kuwa ƙasa da kai yayi yana murmushi.


Ita kuwa khausar kallon Hajja Nana tayi tace.

“Wai waya ce Miki karatun Arnanci mukeyi?”.

Hannu Yaya Abba ya ɗaya mata alamar tayi shiru!.

Khausar kuwa ta wani juya masa manyan Idanunta tace.

“Taya ba karatun Arnanci mukeyi ba tace karatun Arnanci mukeyi ko ance mata acoci muke zuwa
karatun?”.

Kallonta Abba yayi cikin harshen turanci yace.

“Please Khausar Enough, Don't sey anything again”.

Zare Ido Hajja Nana tayi tace.

“Abbah zagina kayi ka juya yare zaka zageni da yaren Arna!??”.

Kai Yaya Abba ya girgiza yace.

“Wallahi ba zaginki nayi ba Goggo Hajja na isa in zageki?,Ai Babana ma bai isa ya zageki ba bareni”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Oooo”.

khausar kuwa murmushi tayi tace.

“Hajja Nana zamu tafi!".

Kai ta gyaɗa alamar toh kasancewar duk sun gama zuwa, Sai kuma ta kalli Dije tace.

“Ki ɗauke ta ki zagaya da ita gidajen kowa ki gabatar da ita”.

Kai Dije ta gyaɗa sannan suka miƙe suka tafi kamar yanda Hajja Nana ta faɗa haka Dije ta riƙe zagayawa
da Khausar duk gida jen ƙannen Hajja Nana da kuma 'yan uwa aƙarshe suka shiga gida Umar Autansu
Hajja Nana...

Abakin ƙofa suka samu Baffa Umaru kallo ɗaya zaka masa kasan jarumin namiji ne mai cike da haiba da
kuma ƙwarjini.
Ya dubi Khausar da murmushi afuskarsa yace.

“Girman biredi wayon shayi”.

Murmushi tayi tace.

“Ni dai ba girman biredi bace”.

Yana dariya yace.

“Shekaranki nawa?".

Tayi murmushi da faɗin.

“Sha takwas".

Ya wara ido yace.

“A'a, ai babanki ma da kaɗan yafi haka”.

Ɓata fuska tayi tace.

Meyesa kuma zaka sa Babana?banaso shi kam baya rasu ba abarshi ya huta mana”.

Murmushi mai cike da ciwo yayi tare da janyo hannunta ya ajiye ta gefensa kana a yace.

“Ai nima Babanki mutumi nane Shiyasa duk maganata nake kawo sunansa saboda banaso amanta dashi.

Ni sa'an sane tare muka taso mukayi wasan ƙasa banaso amance shi ina so ko yaushe arika kiran sunan
sa ana masa addu'a”.

Khausar kuwa murmushi tayi tace.

“Nagode sosai Allah ya saka da alkhairi”.

“Ameen”,Ya amsa sannan ya kamata hannunta suka shiga cikin gida.

Da fara'a matarsa mai suna Adama ta yi musu sannu da zuwa sannan ta shimfiɗa musu abin zama bayan
sun zauna ta kawo musu ɗumamen tuwon shinkafa da miyar taushe sai kuma madaran shanu mai zafi.

Kallon Umaru Khausar tayi tace.


“Har matarka ta gama abinci?”.

Kai ya gyaɗa ita kuma matarsa murmushi tayi kana tace.

“Eh saboda shi jarumi ne baya son zama da yunwa kinsan shine garkuwan rugan nan”.

Wara Ido Khausar tayi tana dariya tace.

“Ba wani Garkuwa kawai de kina kurara sane”.

Murmushi Adama tayi tace.

“Shikenan duk lokacin da Arnan maƙota suka kawo farmaki zakisan shine garkuwan rugan nan".

Murmushi sukayi Dukansu sannan ya fice Khausar da Dije suka wanke hannu suka fara cin abincin bayan
sun gama ne suka tafi.

Kai tsaye Ruga suka nufa suna isa Rugar aka ɗaurewa Khausar shanu sannan Dije ta shafa mata man
shanu ayatsu saboda yayi santsi tsugunnawa tayi aka ɗaura mata ƙwayar ya akan cinyarta kana cikin
azama ta kai tatsuniya kan bakin n......!

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_Page 6_

_NA_

*AYSHA ALIYU GARKUWA*


🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*FREE PAGE*

*LITTAFIN SAKAYYAH na kuɗine, wannan Free page ne, ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin
wani a kanki 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta
WHATSAPP

09097853276.

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*

Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne
masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na
daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka
ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar
da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari
maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276
domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA
ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba
Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA


😘

*(GARKUWAR MA'AURATA)*

Cike da mamaki Sadik ke kallon yanda take ta tsar Nonon cike da tsantsar ƙwarewa da rashin tsoro.

Fuskarsa ɗauke da murmushi ya juya ya kalli Baffa Jauro kafin yace.

“Ikon Allah Baffa kalli yanda take tatsan”.

Murmushi Baffa Jauro yayi yace.

“Ai ‘yar na gadana tafi ‘yar na koya gadonta ne fa abune da ajinin mu yake in Bata iya ba ai sai muce ba
tsatson mu bace”.
Ita kuwa khausar murmushi tayi ita da kanta tana mamakin yanda ta riƙe bakin Nonon shanun tana tatsa
Shar-shar kawai Nono mai ɗumi yana zubowa.

Ƙwayar dake cinyarta ne ya cika Dije ta janye ta sake sanya mata wani cike da shauƙi da kuma jin daɗi
take cigaba da ta tsar Nonon kamar wacce tunda canma ta iya.

Baffa Jauro na murmushi ya janye ƙwarya ta biyu ya sake saka mata wani yana murmushi yace.

“Zan kaiwa Addah Hajja Nonon da kika tatsa da hannunki”.

Murmushi kawai tayi yayin da Sadik da Dije ke cigaba da mamakin ƙwarewarta.

Bayan ta tatso na ƙarshe ne Baffa Jauro yace.

“Kusha toh”.

Ita kuwa khausar ɗaga ƙwaryan tayi ta kai bakinta sai kuma ta cire kana ta mayar da kallonta kan Baffa
Jauro tace.

“Nikam bazan iya sha ba suga ba”.

Murmushi Baffa Jauro yayi tare da buɗe tandu duma dake hannunsa wanda ke ɗauke da zuma ya zuba
mata aciki kana yace.

“Toh kusha”.

Kai Khausar ta gyaɗa masa sannan takai ƙwaryar ɗanyen madaran mai ɗumi bakinta tasha sosai tana
lumshe Idanunta kafin ta miƙawa Sadik yasha kana ya bawa Dije sauran.

Bayan sun shanye suka ɗauko hanyar komawa gida.

Khausar ta ɗaga Kaita kalli gefen damanta inda taji muryar Yaya Abba, ta hango Yaya Abba da Sule yayan
Dije da take bi zaune acikin shagon caji da kuma kati wanda duk lokacin da Yaya Abba ya koma
makaranta Sule ke zama ashagon kallon Sadik da Dije Khausar tayi tace.

“Ayyah mu biya ta wajen Yaya Abba mu gaisa”.

“Toh”

Suka ce sannan suka nufi shagon kana suka gaisa.


Kallon Khausar Yaya Abba yayi yace.

“Khausar kisan yanda zaki zauna da Goggon mu kar kinayi mata gautsin baki ba daɗi gsky”.

Khausar kuwa jin abinda Yaya Abba yace yasa ta taɓe baki kafin tace.

“Ni gaba ɗaya haushin matar nan nakeji idan ita bata sani ba ita tasa na tsani zuwa Rugar nan ba abinda
yake ban haushi da Rugar nan kamar rashin wuta,Jiya duhu kamar zai kashe mutane sannan gashi ta
ajiye Kuliya aɗakinta baki ɗaya garin ba daɗi wallahi”.

Ta ƙarashe tana mai ya mutse fuska.

Murmushi Abba yayi yace.

“Shine kenan matsalar duhu na damunki!?”.

Kai ta gyaɗa masa kai da faɗin.

“Eh”.

Yace.

“Shikenan toh za'a haɗa wutan Gen.ɗin nan dana ɗakinta shikenan ko?, Saboda kar kuna samun matsala
atsakaninku bakisan yanda take son Babanki ba kema kullum zakiji tana maganarki amma ta shedeki
cewa kina da gautsin baki ke ba irin Nanne data raina bace kinga su suna mata biyayya duk abinda take
so”.

Kallon sa Khausar tayi kafin tace.

“Toh sude sunga zasu iya ne wannan ai mulkin mallaka takeyi mutum bashi da ‘yancin yin abu saida
izininta, kuma batun wuta nifa ba kwana zanyi a gidanta ba tunda naga kuliyoyi take kiwatawa”.

Kusan a tare Sadik da Dije suka haɗa baki wajen cewa.

“Ki daure ki riƙa yin abinda takeso zaku shirya”.

Shiru kawai ta musu amma bata tunanin yin haka hira suka sake taɓawa kana daga bisani sukayi wa Yaya
Abba sallama sannan suka shiga cikin gida...
Akwana atashi ba wuya yau kwanakin Khausar Biyar acikin Rugar Jauro Yaya ta fara sabawa da mutanen
garin Sosai Musamman ma Dije ta sun zama ƙawaye dan agidansu take kwana ita da zuwa gidan Hajja
Nana sai da safe take zuwa tayi mata shara sannan duk lokacin da sukaje sukayi tatsa zasu kai mata
Nono.

Kasancewar duk gidajen ƙannenta taran ne ko yaushe sukayi tatsa zasu kai mata madara Shiyasa koda
duk Rugar za'a rasa Madara da zuma ba'a rasawa a wurinta.

Kullum da rana gidan Hajja Nana Khausar ke zuwa cin abinci saboda anan ne zata zaɓi wanda ranta keso
duk sanda ta zata buɗe kwanikan ta zaɓi wanda ranta keso Hajja Nana za tace ba tasa son ƙaƙale duk
wanda ta fara buɗewa shi zata ci ita kuwa khausar tace bataji abunta haka ba domin Hajja Nana ta
kasance irin tsofi nan masu sa ido bata gani sai ta tanka to kullum cikin faɗa suke ko yaushe Dije na
maƙale da Khausar sosai Shaƙuwa ya sake shiga tsakaninsu sai kuma Ma'u yar bappa Garga sai dai ita
bata karisasu girmaba,

sannan sosai take walwala domin garin ya mata daɗi sai dai kullum cikin kewar Mahaifiyarta da kuma
ƙannenta take .

Washe gari, da safe Khausar na zaune gefen Hajja Nana tana matsa mata ƙafa.

Hajja Nana tayi saurin janye ƙafarta azabure tana watsawa Khausar kallon banza azafafe tace.

“Idan ba zaki matsa min ƙafarba aise ki bari bawai kizo kina min mugunta ba”.

Sheƙeƙe Khausar ke Kallonta da mamaki.

Ta janye hannunta daga kan ƙafar Hajja Nana tace.

“Ashe abin arziƙi yana zama na tsiya daga temako sai kiyi min ƙazafi”.

Kallon Banza Hajja Nana ta warsa mata kafin tace.

“Saboda baki da kunya nice zanyi miki ƙazafin?”.

Khausar data buɗe baki da niyyar magana ta fasa jin Sallamar Yaya Abba zama yayi tare da gaishe da
Hajja Nana cike da ladabi Amsawa tayi tana sanya masa albarka.

Kallonsa Khausar tayi tace.

“Good Morning Yaya Abba”.


Da murmushi afuskarsa yace.

“Morning Khausar how was your night?”.

“Fine”. Tace tana ɗan murmushin tsokana tasan kwanan zance,

Ai kuwa taɓe baki Hajja Nana tayi tace.

“Wato Abba ƙafara koyon munafurci irin na baƙaƙen kafuran nan ko kazo har gaba kana zagina?”.

Kai Yaya Abba ya girgiza yace.

“Wallahi ba munafurci ko zagi muke ba Goggo Hajja kawai gaisawa muke”.

Ta gyaɗa kai tace.

“Toh adai dinga magana da yaren da zanji dan Manzon Allah (S.A.W)Yayi Hani da idan mutane na zaune
wasu daga ciki su sauya harshe zuwa wanda sauran basaji koda ba zaginsu zasuyi ba amma wanda baijin
Yaren zai tsargu dan haka ku kula hegiya gantalelliya mai kaɗifiri”.

Kai Yaya Abba ya gyaɗa cike da ladabi yace.

“Insha Allah zamu kiyaye”.

Ita kuwa khausar baki ta taɓe aranta tace wannan tsohuwa ta fiye mita da takalan magana. Ta fara da
fadin Manzon Allah a karshe kuma ta buge da masifa da cemin gantalelliya.

Azahiri kuwa sai ta saki fursakarta ta matsa kusa da yaya Abba tace.

“Ayyah Yaya Abba ka sammin wayarka zan kira Mommy na mugaisa”.

Juyowa yayi ya kalleta tare da cewa.

“Ok ba matsala anjima zan baki sai Khadijah ta rakaki bishiyar ƙare zancen ka kuyi magana”.

Cikin jin dadi tace.

“Toh shikenan Nagode”.

Sallama yayi musu kana ya tafi.


Da yammaci Khausar na zaune adakali Dije kuma na shara suna hira sai da ta kammala sharan Khausar ta
dube tace.

“Dije muje ki rakini wajen Yaya Abba in karɓi wayarsa”.

Kai Dije ta gyaɗa da faɗin.

“Toh”,sannan suka fice suna hira har suka isa.

Yaya Abba kuwa yana ganinsu ya miƙe tare da zuwa kusa dasu Idanunsa akan Khausar yace.

“Kinzo”.

Kai ta gyaɗa alamar eh.

Yace.

“Ok mutafi nima zanje taya ƙanina Ibrahim ɗiban ƙwai”.

Ɗan murmushi tayi tare da faɗin.

“Yaya Abba kaima kana aikin?”.

“Sosai ma aikin gado ne ai duk da cewa ina shirin kammala degree na acikin Ɓadamaya bazai hana nayi
aikin gadona ba”.

Cewar Abba

Kai ta jinjina kana tace.

“Allah yataimaka”.

Ya amsa da.

“Ameen”.

Suna isa Gindin bishiyar Khausar ta juya ta kalli Dije tace.

“Dole sai na hau bishiyar network zai zo”.

Dije ta girgiza kai tace.

“A'a ko kan duwatsun nan kika zauna zaki samu network inde ba'a cika ba abinda yasa wasu ke hawa
bishiyar saboda kafin su zo duk an cika saman duwatsun idan kasamu ancika dole sai kan bishiyar”.

Kai ta gyaɗa kafin ta ƙarasa ainihin inda ƙarƙashin bishiyar yake Sadik ta gani zaune yana waya.
Murmushi ta sakar masa tare da zama gefensa sannan ta sanya number Mommy. ringing ɗaya ana biyu
Mommy tayi picking.

Ita kuwa khausar cike da zumuɗin jin Mommy tayi picking call ɗin tace.

“Mommy na”.

Aɓangaren Mommy kuwa jin Muryar Khausar yasa ta saki murmushi mai sanyi kafin tace.

“Khausar”.

Murmushi mai nuni da zallan farin ciki Khausar tayi tace.

“Na'am Mommy na nayi missing ɗinki”.

“Nima nayi missing ɗinki Mamana”.

Dariya Khausar tayi tace.

”Mommy Ina Raudat?,Ina Haiydar?, Ina Ramadan??”.

Murmushi Mommy tayi tace.

“Duk suna lafiya”.

Haiydar dake gefen Mommy yace.

“Gani nan Maman Fitina nayi missing ɗinki tunda kika tafi babu mai min faɗa babu wanda zai ce na
renasa sannan babu mai nuna min iko da mulkin mallaka”.

Dariya Khausar tayi tace.

“Hmmm ai nagane ɗan uwa ko ina nuna maka iko da mulkin mallaka gada nayi in faɗa maka na samu
wacce ta cuna Ni komai da ƙa'ida akeyi ko kallo zakayi sai an maka tsarin kallon da zaka yiwa mutum
shi”.

Murmushi Haiydar yayi yace.

“Allah Hajja Nana ko?”.

Dariya tayi tace.


“Ita dai fitinanniyar tsohuwa, tsohuwa sai Bala'i ba'a zaman lafiya da ita".

Mommy dake gefe ta amshi wayar da faɗin.

“Um,Um Khausar karfa ta jiki”.

Murmushi Khausar tayi tace.

“Toh idan ta jini ma ya ta iya dani bare ma tana can gida mun barta tana gyaɗa kai muku ma munzo
wajen bishiyar ƙare zancenka ne ko surutunka ne ohon musu!”.

Haiydar ne yayi Dariya kasancewar wayar a speaker yake yana jin komai yace.

“Wani irin bishiya ne kuma ƙare zencen ka”.

Ita kuwa khausar cewa tayi.

“Hmm garin fa basu da network sai wajen bishiya ɗaya suke zuwa yanzu ma haka wurin bishiyar nake”.

Dariya Haiydar yayi yace.

“Ai dama kin iya ɗale-ɗalen bishiya kina nan kamar Biri”.

Murmushi tayi sai kuma ta ɓata fuska tace.

Ni sa'arkace za kace ina tsalle kamar Biri??”.

Murmushi tare da faɗin.

“Addah Khausar Sarkin son girma kiyi haƙuri to yar uwa”.

sakin murmushi tayi kafin tace.

“Bawa Ramadan”.

Miƙa masa Haiydar yayi.

Ramadan yace.

“Addah Khausi nayi kewarki”.


Cike da ƙaunar ƙannen nata tace.

“Nima nayi kewarka ɗan ƙanina Insha Allah na kusa dawowa”.

Amsar wayar Mommy tayi tace.

“Kin Kusa dawowa haka kukayi da Hajja Nana nan?”.

fuska ta ya mutsa kana tace.

“Sai munyi da ita Mommy yau kwanana biyarfa ana shida nake idan nayi sati biyu zan dawo ai”.

Mommy tayi murmushi tace.

“Tsakaninku de ni yanzu ba ruwana nima ba bari na tayi ba”.

Dariya Khausar tayi tace.

“Ina Raudat? Su Ramadan na zuwa hadda ko?”.

Kai Mommy ta gyaɗa tace.

“Ai Asma'u ma tazo tace malamai nata tambayarki sunce taya zakiyi tafiya baki sanar musu ba kodan ba
boko ne sai hadda ne kawai wato?”.

Girarta ta ɗan shafa da yatsarta manuniya kana tace.

“Hmmm ai kuwa na faɗawa Asma'u ta sanar musu wataƙil ta manta ne”

“To ai yanzu kam sai in kin dawo.

Ki dai bi tsohuwar ahankali saboda ki samu tabarki ki dawo akan lokaci”.

Cewar Mommy.

Itako Khausar kai ta gyaɗa kafin tace.

“Toh shikenan Mommy na zanyi duk yanda kika ce. Yawwa Mommy ki turo min Number Ummin
Asma'u”.

”Toh”Mommy tace sannan ta katse kiran.

Ita kuwa Khausar juyawa tayi tare da kallon yaya Abba dake tsaye ta langwaɓar da kai kafin tace.
“Ayyah Yaya Abba in ƙara Kiran wata ƙawata?”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Ki kira ba matsala”.

“Toh”,

tace tare da maida kallonta kan wayar da text ɗin Number ya shigo copy tayi tare da dearling.

Tana kira ringing ɗaya Ummi ta ɗauka.

Khausar tace.

“Ummina”.

Murmushi Ummi tayi tace.

“A'a Khausar kece? Ya mutanen Ruga fatan kun same su lafiya?”.

“Lafiya lau Ummi. Ina Asma'u”. Cewar Khausar

“Gata nan tana tsifa”. Ummi ta faɗa tare da miƙa wa Asma'u wayar.

Asma'u na amsar wayar ta maƙala akunnenta tare da ƙyalƙyalewa da dariya tace.

“Na sani”.

Ita kuwa Khausar hararan wayar tayi jin Dariyar da Asma'u keyi tace.

“Kinsan me?”.

Asma'u tace.

“Na sani tsoron Yah Moddibo kike yasa kika gudu kika tafi Rugar nan inba haka ba keda baki ƙaunar
tafiyar nan amma daga arba dashi kika tafi Ruga”.

Ƙwafa Khausar tayi tace.

“Ba dole in tafiba tunda kika kaini kafin in dawo wala Allah ya huce”.
Cike da zolaya Asma'u tace.

“Wai ai Yah Moddibo baya mantuwa duk abinda aka masa".

Wara ido Khausar tayi sai kuma tace.

“Asma'u duk kece kika janyo min da baki kaini gidansu ba da haka bai faru ba wlh”.

Asma'u kuwa murmushi ya subce mata kafin tace.

“Calm down wasa nake Miki shi idan abu ya wuce kwana uku ma wata ƙil mancewa”.

Ita kuwa khausar jin haka yasa ta saki ajiyar zuciya da faɗin.

“Alhamdulillah". Sai kuma ta harari wayar tare da cewa.

“Au wata ƙil nema kenan”.

Dariya Asma'u tayi kana tace.

“Yaushe zaki dawo?”

Taɓe baki Khausar tayi tace.

“Waya sanma wannan tsohuwar wataƙila nan da sati biyu ko kuma sati ɗaya idan nayi sa'a tabarni in
dawo anata wuceni ahadda ko?”.

Da sauri Asma'u tace.

“Eh ana wuce ki kam”.

Ita kuwa Khausar ɗan jim taui kafin tace.

“Insha Allah nima dai na kusa dawowa”.

“Toh Allah yasa”. Asma'u ta faɗa kana sukayi Sallama tare da katse kiran.

Kallon Khausar yaya Abba yayi yace.

“Koda kuna hutun ana baku hadda ne?”.

Kai ta gyaɗa da faɗin.

“Eh Yaya Abba muna zuwa hadda”.


“To ai babu matsala inde hadda ne ki riƙa zuwa wajen Babanmu yana ƙara miki ai zai baki hadda ki
cigaba kada awuceki”.

Cewar Abba.

Khausar kuwa cike da farin ciki tace.

“Toh shikenan Yaya Abba insha Allah kuwa”.

Daga haka suka miƙe suka taho kai tsaye gidansu Abba suka nufa bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga.

Kallon Dije da Ibrahim Yaya Abba yayi yace.

“Bari na rakata wajen Liman”.

Kai suka gyaɗa sannan yayiwa Khausar jagora zuwa ɗakin Mahaifinsa bakinsu ɗauke da Sallama suka
shiga ɗakin.

Ɗaki ne irin na bukka mai shatin kwabo baki ɗaya ɗakin kewaye yake da littattafan Addini kana da
qura'anai bugu da ban bugun misira da warash.

Cike da ladibi Khausar ta gaishesa Amsawa yayi cikin sakin fuska kafin ya kalleta da murmushi yace.

“Matso mana”.

Kai ta gyaɗa tare da Matsawa kusa dashi ta zauna akan buzunsa.

Yana murmushi yace.

“Lafiya? ko dai ƙaran Addata kika kawo?”.

Murmushi tayi tace.

“Ni Meye ruwana da ita da zan kawo ƙaranta, dama karatune muna hadda Acan toh kuma na tsaya za'a
iya wuceni”.

Kai Ya jinjina kana yace.

“Wacce surah kuke?”.

Anutse tace.
“Suratul Taubah muke munyi shafi huɗu zan tashi ashafi na biyar”.

Cikin gamsuwa ya gyaɗa kai tare da faɗin.

“Karanta inda kukayi naji”.

Gyara zamanta tayi tare da gyaɗa kai kana taja sassayan numfashi cikin zazzaƙan Muryanta tayi basmala
kana ta fara rerewa karatun cike da jan Tajwidan Tartilan.

Kai Malam Liman ya jinjina da faɗin.

“Masha Allah”.

Yaya Abba kuwa lumshe Idanunsa tun lokacin data fara karatu kana ya buɗe su alokacin da takai ƙarshen
ayan yace.

“Masha Allah Allah ya baki zaƙin murya Hafiza”.

Jin abinda yace.

Yasa Khausar sakin sakin ɗan guntun murmushi

Malam Liman ne yace.

“Masha Allah, yanzu dai kullum ki ringa zuwa irin wannan lokacin kina ɗauka darasin saboda maza basu
fara zuwa ba, dalibai yara kuma sun tashi. kullum zan dinga baki awa ɗaya sai ki dinga zuwa ina ƙara miki
sannan da wasu littattafan ma idan kunayi ki faɗa zan dinga ƙara miki”.

Cikin daɗi tace.

“Toh ba matsala Insha Allah sannan munayin littafin Tajweed, Tauheed, Urasatul Nurul yaƙin, Nahwu, da
kuma Mi'atu Hadith da dai sauransu”.

Gyara zaman babbar rigarsa yayi tare da faɗin.

“Insha Allah zaku riƙa zuwa ina ƙara miki keda Dija da Ma'u tunda dama sunyi sauƙa”.

Sannan ya buɗe kur'ani ya miƙa mata shi kuma ya shiga karanta mata akai yayin da yake bin ko wanne
harafi yana basa haƙƙinsa saida yakai har ƙarshen shafin kafin ya dubeta yace.

“In mai-maita Miki?”.

Kai ta girgiza alamar a'a tana jinjina baiwar ilimi da zaƙin murya da Allah ya masa.

Anutse yace.
“Ki hadda ce su kafin gobe sannan ki kawo min”.

Khausar kuwa kai ta gyaɗa tace.

“Insha Allah zan dage Malam amman dai goben ma zan biya sai jibi a ƙara min ko?”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“La ba'as”.

Miƙewa tayi Sannan tace.

“Zan tafi da Kur'anin”.

“Toh” ya cemata

Sannan suka fice bayan fitansu ta dubi Dije tace.

“Muje gidan garkuwan rugan ki”.

Murmushi Dije tayi tace.

“Gidan Baffa Umaru”.

Kai Khausar ta gyaɗa sannan suka nufi gidan Baffa Umaru.

Aƙofar gida suka samesa yana tare da baƙi,

Juyawa yayi ya kallesu kafin yace.

“Kushiga ciki ina zuwa".

Kai suka gyaɗa sannan suka shiga cikin gidan bakinsu ɗauke da Sallama,kallon cikin gidan Khausar tayi ko
ina ashere fes-fes babu alamar datti ko ƙazanta.

Adama kuwa murmushi fuskarta ta faɗaɗa tace.

“Su Khausar ne sannun ku da zuwa”.

Dije tace.

“Yawwa Goggo Adama ya gida”.

Ta amsa da lafiya lau sannan ta miƙe ta kawo musu faten doya da ruwa arandan ƙasa mai sanyi.
Ita kuwa khausar murmushi tayi tana jinjina mutunci da karancin Goggo Adama atare sukaci kana suka
gabatar da sallan Azahar sannan sukayi mata har zuwa lokacin Baffa Umaru bai shigo ba.

Bayan fitarsu agidan Baffa Umaru Khausar ta juya ta kalli Dije tace.

“Muje gidan Hajja Nana in ɗauki kayana”.

Dije tace.

“Toh”.

Sannan suka nufi gidan Hajja Nana ba suyi wani tafiya mai tsawo ba suka isa gidan, Atsakar gida suka
tarar da Hajja Nana.

Harara Hajja Nana ta watsa mata tace.

“Ke kam Uwar gantali kina nan kina ta yawo bazan ganki ba bare in Zauna dake”.

Fuska Khausar ta ɓata da faɗin.

“Wani irin gantali duk ba gidan ƙannenki da ‘ya‘yanki nake zuwa ba kuma ɗazun nan ina anan na tashi
zaki ce amma yanzu zaki ce min gantali na tafi to nide gaskiya ba gantalalliya bace yawwa zaki wani
cemin gantali ba gidan ƙannenki na tafi ba kuma saida na faɗa miki zamuje Bishiyar ƙare zancenka in kira
Mommy na sannan yanzu ki wani cemin gantalalliya to nide wallahi ba gantalalliya bace”.

Hajja Nana tace.

“Ke kam wace gantalalliya ce ma ta fiki?,In banda gantali me kika iya?".

Ita kuwa khausar juya manyan Idanunta dake lumshe kafin tace.

“Wallahi da abinda na iya”.

Hajja Nana kuwa kai ta gyaɗa tace.

“ƙwarai da abinda kika iya fitsara ba gashi ma yanzu kina yi bayan shi babu wani abu da kika iya”.

Khausar za tayi magana Dije tayi saurin riƙe hannunta cikin ƙasa da murya tace.

“Dan Allah kiyi shiru ki ƙyaleta”.


Kai ta gyaɗawa Dije tare da tsuke bakinta.

Hajja Nana kuwa fuska ta tsuke Idanunta akan Khausar tace.

“Bari in samiki doka gidan Jauro da kike zuwa ki kwana bazan hanaki ba tunda kince kinfi farar kura
tsoro.

Amma gobe ana sallar asuba na ganki anan dan zaki riƙa tayani aiki.

Baki Khausar ta taɓe da faɗin.

“Allah ya kaimu sannan bawai ana idar da Sallah bane zanzo saina yi Azkharul sabah da kuma karatuna”.

Harara Hajja Nana ta watsa mata tace.

“Toh Al-huda-huda sarkin karatu”.

Khausar kuwa baki ta taɓe tace.

“Koma de menene”. Sannan ta juya ta shiga ɗaki ta dauko kayanta tana fitowa ne taji Hajja Nana na
cewa Dije.

“Kar kice zaki koyi rashin kunyar wannan yarinyar".

Dije kam murmushi tayi ita kuwa khausar batare data tanka taba ta fice Dije tabi bayanta...

GEMBILA

Acan ɓangare Moddibo kuwa kwance yake akan makeken gadonsa daya sha shimfiɗa na Alfarma yayin
da hannunsa biyu ke haɗa yana addu'ar bacci ya ɗauki kimanin minti goma kafin yasha fa addu'ar ya
gyara kwanciyarsa yana mai lumshe idanunsa da haka bacci ya ɗauke sa can cikin baccinsa yaji wayarsa
na ruri ya buɗe idanunsa kasancewar sa ba mutum ne mai nauyin bacci ba yasa hannu ya janyo wayar
yana kallon screen ɗin Bahrain shine sunan dake ƙasan screen ɗin.

Picking Yayi tare da kai wayar kunnensa tare da sallama.

Amsawa Jalaludeen yayi da faɗin.


“Ya yatsun ƙafar naka sun warke ne!?”.

Moddibo kuwa gyara kwanciyarsa yayi da faɗin.

“Jameel ya faɗa maka kenan?".

Jalaludeen yace.

“Kamar dai baka sanni ba sai Jameel ya faɗa min zan sani?”.

Moddibo kuwa kwanciyar sa ya gyara kana yace.

“Eh ainaga kunyi waya ne bayan abin ya faru”.

Jalaludeen yace.

“Wallahi Jameel bai faɗa min ba lokacin da abin yafaru ma ai ina nan”.

Shi kuwa Moddibo kwanciyarsa ya gyada tare da faɗin.

“Hmmm yayi kyau ka kawo mana ziyara kenan”.

“Eh nakawo muku ziyara Barka da jumma'a ai tare mukayi jam'in sallan jumma'a ma”.

Sassayan numfashi Moddibo ya fesar kana yace.

“Mungode amma aiba mu gaisa ba".

Murmushi Jalaludeen yayi yace.

“Ai zamu gaisa sai kuma na samu abin kallo ana dramer Shiyasa ba mugaisa ba, na tafi shi Kam Jameel
baima San nazo ba Dan ban faɗa masa ba”.

Kai Moddibo ya jinjina kafin yace.

“Toh yayi kyau ya labarin mutanen England”.

Jalaludeen yace.

“Duk suna nan lafiya”.


Kana sukayi Sallama.

Kallon screen ɗin wayar Moddibo yayi Aransa yace Allah mai kyauta shi Jalaludeen jinsinsa da ban amma
haka yake jin daɗin Mu'amala damu sannan babu cutarwa atsakaninmu da wannan tunani bacci ya
ɗauke sa.

Acan Rugar Jauro yaya kuwa Washe gari da Asubah bayan Khausar ta idar da Sallah tayi Azkharul sabah
da tagama ta juya tare da kollon Dije tace.

“Muje gidan Hajja Nana”.

Dije tace.

“A'a kije Ni zan dafa mana abinda zamu ci kinga Goggo Nanne bata jin daɗi”.

Kai Khausar ta gyaɗa sannan ta miƙe ta fita atsakar gida ta samu Hajja Nana ta jiƙa wankekkdn wakenta
ya jiƙa,

Zama Khausar tayi tace.

“Ina kwana Hajja Nana”.

Ba yabo ba falassa Hajja Nana tace.

“Lafiya".

Sannan ta ɗaura da cewa.

“Ga can wake ki ɗauka ki markaɗamin acan”.

Ta ida maganar tana nunawa Khausar inda ta kafa dutse irin na mutan da saboda basu da inji agarin".

Ita kuwa khausar inda Hajja Nana ta nuna mata da faɗin zatayi markaɗe ta riƙa bi da kallo kafin ta mayar
da kallonta kan Hajja Nana tace.

“Wai in markaɗa Miki me?”.

Hajja Nana tace.

“Waken ƙosai kinga kwana biyu banyi ba tunda kika zo Mai nane ya ƙare sai jiya na samu da Sadik ya
shiga Gembila ya sayo min”.
Ita kuwa khausar da Mamaki tace.

“Kamar ya in miki markaɗe?”.

Kallonta Hajja Nana tayi tace.

“Kiyi min markaɗe nace”.

Ita kuwa Khausar ƙugu ta riƙe tace.

“Ni wallahi ban taɓa ganin yanda akeyi ba ban sani ba kuma ban iya ba”.

Hajja Nana kuwa sheƙeƙe ta dubi Khausar tace.

“Insaki aiki kice baki iya ba?”.

Baki Khausar ta tura tare da riƙe ƙugu tace.

“To ban iya ba ya za'ayi na iya ni Wallahi ba zanyi ba taya ma nasan zan iya riƙe dutsen nan nace zanyi
markaɗe kije ki kirɓasa aturmi mana kawai”.

Haɓa Hajja Nana ta riƙe cike da mamaki tace.

“Ni kike cewa Inje in kirɓa aturmi Meye amfaninki Kai Allah wadaran naka ya lalace ke kam ba irin
Addarki ba sam”.

Ita kuwa khausar hannunta ta harɗe aƙirji Idanunta tsaye akan Hajja Nana tace.

“Toh yanzu tunda kinsan Ni ba irin Addah bace sai kiyi min hakuri Addah na agabanki ta girma duk wani
horonki ta iya Ni Kuma ba agaban ki na girma ba, kuma ban iya ba ya za'ayi kice min haka wata ƙil ma
bakya tuna ta kiyi mata addu'a sai in magana irin haka aya tashi kike tunata”.

Dafe ƙirji Hajja Nana tayi da faɗin.

“La'ilah ha ilallahu Muhammadu Rasulullah (S.A.W) Khausar ni zaki nunawa son Nanne?”.

Ita dai Khausar na riƙe da ƙugu sannan tace baza tayi markaɗe akan dutse ba.

Suna nan atsaye haka Baffa Umaru ya shigo ganinsu tsaye ahaka yasa yace da Khausar.
“Lafiya kuwa”.

Fuskarta babu walwala tace.

“Wai Hajja Nana ce saina yi mata markaɗe akan dutse Ni kuma ban iya ba”.

Baffa Umaru kuwa juyawa yayi ya sake kallon Hajja Nana yaga sai wurgawa Khausar Harara take Kallonsa
ya mayar kan Khausar yace.

“Ayyah Khausar ki gwada mana ba aikin mata bane”.

Da sauri tace.

“Toh ban iya ba Baffa Umaru taya zan gwada”.

Hannunta ya riƙe tare da faɗin.

“Zo in koya miki”.

Ba musu ta matsa kusa dashi ɗan dutsen ya ɗauka ya kafa sannan ya matso da roban waken ya ɗibi wake
cikin hannunsa yace.

“Ki markaɗa”.

Ta gyaɗa masa kai sannan ta fara Markaɗawa ga mamakinta sai taga yana markakaɗuwa har tayi niyyan
zagewa ta markaɗa sai ta fasa ta fara jefar da ɗaɗɗaya tasan muddin tayi mai kyau Hajja Nana zata
mayar dashi aikinta baya ga haka kuma daga riƙe dutsen yatsun hannunta sun sage tun lokacin data faɗo
daga bishiya agidansu Moddibo hannunta bai dawo dai-dai ba.

Ganin tana jefer da waken da guda-guda yasa Hajja Nana cewa.

“Hegiya gantalelliya kibar min abuna”.

Ta ƙarashe maganar tare da amsar dutsen tashiga markaɗawa.

Miƙewa Khausar tayi tare da kaɗe hannunta tace.

“Yafi Nono fari”.

Shi dai Baffa Umaru murmushi yayi tare da yiwa Hajja Nana sallama ya tafi,

Ita kuwa Khausar saurin bin bayansa tayi suka tafi adai-dai ƙofar gidan Malam Liman suka tsaya
tagaishesa cike da ladabi.

Sannan suka cigaba da tafiya suna taɓa hira har suka isa gidansa.
Adda Adama na ganinta ta sakar mata murmushi tare da faɗin.

“Khausar sannu da zuwa ya gida ya gajiyarku na jiya?”.

Murmushi tayi da faɗin.

“Ba gajiya Adda Adama ya Aiki”.

Ta amsa da.

“Alhamdulillah.

Kana tace.

“Ke kam tunda kika zo baki taɓa zuwa kin kwana mana ba”.

Khausar na gyara zama tace.

“Insha Allah yau zan zo mukwana”.

Murmushi Adda Adam tayi da faɗin.

“Aikam Nagode”.

Khausar ta juya tare da kallon Baffa Umaru dake sakin murmushi tace.

“Amma fa ki faɗawa jarumin mijinki ya kawo min abu mai daɗi”.

Murmushi kana tace.

“Inde wannan ne baki da matsala”.

Bayan sun gama hira tayi musu sallama ta tafi.

Da daddare bayan sun idar da Sallah Isha'i Khausar tace da Dije.

“Muje gidan Garkuwan Rugarku mu kwana”.

Dije tace.

“Toh muje”.

Sannan ta miƙe suka shiga ɗaki sukayi wa Goggo Nanne sallama.


Adda Amada dake ɗaki tana jin Sallamar su ta fito fuskarta ɗauke da murmushi tana cewa.

“Ai yanzu nake cewa zanbi sawunku”.

Khausar tayi murmushi tace.

“To aigamu ina Jarumin mijin naki?”.

“Yana nan mai zaki bashi?”.

“Babu abinda zan bashi abin daɗi da yace zai ajiye min zai bani idan kuma babu in tattara in tafi”.

Ta Ida maganar tana murmushi.

Miƙewa Adda Adama tayi tace.

“Toh ki kwantar da hankali ga abin daɗi”.

Tayi maganar tana ajiye musu karamin kwandon kaba dake ɗauke da Inabi, Tuffa, Mangoro, Ruman, da
sauran kayan itatuwa sai kuma kwanon farfesun kifi yana tururi.

Murmushi mai sauti Khausar tayi tace.

“Lallai yana yina ashe wannan gara haka”.

Ita dai Dije murmushi kawai take musu.

Duka suka haɗu suka ci sannan suka kwanta ɗaki ɗaya da Adama.

Shiko Baffa Umaru yana can aɗakinsa ya kwana.

Misalin ƙarfe biyu na dare Khausar ta farka aɗan firgice sakamakon hayaniya da take jiyowa.
Dije ta gani itama zaune tana zazzare idanu ganin sukayi Adda Adama ta fice aɗakin da mugun sauri
suma cikin sauri suka bi bayanta.

Da gudu Adam ta nufi ɗakin mijinta dai-dai lokacin daya fito.

Hannunsa ta riƙe cikin raunin murya tace.

“Dan Allah kada ka fita da alama suna da yawa kaji hayaniyar su”.

Da sauri ya juya ya kalleta tare da faɗin.

“Idan ban fita ba wa zai dakatar da su wannan daga ji mutanen Ƙauyen Garinga ne bamusan mai suka zo
dashi ba dare dare zasu zo mana haka babu yanda za'ayi dole in fita”.

Ta girgiza kai tare da riƙe sa kana tace.

“Dan Allah kada ka fita".

Tureta yayi daga jikinsa ya fita yana fita ya hango Arnan mutanen Garinga ne wanda yawansu zai kai
kimanin mutum ɗari da sauri ya nufi hanyar jejin yayin da bayansa ke rataye da kwari da baka hannunsa
na riƙe da touch light mai masifar haske.

Cikin fushi da tsawa ya haskasu da touch light ɗin hannunsa mai masifar kashe ido yace.

“Menene wai ma tukun ina kuka nufa!?”.

Ɗaya daga cikinsu wanda ya kasance babban su yace.

“Ƴar mu muke nema ta ɓata”.

Duk da acikin duhu ne hakan bai hana shi watsa musu kallon banza ba yace.

“Ƴarku ta ɓata shine dare-dare haka zaku zo wajenmu nemanta?”.

Biyu Daga cikin su suka ce.

“Ai kidnapping ɗinta akayi”.

Afusace yace.
“Kuma in kidnapping ɗinta akayi sai akace muku tana nan Rugarnu?”.

Babban cikinsu yace.

“Tana nan Rugarku dama Fulanin ku ai sune suka sace ta suka kawota dan haka an saceta tana nan mu
nan muke zargi”.

Cikin tsananin fushi da zuciya Baffa Umaru yace.

“Baku isa ba babu yanda za'ayi haka ya faru!”.

Babban cikinsu yace.

“Dole sai mun shiga garinku gida-gida ɗaki-ɗaki mun bincika”.

Cikin tsananin fusata Baffa Umaru yace.

“Wallahi in dai ina raye baku isa ba babu wanda ya isa yashiga garinmu yace yayi bin cike indai haka kuke
so kuje kuzo da rana muyi magana”.

Babban su yace.

“Mu adaren nan muke so muyi magana”.

Baffa Umaru yace.

“Toh baku isa ba”.

Dumfaro sa sukayi da niyyar shiga Rugar gadan-gadan.

Shi kuwa baya yaja tare da jan kwari da baka yace.

“Duk wanda yake jin shi Jarumi ne kuma ya kai to ya kuskura ya shiga mana cikin Ruga yaga abinda zai
faru”.

Tsayawa su kayi akuma dai-dai lokacin ne sauran mazan cikin Rugar suka fiffito mafi yawa ma sautin
Baffa Umaru ne ya tashe su dan shi mutum ne mai zafin gaske musamman ma idan ransa ya ɓaci.

Acan bakin ƙofar gida kuwa sosai Khausar ta shiga mamaki sai asannan ta tabbatar da maganar Adama
da tace mijinta Jarumi ne kuma Garkuwan Rugar.
Malam Liman ne yayi gyaran murya bayan isan su wajen yace.

“Tun da kunce haka yanzu ku koma da safe sai kuzo aje wajen Mai gari sai ayi magana”.

“Toh”, Babban su yace sannan suka juya suka tafi badan ransu ya soba.

Washe gari da safe bayan sunyi ta tsansu sun daddawo da hantsi Arnan garin Garinga suka zo suka haɗu
aƙofar gidan Jauro.

Bayan sun gama gaisawa Jauro ya dubesu Anutse cike da kamala irin na shugaba yace.

“Mai yafaru muna sauraron ku".

Babban su yayi gyaran murya yace.

“Ƴar muce buke ce akayi kidnapping sannan muna zargin tana cikin wannan Rugar”.

Cikin danne takaicin ƙazafin da arnan ke son yi musu Jauro ya jinjina kai kana yace.

“Kun tabbatar tana cikin wannan Rugar?”.

Kai Babban su ya jinjina yace.

“Ƙwarai mun tabbatar sannan mun zo zamu shiga Umaru ya hana mu sannan Umaru shi yake sa mana
Ido komai akayi bamu isa muyi magana ba sam Bama ƙaunar abinda Umaru yake mana yayi rayuwarsa
muyi rayuwar mu!”.

Wani banzan kallo Baffa Umaru ya watsa musu cikin yanayin zafinsa yace.

“Ba zanyi rayuwata kuyi rayuwarku ba muddin kuna so nayi rayuwata kuyi naku to ku fita sabgarmu
banga wanda ya isa ya shigo cikin Rugar mu yace zai taka mu inbar saba”.

Da sauri Jauro ya ɗaga masa hannu hakan yasa Baffa Umaru yayi shiru.

Baffa Jauro kuwa maida kallonsa garesu yayi kan yace.

“Munji mun yarda an sace muku yarinya anyi Kidnapping ɗinta”.

Sai kuma ya maida kallonsa kan Malam Liman yace.

“Ɗauko mana Bible agidanka”.


Kallon Yaya Abba Malam Liman yayi yace.

“Jeka ɗauko min asalin Bible na da acikin littatafai na”.

Miƙewa Yaya Abba yayi babu daɗewa ya dawo hannunsa riƙe da Bible ɗin ya mikawa Jauro.

Karɓa Jauro yayi tare da miƙawa Babban su yace.

“Gashi ku rantse da littafin ku tunda kuce ƴarku ta ɓata kuma tana garin nan”.

Ƙin amsa Babban su yayi.

Cikin sanyi Jauro yace.

“Inde ka tabbata ƴarku ta nan to ka karba ka rantse Inde ka rantse.

To mukuma zamu baku damar shiga sannan muma zamu rantse da Alkur'anin mu mai girma cewa
‘yarku bata nan amma duk da haka idan kun rantse zamu baku damar shiga cikin gida-gida ɗaki-ɗaki kuyi
bin cike”.

Shi dai babban nasu kin rantse wa yayi sai wuƙi-wuƙi yakeyi da ido.

Ganin haka yasa Jauro ya kalli sauran na bayansa yace.

“To ɗaya daga cikin ku ya karɓa ya rantse”.

Still suma ƙin karɓa sukayi.

Afusace Baffa Umaru yace.

“Ba gashi ba basu da gaskiya Arnan nan neman fitina suke damu sam babu gaskiya alamarin su bayan
sace-sacen dabbobi da kuke mana sai kun nemi fitina damu”.

Babban su ya juya ya kalli Baffa Umaru yace.

“Wani irin sace-sace kuma?".

Harara Baffa Umaru ya watsa masa yace.

“kana tunanin bamusan kune kuke sace mana dabbobin muba to yanzu ga Bible ka karɓa ka rantse da
littafin ku cewa ƴarku ta ɓata duk alamun rashin gaskiya ya bayyana atare da ku kawai ku taru dare-dare
kuzo mana da mugun nufi”.
Anutse Jauro yace.

“Umaru kayi haƙuri kaki”.

Yasan idan ransa ya ɓaci babu wanda zai iya shawo kansa.

Malam Liman ya dubesu yace.

“Tunda har baku rantse da littafin kuba kenan ƴarku bata ɓata ba in kuma ta ɓata to baku da tabbacin
tana garinmu”.

Babban su yace.

“Shikenan babu matsala tunda zaku iya rantse wa da littafin ku munsan bata Rugarku yanzu magana ya
ƙare.

Amma Jauro da malam Liman ku jawo Umaru kunne ya fita sabgarmu”.

Miƙewa Baffa Umaru yayi tare da nuna kansa da hannu yace.

“Ni ɗin nan ka ganni nan Babu wanda nake tsoro sai Allah daya hallicceni".

Ƙwafa Babban su yayi yace.

“Tun da haka kace shikenan amma zaka ga abinda kake tsoro”.

Da sauri Jauro ya juya ya kalli Babbansu yace.

“Mu ba mason fitina me kake nufi da zaiga abinda yake tsoro?”.

Babban su yace.

“Indai zai shiga sabgarmu to zaiga abu da yawa”.

Jauro yace.

“Toh bama son fitina tunda kuda kanku kun tabbatar da ‘Yarku bata cikin Garinmu sannan kuda kanku
kunsan baku da gaskiya kun ƙi ku rantse, karku sake shigo mana Rugar mu haka ba maso idan kuma kuka
sake to zamu haɗa ku da Sarkin cikin Gembila”.

Jin Jauro yace zai haɗa su da Sarkin Gembila yasa suka ce.

“To ayi hakuri ba zasu sake ba”.


Sannan suka juya suka tafi cike da baƙi ciki badan Umar daya hana su shiga ba adaren da sun samu
damar kwasan dabbobi damar saboda haka suka ce ansace musu ‘yarsu.

Bayan kwana biyu Komai ya lafa ba fitina da hantsi Khausar da Dije da Ma'u sun ɗebo kayan marmari
arafi suna fitowa daga cikin rafin suka hango wata mota fake agefen Rugar tasu sai kuma hango wasu
mutane biyu ɗaya ya fito daga gefen dama ɗaya kuma daga gefen hagu da gudu suka shiga motar kafin
su Dije su ƙara so sun figi motar.

Khausar kuwa sosai tsura fuskokin su ido kafin su shiga motar, sosai ta riƙe kamanninsu. sannan tabi
motar da kallo lokaci ɗaya ta riƙe Number motar Dije da sauran 'yan matan kuwa mamaki suka shiga yi
shin mai ya kawo masu motar garin sannan mai yasa da suka gansu suka gudu bayan sun san a irin
wannan lokacin, duk mazan garin basa nan makiyaya sun tafi kiwo saura kuma su tafi jeji wa'anda ke rafi
kuma sun tafi lambu jiki Asanyaye suka tafi.

Bayan kwana biyu da daddare Khausar na bacci, yayi da take ta takurewa wuri ɗaya sabida wani irin
masifeffen sayin da ake tsula musu.

A hankali taja dogon numfashi kana ta fesar a hankali tayi lib.

Can cikin baccinta kuwa cikin wani ƙaton fili mai yalce da yashi fari ƙal-ƙal tana zaune bisa wani dutse
tana fuskantar yamma kana daga bayanta kuma wani garden ne mai masifar kyau da girma babu kalan
bishiya da sirran da baya ciki, wani irin ni'imtaccen iskane mai cike da ƙamshi furanni ke buso masu wata
irin iska mai ɗan karen sanyi.

Gefen damanta ta juya ga mamakinta M Jameel ne zaune bisa wani dutse yana murmushi, da sauri ta
juya gefen hagunta kuma, Adda Adama ce ta gani zaune bisa dutse tanata murmushi.

A can gabanta kuwa Mod....! *NO EDITING*

*Kuyi haƙuri sai yanzu na samu caji gashi ba editing. KUNSHA TYPING ERRORS*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*
_Page 7_

_NA_

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*FREE PAGE NE YAN UWA, BA WAI FREE BOOK BANE! INA GAMA SAKIN FREE PAGE, KO KINGA an
fiddashi waje na satane. Na kuma Yaseen ne doguwa. Dan haka ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin
wani a kanki 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta
WHATSAPP 09097853276. Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa biya ki karanta*

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace wanda bani da haufi kansa 7k ne kacal sai dai yar musilar robace., Kana
masin Daɗi har Maɗigan yana da masigar kyau da tsatstsafo da ni'ima, wlh wasu in sunyi amfani dashi
pan biyu sabida yadda zakiyi ta tsiyaya. 5k ne Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da
ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa 8k ne, Zumar goron tula
mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da
ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi
sadidan wanda wlh koda sanyin cikin mahaifane fes yake wanke shi kuma ko mai ciki zata shashi baida
illa, kama budurwa ko bazawara duk zasu iya sha harma da yara. Set ɗin da 10k ne innkuma za'a sa miki
komai rabi-rabi ne 5k ne, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda
ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

Moddibo ta hango zaune a gefen gabas yana fuskantar tata, bima'ana yana kallon yamma, zaune yake
akan wani dutse mai masifar sheƙi kana wasu mutane biyu na tsaye gefen hagu da damansa,

Sannan da buta gabansa bisa alama Al'wala yayi domin farin yashin daya mamaye wajen daga gabansa a
jiƙe yake, kana yana mai fidda wani irin ni'imtaccen ƙamshi maisa ɗan Adam lumshe ido. Baki ɗaya haske
ya mamaye ilahirin filin wajen hakan yasa itada Moddibo suna fuskantar juna yayin da M Jameel da Adda
Adama matar Baffan Umaru suma ke fuskantar juna.

Kana lambu dake can bayanta kuwa yake feso musu iskar yammaci dana lambun suka haɗu waje ɗaya
daga sama kuma rana ne yayi Ja yana shirin faɗuwa.

A hankali ta sauƙe numfashi mai nauyi tare da lumshe idanunta.

Da sauri ta buɗe idanun nata, jin wani irin sassayan sautin dariya mai cike da shauƙi da Moddibo yakeyi.

Cike da mamaki duk suka zuba mishi idanu.

Yayinda Adda Adama ma tuni ta fara dariya mai sauti.

Ita kuwa Khausar haka nan taji jikinta yana tsuma tare da sakewa, da sauri ta juya ta kalli M Jameel ga
mamakinta shima ita yake kallo, da idonshi ya nuna mata Moddibo yana mai yin lallausan Murmushi, da
sauri ta maida kallonta kan Kekkyawar fuskar Moddibo, wacce tunda take a rayuwarta dashi bata taɓa
ganin yayi dariyar da har haƙoransa na gaba zasu baiyana ba.
“Fatabarakallahu fih hasanil khaliƙeen”.

Ta furga a saman lips ɗinta, lokacin da ta sauƙe ƙwayar idanunta kan fuskar Moddibo, da sauri ta kuma
lumshe manyan Idanunta sabida wani irin masifeffen sheƙi da ta hango sajenshi dake kwance lip-lip
yanayi,

Sautin dariyarsa da har yanzu yake ne yasata saurin buɗe idanun.

“Subahanallah, tsarki ya tabbata ga Ubangiji da ya halicci wannan bawa ya kuma bashi waɗan nan
haƙoran”.

Ta faɗa a fili lokacin da taga ƙyellin da haƙoransa keyi har yana ɗauke mata idanunta,

Lobgoɓar da kanta tayi bisa kafaɗarta.

Wani irin sassayan numfashi ta fesar tare da tsaida idanunta a kanshi.

Shi kuwa Moddibo dariya yakeyi mai sayyan sauti wanda yake da daɗin ji, har maƙolloton wuyanshi yana
ɗan haurawa yayi sama kana ya dawo ƙasa.

Yayinda ya ɗaura tafin hannunsa kan ƙirjinsa.

Cikin tsananin dariyar ya samu ya ɗan tsagaita tare da furta.

“Astagfurillah watubu ilaik”.

Sai kuma ya ɗago ya kalli M Jameel lokaci ɗaya kuma ya sake sakin dariya mai sauti yana cewa.

“Astagafitillah Wayyo cikina”.

Cikin rage girman idanunta take kallon gashin girarsa dake kwance lip.

Jameel kuwa sai Murmushi yakeyi tare da girgiza kansa.

Yayinda Adda Adama ma dariyar takeyi harda riƙe ciki.

Ita kuwa Khausar gaba ɗaya ta kasa ɗauke idonta daga kansa.

A haka har rana tayi mudun kuyanƙi alamun yana gab da faɗuwa.

amma kafin ya faɗi saiya rabu kashi biyu.


Yayinda Khausar kuwa ke zaune tana fuskantar yamma hakan yasata ganin abin.

Atake hankalin ta ya tashi ganin yanda ranan ya rabu kashi biyu.

Ita kuwa Adda Adama hannu tasa ta dafe ƙirjinta tare da faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n yau mun shiga ukun mu ku dubi yanda ranar tayi fa!”.

Tana faɗin haka duk dariya da murmushin da sukeyi ya tsaya.

Moddibo kuwa daga inda yake zaune ya ɗaga kansa sama tare da juyawa bayanshi kana a hankali yace.

“Ya Salam ya ilahi ya mujabat da'awati meke Shirin faruwa”.

Cikin tsananin gigita da tashin hankali da firgici Khausar ɗin ta saki kuka mai cike da rauni tare da cewa.

“Innalillahi wa innailaihi raji'un, hasbunallahiwani'imanwakil, mun shiga uku”.

Sai kuma ta juyo ta kalli Moddibo da ya gyara zamanshi kana a hankali yace.

“Babu abinda zai faru wanda Allah bai sani ba, Insha Allah Ubangiji zai mana maganin duk kan abinda
yayi tsanani”.

M Jameel kuwa kasa furta komai yayi sai hawaye dake kwaranya daga idanunsa.

ita kuwa Khausar ganin M Jameel na Hawaye kawai sai itama tashiga yin kuka amma ba mai sauti ba.

Cikin wani irin yanayin da bazai misaltuba Moddibo ya dubesa kafin yace.

“Haba J. Kamar ba namiji ba addu'a ya kamata muyi duk kan tsanani yana tare da sauƙi”.

Still dai M Jameel baice komai ba.

Shi kuwa Moddibo cikin sanyin jiki ya fuskanci Khausar cikin wata iriyar murya yace.

“Khausar tausayi na kike ji ne?”.

Cikin kwaranyar hawaye ta gyaɗa mishi kai tare da sakin raunataccen kuka mai cushe numfashi, lokaci
ɗaya numfashin ta ya fara cushewa yana ɗauke wa, cikin yanayi wahalar neman numfashi taga Moddibo
ya...!

Dai-dai lokacin kuwa ta farka daga baccin da takeyi ciki razana tare da kaɗuwa ta dafe kanta da takeji
yana jujjuyawa.
Kana duk da sanyi da ake tsulawa a garin wani irin zufane ke tsastsafo mata ta ko ina.

Cikin sauƙe ajiyar zuciya, ta juya gefen hagunta ta karanta A'uziyya ƙafa uku kana ta canza hannun
kwanciyar ta zuwa dama.

Sai dai sam baccin yaƙi zuwa mata, sai ta kama karatun Alqur'ani cikin sassayan sauti,

Cikin ikon Allah ta samu bacci ya kuma yin awon gaba da ita.

Baki ɗaya Wunin wannan ranan akasalance tayi koda abinci ta kasa ci haka zalika koda yawan surutu sai
ta rage sosai mafarkin ya tsaya mata arai da zaran ta tuna irin mafarkin da tayi sai taji zuciyarta ta buga
da ƙarfin gaske.

Da daddare cikin ikon Allah data karanta Alkur'ani mai girma tare da bin haddarta da Malam Liman ya
bata sai taji sauƙin abin aranta duk da kuwa bawai ta daina jin tsinkewar zuciyar bane amma ya ragu
sosai.

Da misalin ƙarfe takwas da rabi na dare Khausar suna zaune a farfajiya gidan Hajja Nana su uku ita Yaya
Abba da kuma Dije suna hira jefi-jefi take sanya musu baki aciki daga ƙarshe ma ta miƙe tace zata je ta
kwanta sai Dije ma ta miƙe ganin haka yasa Yaya Abba ya musu rakiya har gida.

Washe gari:Da safe still haka Khausar ta tashi bata da wani ku zari koda abinci ne ta kasa ci iyakacinta
tasha Tea ko ruwan kunu sannan ta kasa faɗawa kowa irin mafarkin da tayi domin jikinta ya mutu sosai
da mafarkin.

Da daddare ba kinta ɗauke da Sallama tashiga gidan Hajja Nana.

Asaman laɓɓa Hajja Nana ta amsa mata Sallamar tana binta da harara dan tunda taƙi markaɗa mata
wake take jin haushi ta.

Ita kuwa khausar bata masan Hajja Nana nayi ba ta nemi waje ta zauna tare da kallon Hajja Nana tace.

“Yunwa nakeji ki bani abinci zanci”.

ta faɗa tana kallon ƙorenta dake jere guda goma sha Uku.

Harara Hajja Nana ta wurga mata tace.

“Gashi ki ɗauka ki ci”.


Kai Khausar ta gyaɗa tare da Matsawa jikin ƙoren tashiga buɗewa ɗaya bayan ɗaya tana dubawa saboda
taga gidan Malam Liman anyanka kaji cikin Sa'a kuwa tana buɗe ɗayan taga Jan miyar dage-dage da
kuma tuƙeƙƙen tuwon shinkafa.

Ta gyara zamanta tare da wanke hannunta ta fara cin tuwon cikin Mintuna kaɗan ta cinye tass sannan ta
kuma janyo wani Ƙoren dan sosai take jin yunwa sannan bata wasa da cikinta dan ita dai ko ciwo bai cika
hanata cin abinciba karo na forko kenan a rayuwarta da abu ya tsaya mata a rai har ya hanata cin abinci
na kwana biyu son ta Tara yunwar shiyasa.

ta cinye ƙore biyun tas dan dama tuwon ba wani mai yawa ake samata ba tunda akwai yawan kanukan.

Hajja Nana kuwa juyawa tayi da mamaki ta kalleta kafin tace.

“Yanzu har kin cinye tuwon nan”.

Kai Khausar ta gyaɗa mata tace.

“Na cinye mana kuma yanzu ma ƙarawa zanyi dan yunwa nakeji rabo na da abinci tun shekaran jiya da
daddare fa sai dai in ta Shan abu mai ruwa-ruwa”.

Taɓe baki Hajja Nana ta kuma yi tace.

“Toh bubbuga rumbu ga shican ki ƙara ki cinye duka ma in Kinga dama”.

Ta Faɗa tare da tura mata wani akoshin.

Ɗauka Khausar tayi kamar wasa ta cinye dake abincin ba wani da yawa ake sawa aƙoron ba dake sun san
cewa ƙorenta da yawa mafi yawan lokuta ma loma ɗaɗɗaya takeyi ako wani ƙoren idan tayi loma sha
uku ya wadatar mata a dai cikin tsohuwa ta kuma tsinci nama ta cinye to shiyasa ba'asa mai yawa.

Ita kuwa Hajja Nana ganin yanda Khausar ke cin abinci yasa tayi zaton gatse take mata ta harareta da
faɗin.

“Mutum kamar jaki wannan ci haka ki cinye wannan ƙoren ki cinye wancan”.

Ta ida maganar tare da sake tura mata wani ƙoren.


Ita kuwa khausar ta ƙoshi amma saboda ta ƙular da ita yasa ta janyo ta buɗe naman kan abincin ta cinye
sannan ta gutsiri kamar loma biyar ta zuba akwanan dake empty.

Wani kwanon Hajja Nana ta kuma tura mata still ta cinye naman ta kuma gutsura ta zuba a sauran
kwanon.

Hajja Nana ta dube ta cikin tsareta da ido tace.

“Wai har yanzu baki ƙoshi ba?”.

Khausar cikin yamutsa fuska ta gyaɗa kai kana tace.

“Eyyy ban ƙoshi ba”.

Wani akoshin Hajja Nana ta sake tura mata, Khausar kuwa laluma ta cigaba dayi idan taji da nama ta
cinye ta gutsits-tsira tuwon ta bari.

Ita kuwa Hajja Nana kamar wacce akace ta leƙa taga aika-aikan da Khausar keyi da tuwon ta miƙe cikin
fushi tace.

“Shegiyar yarinya gantalelliya ni kike nunawa barikanci, 'yar banza kinje kin zauna gidan Mayu kema kin
koma kamar Mayya, sai cin nama kamar kura, wato ma duk naman kike lalubewa dan mayta ai dai na
sani in dai ba cikin zanine da keba ai yaci ki ƙoshi”.

Ya mutsa fuska Khausar tayi tare da riƙe ƙugunta tace.

“Naci ɗin idan ni Mayya ce kinsan inda na samu maita, tunda nazo saboda shegen maƙo ko zabuwa ɗaya
kin kasa yanka min gaki da Zabbi kamar zasu kashe ki ga shanu kuma aina Babana ne”.

Salati Hajja Nana tayi tare da fashewa da kuka.

Kasancewar duk dare aƙofar gidan ta suke zama yasa Baffa Umaru daya ji sautin kukan ta ya miƙe
kasancewar Allah ya bashi kunne komai ƙanƙantar sautin abu ya kan iya ji.

Ganin Hajja Nana na kuka yasa Baffa Umaru nufarta tare da cewa.

“Addah Nana Meya faru?”.

Nuna Khausar tayi da hannu kana tace.


“Wannan ‘yar Usmanu har zata min gori wai gadon Ubanta na riƙe kaji shegiyar gantalalla yarinya dan
ma Allah yayi dan ke macece!”

Ƙasa da murya Baffa Umaru yayi yace.

“Dan Allah Addah Nana kiyi haƙuri kinsan yarinta ke damunta idan ta girma ba zatayi ba”.

Ya ida maganar tare da jan hannun Khausar suka fice waje.

Bayan sun fita ya juya ya kalleta yace.

“Haba Khausar kidena ki koyi yanda zaki zauna da manya kinga Addah Nana tsufa ya kamata tana
buƙatar rarrashi da lallami, kinga duniyar nan ba matabbata bace idan yau kaine gobe ba kai bane ita
rayuwar nan bata da tabbas, ki koyi magana mai daɗi ke idan Mahaifinki ina ita fa ɗan ta ne data haifa
acikinta kuma ɗan ta mafi soyuwa agareta kada ki sake haka kinji Khausar am”.

Ta gyaɗa masa kai da faɗin.

“Toh shikenan Insha Allah bazan sake ba”.

Ya shafa kanta yana murmushi yace.

“Allah ya miki albarka kizo muje gidana mu kwana zansa ayanka miki Zabbi kici tun da mun gama cin
abinci".

Kai ta gyaɗa tare da yin murmushi tace.

“Toh”.

Ya riƙe Hannunta suka tafi suna tafiya suna hira har suka isa gidan bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga
gidan Adda Adama ta fito daga ɗaki tare da amsa musu sallamar.

Kallon Adama Baffa Umaru yayi yace.

“Akwai nama ne?”

Adama tace.

“Eh akwai Zabbin da aka yanka da yamma yanzu nake ƙarasa dahuwarsu”.
Yace.

“Toh shikenan ki ƙara sa gyarasu ki kawo ma wannan Kuran Birnin taci”.

Dariya Khausar tayi tana zama akan taburman da Adama ta shimfiɗa musu, shi kuma Baffa Umaru ya
zauna daga gefenta yayin da Adama taje taci gaba da aikinta kasancewar farin wata ya haska ilahirin
garin.

Anutse Baffa Umaru ya kira sunanta da faɗin.

“Khausar”.

Ta ɗago kanta tana kallon fuskarsa acikin farin watan kafin tace.

“Na'am”.

Idanunsa kanta yace.

“Kinsan kamannin Babanki?”.

Kai ta girgiza masa tare da faɗin.

“A'a bansan kamanninsa ba”.

A sanyaye yace.

“Amma kin san akwai Baffanki ai yayan Babanki Hammadu Ɓadamaya ko?”.

Tace.

“Eh amma Ɓadamaya yake ko?”.

Yace da ita.

“Eh yana can Ɓadamaya dashi da Iyalansa da kuma ahalinsa gaba ɗaya.

Insha Allah wataran Zakije shida Babanki Uwa ɗaya Uba ɗaya".

Kai ta jinjina da faɗin.

“Eh Mommy na tafaɗa min cewa inada Baffa yana can Ɓadamaya dashi da matarsa da kuma ‘Ya‘yansa”.
Murmushi yayi yace.

“Toh idan kinje zaki ga mai kamannin Mahaifinki sak da sakin sunan sa Aliyu shine yake kama da
Mahaifinki ya gaji Babanki komai da komai kuma shine aka aurawa yayarki Nenne”.

Kai ta gyaɗa tace.

“Toh yaushe zanje in gansa?”

Yace.

“Kinga kamannin Mahaifinki kamar balarabe kinga ba yabon kai ba mutanen Rugar mu duka kyawawa ne
amma kyawun mahaifin ki ya fita da ban farin Mutum ne kyakkyawa ga kuma gashin kansa mai tsawo da
sheƙi wannan gashin naki ma shi kika ɗauka”.

Idanunta ta lumshe cike da kewar mahaifinta sai kuma ta buɗe su tace.

“Aikam nasan gashin sa na ɗauka ba Mamansa ba da kai agwagwiye".

Murmushinsa ya faɗaɗa da faɗin.

“Ina Addar tawa kike yiwa ba'a itama tsufa ce yasa gashinta kaɗewa”.

Murmushi tayi tace.

“Ai lalle kam”.

Sai kuma ta dai-dai-ta nutsuwarta tace.

“Ku kuma dama nan ne asalin Rugarku?”.

Kai ya gyaɗa mata yace.

“Eh asali nan ne Rugar mu iyaye da kakanni”.

Tace.

“Toh Meyesa ita Hajja Nana ta dawo nan kuma ina ne asalin garinsu Babanmu?”

Murmushi yayi yace.

“Asalin garinsu Babanki yana da nisa lokacin da Addarmu tayi aure ta daɗe kafin tazo ta samu haihuwa
to data haifi na farko sai Allah ya sake kawo wasu akan lokaci ta haifi yara uku sai Allah yayiwa kakanki
daya haifi Babanki rasuwa,sai ta nemi zata dawo to data nemi zata dawo sai sukace tabarmu su yaran ita
kuma tana son yaran sosai sai tace Inde akan dukiya ne tabar musu duka subarta ta taho da ‘Ya‘yanta”.
Zama Khausar ta gyara tana sauransa da kyau.

Shi ko a hankali ya cigaba da cewa.

“Dake dangin Mahaifinki mutane ne masu karamci sai sukace su ba dukiyar su suke buƙatar ba kawai dai
suna so suriƙa ganin ɗan uwansu ne sannan ita macece kada subar mata nauyi amma tunda tana son
Zama da ‘ya’yanta baza su hanata ba sai suka bata duka gadon Mahaifinki da kuma na Baffanki da
ƙannensa mata biyu hadda mai sunanki.

A ranar da tashigo Rugar nan tashigo da aƙalla shanu sun kai ɗari biyu sannan harda raƙuma da tumakai
duk gadon sune aka ɗauka aka basu suka dawo”.

Sassayan ajiyar zuciya ta saki tana jinjinawa lamarin.

Baffa Umaru ya cigaba da cewa.

“Toh tun daga lokacin ne zamanta ya dawo nan daga baya Allah yayiwa mahaifan mu rasuwa da gida
huɗu ne kacal anan mahaifinmu su suka fara kafata da duk nan dajine mahaifinmu ne ya sare bayan
rasuwar mahaifinmu da kuma mahaifiyarmu,

itace ta zame mana Uwa da uba tun muna yara itace ta renemu nida Mahaifinki mun taso tare atare
mukayi wasan ƙasa ta raine mu tare ta zame mana kamar uwa Shiyasa mu awajen mu Adda Nana ba ya
bace kaɗai uwa ace a garemu”.

Ita kuwa khausar Ajiyar zuciya ta kuma saki tare da faɗin.

“Ikon Allah Allah mai iko Mabuwayi Gagara misali”.

Murmushi Baffa Umaru yayi yace.

“Kin gane ko mu Addah Nana Uwace agaremu ba Ya ba sannan maganarta Umarni ne awajenmu muda
‘Ya’yanmu babu mai saɓa mata har jikokin mu kinga keda kika zo kina wannan abin sai akaga lallai ta
samu karan tsaye”.

Murmushi Khausar tayi tace.

“Lallai dai kam,to amma ina ne asalin su Babanmu?”.

Murmushi yayi yace.

Gobe zan faɗa Miki Idan Allah yakaimu rai da Lafiya zan ƙara sa baki labarin insha Allahu”.
“Toh Allah ya kaimu goben lafiya”. Cewar Khausar

Cikin sauƙe numfashi yace.

“Naji ma Addah Nana na cewa kafin ki koma Abbah zai kaiki Ɓadamaya kije kiga Baffanki da ‘Ya‘yansa”.

“Toh ina kuma ance da nisa?”.

Khausar ta tambaya

“Eh danisa amma ai tafiyar wuni ɗaya ce zaku isa”.

Ya bata amsa.

Miƙe sawunta tayi bisa taburmar tare da cewa.

“Toh shikenan ba matsala, Insha Allahu zamuje, nima ingansa sannan kodan inga mai kama da Babana”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Sannan kuma kafin ku tafi zakuje kiga Addarki ‘yar Baffanki da yake Ɓadamaya tana nan Rugar Fulani
dake ma ƙobtanmu Adda Ikki aikin santa?”.

Murmushi tayi tare da gyaɗa masa kai tace.

“Eh na santa ai itakam tana zuwa har gidanmu ta dubani duk dangin Babana ma ita nafi sani”.

Yace.

“Toh shikenan Zakije wajenta kiyi kwana biyu”.

Tace.

“Tun kwanaki nake cewa Hajja Nana zanje in dubata, tace min ba yanzu ba, wai in bari ingama sanin
mutanen garin nan”.

Adama dake sauraron hiransu ta miƙe hannunta riƙe da kwanan da ta gama gashin Zabbin dake ta
tashin ƙamshi sannan ta haɗo musu da madara mai ɗumi.

Akan tabarmu ta ajiye musu su duka ukun atare sukaci.


Gyatsa mai sanyi Khausar kana tace.

“Kai gaskiya naci naji daɗi Nagode”.

Bayan sun kammala ne Khausar tashiga ɗakin Adama ta kwanta Adama kuwa ta nufi ɗakin mijinta suka
kwanta tare.

Can cikin dare kamar misalin ƙarfe biyu Baffa Umaru ya miƙe zaune, tare da kasa kunnensa sosai wanda
hakan ya kasance ɗabi'arsa ne,

domin shine Garkuwar Rugar tasu, jin motsin tashin sa yasa Adama miƙewa ita ma ta zauna, kusa dashi
tana faɗin.

“Lafiya”.

Ajiyar zuciya ya saki da faɗin.

“Naji tsayuwar mota daga can nesa sannan naga haske yashigo har cikin garin nan kamar da akwai wani
abu ko dai munyi baƙi ko kuma wani abu!".

Ahankali tace.

“Toh yanzu fita zakayi kenan?”.

“Dole in fita ai Adama idan ban fita ba ‘yan uwana zan bari wani abu yazo ya ritsa da mune ai bazan bari
ba dole in fita inga ko menene”.

Ya faɗa a hankali.

Ita kuwa Adama riƙe hannunsa tayi fuskarta na bayyanar da tashin hankali tace.

“Nikam ina tsoro wallahi”.

Da sauri yace.

“Kada ki damu Insha Allah babu abinda zai faru wanda Ubangijin bai sani ba”.
Kai ta girgiza kana tace.

“Kai rashin network ɗin garin nan yana damun mu wallahi, kaga da akwai network tunda yawanci kowa
yana da waya zaka kik kira su awaya kowa ya fito kaga idan yaso sai sufito ku haɗu Atsakiyar garin amma
Ni ina tsoron fitarka kai kaɗai”.

Suna cikin Maganar ne sukaji antura ƙofar gidansu anshigo Murfin ya fadi ƙasa Kifff kasancewar ba wani
Murfin kirki bane gadon kara ne da gwafa aka haɗa.

Cikin han zari ya mike ya tsaya.

Itama miƙewa tayi da saurin ta riƙe hannunsa tace.

“Fita zakayi dan Allah kada ka fita ka tsaya dan Allah kar ka fita”.

Ya juya ya fuskanceta yace.

“Ya kike so inyi idan ban fita ba kina jifa anshigo gidan nan”.

Yana ida maganar ya fin cike hannunta dake cikin nasa ya fita.

Cikin sauri ta shari gabansa ta fito ya zama na itace agaba shi yana bayanta.

Suna fitowa idanunsu ya sauƙa akan mutanen uku dake sanye cikin baƙaƙen kaya hannunsu riƙe da
bindigi da kuma toch ligh mai masifar haske.

Arazane Adama tace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin”.

Ƙaran buɗe ƙofa da kuma sautin Muryan Adama ne ya fito da Khausar daga ɗaki wacce farkawanta babu
daɗewa tana fitowa sukayi saurin kashe mata ido da hasken toch ligh dinsu ita da Adama.

Cikin daga Murya suka ce da Adama

“Ki matsa agabansa kada jini ya taɓa ki ki matsa kada mu illataki!”.

Aruɗe tace.

“In matsa agabansa!?Bazan matsa ba, ku suwaye ne? sannan me kuke nema? me kuka zo yimana acikin
daren nan?”.
Ɗaya daga cikin sune yace.

“Kashe sa muka zo yi!”..

Cikin tsananin tashin hankali tace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n hasbunallahiwani'imanwakil.

dan Allah kada ku kashesa,me yayi muku zaku kashe sa?,Meyesa?”.

Ɗaya daga cikinsu ba wanda yayi magana da farko ba yace.

“Saboda yana hanamu rawan gaban hantsi zamu kashe sa muga takan tsiya bashi yace taurin kai ba”.

Baffa Umaru kuwa murmushi yayi mai cike da Jarumtaka da kuma rashin tsoro yace.

“Ni zaku kashe?,To idan kunga na mutu kwana nane ya ƙare,Kuma Ubangiji shi ya ɗauki raina.

Amma ku baku isa ba babu mai rayawa babu mai kashewa sai ubangiji.

Dan haka raina baya hannunku kuma ajalina baya hannunku idan kunga na mutu ma kada kusa aranku
ku kuka kashe ni!”.

Ya ida maganar tare da zabura zai shiga ɗaki dan ɗauko kwari da bakasan.

Ita kuma Adam da saurin riƙesa dai-dai lokacin da suka harbesa akafaɗarsa na dama.

Ƙaran harbin ne ya tashi gaba ɗaya ilahirin mutanen garin Aɓangaren Hajja Nana kuwa tana tashi daga
bacci sanadiyyar ƙaran harbin ta dafe kanta da faɗin.

“Wayyo Umaru na Allah ka kare mana Umaru” domin shine mutum na farko daya faɗo mata arai cikin
rawan jiki ta miƙe tare da ɗaukar zaninta ta ɗaura kana ta ɗauki mayani ta yana.

Aɓangaren Baffa Jauro yana miƙewa yace.

“Umaru”.

Ya kira sunan sa cikin daga murya.

Baki ɗaya ‘Yan uwansu da sauran jama'a babu wanda ya faɗo masu arai sai Baffa Umaru ko wannensu
daya farka zai ce.
“Wayyo! Umarunmu”.

Shi kuwa Umaru juyawan da zai yi sai suka samu damar sake harbinsa ahaƙarƙarinsa na hagu.

Cikin ƙarfin hali da ɗaga sautin Muryar sa yace.

“La'ilah ha Illallahu Muhammad Rasulullahi(S.A.W) Adda Nana ki yafemin yau kam zasu kashe ni ki
yafemin kece madadin Uwa awajena duk abinda nayi ki yafemin yau kam sun kasheni sun kashe ni,Yaya
Jauro, Yaya Sadu, Yaya, GarGa, Yaya Liman, Yaya Garba,Yaya Sale yau kam sun kasheni sun cire muku
ɗaya cikin goma kun zama ku tara!”.

Adama kuwa Aruɗe ta riƙesa jikinta na kyarma taja numfashi amma ta gagara sakewa.

Ita kuwa Khausar numfashin taja amma ta gagara sakewa saboda tsananin ruɗu da tashin hankali da
tashiga kamar zata shiɗe!.

Ihun da kiran sunan da yake yasa suka janye toch ligh ɗin su dake fuskar Khausar da Adama suka mai
dashi sama wannan dalili ya bawa Khausar damar kallon fuskokinsu da kyau amma baki ɗaya jikinta ya
sandare bata da wani kataɓus ɗin motsawa.

Su kuwa ƙirjinsa suka saita suka sake harbinsa akwai wani ƙaton tukunya agefen ya ratsa ya ɓula.

Shi kuwa Baffa Umaru ƙirjinsa ya dafe da faɗin.

“Laila Ha'illalhu Muhammad Rasulullahi (S.A.W)” Shikenan rai yayi halinsa.

Su kuwa mutanen garin baki ɗaya gidan Baffa Umaru suka nufo ko wannensu na rataye da kwari da
bakansa sukuwa jin hayaniyar mutanen yasa suka ɓulla ta bayan gidansa suka fice tare da zuwa inda
suka bar motarsu suka shiga.

Shi kuwa Baffa Umaru ta cikin tukunyar gefensa ya faɗa jini nata ɓulɓula.

Hajja Nana ce farkon shigowa yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa tana isa tsakiyar gidan,

Ƙofar dakinsa ta nufa, tana isa inda yake ta janyo gawar ta rungume tana kuka tare da faɗin.

“Umaru! Umaru!! Umaru!!! Yau kuma mai zan gani gawar Umaru zan riƙe ahannuna kamar yanda na
riƙe gawar Usmanuna!”.Cikin kuka sosai take maganar.
Su Baffa Jauro da sauran mutanen ne suka shigo sudai Allah Allah suke su ƙarasa cikin gidan suga abinda
ya faru dashi sam basu yi tunanin bin bayan mutanen ba.

Ita kuwa khausar hanyar da suka bi suka fita take nuna musu da yatsa ta kasa furta komai bare kuma ta
taɓuka wani abun Yaya Abba ne da ya shigo yace.

“Yayane Khausar!?”.

Cikin matsananci kuka da tashin hankali tace.

“Yaya Abba sun gudu sun kashe shi sun gudu sunbi ta nan na gansu sunbi tanan!”.

Azabure Matasan suka bi wajen ina tuni sun shiga motarsu sun gudu sukuma su Baffa Jauro, Baffa, Sadu
da sauran rungume gawar ƙaninsu sukayi suna kuka.

Hajja Nana kuwa tattaɓa jikinsa tayi, Sadik yace.

“Baba mu ɗaukesa mu kaisa asibiti”.

Sake rungume gawarsa Hajja Nana tayi tace.

“Saddiƙu wani asibiti zamu kaisa bayan sun kashe sa baya numfashi bashi da rai!?”.

Jauro ne ya karɓesa ya duba shima ya rungumesa ganin ya rasu Baki ɗayan su akan Gawarsa suka kwana.

Ita kuwa khausar gaba ɗaya ta rikice ta duburburce bata taɓa gani ankashe mutum agaban ta ba sai
lokacin tayi kuka har ta godewa Allah manyan Idanunta sunyi luhu-luhu dasu ba abinda ke faɗo mata
arai kamar yanda sukayi hira dashi.

Washe gari akaje aka kira

Ƴan sanda acikin gari suka je sukayi bin cike tare da rubuce-rubucen su na banza da wofi sannan akayi
masa sallah aka kaisa gidan sa na gaskiya.

Kana akazo aka zauna zaman makoki, Addar Khausar Ikki da zata je wajenta a Rugar Fulani ce tazo da taji
labarin rasuwar Baffa Umaru tana zuwa kai tsaye gidan Baffan Umaru ta nufa duk ‘yan uwan suna can
suna karɓan gaisuwa.

Khausar na ganinta ta tashi da gudu ta Rungumeta tana kuka tace.


“Addah Ikki agaba na agabana fa suka kashe shi sun harbesa sun kashe sa ya rasu har lahira!”.

Addah Ikki tace.

Kiyi shiru Khausar duk mai rai mamacine addu'ar mu yake buƙata”.

Kai Khausar ta gyaɗa amma ta gaza tsaida kukan ta Ganin haka yasa Addah Ikki taja hannunta suka fita
zuwa gidan Hajja Nana.

Suna Shiga Khausar ta tsaya cikin Muryanta daya dishe da kuka tace.

“Ni ina tsoro bazan shiga ɗakinta ba akwai kuliya”.

Addah Ikki tace to kitsaya na koreta sannan tashiga ɗakin ta fito da kuliyar tasa awani ɗaki ta rufe.

Sai asannan Khausar ta yarda tashiga ɗakin bayan sun zauna Addah Ikki ta zauna ta riƙa yi mata nasiyya
tare da kwantar mata da hankali.

Yaya Abba ne ya ɗauki wayarsa ya tafi Bishiyar ƙare zancenka ya kira duk dangi na nesa ya riƙa sanar da
su har ya kira Baffa Hammadu na Ɓadamaya ya sanar masa.

Shima washe gari Baffa Hammadu ya ɗauko iyalansa baki ɗaya suka taho da yammaci gab maghariba
motocinsi su guda biyu ajere suka shigo Rugar kai tsaye ƙofar Hajja Nana suka nufa sukayi parking
motocinsu.

Ita kuwa Khausar na cikin ɗakin Hajja Nana manne da jikin Addarta Ikki suka jiyo Sallama,

Addah Ikki ce ta miƙe da faɗin.

“Laaa Umma na sannan sai Baffanta yashigo daga bayansa kuma wani kyakkyawan matsakaici mutun ne
fari ƙal kamar balarabe yayin da Yaya Abba ke biye dasu abaya.

Durƙusawa Khausar tayi tare da fashewa da kuka kalaman Baffa Umaru ne kawai keyi mata suwwa
akunne.

Rarrashinta Addah Ikki ta shiga yi tana bata haƙuri da kyar ta tsaida kukan tace.

“Addah Jiya da daddare Baffa Umaru kece min Baffana na Ɓadamaya yana da wani ɗan sa dake tsananin
kama da Babana Addah Ikki wannan shine ke kama da Babana?”.

Cikin matsanancin kuka ta ida maganar.


Kai Addah Ikki ta gyaɗa mata alamar Eh.

Ita kuwa khausar kanta ta kife acinyar Addah Ikki ta cigaba da rera kukanta.

Baffan Hammadu ne ya riƙe hannunta ya cewa.

“Khausar kiyi shiru kada kiyi kukan rashin Uba nima Mahaifine agareki ni zan tsaya Miki madadin Uba
ako ina dan dai Banason rabaki da mahaifiyar kice Shiyasa na barki kike zaune tare da ita muddin ina
raye zan maye Miki gurbin Uba”.

Cikin raunin murya tace.

“ Baffa Allah hokke sabbugo”.

Ameen thumma ameen suka amsa.k

Kana suka tafi gida Baffa Umarun.

Bayan angama zaman Makoki Khausar tabi Addarta Ikki can Rugar Fulani tayi kwana biyu sannan suka
dawo bayan sun dawo akayi addu'ar bakwai Baffanta na Ɓadamaya yafara shirin tafiya sai asannan
Khausar taga sauran ‘ya‘yan sa daya zo dasu harda Mata bayan sun sake ganawa ne suka tafi.

Akwana atashi ba wuya Khausar ta cika Makwanni uku Arugar Jauro yaya yayin da Baffa Umaru keda
mako biyu da rasuwa kullum ‘Yan uwansa matarsa kuma jama'ar gari cikin yi masa addu'a suke domin
baza su taɓa mantawa dashi atarihin rayuwarsu ba da kuma irin gwagwarmayar da yayi adomin kare
rayukansu.

GEMBILA

Acan ɓangare makarantarsu Khausar kuwa ayaune aka gama gyara ilahirin makarantar daga nesa idan ka
hango ginin ba zakayi zaton cewa a Gembila makarantar take ba koda a ƙasashen turawa ne sai ’Ya’yan
wane da wane saboda yanda aka ƙawata ginin Makarantar fentin ya kasance Maroon and White haka
zalika gate din Maroon anda white ne daga sama An rubuta

*Al'ANSAR ACADEMIC SCHOOL* Rubutun ma Maroon and White ne.


Acikin harabar makarantar kuwa Moddibo ne tsaye hannunsa harɗe aƙirji ya yinda manyan idanunsa ke
lumshe yana kallon tsarin ginin Makarantar da akayi wani irin Up stair cycle daga cikin harabar
makarantar zagaye yake flowers masu kyau da tsari.

M Jameel ne yace.

“Gaskiya Moddibo kayi ƙoƙari makarantar yayi masifan tsaruwa”.

Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙarawa fuskarsa kyau yace.

“Masha Allah haka akeso”.

Ya ida maganar tare da juyewa cikin nutsuwarsa yake tafiya har suka fita acikin harabar makarantar suka
shiga motarsu dake gefe afake.

Moddibo ke Driving yayin da M Jameel ke gefen mai zaman banza ƙira'an Sudai's na tashi cikin suratul
Nisi'i Moddibo kuwa jinjina kai yayi ayoyin na ratsa sa.

M Jameel ya juya ya kalli Moddibo da bakinsa ke motsi alamar karatun yake bi yace.

“Moddibo kamar akwai motar dake bin mu fa”.

Kai Moddibo ya girgiza yace.

“A'a ba binmu akeyi ba”.

Kai M Jameel ya gyaɗa still yana kallon mirror bai dai ce komai.

Daga nan suka ci gaba da tafiya ganin still kamar binsu akeyi yasa Moddibo ya tsaya.

Ga mamakin su ganin su tsaya yasa wancan motar tayo kansu gadan-gadan...!

*Wasan fa yanzu aka farashi. Bakin zaren labarin sun kai 12 dozi. Kenan. Akwai ababen dake a duhu fa.
Saninsu sai kun bibiyu Al'ƙalamin Shatu yar Aliyu Garkuwa. Jikar Muhammad Babayo Maiturare. Kana
kuma (BODDIN DEDDE)*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️
*SAKAYYAH*

_Page 8_

_NA_

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*Free page ne ƴar uwa in sun ƙare ko kinga littafin SAKAYYAH a a waje ba a cikin Groups na na
SAKAYYAH ɗin da nabuɗeba, toh na satane kuma na Allah ya isane, kana na Yaseen doguwane😂
bulluƙutu kuma baƙar mutuwa... Dan haka biya ki karanta cikin Salamah yar uwa ba haƙƙin kowa kanki,
littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar
biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ki karanta abinki Nana lfy fata lfy*

Masu son kayan Ɗa'a akwaisu Available.

Motar tayo kansu gadan-gadan.

Aruɗe M Jameel yace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!Hasbunallahu wani'imal wakin!! A'a su waye wannan suna da hankali
kuwa!?”.

Cike da al'ajabi Moddibo ya zuba musu ido tare da ƙoƙarin yiwa motar key sai kuma ya gaza yin komai ya
zubawa motar ido ganin gada-gadan fa ta nufi kansu haiƙan ƙadaran.

Sai da motar tazo gab dasu sai kuma ta kauce ta hau titi ta wuce.

Wani irin nannauyan ajinyan zuciya mai masifan ƙarfin M Jameel ya dire tare da meda kansa ya jingina
da kujerar.
Shi kuwa Moddibo Idonu ya tsirawa motar cike da mamaki sai kuma ya motsa laɓɓansa a saman lips
ɗinshi ya furta.

“Wannan wani irin tuƙi ne?.

Tuƙin ganganci ne ko kuwa dai da nufi ne?”.

Dalilin da yasa ya tsaya ma atunanin sa ko ɗaya daga cikin ‘Ya‘yan Malam Arɗo ne sai kuma yaga saɓanin
haka.

Key yayiwa motar tare da kallon M Jameel dake lumshe da ido a hankali yace.

“J nayi zaton ɗaya daga cikin ‘Ya‘yan Malam Arɗo ne ya biyo mu shiyasa na tsaya, amma inaga basu bane
wata ƙil ɗan koyon tuƙi ne”.

Ya ida Maganar batare daya ɗauki abin da muhimmanci ba.

Kai M Jameel ya gyaɗa da faɗin.

“Allah ya kyauta amma na tsorata da ganin yanda sukayo kanmu kamar da gayya suka yi sun tsinka min
zuciya saura kaɗan fa su hau kanmu”.

Girgiza Kai Moddibo yayi kana yace.

“Da alama dai 'yan koyo ne!”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare da gyara zamansa, kana suka cigaba da tafiya.

Kai tsaye masallaci suka nufa kasancewar lokacin sallar Azahar yayi, bayan sunyi parking ne suka fito
suka nufi cikin masallacin, aƙofar masallacin suka tsaya kusan tare sukay addu'ar shiga masallacin.

_“Auzubillahil Azim,Wabiwajhihil Kareem,Wasulɗanihil Ƙadiym,Minal Bismillahi Wassatu Wassalamu Ala


Rasulullah.Allahummaftahliy Abwabal Rahmatik”_.

kana suka shiga.

Bayan sun idar sun fito daga masallacin M Jameel ya juya ya kalli Moddibo yace.

“Muje gida muci abinci”.

Da gefen ido

Moddibo ya kalleshi tare damotsa lips enshi zaiyi magana.


M Jameel yayi saurin ɓata fuska tare da cewa.

“Ba zakaje ba ko?”.

Murmushi Moddibo yayi tare da juyawa akalar motar zuwa gidansu M Jameel.

Yanzu ƙira'ar Sheykh Jabeer suke saurara har suka isa.

Bayan sunyi parking suka shiga Babban falon gida Adining suka zauna sukaci abincin shikam Moddibo
kaɗan yaci ya bari.

Miƙewa sukayi suka fita Fitowarsu daga falon yayi dai-dai da ƙarasowar Hajiya Karima wajen M Jameel
yace.

“Aunty Karima ina yini”.

Ba tare data amsa ba ta watsawa Moddibo kallon tsana tace.

“Maƙale anzo kenan?”.

Cikin ɗan sakin fuska yace.

“Ehh”.

Cike da mamakin halayensa da ƙarfin halinsa tace.

“To wai kai dan Allah ka rabu da bawan Allah nan da dukiyar mahaifinsa mana ko zai samu yayi abin
kansa!”.

Cikin takaici M Jameel yace.

“Dan Allah Aunty ki ƙyale Moddibo da irin wa'annan kalaman mana, na sha faɗa miki shi ba irin mutunen
da kike zato bane, ta ya zan fahimtar da ke?”.

Baki ta taɓe tare da juyawa tabar wajen kamar zata tashi sama.

Shi kuwa Moddibo lumshe idanunsa yayi tare da cije laɓaɓɓansa na ƙasa tare da kiran sunan Allah
aransa.

Araunane M Jameel yace.

“Dan Allah Moddibo kayi haƙuri da abinda Aunty Karima keyi maka”.
Cikin kula Moddibo ya dubesa cikin yanayin nutsuwarsa da kuma ƙasaitarsa yace.

“J.kada ka damu inda sabo ai yaci ace na saba da halin Aunty abinda tun tasowar mu a haka nake da ita
abinda tun bamu wuce shekaru shida-shida a duniya ba take min, har yanzu da muka bawa talatin baya,
ai ya zama man shafawa kawai dai abu biyu ke sawa ban taɓa yi mata wonkin babban borgoba”.

Ya ƙare mgn tare da nufar ɗakin M Jameel.

Cikin jinjina kai M Jameel ya bi bayansa yana mai al'ajabi abinda Modiyke ɓoyewa tsawon shekaru da
yake cewa dalilin dake hanasa taka mata birki, yayi ya gaya masa kuma sam yaƙi.

A ha dai suka isa, suna shiga ɗakin Moddibo ya kwanta bisa kujera tare da lumshe idanunsa alamun
bacci zaiyi.

Acan gidansu Lamiɗo kuwa Mommy ce zaune yayin da Asma'u ke zaune daga ƙasa gefen ƙafafunta ta
ɗago kanta tace.

Mommy asatin nan zamu koma makaranta gashi har yanzu Khausar bata dawo ba”.

“Wallahi kuwa gashi duk kwana biyun nan ba muyi waya ba, dan munfi sati da yin mgn”.

“Ayyah Allah Andi Meyesa”.

Cewar Asma'u

Kai Mommy ta jinjina tare da cewa.

“Kuma Idan ka kiransu ba zai shiga ba sai dai idan su suka kira ka”.

Gyara zama Asma'u tayi tare da cewa.

“Gaskiya Mommy Idan ta kira kice ta dawo tasan ana komawa za'a fara karatu gadan-gadan”.

Mommy tace.

“Inasha Allah zan faɗa mata”.


Daga nan sai suka ɗan ci gaba da hida, daga bisani sukayi

Sallama sannan ta tafi.

Acan Rugar Jauro Yaya kuwa yau sati da rasuwar Baffa Umaru baki ɗaya basu da cikakkiyar walwala duk
da cewa sun dawo da sabgoginsu kamar da sai dai ciwon na nan aransu.

Khausar kuwa sosai tayi sanyi tun da akayi rasuwar bata cikin hayyacinta shiyasa bata samu ta kira
Mommy ta ba.

Kasancewar jiya akayi adduo'ar bakwai Baffanta da yaransa duk sun koma bayan sunyi exchange na
number ita dai ta Mommy ta basu. tare da yiwa Khausar al'ƙawarin kai mata ziyara wataran...

Anutse Khausar ta juya ta kalli Yaya Abba cikin sanyin murya tace.

“Ayyah yaya Abba dan Allah ka bani wayarka zan kira Mommy na”.

Kallonta Yaya Abba yayi cike da tausayi duk tayi wata iri yace.

“Toh shikenan amma ki bari sai gobe ki kirasu dan yau network bashi da kyau koda kin hau kan Bishiyar
ma ba zaki ji magana ba”.

Kai ta gyaɗa masa kana tace.

“Toh Allah ya kaimu”.

“Amin”.

Ya amsa tare da miƙewa ya fita.

*GEMBILA*

Washe gari da safe tunda gari ya waye Malam Arɗo ke ta kiran wayar Moddibo awaya amma ba'a
ɗagawa.

Shi kuwa Moddibo Anutse ya farka daga baccin daya koma tare da furta.

_“Alhamdulillahil Lazi ahyana bada amatana wa'ilaihil nushur”_

Wayarsa dake gefe ya janyo ganin Miss call ɗin malam Arɗo bar katai da yayi ne ya sashi ajiye wayar.
Kana ya miƙe ya shiga toilet.

Tare da addu'a a baki nai

Wanka yayi wanda ya ɗauke sa kimanin minti talatin kana ya fito yana mai faɗin.

_“Gufranaka”_

Suman kansa yake tsanewa da baby pink towel mai taushi.

Yayinda yake sanye da jibgegiyar bathrobe pink color mai masifar taushi wacce ya saƙale igiyoyinta a
ƙugunsa.

A hankali ya zauna agaban dressing mirrow tare da,

Jona handdryer kana ya kunna tare da gyara zamansa da kyau bisa kujerar, dressing mirror ɗin tare da
fara busar da sumar kansa mai ɗan karen sulɓi.

56 seconds yayi zuwa 1 minute yayi yana jujjuya kan handdryer ɗin tare da sa hannunsa ɗaya dake riƙe
da madaidaicin Kum.

A hankali ya ajiye dryer din tare, da buɗe wani gora mai haɗe da man gashi na musamman, wanda Ummi
ce ke haɗa musu, ɗan tsiyaya yayi kana ya murza tafin hannunsa tare da shafa.

Wani irin sheƙi da ƙyalli mai ɗaukan ido suman nasa ya farayi tare da fidda wani ni'imtaccen ƙamshi.

wani ƙum mai laushi wanda yafi na farin ya ɗauka tare da bin gashin nasa ya mishi tafiyar tsutsa,

Wow masha Allah, kamar saƙan taburma haka gashin ya kwanta da salo mai burgewa.

Goge tafin hannunsa yayi da towel ɗin dake bisa ƙafaɗarsa, kanaya

lakato lotion ɗin sa mai daɗin ƙamshi ya shafa jikinsa baki ɗaya.

idonsa ya lumshe tare da kauda kansa lokacin da yake shafawa cinyoyinsa mayin,

fuskarsa ya ɗan shafawa, mai ɗin tare da sa yatsarsa babba ya kwantar da gashin giransa na gefen dama,
kana yasa babbar yatsar na hagu ya kwantar da na gefen hagun. sannan ya ɗan tsiyayi man kanshin ya
shafawa tattausan sajensa dake kwance lip-lip ya shafa, wani irin sheƙi sajen keyi yana fitar da sanyayyan
ƙamshi.

Anutse ya Miƙe ya buɗe durowarsa ya ɗauki jallabiyarsa mai masifar tsada da taushi Kalar Army green,
kana ya zaro tattausan boxer and singlet farare ƙal-ƙal,

ɗan sunkuyawa yayi ya sanya boxer ɗin ba tare da kalli surarsa ba.

Kana ya miƙa tare da dai-dai ta zaman robor a gugunsa,


Bathrobe din ya kwance, kana ya saƙalashi bisa wata yar Kekkyawar masaƙali dake gefen drowersa,
singlet ɗin ya saka, kana ya zira tattausar jallabiyar dake zuba sheƙi da ƙyalli wacce kai da ka gani kasan
taja kuɗi.

baƙin hirami ya jawo, sanya kana ya naɗe kansa da hirami tare da sako jelar ɗaurin ta gefensa na hagu
tsayawa yayi agaban Dressing mirrow tare da ɗaukar kwalbar turaren mai masifar ƙamshi ya feshe
ilahirin jikinsa dashi wayarsa ya ɗauka tare da sanya wa a aljihun gaban rigarsa kana ya fice.

A motarsa ya shiga bayan ya buɗe gate sannan ya fice kana ya sake fitowa ya rufe gate ɗin.

Aƙofar gate ɗin gidan Malam Arɗo yayi Hong mai gadi ya buɗe masa yashiga Babban gida ne sosai sai dai
kallo ɗaya zaka yiwa gidan kasan mamallakin gidan mutum nai mugun maƙo da kirta babu wani fentin
arziƙi ajikin ginin gidan haka zalika ginin ɗakunan single rooms ne cikin haraban gidan kuwa koda flow
babu daga can kusan ƙaramin ƙofar da zai sadaka da cikin gidan rijiya ce babba anyi masa murfin ƙarfe
fitowa Malam Arɗo yayi yana murmushi.

Ɗan guntun Murmushin gefen baki Moddibo ya mayar masa tare da cewa.

“Ina kwana Malam ɗazu ka kira ina bacci”.

Ya ida maganar yana shiga ɗakin ɗaya daga cikin matan Malam Arɗo mai suna Hajiya Zainabu domin
Malam Arɗo ya ɗauki Moddibo tamkar jika.

Wara ido Moddibo yayi yana kallon Hajiya Zainabu yace.

“Hajiya ina kujerun ɗakin?

Indai ba kujera Ni gaskiya bazan zauna ba”.

Sai kuma ya juya tare da kallon Malam Arɗo yace.

“Malam dan Allah asamu kujeru saboda idan sukayi baƙi su samu inda zasu zauna”.

Hararansa Malam Arɗo yayi tare da cewa.

“Ba kai bane kake lissafin duk abinda zai cin yemin aljihu kasan yanda gyaran makarantar nan ya cinye
min kuɗi kuwa?.
Yanzu ma abu biyune yasa na kira ka na farko motata ta ɓaci zaka kaini Rugar Jauro yaya sannan kuma
muyi magana akan ƙara kudin school fees ɗin yara dan gaskiya saina fanshe kuɗin dana kashe a school
fees ɗin forko Aradun Allah.

Kai Moddibo ya jujjuya tare da yar kwaffa hana yace.

“Toh ba matsala ai ka'ida iyayen yara.

Yau kuma mai yasami motar ta lalace ne? Ko kuma sa maine bazaka iya ba”.

Yana mai laluben aljihunsa yace.

“Duka biyu, ta lalacen kuma yau du-du-du da naira ashirin da biyar na tashi”.

Kai Moddibo ya sunkuyar yana mai kallon wayarshi yace.

“Kuma har ina Rugar Jauro Yaya yake da nisa ne!?”.

Da sauri Malam Arɗo Yace.

“Koma da nisa kai zaka kaini dan badan ka matsa min akan gyaran makarantar nan ba da wataƙil in
canza mota kuma da ko ban canza a ai bazan rasa kuɗin da mai ba”.

Murmushi Moddibo yayi kana yace.

“Dama wataƙil ne Malam koba ayi gyaran makaranta ba da wuya ka canza wannan motar.

Dariya Hajiya Zainabu tayi tace.

“Aikam Moddibo ka faɗi gaskiya”.

Anutse Moddibo yace.

“Koma dai menene dan Allah Malam ayi ƙoƙari asa musu kujeru dubi fa ba laida ba Capet ba kujere ba
tiles sai siminti kawai dan Allah ka daure kasamu tiles da kujeru”.

Murmushi Hajiya Zainabu tayi tare da yiwa Moddibo alamar jinjina da hannu kana tace.

“Allah ya maka albarka”.


Tayi maganar yanda Malam Arɗo ba zai jiba.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa da faɗin.

“Naji wuce muje".

Taɓe baki Moddibo yayi kana suka fita.

Ɗakin Uwar gidan Malam Arɗo suka shiga mai suna Hajiya Ramatu,

Kwance suka same ta akan faranda ta shimfiɗa ta burma.

Gefenta Moddibo ya ɗan zauna bisa dakalin dake mazaunin Mlma Arɗo cikin mutuntaka yace.

“Ina kwana Hajiya ya jikin?”.

“Da sauƙi Moddibo ya ƙoƙari?”.

Tace tana mai kallonsa, kauda kansa yayi tare da cewa.

“Alhamdulillah”. yana miƙewa.

Yace.

“Ai dole ma sanyi yata kamaku ba Capet ba kujeru asanyin garin nan kam dan Allah Malam asamu kujeru
inba haka ba zasu ta cutuwa sanyi zaita kamasu sannan ya batun fitar da ita wajen?”.

Tsaresa da Ido Malam Arɗo yayi kafin yace.

“Moddibo! Moddibo!! Moddibo Kafita idona baka iya lissafin komai ba sai lissafin yanda za'a cinye min
kuɗina ko”.

Shi kuwa Moddibo kai ya karya kana cikin sanyi yace.

“Ai gaskiya ne Malam ita lafiyar nan dole aneme ta”.

Harara ya galla masa tare da faɗin.

“Ai mun gama magana da Basiru na basa kuɗin da zai isa".


Shi kuwa Moddibo kai ya jinjina yace.

Malam munyi magana da Basheer kuɗin ba zai isa ba Malam fita waje fa ba abune mai sauƙi ba”.

Saurin Kallonsa Malam Arɗo yayi yace.

“Na fahimta wato har ƙarana suke kaiwa wajenka to kaiɗin Ubana ne da zaka sani inyi!?”.

Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙarawa fuskarsa kyau yace.

“A'a Malam niba Babanka bane ai shawara ce dai”.

Shi kuwa Malam Arɗo kai ya gyaɗa yace.

“Toh shikenan naji zanyi”.

Sallama Moddibo yayi wa Hajiya Ramatu sannan suka wuce ɗakin Malam Arɗo.

Kallon Moddibo Malam Arɗo yayi yace.

“Ya batun ƙara school fees ɗin yaran nan?”.

Shi ma Moddibo Kallonsa yayi kafin yace.

“Malam duk gyaran makarantar nan da akayi a asusun makaranta akayi school fees ɗin yaran yayi dan
angyara makaranta baya nufin sai anƙarawa ɗalibai school fees zaka kashe makarantar ida kuɗin yayi
yawa”.

Baki Malam Arɗo ya cuna har Moddibo ya ida magana sai kuma yace.

“In kashe makaranta fa kace?

Bayan na gyara makaranta sannan kuma ga lafiyayyun malamai masu ilimi yara suna samun wadataccen
ilimi ko za'a samu ilimi abanza ne? zan ƙara school fees Tabbas zan ƙara”.

Murmushi Moddibo yayi yace.

“Toh shikenan kamar nawa za'a ƙara?".

Sai asannan Malam Arɗo yayi Murmushi yace.


“Za'a ƙarawa ko wani ɗalibi dubu Ashirin”.

Wara ido Moddibo yayi yace.

“Innalillahi gaskiya Malam yayi yawa inma za'a ƙara ya kama dole to bazai wuce aƙara dubu biyar biyar
za'a ƙara shima saboda za’a ƙara sabbin malamai ne da kuma sabbin tsare-tsare”.

Kai Malam Arɗo ya jinjina yace.

“Toh shikenan tunda ka matsa zan barshi ahaka”.

Zama Moddibo ya gyara yace.

“Akwai kuma maganar tafiya musabaƙa na gasar hadda da za'ayi za'aje Noka”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa da faɗin.

“Wannan ba matsala ashirya komai”.

Murmushin gefen baki Moddibo ya kumayi idanunsa akan Malam Arɗo yace.

“Eh badamuwa Malam wato tunda kasan wannan iyayen yarane zasu biya kuɗin motar da sungulla da
komai”.

Dariya Malam Arɗo yayi yace.

“Atoh ainima dai ina ƙoƙari tunda motoci makarantar nanne ake tafiya dasu ko”.

Kai Moddibo ya jinjina yace.

“Ai Malam, Ƙarfe nawa zamu tafi can jauro yayan sannan mai zakaje yi?”.

Cikin sanyi yace.

“Wata Rugar Fulani ce amma gaskiya akwai tafiya zamu tafi da yanzu tun da kaga ƙarfe tara zuwa sha
ɗaya zamu isa Insha Allah,Yawanci ina zuwa karatu can wajen wani Malam Aliyu limamin Rugar tasu
sannan kuma anyi masa rasuwa shine nakeso Inje inyi masa ta'aziyya to kaga motata ta samu matsala”.

Jinjina kai Moddibo yayi da faɗin.


“Allah yajiƙan musulmi toh ba matsala muje tunda dama yanzu babu abinda nake yi, amma dai zamu
dawo da wuri ko tunda kasan akwai ‘yan hadda?”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa yace.

Toh ba matsala Allah dai ya kaimu lafiya”.

“Amin”. Yace

Sannan ya miƙe suka shiga mota suka fice kasancewar Ashirye suke.

Moddibo kuwa ƙira'ar Sheykh Jabeer ya kunna suna tafiya yana saurara tare da bin bakinsa tafiya mai
ɗan nisa sukayi a haka.

Malam Arɗo ne ya katse shirun da faɗin.

“Gaskiya wannan tsarin ginin Makarantar yayi kyau Moddibo kayi ƙoƙari”.

Murmushi Moddibo yayi yace.

“Uhum Masha Allah”.

Haka suka cigaba da tafiya suna taɓa hira jefi-jefi wanda mafi yawan hiran Malam Arɗo keyi shi dai
Moddibo daga Uhm sai um-um. Koko yace Masha Allah ko Alhamdulillah.

Suna dosan Rugar Moddibo yaga wajen kamar Rafi hayaƙi na tasowa lokaci ɗaya wani irin sanyi mai
ratsa jiki ya ratsa gaba ɗaya ilahirin jikinsa Atake ya lumshe idanunsa tare da cije laɓɓansa na ƙasa.

Ahankali ya juya ya kalli malam Arɗo yace.

“Kai Malam garin nan akwai sanyi”.

Murmushi malam Arɗo yayi yace.

“Sosai ma kuwa garin akwai sanyi”.

Kai ya jinjina tare da jan numfashi kana ya fesar da huci mai ɗan karen ɗumi.

Dai-dai lokacin yayi parking a ƙofar gidan malam liman kana yana motsa laɓɓansa alamar Tasbihi yake.

“Subahanallahi”. Ya furta a hankali sabida tsarin garin yayi matuƙar ratsa shi.
Yaya Abba da shigowarsa kenan ya isa garesu tare da miƙawa Moddibo hannu sukayi musabaha kana
yace.

“Sannun ku da zuwa fatan kunzo lafiya?”

Kai Moddibo ya gyaɗa da faɗin.

“Alhamdulillah".

Kallon Malam Arɗo Yaya Abba yayi yace.

“Tsoho mai ran ƙarfe”.

Murmushi Malam Arɗo yayi da faɗin.

“Ya akayi ɗan saurayi”.

Cikin alamun sanayya yayi musu jagora, har cikin ɗakin Malam Liman.

Cike da mutuntaka daddataku Malam Liman yake musu marhabin da zuwa.

“A'a Malam Arɗo kaine tafe, sannu da zuwa, on laleko mon njabɓa ma mon laleko bagare”.

Sai kuma ya juyo ya kalli

Yaya Abba kana yace.

“Jeka kawo musu abin taɓa wa”.

Kai yaya Abba ya gyaɗa sannan ya miƙe ya shiga cikin gida.

Ba jimawa ya dawo hannunsa riƙe da Akwashi guda biyu akan faranti sannan ya koma ya sake ɗauko
kofi guda biyu ya buɗe akwashin daya fi girma Gashesh-shen naman ragone da aka masa gashin ruwa
ruwa yayin da ɗaya akwashin ke ɗauke da madaran shanu mai ɗumi Yaya Abba yace.

“Bismilla kuci”.

Bai jira jin mai zasu ceba ya miƙe yabar wajen.

Shi kuwa Moddibo lumshe idanunsa yayi sakamakon ƙamahin naman daya ratsa hancinsa da kuma
yanda gashin yayi kyau a ido da farko baiyi niyyan ciba amma ganin yanda gidan yake atsaftace da kuma
masu gidan ga wani irin ƙamshi dake tashi yasa ya fara cin naman cikin nutsuwa tare da zuba madaran
sosai yaci dan baƙaramin daɗi naman yayi ba, gashi dama baiyi breakfast ba.
Malam Arɗo ma sosai yaci sannan yasha madaran wanda shi kuwa kirtansa ke hamada ci sai yazo nan
yake kashe tsatsan haƙoransa shiyasa ba cika fashin zuwa duk wata yana zuwa sai biyu.

Bayan sun kammala ne Malam Liman yashigo ya zauna daga gefen Malam Arɗo ya bashi hannu sukayi
musabaha.

Malam Arɗo yace.

“Fatan mun same ku lafiya ya kuma muka ji da ƙarin haƙuri?”.

Kai Malam Liman gyaɗa tare da faɗin.

“Hakuri mungode Allah”.

Malam Arɗo yace.

“Allah ya jiƙansa da rahma da kuma dukkan musulman da suka rigamu gidan gaskiya”.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.

ya amsa.

Shima Moddibo cike da girmamawa yace.

“Malam ya mukaji da haƙuri Ubangiji Allah ya jikansa da Rahman Allah ya haskaka makwancinsa”.

Malam Liman ya amsa da.

“Ameen”.

Baffa Liman ya kalli Malam Arɗo yace.

“Muje ka gaida Babbar Addarmu wacce take madadin mahaifiyarmu”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace.

“Toh ba matsala muje”.

Ya ida Maganar suna miƙewa.

Baffa Liman da malam Arɗo na gaba yayin da Moddibo da yaya Abba ke bayansu Moddibo na ƙarewa
yanayin garin kallon sosai garin ya burgesa ko ina ka duba tsaf-tsaf babu alamar ƙazanta ko datti.
Bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga gidan Hajja Nana lokacin tana zaune atsakar gidan kan ta burma.

Baffa Liman ya kalli Hajja Nana yace.

“Ga Yayana kuma ɗalibina yazo zai gaisheki”.

Tace.

“Ayyah sannunku da zuwa”.

Sannan ta miƙe ta shimfiɗa musu darduma dake tsaf dashi babu alamar datti ajiki komai na gidanta tsaf
babu datti duk da stufanta amma komai nata tsaf yake.

Sosai garin da mutanen garin suka burge Moddibo komai na garin akimtse.

Gaisawa sukayi da Hajja Nana sannan suka yi mata ta'aziyya madara mai ɗumi tasa aka kawo musu. Koda
sukace Alhamdulillah fir tace dolefa susha ita baƙo baya zuwa wurinta ya fita baici komaiba.

Madarar kawai Moddibo yasha kasancewar ya ƙoshi agidan malam Liman Aransa kuwa sai yaba karamci
da dattakon mutanen yake.

Aɓangaren Khausar kuwa tana can rafi tare da Dije da Sadik sunje ɗiban ƙwan Zabbi da kuma kayan
lambu dake hannun Khausar bayan sun gama suka fito kallon Sadik da Dije Khausar tayi tace.

“Tunda wayar yaya Abba na hannu na zanje Bishiyar ƙare zancenka in Kira Mommy na”.

Kai suka gyaɗa mata da faɗin.

“Muje toh”.

Bayan fitowarsu daga gidan Hajja Nana Moddibo ya ciro wayarsa da niyyar kira sai yaga ba network
kallon Yaya Abba yayi yace.

“Baku da network ne?”.

Kai Yaya Abba ya gyaɗa yace.

“Eh bamu dashi amma akwai inda zaka samu idan kana da buƙata sai muje in kaika wajen akwai service
ta nan nede babu”.
Kai Moddibo ya gyaɗa yace.

“Eh inada buƙata gaskiya muje”.

Sai kuma ya juya ya kalli Malam Arɗo da Baffa Liman yace.

“Bari zamuje ya rakani in sami network ina so zanyi kira”.

Baffa Liman yayi Murmushi yace.

“Yau ka shigo Rugar Fulanin da basu da network sai anje annema ko?”.

Dan murmushin Moddibo yayi tare da shafa sajensa zuwa gyamunsa daya ƙawata kyawun fuskarsa.

Malam Liman ne yace.

“Abba in kunje ku karasa cikin Rafi Modibbo yayiwa Jauron garin nan ta'aziyya sannan kuce yazo
munada boƙo ne”.

Jinjina kai Abba yayi sannan suka fita shi kuma Malam Arɗo da Baffa Liman suka wuce can gida domin
ƙara karatu.

Suna fita Moddibo ya kalli Yaya Abba yace.

“Kai sanyin garin kun nan yayi yawa bari na ɗauki Jacket nasa”.

Ya faɗa tare da nufar motar ya buɗe ya ɗauki farin Jacket ya ɗaura akan Army green ɗin jallabiyarsa da
yayi masifar yi masa kyau.

Murmushi Yaya Abba yayi Aransa yana yaba baiwar kyawunsa da kuma iya Dressing ɗin sa.

Ta cikin wata siririyar hanya dake ɗauke da korayen ciyayi masu kyau da ƙamshi suka ratsa.

Sai wani lumshe ido Moddibo keyi yana jin kamar ya tabbata awajen saboda yanda garin ya tsaru komai
nasu mai kyaune.

Ta Cikin wannan Hanyar suka ɓulla har Rafi Yaya Abba nata yi masa hira shi dai daga Uhm sai Um-um
saiko Masha Allah.

kasancewar sa ba mutum nai me surutu ba.


Suna shiga cikin Rafin Moddibo ya dunƙule hannunsa waje ɗaya jin sanyin wajen yafi na cikin garin
juyawa yayi ya kalli Yaya Abba kana yace.

“Muma muna da sanyi amma sanyin ku yafi namu sosai”.

Kai Yaya Abba ya gyaɗa yace.

“Sosai ma ai tanan kam munfi sanyi”.

Jinjina kai Moddibo yayi yace.

“To ku riƙa rage Bishiyoyi mana sanyin be damun ku?”.

Yaya Abba yace.

“Aikuwa mu munajin daɗin sanyin”.

Moddibo yace.

“Masha Allah”.

Acan cikin rafi kuwa Sadik riƙe yake da ƙwan Zabbi mai yawa yayin da Khausar ke riƙe da ma daidaicin
kwando ahannunta wanda ke ɗauke da,Inabi,Tuffa, Mangoro,Abarba,Kwakwa, Lemo,da sauran kayan
itatuwa yayin da ɗaya hannunta ke riƙe da wayar Yaya Abba tana dannawa Sadik ya juya ya kalleta yace.

“Khausar da kin haƙura da danna wayar nan sai mun tsallake wannan ruwan dake gudu kinga akwai
duwatsu aciki”.

Still hankalinta na kan wayar tace.

“Kada ka damu ai ina kallo”.

Kai ya gyaɗa mata sannan suka cigaba da tafiya.

Yaya Abba kuwa yana ƙoƙarin karya kwanar da zai sadasu da Bishiyar ƙare zancenka ya hango Baffa
Jauro acikin Rafi juyawa yayi ya kalli Moddibo yace.

Gacan Baffa na Jauron garin nan da Malam yace mubiya kamasa ta'aziyya”.
Kai Moddibo ya gyaɗa yace.

“Toh mu ƙara sa".

Kai Yaya Abba ya gyaɗa sannan suka nufi wajen Moddibo kuwa wayarsa ya ciro a aljihu yana duba ko
akwai network ata wajen Dai-dai lokacin da Khausar ta iso wajen baki ɗaya hankalinta da nutsuwar ta
nakan wayar tana saka number Mommy.

Kallon Dije Yaya Abba yayi wacce tuni ta tsallake ƙoramar ruwan yace.

“Dije har kun ɗebo ƙwoyin?”.

Kai Dije ta gyaɗa masa kana tace.

“Eh Ya Abba".

Moddibo kuwa sam bai lura da mutum agabansa ba, ya ɗago ƙafarsa na dama zai tsallaka yashiga rafin
kenan, ita kuma Khausar ta ɗago ƙafarta na hagu zata tsallaka tafita a rafin ji kake gub suka bugi juna da
ƙafafunsu.

Tagal-tagal Khausar tayi baya zata fadi yayin da shikuma Moddibo da ƙyar ya tsaida kansa daga faduwar
da zai yi.

Ita kuwa khausar Atsorace ta saki kwandon kayan Marmarin dake hannunta tare da kai hannu ta riƙe
rigarsa da hannu ɗaya yayin da ɗaya hannun ke riƙe gam da wayar Yaya Abba.

A kuma lokaci guda ta rumtse idanunta tare da sakin kara.

Shi kuwa Moddibo cikin hanzari yakai hannu ya riƙota sai alokacin idanunsa suka sauƙa akan fuskarta ita.

Ita kuwa Khausar sassayan numfashi ta fesar jin an riƙeta bata faɗiba yasa ta ɗago kan Idanunta ne suka
sauƙa akan fuskar Moddibo.

Lokaci ɗaya jikinta ya ɗauki rawa na tsananin tsoro da firgicin ganinsa kawai sai ta sake hannunsa tare da
rintse Idanunta tayi baya zata faɗa cikin ruwan,Cikin zafin nama yasanya Lallausan tafin hannunsa ya riƙo
hannunta tare da fisgota ta tsallaka sai yayi wucewarsa batare daya juya ya kalleta ba.

Ita kuwa khausar banda rawa babu abinda jikinta keyi cikin rawan murya tace.

Ka-ka-kayi ha-ƙuri ban gankaba shiyasa, shi kuwa Moddibo ko juyawa baiyi ba bare yaji abinda take faɗa
yabar wajen.

Sai alokacin Yaya Abba ya lura da yayan itatuwan ta data zubar yace.
“Ya haka Khausar mai yasa bakya kallon gabanki in kina tafiya?”.

Cikin rawan murya tace.

“Tsautsayine”.

Tafaɗa tare da barin wajen aranta kuwa tunani take yau kuna Moddibo Arugar mu me ya kawo sa? kuma
mai ya haɗa sa da yaya Abba? to me ya zoyi? da wannan tunanin ta isa Bishiyar ƙare zancenka tana isa ta
hau kan dutse. dake farko ta zauna tare da sa hannunta ta riƙe reshen, kana ta kiran number Mommy.

Shi kuwa Moddibo bayan sun karasa wajen Baffa Jauro.

yace.

“Ina yini Baffa fatan mun same ku lafiya ya kuma ƙarin haƙuri?”.

Baffa Jauro kuwa cikin yanayin sauƙin kansa da kuma dattako ya amsa da.

“Haƙuri Alhamdulillah fatan kunzo lafiya?”.

Moddibo ya amsa da. “Lafiya Ubangij Allah yajiƙan sa da rahma idan kuma tamu tazo Allah yasa mu cika
da Imani”.

Baffa Jauro ya amsa da.

“Ameen”.

Yaya Abba ya kalli Baffa Jauro da faɗin.

“Bari muje na rakasa Bishiyar ƙare zencen ka kuma Baba Yace kaje tare suke da Malam Arɗo".

Kai Baffa Jauro ya gyaɗa kana yace.

“Adawo lafiya”.

Miƙewa sukayi suka nufi Bishiyar ƙare zancenka tun kafin su isa Moddibo ke jiyo suturatai da dariyar
mutane Aransa yace to lafiya dai.

Suna ƙarasawa yaga tsoffi,Matasa,maza,da mata kowa maƙale da waya akunnensa ahankali
kunnuwansu ke jiyo masa kamar sautin Muryan Khausar da mamaki ya ɗaga kansa gefen yamma
idanunsa suka sauƙa akanta saman dutse kana kanta na bisa reshen Bishiyar.
Aransa yace to ashe ga inda ta samo ɗabi'ar hawa bishiya wato garin ne dole sai akan bishiya ake waya
wannan shine gado.

Ya juya tare da kallon yaya Abba yace.

“Dole sai na hau kan Bishiya zanyi wayar?”.

Girgiza kai Yaya Abba yayi yace.

“A'a ko akan dutsen ma zaka samu network”.

Jinjina kai Moddibo yayi yace.

“To ku maida ƙa'ida mana mata su hau kan duwatsu maza su hau kan Bishiya idan ya kama dole ne sai an
hau kan Bishiya ko kuma ku maida lokacin yin wayar mata daban lokacin yi. Wayar maza da ban kusa
tsari da ƙa'idar musulunci ku dena gwamutsuwa haka”.

Jinjina kai Yaya Abba yayi yace.

“Gaskiya ne kabamu shawarar data dace Insha Allah za'ayi haka zan faɗawa Baffa Jauro ayi haka”.

Moddibo kuwa cewa yayi.

“Ai ya kamata ayi haka yanzu Meye amfanin ga mata asama sannan ga maza aƙasa ko kuma duk suna
gwamutse maza da mata ko da duk kan ku 'yan uwane ai yakamata ayi abu duka bisa tsarin Addini ko ba
haka ba bai dace ba duk da cewa yawancin ku ’yan uwane amma akwai auratayya atsakanin wasu”.

Cikin jin daɗin Nasiyyar da ya masa da gamsuwa Yaya Abba yace.

“Hakane Insha Allah za'a gyara malam”.

Ita kuwa khausar sam batasan Moddibo sun zo wajen ba.

Bayan sun gama gaisawa da Mommy.

Mommy tace.

“Khausar kwana biyu baki kira ba kuma kinsan ba zai yiwu na kira kiba”.

Araunane Khausar da mutuwar Baffa Umaru ya dawo mata sabo tace.


“Mommy ankashe Baffa Umaru har gida aka kashesa Mommy agaban idanuna aka kashesa!”.

Shi kuwa Moddibo hankalinsa na kan yiwa Yaya Abba magana bai san mai take faɗa ba juyawar da zai yi
yaji tana cewa.

“Mommy har anyi sadakan bakwai hankalina ne bai kwanta ba”.

ta faɗa hawaye na zuba daga idanunta.

Shi kuwa Moddibo ido ya zuba mata ganin yanda hawaye ke kwaranya daga idanunta.

Khausar tace.

“Mommy ai zakizo kiyi mana ta'aziyya ko?”.

Mommy da mutuwar ya kashe mata jiki tace.

“Insha Allahu zamu zo, nasan idan na faɗawa Abbanki ba zai hana ba, ki shirya idan nazo zamu taho tare,
dan Asma'u tazo tayi min magana batun zaku koma makaranta, kishirya kayanki idan muka zo zamu tafi
tare idan Hajja Nana ta yarda”.

lumshe Idanunta tayi tace.

“Baza ma ta hana ba Insha Allah idan kunzo zamu tafi tare dan dama tace zanje Ɓadamaye wajen Baffa
na nacan kuma sunzo ta'aziyya mun haɗu dasu, sannan ma Addata Ikki tazo mun haɗu da ita sai wani
lokaci zanje Ɓadamaye nama karɓi number su, suma sunce dan suna sauri ne kuma mun haɗu amma da
zasu je su duba ni anma munyi canjin number”.

Cikin sanyi Mommy tace.

“Toh shikenan babu damuwa ki shirya idan nazo zamu taho Insha Allah gobe zamu zo ta'aziyya”.

Sallama Mommy ta mata.

Juyawar da zatayi Idanunta suka sauƙa akan Moddibo daya tsareta da ido saida ta kusa faɗuwa saboda
tsoron ganinsa.

Da ido ya mata alamar ta saƙƙo kafin ƙiftawa da Bismillah kuwa ta diro ƙasa.

Kallon Dije dake jiranta tayi tace.

“Mu tafi”
Yaya Abba ya miƙa mata kwandon kayan Marmarin ta data zubar yace.

“Gashi kin zubar dasu na ɗebo miki”.

Kamar wacce aka fisgo maganar daga bakinta tace.

“Banaso ka bashi na bashi”.

Sai da ta rufe bakinta asannan ta tuna mai ta faɗa hannu Dije ta fusga tace.

“Mutafi".

Shi kuwa Yaya Abba gyara riƙon kondon yayi.

Shi kuwa Moddibo ɗaya daga cikin duwatsun wajen ya samu ya zauna tare da kiran wayar M Jameel.

M Jameel na ɗagawa Yayi Sallama.

Amsawa Moddibo yayi tare da faɗin.

“Kada kaje kata nemana nasan zaka ne meni bana nan sannan ka kira wayata kaji akashe ina wani ƙauye
ne da mukaje da Malam Arɗo amma Insha Allah zamu dawo kafin Azahar".

M Jameel yace.

“Toh meyasa baka gaya min ba tun ɗazu”.

Cikin yanayin shaƙuwa yace.

“Nima zuwan ba zata ne, kuma lokacin nasan kana bacci”.

Cikin sauƙe numfashi M Jameel yace.

“Toh badamuwa Allah ya dawo daku lafiya”.

“Ameen”. Yace tare da katse kiran.

Bayan ankira sallan Azahar sun idar kai tsaye wajen motarsu suka nufa Yaya Abba ne ya zo ya miƙa masa
kwandon kayan Marmarin da Khausar tace abashi.
Cikin yanayin nutsuwarsa da kuma sanyin murya sa yace.

“A'a Nagode amma ka ajiye awajenka”

Murmushi yaya Abba yayi yace.

“To ai bani ce na baka ba Khausar ce tace abaka”.

Yana gama faɗa ya buɗe bayan motar ya saka masa.

Malam Liman ma ya basu Zabbi Baffa Jauro kuma ya aiko musu da ƙwan Zabbi Hajja Nana kuma ta aiko
musu da zuma sannan suka yi musu sallama suka tafi Moddibo kuwa yaba karamci ci halaccin mutanen
sukayi.

Suna shiga cikin gari ya wuce da Malam Arɗo gidansa ya ajiye sa sannan ya sauke masa ƙwan Zabbin da
kuma Zabbin da goran zuma.

Malam Arɗo yace.

“Ka ɗauki Zabbin da kuma ƙwoyin mana”.

Kai Moddibo ya girgiza yace.

“A'a wannan zumar ma ya isheni”.

Ya ida maganar tare da jan motar ya fice zuwa gidansa.

Acan ɓangaren Mommy kuwa da daren ta samu Lamiɗo ta faɗa masa maganar rasuwar da kuma son
zuwanta suyi ta'aziyya, Cikin jimami yace toh Allah ya kaimu gobe zasu zo.

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

Washe gari Da safe suka ɗauki hanya zuwa Rugar Jauro Yaya sukayi ta'aziyya.

Bayan sun gama gaisawa ne Mommy tace.

“Hajja Nana zamu koma da Khausar dan gobe Insha Allah zasu koma makaranta”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa dan mutuwar ƙaninnata yasa tayi sanyi baki ɗaya.

Tace.

“Badamuwa ku koma da ita amma idan an kwana biyu ta riƙa zuwa saboda su saba da ‘Yan uwanta”.
Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.

“Badamuwa Insha Allah zata zo”.

Kasancewar dama Khausar ta haɗa kayanta tun daren jiya yasa ta dauko jakarta sai kuma ta Rungume
Hajja Nana tace.

“Hajja Nana zanyi kewarki ki riƙa zuwa bishiyar ƙare zancenka kina kirana dan Allah”.

Murmushi Hajja Nana tayi kana tace.

“Sai kace kin damu dani bayan rashin kunya kike min".

ƙaramin bakinta ta tura tare da ficewa tana cewa nidai zanyi kewarki.

Baki ɗaya Kakannints suka rakata jikin mota bayan sun haɗa mata tsaraba iri-iri Kama daga, Zabbi, Kaji,
Ƙwan Zabbi, Nono jarka-jarka da kuma zuma man shanu.

Kawai sai Khausar ta fashe da kuka cikin raunin murya.

Tace.

“Aranan da nazo kamar haka da Baffa Umaru aka tareni yau kuma gashi babu shi!".

Hannunta Baffa Garga ya riƙe cikin rauni da zuba hawaye yace.

“Kiyi haƙuri Khausar haka rayuwar take idan kaini yau gobe ba kai bane, kuma in sha Allah zasuga
SAKAYYAH”.

Hawayenta ta share tare da shiga mota tana ɗaga musu hannu Dije ma kan sosai tasha kukan rabuwa da
Khausar.

Fatan sauƙa lafiya suka musu sannan suka ja motar suka tafi.

Khausar kuwa motarsu na isa harabar gidan Haiydar, Raudat da Ramadan suka taho da gudu suka
rungumeta Ramadan ne yace.

“Addah Khausi nayi missing ɗinki”.

Kansa ta shafa tare da cewa.


“Nima nayi missing naku”.

“Addah Khausar Barka da dawowa daga zuwanki har gidan yayi haske, amma da bakinan duk saiyayi
duhu”.

Cewar Haiydar

Ta wani wara manyan Idanunta tace.

“Kada kayi masu gidan suji”

ta faɗa tare da ɗaukar Ramadan suka shiga ciki afalon suka zube suna ta hiran bayan rabuwa.

Cikin sakin fuska Khausar ta kalli Raudat dake zuzzuɓura baki tace.

“A'a My happiness sis ya akayi ne?”.

Baki Raudat ta kuma turawa tare da cewa.

“Ba wani ai naga kinfi son Ramadan”.

Dariya mai sauti tayi tare da jawota ta ruggumeta.

Kana suka ci gaba da hirar yaushe gama. sallah kaɗai ke ɗagasu.

Bayan kwana biyu ya kama yau Asabar zasu koma makaranta kasancewar Asabar ne farkon satinsu
Alhamis da juma'a kuma Weekend.

Tun wuri Khausar ta tashi bayan ta idar da sallar asbah tayi Azkharul sabah toilet ta shiga tayi wanka
kana ta fito ta zauna gaban dressing mirrow ta shafe jikinta da lotion ɗinta kana ta shafa kajol a manyan
Idanunta masu haske sai kuma ta shafa lips dinta Kaɗan tulin sumar kanta dake tsefe ta sanya farin
Ribont ta kama ahankali ta buɗe duro ta ɗauki uniform ɗin ta dake goge maroon din wandon ta fara
sanya wa sannan tasa ka farin riga sai kuma ta ɗauki farin ɗankwali ta ɗaura kana ta ɗauki maroon din
hijab ta Sanya Wanda ya tsaya gwiwarta wani irin kyau tayi na ban mamaki sosai Uniform din ya amshets
tamkar dan ita akayi.

A gaban Dressing mirrow ta tsaya ta ɗauki kwalban turare sun kai kala biyar ta feshe ilahirin jikinta dashi
sannan ta ɗauki combos Fari ta Sanya tare da ɗaukar school bag ɗinta ta rataya kana ta fito falo.

Murmushi Mommy tayi tace.


“Manana kinyi kyau”.

Ta juya manyan Idanunta tace.

“Nogode Mommy na”.

Haiydar kam murmushi yayi yace.

“Yau za'ayi ruwa da ƙanƙara shugaban ’yan letti ta riga kowa shiryawa”.

Harara ta maka masa batare da tace komai ba ta shirya Raudat sannan sukayi Breakfast suka shiga mota
Amina sai Harara take watsa mata ita kuwa khausar bata ma san tana yiba domin aƙasan ranta tunanin
haɗuwarta da Moddibo take da kuma irin hukuncin da zai yanke mata.

Suna isa Makarantar lokacin har anfara shiga class cikin sauri sauri Khausar ta riƙe hannun Raudat suka
nufi side dinsu Raudat ta ajiyeta a class kana da sauri ta juya, zata fita class ɗin kenan.

Taji Raudat ta saki ƙara tare da kiranta.

Da sauri ta juya tare da kamo Raudat ɗin da taga tana jujjuyawa, tsugunawa tayi tare da cewa.

“Raudat menene ya faru”.

Cikin kuka da yarfa hannu Raudat tace.

“Wayyo idona Adda Khausy ido, borkono".

Da sauri ta jawota tare da fara hura mata idon.

Sai kuma ta amshi goron ruwar da Antin su ke miƙa mata.

Wonke mata fuskar ta ta farayi tare da murza mata idon.

Cikin Sa'a kuwa ɗan abin da ta shiga idon ya fita.

A hankali ta buɗe idann nata, da tuni yayi jazir.

Cikin sanyi tace.

“Ayyah Raudy na sannu ko, yanzu dai ya fita ko?”.

Kai ta gyaɗa mata tare da kama hannun Antin nasu.

Ganin hakane yasa Khausar juyawa da sauri ta fito ta nufi harabar makarantar.
Shiru ba kowa a tsakiyar harabar alamun an gama shiga class kenan.

Cikin sassarfa ta fito daga side din ’yan nursery.

Kana ta nufi sude ɗinsu.

Da sassarfa ta nufi kan step ɗin.

Dai-dai lokacin kuma Moddibo ya fito daga class dinsu ya nufi ƙasa, a hankali yake take steps din
yayinda hankalinsa baki ɗaya yana kan....!

Ki biya ki karanta, kiji ainin manufar labarin kiyi dariya kiyi shauƙi kibi haushi kiki tausayi kiyi kuka. Kiyi
murmushi

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_Page 9_

NA

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*FREE PAGE NE ƴar uwa ki biya ki karanta abinki cikin Salamah, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal
0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP
09097853276. Kana in saki a Groups da na buɗe ba SAKAYYAH in da zaki karanta abinki salamun ƙaulum
min rabbil rahim. Nama lfy fata lfy. Ba ruwan ki da jiran na sata na Allah ya isa*

Cikin nitsuwa yake tafiya, tare da taka steps ɗin a hankali, yana sauƙa ƙasa, yayinda hankalishi baki ɗaya
ke bisa system nashi dayake kan hannunsa na dama yana daddanashi da hannun hagunsa, bisa dukkan
alamu.

Abu mai mahimmanci ne yakeyi.

A dai-dai lokacin kuma Khausar ta iso bakin steps ɗin, cikin sauri take tafiya, da alamun tsoron kada
malami ya rigata shiga aji ne.

Da sauri take tattaka steps ɗin tanayi sama.

Steps biyu ta taka ana uku, taji juyo da kanta da sauri dan jiyo muryar M Jameel na ce mata.

“Khausar sai yanzu?”.

Ba tare da ta tsaya ba, kana bata kuma juyo kanta ba taci gaba da tafiya a haka, hannunta na kan da
ƙarfe dake gefen steps ɗin cikin yanayin sakewarta da M Jameel ɗin tace.

“Wallahi tun ɗazu muka iso fa Malam”.

Yana mai binta da ido yace.

“To kuma meya hanaki shiga class?”.

Still bata janye kanta daga kallonsa ba, kana bata tsaya daga haurawa saman da takeyi ba tace.

“Raudat ce ta tsaidani a side ɗin su”.

Da sauri yace.

“Da me ta tsaida ki?”.

Ɗan guntun murmushi tayi tare da cewa.

“Wai ƙwarone ya shiga idonta, shinefa tai ta ihu taƙi sakina dole saida aka cire matashi Allah sai kaga
yadda idonta yayi jazir”.

Kanshi ya sunkuyar yana ɗan murza zaɓen azurfan dake yatsar yace.

“Ayya kwaro bai kyauta ba ya shiga idon Gimbiya Raudat”.


“Ai dai kam fa”.

Ta faɗina tana mai ƙoƙarin juyo kanta.

Cikin tsokana yace.

“Gashi kuwa har Malam Moddibo ya shiga ajinku”.

Cikin sauri ta kuma juyo kanta da dama bata gama juyashi ba cike da kaɗuwa tace.

“Da gaske?”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.

“Tun ɗazuma kuwa”

Cikin yanayin tsoro ta ɗan zaro manyan udanunta tare da cewa.

“Na shiga ukuna”.

Murmushi M Jameel yayi tare da cewa.

“Ato kiyi sauri ki hau, in kinyi sa'a ya barki ki shiga”.

Jin haka yasa ta juyo da sauri tare da taka step ɗin gaba kana tayi kwanan haurawa kam steps ɗin da zai
sadata da sama.

Wanda kuma dai-dai lokacin Moddibo ma ya taka step na ƙarshen kwanan.

Unexpected taji tayi karo da mutu.

Shi ma Moddibo ba zato ba tsammani yaji kanta ya bugi ƙirjinsa yayinda hannunta ya bugi System ɗin
dake hannunsa ya subce ya tafi ƙasa da sauri ya sunkuyo ya cafe system ɗin da kana ya miƙe tsaye,

Ita kuwa Khausar cikin sauri ta ɗago kanta dai dai lokacin kuwa ya ɗago kansa shima ido cikon ido suka
kalli juna kamar a fuzge ya furta.

“Again?”. a lokacin guda kuma, cikin tsananin takaici da zafin rai ya ɗaga tafin hannunsa na hagu ya yarfa
mata wani irin gigitaccen mari mai masifar zafi gami da raɗaɗi.

M Jameel kuwa jin sautin sauƙan marin ne yashi ɗago kansa da sauri.
Ita kuwa Khausar wani irin gigitaccen ihu mai cike da rauni tare raɗaɗi ta saki, tare da dafe kuncinta kana
ta rumtse idonta wanda duhu mai tarin yawa ya mamaye mata gani, kana tayi taga-taga ta koma baya
zata faɗi, jin ta tafi suuuuu ƙafarta ta sule yasa takuma sakin wani ƙaran tare da buɗe idanunta, sai kuma
tayi sauri ta medasu ta rufe sabida ganin wasu irin taurarin masu wutsiya da tartsatsi suna gilmawa
ganinta sabida zafin marin da yasa suka mamayewa ganinta.

Gaba ɗaya ta sadakar domin tasan muddin ta faɗo nan to ita da karaya sun zama aminan juna.

M Jameel kuwa kanshi ya riƙe da hannu bibbiyu tare da faɗin.

“Innalillahi!!”.

Wanda faɗin hakane ya jawo hankalin Malam isa da yazo wucewa ta gefensa.

Shima ma Malam isa idonsa ya rumtse da ƙarfi tare da cewa.

“Yah Salam”.

Shi kuwa Moddibo cikin takaici yayi sauri miƙa hannunsa da nufin kamo hannunta amman ina tuni tayi
nisa.

Sai yatsunta biyu ya samu ya riƙe da masifan ƙarfi.

Wanda saida suka bada sautin ƙas-ƙas.

Cikin zafin nama ya fincikota da ƙarfi wanda hakan yasa ta afka jikinsa.

Ita kuwa Khausar jinta a jikin mutum ne yasa tayi masa wani irin sahihin rugguma mai cike da razani dan
gani take kamar dai har yanzu bata tsira ba.

Kanta ta cusa cikin ƙirjinsa tana mai shaƙan turarensa mai masifar ƙamshi.

Wanda a take nitsuwarta ta fara dawowa.

Shi kuwa Moddibo cikin tsoro da wani irin masifeffen abu da yaji ya soƙi tsakiyar kansa har zuwa cikin
ƙahon zuciyarsa kana ya harba masa wasu irin masifaffun baƙin al'amuran a cikin jijiyoyin jikinsa da suka
sa jikinsa sakin wani irin masifeffen karkarwa da sabauta aniyarsa, ya ware hannunsa tare da rumtse
idanunsa da masifan ƙarfi.
M Jameel kuwa ajiyan zuciya mai ƙarfi ya sake tare da jingina bayansa da jikin ƙarfen.

a hankali ya kuma sakin numfashi tare da kallon yadda Moddibo ya buɗa hannayensa duka biyu kana ita
kuma Khausar tana kwance bisa ƙirjinsa tayi lip tana ruggume dashi da masifan ƙarfi.

Wani irin shu'umin dariya mai sauti M Jameel ya sake.

Wanda hakan yasa Moddibo buɗe idanunsa kana dai-dai lokacin yaji gaba ɗaya tsikar jikinsa na tashi.

Malam isa kuwa sunkuyar da kansa yayi yana murmushi.

M Jameel kuwa dariya yake tare da nuna Modibbo da Khausar ɗin wacce tuni fuskarta tayi jazir shatin
yatsun hannunsa sunyi ruɗu-ruɗu a farar fatarta.

Cikin sauri Moddibo ya ɓalle hannunta daga jikinsa tare da matsawa gefe da sauri.

Wani irin tsuke fuskarsa yayi tare da watsa mata kallon da yasa hantar cikinta kaɗawa.

Wanda cikin rawan jiki da rawan murya cike da rauni tace.

“Ana Aspet ya Mu'allim Allah mi larai ma on! Please! Kayi haƙuri”.

Ta ƙare mgnar cikin tsoro tare da gwamusa yaruka hudu duk a wuri ɗaya dan neman afuwa.

Shi kuwa Moddibo juyawa yayi tare da ratsa gefenta ya wuce kana cikin wata fusatacciyar murya mai
matuƙar firgitarwa yace.

“Biyoni!”.

Cikin ɓarin jiki tace.

“Toh”.

Sannan ta miƙe tabi bayansa.

M Jameel dake riƙe da System ɗin yana juyawa yayi saurin bin bayansa da faɗin.

“Alhamdulillah kamar babu abinda ya samu System ɗin”.

Shi dai Moddibo ko juyawa baiyi ba bare kuma ya tankawa M Jameel.


Malam Isa kuwa dake ƙasa ido ya zirawa Khausar dake sauƙwa dafe kuncinta da kunne ya da tun da
tasha marin ya bada sautin kauwww har yanzu ƙaran takeji, kana ga idanunta da suka kaɗa sukayi jawur
asanda ta saƙƙo yace.

Fattanah sam bakya yin abinda ya dace a rayuwarki”.

Cikin zafin raɗaɗin marin da fuskarta keyi ta ɗago Idanunta da suke sake girma da ja ta kalli Malam Isa
sai kuma tace.

“Wallahi bansa niba ne na juya ina kallon Malam Jameel ne dake yimin magana ne mukayi karo”.

Bata jira jin abinda zai ce ba tabi bayan M Jameel dake biye da Moddibo.

Cak Khausar ta tsaya daga bakin Office ɗin, karo na farko kenan arayuwarta da zata fara shiga Office
ɗinsa, duk da cewa da basu da office da yawa, amma yanzu gyaran da akayi an haɗa Malamai biyu akan
Office ɗaya Office din ba wasu masu girma bane, haka zalika ba ƙanana bane, sannan duk kusan ajere
suke.

Ahankali Khausar ta maida Idanunta bakin office ɗin da akasa wasu irin flowes masu launi mai kyau da
ɗaukar hankali aka jera suna fitar da wani irin sanyayyan ƙamshi.

Cikin Office ɗin kuwa Madaidaitan deks ne da kujeru ɗaya na fuskantar gabar ɗaya na fuskantar yamma
daga gaban ko wanne kuma akwai kujeru guda biyu daga kan deks ɗin daga gefen damar sa akwai wani
Cubet kamar kanta dake ɗauke da tarin littattafai na addini da kuma na boko cikin wajen kamar dai
Library haka wurin yake.

Daga gefen hagunsa kuma flowes ne masu kyau da tsari daga jikin bangon kuma Room hitane ne maƙale
abango yana fitar da ɗumi mai daɗi a jiki,

Sai kuma labulayen window da suka kasance farare sol Sanyayyan iska na kaɗawa daga bangon kudu
dake kallon yamma TV ne maƙale abango daga tsakiya kuwa wani irin dakekken turkey carpet mai yawan
gashi fari sai ratsin maroon kaɗan. sosai Office ɗin yayi kyau.

Shi kuwa Moddibo cikin nutsuwa da kuma zafin da zuciyarsa keyi masa ya zauna akan kujeran dake
gabar yana fuskantar yamma yayin da M Jameel ya zauna akan kujeran dake yamma yana fuskantar
gabar kana da sunan ko wannensu ajiki kujerarsa.
Ita kuwa khausar cikin tsananin tsoro ta ƙarasa shiga office ɗin tare da tsugunnawa agaban table ɗin da
Moddibo ke zaune.

Ta riƙe kunnenta Muryanta Araunane wanda ke nuni da tsantsar tsoro da tashin hankali tace.

“Malam kayi haƙuri bansan kana tahowa ba”.

Shi kuwa Moddibo ko kallonta baiyi ba saboda yanda zuciyarsa ke tsananin ta farfasa ya tabbata idan
yace zai daketa to zai iya karyata ko kuma ya sumar da ita hakan yasa ya janyo kujeran dake kusa dashi
ya ɗaura ƙafafunsa akai kana ya lumshe idanunsa tare dasa hannu ya janyo Hiramin dake kansa ya rufe
saman Idanunsa.

Cikin tsantsar nutsuwa da kuma sanyayyan sautin muryarsa mai zaƙi ya fara rara Ƙira'a acikin suratul
Rahman yasan hakan shine kaɗai zai sanyaya masa ransa da zuciyarsa yasan muddin yace zai daketa
ayanzu zai iya sumar da ita ko kuma karyata.

Saboda abubuwan da yarinyar ke masa yayi yawa.

Sabida tsabar raini da rashin kunya fa har gidansu ta bisa tayi masa rashin kunya sannan ta jima sa ciwo
ayatsun ƙafansa wanda ya ɗauki tsawon kwanaki yana fama da ciwo.

Kana yaje ƙauyen su nan ma bata barshi ba saida ta bisa tayi masa rashin kunya ta nemi jefa shi acikin
ruwa da wannan masifeffen sanyin garin nasu,

kana amakaranta ma bata barsa ba shin tsaranta ta mayar dashi kome?.

Ita kuwa khausar cikin Sanyayyar Muryanta me cike da tsoro tace.

“Ayyah malam na tuba kayi haƙuri wallahi bansani bane”.

Ƙin tanka mata Moddibo yayi ya cigaba da rera karatunsa cikin zazzaƙan muryansa.

Shi kuwa M Jameel Gyaran murya yayi hakan yasa Khausar tayi saurin Kallonsa da manyan Idanunta da
suka kaɗa sukayi jawur.

Da ido yanuna mata Moddibo alamar ta cigaba da basa haƙuri.

Kai ta gyaɗa sannan ta cigaba da cewa.

“Ayyah Malam na roƙeka kayi haƙuri bazan sake ba”.


Acan sama ajinsu Khausar kuwa wani irin tsarin gini ne mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali wasu irin
windon Glass ne tsala-tsala masu tsayi da kyan tsari sannan ga flowes masu fitar da sanyayyan ƙamshi
kana ga Room hita guda biyu gaba da baya daga farkon shiga class ɗin kuwa wani irin Black Board ne
mai tsari irin wanda ake amfani dasu a manyan makarantu, kana ga wasu irin kujeru na zaman ɗalibai
masu taushi da kyau, agaban ko wani kujeran ɗalibi akwai sunan sa ajiki, hakan yasa duk ɗalibar data
shiga baza tasha wahala neman wajen zamanta ba wanda kuma manna sunan ake bisa alamu in an tashi
kawai ɓarewa za'ayi a saka sunayen sabbin waɗanda zasu shigo ajin, kujeran Khausar shine na farko
acikin jerin kujerun dake gaba da sunanta manne kamar haka _Khausar Usman Abubukar Lelewal._

Samira Sani ce ta ɗan juya Idanunta kan kujerar dake gefenta.

Wanda sunan Khausar dake manne kujerar afarkon.

Wani irin ya mutsa fuska tayi tamkar wacce taga wani abin ƙi cikin taɓe baki da tsanar mamallakiyar
sunan tace.

“Ikon Allah wannan shine suna mai buƙatar hadda sunaye huɗu duk masu tsawo!”.

Ta Ida maganar tare da bankawa kujeran harara tamkar Khausar ɗin na kai, kana ta zauna daga baya
inda sunan ta ke kai.

Asma'u dake gefe azaune tace.

“Ha'a sunane de ai ba wani abu ba kuma duk sunayene masu inganci da Kekkyawar nasaba naga dai
sunanta sunane na ɗiya ga Annabi Muhammad (S.A.W) sannan sunan mahaifinta sune na sahabin
Manzon Allah (S.A.W) haka zalika sunan kakanta sune na sahabin Manzon Allah (S.A.W).

Lelewal kuwa naga suna ne da kowa ke fatansa”.

Abeeda Sule ne ta watsa wa Asma'u harara tare da faɗin.

“Ke kuma wayasa bakin ki?”.

Taɓe baki Asma'u tayi kana tace.

“Ai gaskiyane daga kallon sunan baiwar Allah zata fara ƙanan magana”.

Ɗaya daga cikinsu manyan matan ajin nasu ne wacce bata fiye magana Hajia Khadija tace.

“Da wannan hatsaniyar da kukeyi tunda Moddibo ya fita tun ɗazu akan zaije ya dawo bai dawo ba
aigwara kuje ku duba ko lafiya mai ya tsaida shi aji ba kowa kuma shine muke da First period?”.
Cikin zumuɗi Samira Sani tace.

“Gaskiya ne kam bari naje na kirasa”.

ta ida maganar tare da ficewa ta sauƙa ƙasa.

Cikin yauƙi ta nufi Office

Tana isa idanunta suka sauƙa akan Khausar dake riƙe da kunnenta, ga kuma Idanunta da suka sauya,

yayin da shi kuwa Moddibo idanunsa ke lumshe yana rera karatun Alkur'ani cikin Sanyayyar sautin
muryansa daya haɗu da ɗumin room hita ga ƙamshin daddaɗan tularensa.

Numfashi mai nauyi ta fesar tare da tsirawa yalwataccen sajensa daya ƙawata kyawun fuskarsa idanu sai
kuma ta maida kallonta kan zara-zaran yatsun hannunsa dake kan table yana ɗan bubbugasu ahankali
cike da shauƙi tace.

“Wowww”.Faɗar hakan da tayi shi ya janyo hankalin M Jameel yayi saurin juyawa ganinta tsaye acikin
Office din yasa shi faɗin.

“Lafiya?”.

Sai asannan ta dawo cikin nutsuwarta still Idanunta na kan Moddibo tace.

“Malam Barka da safiya”.

“Barka dai”.

Still idanunta na akan Moddibo tace.

“Malam dama munzo kiran Malam Moddibo ne, shine muke dashi tun ɗazu ya sauƙa, akan cewa zai zo
ya ɗauki wani abu sannan kuma bai koma ba”.

Da ido M Jameel ya nuna mata Moddibo da har zuwa lokacin idanunsa ke lumshe yana karatu sai dai ya
rage sautin muryansa ya koma fita asaman laɓɓansa.
Shi kuwa Moddibo jin Muryanta yasa ya janye Hiramin dake fuskarsa kana ya buɗe idanunsa da har zuwa
yanzu akwai alamun ɓacin rai acikinsu, kallo ɗaya ya mata ya kawar da kansa gefe.

Ita kuwa Samira gefe ta koma ta tsaya.

Khausar kuwa lumshe Idanunta da suka kaɗa sukayi jawur tayi sai kuma ta buɗe su still Hannunta nakan
kunnenta tace.

“Ayyah Malam kayi haƙuri”.

Shi kuwa Moddibo juyawa yayi tare da kallon M Jameel yace.

“J ka da keta”.

Da sauri M Jameel ya juya tare da nuna kansa da babban yatsa kana yace.

“Ni!?”.

Cike da tsuke fuska Moddibo ya gyaɗa masa kai kana yace.

“Eh ka daketa!”.

Zare Ido M Jameel yayi tare da cewa

“Meyesa?”.

A kufule Moddibo yace.

“J kadaketa nace!”.

Kallon mamaki M Jameel yake masa tare da cewa.

“Akan me zan daketa?”.

Cike da ɓacin rai Moddibo yace.

“Idan fa ka bari nace ni zan daketa zan sumar da ita fa!, zan karyata fa!!”.

Cikin tsananin fusata ya ida maganar.

Ita kuwa Khausar tuni jikinta ya hau rawa Allah ya sani bata son duka, sannan mari ɗaya daya mata ya
mugun gigita mata ƙwaƙwalwa wanda har zuwa yanzu take jin raɗaɗin sa asaman fuskarta.

Fuskarsa babu walwala yace.


“Idan har nace zan daketa zan sumar da ita”.

Ita kuwa Khausar jin azaban mari ɗaya daya mata, aranta tace Ashe Allah ya rufa min asiri da yasa duk
lokacin da nayiwa Moddibo laifi baya duka na yake sa Malam Adam display master ke dukana na tabbata
dashi yake dukana kullum da tuni ya kasheni!.

Cikin hanzari ta juya tare da kallon M Jameel ta miƙa masa hannu Muryanta na rawa tace.

“Malam ka dakeni!”.

Girgiza kai M Jameel yayi cikin sanyin murya yace.

“Ni dai kam bazan iya ba bazan iya dukanta ba Moddibo, ka dubi fuskarta fa mari ɗaya da ka mata kalli
fuskarta fa ai ya wadatar wani hukunci ya rage bayan wannan?”.

Ya kare mgnar a hankali

Moddibo kuwa cikin fushi yace.

“Kada keta in kuma baza ka daketa ba zan daketa da kaina fa”.

Cikin sauri M Jameel ya fara girgiza kai yayi cikin wata Sanyayyar murya me cike da zallar jin ƙai tare da
tarin tausayi gami da rauni yace.

“La! La!! La!!! A.J bazan iya ba! Wlh Bazan iyaba ba wannan ba hurumina bane hurumin taɓa ta
awajenka yake bani da karsashi ko ƙwarin gwiwar da zan iya taɓa ta!”.

Ya ida maganar cikin wani irin salo na daban, kana dai-dai lokacin Amina tazo Office ɗin domin kiran M
Jameel ya shiga ajinsu wani irin sarawa kanta yayi jin yanda yake cewa bazai iya ba.

Da sauri ta dafe ƙofar office ɗin jin jiri na ɗibarta kadde ace dokon soyayyarsa za tayi abanza, kadde
Khausar yake so yanda ya ƙarashe maganar na nuni tamkar itace rayuwar sa.

Da sauri Moddibo ya juya ya kalli M Jameel jin yanda yayi magana da kuma yanda ya lanƙwasa
harshensa abun ya bashi mamaki.

Azuciye Moddibo yace.

“In daketa kenan?”.

Langwaɓar da kai M Jameel yayi cikin sanyin murya yace.


“Kayi haƙuri ina mai bada haƙuri amada dinta ka nemi wani punishment ɗin ka bata amadadin wannan,
amma nikam bazan iya dukan taba sannan kaima banaso ka daketa!”.

Baki ɗayan su kallon Mamaki suka bi M Jameel dashi ganin yanda yake lanƙwasar da murya tare da
nemawa Khausar ya fiya, ita kuwa Amina wasu hawaye ne masu zafin gaske ne na tsananin kishi da
baƙin ciki, suka zubo mata saurin ta sanya hannu ta share.

Kwantar da Murya M Jameel ya kuma sakeyi ya cigaba da cewa.

“Kallifa A.J mari ɗayan nan da kamata kalli fuskarta fa ka daketa awaje mafi daraja”.

Moddibo kuwa lumshe idanunsa yayi kana ya buɗesu akan M Jameel tare da cewa.

“J kadaketa ni idan nace zan daketa bazai mata daɗi bafa”.

Sake Langwaɓar da kai M Jameel yayi kana yace.

“Kayi haƙuri Moddibo ni bazan iya dukanta ba!”.

Ita kuwa Samari Sani na tsaye agefe ta harɗe hannayenta aƙirji yayin da ta zubawa Moddibo ƙananun
Idanunta ko ƙyaftawa ba tayi.

Ita kuwa Amina Idanun ta nakan M Jameel da idanunsa ke kan Khausar zuciyarta nayi mata zafi.

Khausar kuwa kallon M Jameel ta sakeyi akaro na barkatai tace.

“Malam Jameel ni dai ka dakeni”.

Kai ya girgiza mata tare da faɗin.

“Bazan iya dukan ki ba Khausar!”.

Shi kuwa Moddibo cikin tsananin ɓacin rai ya juya ya kalleta a kufule yace.

“Toh inda keta da kaina!?”.

Girgiza kai M Jameel yayi sai kuma yace.

“A'a asassauta mana dan Allah”.

Ƙwafa Moddibo yayi da faɗin.


“Shikenan kije ki kaɗe ɗan kwali sau ashirin”.

Cike da tsoro ta zaro ido domin kaɗe ɗan kwallon da yace yana nufin ta cire ɗan kwalinta tasa abokitin
ruwa ta matse kana ta kaɗe har sai ya bushe,

sannan ta sake sakawa cikin ruwa ta matse kana tayi ta kadewa har sai ya bushe.

Tofa jin haka ne yasa a tsorace ta zare Ido Jin hukuncin daya yanke mata ba zata manta lokacin daya sata
kaɗewa sau goma ba awannan lokacin ma saida tayi sati biyu gaɓɓanta na ciwo ko abu zata ɗauka da
ƙyar take iyawa.

Cikin yanayin neman alfarma M Jameel ya sake langwaɓar da kai kana yace.

“Dan Allah ka sassauta mata karage mata”.

Jin Muryan M Jameel yasa ita ma ta kalli Moddibo cikin wata raunatacciyar murya tace.

“Dan girman Allah Malam kayi haƙuri karage min”.

Shi kuwa Moddibo wani kallo ya watsa mata cikin haɗe girar sama dana ƙasa yace.

“Kada ki sake haɗa ni da girman Allah da kinsan darajar girman Allah da zaki mutunta Malama ki,

kije kiyi shabiyar kinci darajar girman Allah.

idan kika sake cemin dan Allah in rage miki kuwa nida ke bibbiyu!”.

Gyaɗa kai tayi kana tace.

“Toh shikenan”.

Shi kuwa M Jameel kallon Moddibo yayi cikin jujjuya ido yace.

“Ina neman alfarma abarta tashiga aji tayi karatu idan antashi Break sai tayi”.

Shi kuwa Moddibo Ɓata fuska yayi yace.

“Bana son ganinta a aji Idan naganta a aji zan kakkaryata in wurgar ta window”.

Ita kuwa Samira Sani cikin lanƙawasa harshe tace.

“Malam Moddibo mu tafi”.


Sake tamke fuska yayi tare da juyawa ya watsa mata wani bayyane harara sai kuma ya nuna mata ƙofa
alamar ta ɓace masa da gani.

Sum sum ta juya da sauri ta fice.

Da harara yabi bayanta Aransa yace.

Shegiyar yarinya mai kama da Mayya,

sai shegen kallon jaraba tasani gaba zakiyi dan rashin kunya.

Samira Sani kuwa tana shiga ajinsu ta lumshe Idanunta tare da kallon gefen ko wannen kujera dake
ɗauke da flowes ta saki murmushi mai cike da jin daɗi,

tasan wannan aikin Moddibo ne domin kaf cikin Malaman shike son flowers.

Hajia Ruƙayya ce ta dubi Samira data shigo kana tace.

“Ni kam ya banga Khausar ta shigo ba har yanzu kuma ɗazu na hangota kafin na haura”.

Juye Ido Samira tayi tare da faɗin.

“Tana can tayiwa Moddibo rashin kunya yana cin Ubanta, shegiyar yarinya fitsararriya ‘yar marasa
tarbiyya!".

Asma'u ce ta juya ta kalleta rai a haɗe tace.

“Haba Samira meyesa zaki zagi iyayenta ai bai kamata ki zagi iyayenta komai yaya iyaye nada daraja”.

Harara Samira ta wurga was Asma'u kana ta buɗe baki da niyyar magana ta fasa sakamakon shigowar
Moddibo.

Ganin shigowar Moddibo yasa ta tsuke bakinta tare da neman waje ta zauna cike.

Cike da ladabi suka gaishesa cikin harshen larabci tare da faɗin.

”‫“صبحل خير ىاعثتذ‬

Ya Amsa da.

“‫“صبحل نور كىفل قراء‬.


Suka amsa da.

”‫“الحمد الله‬

Kasancewar Tafseer zasuyi dake yanzu lokacin Islamiyya ne yasa yace.

“Kuyi muraja”.

Cikin bawa ko wanne harafi hukuncinsa suka shiga karanta suratul Muhammad har zuwa karshe.

Bayan sun gama kawo haddan ya jinjina kai tare da faɗin.

“Sai gobe Insha Allah zamu fara tafsirin sa”.

Aɓangaren M Jameel kuwa tare suka jera da Amina suka nufi ajinsu yayin da azuciyar Amina yayi
baƙiƙƙirin data tuna yanda M Jameel ke karyar da murya akan Khausar har suka isa ajin tunanin da take
aranta kenan yanayin yanda tsarin ajinsu Khausar yake haka ko wanne aji yake cike da ƙwarewa M
Jameel ya shiga yi musu ƙarin Mi'atu Hadith daga na Arba'in bayan sun karanta masa.

Ko wanne aji da Malami aciki suna darasi.

Ita kuwa Khausar ita kaɗai ce tsaye aharabar Makarantar cikin gajiyawa ta ɗaga boket ɗin ruwan ta koma
rana wai ko zata samu yafi bushewa da wuri, tsoma ɗan kwalin tayi aciki kana ta matse sannan ta fara
kaɗewa.

Nannauyan ajiyar zuciya ta saki tun akaɗewa na uku taji hannunta ya sage aranta tace.

“Insha Allah Ina komawa gida zan nemi ɗankwali mai shara-shara mara nauyi wanda kodan irin rana ta
yau ta faru zaimin sauƙi.

Cike da gajiya ta miƙe ta riƙe ƙugunta da hannu ɗaya ta lumshe idanunta sosai ta gaji.

Shi kuwa Moddibo daga can sama acikin ajinsu Khausar yake kallonta tana kaɗe-kaɗen ganin ta tsaye ta
riƙe ƙugu gaban ƙirjinta duk ya jiƙe da fuskanta, ganin ta tsayanne yasa ya buɗe glass ɗin window dake
saitin ta tare da ziro hannunsa ya ƙyasta yatsunsa da ƙarfi wanda hakab yaja hankalin Khausar da saurin
ta ɗaga kanta.

Ganin abinda yayi yasa da sauri ta cigaba da kaɗewa tana mai rintse Idanunta.
Har Moddibo ya gama teaching ɗinsa ya fita Khausar nakan punishment Koda ya saƙƙo ya ganta Harara
ya watsa mata kana a kufule yace.

“Ba zaki shiga ajiba yau har sai kin gama abinda nasaki”.

Fuska ta Shagwaɓe tare da langwaɓar da kai tace.

“Ayyah Malam dan Allah kayafemin duk ɗan Adam ajizine!”.

Harara ya watsa mata ya wuce batare daya bata amsa ba,

bayansa tabi da kallo tana tura ƙaramin bakinta, to har wani malami ya sake shiga yayi darasi Khausar
bata gama ba sai sha biyu dai-dai lokacin tashin matan Aure sannan Yara da ‘Yan mata suyi suci abinci su
koma ajin boko.

Hajiya Ruƙayya ce da Aunty Khadija ne suka fito tare da ƙarasawa kusa da Khausar dai-dai lokacin da
Khausar ke faɗin.

“Wayyo hannuna”.

Ta faɗa tana matsa yatsunta dake raɗaɗi.

Dafata Hajiya Ruƙayya tayi kana tace.

“Ayyah sannu Khausar kece bakyaji me kika yiwa Moddibo!?”.

Langwaɓar da kai Khausar tayi tare da marairaice murya tace.

“Allah babu abinda na masa kawai ina tahowa ne mukayi karo dashi har System ɗinsa ya faɗi kuma ma
naji malam Jameel yace System ɗin beyi komai ba amma sai da ya sani wannan kaɗe-kaɗen sabida in
baici zalina ba baya jin daɗi rayuwarsa ta duniya”.

Ta ida maganar da faɗin.

“Affan zo”,tare da miƙa masa hannu.

Murmushi Aunty Khadija tana mai jujjuya kai.

Ita kuwa Hajia Rukayya

Miƙa mata yaron dake ta faman ƙyalƙyala mata Dariya Aunty Ruƙayya tayi Sai kuma tayi saurin janye
hannunta tana cewa.

“Wayyo Aunty Ruƙayya hannu na ya gaji yaukam bazan iya riƙe sa ba”.
Ta ƙare mgnar tana ƙara matsowa kusa da Aunty Ruƙayya kan kumatunsa ta sumbata tana faɗin.

“Affan gaye".

Shi kuwa yaron sai dariya yake ƙyalƙyala mata tare da miƙa mata hannu alamar yana so ta ɗauke sa dan
sosai yaron ya saba da ita saboda Aunty Ruƙayya na zumunci da Mommy Khausar sannan Khausar na
shiga lokaci zuwa lokaci.

Samira Sani da Abeeda Sule ne suka ƙaraso wajen Kallon Abeeda Sule Samira tayi da faɗin.

“Ai Moddibo shike maganin tantirai marasa mutunci ’ya'yan Fitsararru awannan makarantar yana min
dai-dai!”.

Sake hannun Affan Khausar tayi ta juya ta kalli Samira da kyau tace.

“Waye ‘Yar marasa mutuncin?

Akwai ‘Yar marasa mutunci daya wucike ne ‘Yar magulmata Munafuka kawai! Inbanda munafurci da
gulma da biye-biyen bokaye Me kuka iya!?”.

Afusace tace.

“Ke Khausar zanci Ubanki fa!".

Wara ido Khausar tayi kana tace.

“Ubana kuma, uhmm saide Kici naki uban domin ni kam nawa Ubana tuni Ubangiji ya daɗe da yimasa
sutura sai dai kije kici naki ‘Yar matsiyata?”.

Ta ida mgnar cikin tsiwa,.

Abeeda Sule ne tace.

“Ke akwai ma ƴar matsiyata irinki, kina tsammanin bamu san cewa munsan ke Agwola bace acikin gidan
sarki da kike nunawa kamar gidan ku ne?”.

Dariya Khausar tayi kana tace.

“Dan Allah rufe mana baki ‘Yar Alhaji sule baka layya kibari tukunna in Babanki ya fara layya saiki faɗa
wa mutane Magana?”.
Zare ido Abeeda tayi tare da hayayya ƙowa tace.

“ ‘Yar iska ni zaki cewa Ubana baya layya”.

Taɓe baki Khausar tayi tare da faɗin.

“Ke rufe min baki ai bani na faɗa ba Inkiyarsa ce hakan, ko ba sunan sa bane? Alhaji Sule baka layya!! ko
kuma ni nasa masa ko kuma dan tsoronki sai inki kiransa da sunan da aka sa mishi”.

Hajiya Ruƙayya ce tace.

“Khausar rabu dasu”.

Gyaɗa kai tayi.

Ita kuwa Samira cikin takaici tace.

“ ‘Yar banza kawai agola”.

Dariyar rainin hankalin Khausar tayi sannan tace.

“Eh koma menene inma ni Agolace inada daraja sannan ina da tushe dama ni ban ɓoyewa cewa Agola
bace Ni saboda idan kinga sunan su Amina da sunana kin san ba yar gidan bane,

Ni sunana Khausar Usman Abubukar Lelewal sukuwa kinga ba haka sunan su yake ba daga nan ma
mutum yasan Ni Agola ce ko dama anɓoye miki ne?”.

Hannunta Hajiya Ruƙayya taja suka bar wajen zuwa gefe tace.

“Khausar kifita har ƙansu kiyi abinda ke gabanki kinga duk yau baki samu karatu ba”.

Kai Khausar ta gyaɗa mata sannan tayi mata Sallama ta tafi.

Asma'u ce ta ƙaraso wajen Idanunta akan Samira da Abeeda dake zagin Khausar cikin yanayin sanyin
muryanta tace.

“Khausar kifita sabgar wa'annan yaran dan Allah keda su ba ɗaya bane kada ki ringa biye musu muta nen
da ƙwaƙwalensu basa ja, kinga fa yanzu da ya kamata suna SS 3 nefa daƙiƙancinsa kesa kullum basa gaba
sunan a jaɓe har muka isosu”.

Yamutse fuska Khausar tayi kana tana matsa yatsun hannunta tace.
“Kinsan Allah Asma'u Indai basu fita sabgata ba zan basu mamaki zan nuna musu Khausar Usman
Abubakar Lelewal ba kanwar lasa bace”.

Hannunta Asma'u ta riƙe tace.

“Ni dai dan Allah ki fita sangarsu ai ko kare bai haushi shi kaɗai tukunna wai me kika yiwa Moddibo ya
saki Punishment?”.

Rau-rau da ido Khausar tayi sai kuma ta ya mutse fuska tare da jan tsaki kana tace.

“Mutum yana nan kamar wani sabon boss sam fuskarsa babu fara'a yana nan sai baƙin mugunta.

Kuma wallahi Wuta bal-bal ban yafe masa ba, ai bani kaɗai nayi kuskuren ba shima yayi yana tafiya
kamar makaho, kuma yaseen saƙo na baki ki faɗa masa ehe”.

Ta ida mgnar cike da tsiwa da murguɗa baki

Asma'u kuwa dariyar dake cinta ta danne kana tace.

“Aikuwa gashi nan abayanki yana ma jinki ba sai na faɗa masa ba”.

Arazane Khausar ta saki ihu tare da rintse Idanunta cikin tsananin tsoro da rawan jiki ta juya tana mai
faɗin.

“Dan Allah! Dan Allah!! Dan Allah!!! kayi haƙuri Allah bada kai nake ba kuskuren harshene ni da kainama
nakeyi”,

Ta ida maganar tana buɗe Idanunta jin be tanka taba ga mamakinta bata gansa ba.

Kallon Asma'u tayi wacce zuwa lokacin ta saki dariyar ta tace.

“Fattanah sarkin tsiwa dama gwada ki nayi inga da gaske saƙon kika bani”.

Harara Khausar ta zabga wa Asma'u amma batace Komai ba.

Murmushi Asma'u tayi tare da jan hannunta zuwa resting chair dake cikin harabar makarantar suka
zauna Asma'u ta fito da kula da ɗauke da pride rice da yaji kayan hadi da namar kaza suka ci.

Bayan sun gama cin wannan Khausar ta buɗe bata kukan.

Peper checking ne guzurin zabbin data dawo dasu.


Sunaci suna ɗan hirarsu dai har suka gama, suka mike tare da zagaya classes din makarantar suna kallon
yanda aka tsara makarantar kamar ba shiba.

12:10 suka koma aji.

Bayan komawar su Malam Isa dake ɗaukar su Economist ya shiga ya koyar musu sosai Khausar da
Asma'u ke fahimtar karatun 1:15 dai-dai suka fita sallah.

Bayan sun fita Al'wala sukaje wajen da aka tanada dan alwala sukayi gefen maza da ban na mata da ban
Amma masallacin guda daya ne saidai anraba daga tsakiya anyi katanga mata zasu shiga ta gefen dama
maza tagefen hagu.

Bayan sun idar da Sallah ƙarfe 1:30 suka koma aji wasu Malaman suka sake shiga.

Sosai Malaman suka dage wajen koyar dasu domin anƙara musu Salarie sannan ankawo sabbin Malamai
hakan yasa babu period din dake wucewa ba tare da anshiga ba 5:00 dai-dai suka tashi motar su
Khausar tazo ta ɗauke su.

Washe gari.

Ma haka suka gudanar da karatunsu kamar na jiya.

Acikin satin karatu suke gadan gadan babu kama ƙafar yaro saboda suna son dai-dai-ta komai na lokacin
daya wuce ahutu koda wasa Khausar bata sake yin ganganci wani abu ya haɗa ta da Moddibo ba bare
tayi masa laifi da zaran ya shiga ajinsu zata tattara duk kan nutsuwarta akansa tana sauraron abinda
yake koyar musu kuma sosai take fahimta yayin da ita kuma Samira Sani zata tsaya aikin Kallonsa aduk
sanda ya shiga musu shikuwa Moddibo duk yana lura da yanayin ko wannensu.

Yau Alhamis ya kasance babu makaranta suna hutu.

Khausar ce zaune a falon Mommy ta tana duba Mi'atu Hadith,Mommy dake Bedroom ta ƙwala mata kira
Amsawa tayi tare da ajiye Hadith ta fita.

Bakinta ɗauke da Sallama tashiga Bedroom din Kallonta Mommy tayi tace.

“Khausar ɗibi wannan kayan ki kaiwa Hajiya Bunayya kala ɗaya nasiya mana”.

Kallon mamaki Khausar ta yiwa Mommy anma wannan basabon abu bane ko yaushe Mommy na zaune
zuciya ɗaya da ita tana kyautata mata, amma ita Hajiya Bunayya ba da zuciya ɗaya take zaune dasu ba.

Gyaran Murya Mommy tayi tace.


“Khausar tunanin me kike?”

Murmushi Khausar tayi tare da ɗiban kayan tace.

“Toh”,Mommy sannan ta fice.

Bakinta ɗauke da Sallama ta shiga falon Hajiya Bunayya kana ta nemi waje ta zauna aɗaya daga cikin
kujerun dake falon tace.

“Ummah gashi Mommy na ta siya musu iri daya”.

Washe baki Hajiya Bunayya tayi tare da kallon turamen Zannuwa da tsadaddun less ɗin tace.

“Aaaa lalle kam Khausar Nagode Allah yayiwa ƙanwata al'barka muje inyi mata godiya”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da miƙewa dai-dai lokacin Hajiya Lami mahaifiyar Samira Sani tayi sallama suka
shigo atare.

Kallon Khausar Hajiya tayi tace.

“Khausar jeki nayi baƙi kice mata Nagode zan shigo anjima”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da ficewa yayin da Samira ta bita da mugun kallo.

Kallon Hajiya Lami Hajiya Bunayya tayi kana ta mika mata hannu suka tafa Dariyar ƙeta Hajiya Bunayya
tayi tace.

“Kalli Sokuwarki wai kaya ta saya mana iri ɗaya”.

Dariya Hajiya Lami ta fashe dashi tare da cewa

“Aaaa Ikon Allah sokuwa ta ƙarshen zamani kuwa wato hadda siya muku anko”.

Tsaki Hajiya Bunayya tayi tace.

“Bar ‘yar banza mai kama da ‘ya‘yan mayu tazo ta liƙewa mijina”.

Hajiya Lami tace.

“Aikam wa'annan mutanen sai Allah aike kika sake kika basu dama, kika bar mijinki ya ƙara aure ni yanzu
Baban Samira ya isa yace zai ƙara aure ne, sannan bayan kin bari yayi auren ma kika barta tahaifi
santalelen yaro me jikin girma bayan shi hadda ‘yan biyu da kawunansu kamar ‘Ya‘yan ruwa ga shegen
gashi kamar ‘ya‘yan Aljanu”.

Ƙwafa Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Ai wallahi nayi sake amma daga ‘yan tagwayen babu ita ba sake haihuwa ina lura da ita kwannan kamar
cikine da ita to bazan bari ta haife sa ba zanje wajen boka Kar'uzu azubar dama duk cikin ta uku kafin
’yan biyu ni nake sawa azubar shegiya ai bazan barta ba kenan yanzu ma inada niyya zanje wajenki jibi
muje wajen Malami”.

Gyara zama Hajiya Lami tayi tare da faɗin.

“Aini ma abinda ya kawoni kenan Hajiya Bunayya in sanar miki”.

Kallonta Hajiya Bunayya tayi tace.

“Toh Meye faru?”.

Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauƙe tace.

“Akwai wani Malami ne amakarantar su Samira take sonshi”.

Cikin don jin ƙarshen zancen Hajiya Bunayya tace.

“Toh wani Malami?”.

“Wai shi malam Moddibo tana masifar sonshi shi kuma yana nan kamar Waliyi ko ta kanta bayayi”.

“Ikon Allah”.

Cewar Hajia Bunayya

“Toh fa shine nake son zamu kai sunansa wajen Malami ya jawo mana hankalinsa da tunaninsa”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Eh hakan ma yayi shine dai-dai, gwara ajashi ya dawo yana binta, nima dama abinda zai kaini kenan
harda batun Amina itama wani Malamin su take so”.
Cikin mamaki Hajia Kamu tace.

“Ita kuma wani Malamin take so?”.

Da sauri Hajiya Bunayya tace.

“Eh wani Malami take so wai shi M Jameel shi kuma baki ɗaya hankalinsa nakan wannan ‘yar
matsiyatan!”.

Cikin zato ido Hajiya Lami tace.

“Wa kenan?".

“Khausar mana”.

Hajiya Lami kam baki ta saki tare da riƙe haɓa kana ta saki salati tace.

“Ikon Allah Uwarta ta hanaki rawan gaban hantsi, sannan itama Khausar tun yanzu zata hana ‘yarki
rawan gaban hantsi, ta hana ta samun abinda take so, to ko lallai kinada aiki ja a gabanki

Yakamata muyi aggawan zuwa mu ɗauki mataki dan bata isa ba amma shi Jameel din ɗan gidan
waye!?”.

Murmushi Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Ɗan gidan Alh Bashir Mafindi.

Ko da yake yanzu anfi saninshi da Maidala ne”.

Kai Hajiya Lami ta jinjina tace.

“Kai-kai lallai kice babban kamu ne ina zamu yarda muyi wasa dashi waye bai san Alhaji Bashir Maidala
ba”

“Ai dai kam ɗan masu kuɗi ina zamu bari muyi wasa da wannan damar tamu.
Ai wlh koda zan tafi tsirara bazan taɓa bari ya auri Khausar ba, sannan Insha Allah zanyi kokarin ganin
anja mana hankalinsa yaji ya tsaneta ya riƙa cin Ubanta kamar yanda Moddibo keyi mata amakaranta
shine abinda yafi mana a'ala da kwanciyar hankali”.

Acan waje kuwa Khausar ce tsaye aƙarshen Barandar Hajiya Bunayya cikin tarin al'ajabi da mamaki ta
jinjina kanta bayan ta gama sauraron abinda suka faɗa.....!

*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son
k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman
lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun
matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa
ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki
tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones
dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da
tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da
ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda
ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya
wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka
kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki
da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp
in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta,
muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina
nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a
ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta
wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki Ka mota, duk ƙasar da kike kayana zaije
gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nane🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.

GARKUWAR MA'AURATA

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_Page10_

_NA_

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NA DAI FA KUSA GAMA FREE PAGE, SAURA KAƊAN. Yar uwa baki makara ba ki biya ki karanta cikin
Aminci, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min
shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Kana in saki a Groups ɗin dana buɗe na littafin SAKAYYAH
wanda in dai ba a cikinsa kikeba toh yar uwa na sata kike gani. Amman na yanzu dai Free page ne*

Ita kuwa Khausar Jinjina kanta tayi, yayin da idanunta ya cika da ruwan hawaye aranta tace.

“Ta Allah bata ku ba amma kam yardan da Mommy na tayi miki ya ƙazanta ta gaza gane cewa ke ɗin
kara da kiyashi ne ɗaukar rashin sani.

Sai kuma ta juya cikin mutuwar jiki ta juya ta koma falon nasu bakinta ɗauke da Sallama.
Zaune ta samu Mommy afalo Idanunta alumshe yayin da ta jingina bayanta da jikin kujeran.

Ƙara sawa kusa da ita Khausar tayi tare da zama tace.

“Mommy yadai baki shiga kichen ɗin ba?”.

Ahankali Mommy ta ɓude Idanunta dake lumshe kana tace.

“Wallahi Khausar bacci nake ji duk jikina babu ƙarfi!”.

Jinjina Kai Khausar tayi cikin sanyu tace.

“To kiyi baccin Mommy bari nashiga kichen nayi girkin”.

Kai Mommy ta gyaɗa still Idanunta alumshe tace.

“Toh”.

Juyawa Khausar tayi ta shiga kichen ajikin sink din ta jingina asaman laɓɓanta tace.

“Kenan yawan baccin da Mommy na keyi kwanan nan, ciki ne da ita wanda Hajiya Bunayya ke ƙoƙarin
zubarwa”.

A hankali ta saki Ajiyar zuciya da faɗin.

“Allah mai iko”.

Sai kuma ta juya ta ɗauki tukunya tasa ruwa ta ɗauraye cikin sannan ta tari ruwa da yawa aciki tarufe
Sannan ta juya ta kunna Gas ta ɗaura ruwa,

Jiki a mace ta buɗe drower Na'a na'a ta ɗiba tare da citta, kanamfari, da masoro kaɗan, gyara su tayi
kana ta ɗaureyesu sannan ta saka cikin tukunyar.

Doya ta ɗauko manya guda huɗu, ta fara ferewa.

Hummmm taja sassayan numfashi lokacin da taji tea ɗin data ɗaura yanata baza ƙamshi alamun ya dafu,
da sauri ta ƙarasa free doyan, kana ta wonkesu fes bayan ta rarraba su.

Hannunta ta ɗauraye bayan ta stabtace wurin da ta feren.

Flacks ta ɗauko guda huɗu cikasu tayi baki ɗaya, kana ta maidasu wurin zamansu.

Wannan tukunyar ta kuma ɗaurayewa kana tasa ruwa ɗan madaidaici.


Doyan ta ƙara sassarewa tayisu yan ma dai-dai-ta dai'dai sawa a baki, kana ta kuma wankewa ta tsanesu,
kana ta juyeshi a tukunyar, gishiri ta ɗan tarfa a kai, sannan ta rufe tukunyar tare da ɗan dai-dai-ta
wutan.

Drower gefen dama ta ta kuma buɗe wa, wani farin roba ta jawo mai cike da ƙuli-ƙuli irin dogayen nan
plate ta ɗauka saida ta cikashi kana ta maida ta rufe.

Sannan ta ɗebi borkono dai-dai misali.

Tasa a turmi kana ta sa kanamfari tare da Maggi star, Noo, Tera, Rayco, da dai sauransu, dakasu tayi ,
sannan tasa ƙaragon duk ta haɗa su ta dake su luƙui.

Kana ta kwashesa a wasu ƴan robobi masu masifar kyau da yan marafensu guda huɗu.

Fridge ɗin dake gefenta ta bude ta dauko goran ma shanu, ɗan wani tukunyan ƙasa ta ɗauka tare da
tsulala manshanun,

Daya gefen ta kunna gas ɗin, kana ta ɗaura, sai kuma ta ɗauki manyan albasa har guda huɗu, gyarasu
tayi kana ta yayyankasu.

Tukunyar da doyan ke ciki ta buɗe,

Kai ta jinjina ganin ya kusa dafuwa, da sauri ta watsa rabin albasan da ta yanka ɗin a kai.

Kana ta maida marfin ta rufe, tare da rage wutan.

Ɗan ludayi, tasa cikin man shanun jin ya daina bada sauti alamun ruwan ciki ya ƙare, sake raba albasan
biyu tayi ta watsashi cikin man shanun.

Hhummmmmm taja wani dogon numfashi sabida wani irin masifeffen ƙamshi mai tsinka yawun mutun
daya buɗe illahirin gidan.

Kashe wutan babbar tukunyar tayi dan ya dafu albasar, ta razanu.

Kana ta ɗauko kulli ta kwashe na sashin Hajia Bunayya tare dana Gimbiya Dadu.

Sai kuma na Abbansu,

Sannan na side dinsu.


Sauƙe man tayi kana ta cire wannan albasan daya fara ƙonewa, sai kuma ta juye wannan sauran,
shuyuuuu ya bada sautin soyuwa da zafin man.

ɗaya daga cikin manyan ƙullin naman dake cikin fridge ta ɗauka mai sokoki zalla anyi ta kansu dogo-
dogo.

Ɗaurayewa tayi tasa a yar madaidaicin tukunya ta zuba naman,

dama already ta jajjaga ɗanyen citta da tafarnuwa ta buɗe ta zuba aciki sannan ta Marmasa Maggi da
time kana ta jajjaga attaruhu da albasa ta zuba tare da diban man shanun data soya ta watsa a ciki da
duk sauran spices,Cikin Mintuna kaɗan kichen ɗin ya ɗauki mayataccen ƙamshin girkin dana man shanu
daya wadata aciki zazzafan gashin da takeyiwa Abban.

Mommy kuwa ahankali ta miƙe tashiga kichen ɗin Idanunta akan Khausar dake wanke yan kwanunkan
data ɓata, cikin alamun bacci tace.

“Ƙamshin girkin ki ne ya tasheni da gaba baccin.

nazo in tayaki gashi kuma naga kamar ma kin gama”.

Murmushi Khausar tayi tana motsa gashin naman mai romon da takeyi wanda tuni yanata ɓararraka kai
ta jinjina kana tace.

“Mommy kije ki huta nama gama fa”.

Murmushi Mommy tayi kana tace.

“A'a kada ki damu ai baccin ya sakeni”.

Kai kawai Khausar ta gyaɗa sannan ta cigaba da aikinta tana sauƙe gashin Mommy ta taimaka mata suka
juye kulan Abba da kuma na Dadu, saura kuma suka sawa Hajia Bunayya saura kuma suka barwa kansu.

“Yauwa ɗauki na Ummanki ki kai mata”.

cewar Mommy, cikin sauƙe numfashi Khausar ta ɗauka bayan ta sa jera yan robobin man shanun da
yajin ƙuli-ƙulin, sai yar kulan gashin naman.

Kana ta nufi sashen bakinta ɗauke da sallama tashiga.

Amina dake zaune riƙe da waya ahannu ta watsa mata kallon tsana batare data amsa sallamar taba tace.

“Agola kin zo kina wani tunƙaho kamar gidan tsohonki ne Masarautar very soon zaki bar gidan nan dan
nafi ƙarfin nayi shearing abinda nake so dake”.
Ya mutsa fuska Khausar tayi tare da jan siririn tsaki tace.

“Iska na wahalar dame kayan kara wannan ƴar masarautar kike mgn a kai har wata siyace”.

tana ida maganar ta fice batare data jira jin abinda Amina zata ceba.

Kai tsaye kichen ta nufa tsaye ta samu Mommy tana ɗauraye tukwanen da Khausar tayi amfani dashi
kallon ta tayi tace.

“Ki ɗauki kular Gimbiya Dadu ki kai mata”.

Langwaɓar da kai Khausar tayi tace.

“Ayyah Mommy Haiydar ya Kai mana”.

Juyawa Mommy tayi ta kalleta da faɗin.

“Wai Khausar Meyesa idan na aike ki sashen Gimbiya Dadu sai kice in aiki Haiydar bana jin daɗin abinda
kike min fa wato kina nuna min cewa ke ba jikarta bace?”.

Girgiza kai Khausar tayi tace.

“Wallahi Mommy Ina tsoron zuwa wajenta bana shiri da ita”.

Kallon Mamaki Mommy tayi mata kafin ta watsa mata harara da faɗin.

“Rufe min baki zakiji tsoronta ita ɗin kurace? wato kinje kakar ki tasa Miki ra'ayi da batun cewa ita
Mayya ce da sauransu ko?”.

Girgiza kai Khausar tayi Idanunta cike da ruwan hawaye aranta tace. har yanzu Mommy ba zata gane ba
taya zan ganar da ita cewa ni kaina na gamsu da cewa matar nan Mayya ce.

Amma nasan kona faɗa ba zata yarda ba dan yanda take haƙiƙan cewa akan ba Mayya bace ko ‘ya‘yan
cikinta basa haƙiƙan cewa akan hakan, ita babu dama ace Gimbiya Dadu Mayya ce bayan ni da kaina
naga alamomin hakan kuma ya fito da bakinta ta faɗa min ita Mayyace kawai ya rage amma sam
Mommy taƙi yarda idan taji mutum ya fadawa Gimbiya Dadu Mayya aita bala'i da ita se kace Uwarta aka
kira Mayya.

Ita kuwa Mommy ganin yanda Khausar ta tsirawa waje ɗaya idanu yasa aɗan fusace tace.

“Khausar ba magana nake Miki ba ko baza kije bane Inje da kaina?!”.

Asanyaye tace.
“Ayyah Mommy kiyi haƙuri zanje”.

Ta Faɗa tare da ɗaukar kulan ta fice tana furta.

”‫“اعذبكلمتلله تممت منشررم حلق‬.

Bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon akan darduma taga Gimbiya Dadu na sallar maghariba cikin sauri
ta ajiye kular.

Ita kuwa Gimbiya jin Muryan Khausar yasa cikin hanzari tayi sallama batare data idar ba ta juya ta zuba
mata Na mujiya.

Ita kuwa Khausar cikin sauri ta juya ta fice daga sashen ta nufi sashen su tana sakin Ajiyar zuciya sai
kuma ta furta.

“Alhamdulillah”.

Sosai tayi farin cikin tarar da Gimbiya Dadu tana Sallah.

Koda ta shiga Falon nasu bata samu Mommy ba da alama tana ciki tana sallah kai tsaye Bedroom ɗin su
ta wuce tare da shiga toilet bayan tayi addu'a.

Anutse tayi alwala tare da fitowa da ƙafar dama.

Darduma mai taushi dake fitar da sanyayyan ƙamshi ta shimfiɗa kana ta sanya dogon hijabinta ta
fuskanci alƙibla cikin nutsuwa tare da maida komai zuwa ga mahalicci ta gabatar da sallah bayan ta idar
ta ɗaga hannunta biyu sama tare da lumshe Idanunta cikin tsantsar nutsuwa tare da ladabi alokacin
neman wani buƙata ga Ubangiji mabuwayi gagara Misali ta ɗaga hannunta biyu tace.

“Ya waduud,Ya zul'arshil Majeed,Ya fa'alil lima yureed As'aluka bi izzatil lati la yura wa mulki kallazi la
yurad wa nuru wajihikallazi mala alkana arshik najjini min hazal mujrimin ya Allah ka tsare min
mahaifiyata da abinda ke cikinta daga sharrin Mai sharri”.

ta faɗa tare da shafawa Alkur'ani ta ɗauka ta fara Muraja'a tun daga Kahf sai data je Hajj kafin ta tsaya ta
miƙe ta ida da Isha'i awajen ta kishingiɗa da haka bacci ya ɗauke ta.

Washe gari juma'a Khausar na zauna afalon Mommy akan Lallausan Capet yayin da Mommy ke saman
kujera Khausar na matsa mata ƙafafunta ahankali Khausar ta ɗago kai tare da kallon Mommy da
Idanunta ke lumshe tace.

“Mommy wallahi nayi missing Hajja Nana, Baffa Jauro Sadik, Dije duka mutanen Rugar ma nayi kewarsu
gashi babu network bare nakira naji Muryansa”.
Murmushi Mommy tayi tare da jan numfashi kana ta buɗe Idanunta dake lumshe tace.

“Lalle kam Khausar yau kece ke faɗin Kinyi kewar Hajja Nana da bakin ki?”.

Murmushi Khausar tayi wanda ya lotsar da dimple ɗin ta kana tana cigaba da yiwa Mommy massaging
ƙafafunta tace.

“Allah tana da daɗin zama kawai dai faɗanta da kuma mulkin mallaka da take nunawa yasa bamu jituwa
amma tanason Babana da yawa sannan tana masa addu'a ni kuwa kinga duk mai yiwa Babana addu'a ina
ƙaunarsa”.

Ta ƙarashe tare da buɗe Idanunta dake lumshe wanda ruwan hawaye ya cika su.

Shafa kanta Mommy tayi tare tace.

“Ubangiji Allah yajiƙan sa da rahma Allah ya gafarta masa Ubangiji ya jiƙan dukkan musulman da suka
rigamu gidan gaskiya”.

Sanyayyar Ajiyar zuciya me haɗe da kyewa Khausar ta saki kana ahankali ta furta.

“Ameen”.

Mommy tace.

“Sai ki shirya idan kunyi wani hutun kije ki gansu”.

Wara ido Khausar tayi tare da gyara zamanta kana fuskarta ɗauke da murmushi tace.

“Ai lalle kam”.

Sai kuma tayi saurin juyawa jin Muryan Asma'u na sallama.

Ƙarasawa Falon Asma'u tayi tare da zama daga gefen hagun Khausar ta ajiye Handbag dake hannunta ta
shiga Matsawa Mommy ƙafanta na hagu da faɗin.

“Mommy ina kwana yasu Raudat?”.

Hannu Mommy ta sanya ta shafa kanta da faɗin.

“Lafiya lau Asma'u ya gida yasu Umminki?”.

Asma'u na cigaba da Matsawa Mommy ƙafanta tace.

“Tana lafiya tace na gaisheki”.


Mommy tace.

“Ina amsawa”.

Ita kuwa khausar kallon Asma'u tayi tace.

“Sannu da zuwa taso mu shiga ciki”.

Kai Asma'u ta gyaɗa sannan ta miƙe ta ɗauki Handbag ɗin ta suka shiga.

Zama tayi agefen gadon Idanunta akan Khausar data buɗe ƙaramin fridge ta ɗebo mata kayan marmari
tace.

“Anbani saƙon gaisuwa in kawo miki”.

Ajiye ƙaramin Plate ɗin Khausar tayi tare da zama tace.

“Toh ina Amsawa wani bawan Allah ne?”.

Da sauri Asma'u ta ƙumshe dariyar dake cikinta kana tace.

“Moddibo ne yace agaisheki da hannu”.

Zare idanu Khausar tayi lokaci ɗaya ta ƙware da Inabi dake bakinta da dugu ta miƙe ta nufi fridge ta ɓude
Goran Swan water ta ɓude ta kafa abakinta saida tasha fiye da rabi kafin ta janye roban daga bakinta
tana maida numfashi.

Asma'u kuwa kasa riƙe dariyar ta tayi cikin dariya sosai tace.

“Me haka Khausar daga jin sunan Moddibo zaki wani ruɗe haka?,sai kace wani abin tsoro!?”.

Zama Khausar tayi tana maida numfashi tace.

“Wallahi mutumin nan ya wuce inda kike tunani yanda kika san bashida zuciya aƙirjinsa baya jin bada
haƙuri fa”.

Ta ida maganar tare da jan siririn tsaki tana tuno fuskar Moddibo lokacin da take bashi haƙuri.

Asma'u ta katse shirun tare da buɗe Handbag ɗin ta ta ciro takardan Economics da Mi'atu Hadith da
sauran darasin da sukayi ta miƙa mata tace.
“Gashi ki kwafa sannan kiyi karatu akai”.

Amsa Khausar tayi tare da budewa tace.

“Toh shikenan ba matsala zan duba”.

Bayan sun sake taɓa hira Asma'u tace.

“Zan tafi”.

Khausar tace.

“Tun yanzu?”.

Hararanta Asma'u tayi tayi tace.

“Eyyyyy lalle kam aigwara ni dakeke sai ki kusan shekara bakije gidanmu ba”.

Tana gama Fadar haka ta Miƙe ta fita.

Dariya Khausar tayi tare da sanya Blue Black ɗin hijabinta ta fice afalon ta samu Asma'u nayiwa Mommy
Sallama bayanta tabi suka fice.

Washe gari ta kama ranar.

Asabar Hajiya Bunayya da Hajiya Lami ce acikin mota, suka nufi unguwar shamaƙi, yayin da Hajiya
Bunayya ke tuƙi suna sauraron wakar Nazeer Sarkin Waƙa mai taken Bamu babu ku,kuma baku babu
mu.

Cike da nishaɗi Hajiya Lami tace.

“Hajiya Bunayya Matsalar mu tazo ƙarshe da zaran munje wajen wannan mutumin komai yazo ƙarshe
dan ina da tabbacin aikinsa”.

Dariya Hajiya Bunayya ta sheƙe dashi tare da buga stairing motar tace.

“Kedai bari nayi al'ƙawari saina tarwatsa wannan matar”.

Da wannan hiran suka isa unguwar daga can bakin hanya sukayi parking motarsu.

Kana suka ɗanyi tafiyar ƙafa kaɗan suka tsallaka titin, suka nufi wani ƙaton kango mai zagaye da dogon
katanga da duhuwar bishiyoyi,
da baya-baya suka fara shiga cikin wajen da manyan bishiyoyin Tsamiya dana kuka suka masa ƙawanya
sai kuma wasu manyan bishiyoyi irin na Ceɗiya masu masifar tsawo da duhu kana sai wani ƙaramin
bukka daya kasance Atsakiyar bishiyoyin,

jikin bukkar ke waye yake da jajayen ƙyalle da wasu irin ƙwarya masu masifar munin gani ajikin ƙwaryan
akwai kuratandu sai kuma wasu baƙaƙen ƙaho masu siffar fuskan bil Adam.

Daga nesa suka ajiye takalmansu kana suka cigaba da tafiya da baya har suka shiga cikin gidan da ƙafar
hagu yayinda wani masifaffen ɗoyi ya cika gidan baki daya ya mamaye ilahirin gidan.

Cikin ɗaga sautin murya suka haɗa baki wajen faɗin".

“An gaida Boka Kar'uzu uban bokaye angaida la'anannen Uban la'anannu mugu uban mugaye

Hatsabibi uban hatsabibai”.

Daga ciki kuwa wata daskararriyar murya mai firgitarwa mara daɗin saurara yace.

“Kushigo da baya-baya kana ku tabbata ƙafar hagu zaku riƙa takawa har ku iso gareni”.

Cikin tsinkewar zuciya da matsanancin tsoron kada su saɓa masa doka cike da biyayya suka gyaɗa masa
kai tare da ƙara sawa kusa dashi suka zauna suna maida numfashi.

Cikin daskararriyar muryarsa mara daɗin sauraro yace.

“Ku tashi anan suna zaune zaku danne ɗan ƙundalo mai ido agoshi! Maza ku koma ta gefen hagu bana
ƙaunar ganin ku.

A dama saboda ba aikin dama zamu yiba”.

Tsaban tsoro saidai Hajiya Bunayya ta dungura tare da kurje hannunta kana jikinsu na rawa suka koma
gefen hagunsa.

Kallon Hajiya Bunayya yayi ya kece da wata mahaukaciyar dariya me tsananin razanarwa, ya nunata da
wani mummunan yatsansa da farce yayi tsawo kana yace.

“Kin makara cikinta har ya kusa wata uku amma zamu jijjigesa da ƙarfin ikon mu zamu fito dashi!”.

Ita kuwa Hajiya Bunayya Atake taji tsoron ta ya tafi ta washe baki da faɗin.

“Laaa Malam kasan abinda ke tafe dani?”.


Cikin fushi yace.

“Sunana ba Malam ba Kur'ani kika gani agabana ko hadisai da za ki kirani da Malam ki kirani da Boka
Kar'uzu uban bokaye La'anannen uban la'anannu Mugu Uban Mugaye”.

Ƙasa da kai tayi tana cewa.

“Tuba nake Boka Kar'uzu bazan sake ba”.

Kai ya gyaɗa mata yace.

“Sai kuma batun Jameel da ’yarki Amina”

Cikin rawan jiki tace.

“Eh boka Kar'uzu”.

Ya kece da wata mahaukaciyar dariya yace.

“Ai ƙaddarar abai-bai take,Ai ƙaddarar abai-bai take, ƙaddarar abai-bai take!”.

Ita kuwa Hajiya Lami cikin zaƙuwa take gyaɗa kai.

Hajiya Bunayya tace.

“Boka kamar ya ƙaddara abai-bai take ban fahimta ba”.

Yace.

“Babu damuwa za'ayi Miki aiki”.

Hajiya Lami ta gyara zama sosai tace.

“Toh Boka Kar'uzu ni ya batun ‘yata?”.

Ya sake kecewa da wata mahaukaciyar dariya yace.

“Aike batun ki mai sauƙi ne shi wannan babu wata Aransa shi wannan dakike gani yana nan kamar Waliyi
ne, koko ince katako, sai dai fa akwai ganye bishiya da yake tsirowa ajikinsa har ta fara jijiya ajikinsa tana
gab da zuba rassuna”.

Hajiya Lami tace.


“Boka koma wani irin ganye ne Indai bana Samira bace atun ɓukesa”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Angama angama”.

Cikin jin dadi ta juya ta kalli Hajiya Bunayya tana sakar mata da murmushi alamar da akwai Nasara.

Sai kuma ta juya ta kalli Boka Kar'uzu tace.

“Ya batun abubuwan aiki?”.

A tsawace boka Kar'uzu yace.

“Zaku kawo Fararen Bunsuraye guda uku, Da baƙaken karnuka guda biyu da baƙar kaza mai bungi-bungi
guda ɗaya na batun aikin zubar da ciki.

Batun Jameel kuwa zaki kawo gurguwar jaka mace sannan ki samu makauniyar tinkiya me watanni
bakwai sai kuma agwagwa fara mai ƙafa ɗaya”.

Zare Idanu sukayi Atsorace jin abubuwan da ake buƙata.

Ya cigaba da cewa.

“Batun aikin Moddibo kuwa zaku kawo Gurguwar shanu ja mai Ido ɗaya da kuma namijin doki fari soll
wanda aka haifesa acikin gida sai kuma ku samo Alade guda biyu mace dana miji”.

Cikin tashin hankali da damuwa Hajiya Lami tace.

“Boka a ina zamu iya samo wa'annan abubuwan aise kai saidai mu bayar asamo”.

Yace.

“Toh ku ajiye kuɗin masu tarin yawa”.

Cikin rawan jiki Hajiya Bunayya tasa hannu a jakarta ta ciro kuɗi wanda batasan adadin suba ta ajiye
masa”.

Kallon kuɗin yayi yace.

“Kuje bayan sati biyu kuzo ku karɓi kayan aikinku sha yanzu magani yanzu”.

Godiya suka masa kana suka tashi suka fita kamar yanda suka shigo.
Acan ɓangaren su Khausar kuwa karatu suke sosai babu kama ƙafar yaro sabbin Malamai da aka kawo
musu sun zage damtse wajen koyar da ɗalibai ga kuma sabbin ɗalibai da ake shigowa dasu saboda yanda
aka tsara Makarantar sosai makarantar ya sake samun ɗaukaka fiye da farko ga kuma shirye-shiryen
musabaƙa da akeyi na Jahar Taraba baki ɗaya Khausar da Asma'u sun sake dagewa.

Bayan sati biyu Hajiya Bunayya da Hajiya Lami ce zaune agaban Boka Kar'uzu.

Wani ƙullin magani ya ɗauka tare da kallon Hajiya Bunayya ya miƙa mata kana yace.

“Wannan ki dafa shi da farfesun kayan ciki ki bawa Hajiya Aysha tana ciki, sunan cikinta anyi angama
saide wani cikin bashi ba!.

Sannan idan kin shirya kizo za'a zazzage mata mahaifa asa mata ajiya yanda baza ta sake ɗaukar wani
cikin ba, sannan kuma mijinta zai tsaneta ba zai sake sha'awar kusantar taba!”.

Murmushin samun nasara Hajiya Bunayya tayi tace.

“Boka Indai cikin nan ya zube zan dawo akan aikin amma yanzu burina cikin ya zube sannan ajawo
hankalin Jameel kan Amina”.

Wata mahaukaciyar dariya Boka Kar'uzu ya sheƙe dashi yace.

“Ga wannan”.

Hannu bibbiyu Hajiya Bunayya tasa amshi ƙullin maganin tana jujjuyawa yace.

“Ki bawa ‘Yarki Amina tayi wanka dashi sannan tayi hayaƙi idan zatayi hayaƙin ta ɗago kaskon ta kawo
bakinta ta riƙa kiran Jameel!, Jameel!!, Jameel!!! na tsawon kwanaki uku sannan ta tsallake kwana uku
ta sake na kwana uku na sannan ta sake kwana uku ta tsallake kwana uku sannan ta sake kwana uku
kuma ko wanne idan tazo hayaƙin sai takai kaskon bakinta ta kira sunansa kada ku yarda asamu kuskure
dan in an fa samu kuskure abun bazaiyi kyau ba”.

Kallon Hajiya Lami Hajiya Bunayya tayi tare da jinjina mata hannu tana murmushi cikin ƙasa da murya
tace.

“Alhamdulillah nakusa ganin ƙarshen wannan matsiyatan”.

Martanin Murmushin Hajiya Lami ta mata itama ranta fess burinsu ya kusa cika.

Tunda Boka Kar'uzu yace.


“Muddin tayi na tsawon wannan kwanakin shida kansa zai kawo kansa gareta idan kuma wannan baiyi
ba akwai wanda zamu sakeyi saidai shi wannan kankat ne amma shi sai farkon damuna tukunna zamu
samu ayishi”.

Cike da farin ciki Hajiya Bunayya tace.

“Boka Kar'uzu Uban bokaye Insha Allahu ma nasan wannan aikin zaici”.

Cikin wata razananniyar tsawa yace.

“Oho Ni dai nace kada ki sake kiramin sunan Allah anan domin da kina jin tsoronsa ba zaki zo nanba bare
har kinemi aikata mugun abu akan wani idan kuma kina son aikin ki ya ɓaci ki sake kiran Allah anan”.

Cikin rawan baki da tsoron kada aikinta yaƙi ci tace.

“Tuba nake Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye da ikon ka
wannan aiki zaici”.

Ya sheƙe da wata mahaukaciyar dariya mai kama da sautin ƙaran lalataccen Injin Markaɗe yace.

“Yanzu ne aikin ki zaiyi yanzu ne kika yi magana mai ma'ana”.

Ta saki ajiyar zuciya cike da farin ciki.

Hajiya Lami ta matso kusa tare da gyara zama sosai tana fuskantar Boka tace.

“Ni kuma ya maganar ’yata?”.

Wani irin kallo ya mata kana yace.

“Na ‘yarki sai anyi babban shiri domin wannan da kike gani shida saƙago basu da banbanci baya kallon
mace ako wani irin mataki daya wuce ɗaliba ya karantar da ita ya kuma bata ilimi da tarbiyya shi koda
mace zata wuce tsirara agabansa babu abinda zai damesa da ita tamkar zuciyar dutse ne aƙirjinsa!”.

Ta gumi Hajiya Lami tayi tare da faɗin.

“Ikon Allah aƙasan ranta”.

Boka Kar'uzu ya cigaba da cewa.


“Sai munyi mata shiri sosai yanda lokaci ɗaya zata jawo hankalin sa gareta sai bayan wata biyu zaki zo ki
karɓi haɗin da muke tsuma shi sannan tayi kokari ta bashi yaci daya ci aiki ya gama”.

Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta saki tace.

“Da ƙarfin ikon ka zamuyi hakan boka”.

Ya kece da wata mahaukaciyar dare yace.

“Na gama daku zaku iya tafiya”.

Miƙewa sukayi suka ce. “Godiya muke Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu
Uban mugaye”.

Shikuwa Dariya ya kece dashi yana jin daɗin kirarin da ake masa kamar yanda suka saba shiga haka suka
fita da baya.

Cikin tsananin farin ciki Amina ke kallon Hajiya Bunayya dake mata bayani karɓan maganin tayi tare da
rungume Hajiya Bunayya tace.

“Nagode Umma”.

Ƙullin maganin ta karɓa sannan ta shiga ban ɗaki tayi wanka dashi tana fitowa Hajiya Bunayya ta kawo
mata wuta akasko ta bata zama Amina tayi tare da kai saitin kaskon bakinta tace.

“Jameel!, Jameel!!, Jameel!!!”.

Ta faɗa da ƙarfi yayin da hayaƙin ke bin ilahirin jikinta kallon Hajiya Bunayya tayi cikin jin daɗi tace.

“Umma M Jameel ya Kusa zama mallakina?”.

Dariya Hajiya Bunayya tayi tace.

“Ƙwarai kuwa?”.

Asiya ce tashigo falon da Sallama da sauri ta toshe hancinta jin wani masifaffen wari da ƙauri tayi saurin
kallon ƙofar Bedroom ɗin Hajiya Bunayya inda nan take jin wari da ƙaurin ke fita.

Tana ƙoƙarin shiga Hajiya Bunayya ta fito Kallonta Asiya tayi tace.

“Ummah warin meke fita daga ɗakinki?”.

Harara Hajiya Bunayya ta watsa mata tace.

“Warin lafiya ko kuma ke ki kafi kowa hanci?”.


Girgiza kai Asiya tayi tace.

“Wallahi Ummah da gaske akwai..”.

Tsawa Hajiya Bunayya ta buga mata da faɗin.

“Ki wuce kibani waje sakaryar banza mara tunani”.

Ahankali Asiya tace.

“Allah yabaki haƙuri Ummah”.

Kana ta juya cikin mutuwar jiki ta nufi ɗakinta.

Bayan wata ɗaya:

Amina ta gama amfani da duk maganin da Hajiya Bunayya ta karɓo mata awajen Boka Kar'uzu cike da
farin ciki ta dubi Hajiya Bunayya asanda take sanya uniform ɗinta tace.

“Ummah na matsu na isa Makaranta inga irin tarban da Jameel zai min!”.

Murmushi Hajiya Bunayya tayi da faɗin.

“Kede ki kama kanki karki bari ya gane kina sonshi ya rainaki dan yanzu sai yanda mukayi dashi”.

Asiya data fito daga kichen hannunta riƙe da Cup ɗin tea dake tururi ta zauna akan ɗaya daga cikin
kujerun falon Idanunta akan Amina tace.

“Amina ki maida hankali akan karatunki kada kice zakiyi wasa da damarki komai da kika gani arayuwa
muƙaddari ne daga Ubangiji”.

Cikin tsawa Hajiya Bunayya tace.

“Asiya zanci Ubanki fa idan baki fita sabgar Amina ba shegiyar yarinya me baƙin halin tsiya.

Niko anya ma ba canza min ke akayi ba, dan wallahi badan kamannin dake tsakanin mu ba sai ince sauya
min ke akayi”.

Miƙewa Asiya tayi tace.

“Allah ya baki haƙuri Umma amma ita gaskiya ɗaya ce”.

Harara Amina ta watsa mata tace.

“Ke har wani gaskiya ce dake to ki riƙe gaskiyar ki bama bukata”.


tana gama fadar haka ta fice.

Atare suka fito da Khausar dake riƙe da hannun Raudat kallo ɗaya Khausar ta mata ta kawar da kanta
gefe,

Ita kuwa Amina murmushi mai cike da ma'anoni ta sakarwa Khausar sannan tashiga motar yayin da
Khausar tabi bayan ta suka shiga sannan driver yaja motar suka tafi.

Motar na tsayawa kowa ya nufi ajinsu kamar kullum saida Khausar takai Raudat ajinsu kafin ta wuce
ajinsu.

Aɓangaren Amina kuwa kai tsaye ajinsu ta nufa tare da zama tana sakin murmushi duk da Amina da
Khausar

Shigansu baa daɗewa M Jameel ya shigo ajin cikin wata farar gezner me kyau yayin da kansa ke sanye da
baƙin hula gashinsa ya fito ta ƙeya ƙafarsa sanye da sau ciki baƙi jikinsa na fitar da sanyayyan ƙamshi
Amina kuwa ta gumi tayi tare da zu bawa sajensa zuwa gemunsa idanu tana mai furta.

“Wowww”.

Shi kuwa M Jameel hankalinsa ya mayar kan Black Board.

Cikin karya murya tare da lanƙwasa harshe Amina tace.

“Malam Barka da safiya”.

Anutse M Jameel ya juya ya kalleta cikin sauri ya runtse Idanunsa da ƙarfin gaske.

Sai kuma ya sake buɗewa akan fuskarta still da sauri ya sake runtse Idanunsa yana mai furta.

“Hasbunallahu wani'imal wakil.

Astagfirullah wa'atubu ilaik”.

Ita kuwa Amina cike da ƙissa ta sake karya harshe tana juya Idanunta tace.

“Malam ina kwana”.

Shi kuwa M Jameel Batare daya juya ya kalleta ba ya ɗaga mata hannu, domin tun sanda ya kalli fuskarta
sau ɗaya yaga kamar an ƙona fuskar Biri, sosai ta masa muni tunda yake kallon fuskar yarinyar bai taɓa
ganin tayi masa muni irin na yau ba, baki ɗaya fuskarta babu haske bare annuri Kawar da kansa yayi ya
cigaba da koyar wansa batare daya yarda ya sake kollon inda take ba har yagama ya fita.

Ita kuwa Amina bata kawo komai aranta ba domin atunaninta maganin ne ya fara aiki.

Acan ajinsu Khausar kuwa Moddibo ne tsaye jikin Black Board Ya rubuta Geography ajiki,

Da alama shine subject ɗin da zai riƙa ɗaukansu.

Jikinsa sanye da Jallabiya Coffee color yayin da kansa ke naɗe da hirami siririn sajensa zuwa gemunsa
yasha gyara sai sheƙi yake jikinsa na fitar da sanyayyan ƙamshi tularen Oud.

Cikin nutsuwa da kuma sanyin Muryansa ya gyara tsayuwar sa tare da harɗe hannayensa aƙirji kana ya
ɗan lumshe idanunsa kafin yace.

“Class What is Geogry?”.

ya ƙare tambayar cikin tsananin tsuke fuska da tsare hirar samata ƙasa, sabida yanayin dariasin in yayi
garaje yara zasu rainasa, Allah ya sani ba ƙaunar darasin yakeba sabida yanayin abubuwan dake ƙunshe
a ciki masu cin karo da addini.

Shiru class din yayi ba wanda yayi magana sabida yadda baya kallon idonsu haka suna kan suke shayin
koda motsi bare Kallonsa.

Khausar da Idanunta ke lumshe ta buɗe tare da zaro harshe ta ɗan lashi lips ɗin ta sai kuma ahankali ta
ɗaga siririn hannunta dake maƙale da zoben azurfa da kuma Gold.

Shi kuwa Moddibo ahankali ya maida da idanunsa zuwa ta inda take.

Kana tsare sashin da taken yayi da ido amman ba fuskantar yake kalloba, ƙara tsuke fuska yayi tare da sa
hannunsa ya shafa yalwataccen sajen dake fuskarsa kana ya mata alamun ta tashi.

Cikin nutsuwa tare da taka tsan-tsan akan gudun lefin da zatayi ta motsa lips ɗin ta da yayi pich saboda
man baki data shafa kana ta lumshe Idanunta tace.

“Geography can be defined as the discription of the Earth”.

Jinjina kai Moddibo yayi tare da faɗin.

“Dayyit, sit-down”.

Kai ta gyaɗa tare da zama.

Ahankali ya motsa lips ɗinsa da faɗin.


"Yah Salam". Yayi mgnar yadda ba mai jinshi.

gajeren tsaki, Samira Sani taja dan ji tayi kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu saboda baƙin ciki taso ace itace
zatayi wannan karatun

Shikuwa Moddibo kallon Khausar yayi tare da yimata alamar tazo cikin sauri ta miƙe ta isa gabansa, ba
tare da yace mata komai baya miƙa mata hannunsa.

Kallon tattausan farin tafin hannunsa dake ɗauke da zara-zaran yatsu da ga wasu zoben azurfa fari da
baki daya ƙawata yatsun.

Cikin rawan murya tace.

“Malam mai zanyi?”.

Ya mutsa fuska yayi tare da watsa mata harara daya sa ‘ya‘yan hanjinta kaɗawa da ido ya nuna mata
zobunan hannunta.

Cikin rawan jiki ta cire ta basa lokaci ɗaya Idanunta suka sauya launi sosai take masifar son zoben ɗaya
Mommy tace ta bata ɗaya kuma Hajja Nana ce ta bata ta kuma shaida mata tun na babantane na
azurfan.

Saida ta koma ta zauna yace.

“Nasha faɗa muku cewa nan ba wajen ado bane idan kowa yace zaiyi ado yazo ai wasu ma baza agansu
ba”.

Ya ida maganar tare da juyawa ya cigaba da koyar musu cike da ƙwarewa tare da kare ƙa'idar musulunci
gudun dulmuyar tunanin ɗalibai.

Bayan kwana uku baki daya Amina tashiga damuwa da tashin hankali koda ta gaida M Jameel baya
Amsawa sai dai ya ɗaga mata hannu, gwara ma da yana kallonta Sannan wataran yakan mata murmushi
amma yanzu koda kallonta baya ƙaunar yi.

Bayan antashi tana komawa gida.

Kai tsaye Bedroom din Hajiya Bunayya ta nufa.

Zaune ta samu Hajiya Bunayya riƙe da kofin tea mai ɗumi ahannunta.

Zama tayi agefen Hajiya Bunayya cikin raunin murya tace.


“Ummah tunda fa nagama aiki da maganin M Jameel Koda kallona ne baya ƙaunaryi, ko gaishesa nayi
saidai ya ɗaga min hannun!”.

Da Mamaki Hajiya Bunayya tace.

“Ikon Allah to ya zama dole inshirya na koma gidan Boka Kar'uzu inji me yesa”.

Gyaɗa kai Amina tayi tace.

“Gaskiya ya kamata dai Ummah".

Hajiya Bunayya tace.

“Gashi nima yau nakeso in fara na wannan matsiyaciyar matar dan nafi so dama sai kin gama naki sai in
dafa in bata”.

Amina tace.

“Ya kamata dai kam yazo tana ta cika mana gida da yara”.

Ita kuwa Hajiya Bunayya miƙewa tayi da kanta ta shiga kichen ta buɗe fridge ta ɗauko kayan ciki ta haɗa
masa kayan ƙamshi da kayan hadi Sosai sai tashin ƙamshi yake.

Warmers ta ɗauka ta juye kana ta dauko ƙullin maganin da boka Kar'uzu ya bata ta barbaɗa akai sannan
ta ɗauka ta nufi sashen Hajiya Aysha dashi.

Mommy na zaune afalo ta miƙe ƙafafunta ta jiyo Sallamar Hajiya Bunayya murmushi tayi tare da tace.

“Yaya kece da kanki sannu da zuwa”.

Murmushi Hajiya Bunayya tayi tace.

“Wallahi kuwa kinga Perpesoup nayi na kayan ciki, nasan kuma kina so, shiyasa nace nari na kawo miki,
idan kinsha da dan ruwan Tea mai ɗumi zakaji daɗi asanyin da ake”.

Murmushi Mommy tayi tace.

“Aikuwa Nagode yanzu nake tunanin tashi in dafa ko indomie ne naci dan na gagara cin tuwon".

Murmushi Hajiya Bunayya tayi tace.

“Ayyah ƙanwata to ga wannan sai kisha ai zakiji daɗinsa”.


Acan ɗaki kuwa Khausar ce tsaye jikin wodurobe tana gyara kayansu da Raudat ta burkitasu.

Siririn tsaki ta saki tare da kallon tulin kayansu dake burkice kamar basu taɓa ganin ninkiba bare guga
stool taja ta zauna tana ninke kayan.

Acan falo kuwa yunƙurawa Mommy tayi da faɗin.

“Bari na ɗauko Plate".

Da sauri Hajiya Bunayya ta mike tare da cewa.

“A'a bari na ɗauko Miki”.

Ta Faɗa tare da shiga kichen ɗin.

Ita kuwa Mommy murmushi tayi aranta tana jinjinawa ƙaunar da Hajiya Bunayya ke nuna mata tabbas
samun irinta acikin kishiyoyi sai antona.

Hajiya Bunayya kuwa nashiga kichen ta fashe da dariya mai ɗan sauti tace.

“Shegiyar mata zaki ci Ubanki atunaninki har ƙasan raina nake sonki”.

Sai kuma ta sake tun tsirewa da wata dariya mai sauti can ƙasa, kana ta ɗauki cup ta zuba mata Tea kana
ta ɗauki Plate da spoon ta fita.

Miƙa wa Mommy plate ɗin tayi tare sa faɗin.

“Naga kamar kwana biyu bakyajin daɗi”.

Ya mutse fuska Mommy tayi kana tace.

“Wallahi kuwa gaba ɗaya bana jin daɗin jikina wannan karon kuma da laulayi sosai yazo min”.

Cike da tausayawa Hajiya Bunayya tace.

“Ayyah sannu Ubangiji Allah ya inganta”.

Aranta kuwa cewa tayi Allah ya tarwatsa matsiyaciya.

Ita ko Mommy tace.

“Ameen ya Allah”.
Miƙewa Hajiya Bunayya tayi tare da ɗaukan Plate din ta ɓude perpesoup ɗin dake tururi yana tashin
ƙamshi ta zubawa Mommy tare da miƙa mata da kofin shayin.

Lumshe idanu tayi sosai ƙamshin ya bugeta, a take yawunta ya tsinke abinka da mai cike lokaci ɗaya taji
ranta yabiya da Perpesoup ɗin hannu tasa ta amsa tare da ajiye plate ɗin bisa cinyarta kana tasa spoon
ɗin da sauri ta ɗebo sokar hanta da rokon ta perpesoup ɗin takai bakinta.....!

*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son
k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman
lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun
matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa
ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki
tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones
dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da
tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da
ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda
ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya
wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka
kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki
da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp
in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta,
muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina
nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a
ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.

0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta
wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije
gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.
GARKUWAR MA'AURATA

_By_

*GARKUWAN MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_Page 11_

_NA_

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*FREE PAGE fa ya kusa ƙarewa*

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine wannan Free page ne ƴar uwa 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA
ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ɗin.*

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

Cikin lumshe Ido Mommy ke cin perpesoup ɗin yayin da daɗinsa ke ratsa ilahirin jikinta,

kallonta Hajiya Bunayya dake murmushi tayi tare da ɗiban romon da cokali takai bakinta kana ta buɗe
Idanunta dake lumshe.

Tace.

“Gaskiya Yaya Nagode wallahi bakiji yanda naji daɗin Perpesoup ɗin nan ba, dama sai tunanin a binda
zanci nake tuntuni sai kuma gashi Allah ya kawo ki”.

Murmushi mai cike da Ma'anoni Hajiya Bunayya tayi kana ta muskuta tare da gyara zamanta tace.

“Lallai de kam aidama sanyin nan saida abu mai ɗumi da ɗan yaji-yaji”.
Yayin da aƙasan ranta wani irin farin cikine mara misaltuwa wanda har yakasa ɓoyuwa asaman fuskanta.

Ita kuwa Mommy Sosai take cin perpesoup ɗin tana mai lumshe Idanunta yayin da daɗin sa ke ratsa har
ƙwaƙwalwar kanta tace.

“Yaya perpesoup ɗin nan yaji kayan yaji”.

Dariya Hajiya Bunayya tayi tace.

“Dama Alhaji nayiwa nace bari na zubo miki dan nasan zaki ji daɗin sa”.

Kai Mommy ta gyaɗa da faɗin.

“Aikam gashi yamin daɗi sosai”.

Acan ɗaki kuwa miƙewa tsaye Khausar tayi daga kan stool tare da riƙe ƙugunta ta bayan ta gama nin ke
kayan asaman laɓɓannta ta furta.

“Wash Allah!, Gashi yanzu na gama gyara kayan nan, amma Raudat na zuwa ɗaukan abu ɗaya zata
wargaza shi kab, ya zama kamar ba'a taɓa gyarashi, amma Insha Allah next time, Idan ta ƙara har
gitsashi, sama Zan mayar dan kayanta, ta yanda idan tazo baza ta iya ɗauka ba sai ta kirani in bata yafiye
min sauƙi”.

Ta Ida maganar tare da fitowa falon tana riƙe da ƙugunta da hannu ɗaya yayin da ɗaya hannun ke dafe
asaman wuyanta.

Cike da mamaki take kallon Hajiya Bunayya dake zaune yayin da Mommy ta ke shan perpesoup ɗin da
kaɗan ya rage asaman Plate ɗin.

Cikin yanayin tashin hankali da razana Khausar ta ɗaga Muryanta tace.

“Mommy me kike ci?".

Anitse Mommy ta ɗago kanta dan sam batasan ta fito ba sai da taji muryanta, gyara rikon Plate din
Mommy tayi kafin tace.

“Perpersoup ne ko zaki cine?”.

Ita kuwa Khausar kai ta girgiza cikin rawan murya tace.

“A'a nikam bazan ciba Mommy kekam Komai kika samu sai kinci, ba zaki tsaya ki duba ingancin sa da
kuma rashin ingancin saba”.

Baki Mommy ta sake tana kallon Khausar da Mamaki.


Ita kuwa Hajiya Bunayya wani mugun Harara ta galla mata cike da tsanarta tace.

“Komai ta samu saita ci ke kin isa ki hanata cine?, Khausar!, Khausar!!, Khausar!!! ki kiyayeni fa”.

Ta Ida maganar tana dariya irin abin awasa takeyin sa, yayin da kuwa azuciyarta ba haka bane.

Ita kuwa Mommy taɓe Baki tayi tace.

“Yaya rabu da ita itama kanta kwaɗayin ya kawota ƙilan so take in bata”.

Fuska Khausar ta ɓata cike da damuwa tace.

“Wallahi nikam ba zanci ba Mommy kema Meyesa zakici, kema daga ganin abu saiki hau ci, batare da kin
duba ingancin sa ba Allah ma dai yasa kinyi Bismillah”.

Dafe kai Mommy tayi tace.

“Aikuwa de Wallahi kwaɗayin sa yasa na shafa banyi Bismillah ba, Anma bari nayi.

Bismillahi feh Auwalihi Wa'ahirihi”.

Ta faɗa tare da cigaba da shan perpesoup ɗin.

Wani banzan kallo me cike da tsana Hajiya Bunayya ta watsa wa Khausar aranta tace, shegiyar yarinya,
wannan yarinyar saina bi takan ta tukunna zata gane kurenta, bari dai ingama da matsalolin dake
gabana”.

Ita kuwa Khausar kallon mahaifiyarta da har zuwa yanzu take shan perpesoup ɗin tayi tace.

“Wai Mommy ba zaki haƙura dasha haka ba?".

Girgiza Kai Mommy tayi kana tace.

“Kema Idan zaki ci ga shican akula Khausar ban hana kiba, amma wannan tambayoyin naki sun fara
isata”.

Ƙwafa Hajiya Bunayya tayi tace.

“Ƙyaleta bare ma ni bazan bar mata ba ina kedai ya isheki?”.

Cikin sakin fuska Mommy ta gyaɗa kai tare da faɗin.

“Eh Alhamdulillah ya isheni”.


“Aiko buƙatar maje haji salla, ba zan bar matashi ba, tunda dai ke kinsha ai hikenan, idan tanaso ta
biyoni ɗakina”.

Ta ida maganar tare da ɗaukan kularta ta fice bayan ta yiwa Mommy sai anjima.

Zama Khausar tayi agaban mahaifiyarta cikin raunin murya da yanayin damuwa tace.

“Mommy meyesa!?, Rayuwar nan fa ba yanda kika ɗauke ta da yanda zuciyarki take ace haka na kowa
yake da munji daɗin duniyar nan fa, amma Mommy meyesa daga kawo miki abu zaki ɗauka kici yanzu
kuma idan abin cutarwa ne fa?”.

Kallonta Mommy tayi cikin tsukr fuska kana cikin fushi tace.

“Khausar ki kiyayeni fa, bana son wannan baƙin halin da kike ɗaurawa rayuwarki fa. Ni bakiga ina
nunawa matar nan baƙin hali ba haka zalika itama da zuciya ɗaya take zaune damu, zaman lafiya mukeyi
babu kishi bare tsangoma ko hassada, amma meyesa zaki sawa ranki rashin yarda akan n

Me kike zaton zata cutar dani, babu abinda zata yimin dan haka ki kiyaye”.

Ita kuwa khausar hawaye da ya cika mata Idanunta tashiga ƙoƙarin mayarwa sabida takaici,
mahaifiyarta ta ɗauki duk kan yarda da amana ta basu, amma sukuma da wannan damar suke amfani
ganin sun cutar da rayuwarta.

Ƙasa Tayi da kanta kana tace.

“Shikenan Mommy Komai na faɗa miki ba zaki yarda dani ba, amma babu komai Ubangiji Allah yatsareki
ya kuma kareki".

“Ameen”Mommy ta amsa a kufule.

Ita kuwa Khausar cikin mutuwar jiki ta miƙe tare da wucewa Bedroom ɗinta tana maijin wani irin zafi
azuciyarta.

Da kallo Mommy tabi bayanta tana ayyana abubuwa da yawa akanta, tarasa ina Khausar ta ɗauko
wannan halin baki ɗaya bata da yarda muddin Hajiya Bunayya zata kawo mata abu ko Haiydar saita
tsaya tana musu tambayoyi akai, da faɗin kada suci kada suyi kaza da kaza.

Jin ƙiran sallah magriba yasa ta miƙe tashiga Bedroom ɗin ta dan gabatar da Sallah.

Aɓangaren Khausar kuwa tana shiga ɗaki ta lumshe Idanunta tare da manna bayanta da jikin ƙofa.
Hawaye masu ɗumi suka zubo mata jikinta na bata da wani makircin da Hajiya Bunayya ta shiryawa
mahaifiyarta sam bata yarda da wannan perpesoup ɗin da takowo mata ba,

shin wai ma ta wani hanya zatabi ta fahimtar da mahaifiyar?.

Sosai ta zurfafa acikin tunanin da take har aka shiga Masallaci sai, asannan ta sauƙe gauron numfashi
tare da nufar toilet cikin nutsuwa ta ɗaura alwala kana ta fito, tare da shimfiɗa darduma duk da yanayin
zullumi da take ciki bai hanata tattara nutsuwarta zuwa ga Ubangiji mabuwayi gagara Misali ba,

bayan ta sallame ta ɗaga hannayenta biyu zuwa sama kana tace.

“Ya Allah baka zalinci sannan kai ka hana zalunci atsakaninmu ya Allah baka gyan-gyaɗi bare bacci ya
Allah kada ka bawa wannan baiwar taka daman cutar damu ya Allah ka kare mahaifiyata al'farma
Annabi da al'ƙur'ani”.

Kana ta shafa addu'ar tana mai zubar da hawaye har aka idar da Isha'i bata fita ba saima miƙewa da tayi
ta kwanta agado lamo cike da tunanin rayuwa da haka bacci mara daɗi ya ɗauke ta.

Cikin ikon Allah haka Mommy ta kwana lafiya lau batare da wani mugun abu ba, tun Khausar na jira taji
Mommy tace wani wajen nayi mata ciwo ko kuma taga zubewan cikin Mommy kamar yanda Hajiya
Bunayya ta faɗa taji shiru,

hakan yasa ta watsar da abin aranta yayin da Aɓangaren Hajiya Bunayya baki ɗaya kunnenta ke
sauraron jin wani labari daga bakin Mommy sai dai shiru amma tace bari ta kara jira kaɗan ta gani.

Yau kwanan Mommy uku da cin perpesoup ɗin da Hajiya Bunayya ta kawo mata tana zaune a Bedroom
ɗin ta cike da kasala.

Cikin rumtse idonta ta zabura tare da dafe ƙasan maranta da yayi wani masifan murɗawa ahankali ta
furta.

“Wash! Allah na”.

Sai kuma ta koma ta zauna tare da lumshe Idanunta yayin da hannunta na dama ke dafe asaman
maranta sai ka ta miƙe tare da fitowa falon tana takawa ahankali.

Khausar dake zaune a asaman 3sitter Jikinta sanye da half gownt na bacci yayin da ta tura tulin sumar
kanta acikin hular Net Idanunta na kan takardan Geography dake riƙe ahannunta yayin da Nahawu ke
ajiye gefe ta ɗago manyan Idanunta ta zubasu akan Mommy dake ya mutse fuska alamar bata jin daɗin
jikinta, zama tayi akan 1 sitter kana a hankali tace.

“Khausar har yanzu baki shiga ba?”.


ta ida mgnar tana mai cije lips ɗinta.

Ita kuwa Khausar kai ta gyaɗa mata tace.

“Eh Mommy karatu nakeyi, gobe Idan Allah ya kaimu zamu fara Exam ɗin First term, lokacin ai ya tafi
amma Mommy lafiya na ganki haka?”.

Ta ƙare mgnar tana kafe mata ido.

Ya mutse fuska Mommy tayi tare da lumshe Idanunta still cikin na damƙarta tace.

“Wallahi cikina ke ɗan min ciwo Khausar”.

Cike da tausayawa Khausar tace.

“Cikin ki kuma Mommy?”.

Kai Mommy ta gyaɗa tace”.

“Eh”.

Ita kuwa Khausar ajiye takardan hannunta tayi tare da tsirawa mahaifiyarta ta Ido cikin tausayawa tace.

“Mommy kodai in faɗawa Abba Azo atafi Asibiti ne?".

Kai Mommy ta girgiza kana tace.

“A'a ai beyi tsanani har haka ba”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da sauƙe numfashi tace.

“Toh Allah ya sawwaƙe”.

Mommy da hannunta ke dafe asaman cikinta still Idanunta na lumshe tace.

“Ameen”

Miƙewa Mommy tayi ta koma kan 3sitter ta kwanta kamar minti biyu da kwanciyarta ta sai kuma sake
miƙewa ta zauna tana yamutse fuska.

Ita kuwa khausar cikin yanayin damuwa tace.

“Sannu Mommy kode in Kira Abba ne?”.


Girgiza kai Mommy ta kumayi sannan tace.

“A'a tashi ki koma ɗaki nima yanzu zan shiga na kwanta”.

Girgiza kai Khausar tayi tace.

“A'a Mommy Zan zauna dake”.

Lumshe idanu tayi tare da cije laɓɓanta na ƙasa tace.

“Kada ki damu kije ki kwanta na faɗa miki naji sauƙi kuma nima yanzu zan shiga na kwanta”.

Cikin sanyin jiki ta mike kana tace.

“Saida safe Allah yaƙara sauki”.

Mommy ta amsa da “Ameen”.

Ita kuwa Khausar tana shiga ɗaki ta zube akan gadonta tare da faɗa wa duniyar tunanu, a haka bacci ya
ɗauke ta kasancewar dare yaja batayi bacci ba ga kuma gajiya.

A ɓangaren Mommy kuwa haka ta kwana cikin mawuyacin hali tare da murƙusoso cikin matsanancin
ciwon ciki.

Washe gari.

Da safe bayan Khausar na idar da Sallah tayi Azkhar ta nufi ɗakin Mommy bakinta ɗauke da sallama.

Mommy dake kishingiɗe kan darduma ta ɗago kanta tare da amsa sallamar Khausar.

Kusa da ita Khausar ta tsugunna tare da riƙe hannunta tace.

“Mommy ina kwana ya cikin naki?”.

“Murmushin Ƙarfin hali Mommy tayi kana tace.

“Naji sauƙi Khausar kije ki haɗa muku abin Breakfast kada lokaci ya ƙure”.

Kai Khausar ta gyaɗa kana tace.

“Amma da sauki Mommy kodai daurewa kike yi?”.


Murmushi Mommy tayi tace.

“Eh jeki shirya muku”.

Kai ta gyaɗa sannan ta fice kai tsaye kichen ta nufa.

Tana shiga tasa ruwa kadan atukunya yanda zai wadatar mata bayan ya tafasa ta ɗan zuba mai kana ta
zuba Couscous kamar minti goma ta buɗe taga ya dahu yayi sar gwanin kyau, amfanin ɗiga man kenan.

Sauƙewa tayi sannan ta buɗe fridge ta ɗauko miyan stwe da yaji naman kaza ta ɗumama sai kuma ta
dauko lunch box din Raudat, Ramadan da Haiydar da kuma nata ta zuba musu, sai kuma ta koma ɗaki
tashiga toilet tayi wanka Agurguje ta fito ɗaure da towel mai ɗan girma sannan ta cirewa Raudat kayanta
tayi mata wanka bayan sun fito tashafa mata mai kana ta sanya mata Uniform sannan itama ta shirya
cikin Uniform da yayi matukar amsar jikinta hannu Raudat taja suka fita dai-dai lokacin da Haiydar suka
fito da Ramadan cikin shiri ko wannensu ya nufi inda lunch box ɗin da yake ya ɗauka kana suka fice
harabar gidan suka shiga mota.

Kamar ko yaushe motar na parking Khausar ta fito riƙe da hannun Raudat,

Sai da ta kaita ajinsu sannan cikin sauri ta juya ta kama hanyar koma ajinsu daga baya taji ankira sunan
ta da faɗin.

“Lelewal ke kullum sai kowa ya riga ki shiga cikin aji ko?”.

Ahankali ta juya tare da sauƙe manyan Idanunta akan Malam Isa dake tsayi murmushi tayi da faɗin.

“Ba haka bane Malam na tsaya kai Raudat ajinsu ne shiyasa”.

Kai ya gyaɗa still Idanunsa akanta hakanan yarinyar ke burgesa ahankali yace.

“To ki tafi kar araba musu questions paper ba kyanan”.

Kai ta gyaɗa tare da juyawa cikin sassarfa da sanin darajar kanta take tafiya har ta isa cikin ajin.

Aɓangaren Amina kuwa koda M Jameel yashiga class da niyyar raba musu questions paper ƙasa tayi da
kanta ta amsa batare data kalli fuskarsa ba domin koda gaishesa ne ta dena tunda ta lura da baya buƙata
kallon fuskanta, to shima M Jameel Sosai yaji daɗi da yarinyar ta daina gaishesa, dan ko kaɗan baya
ƙaunar kallon fuskarta, bare kuma wata magana ta haɗa su.
Acan gida kuwa tun bayan tafiyar su Khausar Makaranta cikin Mommy ya tsananta da ciwo da ƙyar ta
yunƙura ta miƙe tana mai rintse Idanunta jini taga yana bin ƙafafunta da sauri ta dafe cikinta da ƙyar ta
iya furta.

“Ya Allah wannan ciwon cikin kuma na menene?”.

Da ƙyar taja ƙafanta zuwa jikin beside drawer ta ɗaga wayarta tare da kiran number Hajiya Bunayya,
kafin ya katse Hajiya Bunayya tayi picking tare da Sallama.

Mommy kuwa cikin azaban ciwon da cikinta ke mata ta rintse Idanunta kana tace.

“Yaya”.

Da sauri Hajiya Bunayya ta katseta da faɗin.

“Ƙanwata lafiya naji muryanki haka?”.

cike da yarda ta rintse Idanunta cikin yanayin azaban ciwon da cikinta keyi tace.

“Wallahi Yaya cikina ciwo yake tun daren jiya, haka na kwana banyi bacci ba yanzu kuma gashi jini ya
ɓalle min!

Dan Allah ki faɗawa Alhj mutafi asibiti”.

Hajiya Bunayya kuwa da damuwa amuryanta tace.

“Subhanallahi! bari na faɗa masa yanzu ma kuwa”.

Sannan ta katse wayar ta nufi ɗakin Lamiɗo ranta fari Sol burinta ya cika abakin ƙofa suka haɗu yana
shirin fita.

A take ta wani marairaice fuska kana cikin yanayin damuwa tace.

“Yanzu Mommyn Khausar ta kirani.

Wai jiya da ciwon ciki ta kwana yanzu kuma jini ya ɓalle mata”.

Ai bai ma gama sauraron abinda zata faɗa ba ya ratsa ta ya wuce sashen Mommy cike da damuwa.

Hajiya Bunayya kuwa da harara tabi bayansa kafin taja siririn tsaki ta mara masa baya.

Tana shiga Bedroom ɗin ta samu Lamiɗo tsugunne akan Mommy da sauri ta tsugunna daga gefensa ta
riƙo hannun Mommy.
Cike da tausayawa kamar za tayi kuka tace.

“Sannu Aysha ciwon ciki amma baki yi magana ba, gashi har ya tsananta jini na zuba”.

Ta ida maganar zufa na karyo mata wanda in kagani zakayi zaton na tsananin damuwa ce, nan kuwa na
tsananin farin cikin burinta ya cika ne.

Lamiɗo kuwa miƙewa yayi tare da naɗe hannun rigarsa zai ɗauke ta Ganin haka ne yasa Hajiya Bunayya
tayi saurin miƙewa tare da tallafo Mommy jikinta suka fita,

agidan baya suka zauna Lamiɗo kuma ya shiga gefen mai zaman banza Driver yaja suka tafi Hajiya
Bunayya sai faman sannu take yiwa Mommy.

Suna isa asibitin aka karɓe su kai tsaye emergency aka nufa da ita ganin cikin ya riga ya zube yasa likitoci
suka nufi wani ɗaki da ita tare da yi mata wankin ciki kana suka yi mata allurai nanda nan bacci wahala
ya ɗauke ta Lamiɗo kuwa kasa Matsawa daga kusa da ita yayi ya cike da kulawa ya zauna a bakin gadon
tare da riƙe tafin hannunta cike da tausayinta.

Hajiya Bunayya data shaƙa ta cika kuwa.

Wani lalataccen harara ta watsawa ƙeyansa cikin ranta tace, tabbas sai tayi wani abu akan wannan
rawan jikin da yake mata.

A zahiri kuwa dafa kafaɗar sa tayi, ahankali ya ɗago kansa ya kalleta da idanunsa dake cike da damuwa
amma baice komai ba.

Cike da kirsa ta ƙirƙiri murmushin da bai kai zuciba kana tace.

“Dan Allah ka rage damuwar nan, babu yanda zamuyi da ƙaddara haka Ubangiji ya tsara wannan ɗin ma
ba rabo bane, ayanzu addu'ar lafiya take da buƙata awajenmu”.

A hankali ya sauƙe nannuyar Ajiyar zuciya tare da mayar da Kallonsa ga Mommy dake bacci tamkar babu
abinda ke damunta.

Lumshe idanunsa yayi yace.

“Ina matuƙar tausayawa Aysha tun bayan haihuwar Haiydar take fama da wannan matsalar sannan ko
wanne cikin sai ya wahalar da ita kafin ya fita”.

Da sauri Hajiya Bunayya ta katsesa da faɗin.


“Ya zamuyi da rubutacciyar ƙaddara, ai kaga da Ubangiji yaga dama ai cikin Raudat da Ramadan ya
zauna”.

Kai ya jinjina amma baice komai ba.

Ita kuwa cikin ɓoye farin cikinta ta sauƙe ajiyar zuciya da faɗin.

“Zan koma gida kafin ‘yan makaranta su dawo, naga lokaci yaja amma Insha Allah anjima zan dawo”.

Kai ya gyaɗa ba tare da yace komai ba still Idanunsa na kan Mommy.

Hajiya Bunayya kuwa ficewa tayi ranta fari fess kana tasa Driver ya maida ta.

Acan Makarantar su Khausar kuwa koda suka gama Exam ba abasu damar tafiya ba bayan sunyi sallar
la'asar suka shiga haddar Alkur'ani sai ƙarfe biyar aka tashe su, kana suka shigo mota suka nufi gida,
motar na parking Raudat ta fice da gudu ta nufi sashen su

Tana shiga falo ta fara kiran.

“Mommy! Mommy!! na mun dawo”.

Jin shiru yasa ta nufi Bedroom ɗinta da gudu ta buɗe ta shiga tana kiran.

“Mommy!, Mommy!!, Ina kika shiga”.

Still Bata ganta ba da gudu ta juya ta fito falon dai-dai lokacin Khausar kuma ta shigo ƙara sawa kusa da
Khausar tayi ta riƙe hannunta kana tace.

“Addah Khausy Ina Mommy?”.

Kallonta Khausar tayi kafin tace.

“Bata ɗaki ne?”.

Kai Raudat ta gyaɗa mata alamar Eh,

Sake hannunta Khausar tayi kana ta nufi kichen ta buɗe wayam tagani alamar bata nan komawa tayi ta
shiga Bedroom din ta ɓude still ba tanan jikin toilet ta nufa ta manna kunnenta ajiki tare da faɗin.

“Mommy Mommy kina ciki kuwa?”.

Jin shiru yasa ta tura ƙofar toilet din still bata nan fitowa tsakiyar falon Khausar tayi tare dasa hannun
damanta ta riƙe ƙugunta tana tunanin ina Mommy ta shiga haka, bayan tasan bata fiye fitar yamma ba
kuma koda zata fita tun safe kafin su tafi makaranta zata faɗa musu bare kuma yau da suka barta bata
jin daɗi.
Da sauri ta kalli Raudat sai kuma tace.

“Jirani anan ina zuwa”.

ta faɗa tare da ficewa kai tsaye sashen Hajiya Bunayya ta nufa bakinta ɗauke da sallama tana faɗin.

“Ummah”.

Shigar ta yayi dai-dai da lokacin da Hajiya Bunayya ke riƙe da waya tana cewa.

“Kedai Hajiya Lami bari buƙata ɗaya ta biya saura ɗaya, tana can kwance a asibiti cikin ya zube yabi
makwarari, saura ɗayan daman jira nake inga ya zata kaya ne ki shirya jibi zamu koma”.

Komai Hajiya Lami ta faɗa ohon musu, ita dai Hajiya Bunayya cikin jin dadi ta kece da wata
mahaukaciyar dariya mai nuni da tsantsar farin ciki.

Lokaci ɗaya kuma dariyar nata ya tsaya ganin Khausar tsaye, sai kuma ta katse kiran tare da kallon
Khausar.

Kafin tace wani abu Khausar tayi saurin cewa.

“Ummah ina Mommy mu?”.

Hajiya Bunayya ta wani langwaɓar da kai kana tace.

“Ayyah Khausar am Mommy ku tana asibiti bata da lafiya wallahi cikinta ya zube”.

Da sauri Khausar da kanta ke ƙasa ta ɗago ta kalli Hajiya Bunayya tana sake maimaita kalmar cikinta ya
zube akasan ranta lokacin ɗaya hawaye masu zafin gaske suka cika kwarmin Idanunta.

Sai kuma tayi saurin maida hawayen ta kafin tace.

“Shikenan ɓuƙatar magauta tabiya hankali ya kwanta. Allah ya raya mata wa anda ta haifa. Ubangiji ya
tsaresu daga sharrin mai sharrin”.

Ta ida maganar tana ƙoƙarin fita.

Da sauri Hajiya Bunayya tace.

“Ke Khausar zo nan Me kike nufi?”.


Anutse Khausar ta juya tare da sauƙe manyan Idanunta da suka sauya launi zuwa ja ta zubawa Hajiya
Bunayya kana tace.

“A'a Ummah babu abinda nake nufi, kawai dai addu'a ce nayi”.

Cikin tsuke fuska Hajiya Bunayya ta watsa mata Harara da faɗin.

“Sannan su waye ne Magautan?”.

Ware hannu Khausar tayi tare da faɗin.

“Nikam ban sansu ba, amma dai nasan Allah Mabuwayi gagara Misali ya sansu kuma zaiyi maganin su,
domin ai bahaushe yace rana dubu ta ɓarawo rana ɗaya ta mai kaya, suji tsoron ranan da Ubangiji zai
musu kamun talala!”.

Cike da Mamaki Hajiya Bunayya tace.

“Wai Khausar me kike magana kamar habaici kike min ko kuma hannunka mai sanda!?.”

Ware ido Khausar tayi tace.

“Haba Ummah in Miki habaici kuma ayanda kike ƙaunar Mommyn mu kinfi ƙarfin habaici ko hannunka
mai sanda kin wuce haka sai dai mgnar ce tazo kamar zaurance”.

Ɓoyeyyen Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta saki domin tayi zaton yarinyar ta gano lagonta ne.

Khausar kuwa murmushi tayi tare da faɗin.

“Bari na tafi asibitin kar dare yayi”.

Da sauri Hajiya Bunayya ta gyara zamanta Idanunta akan Khausar tace.

“Toh kibari in ƙara sa abinci mana sai ki tafi dashi”.

Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.

“Toh amma bari na shiga gidan Aunty Ruƙayya kafin ki ƙarasa”.

Kai Hajia Bunayya ta gyaɗa tare da faɗin.

“Toh ki gaisheta”.
Kai kawai Khausar ta gyaɗa Sannan ta wuce sashen su.

Tana shiga Bedroom direct toilet ta wuce ta cire Uniform ɗin ta sannan ta watsa ruwa bayan ta fito ta
dauki dogon rigar material pinch colour ta sanya, kana ta nufi kichen Agurguje ta dafawa su Haiydar
jollof ɗin shin kafa da yaji bushesh-shen kifi da kayan ƙamshi nan da nan kichen ɗin ya ɗauki ƙamshi
Warmers ta ɗauka ta juye sannan ta tafasa musu tea kana ta ɗura musushi, sannan ta fita falon dai-dai
lokacin da Haiydar ya shigo.

Kallonsa Khausar tayi tare da kiran sunansa tace.

“Haiydar”.

Ya amsa da.

“Na'am”.

Cikin sanyi tayi ƙasa da muryanta tare da faɗin.

“Dan Allah Haiydar ka kwana anan kai da Ramadan, Raudat kuma zamu tafi da ita asibiti sai mu kwana
da Mommy”.

Kai ya gyaɗa mata sai kuma yace.

“Nima ai inaso naje na dubata”.

Jinjina kai Khausar tayi tace.

“Ba damuwa kazo mutafi dukan mu amma yanzu zan fara shiga gidan Aunty Ruƙayya in sanar mata, idan
yaso kai da Ramadan ku taho tare da Ummah,

In yaso sai ku dawo tare amma kubar min Raudat dan zamu kwana tare”.

“Toh shikenan Allah ya bata lafiya”.

“Ameen”,

Tace kana ta juya ta tafi har ta kusa fita ta sake juyawa ta kalli Haiydar dake tsaye Ahankali tace.
“Dan Allah Haiydar ka kula, bakomai za'a baka kaci ba, akwai abinci na dafa muku sannan duk wani abu
da zaku buƙata akwai”.

Da sauri ya dafe kansa tare da faɗin.

“Ke dai jeki da rashin yardan ki kedai haka Allah ya halicce ki baki da yarda”.

Cikin sanyi ta girgiza kai kana tace.

“Shikenan ni dai ban san sai yaushe zaku yarda dani ba”.

Ta ida maganar tare da ficewa”.

Kai tsaye gidan Aunty Ruƙayya ta nufa.

Tare da Sallama tashiga Babban falon da yaji kayan alfarma kujerun set biyu aciki Black and Ash sai
kuma babban tv plasma dake Manne abango daga ƙasansa kuma horm teater ne ƙasan falon kuma
shimfiɗe yake da chanis capet.

Aunty Ruƙayya dake bedroom ta fito fuskarta ɗauke da murmushi tace.

“Khausar kece sannu da zuwa, shigo ciki”.

Da sauri tace.

“A'a Aunty sauri nakeyi ai”.

Cikin kulawa tace.

“Yo yasu Mommy ki?”.

Murmushi Khausar tayi tace.

“Wallahi Aunty Ruƙayya Mommy ce ke asibiti bata da lafiya, shine nace bari nazo na faɗa miki, Ni yanzu
ma zan wuce ko za muje tare?”.

Cike da tausayawa Aunty Ruƙayya tace.

“Ayyah Allah ya bata lafiya zanje bari ina zuwa mu tafi tare”.

Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.


“Toh”.

Aunty Ruƙayya kuwa bedroom ta shiga tare kiran mijinta a waya, bayan ya bata izinine, ta ɗauko key
mota da mayafinta suka fita,

suka shiga mota,

jingina kai Khausar tayi da jikin motar kalaman Hajiya Bunayya nayi mata suwwa akunne.

Juyawa Aunty Ruƙayya tayi ganin yanda Khausar ta zurfafa cikin tunani yasa tace.

“Ki riƙa yi mata addu'a”.

Kai kawai Khausar ta iya gyaɗa mata.

Cikin Mintuna kaɗan suka isa Asibitin bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga ɗakin da aka kwantar da
Mommy saboda Hajiya Bunayya ta faɗa mata.

Kwance akan gado suka tarar da ita yayin da Lamiɗo ke gefenta akan kujera hannunsa riƙe da kofin tea
yana miƙa mata da faɗin.

“Ki tashi kisha”.

Yana jin Sallamar Khausar ya juya yana kallonta har ta isa kusa dashi.

Cike da kulawa yace.

“Khausar har kun dawo?”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Eh Abba ya jikin Mommy!?”.

Sai da ya ɗan kalli Mommy dake jingine da pillow sai kuma ya mayar da Kallonsa kan Khausar yace.

“Da sauƙi”.

Sai asannan ya lura da Hajiya Rukayya ya ɗan yi murmushi da faɗin.

“Hajiya Ruƙayya sannu da zuwa”.

Zama tayi akujeran dake kusa da ita tana cewa.

“Yawwa ya Hajiya Aysha da jikin kuma?”.

Ɗan Murmushi yayi kana yace.


“Da sauƙi”.

Tana kallon Mommy tace.

“Ubangiji Allah ya ƙara sauki”.

Ya amsa da.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.

Khausar kuwa bakin gadon ta ƙarasa ta riƙe hannun Mommy acikin nata.

Cikin raunin murya tare da tausayawa mahaifiyar tata tace.

“Sannu Mommy ya Jikin?”.

Lumshe idanu Mommy tayi kana ta buɗe su a hankali tace.

“Da sauƙi Khausar bana jin komai in dan ta nice ma, da su sallame ni in koma gida mu kwana tare, dan
bana jin ciwon cikin yayi sauƙi babu inda yake min ciwo!”.

Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da faɗin.

“Masha Allah Mommy Allah yaƙara sauƙi Ubangiji ya ƙara tsarewa ya kare”.

A ranta kuwa cewa tace.

Ayyah da ace duk addu'o'in da takeyiwa Mommynta tun randa taci ferfesun da ace tana haɗa addu'ar da
yaron cikin wata ƙil da bai zube ba.

Shafa kanta Mommy tayi cike da ƙaunar ta tace.

“Ameen Khausar ki kwantar da hankalin ki ba najin Komai”.

Ta faɗi hakan ganin yanda Khausar tayi zuru-zuru da ita.

Hajiya Ruƙayyance ta kalli Mommy kana tace.

“Hajiya Aysha ya ƙarfin jikin!?”

Murmushi Mommy tayi kana tace.


“Dasauƙi Hajiya Ruƙayya ya ‘Yar taki ya kuma rigima a makaranta!?".

Kallon Khausar Hajiya Ruƙayya tayi kana tace.

“A'a yanzu ai ta daina ta fara girma!”.

Jin haka yasa Khausar tayi murmushi.

Lamiɗo kuwa miƙewa yayi idanunsa akan Mommy yace.

“Toh shikenan bari na tafi dama ganin babu kowa ne yasa nake zaune bari na samu naje nayi wanka dan
tunda muka zo ban samu na koma gida ba”.

Hajiya Ruƙayya tace.

“Ayyah ai babu komai Alhaji kaje”.

Jinjina kai Mommy tayi tace.

“Allah ya tsare”.

Ya Amsa da.

“Ameen”sannan ya juya ya fice.

Tafiyar Lamiɗo babu daɗewa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka zo Raudat na riƙe da hannunta.

Suna shiga Hajiya Bunayya ta zauna daga gefen gadon tare da kallon Mommy tace.

“Sannu ƙanwata ya ƙarfin jikin?”.

Murmushi Mommy tayi kana tace.

“Ai naji sauki Yaya”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi cikin yanayin tausayawa tace.

“Allah ya baki lafiya”.

Hajiya Ruƙayya kuwa kallo ɗaya tayi wa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami taji sam basu kwanta mata arai
ba musanman ma Hajiya Bunayya dake wani shish-shugewa Mommy.

Ta dai daure tace.


“Sannunku da zuwa”.

Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka haɗa baki wajen cewa.

“Yawwa ya mai jikin”.

Ataƙaice Hajiya Ruƙayya tace.

“Da sauƙi”.

Hajiya Lami kuwa jikin gadon ta matasa Idanunta akan Mommy tace.

“Ayyah Sannu Hajiya Aysha Ashe ga abinda ya faru kuma? Amma wannan abu yayi yawa ai gwara Alhj
yayi ƙoƙari ya fitar dake waje wannan matsalar ko yaushe da ansamu ciki ya zube ai babu daɗi!”.

Kafin Mommy tayi magana Hajiya Bunayya tayi saurin cewa.

“Kede bari Hajiya Lami abin nan yana damun mu, gaba ɗaya mun kasa gane menene ainihin matsalar,
amma hankalinmu na tashi kullum cikin yanayin nan, abin babu daɗi yanzu ciki takwas kenan yana
zubewa abin ai babu daɗi!”.

Taɓe baki Khausar da Hajiya Rukayya sukayi alokaci ɗaya.

Ahankali Mommy ta gyara matashin data kishingiɗa akai kana tace.

“Uyummm ya za'ayi da abinda Allah ya tsara, amma ni inaga nin ba wani matsala bane, tun da gashi na
haihu bayan haihuwar Haiydar ma haka nata fama da ɓare-ɓaren nan, kuma daga baya da Allah ya kawo
Ramadan da Raudat an haifesu ba komai ai”.

Cike da kirsa Hajiya Bunayya tayi yaƙe kana tace.

“Hakane kam, toh Allah ya kawo masu albarka”.

Hajiya Lami kuwa harara ta gallawa Mommy tare da taɓe baki aranta tace shegiya me iyayin jaraba keda
haihuwa sai dai kiga anayi.

Idanun Hajiya Ruƙayya da Khausar na kan Hajiya Lami alokacin data taɓe baki ta harari Mommy,

Juyawa Hajiya Ruƙayya tayi ta kalli Khausar tare da jinjina kai itama Khausar kai ta jinjina.
Miƙewa Hajiya Ruƙayya tayi tare da kallon Mommy tace.

“Toh Hajiya Aysha Ubangiji Allah ya ƙara sauki sannan Allah ya tsareki daga sharrin abin ƙi ni zan wuce!”.

A hankali Mommy ta ɗan yunƙura tare da lumshe Idanunta kana tace.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum Hajiya Ruƙayya Nagode”.

Hajiya Lami da Hajiya Bunayya kuwa baki suka saki suna kallon Hajiya Ruƙayya da Mamaki aransu suka
ce kaji shegiyar mata da iyayi uban wa takewa wannan addu'ar.

Miƙewa Raudat tayi tare da riƙe hannun Hajiya Ruƙayya tace.

“Aunty Ruƙayya ni zan biki gidanki, Inje in kwana dasu Salman tun da gobe babu makarata”.

Da sauri Khausar ta kalli Raudat dake riƙe da hannun Aunty Ruƙayya tace.

“Ayyah Raudat am baza mu kwana ba?”.

Girgiza kai Raudat tayi tare da langwaɓar da kai kana tace.

“ Ni dai Ina tsoro ni bazan zauna ba”.

Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.

“Shikenan kibi Aunty Ruƙayya”.

Murmushi Aunty Ruƙayya tayi tare da jan hannun Khausar dake cikin nata

Har sun kai ƙofa Hajiya Bunayya ta ƙirƙiri murmushi tana kallon bayan Raudat tace.

“Oohhh Raudat ba zaki bini mu tafi gida ba?”.

Kafaɗa Raudat ta maƙale tace.

“A'a ni zanbi Aunty Ruƙayya”.

Aunyty Ruƙayya kuwa jan hannun Raudat tayi suka fice batare data sake jiran jin Abinda Hajiya Bunayya
zata ceba.

Bayan tafiyar Aunty Ruƙayya babu da ɗewa Hajiya Bunayya ta miƙe tare da kallon Mommy tace.
“Toh ƙanwata zamu wuce Allah yaƙara sauƙi”.

Murmushi Mommy tayi da faɗin.

“Nagode Yaya ahuta gajiya”.

Hajiya Lami tace.

“Babu Gajiya”.

Sannan suka fice Khausar kuwa jinginar da kai tayi kamar mai bacci.

Da daddare Khausar ta miƙe daga kan dogon kujeran asibitin da take kwance ta dubi Mommy da bacci ya
fara fisgarta tace.

“Mommy”.

Buɗe idanu Mommy tayi tare da kallon Khausar tace.

“Na'am Khausar ya akayi?”.

Ajiyar zuciya Khausar ta saki tana wasa da yatsun hannunta tace.

“Mommy baki zargi perpesoup ɗin nan da kika ci azubewar cikin nan ba!?”.

Sosai Mommy ta tsira mata ido na second uku zuwa biyar sai kuma ta miƙe daga kwanciyar da take
Atake fara'ar dake fuskanta ya gushe cikin ɗaure fuska cikin kakkausan Murya tace.

“Khausar!, Khausar!!, Khausar!!!, Ki cigaba Nagode da abinda kike min Khausar, duk irin tarbiyyan da
nake baki fatali kike dashi ko, kina ɗaukar rashin yarda kina ɗaurawa mutane ki sani Manzon Allah
(S.A.W) Yace.

:Azzana zambu walau kana haƙƙun”.

Khausar kuwa ƙasa da kai tayi hawaye masu zafi suka cika Idanunta shin sai yaushe mahaifiyarta zata
amince da gaskiyar da take so ta sani akan Hajiya Bunayya basa ƙaunarta cutar da ita suke sonyi.

Cikin sanyi murya tare da rauni gami da ban haƙuri tace.

“Shikenan Mommy kiyi haƙuri Allah ya huci zuciyarki”.

Mommy bata tanka taba ta juya ta gyara kwanciyar, ta itama Khausar juyawa tayi ta kwanta zuciyarta
babu daɗi.
Washe gari Alhamis Da safe Dr ya shiga ya basu sallama dan jikinta yayi sauƙi Sosai Lamiɗo da kansa yaje
ya maido su gida.

Suna dawowa Hajiya Bunayya ta shigo hannunta riƙe da babban Warmers da tayi Perpesoup ɗin Kaji ta
shigo dashi.

Zama tayi akan 2sitter tace.

“Sannu ƙanwata ya ƙarfin jikin?”.

Mommy tayi yar dariya tare da faɗin.

“Jiki yayi sauƙi Yaya sai faman hidima kike dani kamar wacce tayi haihuwar farko?”.

Dariya Hajiya Bunayya tayi da faɗin.

“Ai mai ɓari yafi son akula dashi fiye da mai haihuwa”.

Khausar dake tsaye duk takaici ya gama cikita gashi babu dama ta faɗawa mahaifiyarta gaskiya sai ta hau
kanta da faɗa bayan da ta iya daga ƙarshe ma Saboda takaici kawai sai ta koma Bedroom ɗin ta ta fara
karatu.

Wunin ranan haka Hajiya Bunayya ta yini tare da Mommy ta cigaba da kulawa da ita.

Washe gari juma'a dai-dai lokacin da maza suka tafi Juma'a dai-dai lokacin da kowa ya tafi Sallar juma'a
Akuma lokacin ne Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka tafi gidan Boka Kar'uzu.

Khausar da Mommy ne zaune suna hira sosai jikin Mommy yayi ƙarfi abinka da mai juriya ga kuma
kulawa da take samu.

Sallamar Aunty Ruƙayya ya katse musu hirar da suke.

Khausar ta faɗaɗa fara'ar fuskarta kana tace.

“Aunty Ruƙayya sannu da zuwa ina Affan?”.

Murmushi Aunty Ruƙayya tayi tana zama tace.

“Affan yana lafiya bacci ma yake ya mai jikin”.

Khausar tace.

“Jiki da sauƙi”.
Aunty Ruƙayya tace.

“Masha Allah Ubangiji ya ƙara sauki”.

Cikin sakin fuska Mommy ta gyara zaman hular dake kanta tace.

“Hajiya Ruƙayya sannu da zuwa ya gajiyarki?”.

“Hajiya Ruƙayya tayi murmushi da faɗin.

“Babu gajiya ya jikin naki?”.

“Jiki yayi sauƙi ya yara?”.

Alhamdulillah ta bata amsa.

Khausar kuwa miƙewa tayi cikin neman izinin tace.

“Ayyah Mommy zanje gidan su Asma'u?”.

Ido Mommy ta zuma mata, na tsawon second bakwai tana kallonta kana tace.

“Toh yayi kyau”.

Khausar kuwa juyawa tayi ta shiga Bedroom Dogon rigar dake jikinta ta cire tare da ɗaura towel tashiga
toilet,

shawer ta ɓude ta sakarwa kanta ruwan ɗumi,

ta ɗauki kusan minti shabiyar kafin ta fito ɗaure da towel da tsawon sa bai wuce gwiwar taba yayin da
ƙarami ke kanta tana tsane ruwan kanta.

Stool ta janyo ta zaune tare da goge ruwan jikinta ta ɗauki Vassiline lotion ta shafa kana ta ɗauki powder
ta shafe sai kuma Kajol ta zizara a idanunta mascara ta ɗauka ta taje gashin Idonta da sukayi tsayi tamkar
tasa Eyelashes golb mai sheƙi ta ɗauka ta shafa asaman pinch lips ɗin ta sai yayi kamar jan baki ta shafa
kallon fuskarta tayi a mirrow sosai tayi kyau.

Miƙewa tayi ta nufi jikin durowar ta buɗe uban kayan dake ciki ta zubawa ido ahankali Idanunta suka
sauka akan wani Less Coffee da aka masa adon cycle da rastin Milk colour ta janyo ta sanya Masha Allah
Sosai ɗinkin less ɗin ya mata kyau tare da fitar da shape din jikinta skirt ɗin ya zaune ɗass ajikinta tare da
fitar mata da tsarerrenn ƙugunta haka ma rigar ta zauna ɗass ajikinta ɗan kwalin ta ɗauka tayi ɗauri mai
kyau sai kuma ta ɗauki glaye medium size milk color kana ta feshe jikinta da turarukanta masu daɗin
ƙamshi.

Falon ta fita tun kan ta isa Aunty Ruƙayya ta ɗago kanta tare da tsira mata Idanunta jin ƙamshin daya
ratsa hancinta ta saki murmushi kana tace.

“Iyeee Masha Allah Khausar irin wannan kyau sai kace preety ta ƙasar India”.

Hannu Khausar ta sanya ta rufe fuskarta tana dariya sai kuma ta buɗe tace.

“Kai Aunty Ruƙayya Ina Zan samu koda rabin kyawunta ne?”.

Ware ido Aunty Ruƙayya tayi kana tace.

“Allah kuna kama dan da zakije India ma cewa za'ayi ke ƙanwarta ce, har rawan kanki ma irin natane a
Film ɗin Chori-Chori Cubke-Cubke ne”.

Mommy Kam murmushi take musu batare da tace komai ba.

Khausar kuwa Murmushin jin daɗi tayi tare da tsugunnawa ta ɗauki wayar Mommy tace.

“Mommy zan tafi da wayarki".

Kai kawai Mommy ta gyaɗa mata sannan ta ɗauƙi wayar tare da faɗin.

“Na tafi”.

ta ida maganar tana gyara zaman Handbag din Hannunta tare da ciro earpiece aciki

Suka haɗa baki wajen faɗin.

“Adawo lafiya".

Kai ta jinjina tare da ficewa,

Abokin gate ta haɗu da Haiydar riƙe da MP ɗin sa, cikin sauri tace.

“Yauwa Haiydar dan Allah aramin MP ɗinka”.

Cike da mamaki ya zuba mata ido tare da cewa.

“Yau kuma to ke kuma da ba jin kiɗa ya dameki ba, me zakiyi dashi?”.

Kai ta ɗan jinjina tare da cewa.

“Wallahi yau dai shauƙi nakeji zanje wurin Asma'u mu ɗan rausaya”.
Murmushi yayi yana mamakin wai yau Khausar ce da cewa zata sha ƙiɗa, kawai miƙa mata yayi. Tare da
cewa.

“Kuma kikasa gyale ko?”.

Cikin daɗi tace.

“Ngd kai rabani kullum mutum liƙe da hijabi kamar maitakaba” na mgnar tana fita ta tari adaidaita sahu
ta shiga.

Acan ɓangaren Moddibo kuwa bayan an idar da Sallah juma'a ya kalli M Jameel dake Driving yace.

“J yakamaya muje mu gaida Ummi kafin mu koma gida!”.

Kai ya Jinjina kana yace.

“Dama abinda nake son faɗa kenan ka rigani”.

Gyara zama Moddibo yayi tare da lumshe idanunsa yana sauraron ƙira'ar dake tashi amotar kana ya
shafa sajensa yace.

“Muje toh”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare da juya akalar motar zuwa unguwar su Ummi.

Suna cikin tafiya wayar M Jameel ya hau ruri yana duba screen ɗin wayar yaga Bahrain ba suna sai
Number Dariya M Jameel yayi still hankalinsa nakan Driving din yace.

“Jalaludden! Wallahi Jalaludeen!! nayi mana abinda ransa keso”.

Moddibo da Idanunsa ke lumshe yayi ɗan guntun Murmushi ba tare daya buɗe idanun ba yace.

“Toh ka ɗaga mana kar ya yanke”.

Picking M Jameel yayi tare da Sallama.

Amsawa Jalaludeen yayi da faɗin.

“Idan kun isa ku gaishe da Ummi”.

M Jameel yayi Murmushi kana yace.

“Kana biye da mu ne?”.


“A'a bana biye daku na dai rigaku zuwa na gaisheta”.

Cewar Jalaluddeen

Dariya M Jameel yayi sai kuma ya zare ido yace.

“Wallahi Jalaludeen kada ka razana mana tsohuwa!”.

Murmushi Jalaludeen yayi yace.

“A'a bazata ra zanata ba sannan ba zata tsorata ba ai mun taɓa zuwa tare daku baku dai sani bane kuma
na bayyana mata ta ganni”.

“Wallahi Jalaludeen ka kiyaye mufa”.

Dariya Jalaludeen yayi kana yace.

“Tare dai mukayi sallama jumma'a a sahu daya.

Yanzu kuma Na dai hango ku ahanya zakuje yanzu ina katakon nan?”.

Da sauri M Jameel yace.

“Wani katakon?”.

Cike da tsokana Jalaludeen yace.

“Katakon dake gefenka”.

Murmushi M Jameel yayi tare da kallon Moddibo yace.

“A.J ɗin nawa ne katako?”.

“Eh inba katako ba shi menene? ka faɗa masa cewa akwai furen dake ƙoƙarin tsiro a jikinsa tun daga
ƙasa har ya isa zuciya ya gab da kanshi tuni ma ya ratsa zuciyarsa amma bai sani ba”.

Murmushi M Jameel yayi tare da kallon Moddibo da still Idanunsa ke lumshe kamar mai bacci kana
yace.

“Wai yace in faɗa maka akwai furen da zai fito tsakiyar kanka yama ratsa zuciyarka”.
Sai asannan Moddibo ya buɗe idanunsa ya kalli M Jameel tare da faɗin.

“Ka ganni karabu dani da kalaman Jalaludeen, shiya sani can yaje yata faman maganganunsa da baza ka
gane kansu ba bare gindinsu ya riƙa yi mana maganar damu mutane zamu gane ba sai wanda sai sune
masu ganewa ba”.

Dariya Jalaludeen yayi yace.

“Zaka gane ne ai lokaci ne yana zuwa”.

Dariya M Jameel yayi tare da hong aƙofar gidan Ummi ganin shiru ba'a buɗe masu bane yasa, M Jameel
fitowa ya buɗe, kana ya dawo yaja motar still kafaɗarsa saƙale da wayar

Jalaludeen ne yace.

“Ku gaishe da Ummi idan kun shiga”.

Sannan ya katse wayar kana shi kuma ya kutsa kai cikin gidan.

Dai-dai lokacin da a dai-dai-ta ya ajiye Khausar kudinsa ta basa tare da buɗe ƙaramin ƙofar dake maƙale
da gate ɗin tashiga,

Batama lura da babban gete ɗin dake ɗan buɗe ba,

ganin mota a fake a harabar gidan yasa ta isa wajen kasancewar glass ɗin tink-tenk ne yasa bata fahimci
da mutane aciki ba rawar kanta kuma ya hanata fahimtar alamun yanzu motar ta tsaya.

Jikin gefen mai zaman banza ta nufi tare da kallon fuskarta ajikin mirrow sai kuma ta juya manyan
Idanunta kalaman Aunty Ruƙayya suka dawo mata kunne tana kama da Preety matsa pinch lips ɗin ta
tayi tare da lasa kadan sai kuma ta juya manyan Idanunta.

M Jameel kuwa dake mazaunin Driver murmushi ya saki domin ya tabbata bata san da mutane aciki ba.

Acan ɓangaren su Hajiya Bunayya kuwa zaune suke gaban boka Kar'uzu cikin tsananin ɓacin rai da fushi
Boka Kar'uzu ya buga musu wata razananniyar tsawa cikin sautin muryarsa mara daɗin sauti

bayan ya gama sauraron Hajiya Bunayya yace.


“Ai seda na faɗa muku aduk lokacin data fara aiki da maganin kada tayi alwala da sallah na tsawon wata
ɗaya amma saboda taurin kai kuka bari tayi alwala tayi sallah shiyasa yake kallon fuskar ta kamar na
ƙonennen Biri”.

Atsorace Hajiya Bunayya ta juya ta kalli Hajiya Lami da itama ɗin Iran take kallo.

Sun kasa hafimtar sharrin boka na wasa da hankali da ƙarya sun kasa tuna sam bai faɗa musu hakanba a
lokacin, su kasa aminta mgnar boka dubune babu gsky ko ɗaya sai yaudara da taɓewa.

Acan ɓangaren su Moddibo kuwa sake kallon madubi Khausar tayi tare dasa hannu ta gyara man lips ɗin
ta sai kuma danna MP ɗin cikin Sa'a kuwa sautin waƙar BUGA ya fara tashi.

A hankali ta gyara tsayuwar ta, tare da fara jujjuya ƙugunta a hankali tana mai rausaya jikinta.

Zuwa tsakiyar waƙar kam fa da abu ya jiƙa, sai ga mayafinta bisa kafaɗarta gefe ɗaya, sosai take jujjuya
mazaunenta tare da motsa dukkan jikinta, tana mai kallon kanta a madubi.

Sai kuma ta kalli Glass ɗin tare da ɗaura bakinta akai ta saki zazzafan kiss muahhhh.

Shi kuwa Moddibo dake zaune idanu ya zuba mata tare da manna kumatunsa adai-dai glass ɗin sai kuma
hakan yasa lips ɗinta sauƙa kan....!

FREE page sun kusa ƙarewa 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA ki biya 1k dinki ya isheki

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_Page 12_

_NA_

*AYSHA ALIYU GARKUWA*


🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine wannan Free page ne ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci 1k ne kacal
0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276
saura shafi huɗune kacal ana biyar na gama Free page*

Da sauri Modibbo ya rintse idanunsa, tare da shafa sajensa domin, badan glass dake tsakani ba da akan
tattausan sajensa sumbatar zata sauƙa.

Shi kuwa M Jameel cikin sauri ya lumshe idanunsa tare da gyara zamansa yana fuskantar ta da kyau.

Ita kuwa Khausar hannu tasa tare da gyara zaman ɗaurin ɗan kwalinta, sai kuma ta canza Baitin da take ji
zuwa.

Waƙar Lamba tana marming tamkar zabia kai kace itace ta raira waƙar, bin baitukan takeyi tana jujjuya
manyan idanunta, tana mai girgiza jikinta zuwa ƙugunta.

lumshe manyan Idanunta kumayi tare da fitar da sautin zazzaƙar muryanta a fili ta tace.

“Kai zan yiwa kalamaina.

Kai zan baiwa muƙamai na. Ungo makullaina ka riƙe.

Ta ida bautin tare da nuna saitin fuskar Moddibo da yar yatsarta ma nuniya.

Wani irin shu'umin murmushi M Jameel ya sake tare da sa hannunsa ya riƙon hannun Moddibo da ya
yunƙura zai ɓalle karfin motar.

Ita kuwa Khausar, cikin azama taci gaba da bin waƙar cike da zazzafan shauƙi tace.

“Ni ban furta da wasa ba, samari dukka basu kai ba, kana nan banganin kowa da ido, dan basu isheni
kalloba”.

Tayi mgnar bisa alamu daga ainihin cikin ranta take bin waƙar, M Jameel kam murmushi yakeyi cike da
shauƙi.
Modibbo kuwa ya cika yayi fam dan har ransa yakeji yarinyar ta tarainashi gani yake kai tsaye ma dashi
takeyi, gashi kuwa M Jameel ya riƙe masa hannunsa ƙam-ƙam.

Ita kuwa Khausar mazari uwar rawa, ƙugunta da ƙirjinta take motsawa a slowly tana mai ci gaba da
cewa.

“Kai zaka zauna adamana, kuma ka bani gurin kwana, wannan shine fassarar mafarkin da nake kullum
cikin baccina”.

Wani irin yar-yar Moddibo yaji tsikar jikinsa na tashi domin suna jinta ras kasan cewar Glass ɗin bayan
motar a suna ƙasa kaɗan.

Ita kuwa Khausar

ida baitin tayi tana mai nuna Moddibo dake kwance jikin kujeran Idanunsa alumshe da yatsan hannunta
tana murmushin dake ƙarawa fuskarta kyau.

Shi kuwa Moddibo Cikin fushi ya fuzge hannunsa daga riƙon da M Jameel yayi masa tare da sanya
tattauaan tafin hannunsa da niyyan buɗe motar.

Shi kuwa M Jameel cikin sauri ya riƙe tafukan hannunsa da ƙarfi tare da girgiza masa kai alamar ya bari
suga iya gudun ruwanta.

Ƙwafa Moddibo yayi tare da jingina bayansa da jikin kujeran ya cigaba da kallonta.

Ita kuwa rawanta ta cigaba dayi tana Girgiza jikinta ganin abin nata ba mai ƙare wa bane yasa Moddibo
buɗe motar cike da tsananin fusata.

Kamar walƙiya ko wanda ya diro daga sama haka taga Moddibo a gabanta,

Cikin tsoro, mamaki, da kiɗima kalli fuskarsa cikin zare ido ta tayi ƙasa da kanta,

domin bata tsammaci da mutum aciki ba.

Shikuwa Moddibo cikin nutsuwarsa da kuma kamala ya fito daga motar tare da tsaida idanunsa akanta
yana mai ƙara tsananta suƙe fuskarta da ya ƙara razanata.
Ita kuwa cikin tsananin ruɗu da tashin hankali mara misaltuwa ta ɗaura hannunta akai.

tare da zubewa akan gwiwoyinta tana mai girgiza kanta gaba ɗaya ta gaza cewa komai.

M Jameel kuwa gefen Driver ya buɗe tare da fitowa yana dariya mai sassayan sauti,

dai-dai lokacin da Ummi da Asma'u suka fito daga cikin gidan zuwa harabar gidan.

Idanu Ummi ne suka sauƙa akan Moddibo da M Jameel kafin kuma ta maida ganinta kan Khausar dake
durƙushe ta kama kai da hannunta duka biyu,

cike da mamaki asaman fuskarta Ummu tace.

“A'a ikon Allah Khausar lafiya ya dai haka!?”.

Kasa cewa komai Khausar tayi, still hannunta na kanta haka zalika ta kasa ɗago kanta banda bugawa da
ƙarfi babu abinda zuciyarta keyi da ƙarfi.

Ganin Ummi da tambayar da take yiwa Khausar yasa Moddibo basarwa kamar baisan da ruwan ɗigon
Khausar dake tsugunne gabansa ba,

cike da nutsuwa da kuma takun ƙasaita ya janye ƙafarsa da ya ɗaga da niyar zaiyi wasan ƙollo da Khausar
ɗin yana mai maida fushinsa ya haɗiye ya juya ya nufi gaban Ummi.

Murmushi Ummi tayi Idanunta akan Moddibo tace.

“Sannun ku da zuwa Babana, dama yanzu nake shirin zuwa unguwa zanje duba jikin Maman Khausar”.

Ta ida mgnar ta maida kallonta kan Khausar da har zuwa yanzu take durƙushe sai dib dab dib dab da
sautin zuciyarta ke badawa, cikin kula tace.

“A'a Khausar yaushe kika zo? ya jikin Mommyn ki?”

Ita dai Khausar bata ɗago ba bare kuma ta motsa, gani take aduk lokacin da tayi kuskuren ɗaga kanta
Moddibo zai iya kifeta da azabebben marinsan nan mai sa mutum ganin taurari masu wutsiya.

Cikin kula Ummi ta juya ta kalli Moddibo dake tsaye hannunsa na acikin aljihu murmushi tayi kana tace.

“Allah yayi zaku zo ku sameni, kuzo mushiga daga ciki”.

Kai suka jinjina tare da wuceta, ita kuwa Ummi juyawa tayi zuwa gaban Khausar ɗan tsugunna tayi tare
da riƙo hannun Khausar tace.
“Duk cikin gaishe da Malama ne har haka Khausar? to taso mu tafi”.

Sai asannan Khausar ta ɗago kanta tare da sakin wani nan-nauyan ajiyar zuciya, ganin Moddibo bai nan
cikin mutuwar jiki tabi Ummi falon.

Suna shiga Khausar tayi saurin janye hannunta daga cikin na Ummi, kana ta kama na Asma'u suka nufi
Bedroom ɗinta”.

Suna shiga Bedroom ɗin Khausar ta janye hannunta daga na Asma'u ta zauna agefen gadon Idanunta
cike da ruwan hawaye ta dafe ƙirjinta tare da cewa.

“Asma'u nashiga ukuna!nikam yau naga ta kaina, Allah yana jarabtana ta hanyar haɗani da Moddibo a
bauɗaɗɗen yanayi,

zuwa na kenan naji wata waƙa tamin daɗi na tsaya ina bi uwa zabiya.

Kuma kin sanima fa ni ban fiye jin waƙa ba, sannan bai dameni ba amma kawai ɗazu naji wata waƙa MP
din Haiydar Wai ita Buga da Lamba kuma wallahi nasan Haiydar ne ya haxa min da bai bani aron MP
ɗinsa ba ai da banjita ba bare inji yamin daɗi, kawai na kama rawa tamkar yar gala,

ashe Moddibo na kallona nikam bansan irin hukuncin da zai minba gobe amakaranta, ƙilan ma ya sake
sakani kaɗe ɗan kwali nikam nashiga Ukuna! Laifi kan laifi gashi gyale na yafa ga uban turaren dana
zumbuɗa ga rawa dajin waƙa Wayyo ni Batula Faɗimatuzzahara naga ta kaina!”.

Ta gumi Asma'u tayi tare da kallon, Khausar da tayi narai-narai da ido kana tace.

“Ke kam dai Khausar kamar saɓani Allah yake haɗaki dashi”.

Narai-narai tayi da ido tare da dafe kuncinta da hannun biyu kana tace.

“Mummunan saɓani ma kuwa, na sharri ma ya Allah kashiga tsakanin na gari da mugu, Allah kara bani
dashi ya Allah kada ka bashi ikon zalunta na, tun da dai arashin sani nayi kuma babu wanda yafi ƙarfin
kuskure ai seya min uzuri ko?”.

Janye mata tagumin Asma'u tayi tana dariya tace.

“Kece Khausar wani zubin sai ahankali, kawai daga zuwa saiki hau rawa kamar mazari da anyi magana ki
wani ce Allah yashiga tsakanin na gari da mugu sannan da kike maganar uzuri a'a ba'asi za amiki ba uzuri
ba kuma waye mugun waye na garin”.
Sheƙeƙe Khausar ta ɗago kai tare da tsirawa Asma'u Idanu kana tace.

“Nifa na lura dake tun ba yanzu ba, kinfi ƙaunar Moddibo dani wato har kina goyon bayan sa akan ni kin
zaɓe sa kin barni? Yoh shine mugu mana ni ta gari”.

Ware idanu Asma'u tayi tare da langwaɓar da kai tana dariya tace.

“Haba ƙawar arziƙi matsayinki yafi haka, dan Allah kada ki sake faɗan hakan aise kisa ayimina dariya”.

Taɓe baki Khausar tayi tare da faɗin.

“Kinsan gwara in gane matsayina ai tun wurima,

idan kinfi ƙaunar Moddibo insan matsayina”.

Dariya mai sauti Asma'u tayi da faɗin.

“Maida wuƙar ranki shi daɗe Fattanah”.

Murmushi Khausar tayi tare da kishingiɗa akan gadon.

Acan falo kuwa bayan Moddibo da M Jameel sun sake gaisawa da Ummi ta miƙe tashiga kichen ba
daɗewa ta fito hannunta riƙe da babban tray dake ɗauke da Warmers ta ajiye musu.

Murmushi Moddibo yayi yace.

“Sannu da gajiya Ummi”.

Murmushi tayi tace.

“Yawwa Babana”.

M Jameel kuwa miƙewa yayi yashiga kichen ya dauko musu Plate da cups guda biyu kana ya dawo ya
zauna.

Kulan ya buɗe, da sauri ya gyara zamansa jin wani ƙamshi mai daɗin ya ratsa hancinsu.

M Jameel ya lumshe ido tare da zuba musu akan Plate.

Moddibo ya matso tare da tsirawa Pride rice ɗin da yaji vegetables da naman kaza amsar spoon ɗin da M
Jameel ke miƙa masa yayi, cikin fesar da numfashi Moddibo ya ɗibi abincin ya kai bakinsa, lokaci ɗaya
yaji daɗi ya mamaye masa baki, kallon Ummi yayi tare da faɗin.

“Ummi wannan girkin yayi daɗi”.


murmushi tayi tare da tsiyaya musu tea mai ɗumi.

Bayan sun gama ci.

M Jameel ya goge bakinsa da tissue kana yace.

“Ummi ɗazun ina zakije dama?”.

Tana matsar da Flaks ɗin tea tace.

“Wallahi Maman Khausar zanje dubawa, bata da lafiya shekaran jiya a asibiti suka kwana jiya ne aka
sallame su da safe”.

Girgiza kai yayu kana yace.

“Ayyah Subhanallah Allah yabata lafiya Allah yasa zakkan jikine”.

Amin Ummu tace.

Yayinda shi kuwa Moddibo Aransa yace. “Uhhhm yarinyar kamar aljana ita da mahaifiyar ta babu lafiya
har ankwantar da ita a asibiti jiya-jiya aka sallame su, amma yau har ta gararo yawo, har tana rawa
agidan mutane kamar wacce aka yiwa bushara da Aljanna, ita kuwa wannan daɗin me takeji”. sai kuma
ya taɓe baki takaicin halayyar yarinya yasa bece musu komai amaganar ba.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da faɗin.

“Toh Ummi mu zamu tafi”.

Ummi ta juya ta kallesa da murmushi afuskarta tace.

“Da wuri haka Babana?”.

M Jameel ne yace.

“Ai dama a gaggauce muka zo Ummi, dan kwana biyun nan naga ya maida hankalinsa akan rubutun da
yake inagama ya kusan gamawa”.

Ummi kuwa kallonta ta mayar kan Moddibo kana tace.

“Masha Allah Ubangiji Allah ya taimaka, ya kuma baku sa'a ka kusa gama wa kenan?”.

Cike da nitsuwa Moddibo ya amsa da.


“Ameen”,Kana yace.

“Eh Ummi na kusa gamawa, amma waɗan da na tura ƙasar Ɓadamaya ma tukunna wanda na turawa,
Sheykh Jabeer ya duba min su har yau basu dawo ba, to inaso kawai na haɗa wa'annan ma dake wancan
bugun Hafs ne wannan kuma Warash ne”.

Yai da mgnar tare sauƙe numfashi kana ya cigaba da cewa.

Warash ne nake rubuta wa to inaso idan nagama rubuta wannan ɗin na tura masa, wala Allah ya tuna
mishi da duba wancan ɗin.

Nasani abubuwa ne suka masa yawa da yake ya wanci yakin arewacin nan duk wanda ya rubuta Kur'ani
shi ya ake turawa sai ya duba yagani toh zanyi ƙoƙari na gama rubuta wannan ɗin sai ahaɗa akai gaba
ɗaya ko zan samu ya haɗa min su lokaci ɗaya idan ya duba ingancin su”.

Jinjina kai Ummu tayi cike da yabawa jajurcewarsa da kuma ƙoƙarin sa tace.

“Masha Allah Allah yatemaka Allah ya bada sa'a abu yayi kyau Allah yabar mana irinku Moddibo Allah
yayi jagora”.

Moddibo kuwa cikin jin daɗin addu'ar ta yace.

“Ameen Ummi Allah ya amsa Nagode”.

Miƙewa M Jameel yayi idanunsa akan Ummin sa yace.

“Ummi zamu tafi”.

Tana ƙoƙarin kwashe Plate da sukayi amfani dashi tace.

“Toh Nagode Allah ya muku albarka”.

Suka haɗa baki wajen faɗin.

“Ameen”.

kana suka fice.

Bayan sun ɗauki hanya M Jameel ya dubi Moddibo wanda shike Driving ɗin yanzu yace.

“Ni ka sauƙe ni agida”.

Moddibo da still hankalin sa ke kan Driving yace.


“Ba zamu tafi tare ba?”.

Girgiza kai M Jameel yayi kana yace.

“A'a nasan rubuta zaka je kayi sannan Abba ya kirani akan batun yana so naje Ɓadamaye batun
Company sa akwai sabbin Injina da aka kawo, za'a saka kaga na daɗe ban jeba, amma wannan karon ko
naje baze wuce kwana biyu zanyi in dawo ba”.

Moddibo kuwa jinjina kai yayi kana yace.

“Toh yaushene tafiyar?”.

Kai M Jameel ya Girgiza tare da faɗin.

“Toh dai ban sani ba tukun”.

Moddibo dake ƙoƙarin shan kwana yace.

“Yawwa zanyi ƙoƙari inga na gama rubutunan idan zaka tafi sai ka tafi min dashi”.

Shi kuwa M Jameel Kai ya gyaɗa cike da gamsuwa da maganarsa yace.

“Toh shikenan hakan ma yayi Allah yatemaka”.

Moddibo ya amsa da.

“Ameen”,tare da parking motar bayan ya isa ƙofar gidan su M Jameel.

Sauƙa M Jameel yayi tare da yi masa sai anjima, kai Moddibo ya gyaɗa kana yaja motar ya tafi.

Yana isa gida bayan yayi Parking motarsa ya wuce Bedroom ɗinsa kasancewar yana da alwala yasa ya
ɗauko abubuwan buƙatar sa na rubun Alkur'ani da yakeyu kana yaciigaba da rubutu, saida aka kira sallar
La'asar sannan ya tashi yaje masallaci ya gabatar da sallan la'asar, bayan ya dawo kuma, yazo ya cigaba
da rubutun, yana yi yana karantar Suratul Kahfi kasancewar yammacin jumma'a ne, sai misalin ƙarfe
biyar kafin ya ajiye Kur'ani.

Acan ɓangaren Innayi kuwa zaune take akan kujera ’yar tsugunno acikin kichen tana juya miyar zogala
wanda yaji namar Rago da kuma wadataccen man Shanu da wake yana tashin ƙamshi bayan ta sauƙe
miyar ta ɗaura Ruwan shayi daya ji na'ana, kaninfari da kuma ɗanyan citta yana tafasowa yana ƙamashi
mai daɗin shaka.
Flaks guda biyu ta ɗauka ta juye sannan ta ɗauki ɗaya ta nufi sashen Moddibo dashi.

Acan gidansu Asma'u kuwa bayan tafiyar Moddibo da M Jameel Khausar ta miƙe tare da fitowa falon
Idanunta akan Ummi tace.

“Toh Ummi mu tafi ba dama kince gidan mu zaki jeba”.

Jinjina kai Ummi tayi tace.

“Eh Khausar inaso naje na duba jikin Mommyn ki”.

Ba tare data zauna ba tace.

“Toh Ummi mu tafi”.

Kai Ummi ta jinjina kana ta miƙe suka fita su ukun Bashir ƙanin Asma'u ne kaɗai suka bari agida Ummi da
kanta take Driving Khausar da Asma'u na baya suna hira.

Acan ɓangaren su Hajiya Bunayya kuwa Kallonsu Boka Kar'uzu yayi cikin wata razananniyar tsawa yace.

“Wannan maganin ya riga daya ɓaci, ta lalata komai yanzu sai anyi aikin dai-dai-ta fuskarta ma tukunna
kafin azo ayi aikin jawo hankalinsa, yaran nan biyu da kuka gani kuke magana akansu yarane dasu na
tsaye da sunan Allah da riƙo da Ibada, musamman ma Moddibo da kuke magana akansa kwata-kwata
baya rabuwa da alwala ajikinsa ka masa zaiyi wuya”.

Cikin tashin hankali Hajiya Bunayya ta juya ta kalli Hajiya Lami da duk tagama shiga ruɗu.

Boka Kar'uzu kuwa cigaba yayi da cewa.

“Yanzu sai munyi aikin wata uku kafin fuskarta ya dawo dai-dai sannan sai tabar Sallah na tsawon
watanni shida kafin mu samu mu fara aiki shiko aikin za'ayi na tsawon watanni shida kafin ta fara nuna
masa muradanta”.

Kana ya maida kallonsa ga Hajiya Lami data zabga uban tagumin tana kallon sa cikin Muryansa Mara
daɗin Amo yace.

“Kema naki hakanne sai tayi wannan watannin”.

Dafe ƙirji Hajiya Lami tayi tare da zare Ido kana tace.

“Har Watanni shida shida Boka kafin wannan lokacin fa har sun kusa gama Ss 2 ma zasu tafi 3 awannan
lokacin daka ɗiba mana”.
Cikin tsawa da hargagi yace.

“Dole sai anbi wannan ƙa'ida idan ba haka ba babu abinda zaku samu ya tafi dai-dai!”.

Ta gumi Hajiya Lami ta rafka kana tace.

“Shikenan Babu damuwa Indai burinmu zai cika tunda ai makarantar basu gama ba zamu bi ahankali”.

Ya yamutse fuska tare da watsa musu wani kallo da jajayen Idanunsa cikin wata murya mara daɗin Amo
yace.

“Ƙa'idah ne yanzu zata je tayi ta aiki da wannan maganin na tsawon watanni ukku fuskarta zai koma dai-
dai a Idanunsa sannan bayan wannan kuma tsawon watanni kar kuyi sallah daga nan kuma zan fara haɗa
magani na tsawon watanni shida kafin su tun kare su daga magana”.

Murmushin Hajiya Bunayya tayi tare da gyara zamanta tana fuskantar Boka Kar'uzu da kyau tace.

“Toh shikenan ba matsala.

Amma fa ciki ya zube aiki yayi kyau!”.

Wani irin mahaukaciyar dariya mai matuƙar razanarwa Boka Kar'uzu ya saki da faɗin.

“Ai dama dole aiki zaiyi kyau idan kun bishi da ƙa'ida wannan ma ku kuka je kuka ɓatashi!”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.

“Godiya muke Boka ana gaba zamu kiyaye”.

Kai ta gyaɗa kana yace.

“Toh ya batun aikin toshe mahaifar!?”.

Kai Hajiya Bunayya ta Girgiza tare da faɗin.

“Boka muga ma da batun aikin Amina tukunna, kaga ga yayar ta ma tana zaune ba tayi aure ba, sannan
ga itama Aminan ta girma shiru, amma ita kace rabonta ne yayi nisa abin ya ɗaure mana kai mun rasa
yanda zamuyi har wajen ƙan wata na tura ta Aƙasar Khautal ko zata samu rabonta acan amma acan ɗin
ma shiru kuma kaga ta dade da gama karatu amma har yau Auren bai samu ba zamu jona mata wani
makarantar ta fara zuwa jami'a kawai, tunda itama kanta Amina dan wasa da karatun take da tayi
shekaru biyu da gamawa amman sai aikin maimaita aji gashi har shegiyar yarinyar nan ta kusan
cimmata”.
Kai Boka Kar'uzu ya ɗago daga bugun ƙasar da yake tare da cewa.

“Babu matsala ita Aseeya rabonta yana nan tafe”.

Cike da jin daɗi Hajiya Bunayya tace.

“Godiya muke Boka Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye Hatsabibi Uban
Hatsabibai!”.

Wata mahaukaciyar dariya Boka Kar'uzu ya kece dashi cikin jin daɗin kirarin da ta masa yace.

“Aikin ki zai tabbata ƙaramar la'ananniya Aljani ɗan ƙundalu mai ido Atsakiyar kai zai cika miki burinki ku
fita da ƙafar hagu ta baya!”.

Miƙewa sukayi suka fice kamar yanda ya faɗa ransu fesss suna tsalle da kafar hagu kamar kutaren
agwagi...

Acan ɓangaren su Ummi kuwa bayan sun isa gidan su Khausar sun gama gaisawa da Mommy da kuma
Hajiya Ruƙayya da har zuwa lokacin suke tare.

Mommy tana murmushin tace.

“Ummi ya fama rigimar Khausar, ɗazun nan tace zata je ta duba ki ashe kina hanya”.

Dariya Ummi tayi tace.

“Ai lalle dai kam Hajiya Aysha babu ruwan Khausar ai”.

Murmushi Mommy tayi tace.

“Kina dai karate ta Amma Khausar ba dai rigima ba?".

Aunty Ruƙayya tayi Dariya kana tace.

“Ai Khausar bata da rigima ita dai baza'ayi gulma agaban Idanunta bane, sannan ba za'a cakake ta ta
haƙura ba, kunga kuwa ai da gaskiyar ta”.

Dariya Ummi tayi tace.

“Aikam de lalle da gaskiyar ta”.


Ita kuwa Mommy Dariya tayi kana suka cigaba da hira.

Washe gari Asabar suka koma makaranta Khausar kuwa cikin tsoro da fargaban abinda Moddibo zai
mata ta zuciyarta ya riƙa bugawa da ƙarfi lokacin da yashigo raba musu questions pepar tayi zaton zai
mata hukunci sai taga baima kalli inda take ba.

Shikuwa Moddibo kawai ya fita sabgarta ne ganin alamar bata da cikikakkiyar nutsuwa in ya biyata zata
zarar dashi.

Akwana atashi haka al'amura suka cigaba da tafiya komai yana wakana Moddibo ya kammala rubutun
Kur'aninsa ya bawa M Jameel ya tafi wa da Sheykh Jabeer Habibullah Nuruddeen Joɗa na Adamawa.

Satin M Jameel biyu ya dawo tare da shedawa Moddibo ya karɓa harma ya fara dubuwa Insha Allah nan
kusa zai turo masa.

Karatun su Khausar na tafiya komai na tafiya dai-dai yanda ake buƙata Anyi gasar musabaƙa jihar Taraba
Makarantarsu Khausar Al'ansar Academic school_ shine yazo na farko Khausar ce tazo na ɗaya a haddar
Izu arba'in yayin da Asma'u tazo na biyu Aishatu Abdullahi tazo na uku ,A haddar Izu biyar Raudat ce tazo
na ɗaya kyaututtuka masu yawa suka samu kana suka dawo cike da nasarori.

Yanzu karatu na tafiya akwana atashi babu wuya wasa gaske yanzu Khausar suna Ss2

thirth term suna shirye shiryen fara Exam gashi kuma Ramadan ya kawo kai yayin da ake ta shirye
shiryen shiga Ramadan tuni Gwamnatin Jaha ta rarraba malamai zuwa inda ko wanne zaiyi Tafseer
kamar yanda aka saba Moddibo da M Jameel antura su Babban Masallacin juma'a dake ƙofar sarki
Gembu anan zasuyi Tafseer ɗin su na Ramadan.

Lokaci natafiya karatun su Khausar na sake tafiya yanda ake buƙata tsakanin Amina da Khausar babu
wani jituwa hasalima gaba ce domin har gobe M Jameel na sake nuna kulawa ta musamman akan
Khausar yayinda Moddibo kuwa kwata-kwata baya lura da al'amuran Khausar hasalima idan tayi laifi zai
yanke mata hukunci fiye dana kowa wannan dalili yasa basa shiri kana babu wata jituwa atsakaninsu.

Alhamdulillah ayaune Khausar suka rubuta exam na ƙarshe kuma da Geography suka rufe.

Taro Moddibo yasa aka haɗa kamar yanda aka saba a kowani ƙarshen hutu ko baki ɗaya Malaman sun
haɗu awajen zamansu haka ma ɗalibai Khausar da Asma'u na zaune awaje ɗaya.
Shi kuwa Moddibo cikin nutsuwarsa da kuma kamala ya nufo wajen as usual cikin shigar sa kaman ko
yaushe sanye yake cikin Jallabiya fari kansa naɗe da hirami idanunsa sanye da ɗan siririn farin glass daya
ƙawata kyawun fuskarsa yalwataccen sajensa zuwa gemunsa ya kwanta luf-luf yana sheƙi.

Cikin tsantsar nutsuwa da sanin darajar kansa ya gyara zaman microphone ɗin tare da hura iska kaɗan
kana yayi gyaran murya yace.

_“Bismillahir Rahmanir Rahim, Innalhamdulillah nahmaduhu wanasta'inuhu wanastaghfiru


wa'nazubillahi min shururi anfusna wamin sayyi ati a'amalina, man yahdillahu fala mudillahlah waman
yudlil fala hadiyala, Wa'ash hadu Allah ilahalillahu, Wa'ash hadu anna Muhammadu Abduhu wa
Rasulullah (S.A.W)”._

Sai kuma ya ɗan lumshe idanunsa tare da sauƙe Ajiyar zuciya kana ya cigaba da cewa.

“Duk kan yabo da godiya su tabbata ga Allah subhanahu wata'ala mai kowa mai komai, da yakawo mu
wannan lokaci da muke shirin karɓan hutu saboda gabatowan wannan wata mai falala, haƙiƙa watan
Ramadan wata ne mai falala da rahma wanda duk kan musulmi yake da burin ganinsa.

Baki ɗaya wajen shiru yayi kowa ya maida nutsuwarsa zuwa garesa yayin da Samira kejin aduk lokacin
data mallakesa babu macen da takaita sa'a a faɗin wannan duniya tamu ta bani adam.

Malam Arɗo kuwa Aransa yake jin Moddibo ne Garkuwa kuma ginshiƙin makarantarsa.

Moddibo kuwa cikin yanayin sanyin Muryar sa mai cike da nutsuwa ya cigaba da cewa.

“An abu Huraira ta radiyallahu anhu,

_Manƙama Ramada Imanan Wahtisaban gufra lahu mata ƙaddama min zambi muttafaƙun Alaik”_

Ma'ana ankarbo daga Abu Huraira Allah ya ƙara masa yarda, yana cewa Duk wanda watan Ramadana ya
kama yana mai Imani da kyautatawa ana kankare masa zunubansa da suka gabata”.

Ya sauƙe sanyayyar Ajiyar zuciya mai sanyi kana ya cigaba cewa.

“Wannan kaɗai zai iya nuna maka muhimmanci da kuma darajar wannan wata hakika wannan watar ba
wata bane na wasa watane daya kamata mu tsaya mu miƙa lamuranmu ga Ubangiji Mabuwayi gagara
Misali, sannan mukasance masu yawan Karatun Alkur'ani, Istigfari, hailala da kuma tasbihi, ba sai na
tsawaita ba ko naja duk abinda zance kun sani”.

Sai kuma ya maida kallonsa ga sauran Malaman yace.


“Koda akwai mai magana?”.

Duk suka girgiza kai alamar babu Moddibo kuwa M Jameel ya miƙawa microphone ɗin kana ya koma ya
zauna shi kuwa M Jameel bayanai ya ƙara akan na Moddibo kana ya sanar dasu Bayan Sallah da sati ɗaya
zasu dawo.

Yana gama Maganar ya juya tare da kallon Khausar da ita adai-dai lokacin Idanunta na kasansa cikin
Sanyayyar Murya yace.

“Lelewal zoki rufe mana da addu'a!”.

Anutse Khausar ta gyaɗa kai tare da miƙewa.

Shikuwa Moddibo kallon mamaki yabin M Jameel dashi amma baice komai ba.

Amina kuwa jitayi tamkar zuciyarta zai buga saboda baƙin ciki da kishi.

Ita kuwa Khausar cike da tsoron Modibbo dake sa ta nemo nutsuwa ta amshi microphone ɗin cikin
zazzaƙan Muryanta tayi addu'a kana aka tashi kowa ya watse dalibai nata murnan hutu kowa ya koma
gidansu cike da farin ciki.

Da daddare Khausar na zaune akan 1sitter hannunta riƙe da wayar Mommy yayin da Mommy kekan
3sitter ta miƙe ƙafafunta Hannunta riƙe da kofin tea.

Anutse Mommy ta ɗago kanta tare da sauƙe Idanunta dake kan Khausar Wacce baki ɗaya hankalinta ke
kan wayar da take dannawa ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.

“Khausar tunda an baku hutu ko dai za kije Jauro Yaya kuyi azumi tare".

Da sauri Khausar ta ajiye wayarta tare dasa hannu ta dafe ƙirjinta tace.

“Nashiga Ukuna! Dan Allah dan darajar Annabi Mommy Kar kiyi Wannan maganar, kibar tsohuwar nan
tunda dai bata ne maba”.

Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.

“Toh shikenan yanzu azumi saura sati amma nasan zaiyi wuya acikin satin nan idan bata neme kiba”.

Marerece fuska Khausar tayi kana tace.

“Allah yasa karma ta nemeni duk da garin yamin daɗi Mommy amma inaso in tayaki aiki”.

Murmushi Mommy tayi kana tace.


“Toh shikenan ba matsala hakan ma Allah ya zaɓa Mana abinda yafi zama alkhairi”.

Acan ɓangaren su Hajiya Lami kuwa zaune take afalon Hajiya Bunayya tare da Samira Sani da kuma
Amina.

Kallon Hajiya Lami Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Yanzu dai saura mana watanni biyu mu gama cika Umarnin Boka Kar'uzu na watanni shida daya ɗiba
mana kada muyi Sallah, kafin na ƙarshe da zamuyi muje mu karɓi maganin su zo suyi aiki dashi”.

Murmushi Hajiya Lami tayi tare da jinjina kai tace.

“Eh haka ne bayan Sallah da sati Uku zamu gama”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.

“Gashi kuma azumi ya gabato amma acikin wannan azumin ma ace ba zamuyi sallah ba kuma watan
falala da ibada!?”.

Wani kallo Hajiya Lami tayi mata kana tace.

“Idan ke zakiyi sallah ki ɓata aikin da kikayi to kinyi na wancan watannin shida da kika samo fuskar ’yar ki
ya dawo dai-dai a idanunsa, sannan yanzu wata ɗaya da rabi daya rage ne zaki ɓata ba zaki iya jira ba.
Agaskiya nikam zan cika ƙa'idata domin in samu cikar burin ‘yata”.

Samira kuwa zama ta gyara tana fuskantar Hajiya Bunayya da kyau tace.

“Agaskiya Ummah kar muyi wasa da wannan damar da muka samu idan yaso idan muka gama sai mu
rama bashin sallah dake kan mu!”.

Ita kuwa Amina Kallon mahaifiyarta tayi tare da ƙanƙance Idanu kana tace.

“Yanzu ke Ummah wasa zakiyi da wannan damar da muka sha wahala tsawon watanni muna yi!?”.

Zare ido Hajiya Bunayya tayi tare da nuna kanta da yatsa tace.

“Ina waya faɗa miki ko an faɗa miki daɗi nake ji ga yayarki azaune gaki kuma kema azaune”.

Ta ida maganar dai-dai lokacin da Asiya ta fito daga Bedroom bayan ta gama sauraron duk abinda suke
faɗa zama tayi akan 1 sitter dake fuskantar Hajiya Bunayya cikin sanyin murya tace.
“Gaskiya Ummah!, Gaskiya Ummah!! Kada neman duniya yasa mu rasa ƙiyama tare da rahamar Ubangiji,
Ummah sallah da arayuwar duniya itace farkon abinda za'a bin ciki mutum dashi aranan gobe hisabi idan
tayi kyau abin cika sauran abubuwa idan kuma ba tayi kyauba, baza ma aje ga sauran abubuwan ba”.

Tayi ƙasa da Idanunta ganin shegen kallonda Umman take bin ta dashi bata damu ba ta cigaba da cewa.

“Ummah aduniya Allah ya Umarceki da kiyi sallah da Azumi amma Boka La'anannen yace kada kiyi,
sannan ki biye masa har ki yarda sannan ki riƙa ɗaura ‘yarki akan gurɓatacciyar hanya nikam wannan
al'amari yana tayar min da hankali, wannan al'amarin sam bai yi ba yanzu dama akan wannan turban
kuke tafiya?”.

Ta saki Ajiyar zuciya tare da gyara zamanta kana tana ƙoƙarin maida hawayen dake ƙoƙarin zubo mata
cikin dauriya ta cigaba da cewa.

“Shiyasa tun da na dawo sati biyu banga kinyi alwala ko Sallah ba?, Ni nayi zaton ma al'ada kike yi,Itama
Amina naga bata sallah dana tambayeta saita kama yimin rashin kunya”.

Amina dake jifanta da mugun hararane tayi saurin katseta tare da cewa.

“Anyi miki rashin kunyar keda ba kyabin Ƙa'ida da Umarnin Bokan baga ki har yanzu baki auru ba!sai
shegen iyayi da kwainane!”.

Asiya da Idanunta suka ciko da ruwan hawaye ta kalli ƙanwar nata cike da mamaki sai kuma tayi
murmushi mai ciwo tace.

“Wannan Allah ne bai nufaba, idan Allah ya saƙƙo da lokaci zanyi shi domin Aure da mutuwa lokacine”.

Atsawace Hajiya Bunayya tace.

“Rufe min baki, keda ma can ba'a haɗa shiri dake ya tafi dai-dai, dama ke da magautana kike tare kina
nan kamar wancan matar ce ta haifeki”.

Asiya ta danne kukan dake neman kufce mata tace.

“Ba haka bane Ummah zanso mu gudu tare mu tsira tare ne, bazan so ganin ku cikin halaka ba Umma
kuyi tunani akan wannan rayuwar da kuka jefa kanku".

Hajiya Lami kuwa cikin fushi tace.


“Wannan dai akwai gantalelliyar yarinya shegiya mai shegen mugun halin jaraba, duk yanda akayi
wancan gafalalliyar kishiyar Uwar taki ta baki nononta kinsha”.

Kallonsu kawai Asiya keyi cike da mamaki.

Hajiya Bunayya kuwa Afusace tace.

“Bana son gaskiyar taki ki riƙe abarki.

ki gudu ke kaɗai mu ma mu gudu mu kaɗai kiga wanda zai riga isa tsakanin mu da ke”.

Cikin tsananin tashin hankali Asiya tace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n.

Allahumma Ajirni fi musibati wa'ahlif khairan minha”.

Ta ida addu'ar tare da miƙewa ta shiga Bedroom ɗin su akan gado ta faɗa tare da dafe kanta tace
wannan wani irin Masifa ce Ummah ta jefa kanta.

Acan falo kuwa Ummah suka cigaba da tattaunawa tare da tsaida matsaya akan idan sun kammala aiki
zasu biya Sallolin da ake binsu.

Washe gari.

Da hantsi misalin 12:00 Khausar na kwance A Bedroom kamar daga sama tajiyo Sallamar Hajja Nana da
sauri ta miƙe tare da zama Atsakiyar gadon ta kasa kunnenta dan tabbatar wa shin ita ɗin ce ko kuwa.

Aikuwa Muryan Mommyn ta taji tana cewa.

“A'a Hajjar Allah Maraba sannu da zuwa Allah raine Jaɓɓama,Jaɓɓama Yottu,yottu”.

Ita kuwa Khausar wani irin zare ido tayi sai kuma ta miƙe da sauri ta fito abakin Bedroom din ta tsaya
Idanunta akan Hajja Nana da Dije dake tsaye agefenta.

Jan zuciya Khausar tayi tare da tsaida idanunta akan Hajja Nana tace.

“Kece?”.

Harara Hajja Nana ta watsa mata da faɗin.


“Toh ki koreni wato ba kyason ganina!?”.

Tura baki Khausar tayi tace.

“A'a".

Sai kuma ta juya tare da kallon Dije dake tsaye tana kallon falon da dugu ta nufi Dije tana cewa.

“Oyoyoo Dije nayi kewarki ya gida ya Goggo Nanne?,Ya Yaya Abba?,Ina Sadik?, Yasu Baffa Jauro?, Baffa
Sadu?,Baffa Liman?, Baffa Garga? Ina Bishiyar Ƙare zencen ka ina Rafi?”.

Murmushi Dije tayi kana tace.

“Duk suna lafiya kuma sunce agaisheki da kyau da kyau”.

Tayi murmushi tace.

“Allah sarki nima nayi kewarsu sosai”.

Cikin sakin fuska Mommy ta fito daga kichen hannunta riƙe da Flaks da kuma kofi biyu ajiyew tayi, kana
ta koma ta ɗauko fruits duk ta ajiye agaban Hajja Nana data hakimce akan kujera sannan ta zauna still
fuskarta da Murmushin daya kasa ɓoyuwa tace.

“Sannu Hajja kunsha hanya ya mutanen gida?”

Ta ida maganar tana tsiyaya mata Tea a kofi.

Amsa Hajja Nana tayi ta kai bakinta.

Mommy kuwa miƙewa tayi ta shiga kichen dan haɗa mata abinci.

Hajja Nana kuwa juyawa tayi tare da kallon Khausar dake maƙale da Dije kana tace.

“Wato ba zaki gaisheni ba, Dije ce kikayi farin cikin ganinta ni bakiyi farin ciki da ganina bako!?”.

Ya mutse fuska Khausar tayi tace.

“Tun ɗazu nake ta gaisheki kina fama da ciye-ciye baki jini ba”.

Sake baki Hajja Nana tayi tare da riƙe haɓa sai kuma tace.

“Ubanki nake baciye-ciye ba”


Hannu Khausar ta buɗe da faɗin.

“Ɗanki kika zaga dama kin barsa ya kwanta cikin kabarinsa acikin salama da yafi”.

Ta ida mgnar idonta na ciko da hawaye dan Allah ya sani bata son a zagar mata mahaifi.

Hajja Nana ta ajiye Kofin shayin dake hannunta ta nuna Khausar da hannu tace.

“Ki kiyaye nifa,Ki kiyayeni fa Khausar”.

Tura baki Khausar tayi kana tace.

“To ai gaskiya na faɗa”.

Ita kuwa Hajja Nana na ɗaukar kofin shayinta tace.

“To ya miki kyau koma mene ki ƙarata can, yanzu kishirya ki haɗa kayanki tare zamu tafi zamu je muyi
azumi acan”.

Kallonta Khausar tayi kana tace.

“Mu tafi ina?”.

Hajja Nana tace.

“Eh mana Khausar mu tafi Jauro Yaya”.

Da sauri Khausar ta maida kallonta gareta kana tace.

“To ai muna zuwa hadda”.

Hajja Nana tace.

“To ai wannan ba abin damuwa bane idan muka je sai Malam Liman ya riƙa ƙara miki”.

Kai Khausar ta girgiza kana tace.

“Baza ki gane bane, inada abubuwan da zanyiwa Mamana ɗin nan da kike gani ina taya ta aiki”.

Hararanta Hajja Nana tayi da faɗin.

“Dama kece mai taya ta aikin ina masu taya ta aikin?”.


Zare ido Khausar tayi kana tace.

“Tayi cikin shege ankoreta ta koma ƙauyensu.

Mai gadin muma ana canza shi saboda shi ya mata ciki”.

Da mamaki Hajja Nana tace.

“Ash'sha Subhanallahi ashe gidan naku babu tsaro kenan, ashe ku gidan bayan maita hadda rashin tsaro
a'a maza-maza shirya mu tafi”.

Dai-dai lokacin da Mommy ta fito girgiza kai tayi tace.

“Kai Khausar bakyajin magana maza ki ɗauka wa Dije abinci ku wuce ɗakin ki”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da wucewa kichen ta daukawa Dije abincin sannan suka wuce Bedroom ɗin.

Mommy kuwa zama tayi agefen Hajja Nana tare da ajiye mata tiren abinci cikin sanyin murya tace.

“Hajja Nana kiyi haƙuri da halin Khausar zaku tafi idan hakan kike so”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa kana tace.

“Toh babu damuwa amma tace min baki da lafiya da gaske ne?”.

Kai Mommy ta Jinjina kana tace.

“Eh wallahi kwanakin nan duka ban cika jin daɗi ba bansan meke damuna ba!”.

Jinjina kai Hajja Nana tayi kana tace.

“Subhanallah Allah ya sawwaƙa Allah ya yaye.

Kuma da gaske ne mai aikin ku ta haihu cikin shege?".

Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya da Amina suka shigo falon.

Ɗaga kai Mommy tayi tare da kallon Hajiya Bunayya data zauna tace.

“Hajiya ga Kakar Khausar”.

Murmushi Hajiya Bunayya tayi Idanunta akan Khausar tace.

“Ai na ganeta Hajja Nana sannu da zuwa ina yini ya gajiya kunzo lafiya?”.
Ita kuwa Amina batare data ƙarasa shiga falon ba ta ɗaga sautin Muryanta da faɗin.

“Khausar!, Khausar!! Khausar!!!,”.

Daga ciki Khausar tace.

“Me?".

Afusace Amina tace.

“Bana son rashin kunya ni zaki yiwa rashin kunya? ina kiranki kina jina ba zaki fito ba aikin san dai tunda
na kira ki ina da ɓuƙatar ki!”.

Jin surutan da take yasa Khausar ta fito tare da tsayawa daga bakin ƙofa ta riƙe ƙugunta kana tace.

“To ai tunda ke kike da ɓuƙatata kinsan inda dakina yake sai ki shiga ki sameni”.

Cike da kirsa Hajiya Bunayya tayi dariya tana kallon Khausar tace.

“Kudai in Kun hadu bakwa rabuwa da faɗa kamar wasu ƙananun yara Allah dai ya kawo muku sauƙi kuna
na kamar wuta da Auduga”.

Juyawa Hajja Nana tayi ta kalli Khausar da Amina kana ta taɓe baki tare da cewa.

“To ai kinsan haka al'amarin yake, mu zuriyarmu bama gani mu ƙyale sannan bama ji muyi shiru, sannan
su kuma mayu haka suke basason mai baki shiyasa baza'ayi shiri ba”.

Hajiya Bunayya tayi saurin cewa.

“Hmmm Hajiya ai tsatsonne na mayu su basu tsotsaba dan mu atsarkake muke”.

Kallon mamaki Mommy tayi mata kana tace.

“Hajiya har ke kin yarda da kalmar kenan?”.

Hajiya Bunayya ta taɓe baki kana tace.

“Ha'a abinda ake faɗa musu acikin gari mun isa mu hana ne?”.

Atake fara'ar dake fuskar Mommy ya gushe cikin rashin jin daɗin abinda Hajiya Bunayya ta faɗa tace.

“Wallahi sukam ba Mayu bane har dake ki yarda kefa komin yaya, ita Uwa ce agareki kuma kakar
’ya'yanki kuma Inde har za'ace suna ciki to mijinki ma yana ciki”.
Hajiya Bunayya kuwa cikin sauri tace.

“A'a mijina atsarkake yake.

Uwarsa kuwa ba zan musan ta mata ba yawwa a duniya idan kaji an cewa mutum maye ba zaka
musanta masa ba kawai dai abinda na sani mijina ba yayi nima banayi kuma 'ya'yana na basayi.

Hajja Nana gaskiya kika faɗa taje can ta ƙarata da baƙin halinta inma tanayi can mata inma ba tayi can
mata amma abinda gari dai ake faɗa tana yi, kuma mutum bashida hujjar da zaiyi musu akan hakan,
gwara ma hujjar da mutum zai ɗabbaga tunda ga alamu ke yanzu ko cikin ki dake yawa zubewa bakya ta
Allah ƙashi da ita!?”.

Cikin sauri tare da ɗaure fuska Mommy tace.

“A'a nikam Allah ne ya ƙaddara min zubewar ciki babu wani wanda ya zubar min da ciki”.

Murmushi Hajiya Bunayya tayi aƙasan ranta tace can miki ƙidahuma.

Khausar kuwa kallon mamaki tabi Hajiya Bunayya dashi kana aƙasan ranta tace lalle Hausawa sunyi
gaskiya da suka ce iya ruwa fidda kai”.

Amina dake tsaye ta watsa Khausar Harara kana tace.

“Abbah ke kiranki kizo kakar taki tazo da wasu maza suna waje sai kije ku gaisa”.

Ta ida maganar tare da juyawa ta fice.

Ita kuwa khausar cike da farin ciki ta juya ta fice ta nufi coumpund kasa ɓoye fara'ar fuskarta tayi ganin
Yaya Aliyu tsaye yaron Baffanta na Adamawa tare da Yaya Abba cikin jin dadi ta ware manyan Idanunta
cike da farin ciki tace.

“Yaya Aliyu sannu da zuwa ku ƙara so”.

Ta faɗa tana yin gaba zuwa Falon Lamiɗo dake saukan baki.

Bayan sun shiga falon sun zauna ta dubi Aliyu still Fuskarta da murmushi tace.

“Yaya Aliyu yaushe kazo?".

Gyara zamansa yayi yana fuskantar ta kana fuskarsa ɗauke da murmushi yace.

“Baffanki ne ya tasoni wai sai na kawowa tsohuwar sa kayan azumi shine kuma yanzu Hajja Nana tace sai
munzo”.
Khausar kuwa murmushi tayi kana tace.

“Hajja Nana rigima"

Sai kuma ta maida kallonta kan Yaya Abba dake latsa waya tace.

“Yaya Abba ya karatu?”.

Ahankali ya ɗago kansa da murmushi afuskarsa yace.

“Karatu ya ƙare yanzu wannan karon tare zamu tafi da Aliyu can Adamawa idan Allah ya nufa idan munje
zan samu aiki Insha Allah tunda kinga Baffan Jimeta yana da hanya da manyan mutane Insha Allah za'a
samu”.

aSaki murmushi tayi kana tace.

“Masha Allah abu yayi kyau”.

Lamiɗo ya shigo suka gaisa bayan sun gama gaisawa ya fita, Khausar kuwa Anutse ta miƙe tace.

“Ina zuwa”.

sannan ta fice.

Kai tsaye kichen ɗin su ta nufa ta ɗauko Babban Warmers da faranti ta fita.

Hajja Nana ta bita da kallo baki sake ganin Uban kula me kyau da tsari da tafita dashi.

Ba daɗewa Khausar ta dawo ta sake ɗaukan Flaks da kofuna.

Har takai ƙofa Hajja Nana data kasa haƙuri tace.

“Kede akwai Jaira mara kirki tunda nazo kike wani shan ƙamshi kamar baki so zuwa na ba, ko arzikin
gaisuwa ban samu ba bare insa rai da ruwan sha, amma wa'annan saboda 'yan uwanki ne jiki na rawa kin
wani kinkimi Uban kula kin fita yanzu kin dawo kin ɗauki Flaks”.

Kallonta Khausar tayi tare da taɓe baki tace.

“Kinga sai anjima Ni sauri nake”.

Tana gama fadar haka ta fice bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon.

Amsawa sukayi tare da kallonta.


Zama tayi tare da buɗe Warmers din ta ɗauki babban Plate ta zuba musu shin kafa da miyar da yaji
naman kaza sai kuma haɗin coslow kana ta zuba musu shayi dake tururi.

Yaya Abba yayi Murmushi yace.

“Da'alama wannan girkin kine saboda wannan ƙamshi”.

Murmushi tayi amma batace Komai ba.

Acan ɗaki kuwa bayan ankira sallan Azahar Mommy takai Hajja Nana har toilet ɗin ta tayi alwala kana ta
fito ta gabatar da Sallah bayan ta idar tayi adduo'i.

Ta juya ta kalli Mommy dake riƙe da carbi ahannunta tace.

“Aisha”.

Cike da girmamawa Mommy tayi ƙasa da kanta kana tace.

“Na'am”

Hajja Nana kuwa gyara zamanta tayi tare da tattara duk kan nutsuwarta zuwa kan Mommy tare da cewa.

“Magana ce mai muhimmanci ta kawoni”.

Cikin girmamawa Mommy da kanta ke ƙasa tace.

“Toh ina sauraronki Hajja Nana”.

Hajja Nana kuwa Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.

“Magana ce akan Khausar da kuma ɗan Baffanta wato Aliyu”.

Jinjina kai Mommy tayi cike da ladabi tace.

“Toh Hajja Nana ina jinki”.

Hajja Nana ta gyara zamanta tare da cewa.

“Toh zuwa yanzu dai inaga Khausar ta girma, sannan inaga ta gama karatun ta yanzu idan ma bata gama
ba to ta kusa”.

Jinjina kai Mommy tayi kana tace.


“Eh ta kusa Insha Allah yanzu kam Shekara ɗaya yarage bayan sallah Insha Allah zata tafi ajin ƙarshe na
gama makarantar gaba da primary”.

Cikin jinjina kai Hajja Nana tace.

“Masha Allah Ubangiji ya taimaka”.

Mommy ta amsa da.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.

Hajja Nana kuwa duk kan nutsuwarta ta tattara tare da cewa.

“To ai yanzu dai ta samu ta kori jahilci ta yaƙesa, yanzu batun aurenta za'ayi.

Ga kuma Yayanta kuma ɗan Uwanta za'a aura Matashi magana ya ƙare sannan kuma idan karatun take
so ta cigaba idan sunyi aure zata yi acan jahar Adamawa tunda suna da makarantu manya-manya acan
dan haka yanzu batun aure ne ya kawo mu nazo dashi za'a haɗa bayan sallah in Allah ya yarda”.

Akuma dai-dai lokacin Khausar ta shigo ɗakin, cike ka ɗuwa Idanunta na kan Hajja Nana cikin sauri tace.

“Wai me naji kina cewa?”.

Cikin isa, gadara, Hajja Nana ta wurga mata Harara kana tace.

“Batun Aurenki nakeyi”.

Arazane Khausar ta zare ido kana tace.

“Wa.....!

*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son
k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman
lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun
matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa
ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki
tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones
dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da
tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da
ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda
ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya
wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka
kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki
da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp
in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta,
muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina
nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a
ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.

0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta
wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije
gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.

GARKUWAR MA'AURATA

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_Page 13_

_NA_
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama, ba haƙƙin kowa akanki.
Littafin 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta
WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ɗin littafin inda zan rinƙa posting.

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

Khausar kuwa cikin tsare Hajja Nana da ido ta riƙe ƙugu tare da cewa.

“Gaskiya nikam bana son irin wannan mulkin mallakar naki”.

Da sauri Mommy ta ɗaga mata hannu fuskarta babu walwala ta kalli Khausar kana tace.

“Kifita, daga nan Khausar!”.

Lokaci daya fara'ar data shigo da shi ya gushe ɓacin rai ya mamaye mata zuciya juyawa tayi ta fice daga
Bedroom ɗin Mommy ta nufi nata tana shiga Bedroom ɗin ta jiyo Muryan Asma'u afalo.

Kai tsaye Bedroom ɗin Khausar Asma'u ta shiga tare da cewa.

“Assalamu Alaikum”.

Atare Dije da Khausar suka amsa da.

“Wa'alaikum Salam”.

Asma'u naganin fuskar Khausar ta ware Ido kana tace.

“Ya dai mutuniyar naga fuskarki haka?”.

Wani abu mai masifar ɗaci Khausar ta haɗiye Idanunta akan Asma'u dake tsaye ta gyara zamanta tare da
faɗin.

“Babu komai ƙara so ki zauna”.

Zama Asma'u tayi tare da tsare Khausar da ido ganin yanayin damuwa atare da ita.

Kallon Dije Khausar tayi sai kuma ta juya ta kalli Asma'u tare da faɗin.
“Wannan Itace Dije”.

Murmushi Asma'u tayi Idanunta akan Dije ta ajiye Handbag din dake hannunta kana tace.

“Sannunki”.

Murmushi Dije tayi tare da faɗin.

“Yawwa”.

Juyawa Asma'u tayi tare da kallon Khausar kana tace.

“Khausar wacece ban ganeta ba”.

Muskutawa Khausar tayi tare da gyara zamanta kana tace.

“Dije ce wacce nake baki labarin ta a Jauro Yaya”.

Jinjina kai Asma'u tayi tare da faɗin.

“Ohh Ayyah na tuna ta itace tazo ita da Hajja Nana suka zone?”.

Khausar kuwa kai ta gyaɗa mata kana tace.

“Eh"

Murmushi tayi tare da faɗin.

“Ai lallai dai kam kice muna da manyan baƙi Dije amma zamu daɗe ko?”.

Kai ta girgiza tare da yin murmushi kana tace.

“A'a yau zamu koma ”.

Ware ido Asma'u tayi tare da faɗin.

“A'a yau zaku koma kuma?”.

Sai kuma Asma'u ta juya ta kalli Dije kana tace.

“Shaf-shaf haka?”.

Ita dai Khausar na gefe ta jingina bayanta da jikin gado Idanunta alumshe tana tunanin maganar Hajja
Nana.

Kai Dije ta gyaɗa tare da faɗin.


“Eh ai da Yaya Aliyu muka zo”.

Murmushi Asma'u tayi kana tace.

“Ayyah ai kam munji daɗin ganinki”.

Asma'u kuwa juyawa tayi tare da kallon Khausar wacce ta tsirawa waje ɗaya Idanu cike da kulawa
Asma'u ta dafa kafaɗar ta kana tace.

“Wai Meye ne kike ta haɗa rai!?”.

Iska mai zafi ta furzar tare da kallon Asma'u fuskarta babu walwala ta saki Ajiyar zuciya kana tace.

“Kina ji wata magana da wannan tsohuwar tazo dashi wai batun Aurena!kuji min tsohuwar nan da wani
iyayi ta bari Iyayena suyi magana akai na mana ita kuma kaka wake maganarta!?”.

Asma'u kuwa Dariya mai sauti tayi tare da cewa.

“Iyeeee kice zamu sha bidiri!”.

Dije tayi murmushi kana tace.

“Barta dai kuma ma kinga mijin data samun ne kyakkyawa fa?”.

Baki Khausar ta kuma taɓewa tare da wurga musu Harara kana tace.

“Toni ina ruwana dashi?,

Ni bana so kada ma ayimin wannan maganar tsakani da Allah shi yafara Auren yayata fa Asma'u”.

Da sauri Asma'u ta ɗago kanta tare da cewa.

“Addarki kuma?, Dama ba kece ƴar farin Mommy ba?”.

Jinjina mata kai Dije tayi tare da cewa.

“Eh ba ita bace ƴar fari Akwai Addarta Nenne Amma ta rasu kuma itama Yayanta Aliyu aka aura mata
sunyi aure da shekara biyu ta samu ciki tazo wajen haihuwa ta rasu!”.

Asma'u ta jinjina kai tare da cewa.

“Allah sarki Allah ya gafarta mata,.

Ohh Ashe shiyasa Mommy bata kunyar kiran sunanki nida duk atunanina kece ƴar fari har nace Mommy
ƴar zamani ce bata ɓoye sunan ki”.
Kai Khausar ta girgiza kana tace.

“A'a ba nice ƴar fari ba ni ta biyu ce”.

Murmushi Asma'u tayi tare da faɗin.

“Ohhh lalle kam kice zamu sha biki”.

Khausar kuwa fuska ta tsuke kana tace.

“Zaku sha bikin waye?”.

Dariya Asma'u tayi tare da cewa.

“Bikin ki mana”.

Cikin haɗe rai Khausar kai ta girgiza tare da faɗin.

“Asma'u kiyi min fatan alkhairi mana, kina jin tsohuwar nan da shiririta da shirme wai ko bayan sallah za
ayi ko menene oho?”.

Dije kam kai ta girgiza tare da cewa.

“Bafa cewa tayi bayan sallah ba ita dai alissafinta ki gama karatunki sai anyi idan yaso in kinaso kici gaba
da karatunki sai Yaya Ali ya saki ki cigaba dayi a Adamawa bayan sallan baɗi take nufi”.

Fuska Khausar ta ya mutse kana tace.

“Aima Allah ya kiyaye abar mutum yayi karatunsa mai zurfi mana sannan ai mutum nada tsarin
rayuwarsu da kuma yanda yake so ya kasance haka kawai sai atakura min”.

Dariya Asma'u tayi tare da cewa.

“Mu dai kar ki mana baƙin ciki ki hana mu shan biki”.

Harara Khausar ta maka mata kana tace.

“Ai sai kuyi shagalin ku kuka ɗai”.

Dije na dariya ta dubi Khausar kana tace.

“Yo ina zamuyi shagali ba Amarya ai dan ke za'ayi”.

Baki Khausar ta taɓe kana tace.

“Ai lalle dai kam”.


Mommy ce tashiga ɗakin bakinta ɗauke da sallama kallon Asma'u tayi kana tace.

“A'a Asma'u kece yaushe kika zo”.

Asma'u kuwa zamewa tayi daga kan gadon tare da cewa.

“Ban daɗe da zuwa ba Mommy Ina yini?”.

Mommy ta amsa da.

“Lafiya lau alhamdulillah yasu Umminki?”.

Miƙewa Asma'u tayi tare da zama agefen gadon kana tace.

“Tace agaisheki”.

Masha Allah Mommy ta faɗa tare da maida kallonta kan Dije kana tace.

“Dije kizo Hajja Nana na kiranki wai zaki rakata gidan Aminiyarta”.

Ta ida maganar tare da juyawa ta fice.

Miƙewa Dije tayi tare da kallon Khausar kana tace.

“Khausar mu tafi mana”.

Fuska Khausar taya mutse kana tace.

“A'a kuje kawai Allah ya kiyaye hanya ni bazan jeba, muyita faɗa da ita a gidan mutane muna raba hali
agidan mutane duk inda mukaje sai ansan mu”.

Murmushi Dije tayi tare da faɗin.

“Toh shikenan mun tafi”.

Sannan ta fice kai tsaye ɗakin Mommy ta wuce sannan ta samu Hajja Nana atsaye.

Hajja Nana na kallonta tace.

“Wuce ki kira su Aliyu mu tafi”.

Kai Dije ta gyaɗa sannan ta fice.

Mommy kuwa Jakar data haɗa wa Hajja Nana tsaraba ta ɗauka sannan ta fice.

A coumpund ɗin ta samu Yaya Aliyu da Yaya Abba tsaye jikin mota cike da girmamawa da kuma ladabi Ya
Aliyu ya kalli Mommy tare da cewa.
“Toh Mommy mun gode Allah ya saka da alkhairi Allah yabar zumunci”.

Murmushi Mommy tayi tare da cewa.

“Amin, Allah ya tsare muku hanya”.

Hajja Nana ta amsa da.

“Ameen”.

Tare da buɗe bayan motar tashiga Dije ta zauna agefenta Yaya Aliyu na gefen mai zaman banza Yah
Abba kuwa shike Driving suka fice daga gidan.

Sai da Mommy taga fitar su sannan ta koma cikin gida.

Yaya Abba kuwa kai tsaye gidan su Moddibo ya nufa.

Hajja Nana nayi masa kwatance har suka isa gida suna shiga gidan.

Cikin sauri Yaya Ali ya lumshe Idanunsa kana yace.

“Masha Allah wlh Ina son garin Gembulan nan saboda yana da kyawun tsari dan yafi Adamawa kyawun
tsari da komai akwai yanayin sanyi da daɗi”.

Jinjina kai Yaya Abba yayi yace.

“Aikam sosai ma”.

Yaya Ali ya juya tare da kallon Hajja Nana kana yace.

“Hajja Nana wannan kuma gidan wacece ɗinkin ne?”.

Murmushi Hajja Nana tayi alokacin da take sauƙa amotar ta kalli Ali kana tace.

“Ƙawata ce tare mukaje da ita aikin hajji na farko na biyu ma tare muka je sannan ko daga baya muna
yawan zuwa Umarah tare da ita”.

Murmushi Yaya Ali yayi tare da cewa.

“Ai dai lalle kam kice gidan Aminiyar kice?”.

Dariya Hajja Nana tayi tare da cewa.

“A'a sosai ma kam”.


Dai-dai lokacin da suka isa ƙaramin gate ɗin da zai sadaka da farfajiyar tsakar gidan Innayi.

Innayi dake zaune ta hango Hajja Nana da baƙi abayanta,

Cike da fara'a ta miƙe da sauri fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi mai cike da jin daɗi ta matso
kusa da Hajja Nana kana tace.

“Aaaa Lalle marhaba Hajjaju Makkatun Masha Allah Hajiya Nana mutanen Makka lale marhaba ku iso”.

Ta faɗa tare da juyawa ta shiga ɗaki tare da ɗaukan lallausan Chanis capet ta shimfiɗa musu.

Sai kuma ta fito cike da farin cikin daya kasa ɓoyuwa afuskarta kallon Yaya Ali tayi tare da cewa.

“Wannan shine Mijin namu na Adamawa da kike bamu labarin?”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tana murmushi kana tace.

“Eh”.

Innayi ta juya ta kalli Hajja Nana kana tace.

“Ku shiga”.

Sannan ta kalli Yaya Abba da Yaya Ali kana tace.

“Ku ƙara so”.

Ta faɗa tare da ficewa Innayi ta nufi sashen Moddibo tare da cewa.

“Moddibo, Moddibo ga baƙi munyi”

Shi kuwa Moddibo atare suka miƙe da M Jameel suka fito.

Ɗan sake fuska Moddibo yayi kana yace.

“Sannunku da zuwa ku iso”.

ya faɗa tare da matsa musu.

M Jameel na ganin Yaya Abba ya miƙa masa hannu fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace.

“Ha'a Abba kaine?”.

Murmushi Yaya Abba yayi kana yace.

“Ni ne dai”.
M Jameel yayi dariya kana yace.

“Sannu ku da zuwa”.

Yaya Abba na bin bayansu yace.

“Laaa Jameel nan gidan kune?”.

M Jameel yayi Murmushi tare da shafa sajensa ya kalli Yaya Abba tare da faɗin.

“Eh gidan mune!”

Murmushi Yaya Abba yayi da faɗin.

“Masha Allah”.

sannan suka shiga falon din wanda tuni Ya Ali da Moddibo suka shiga.

Innayi dake tsaye ta juya tare da cewa.

“Moddibo zoka kawo musu abin taɓa wa”.

Daga ciki Moddibo ya miƙe kana yace.

“Toh Innayi”.

Sannan ya fice tare da bin bayanta.

Juyawa Innayi tayi tare da kallon Moddibo dake biye da ita kana tace.

“Kashiga daga ciki ka gaida ƙawata Hajja Nana dana ke ce maka munje aikin Hajji na farko dana biyu
kuma yawanci Umarah ma tare muke zuwa ɗakin mu ɗaya tun da take zuwa gidan nan bata taɓa
samunkaba,

Kai ya gyaɗa da faɗin.

“Na'am”.Ya ida maganar tare da shiga ɗakin bakinsa ɗauke da sallama Idanunsa ya sauƙa akan tsohuwar
da yaje ya yamata ta'aziyya a Jauro Yaya.

Cike da nutsuwa da kuma ladabi ya zauna daga gefenta kana yasa hannu ya shafa sajensa cikin yanayin
rashin walwalarsa yayi ƙasa da kansa tare da cewa.

“Sannun da zuwa”,Ya gaisheta batare daya nuna ya ganeta ba.


Hajja Nana kuwa Kallonsa tayi kana tace.

“A'a kamar nasan wannan fuskarta fa, kwanaki kamar kunje da wani abokin Malam Liman mai suna
Malam Arɗo ko?”.

Kai Moddibo ya jinjina still Kansa a ƙasa kana yace.

“Eh”.

Murmushi Hajja Nana tayi kana tace.

“Ayyah sannun ka ashe dai Jikana ne Allah yayiwa rayuwarka albarka Allah yabaka zuri'a ɗayyiban”.

Still Kansa A ƙasa ya shafa kwantaccen sumar kansa mai sheƙi da yalƙi kana yace.

“Ameen Ngd”.

Ya ida maganar a taƙaice tare da miƙewa ya fice.

Tiren da Innayi ta haɗa Gasassun Zabbi da M jameel yasa ta gasa musu, shinkafa da miyar dage-dage da
yaji naman kaza sai Akwashi dake ɗauke da ƴaƴan itatuwa ta miƙawa Moddibo amsa yayi kana ya nufi
sashen sa dashi.

Bakinsa ɗauke da Sallama yashiga tare da ajiye Tiren akan center table dake tsakiyar falon kana ya maida
kallonsa kan M Jameel dake ta hiran Yaushe gamo da Yaya Abba kai ya girgiza tare da cewa.

“J miƙo musu ruwa acikin fridge ka barsu haka gashi har na dawo baka kawo musu komai ba”.

Murmushi M Jameel yayi kana yace.

“Wallahi muna ta hiran yaushe gamo da Abba nasan sa mun taɓa haɗuwa dashi a Adamawa”.

Jinjina kai Moddibo yayi tare da jingina bayansa da jikin kushin kana ya lumshe idanunsa tare da cewa.

“Ayyah ashe kunsan juna”.

Kai Yaya Abba ya gyaɗa alamar Eh.

Ya Ali kuwa hankalin sa ya mayar kan wayarsa yana latsawa.

Acan ɗakin Innayi kuwa zama Innayi tayu tare da kallon Hajja Nana kana tace.

“Yanzu ma kinzo wajen jikar tamu ce?”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa kana tace.


“Eh wallahi".

Murmushi Innayi tayi tare da cewa.

“Shine baki zomin da ita ba”.

Baki Hajja Nana ta taɓe tare da faɗin.

“Barta ba shiri muke da ita ba fitsararriya ce yanzu ma nazo ne akan batun aurenta da yayan ta amma na
lura ma kamar batason abin ko yayane ohon mata kinsan ƴaƴan yanzu da tsaurin ido su suke zaɓawa
kansu maza yanzu ma na barta tana can tana kumbure kumburen baki”.

Murmushi Dije da ke kurɓan tes tayi aranta tace Dramer Hajja Nana da Khausar bai ƙarewa.

Innayi kuwa murmushi tayi kana tace.

“Ayyah ai da tazo na ganta kice mu shirya akwai shan biki?”.

Dariya Hajja Nana tayi kana tace.

“Ai dai kam Insha Allah akwai shan biki dan biki yana nan yana tafe”.

Innayi kuwa kai ta gyaɗa kana tace.

“Lallai abu yayi kyau amma dai zamu kwana”.

Girgiza kai Hajja Nana tayi kana tace.

“A'a yanzu ma zamu tafi dan mun sallami can kam da zan tafi da jikar tawa ma to sai mahaifiyata take ce
min bata da lafiya don haka na barta saboda tana taimakawa mahaifiyar tan da ɗan aikace-aikacen yau
da kullum”.

Kai Innayi ta jinjina tare da faɗin.

“Ayyah Allah yabata lafiya.

Yaushe zamu koma Umarah bana zaki je na Ramadan?”.

Hajja Nana kuwa kai ta jinjina kana tace.

“Eh Insha Allahu zanje in Allah ya yarda amman ta Adamawa zan tashi kefa zakije kuwa?”.

Murmushi Innayi tayi tare da cewa.

“Nima zanje in Allah ya yarda amman kin san ni ta nan Jaligo zan tashi”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.

“Abu yayi kyau Ubangiji Allah yasanya alkhairi Allah ya bamu sa'a”.

Innayi ta amsa da.

“Ameen”,kana ta cigaba da cewa.

“Nima zamu tafi da jikina da kuma abokinsa tare za muje”.

Dariya Hajja Nana tayi kana tace.

“A'a abu yayi kyau to sai mun haɗu acan ɗin”.

Hiran yaushe gamu suka cigaba dayi yayin da Dije ke gefe tana yagar Gashesh-shen Zabbi da nonon
shanu mai ɗumi.

Acan falon Moddibo kuwa bayan sun gama gaisawa Yaya Abba da Yaya Ali suka sha fruit din kana suka ci
gashshen Naman dake fitar da ƙamshi tare da ruwan Tea mai zafi.

M Jameel ya kalli Yaya Abba daya koma ya zauna tare da rufe Warmers din Cike da kulawa ya sake
Kallonsa kana yace.

“Abba ya bakuci abincin ba”.

Murmushi Yaya Abba yayi kana yace.

“Wallahi aƙoshe muke yanzu ma dan kar kuce munƙi cin komai ne amma Alhamdulillah”.

Murmushi M Jameel yayi kana yace.

“Toh shikenan”.

Miƙewa sukayi Atare jin Innayi na cewa.

“Moddibo kufita Hajja Nana zasu wuce”.

Da to Moddibo ya amsa kana suka fita cike da kulawa M Jameel da Moddibo suka kalli yaya Abba da
yaya Ali atare suka haɗa baki wajen faɗin.

“Toh mun gode da ziyara Allah yabar zumunci”.

Yaya Ali ya amsa da.

“Ameen”.
Sannan Yaya Abba yashiga mazaunin Driver Yaya Ali kuma ya zauna gefen mai zaman Banza yayin da
Hajja Nana da Dije suka zauna abaya M Jameel ya miƙa kansa ta window tare da ajiye wa Hajja Nana
kuɗi akan cinyarta tare da cewa.

“Allah ya tsare”.

Murmushi tayi kana tace.

“Allah ya muku albarka nagode”.

Motar Yaya Abba yaja suka fice saida motar ta fita layinsu kafin Innayi, Moddibo,da kuma M Jameel suka
koma cikin gida.

Cikin awa biyu Hajja Nana suka isa Jauro Yaya Washe gari Da safe yaya Ali ya koma Adamawa dashi da
Abba suka tafi.

A ɓangaren Khausar kuwa tunda daga ranan da Hajja Nana tayi mata maganar aure ta watsar da
maganar kasancewar Momynta bata sake yi mata maganar ba ita ma bata sake tada maganar ba hakan
yasa bata ɗauki maganar da muhimmanci ba ita kuwa Mommy tasa aranta tun daga Ramadan ya kawo
kai ta samu dama ta yanda zata roƙowa ƴar ta al'khairi idan har Aliyu al'khairi ne agareta Allah ya
tabbatar mata da al'khairi idan kuma ba al'khairi bane Allah ya zaɓa mata mafi al'khairi shima kuma
Allah ya musanya masa da mafi al'khairi.

Yau ya rage azumi saura kwana biyu da hantsi Mommy na zaune afalo taji Sallamar sabon mai gadinsu
da aka kawo kallon Khausar dake riƙe da hisnul Muslim tana Azkhar tayi sai kuma ta maida kallonta ga
Haiydar dake danna wayarta ta gyara zamanta tare da cewa.

“Haidar jeka duba lafiya Namadi ke Sallama”.

Kai Haiydar ya gyaɗa kana yace.

“Toh Mommy”.

Sannan ya miƙe ya fita.

Kallon Namadi dake tsaye yayi kana yace.

“Lafiya kuwa”.

Kai Namadi ya gyaɗa tare da faɗin.

“Kayane Alhaji ya aiko dasu Azo ashiga dashi ciki”.


“Ok kashigo dasu”. Ya faɗa tare da juyawa ya koma ciki.

Kallon Mommy Haiydar yayi kana yace.

“Kayan azumine Abbah ya aiko dasu shine Namadi zai shigo dasu”.

Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa.

“Ok”.

Da Sallama Namadi yashigo kansa ɗauke da buhun shin kafa ya ajiye a store kana ya koma ya ɗauko na
ɗanyen shinka yakai, sannan ya kuma kimawa ya rinƙa shigo da catton ɗin indomie, Catoon ɗin
Spaghetti, Cotton ɗin Macoroni, Couscous, Buhun fulawa, Buhun niƙeƙƙen garin gero na kunu, buhun
wake, buhun sugar Corn Flakes, Madara, Patoto, Doya Crate din ƙwoyi Jarkan mai Jarkan man ja haka ya
riƙa shigowa da tarkacen kayan buƙata na Ramadan.

Kamar yanda ya kawo sashen su Khausar haka ya kai sashen Hajiya Bunayya.

Yayinda hakan take a kowani gida haka magidanta suka riƙa shiga da kayan azumi domin shiryawa
wannan wata mai falala.

Acan ɓangaren gidansu Moddibo kuwa shida M Jameel amota Moddibo ke driving yayin da M Jameel ke
gefen mai zaman banza sai kuma wani yaro daga baya mai suna Iro wanda ke musu aika hong sukayi
aƙofar gidansu Moddibo kana suka shiga cikin gidan bayan Iro ya fita ya buɗe musu.

Innayi na zaune atsakar gida akan kujera ƴar tsugunno taji ƙaran mota na shiga cikin harabar gidan
aranta tace yau lafiya Moddibo ke shigowa da mota har cikin gidan.

Moddibo kuwa kusa da Innayi yayi Parking motar tare da buɗe Murfin motar ya zira ƙafarsa ɗaya awaje
ɗaya kuma na ciki M Jameel da Sadik kuma suka fita kusa da Innayi M Jameel ya zauna shi kuwa Sadik
Boot ɗin motar ya buɗe tare da fito da buhun far n gero, Buhun wake, Buhun shinkafa ɗanye da gumi,
Catoon ɗin indomie, Catoon, Spaghetti, Bushesh-shen kifi crate ɗin ƙwoyi, Gongwanaye mayen madara
da Vournvita buhun, Sugar kwalin Lipton sai kuma naman rago da aka gyara gaba ɗaya ga kuma na
shanu ga kifaye duk Sadik yasa su a fridge

Kallon Moddibo Innayi tayi sai kuma ta maida kallonta kan M Jameel dake kusa da ita tayi tare da cewa.

“Lalle kayan Azumi sun saƙƙo ga Azumi sai ƙaratowa yake yau saura kwana biyu ko uku”.
Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.

“Ai dai kam Innayi azumi yazo”.

Ya ida maganar tare dasa hannu acikin aljihunsa ya ciro Bandir ɗin kuɗi kimanin dubu ɗari ya miƙawa
Innayi tare da faɗin.

“Innayi gashi babu yanda banyi da Moddibo ba yabarni in saya miki kayan Azumi amma dake ɗan baƙin
haline baya so in samu lada yaƙi furrr yace komai shi zai siya gashi wannan ki riƙe kiyi yadda kika ga
dama dasu”.

Kallon kuɗin Innayi tare da Girgiza kai kana tace.

“Ayyah Jameel am bana son wannan shungullan yanzu ni kuma me zanyi da wannan kuɗin kabar su
Jameel am ni ba ɓuƙatar su nake ba”.

M Jameel kuwa zama ya gyara tare da fuskantar Innayi da kyau kana cikin wata raunan'niyar Murya ya
lumshe idanunsa tare da cewa.

“Tunda muke tare daku tsawon shekaru Innayi daga ke har Moddibo ban taɓa ɗaukar abu in baku ku
karɓa ba, duk abinda na baku sai kun mayar min dashi baya, ban sani ba wataƙil shi Moddibo yana
ɗaukar Maganar Aunty Karima keyi amatsayin matakin ƙin karɓan abu awajena”.

Lumshe idanu Moddibo yayi tare da jingina kansa da Murfin motar yana sauraron abinda aminsa ke
faɗa.

Ita kuwa Innayi idanu ta zuba masa tana nazarin kalamansa.

M Jameel ya cigaba da cewa.

“Abinda Moddibo bai saniba koya karɓi abu awajena ko karya karɓa ita gani take komai na rayuwarsa Ni
nake masa dan haka gwara ma ya karɓa idan yaso ta tuhumesa da tushe”.

Ya furzar da iska mai zafi kana ya cigaba da cewa.

“Kema kuma Innayi ina ganin maganar mutane kike ɗauka da suke cewa Babana ke daukar ɗawainiyar
ku amma ni nasan ba haka bane. Allah ne kaɗai ya barwa kansa sanin yanda kuke rayuwarku duk da
aminantakar dake tsakani na da Moddibo har yau ɗin nan bansan taya kuke mu'amala da rayuwarku ba
bansan ta yanda kuke samun abinda kuke biyan buƙatar rayuwarku ba kama daga karatun Moddibo kab
babu aƙaramar makaranta zuwa hidimar fitanmu Makarantar waje ina sane ina kuma tunawa Naira biyar
kun ƙi karɓan tallafi awajen Babana ku keyin komai abinda yasa mutanen gari suke ɗaukar haka suna
lura da Moddibo ba wani sana'a yake ba sannan ana mamakin irin buƙatun da kuke yafi ƙarfin samun ku
ko kuma tattalin ku Innayi!”.

Dariya mara sauti Innayi tayi tare da jinjina kai kana ta tsaida idanunta akan Moddibo daya dafe kansa
sai kuma ta kalli M Jameel daya dafe kansa tayi murmushi tare da cewa.

“Abun aduhu ne Jamilu barshi kawai babu ɓuƙatar sai ansani, shi kansa Moddibo bai san komai akan
al'amuran rayuwar nan ba bare ya gaya maka”.

Moddibo kuwa Sanyayyar Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon M Jameel ya buɗe masa hannunsa alamar
kaji dai nima bansan komai ba a cikin abubuwan da kake son sani.

Sai kuma Moddibo ya numfasa tare da lumshe Idanunsa kana cikin sanyin murya mai cike da rauni ya
kalli Innayi tare da cewa.

“Kagani ni kaina ban san komai ba kama daga lokacin dana ke karatu.

Ni dai nasan tana min komai idan nayi magana sai tace gadon Iyayena da suka bar min ne, bansan inda
ta ɓoye kuɗin ba na girma ma yanzu ta bani gadona ahannuna taƙi ko gani take har yanzu ban kai ba
oho.

Kai kuma kana tuhumata kamar acikin aminantakar mu akwai abinda nake ɓoye maka, bayan kuma J ka
sani babu wani shamaƙi tsakaninmu”.

Ya ƙarisa mgnar tare da

runtse idanunsa a take kuma ya buɗe su akan M Jameel da shima shi yake kallo, a hankali ya furzar da
iska mai sanyi tare da cewa.

“J ba'ayi wani abu na duniya da ni Aliyu zan iya ɓoye maka ba, aminantakar mu ta wuce babin in ɓoye
maka wani abu”.

Jinjina kai M Jameel yayi yana kallon amininsa cike da tausayawa.

Innayi kuwa murmushi tayi tare da jinjina kai amma ba tace komaiba ba.

Moddibo kuwa kallon Innayi yayi kana yace.

“Yanzu kuma hidimar da nake kai kan ka kasan inda nake samu tunda muna aiki kuma ana biyan mu
sannan kuma. Ni kaina wataran saidai inga tayi min abu misali yanzu mota dai ni bansa araina ba kafin in
ankara har ta saya anyi komai kafin ma mu dawo”.

Numfashi ya sauke kana ya cigaba da cewa.


“Babu yanda banyi da ita ta faɗa min ba idan ma a kuɗin gado nane tunda na girma ta bani abuna zan iya
sarrafawa”.

Hararansa Innayi tayi kana tace.

“Anƙi abaka”.

Shiru M Jameel da Moddibo kai ya jinjina ba tare da tace komai ba sai tsirawa Innayi ido da sukayi.

Miƙewa M Jameel yayi yace.

“Bari mu tafi Innayi”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Allah ya tsare”

Suka amsa da.

Amin

Shi kuwa Moddibo Kallon Innayi yayi kana yace.

“Innayi har yanzu yarinyar nan bata zoba?"

Jinjina kai Innayi tayi tare da cewa.

“Dama wannan shekarar Ummin Asma'u tace in bari zata turo min Asma'u dan ƴaƴan ƙabilun in sun zo
gaba ɗaya lalata sukeyi sannan basajin magana to Asma'u zata zo ta tayani”.

Cikin kula ya kalli Innayi kana yace.

“Innayi anya Asma'u zata iya ayyukan da suna da yawa fa kinga akwai abincin da za'a dinga fitarwa na
masallaci”.

Jinjina kai Innayi tayi kana tace.

“Zamu iya ai naga Asma'u tana da kuzari kuma nima da kuzarina da kuma lafiyata zan iya”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Toh Allah ya temaka”.

Ta amsa da.

“Ameen”,Kana tace.

“Ai girkin ma na iya tsawon kwana goma sha biyar ne zamuyi”.

Kai M Jameel ya Jinjina kana yace.


”Eh haka ne Innayi”.

Sallama suka mata sannan M Jameel ya Miƙe.

Dama already Moddibo na cikin motar yaja suka tafi.

Kai tsaye kasuwa Moddibo ya sake nufa Kallonsa M Jameel yayi kana yace.

“Mai zamu kuma yi a kasuwa?".

Ba tare da Moddibo ya juya ya kallesa ba ya lumshe idanunsa kana yace.

“Idan muka je za kaga ni”.

Shiru M Jameel yayi har suka isa kasuwar kamar yanda Moddibo yayiwa Innayi siyayya haka ya sake
sayan wasu Kallonsa M Jameel yayi tare da cewa.

“Wannan kayan na waye haka?”.

Anutse Moddibo yace.

“Ina ruwanka”.

Daga haka yaja motar suka fita kai tsaye hanyar gidan Ummi ya nufa.

Da sauri M Jameel ya juya ya kallesa kana yace.

“Ai baka isa ba Ummi ba zata karba ba ai kai ma idan zan kaiwa Innayi abu hana wa kakeyi”.

Moddibo kuwa baki ya taɓe kana yace.

“Ai ba Umminka kai ka ɗai bane harda ni dan haka kabarni in samu lada”.

Murmushi M Jameel yayi Amma baice komaiba.

Koda suka isa aka shigar da kaya, M Jameel yayi wa Ummu bayanin yadda sukayi.

Ita kam Ummi sai ta riƙa sakin murmushi bayan ta gama jin jawabin M Jameel sai kuma ta kalli uban
kayan da aka shigo dasu ta juya ta kalli Moddibo daya tanƙwashe ƙafafunsa tare da sunkuyar da kansa
ƙasa tayi murmushi fuskarta ɗauke da murmushi cike da ƙaunarsu ta saki ajiyar zuciya kana tace.

“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ku Ubangiji Allah ya baku ƴaƴan da zasuyi muku biyayya fiye da
yanda kuke mana”.
Atare suka amsa da.

“Ameen”, Bayan sun sake taɓa hira suka miƙe tare da yimata sallama suka tafi...!

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_Pape 14_

NA

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*Free page ne ƴar uwa saura uku kacal mu gama free page, har yanzu baki makaraba ki biya*

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin wani kanki.
SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta
WHATSAPP 09097853276. Kana sai in saki a Group, ɗin da zan rinƙa posting.*

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

Washe garin washe gari.

Da daddare watan Ramadan ya bayyana.


Haka yasa dukkan ɗauka cin Musliman duniya suka cika da farin ciki tare da yin niyan ɗaukar azumin
watan Ramadan ɗin, kana kowa yana shirya bukatunsa dan miƙa su ga Ubangiji Mabuwayi gagara Misali.

Washe gari Ranar Litinin gaba ɗaya al'ummar Musulman duniya sun tashi da azumin watan Ramadan
abakinsu gaba ɗaya ɗaukan farko ɗauka ɗaya akayi duk duniya abinda aka daɗe ba'a yiba tsawon lokaci
mai yawa wannan shekarar ansamu kowa na cike da farin cikin wannan al'amari azuciyar musulmai.

Da daddare Misalin ƙarfe 9:00 pm Babban masallacin juma'a dake ƙofar gidan Sarki cike yake da.

Al'ummar Musulmi maza da mata wanda duk shekara idan aka shigo Ramadan bayan an idar da sallar
isha'i M Jameel da Moddibo ke gabatar da Tafseer Alkur'ani mai girma duk shekara Moddibo ke jan baƙi
yayin da M Jameel keyin Tafseer yana fassarawa.

Masha Allah kamar yanda suka gabatar ashekarar Bara ayau ma hakane Cikin Masallacin Maƙil yake da
dubban jama'a yayin da Moddibo ke zaune akan wani ƙayatenccen kujera gabansu babban table ne dake
ɗauke da system jikinsa sanye da Jallabiya Armygreen mai yauƙi da sansti kana gaba ɗaya ilahirin jikinsa
na fitar da sanyayyan ƙamshi tularensa, idanunsa alumshe yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi yake.

Yayin da M Jameel ke zaune gefensa cikin shiga na alfarma Bugaggiyar shadda ce fara sol anyi masa ɗin
kin ƴar ciki da gariya sai hula baƙa sosai yayi kyau gaban jikin rigarsa maƙale da microphone.

Cikin tsantsar nutsuwa da kamala M Jameel ya hura microphone ɗin tare da gyara zamansa kana yace.

_“A'uzubillahi Minal Shaiɗanir rajeem Bismillahir Rahmanir Rahim. Innal hamdillah Nahmud
wanastainuhu wanastaghfiru, wa'nazubillahi min shuriri anfusna, wamin sayyi ati a'amalina, manyah
dillahu fala mudillah waman yudil fala hadiyala, Wa'ash hadu Allah ilahalillahu wahdahu lasharika lahu
Wa'ash hadu Anna Muhammad Abduhu warasuluhu._

Ya ɗan sauƙe numfashi tare da sauƙe numfashi kana ya sakin ajiyar zuciya sannan ya cigaba da cewa.

_“Ya ayyuhallazina amanut taƙullaha haƙƙu tuƙatihi wala ta mutunna illah wa'antum Muslimun ya
ayyuhan nabiyu taƙu rabbakummalazi wahida wakalaƙa minha zaujuha wabassa min huma rijalan
kasiran wani sa'a wattaƙullahal lazi tasa aluna bihi wal arhama innalaha bikum kana alaikum raƙibaaa_

Baki ɗaya ciki da wajen masallacin ya kacame da sowa da sassarfan waɗanda ke harabar masallacin da
suke shigowa da sassarfa.
M Jameel kuwa idanu ya lumshe tare da buɗesu kana yace.

“Amma ba'ad faya Ikhwatul musulmi Assalamu alaikum Warahmatullah Wabarkatuhu”.

Gaba ɗaya cikin masallacin da harabarsa suka amsa da faɗin. “Wa'alaikum Salam Warahmatullah
wabarkatuhu”.

Gyara zama M Jameel ya yi tare da kallon ɗumbin jama'ar dake masallacin kana a hankali ya numfasa
sannan yace.

“Insha Allahu zamu cigaba da Tafsirin Alkur'ani mai girma kamar yadda muka saba, zamu kuma ɗaura
daga inda muka tsaya bara. A cikin suratul Nisi'i awancan shekarar mun tsaya akan aya na ɗaya wanda
ya zamana shi muka karanta Ramadan ya ƙare cikin ikon Allah gashi ya sake sada mu acikin watan wanda
da yawa wasu daga cikin wanda mukayi tafsiri dasu wancan shekarar yanzu basa nan kana da yawa
wanda muka fara ayau da ƙyar zamu ga ƙarshen amma muna roƙon Allah daya nuna mana ƙarshen
wannan wata mai falala da kuma al'barka lfy”.

Baki ɗaya wajen suka amsa da faɗin.

“Ameen”.

Domin wasu daga cikin masu sauraron karatun suna zuwa ne saboda yanda M Jameel ya ƙware awajen
Tafseer gashi kuma yana da zafi nama da kwarjinin tafsir.

Juyawa M Jameel yayi tare da kallon Moddibo da kansa ke ƙasa ya tsirawa System ɗin sa idanu ya gyara
zamansa tare da cewa.

“Bismillaha Alaramma jeka cikin Suratul Nisa'i ka karanto mana muji abinda Allah ma ɗauka kin sarki
yake faɗa”.

Jinjina kai Moddibo yayi tare da gyara zamansa kana ya jingina bayansa da jikin kujera sannan ya lumshe
idanunsa cike da nutsuwa ya motsa laɓɓansa kana yayi gyaran Murya cikin Sanyayyar muryarsa mai
daɗin saura da sanya nutsuwa da ratsa zuciyar bani adam ya fara kamar haka;

“Bismillahir Rahmanir.
Gaba ɗaya illahirin yaƙin da sautin muryarsa ya ratsa kunnuwansa, sit sukayi babu abinda wani sauti ko
hayaniya, wurin yayi sit kai kace babu mai rai a wurin bare numfashi, gaba ɗaya an nitsu, wanda hakan
kuma a jinin Modibbo yake, duk hayaniyar wuri muddin yayi basmalla a take kab za'a nutsu.

Idanunsa ya ɗan lumshe kana ya buɗe su a hankali yana kallon taron al'ummar Annabi dake tare maƙil,
cike da nitsuwa ya fara karatu cikin zaƙin murya ya kawo aya ta biyu cikin suratul Nisa.

.2-Wa'atul ystamaa amwalahum,Wala tatabaddalul khabisa biɗɗayyir,Wala ta'akuluu Amwalahum Ila


amwalikum,Innahu kana huban kabira”._

Atake mutanen da masallacin suka shiga lumshe idanunsa yayin da wasu suka shiga sakin ajiyar zuciya
Moddibo mutum ne mai ƙwarjini duk yanda waje keda hayaniya da zaran sautin muryarsa ya fita zakaji
wajen yayi stit.

M Jameel kuwa ya Jinjina kai yayi yana mai jin ayan na ratsa sa cikin yanayin faram-faram ɗinsa yace.

“Gabaaa jeka aya ta gaba Aramma muji mai Allah yace”.

Sanyayyar iska mai sanyi Moddibo ya furzar tare da gyara zamansa kana ya cigaba da jan Ayar kamar
haka;

_3-Wa'in hiftum Allah tuƙsiɗu fil yatama fankihu ma ɗabala lakum Minal Nisa Masna wasulasa
waruba ,Fa'in hiftum Allah ta'adilu fawahidatan Auma malakat aymanukum,Zhalika adnaa Allah
ta'aluun_.

Cikin jin daɗin sauraron muryarsa mafi yawan Ƴan matan dake sauraron karatun suka lumshe idanunsu
suna burin Allah ya mallaka musu shi amatsayin mijin Aure.Yayin da magidanta suke burin ƴaƴan su
suzama kamar Moddibo.

Cikin ɗaga sauti M Jameel ke gyaɗa kansa kana yace.

”Je gaba Aramma muje gaba muji me Ubangiji yace”

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da jingina bayansa ajikin kujera kana ya lumshe Idanunsa tare da
gyara system dake gabansa ya cigaba.

_“4-Wa'atunnisa'a saduƙatihinnah Nihylah,Fa'in ɗibna lakum anshay'in minhu nafsa fakuluhu hani'am
mariyya.5-Wala tu'utussahafa'u Amwa lakumallati ja'alallahu lakum ƙiyama warzuƙuhum fihaa
warkusuhum waƙulu lahum ƙaulan ma'arufah”_.

Ya ƙarashe jan ayar cikin zazzaƙar muryarsa.


Shiko M Jameel gyara zaman Microphone dake gabansa yayi kana yace.

“Masha Allah Aramma”.

Atake masallacin ya kaure da kabbara wasu na buri da fatan Allah ya azurtasu da baiwan murya irin na
Moddibo da yawa daga masu zuwa Tafseer ɗin suna zuwa ne Saboda zaƙin muryan ƙira'ar Moddibo da
kuma nutsuwarsa musamman yanda Laudspeaker ke fitar da zazzaƙan murya Moddibo tare da sanya
nutsuwa,

M Jameel da Moddibo sun iya Tafseer domin shi M Jameel mutum nai mai zafin jini Moddibo kuma ya
kasance mutum mai sanyi komai nasa cikin nutsuwa yake hakan yasa mutane ke matukar ƙaunar Tafseer
ɗin su mutane kan tsallake unguwar su suzo su saurari nasu.

M Jameel kuwa cike da tsantsar ƙwarewa da kuma sanin abinda yake yi ya fara tafsirin ayoyin bayan yayi
muƙaddima ya fara fassarar kamar haka :

_”Aya ta(2) Allah madaukakin sarki nacewa

(Kuma ku baiwa marayu dukiyoyinsu kuma kada ku musanya mummuna da mai kyau.kuma kada kuci
dukiyoyinsu zuwa ga duniyoyin ku, Lalle shiya kasance zunubi ne mai girma”_

Mafiya yawan mutanen dake wajen jikinsu ne yayi sanyi domin ji sukayi Ayar tamkar dasu take magana
cike da nutsuwa suke sauraren.

M Jameel ya numfasa kana ya cigaba da cewa.

_“Aya ta (3) Allah yana cewa.

_Kuma idan kunji tsoron ba za kuyi adalci ba acikin marayu to(akwai yadda za'a yi)ku auri abinda yayi
muku dai-dai daga mata biyu-biyu,Uku-uku ko huɗu-huɗu sa annan idan kunji tsoron baza kuyi adalci ba
to ku auri guda ɗaya ko kuwa abinda hannayenku na dama suka mallaka.wannan shine mafi kusantar
zama baku wuce haddi ba”._

Numfashi wasu daga cikin mata masu kishi suka saki jin Allah da kansa ya bawa maza ikon su ƙara aure yi
shin to wai menene abin kishin hauka duk da cewa dole ne ayi kishi amma ya kamata su rika sassauta.

M Jameel kuwa juyawa yayi tare da kallon Moddibo daya zubawa system ɗin sa idanu numfashi ya sauƙe
cikin yanayin zafin jinjinsa ya cigaba da cewa.

_“Acikin aya ta (4). Allah Mabuwayi gagara Misali cewa yayi.

Kuma ku baiwa mata sadakin su sauƙin bayarwa sannan idan suka yafe muku wani abu daga gareshi a
daɗin rai to kuci shi da jin daɗi da saukar da hadiya”._
Ya ɗago kansa tare da kallon jama'ar dake masallacin cikin ɗaga sautin murya ya gyara zaman hular dake
kansa kana yace.

“Kai Kuce Allahu Akbar”.

Atake masallacin ya ɗauki kabbara da faɗin Allahu Akbar Allah ya ƙara maka nisan kwana.

Murmushi yayi tare dasa hankie ya goge gaban goshinsa kana ya cigaba da cewa.

_“Kada ku baiwa wawaye dukiyar ku Wanda Allah ya sanya ta agareku kuna tsayuwa (ga gyaranta)kuma
ku ciyar dasu cikinta,kuma ku tufar dasu kuma ku gaya musu magana sanyayya ta alkhairi”_.

Atake masallacin ya jure da kabbara cike da jin daɗin tafsirin.

Agefen ɓangaren mata Asma'u ce zauna tare da Innayi sai Khausar dake can gabansu Matsawa Asma'u
tayi tare da taɓa bayan Khausar,juyawa Khausar tayi ganin Asma'u yasa tayi murmushi tare da miƙewa
daga inda take ta dawo kusa da Asma'u.

Tana murmushi ta gyara zamanta tare da cewa.

“Asma'u ya Ummi amma ɗazun da mukayi waya baki ce min zaki zo Tafseer ba”.

Murmushi Asma'u tayi kana tace.

“Ai nadawo gidan Innayi da zama zan riƙa taya ta aiki sai Azumi ya ƙare zan koma gida”.

Bata jira jin Abinda Khausar zata ceba ta juya tare da kallon Innayi data tattara nutsuwarta zuwa ga
tafsirin da jikokin ta keyi hannunta Asma'u ta riƙe kana tace.

“Innayi ga Khausar ƙawata”.

Murmushi Innayi tayi tare da kallon Khausar,Ita kuwa khausar ƙasa tayi da kanta cike da nutsuwa ta
gyara zaman hijabinta kana tace.

“In wuni ya ibada?”.

Murmushi Innayi tayi tare da cewa.

“Lafiya lau Alhamdulillah".

Haka nan Khausar taji tsohuwar ta burgeta Kallon Asma'u tayi cikin ƙasa da murya ta kalli Asma'u tare da
cewa.
“Wacece?”.

Asma'u na murmushi ta juya ta kalli Khausar kana tace.

“Kakar Moddibo ce”.

Taɓe baki Khausar tayi kana tace.

“Itakam tana da kyawawan hali ba iri jikanta ba ko ina ya gado baƙin zuciya ohon mishi mugu”.

Dariya Asma'u tayi amma batace Komai ba.

Bayan M Jameel yayi tafsirin Ayoyi guda goma,ya duba lokaci ganin ƙarfe goma saura minti takwas ya
numfasa tare da faɗin.

“Wasubhanakal Lahumma wabi hamdi Nash'hadu Allah'ila ha Illah anta nastagfirka wanstubu Ilaik”.

Ya rufe system ɗin sa tare da cewa.

“Dan Allah kamar yanda aka saba maza suyi haƙuri mata su fara fita”.

Sai da duk matan suka gama fita kafin maza acan mota Innayi da Asma'u suka jira M Jameel da Moddibo
har gida aka kaisu bayan sun isa gidansu Moddibo kasancewar duk Ramadan agidansu Moddibo M
Jameel keyi saboda yawan hidimarsu.

Suna isa kai tsaye sashen Moddibo M Jameel suka nufa Asma'u da Innayi kuwa sashen ta suka nufa suna
shiga ciki Innayi ta cire dogon hijabin dake jikinta tare da kallon Asma'u tana ajiye hijabin ta sauƙe ajiyar
zuciya da faɗin.

“Asma'u ɗauki abinci ki kaiwa Yayunki tun da akayi buɗa baki ƴaƴan itatuwa da kunu kaɗai suka sha basu
ci wani abu ba”.

Jinjina kai Asma'u tayi kana tace.

“Toh”,Sannan ta ɗauki Faranti Perpesoup ɗin kaza,da Couscous da miyan ƙwai sai perper cheking sai
juice ɗin Abarba da kwakwa sai kuma fruit salad.

Bakinta ɗauke da Sallama tashiga zaune ta same su M Jameel na kan 2sitter yayin da Moddibo ke kan
3sitter Idanunsa alumshe ajiye wa tayi tare da juyawa zata fita.

M Jameel ya ɗago kansa tare da kallon Asma'u dake shirin fita yace.

“Asma'u zo ki zuba mana yunwa nakeji wallahi kinsan Magana ba wasa ne dashi ba”.
Murmushi tayi kana tace.

“Hakane”.

Kam sannan ta tsugunna ta buɗe Warmers din Atake ƙamshi ya bugi hancinsu da sauri M Jameel ya Kalli
Asma'u tare da cewa.

“Asmeey wayayi wannan girkin?”.

Tana zuba musu miyar ƙwoyin akan Couscous ɗin ta ta ajiye kana tace.

“Ya Jameel nice Nayi”.

Ware ido M Jameel yayi.

“Kai Asmeey ki faɗi gaskiya dai”.

Murmushi tayi da faɗin.

“Allah da gaske ni nayi yaya Jameel”.

Abincin ya ɗiba ya kai bakinsa tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Waya koya Miki wanna girkin?”.

Dariya tayi kana tace.

“Khausar ce ta koya min Allah yaya Jameel yawanci idan naje gidan take koya min”.

Moddibo dake kwance ya harareta kana yace.

“Ke dai Arayuwarki komai baki iya ba sai dai wata ce ta koya miki, ki bari mana akoya mikin kawai akayi
ba magana ta ƙare ba ba sai kince ga wacce ta koya miki ba”.

Ya ƙare maganar kamar bashi yayi ba.

Murmushi Asma'u tayi kana tace.

“Allah Yaya Moddibo Khausar ta iya girki sosai saboda kullum tare suke shiga kichen da Mommy ta”.

Baki ya taɓe da faɗin.

“Naji jeki ki gaida Innayi”.

Kai ta gyaɗa tare da yin murmushi har ta kai ƙofa zata fita sai ta kuma ta sake juyawa tare da komawa
ciki kana tace.
“Yaya Jameel ƙofan Innayi babu wata gashi kuma naga nan akwai wuta”.

Moddibo dake kwance ya shafa sajensa kana yace.

“Itace tace bata so gashi har cikin kicin ɗinta taƙi a kaishi ɗakinta”.

Baki Asma'u ta tura tare da Marerece fuska kana tace.

“Nikam gaskiya zama ba wutan nan baimin ba”.

M Jameel dake cin Chicken Peper ya kalleta tare da cewa.

“Toh kije ki faɗa mata wata ƙil wala Allah idan ke kin faɗa ta yarda asa mata”.

Kai Asma'u ta jinjina kana ta miƙe tare da faɗin.

“Toh”,Sannan ta fice ta nufi sashen Innayi.

Bakinta ɗauke da Sallama tashiga ɗakin Innayi zaune ta samu Innayi da lantarta azaune hannunta riƙe da
carbi tana ja.

Zama tayi daga gefen Innayi kana tace.

“Innayi naga an kawo wuta a sashen su Yaya Moddibo Nan kuma babu wallahi rashin wutar nan beyi
ba”.

Anutse Innayi ta juya ta kalleta kana tace.

“Ayyah Asma'u am ni tsoron wutan nan nake ji bana son irin wannan abubuwan ke kuma kina so ko?”.

Jinjina Kai Asma'u tayi tare da faɗin.

“Allah Ni dai inaso”.

Innayi ta kalleta kana tace.

“Zafi kike jine?”.

Girgiza kai Asma'u tayi tare da cewa.

“Ba zafi ba haske dai Innayi ɗan tv nan dai idan alasa zamu riƙa kallon sunna Tv”.

Jinjina kai Innayi tare kana tace.


“Shikenan sai asaka tunda haka kike so insha Allah gobe zan faɗa musu asaka mana”.

Da sauri Asma'u ta miƙe kana tace.

“Bari Inje in faɗa musu yanzu”,Ta ida maganar tare da ficewa.

Kai tsaye sashen ta koma bakinta ɗauke da Sallama tashiga Idanunta akan Moddibo dake kurɓan Juice
ɗin fuskarta ɗauke da murmushi kana tace.

“Yaya Moddibo Wallahi Innayi ta yarda aja mata wuta kuma dan Allah asamar mana Tv zamu riƙa kallon
Tafseer kaga ita yanzu sai dai tayi ta rungumar Radio komai sai dai taji ta Radio”.

Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.

“Toh shikenan Allah ya kaimu goben”.

M Jameel kuwa kallon Asma'u yayi fuskarsa ɗauke da murmushi ya ajiye Plate ɗin hannunsa kana yace.

“Tafff lallai Asma'u ke ta musamman ce kinyi babban sa'a babu yanda ba muyi da ita ba muja mata wuta
taƙi”.

Murmushi Moddibo yayi kana yace.

“Ai Asma'u ta hannun daman Innayi ce”.

Murmushi Asma'u tayi tare da ficewa ta koma falon Innayi suka kwana Misalin biyu da rabi Innayi ta
farka kana ta tashi Asma'u suka fita alwala sukayi suka gabatar da nafilla tare da adduo'i ƙarfe uku dai-
dai Innayi da Asma'u suka shiga kichen Innayi tayi musu ɗumanen tuwan jiya tare da tafasa ruwan shayi
daya ji kayan ƙamshi sai kuma ta ɗumama perpesoup ɗin kazan ita kuwa Asma'u attaruhu da albasa ta
jajjaga tare da ɗauraye tukunya ta sanya akan gas wanda zuwan Asma'u ne Moddibo suka kawo mai ta
zuba kana ta zuba jajjegen tare da zuba spices da Maggi da kuma Curry ta zuba kana ta zuba sanwa
Bushesh-shen kifi dake gyare ta zuba sannan ta ɗauƙi carrots,da grean beans,da kuma cabbage ta shiga
gyarawa jin ruwan na tafasa ta tsaya ta zuba Spaghetti leda ɗaya sannan ta cigaba da gyarawa sai daya
kusa tsotsewa sannan ta zuba cabbage,grean beans,Carrot,aciki Nan da nan gidan ya kaure da ƙamshi
Warmers ta ɗauka ta juye sannan ta zuba sauran a plate ta haɗa kayan duka a babban faranti ta ɗauka
bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon.

Moddibo dake zaune riƙe da Alkur'ani ya ɗago kansa tare da amsa Sallamar bayan ya kai ƙarshen ayan
Moddibo kuwa idanunsa ya ɗauke daga kan system ɗin tare da kallon Warmers din sai kuma ya Kalli
Asma'u dake ajiyewa akan center table ya shafa sajensa tare da cewa.
“Asmeey ya naga kuloli da yawa haka?”.

Murmushi tayi kana tace.

“Wannan ɗumame ne Innayi tayi muku ɗayan kuma ɗumamen perpesoup ɗin jiya ne wannan kuma
jollof nayi muku na Spaghetti”.

Jinjina kai M Jameel yayi kana yace.

“Ni dai kamar nafi son ɗumamen Amma bari naga jollof ɗin naki”.

Ya ida maganar tare da buɗe Kulan cikin sauri ya lumshe idanunsa jin ƙamshin daya ratsa hancinsa.

Kallonta yayi kana yace.

“A'a bazan ci ɗumame ba”.

Juyawa Moddibo yayi tare da kallon M Jameel kana yace.

“Ai kuwa baka Isa ba ɗumame zaka ci, Asma'u Allah ya miki albarka”.

Sai kuma ya sake kallon M Jameel dake murmushi kana yace.

“Ai dolenka ɗumame zaka ci dan kaine Innayi ke yin ɗumame ko wani shekara sai ka ishemu da ɗumame
saboda kai ake liƙa mana”.

Murmushi M Jameel yayi kana yace.

“Ai ɗumamenta yana da daɗi kai kan ka in faɗa maka zakayi missing ɗumanenta idan baka kusa yanzu
ma dan kana tare dashi ne”.

Murmushin gefen baki Moddibo yayi kana yace.

“Um naji amma dai yau shi zaka ci”.

Dariya M Jameel yayi tare da cewa.

“Ba matsala ai ɗumamen Innayi nace”.

Miƙewa Asma'u tayi tare da ficewa Moddibo da M Jameel kuwa Matsawa sukayi tare da fara cin
ɗumamen kaɗan suka ci sannan suka ci jollof ɗin taliya suka sha tea perpesoup din kazar kuwa ko
buɗewa basuyi ba bayan sun gama suka miƙe suka tafi masallaci tare da idar da sallah saida sukayi
Azkhar kafin suka dawo gida suka kwanta bacci kafin wani lokaci su tashi su tafi Tafseer acikin
makarantar su.
Ƙarfe Goma da rabi dai-dai suka farka atare Moddibo ya miƙe bakinsa ɗauke da addu'a kana yashiga
toilet yayi wanka tare da daura al'wala zama yayi tare da shafa lotion mai ƙamshi sannan ya sanya
Jallabiya Marron colour tare da ɗaura baƙin Alkyabba akai kana ya naɗa hirami akansa sosai yayi kyau
tamkar balarabe kana ya feshe jikinsa da turarukansa masu daɗin ƙamshi sallah walha ya gabatar tare da
zama ya fara ƙira'a cikin Suratul Maryam.

Sha daya da rabi dai-dai M Jameel ya fito daga ɗaya Bedroom din cikin shiri da alama ya gabatar da sallar
walhar shima kallon hadaɗɗen agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa yayi kana ya maida kallonsa kan
Moddibo tare da cewa.

“A.J sha biyu ta kusa fa mutafi kasan ana jiranmu”.

Dai-dai lokacin da wayar Moddibo yayi ruri kallon screen ɗin yayi tare da kallon M Jameel kana yace.

“Gashi ma malam Arɗo ke kirana da alama zai ce mu ake jira masallaci ya cika”.

Jinjina kai M Jameel yayi kana yace.

“Mu tafi”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da ɗaukar mukullin motar suka fice.

Kai tsaye masallacin dake cikin makarantarsu suka nufa wanda yake cike da maza da mata ko wanne na
ɓangaren su sai dai mata sunfi yawa ƙarfe 12:00 ya musu acikin masallacin.

Gyaran Murya M Jameel yayi cikin nutsuwa da kuma yanayin zafin jinjinsa ya gyara zamansa tare da
cewa.

_“Innalhamdulillah Nahmaduhu Wanastainuhu wanastaghfiru wa'nazubillahi billahi min shuriri anfusna


wamin sayyi ati a'amalina manyah dillahu fala hadiyala waman mudillah fala hadiyala Wa'ash hadu Allah
ilahalillahu Wa'ash hadu anna Muhammadu Abduhu warasulu amma ba'ad faya Ikhwatul musulmi
Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu”_.

Suka amsa da.

“Wa'alaikum Salam warahmatullah wabarkatuhu”.

Ya numfasa tare da kallon Moddibo da idanunsa ke lumshe sai kuma ya gyara zamansa kana yace.

“Duk kan yabo da godiya su tabbata ga Allah subhanahu wata'ala mai kowa mai komai daya sake nuna
mana wannan wata mai cike da falala da kuma rahma Allah ya nuna mana ƙarshen sa lafiya kamar yanda
ya nuna mana farkon sa Awancan shekarar mun tsaya aƙarshen Suratul Jinni insha Allah yau zamu ɗaura
acikin Suratul Muzammil Aramma jeka cikin suran muji mai Allah yace”.
Gyaɗa kai Moddibo yayi tare da gyara zamansa cikin nutsuwa da sanyin Muryansa tare da kamala kana
yayi A'uziyya tare da basmala ya fara kamar haka;.

_“1-Ya Ayyuhal Muzammil,2-Ƙumullaila illa ƙaliliah 3-Nisfshu awinƙus minhu ƙalila”_

Atake masallacin yayi tsit tamkar babu mahalukin dake numfashi yayin da karatun ke ratsasu.

Shikuwa M Jameel Kai ya gyaɗa da faɗin.

“Yawwa Aramma ci gaba mai Allah yake cewa acikin aya ta gaba”.

Jinjina kai Moddibo yayi tare da manna bayansa da jikin kujera ya cigaba da cewa.

_“4-Auzidhu alaihi warartilill ƙur'ana tartila5-Inna sanulƙi alaika ƙaulan sakila”_.

Numfashi M Jameel yayi kana yace.

“Suratul Muzammil Makiyya ce tana da ayoyi guda ashirin.

Ya numfasa tare da lumshe idanunsa kana ya cigaba da cewa.

“Suratul Muzammil tana karantar da tarbiya da juriya ga Muslimi,domin susami damar tsayuwar da
umarnin Allah”.

Still wajen yayi tamkar babu mahalukin dake numfashi jama'ar dake wajen su tattara duk kan
nutsuwarsu suna sauraron abinda Allah yace Moddibo kuwa System ɗin gabansa ya zubawa Idanu tare
da lumshe idanunsa.

M Jameel ya numfasa tare da cewa.

_“Ya Ayyuhal Muzammil,Ma'ana ya kai wanda ka lulluɓa da mayafi”_

Atake masallacin ya kaure da kabbara suna faɗin.

“Allahu akbar, Allahu akbar Allah yakareka Malam”.

Zama M Jameel ya gyara tare da kallon jama'ar bayan sunyi shiru ya ɗaura da cewa.

_“ƙumillayla illa ƙalila,katsaya domin yin Sallah acikin dare(suka) face kaɗan”._

Nanma kabbara suka sake kaurewa dashi.

Shi kuwa M Jameel numfashi ya sauƙe kana ya cigaba da fadin.


_“Nisfshu awin minƙushu ƙalila,Rabinsa ,ko ka rage Abu kaɗan daga gareshi._

Haka suka cigaba da tafsirin ayoyin.

Ƙarfe ɗaya dai-dai suka tashi ɗaya da kwata sukayi Sallar azahar zama sukayi acikin masallacin suka fara
Muraja'a tun daga suratul tauba zuwa Nahal jin kiran la'asar yasa suka dakata kana suka tashi Moddibo
ne yaja Sallar M Jameel kuwa shi yayi ladanci bayan sun idar ne suka fita kai tsaye masallacin dake
Unguwar su Moddibo suka nufa ƙarfe biyar suka fara gabatar da tafsirin acikin suratul hujurat wannan
kuma na maza ne zalla ƙarfe shida dai-dai suka tashi.

Bayan sun tashi M Jameel yashiga mazaunin Driver Moddibo kuwa gefen mai zaman banza ya zauna tare
da lumshe idanunsa yana sakin numfashi Kallonsa M Jameel yayi tare da murmushi kana yayiwa motar
key.

Wayar Moddibo ne ya hau ruri Anutse ya sanya hannu ya ɗauka ganin sunan Ummi yasa ya gyara
zamansa cike da nutsuwa yayi Picking tare da Sallama kana yace.

“Ummi ina yini”.

Daga ɗaya ɓangare cike da so da kulawa Ummi tayi murmushi kana tace.

“Babana".

Moddibo ya amsa da.

“Na'am Ummina”.

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.

“Babana sannuku da ƙoƙari nasan yanzu baki da hutu Ramadan ya shigo”.

Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.

“Ga munan dai kam Ummi muna fama”.

Cike da kulawa da kuma ƙaunar su tace.

“Allah sarki Allah ya biya ku Allah yaƙara rufa asiri”.

Ya amsa da.

“Ameen”.

Ummi ta gyara wayar akunnenta kana tace.

“Babana nashirya muku abin buɗa baki kuzo kusha ruwa”.


Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.

“Toh Ummi mun gode muna nan tafe yanzu ma Insha Allah zamu zo”.

Kasancewar M Jameel na Jin Komai saboda wayar a handsfree yake yasa ya juya akalar motar zuwa
hanyar gidan Ummi adai-dai ƙofar gidan Ummi M Jameel yayi hong mai gadi ya buɗe musu suka shiga...!

Yau dai ba editing. Dan muna cikin hidiman bikine

By

*GARKUWAN MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_Page 15_

_NA_

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*Saura ƙiris FREE PAGE dai yazo ƙarshe in sha Allah mun kusa gamawa. Yar uwa ki biya ki karanta cikin
Aminci domin littafin SAKAYYAH na kuɗine 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai
ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP. 09097853276. Kana in saki a Groups ɗin da zamuci gaba da
posting.*
*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son
k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman
lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun
matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa
ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki
tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones
dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da
tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da
ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda
ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya
wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka
kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki
da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp
in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta,
muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina
nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a
ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.

0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta
wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije
gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.

GARKUWAR MA'AURATA
Anutse Moddibo da M Jameel suka fito daga motar dai-dai lokacin da Malam Ahmad ya fito daga
harabar gidan ganinsu yasa ya faɗaɗa fara'ar fuskarsa tare da faɗin.

“A'a Masha Allah tagwayen Ummi kunzo?”.

Murmushi sukayi Atare kana suka ƙara sa kusa dashi.

Kallonsu Malam Ahmad yayi fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace.

“Sannunku da zuwa ku isa daga ciki zan dawo mu gaisa”.

Kai suka gyaɗa masa atare kana suka nufi haraban cikin gidan shi kuma ya fice.

Bakin su ɗauke da Sallama suka shiga farfajiyar gidan,

Kusan a tare suka juyo suka kalli juna lokacin da idanunsu, ya sauƙa akan shimfiɗar ƙaton taburma da
Ummi ta shimfiɗe asaman baranda kana ga wani lallausan Chanis capet dake fitar da ƙamshi da wasu
manyan tuntuna guda uku ɗaya na tsakiya biyu na gefe da gefe sai manyan tire guda huɗu akai tiren
farko na kayan fruit ne kama daga,Tuffa, Inabi, Gwanda, Dabino, Abarba, Ayaba, Kankana, Lemo duk anyi
slinzing ɗinsu.

Ɗaya tiren kuma Flaks ɗin tea ne da ma dai-dai-tan kofina masu kyau sai gongomin madara da Bounvita.

Sai kuma ɗayan dake ɗauke da Flaks din kunu agefe, sai kuma na ƙarshe wanda yafi su girma manyan
kulo-line masu kyau kula na farko Perpesoup ɗin jan naman rago ne daya dahu ligif yana fitar da ƙamshi
sai ɗaya kulan kuma soyeyyen dan kalin ne da ƙwai gwanin ban sha'awa.

Jin Sallamar sune yasa Ummi saurin fitowa daga falo tare da faɗaɗa fara'ar dake Samar fuskarta kana
tace.

“Lale marhaba sannunku da zuwa Babana”.

Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙara masa kyawun fuskarsa kana ya lumshe idanunsa
tare da faɗin.

“Barka dai Ummina”.

M Jameel kuwa baki ya tura cike da Shagwaɓa kana ya langwaɓar da kai Idanunsa akan Umminsa sai
kuma ya kalli Moddibo dake ƙoƙarin zama akan shimfiɗar da Ummi tayi kana yace.

“Ni dai gaskiya na fara kishi Ummi mai yasa tun da har haka kike son Aliyun nan bakisa min sunan
Babban naki ba nima ki riƙa cemin Babana?”.

Murmushi Ummi tayi Idanunta akansa ta zauna kana tace.

“To ai kaima Babana ne ko ka manta Kai takwaran kakan kane Baban-Babanka.


Dariya mai sauti yayi kana ya shafa sajensa tare da cewa.

“Ƙwarai kuwa haka Abbana ke kirana da Babana munyi raba dai-dai Ummi ta kiraka da Babanta Ni kuma
Abba na ya kira ni da Babana”.

Gyaɗa kai Moddibo yayi cikin yanayin sanyin Muryansa ya Kalli M Jameel kana yace.

“Oho dai amma nine na hannun daman Ummi”.

Murmushi Ummi tayi cike da ƙaunarsu kana ta zauna daga gefensu Idanunta akan Moddibo dake motsa
bakinsa idanunsa alumshe alamar tasbihi yake.

Ganin haka sai ta miƙe dan kar ta takura masa ta ɗan ɗaga sautin Muryanta tare da cewa.

“Bashir ga Yayanka sun zo baka zo kun gaisa ba”.

Cike da ladabi Bashir ya fito kana yace.

“Ummi kaya na nake gyarawa yanzu nake so in fito”.

Ya Ida maganar tare da zama agefen Moddibo kana yace.

“Yaya Moddibo ina wuni ya Ibada?”.

Moddibo kuwa buɗe idanunsa dake lumshe ya buɗe tare da ɗaura hannunsa akan Bashir yana shafawa
kana yace.

“Lafiya lau Alhamdulillah ya karatu?”.

Bashir ya amsa da.

“Alhamdulillah”,Kana ya maida kallon sa kam M Jameel dake motsa baki da alama shima tasbihi yake ya
kallesa tare da cewa.

“Yaya Jameel Ina wuni ya ibada?”.

M Jameel ya Amsa da.

“Alhamdulillah”.

Miƙewa Bashir yayi ya koma ya cigaba da aikin da yake.

Moddibo kuwa bayan yayi tasbihi sai ya koma Azkharul masa ƙarfe shida da minti Ashirin da biyu aka
kira Sallar maghariba Plate din Dabino da Ummi ta ajiye musu agabansu Anutse Moddibo ya miƙe tare
da ɗaukan ruwa ya kuskure bakinsa kana ya dawo ya zauna.
Shima M Jameel miƙewa yayi ya wanke bakinsa dabino Moddibo ya ɗauka ya buɗe sanan ya sanya
abakinsa bayan ya furta.

“Zahabazzaba'u Wabitallatil,Uruƙu wasu batul Ajri Insha Allah”.

Anutse ya ke cin dabinon inda yaci sai ya sanya ƙwallon atafin hannunsa na hagu.

Guda bakwai yaci kana ya dakata.

M Jameel kuwa dabino Uku yaci kana ya janyo faranti kayan friut ɗin ya fara da Abarba.

Lumshe idanu Moddibo yayi tare da ɗaukar Inabi ya kai bakinsa sai kuma ya buɗe Idanunsa akan Ummin
data ƙara so wajen zama tayi tare da tsirawa M Jameel idanu baki ɗaya hankalinta da nutsuwar ta yana
kansa.

Iska Moddibo ya furzar daga bakinsa tare da jingina bayansa da jikin bangon ya lura da tun zuwansu
wani irin kallon da Ummi ke bin M Jameel dashi kallone mai nuni da tsantsar so, da kuma ƙauna da
shaƙuwa irin wanda uwa ke nunawa ƴaƴan ta.

Ƙasa da kansa yayi yayin da yaji ruwan hawaye masu ɗumi na tsata-tsafo masa saboda ganin shi ya rasa
wannan damar bazai samu irin wannan ba arayuwarsa ba still Kansa na ƙasa ba tare daya ɗago ba ya dai-
dai-ta muryarsa tare da faɗin.

“Ummi kiyi buɗa baki mana”.

Sai asannan Ummi ta lura da kallon da take bin M Jameel dashi, Malam Ahmad ma murmushi yayi domin
ya lura da kallon da Ummi kebin M Jameel dashi Shikuwa M Jameel sai alokacin ya ɗago kansa ya lura da
irin kallon da Umminsa ke binsa dashi.

Murmushi yayi mai cike da so da ƙauna.

Kana yace.

“Ya dai Ummina nayi kyaune ko muni kike ta kallona?”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta ɗan lumshe Idanunta tare da girgiza kai kana tace.

“A'a kawai dai naga azumi ɗaya akayi ana biyu har ka rame”.

Murmushi yayi tare da gyara zamansa kana yace.


“Hmmm Ummi kenan ai kinga mu ba azumin ne kaɗai ba. akwai yawon zirga-zirga sannan abincinma
bama nutsuwa mu cisa yanda ya kamata musamman ma idan na biyewa Babanki”.

Jinjina kai Ummi tayi kana tace.

“To yau kam anan sai kunci kuncika cikin ku sannan in dafa muku na Sahur ma ku tafi dashi”.

Girgiza kai Moddibo yayi kana cikin sauri yace.

“A'a Ummi ki zauna Innayi na mana sannan ga can Asma'u na taya ta yanzu idan mun koma sai mun rasa
inda zamu sanya abincin a cikinmu”.

Jinjina kai tayi kana tace.

“Toh shikenan Babana”.

Murmushi Moddibo yayi kana yace.

“Ummi kici abinci mana”.

Kai ta gyaɗa sannan ta janyo Plate ɗin dabinon ta ci guda uku Bayan tayi addu'ar buɗa baki.

Malam Ahmad ma danino uku yaci sannan Ummi ta ɗauki Flaks da niyyar haɗa musu tea Moddibo dake
cin friut yayi saurin cewa.

“A'a Ummi bari sai munyi Sallah”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Toh shikenan sai kun dawo”.

Miƙewa sukayi M Jameel da Moddibo suka ɗauki buta kana suka ɗaura alwala suka fice Malam Ahmad
kuwa ya riga su fita.

Kai tsaye masallacin ƙofar gidan su Ummi da Baban Asma'u ke limancin suka shiga. Suna idar da Sallar
Maghariba bayan sun idar suka dawo cikin gida shigowarsu yayi dai-dai da rurin da wayar M Jameel keyi.

Kallon Moddibo M Jameel yayi kana yace.

“Innayi ce ke kira”.
Jinjina kai Moddibo yayi tare da cewa.

“Uhm”.

picking call din yayi ya kai kunnensa.

Daga ɗaya ɓangaren Innayi tayi gyaran murya kana tace.

“Jamilu lafiya baku dawo kunyi buɗa baki ba mai kuke yi har yanzu awaje?”.

Sajensa ya shafa kana yace.

“Innayi wallahi Ummi ce ta riƙe mu wai saidai muyi buɗa baki agidan ta”.

Murmushi Innayi tayi kana tace.

“Toh mu kuma na gidan mu ya zamu yi dashi”.

Kallon Moddibo yayi sai kuma yayi Murmushi kana yace.

“Innayi abawa Almajirai dai sai kibar mana na Sahur dan nasan kinyi miyarki mai daɗin nan miyar me
kika mana ma tukunna?”.

Dariya Innayi tayi kana tace.

“Miyar roman da kake so na daddawa da ƙarago shi zanyi muku na Sahur”.

murmushi ya saki tare da faɗin.

“Yauwa ina son wannan miyar”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Toh shikenan sai kun dawo ka gaishe da Ummin”.

Ta faɗa tare da katse kiran.

Suna ida shiga gidan suka samu wajen suka zauna Ummi ta miƙe tare da ɗaukar Flaks da kofina ta haɗa
musu tea mai kauri yana tururi kana ta zuba musu soyeyyen dankali da ƙwai.

Anutse suka fara ci kaɗan Moddibo yaci ya janye hannunsa daga ciki.
Kallonsa Ummi tayi kana tace.

“Ya dai Babana kaci mana”.

Murmushi Moddibo yayi tare da ɗaura hannunsa na dama akan shafefen cikinsa ya shafa kana yace.

“Ummi na ƙoshi”.

Girgiza kai Ummi tayi tare da cewa.

“Kai Babana me ma kuka ci?”.

Ɗan kwaɓe fuska yayi kana cikin sanyin murya mai kama da shagwaɓa ya lumshe idanunsa tare da cewa.

“Ummi kar muje muna sallah abinci yan fitowa ta hancin mu”.

Kallonsa Ummi tayi tare da murmushi kana tace.

“A'a Babana me ma kuka ci da zai zazzago ta hancinku?”.

Murmushi yayi tare da shafa sajensa zuwa gemunsa kana yace.

“Allah Ummi mun ƙoshi ko ba haka ba J?”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare da Hararan Moddibo ya cire hannunsa a Plate din dan kalin.

Hira suka sake taɓawa kana Moddibo ya miƙe tare da kallon Ummi kana yace.

“Ummi zamu tafi”.

Jinjina kai Ummi tayi tare da cewa.

“Idan kunyi sallah Isha'i zaku dawo ta nan?”.

Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.

“A'a Ummi sai wani lokaci”.

Gyaɗa kai tayi tare da cewa.

“Toh ku tafi da kunun nan”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da gyara tsayuwar sa kana yace.

“Toh Ummi ina son kunun abamu zan tafi dashi”.


M Jameel ya juya ya kalli Ummi tare da langwaɓar da kai kana yace.

“Ummi Ni dai ba abani abinda nake so ba”.

Cike da kulawa da kuma so ta juya ta kallesa kana tace.

“Me kake so?”.

Murmushi yayi kana yace.

“Inabin za'a bani in tafi dashi”.

Saurin Kallonsa Moddibo yayi sai kuma ya juya ya kalli Ummi tare da cewa.

“Ummi kar ki basa yasha muna dashi agida”.

Tura baki M Jameel Yayi kana yace.

“Iyeee to na haƙura tunda ba aso ayimin kyautar”.

Ummi Kam murmushi take Cike da ƙaunar su, ji takeyi tamkar su duka biyu a cikinta ta rainesu ta
haifesu.

Sallama suka mata kana suka fice suka shiga mota Moddibo ke mazaunin Driver yayin da M Jameel ke
gefen mai zaman banza kai tsaye Masallacin da suke limancin na ƙofar gidan Sarki suka nufa sunyi tafiya
mai ɗan tsayi kafin suka isa lokacin da suka isa ankira sallar Isha'i suka shiga Moddibo ne yayi limanci
suka idar da Isha'i kana sukayi Asham bayan an watse kana suka fito suka shiga mota wannan karon M
Jameel ke driving Kai tsaye gidan Innayi suka wuce.

Ƙarfe takwas da rabi suka isa gidan bayan sunyi parking sun fito kai tsaye sashen Innayi suka shiga
bakinsu ɗauke da sallama a farfajiyar gidan suka tarar da Innayi da Asma'u zaune Innayi dake gashin
nama akan mangal da tarin gawayi agefenta ta daga kanta tare da Kallonsu kana ta amsa Sallamar su.

Ƙara sawa kusa da ita sukayi M Jameel yaja kujera ya Zauna kana ya Kalli Innayi tare da cewa.

“Innayi ya dai mai ake gasa wasa ne?”.

Murmushi Innayi tayi kana tace.

“Nama nake dan gasawa nasanku da cin nama kamar kuraye!”.

Dariya M Jameel Yayi kana yace.

“Aikam Innayi kin kyauta gashi asalin gashi na gargajiya kike yi”.
Kai ta gyaɗa tana ɗaukar Plate tace.

“Eh ai nasanku”.

Ta ida maganar tare da miƙa musu naman data yayyanka ta zuba a Plate tare dasa musu yaji agefe
sannan ta yaryara ɗa musu man shanu.

Kallon Asma'u dake yi musu sannu da zuwa tayi kana tace.

“Asms'u ɗauko musu capet su zauna”.

Cikin murza kai gefen dama da hagu Modibbo yace.

“Uhmm Innayi kin dai sanshi shi J ɗinki da son nama kamar kura”.

Murmushi M Jameel yayi dan yasan tabbas Modibbo bai cika damuwa da namaba, asalima in dai
gasheshene ko soyayya in dai yaci yanka huɗu zuwa biyar zaice muƙa-muƙinsa sun gaji da taunawa, in
kuma dafaffene wani lokaci da haƙorin gaba zai ɗan tattauna in yaji ya gaji sai ya tura masa naman
gabansa.

Shi kuwa M Jameel Allah ya sani yana masifar son nama, shi kuwa Moddibo yafi bawa ƴaƴan itatuwa
mahimmanci.

Cikin murmushin yace.

“Yoh in ban so namaba me zanso A.J Namafa shine maƙurar daɗi”.

“A wurinka ba, gashi kuma kana son koyamin”.

Cewar Moddibon,

Asma'u kuwa ganin Innayi na kallonta cikin mamakin tace.

“A'a Asma'u ɗauko musu abin zama mana”.

Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta shiga falon ta ɗauko capet ɗin ta shimfiɗa musu awajen da yake
agyare tass babu alamar ƙazanta.

Zama sukayi akai, Innayi ta sake kallon Asma'u tare da cewa.

“Haɗa musu Tea sannan kisa musu zuma yaji”.

Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta zuba musu shayi tare da zuba wadataccen zuma aciki ta kawo musu.

M Jameel kuwa Anutse ya kai yankan naman bakinsa lokaci ɗaya ya lumshe idanunsa tare da buɗe su
akan Innayi kana yace.
“Kai gaskiya gashin nan yayi daɗi sosai”.

Murmushi Innayi tayi tare da kallon Moddibo dake cin naman kamar ko yaushe kamar dai dole, yana ɗan
taunawa kaɗan-kaɗan cikin kula tace.

“Kai kuma fa Moddibo?”.

Ɗago kansa yayi ya kalleta kana yace.

“Uhm yayi”.

Girgiza kai tayi kana tace.

“Wato kai dai baza ka iya Yabawa ba kenan?”.

Kansa ya sake ɗagowa tare da kallonta kana yace.

“Ai gashinan J ya yaba kuma danɗanon harshen mu ɗaya ne ai”.

Murmushi M Jameel da Asma'u sukayi.

Innayi kuwa baki ta taɓe M Jameel da Moddibo suka cigaba daci Ahankali Moddibo ya ɗago hannunsa
tare da kallon tsadedden agogonsa kana ya mayar da Kallonsa kan M Jameel tare da cewa.

“Sai munyi sauri lokaci ya kusa J”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cire hannunsa a Plate din kana yace.

“Toh shikenan mu tafi”.

Miƙewa Moddibo yayi tare da kallon Innayi kana yace.

“Bari naje na canza kaya”.

Daga haka ya juya ya nufi sashen sa, shima M Jameel bayansa yabi.

Moddibo nashiga Bedroom ya sauya kayansa zuwa Jallabiya Coffee color tare da ɗaura farin hirami irin
na samarin larabawa kana ya feshe jikinsa da turarukansa masu daɗin ƙamshi.

Anutse ya fito falo ya samu M Jameel da shima ya canza kayansa buɗe fridge M Jameel Yayi ya ɗauki
goran faro mai sanyi sannan suka jera tare da Moddibo suka sauƙa.
Kai tsaye sashen su Innayi suka koma batare da sun shiga farfajiyar gidan ba .

“Toh Innayi mun tafi”.

Cewar M Jameel

Tana rufe roban yajin da suka ci nama dashi ta ajiye kana tace.

“Toh Allah ya tsare muma yanzu muna bayanku”.

M Jameel na gyara ɗaurin agogon dake tsintsiyar hannunsa ya kalleta kana yace.

“Toh idan za kuje kuzo mu tafi mana sai mu sauƙe ku”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“Ai akwai Napep zamu hau”.

M Jameel kuwa kai ya Girgiza kana yace.

“A'a ai abin baiyi ba bayan tanan muke tafiya kuma kuce zaki shiga Napep kawai kuzo mutafi”.

Jinjina kai Innayi ta gyaɗa kana tace.

“To bari mu tattara da sauri sai mu tafi”.

“Toh”,M Jameel yace Shi kuwa Moddibo bai ce komai ba sai harɗe hannunsa da yayi aƙirji.

Cikin sauri Innayi da Asma'u suka tattare wajen sannan suka sanya hijabansu kana suka rufe kichen da
gidan suka fice abayan Mota suka zauna ita da Asma'u yayin da M Jameel da Moddibo ke gaba.

Suna isa babban masallacin M Jameel yayi Parking Innayi da Asma'u suka fita suka nufi sashen mata su
kuma suka shiga cikin masallacin daya cika sosai da al'umma.

Bayan sun zauna Kamar ko yaushe M jameel ya buɗe musu da addu'o'in kana Moddibo ya gyara system
ɗin sa tare da ƙara rage girms Idanunsa kana yasa lallausan tafin hannunsa ya gyara zaman microphone
din dake gabansa tare dayin gyaran murya cikin sanyayyar sautin muryansa ya fara kamar haka:

_“Auzubillahi Minal Shaiɗanir Rajim, Bismillahir Rahmanir Rahim.


(10) Innalazina ya'akuluna, Amwalal yatama zhulman innama ya'akuluna fiy buɗunihim
naraa,wasayaslauna sa'irah”._

Jama'ar dake wajen masallacin cikin sassarfa suka ƙaraso cikin masallacin dan basa so koda harafi ɗaya
ne su rasa daga cikin karatun Moddibo saboda baiwar muryarsa.

Moddibo kuwa sanyayyar numfashi ya fesar tare da jingina bayansa da kujeran kana ya cigaba kamar
haka:

_“(11)Yusikumullahu fii auladikum,Lilzikri mislu hazzil unsaynan.Fa'in kunna Nisa'a fauƙasnatayni


falahunna sulusa ma tarak,Wa'in kanat wahidatan falahannisf,Wali abwayhi likulli wahidin
Minhumassudusu,Mimma taraka inkana lahuu waladun,Fa'in lam yakun lahu waladu wawarisahuuu
abwahu fali ummihi sulus.Fa'in kana lahu Ikhwatun fali ummihi sudus min ba'adi wasiyyatin yusi biha
audayn,abaukum wa'abna ukum latadruna ayyuhum aƙrabuna lakum naf',a,Faridatan Minallah,Innalaha
kana aliman hakima”._

Ya dire ayar tare da jan numfashin sa da ya riƙe.

Jinjina kai M Jameel Yayi yayinda ayoyin ke ratsa sa cikin yanayin sakewa ya lumshe idanu kana yace.

“Aya ta gaba”.

Jinjina kai Moddibo yayi kana cikin zazzaƙan muryansa mai sanyi da ratsa jiki kana da nutsuwa ya cigaba
da jan ayoyin saida ya kai aya ta Ashirin kana ya tsaya.

Shi kuwa M Jameel Cike da tsantsar ƙwarewa da nutsuwa kana da sanin makaman tafsir ya fara fassara
ayoyin tare da cikekken kaddima da kowa amintattun haɗisai da suka da munasaba da ayoyin harma da
sababul nuzur na ayoyi, lokacin ɗaya cikin masallacin ya sake samun nutsuwa tafsirin na ratsa su.

Ƙarfe goma dai-dai suka tashi tafsir ɗin mata suka fara fita ta ɓangarensu kafin maza suka fita acikin
mota Asma'u da Innayi suka jira M Jameel da Moddibo goma da kwata dai-dai suka fito suka tafi.

Acan ɓangaren Khausar kuwa yauma kamar kullum taje tafsiri ita kaɗai ta dawo duk da masallacin a
ƙofar gidansu yake bakinta ɗauke da Sallama tashiga cikin falonsu Anutse ta cire hijabinta tare da nufar
kichen inda take jiyo motsin Mommyta kasancewar yau itace da girki yasa ko tafsir bata jeba.

Juyiwa Mommy tayi jin motsi abayan ta ganin Khausar yasa ta maida hankalinta kan aikinta kana tace.

“Kin dawo?”.
Kai Khausar ta gyaɗa tana kallon tuƙeƙken tuwon shinkafa da Mommy ke kwashe maran ƙarshe.

Ahankali Khausar ta matsa kusa da Mommy kana tace.

“Mommy ki bari zanyi miyar”.

Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.

“Ok to Miyar zogala za kiyi”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da ɗaukar.

Da fara aikin haɗa miyar zogalen.

Cikin abinda bai gaza awa ɗaya da rabi ba, duk ta haɗa ta sanya komai na buƙata kana.

Ta rufe nan danan kichen ɗin ya kaure da ƙamshin miyar sauran kayan da Mommy tayi amfani dasu ta
haɗa ta wanke tare da sauƙe Miyar ganin tayi tik gwanin kyau.

Bayan ta gama ta buɗe miyar da yayi mugun kyau a ido ta ɗauki kular wani sashe ta zuba miya
kasancewar babban gidana yasa kowa kaina nasa akeyi, na buɗa baki kuwa ki wacce a side ɗinta takeyi,
mai girki zata sawa Lamiɗo, da Dadu, haka tsarin nasu yake.

Shigo wa Mommy tayi fuskarta ɗauke da murmushi ta kalli yanda kichen ɗin yayi fess ga ƙamshin miyar
zogalan da yaki kifi da naman dariko, kallonta ta mayar kan Khausar kana tace.

“Sannu da ƙoƙari ki ɗauki na sashen Hajiya Bunayya ki kai mata”.

Kai Khausar ta gyaɗa sannan ta ɗauka kular Hajiya Bunayya ta wuce Haidar Mommy ta ƙwalawa kira
bayan yazo tace ya ɗauki kular sashen Gimbiya Dadu ya kaimata dan Mommy tunda ta lura da Khausar
batason zuwa yasa ta rage aikanta sashen shi kuwa Haiydar daga sashen Gimbiya Dadu ya wuce sashen
Hajiya Bunayya.

Hajiya Bunayya dake zaune akan kujera ta faɗaɗa fara'ar fuskarta ganin Haiydar ta tsira masa idanu kana
tace.

“Babana kaine dama yanzu nake niyyan zuwa in yi maka albishir”.

Murmushi Haidar yayi tare da zama kana yace.

“Daga sashen Gimbiya Dadu nake nace bari nazo na gaishe ki”.

Murmushi tayi masu cike da Ma'anoni tayi kana tace.


“Insha Allah bayan sallah mashin ɗinka zai zo kaga dama tun shekara biyu baya naso saya maka
Abbanka yace saika ƙara girma kuma kaga yanzu aika girma”.

Jinjina kai Haidar yayi cike da tsananin farin ciki mara mistuwa ya gyara zamansa kana yace.

“Nagode Ummah Allah yarabaki da sharrin maƙiya”.

Murmushin gefen baki tayi kana tace.

“Bana son godiyar nan Babana”.

Cike da farin ciki ya miƙe ya nufi sashen su fuskarsa ɗauke da murmushi ya shiga falon zaune ya samu
Mommy da Khausar.

Kallonsa Mommy tayi kana tace.

“Ina ka tsaya?”.

Zama yayi daga gefen Khausar still.

Fuskarsa da murmushi da yakasa ɓoyewa ya numfasa tare da cewa.

“Mommy Machine ɗina ya Kusa isowa fa, kinga tun shekara biyu baya Umma taso siya min shine Abba
ya hanata yace saina ƙara girma ai yanzu kam dai na sake girma bazai hana ba ta saya min Machine sabo
mai kyau bayan sallah zai iso”.

Khausar kuwa tunda ya fara magana ta tsira masa idanu saida ya kai aya ta sauƙe ajiyar zuciya mai zafi
tare da furzar da iska daga bakinta kana babu walwala afuskarta ta kawar da kanta gefe tare da cewa.

“Kai kuma farin ciki kake ko?”.

Juyawa Haiydar yayi tare da kallon ta kana yace.

“Sosai ma kuwa kema kamata yayi kije kiyi mata godiya”.

Harara Khausar ta ɓalla masa.

Murmushi Mommy tayi kana tace.

“Rabu da ita ai ni zanje.

A yanzu kam aika girma yanda kake da tsawon ƙafan nan”.


Murmushi yayi tare da kallon Khausar kana yace.

“Sosai ma Mommy ai yanzu na girma yanzu fa shekara kusan sha shida nake nema gashi mai shekara sha
takwas ɗinma na fita koda yake sha bakwai ne da yan watanni ne ko gareta”.

Jinjina kai Mommy tayi kana tace.

“Ai lallai dai kam kama cika sha shida kam Allah yasa kafara hawa asa'a.

Ubangiji ya tsareka da sharrin ƙarfe.

Allah yatsare gabanka da bayanka!.

Ubangiji ya makantar da idanun makiyan ka akanka!.

Allah ya tsare ku ga duk kan abinda zai cutar da rayuwar ku! Allah ya muku katangan ƙarfe da dukkan
abin da zai zama sharri acikin rayuwarku!”.

Cike da jin daɗin Addu'ar ta Haiydar yayi Murmushi tare da cewa.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum Mommy na”.

Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da kallon Mommy kana tace.

“Ameen ya Allah Mommy tunda kinyi addu'a magana ta ƙare baza'a ji tsoron komai ba babu bakin uwa
akansu duk kan mai sharri zaiyi ya gama babu abinda zai sameshi da izinin Ubangiji”.

Murmushi Haiydar yayi tare da kallon Khausar kana yace.

“Aikam Addah Khausy babu bakin uwa akaina duk kan wani mai mugun nufi zai ƙare akansa”.

Murmushi Mommy tayi cike da ƙaunar ƴaƴan nata,

kallon ta ta mayar kansu tare da cewa.

“Ku tashi kuje kuyi bacci dan mu samu mu farka da wuri mu kaiwa Ubangiji bukatun mu”.

Miƙewa sukayi tare da yiwa juyawa sai da safe kana kowa ya wuce ɗakinsa ya kwantar.

Misalin ƙarfe ɗaya na dare Mommy ta farka kallon Lamiɗo daya miƙe yashiga toilet tayi sai kuma ta miƙe
ahankali ta tafi side ɗinta.

ɗakin Khausar tashiga tare da kunna haske.


Idanunta suka sauƙa akan Khausar dake sharan bacci ƙara sawa tayi tare da bubbuga ƙafarta kana tace.

“Khausar ki tashi kiyi nafilla”.

Ahankali Khausar ta buɗe Idanunta cikin Muryan bacci ta kalli Mommy kana ta yunƙura ta zaune bakinta
ɗauke da addu'a tace.

“Toh Mommy”,Sannan ta Sauƙa ta shiga toilet.

Juyawa Mommy tayi ta koma ɗakin Lamiɗo lokacin data shiga har ya fara Sallah kai tsaye toilet ta shiga
ta ɗaura Al'wala bayan tayi ta fito tare da shimfiɗa Sallaya ta tada Sallah cikin nutsuwa ta keyi bayan tayi
sujja tayi Subhana Rabbiyal a'ala³ kana ɗaura da du'inta.

“Ya Allah kayuwa ƴata zaɓin alkhairi,Ya Allah kashirya Khausar kasata ahanya madaidaiciya Ya hayyu ya
ƙayyum ka tsare mata imaninta, Ya Allah ka kare min Haiydar ɗina ya Allah katsaresa daga sharrin mai
sharri ya Allah ka kare min ita ya Allah kabawa Ramadan da Raudat ilimi mai albarka da yayunsu dama
dukkan ƴaƴan musulmai. Ya Allah katsare min ƴaƴana daga sharrin,Mutum, aljan da kuma ƙarfe, ya Allah
katse min imanina Allah ka tsaremin zuciyoyinsu, ka tsaresu da sharrin hassada, ƙeta, munafurci, da
ƙyashi ya Allah ka kare min mijina kabiya masa buƙatunsa na Alkhairi dama ɗauka cin al'ummar
musulmai.

Bayan ta idar da nafillah ta ɗauki Alkur'ani ta shiga Muraja'a.

Khausar kuwa ƙarfe biyu da rabi bacci ya riƙa fisgarta akan Sallaya ta kwanta nan da nan bacci mai nauyi
yayi nasarar ɗauke ta.

Can cikin baccinta ta fara wani mafarki mai cike da al'ajabi ganinta tayi.

Gata nan tsaye a wani ƙaton fili.

Baki ɗaya ilahirin filin ashare yake kuma , yashine malale a wurin iya ganinka sai wani irin haske mai
masifar ƙyalli da ɗauke idon da ya cika wajen baki ɗaya, ahankali ta ɗaga kanta ta fuskanci gabas, da
sauri ta rumtse idanunta gani wata ya fito ta gabar juyawa tayi taga yamma da sauri Still nan ya fito ta
yamman sake juyawa kudu tayi still ta nan ma ya fito ahankali ta sake juyawa arewa, wani irin masifeffen
karkarwa jikinta ya farayi, ganin tanan ma watan yafito duk kusurwa huɗu wata ya fito sai asannan ta
lura da haskensa ne yake ɗauke mata ido.

Ahankali taga wani kyakkyawan.

Yaro fari ƙal agabanta yayinda gashin kansa ke kwance lib-lib, daga bayansa ta hango wani kyakkyawan
mutum sai dai fuskarsa na kallon gefe hannunsa na kan yaron yana shafawa cikin wata.

Sanyayyar murya yake kallon yaron kana yace da ita.


“Wannan shine jininmu mahaɗinmu, wannan shine sanadin haɗayyarmu bugun zuƙatanmuuuhh”.

Ya ƙarasa jan kalmar cikin wata iriyar ƙasalalliyar murya mai cike da shauƙi.

Ita kuwa ƙoƙari take taga fuskar mutumin sai dai ta kasa sai iya fuskan kyankyawan yaron take iya kallo.

Dai-dai lokacin kuma ta buɗe Idanunta jin Muryan Mommy nacewa.

“Khausar, Khausar ki tashi zaki makara fa ƙarfe huɗu tayi bakiyi Sahur ba anjima kaɗan zaki fara ce mana
kin fara jin wahalar azumi”, Ta faɗa tana buga ƙafarta da saurin Khausar ta tashi zaune tare da sakin
ajiyar zuciya kana tace.

“Innslillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin Astagfirullah wa'atubu ilaik”.

Sai kuma tayi addu'a ta shafa.

Mommy dake tsaye har yanzu kuwa sake taɓata tayu tare da cewa.

“Khausar kada ki koma bacci fa kitaso”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Mommy na tashi bazan koma ba”.

Juyawa Mommy tayi ta fice ita kuma Khausar toilet ta shiga.

Brush tayi kana ta fito kai tsaye falon ta nufa.

Samu tayi Mommy ta haɗa mata ɗumamen tuwon jiya da Tea mai kauri ahankali ta zauna tare da kai
tuwon bakinta da ƙyar ta haɗiye baki ɗaya jikinta yayi mugun sanyi da mafarkin da tayi.

Mommy dake zaune a kujeran falon ta juya ta kalleta ganin bata cin tuwon yasa ta girgiza kai tare da
cewa.

“Kici abinci fa Khausar kin sanki sarai da cin abinci anjima kaɗan zaki fara cewa yunwa kike ji”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da fesar da iskar bakinta kallon Mommy tayi kana cikin sanyin murya ta
lumshe Idanunta tare da cewa.

“Mommy wallahi tuwon ne nakeji kamar ba zai shiga ba babu wani abu ne?”.

Kai Mommy data tsira mata Idanu ta gyaɗa kana tace.

“Kije kichen akwai indomie dana ɗaura wa Haiydar shima yace ba zai ci tuwo ba to amma ke kam nasan
indomie ba wani riƙe Miki ciki yake yi ba”.
Lumshe Idanunta tayi kana ta buɗe su akan Mommy ahankali ta motsa laɓɓanta tare da cewa.

“Bari in cisa yau ɗin kam amma Mommy da kifi ne koda nama”.

Tayi tambayar ne domin bata fiye son kifi ba.

Kawar da kai gefe Mommy tayi kana tace.

“Da kifi ne idan zaki ci kici idan kuma baza kici ba ki bari”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da jan siririn tsaki kana tace.

“Bari dai inci, tuwon ne naji kamar bazai ciwu ba shi ɗin ma miyar aida kifi”.

Mommy dai Bata sake cewa komai ba ahankali Khausar ta miƙe tashiga kichen ta ɗauki Plate ta ɗibi
yanda zai isheta kana ta fito ta zauna tare da Bismillah ta fara ci bayan ta gama ta ɗauki tea da Mommy
ta haɗa mata da bread taci.

Haiydar ne ya shigo da Sallama idanunsa akan Plate da Khausar ta gama cin indomie.

Kallonsa Mommy tayi kana tace.

“Jeka ɗebo indomie yayi sannan ka taho min da tuwo”.

“Toh",Ya amsa kana ya wuce kichen ɗin ya juye indomie sannan ya zubawa Mommy tuwon ya fito.

Khausar dai na zaune tana lumshe Idanunta tare da tuna irin mafarkin da tayi wanda ya tuno mata
wanda tayi shekaru biyu baya a Jauro Yayah.

Ahankali ta saki ajiyar zuciya tare da juyawa ta kalli Haiydar da yagama Sahur ɗin ta gyara zamanta tare
da cewa.

“Haiydar nikam yanzu wani surah kake?”.

Murmushi yayi kana yace.

“Ke ɗin wace surah kike?”.

Zama ta gyara tare da cewa.

“Hmmm aini nayi nisa ina Maryam kaga insha Allah zan samu sauƙa biyu”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.


“Toh ni ina Yasin Insha Allah zan samu sauƙa uku insha Allah duk azumi goma zanyi sauƙa ɗaya”.

Murmushi Mommy dake duba wani littafin addini tayi kana tace.

“Masha Allah yayi kyau Khausar ya akayi kika tsaya wasa ya wuce ki”.

Langwaɓar da kai tayi kana tace.

“Mommy kinga ai shi baya taya ki yin aiki nice ke tayaki aiki kinga shi duk lokacin daya keso zaiyi karatu.

Jinjina kai Mommy tayi kana tace.

“Eh haka ne da wannan dan wannan amma dai ki dage kema”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Toh shikenan Mommy zan dage insha Allah amma Mommy ke izu nawa kikayi”.

Murmushi Mommy tayi kana tace.

“Insha Allah nima zan samu uku kaman na Haiydar”.

Ware Ido Khausar tayi tare da tura madedecin bakinta kana tace.

“Insha Allah nima zan dage duk azumi goma sai nayi sauƙa”.

Jinjina kai Mommy tayi tare da faɗin.

“Aikam da kin kyauta amma sai kin rage baccin safe”.

Jinjina kai Khausar tayi kana tace.

“Insha Allah zan rage”.

Jin kiran assalatu yasa suka miƙe Haiydar ya tafi masallaci Mommy da Khausar suka shiga ɗaki suka
ɗaura alwala kana suka gabatar da sallah bayan sun idar Khausar ta zauna tayi Azkharul sabah tana
gamawa ta mike ta dawo falo ta gyara tare da sharewa kana ta fita zuwa kofar sashen nasu ta gama
share ko ina sannan ta wuce Bedroom ta kwanta kasancewar akwai mai yi musu wanke-wanke tun kafin
su shiga Sallah ta zo ta kwashe kayan ta wanke.

Ahankali azumi ya cigaba da tafiya kwanaki suna tafiya lokaci yana ja cikin ikon Allah har angama goman
farko goma na marmari inji hausawa ko?. Har an shiga goma na biyu, goma na wuya ko? Yau an kai
azumi na goma sha biyu.
Yayin da Aɓangaren Moddibo da M Jameel sunyi nisa acikin tafsirin Suratul Nisa sun fassara har zuwa
ayoyi na tamanin da tara zasu tashi akan aya na Casa'in

Da daddare Misalin ƙarfe tara M Jameel da Moddibo ne zaune acikin masallaci gaban ko wannensu
ɗauke da system da kuma roban Swan water mai sanyi Moddibo na cikin shigarsa as Usual kamar ko
yaushe Jallabiya Neavy blue kansa ɗaure da Hirami M Jameel kuwa sanye yake cikin gezner blue da
babbar riga.

Cike da nutsuwa M Jameel Yayi gyaran murya tare da hura Microphone ɗin kana yace.

Ya buɗe da addu'a kamar ko yaushe.

Lokaci guda masallacin ya kaure da kabbara tamkar zasu tsaga masallacin saboda yanayin zafin jinjinsa
da kwarjininsa cike da sakin fuska.

Ya cigaba da cewa.

“Anma ba'ad faya Ikhwatul musulmi Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu”.

Atare suka hada baki wajen cewa.

“Wa'alaikum Salam warahmatullah wabarkatuhu”.

A hankali ya numfasa tare da sauƙe nan-nauyan ajiyar zuciya kana ya dubi ɗumbin jama'ar dake zaune
acikin masallacin cikin tsantsar nutsuwa ya juyo da system ɗin gabansa kana yace.

“Acigaba da tafsirin Alkur'ani mai girma Amasallacin. Juma'a dake ƙofar gidan Mai martaba Sarki
Gembulan Lamido Bashiru zamu cigaba da tafsirin Alkur'ani mai girma acikin Suratul Nisa'i zamu tashi a
aya ta cassa'in”.

Sai kuma ya juya ya Kalli Moddibo kana yace.

“Aramma Bismillah”.

Jinjina kai Moddibo yayi tare da gyara zamansa kana ya ɗan jingina bayansa da jikin kujeran cikin
Sanyayyar muryarsa mai cike da nutsuwa da zaƙi yayi basmala kaya ya fara karanta ayoyin kamar haka;

_“(90)Illallazina Yasiluna Ilaƙaumim Bayna Kum wa Bayna hum misaƙun Auja,Ukum hasirat suduruhu an
yuƙatalalukum.Walau sha Allahu lasallaɗhum Alaikum falaƙatalukum.Fa'in'itazalukum falam yuƙatilukum
Wa'alƙau Ilaikumussalama fama ja'alallahu lakum Alaihim Sabila”._
Moddibo ya ida kai Ayar yana mai lumshe idanunsa akuma take tsikar jikinsa suka tashi yayi saurin buɗe
idanunsa tare da ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa kana ya cigaba da furta Aya ta gaba kamar haka.

_“(91)Satajidunah Akharina Yuriduna Anyamanukum Wayamanu Ƙaumahum kullamaraduu Ilalfitnatin


Urkisu fiha.Fa'in lam ya'atazilukum Wayulƙau Ilaikumussalama Wayakfuru Aydiyahum Fahuzuhum
Waƙtuluhum haysu saƙiftumuhum.Wa Ula'ikum ja'alnalakum Alaihim sulɗanammubina”._

Wani irin numfashi M Jameel ya saki tare da rintse idanunsa kana jikinsa ya ɗauki tsuma yana mai jin
fassarar Ayar na yawo Atsakiyar kansa Atake kuma zuciyarsa ta cigaba da bugawa da kaso tamanin cikin
ɗari.

Yayinda gaba ɗaya al'ummar dake cikin masallacin dama wajensa sit kakeji kamar ba mai numfashi
sabida tsananin yadda sautin karatun ke ratsa musu zuƙata da ƙoƙwale.

Shi kuwa Moddibo ya kai minti ɗaya kafin ya saki gauron numfashi gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi sabida
sanin ma'anar ayoyin da zai kawo a gaba, cikin wani irin raunin tare da tsoron Allahu wahidun ƙahhar,
gaba ɗaya muryarsa ta sake rauni cikin dakiya ya cigaba da Karanta Ayar Kamar haka.

_“(92)Wama kana limu'uminun An yaƙtula Mu'uminan Illakhaɗa'a.Waman ƙatala Mu'uminan khaɗa'a


fatahriru Raƙbatatin Mu'uminatin wadiyyatun Musallamatu Ila'ahlihee Illah An yassaddaƙun.Fa'in kana
min ƙaumin Aduwwillakum Wahuwa Mu'uminun Fatahriru Raƙbatin Mu'uminatan.Wa'in kana min
ƙaumim baynakum wa baynahum miysaƙun Fadiyyatun Musallamatun Ila Ahlihi watahriru raƙbatin
mu'uminatin.Famallam yajidu fasiyamu shahraini mutatabi'ayni taubatan Minallah.Wakanallahu Aliman
hakima”._

Wani irin nutsuwa cikin masallacin yayi musamman ma wa'anda suka san fassarar ayoyin wa'anda basu
san fassarar ba kuwa mu'ujiza ta Kur'ani ta dinga ratsasu tare da Sanyayyar sautin Muryar mai karatun.

Moddibo kuwa idanunsa ya lumshe sakamakon wasu zafafan hawaye masu ɗumi da suka cika cikin ƙarfi
ya furzar da iska mai zafin gaske Tabbas kashe ran mumini baƙaramin tashin hankali bane amma baki
ɗaya awannan zamanin an maida rai ba abakin komai ba.

Ya gyara zamansa tare da cigaba da karantar Ayar kamar haka.

_“(93)Waman yaƙtul mu'uminan Muta'ammidan Fajaza's'uhu Jahannama! halidan fiha wagadiballahu


Alaihi wala'anahu! wa'aaddalahu Azaban! Azeeymah!!!!!”_.
Awannan lokacin hawaye ne suka ciko idanun Moddibo jin irin tsananin azaban da Ubangiji ya tana
darwa duk wanda ya kashe ran mumini batare da wani hakkiba.

Walahabahu la'anar Ubangiji kana fajaza'ahun jahannamu khaleedan fiha, fa ubangiji yace kana aka
ɗaura da Azaban Azeeymah!!!, Duk wannan tanadinefa da Ubangiji yayiwa mai kashen ran mumini da
gangan.

Wani irin rawa jikin Moddibo keyi tamkar wanda aka konawa wuta a jikinsa cikin tsananin sheshsheƙan
kukan da yake son dannewa ne ya bu ɗe baki a hankali dan kawo aya ta 94 sai kuma ya juyo cikin
tsananin rauni ya kalli M Jameel da gaba ɗaya j....

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

*By*

*GARKUWAN MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_page 16_

_NA_

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*In sha Allah daga gobe zan gama free page, ƴar uwa baki makara ba ki biya ki karanta cikin Aminci
littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar
biyanki ta WHATSAPP 09097853276 daga wannan page ɗin sai na gobe mun gama free page, ki biya yafi
sauƙi tsira ba haƙƙin kowa kanki.*

*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son
k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*
Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman
lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun
matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa
ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki
tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones
dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da
tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da
ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda
ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya
wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka
kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki
da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp
in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta,
muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina
nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a
ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.

0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta
wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije
gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.

GARKUWAR MA'AURATA

Shiko M Jameel Wani irin tsuma ilahirin jikinsa keyi sakamakon tuni da ayoyin sukayi mishi na jin azabar
da Ubangiji ya tanadar wa da duk wanda ya kashe ran mumini da gangan ba tare da wani haƙiba.

Cikin raunin murya me cike da tsananin tsoron Ubangiji M jameel ɗin ya kawo fassarar aya na 90 da
kuma 91, tsit gaba ɗaya masallacin yayi babu abinda ke tashi sai sautin kukan M Jameel daya kasa ci
gaba, yayinda kukansa yasa da dama cikin mutanen yin kuka.
Middibo kuwa kife tafukan hannunsa yayi kan fuskarsa yana maiyin wani irin sassayan kuka mai masifar
sa rawan jiki, gaba ɗaya fuskarsa tayi jazir.

Cikin ƙarfin hali M Jameel ya fara mgn cikin rawan murya yace.

“A cikin suratul Nisa, Aya ta 92 Allah ma ɗaukakin sarki na cewa, 92:

-:Baya halasta ga mutum da ya kashe ran mumini, sai dai idan ya kasance kuskure ne.”.

Sai kuma ya tsagaita tare da sayan tafin hannunsa ya share hawyen daketa kwaranyowa da idanunsa,
cikin rawan murya yaci gaba da cewa.

“Duk wanda kuma ya kashe! Mumini da kuskure toh, zai ƴanta wuyan Muminin, sannan ya bada Diyya ga
iyalan wanda ya kashe”.

Sai kuma ya dire ayar mgnar tare da rushewa da zazzafan kuka mai cike da tashin hankalin da raunata
zukata aya ta 93.

Cikin rauni yasa hannu ya karɓi hankicif ɗin da ɗan agajin dake bayansa ya miƙa masa, sharce hawayensa
yayi tare da juyowa ya kalli Moddibo da gaba ɗaya jikinsa rawa yake sai sheshsheƙan kuka mai fuzge
numfashin da yakeyi, bazai iya hana kansa kuka ba, bare ya samu iko da damar hana aminin nasa.

Cikin sheshsheƙan kuka M Jameel ya gyara zamanshi tare da cewa.

“Huymmmm, a kuma cikin suratul Nisa ɗin ayata 93, Allah madaukakin sarki nacewa-:

(Duk wanda ya kashe Mumini bisa ganganci, ko Mugunta da zalumci. Toh Sakamakonsa shine wutar
Jahannama”.

Sai kuma ya sake sakin wani irin raunataccen kuka mai cike da tsoro kana yaci gaba da cewa.

“Allah madaukakin sarki cewa yayi-:

Duk wanda ya kashe ran mumini zai dawwamane cikin jahannama, kuma Allah yayi fushi dashi, sannan
kuma ya tsine masa”.

Kawai sai ya kife kansa bisa Table ɗin dake gabansa, shar-shar haka hawayensa ke kwaranyar babu
ƙaƙƙautawa.

Modibbo kuwa cire tafukan hannunsa yayi bisa fuskarsa tare da dafa kafaɗar M Jameel ɗin kawai saka
sufashe da kuka a tare, cikin kukan murya na rawa M Jameel ya buɗe baki da nufin zaiyi mgn amman ina
ya kasa.

Haka yasa Moddibo rumtse idanunsa kana murya na rawa yace.

“Bayan fushi da tsinuwar ubangiji Allah Mabuwayi da komai baya ɓuyar masa yace.

-:Wa ahdalahun Azaban Azeeymah).


Ma'ana ya tandarwa duk wanda ya kashe ran mumini da ganganci Azaba mai girma!!!!.”

Zuwa lokacin wasu daga mutanen cikin masallacin kuka sukeyi da sheshsheƙan mafi akasari kuma duk
jikinsu yayi sanyi.

Shi kuwa Moddibo cikin rauni da sanyi yace.

“Duk waɗannan ugubobin sun ta'allaƙane ga wanda ya kashe ran mumini da ganganci, sakamakonshi
Jahannama, kuma a cikinta zai tabbata, sannan Allah yayi fushi dashi, kana ya tsine masa, kuma ya ƙara
masa da azaba mai girma.

Wannan masifa har ina ɗan adam zai kaishi koda iyayenka ne sukayi fushi da kai taɓewa kakeyi bare
Ubangijin talikai, koda iyayenka ne suka tsine maka lalacewa kakeyi bare tsinuwar Allah, sannan azaba
koda ta tururin tea ne tsoronsa muke bare kuma tabbata ta jahannama sannan da tanadin azaba mai
girma”.

Kawai sai lips inshi suka fara rawa kar-kar shima ɗin ya kasa ci gaba.

Ganin hakane yasa M Jameel sharce hawayensa tare da cewa.

“Aramma kawo mana dukkan wata Ayar Al,qura'ani da Ubangiji yayi magana akan duk wanda ya kashe
ran mumini”.

Cikin tsumar jiki tare da wata raunatacciyar murya mai cike da tsananin tsoron Ubangiji da kuma sanin
hukuncin wanda ya saɓa masa Moddibo yayi gyaran murya dai-dai zai fara karanta Ayar manyan
Malaman dake wajen suka nuna musu agogon dake liƙe a can bayansu a jikin gini.

Wanda hakan ke musu nuni da alamar lokaci yayi.

Nan-nauyan ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da share ƙwallan da suka zuba masa kana cikin raunin
murya yace.

“Lokaci yayi sai dai idan Allah ya kaimu gobe zamu ɗaura daga inda muka tsaya”.

Ya sauƙe nannuyar Ajiyar zuciya tare da cewa.

“Ya Allah Ubangiji yabamu zaman lafiya ya Allah karabamu da sharrin ƴan bindiga daɗi Ubangiji ya tsare
mu da sharrin kidnappers Ubangiji ya bamu zaman lafiya Allah yajiƙan iyayen mu da duk kan musulman
da suka rigamu gidan gaskiya.

Wa subhanakallahumma wabi hamdika ash shahadula'ilahu. nastagfirka wanatuubu Ilaik”.

Tunda ya fara addu'ar suke Amsawa da Ameeen har aka shafa.

Mata ne suka fara fita kafin maza.


Acan ɓangaren Khausar kuwa, bayan ta koma gida kai tsaye Bedroom ɗinta ta wuce batare data shiga
wajen Mommy ba, tana shiga ta kwanta lamo akan gado hawaye na tsiyaya daga kyawawan Idanunta
sosai.

Tafseer ɗin da M Jameel Yayi ya riƙa ratsa jikinta har ƙwaƙwalwar kanta Muryar Modibbo kuwa har
yanzu yana ratsa kunnuwanta, da haka bacci ya ɗauketa batare data shirya ba.

Washe gari Da safe still haka Khausar ta tashi cikin mutuwar jiki Anutse ta fito daga Bedroom ɗin ta
zauna agefen Mommy dake falo.

Lumshe Idanunta tayi kana cikin sanyin murya tace.

“Mommy ina kwana”.

Anutse Mommy ta maida kallonta gareta tare da na zartan yanayin ta batare data amsa gaisuwar data
mata ba ta jefo mata tambya tare da cewa.

“Meke damunki Khausar na lura tun jiya jikin ki Asanyaye”.

Ɗago Kai Khausar tayi Idanunta cike da ruwan hawaye kana cikin sanyi murya tace.

“Wallahi Mommy tun jiya da muka je wajen tafsir ɗin da Malam M Jameel yayi jikina ya mutu hankalina
ya tashi gaba ɗaya na rasa mai yasa tsoro ya kamani”.

Miƙewa Mommy tayi tare da matsowa kusa da Khausar ta shafa kanta kana tace.

“Babu komai wannan masiface-masiface ne da Allah ya jarabci Al'umma wannan ƙarnin saidai mu dage
da addu'a Allah ya yaye mana ya kuma tsaremu da faɗa wa mummunar ƙaddara Allah ya rufa mana asiri
ya karemu da zamewa sanadin mutuwar koda kadagare ne”.

Jinjina kai Khausar tayi tare da cewa.

“Ameen”.

Acan gidansu Moddibo kuwa Innayi ce zaune atsakar gida ta zabga tagumin tunda taji tafsirin da M
Jameel sukayi jikinta yayi masifar sanyi wani irin tsoron Allah mara misaltuwa tashiga hakan fargaba ya
rufeta.

Washe gari.

Da hantsi A hankali Moddibo da M Jameel suka fito, Moddibo na sanye cikin Shigarsa as Usual Jallabiya
Sky blue mai yauƙi da santsi kansa ɗaure da farin Hirami kana takalmamsa farare jikinsa na fitar da
sanyayyan ƙamshi turaren Oud Khareem na tashi.
Shima M Jameel sanye yake cikin irin shigar Modibbo jikinsa na fitar da sanyayyan ƙamshi kai tsaye
sashen Innayi suka nufa,Innayi dake zaune gaban barandar akan kujera ƴar tsugunno ta ɗago kai ta kalli
Moddibo da M Jameel kawai sai taji Idanunta na tsats-tsafowa da ruwan hawaye.

Tsayuwa Moddibo ya gyara kana yace.

“Ya dai Innayi”.

Idanu ta zuba masa batare data iya furta komaiba kawai sai hawaye suka shiga kwaranya daga idanunta.

Cikin yanayin tashin hankali Moddibo ya tsugunna agefenta na dama yayin da M Jameel ya durƙusa
agefenta na hagu kana suka haɗa baki tare da cewa.

“Innayi ya dai me yasame ki?”.

Kallonsu tayi hawaye na cigaba da kwaranya daga idanunta ta sauƙe numfashi kana tace.

“Wa'azinku na jiya ya ratsa jikin mutane wa'azin yasa mutane acikin ɗimuwa wa'azinku na jiya ya tunatar
sannan yasa tashin hankali kuma wannan zamanin muna fama da Masifa Allah dai ya yaye mana jiya
hankalina atashe yake domin ire-iren abubuwan akeyi!”.

Jinjina kai M Jameel yayi tare da sauƙe numfashi kana yace.

“Hakane sosai ma Innayi amma mu cigaba da addu'a babu abinda ya gagari Ubangiji ga dama yazo watan
Ramadan muyita addu'a Allah ya yaye ya taƙaita ya sauƙaƙa mana”.

Atare Modibbo da Innayi suka amsa da.

“Ameeen”.

Miƙewa M Jameel da Moddibo suka atare kana M Jameel ya Kalli Innayi tare da cewa.

“Toh Innayi zamu tafi Tafseer A masallacin makarantar mu”.

Jinjina kai Innayi tayi kana tace.

“Ubangiji Allah ya tsare ku ya kuma sake ɗaukaku”.

Ameeen suka amsa tare da juyawa zasu fita har sun kai ƙofa Innayi ta ɗan ɗaga sautin Muryanta tare da
cewa.

“Yauwa wai niko ya batun tafiyar mu ne?”.

M Jameel ya juya tare da cewa.


“Komai ya kammala na tafiyar mu Insha Allah ranan sha biyar ga wata zamu tashi misalin sha biyu da
rabi na dare jirginmu zai tashi jibi kenan ba in sha Allah, kuma sai munyi tafsir ɗin ranan ma zamu tafi
Taraba”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Allah ya nuna mana Ubangiji Allah ya kaimu lokacin lafiya amman kuma kace sai kunyi tafsirin ranar?”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Eh kinga Tara na dare zamu fara, goma zamu tashi, dama kuma kafin mu tafi zamu gama shirin mu
duka, tsananin mu Gembulan da taraba kuma tafiyar awa ɗaya da rabine, kinga kenan sha ɗaya da rabi
zamu isa, zamu samu awa ɗaya ma acan kafin mu tafi, Abba na kuma su gobe nema zasu tashi”.

Cike da gamsuwa Innayi ta jinjina kai tare da amsawa.

“Allah ya kaimu lfy”.

Ameeen suka amsa a tare kana suka fice mota suka shiga M Jameel ke Driving cikin nutsuwa har suka isa
masallacin.

Suna shiga suka fars gabatar da tafsirin kamar yanda suka saba ƙarfe ɗaya da rabi dai-dai suka gabatar
da sallah Moddibo yayi limanci bayan sun idar suka cigaba kiran sallar La'asar yasa suka dakata da
karatun tare da miƙewa suka gabatar da sallah bayan sun idar suka fito suka shiga mota awannan lokacin
ma M Jameel ke Driving har suka iso gida.

Hong M Jameel Yayi Modibbo ne ya fita ya buɗe musu.

Anutse suka fito tare da furta Bismillahi,

Ahankali Moddibo ya gyara tsayuwarsa tare da fesar da sassayan numfashi.

Ido ya tsirawa bishiyar Ayaba da iska ke kaɗawa har na tsawon sakonni goma, sai kuma ya maida
kallonsa kan Bishiyar mangoro Idanunsa ya lumshe domin Allah ya sani ganin sirrai ya fiye mishi ganin
komai daɗi. sannu ahankali ya riƙa tuna lokacin da yarinyar tashigo gidan har tayi nasaran hawa reshen
bishiyar mangoro mai girma da tsawo, da kuma sanda ta faɗo akan yatsun ƙafarsa.

Da sauri ya buɗe idanunsa

Tare da jan dogon tsaki mai cike da tsanar lamuran yarinyar. Idanunsa ya juya jin M Jameel na cewa.

“A.J tunanin mai kakeyi haka ka tsiwara Bishiya ido?”.


Sanyayyar Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da furzar da iska mai sanyi daga bakinsa kana yasa hannu
ya shafa kwantaccen Sajen fuskarsa ya maida kallonsa kan M Jameel da har zuwa lokacin shiyake
kallo,Ya mutse fuska yayi kana yace.

“Babu komai”.

Daga haka ya wuce gaba Kai M Jameel ya Girgiza tare da bin bayansa suka shiga Babban falon Moddibo
da komai ke kimtse sai tashin ƙamshi yake.

Zama M Jameel Yayi akan 3sitter tare da faɗin.

“Wash' Allah!”.

Kallonsa Moddibo yayi amma bai ce komai ba Bedroom ya nufa tare da janye Hiramin kansa kana ya cire
jallabiyar dake jikinsa ya buɗe ƙofar toilet da addu'a

Kana yashiga shawer ya sakarwa kansa yashiga cuɗe jikinsa ya ɗauki kusan minti ashirin kafin ya fito
zama yayi agaban Dressing mirrow ya shafa Mai sama-sama kana ya miƙe ya sanya Jallabiya Maroon
colour da farin hirami. Feshe jikin sa da turarukansa masu daɗin ƙamshi yayi. shima M Jameel wanka
yayi tare da sauya kan jikinsa zuwa Jallabiya fari kana ya ɗaure kansa da Maroon Hirami Sosai sukayi
kyau atare suka fito zuwa farfajiyar gidan anan suka samu Innayi da Asma'u na aikin abin buɗa baki
kallon Innayi dake soya ƙosai yayi sai kuma ya maida kallonsa kan Asma'u dake dama kunun sadaka na
masallaci har ta gama ta rufe sai kuma suka bita da ido.

Kallon Asma'u dake kwaɓa fulawa, kuka, da kanwa M Jameel Yayi yace.

“Yau kuma ɗan wake ake mana ne Asmeey?”.

Kai ta jinjina kana tace.

“Eh dan naji jiya Yaya Moddibo nacewa ɗan wake mukayi ne shiyasa yau nace bari ayi”.

Murmushi Moddibo yayi ya mai binta da wani irin amintaccen yace.

“Kai kin kyauta mun kuwa, kwana biyu bamuci ba inaga tunda azumi ya kama kamar baku yimana shiba”.

Kallonsa Asma'u tare da ce wa.

“A'a munyi amma ranan baka ciba agidan Ummi kuka sha ruwa ranan”.

Jinjina kai yayi yace.

“Toh yau kam Insha Allah zamu dawo muci ɗanwaken nan”.
Murmushi tayi ta na jefa ɗan waken da cokali tace.

“Allah ya dawo daku lafiya”.

Ameeen suka amsa kana suka mayar da Kallonsu kan Innayi dake musu gashin Zabbi sai tashin ƙamshi
yake.

Idanu M Jameel ya lumshe yace.

“Innayi zamu wuce”.

Da murmushi afuskarta ta kallesu tace.

“Ubangiji Allah ya tsare”.

“Ameen”,Suka amsa sannan suka fice atare kai tsaye masallacin Juma'ar da suke limancin suka nufa cike
da nutsuwa da kuma kamala suka gabatar da tafsirin Alkur'ani acikin Suratul Zariyat yayin da Moddibo
ke jan baƙi M Jameel na tafsiri ƙarfe shida dai-dai suka tashi.

Anutse suka fito daga cikin masallacin suka shiga mota akuma dai-dai lokacin wayar M Jameel ya hau ruri
cike da nutsuwa ya gyara zamansa tare da ciro wayar daga aljihun sa Sunan Abban sa ke yawo a screen
ɗin kallon Moddibo da idanunsa ke lumshe yayi yace.

“Kaga Abba ke kira”.

Ya ƙara sa maganar tare da Amsa kiran yakai kunnensa tare da cewa.

“Assalamu Alaikum”.

Daga ɓangare Abba yace.

“Wa'alaikum Salam Babana”.

M Jameel Yayi murmushi tare da cewa.

“Na'am Abba na”.

Gyaran murya Abba yayi kana yace.

“Nikam laifin me mukayu mukune da kai da Moddibo da baza kuzo mu samu ladan baku buɗa baki
agidan nan ba”.

Murmushi M Jameel Yayi yace.

“Ayyah Abba na laifin me zaku mana mukam a duniyar nan gama A.J ɗin yana jinka”.

Ɗan Matsawa kusa da M Jameel ɗin Moddibo yayi kana yace.


“Abbah mai zaku mana A duniya ko kun yi mana abu baza muyi fushi da kuba waye zaiyi fushi da
iyayensa?”.

Murmushi Abba yayi yace.

“Toh tun da akayi azumi baku zo kunsha ruwa a gidan nan bafa, abin yana damuna yau fa kwana goma
sha uku kenan da baku zo kunsha ruwa agidan nan ba fa”.

Dariya M Jameel Yayi yace.

“Abba ka dai manta mun zo ranan da akayi azumi biyar agidan muka sha ruwa fa”.

Gyara zaman wayar Abba yayi akunnensa kana yace.

“To ai bana nan ba asha ruwan dani ba yau dai so nake kuzo musha ruwa tare”.

Gyara zama Moddibo yayi yace.

“Abba baza mu bari sai gobe ba?”.

“A'a yau nakeson ganinku kuzo musha ruwa anan”.

Cewar Abba.

Jingina kai Moddibo yayi tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Toh shikenan Abba zamu zo insha Allah amma bari mu fara zuwa gida”.

Cikin sauri Abba ya Girgiza kai tare da cewa.

“A'a karfa ku makara kuzo komai ya kammala ku kawai ake jira ga kun lokacin ya ƙarato”.

Atare suka haɗa baki wajen cewa.

“Toh shikenan Abba ga munan zuwa”.

Kallon Moddibo M Jameel dake Driving Yayi kana yace.

“Muje?”.

Moddibo kuwa Idanunsa dake lunshe ya buɗe yace.

“Eh muje mana J”.


Kai M Jameel ya gyaɗa kana ya juya akalar motar zuwa Unguwar su Abba ba abinda ke tashi acikin motar
face ƙira'ar Alkur'ani acikin Suratu Yusuf tare da Sanyayyar ƙamshin tularensu, Wayar Moddibo dake
gaban aljihu ne ya hau ruri Anutse yasanya lallausan tafin hannunsa mai zagaye da gashi ya ciro wayar
tare da kallon sunan mai Kiran Malam Arɗo amsa kiran yayi tare da kai wa kunnensa.

Daga ɗaya ɓangaren Malam Arɗo yayi gyaran murya kana yace.

“Wai kai baza kazo kasha ruwa agidana ba ko sau ɗaya ne Moddibo?”.

Murmushin gefen baki Moddibo yayi tare da shafa kwantaccen Sajensa kana yace.

“To Malam ka gayyace mune ai baka gayyace mu shan ruwa ba”.

Da sauri Malam Arɗo yace.

“To na gayyace ku xo yanzu”.

Girgiza kai Moddibo yayi tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Toh ba yau ba dai sai gobe”.

Da sauri Malam Arɗo ya zare Ido tare da cewa.

“To duk abubuwan da nasa aka dafa muku kuma fa?”.

Murmushin gefen baki Moddibo ya kuma yana imagine fuskarta malam Arɗo kana yace.

“Ka bawa mutanen gida suci ba rabon mu bane

gobe kuma Idan Allah ya kaimu kama na namu kuma ayi da mutanen gida duka”.

Cikin sauri Malam Arɗo yace.

“Wato dai kai ko yaushe sai ka kawo min sabon tsari acikin al'amari na ko”.

Murmushi M Jameel yayi shaƙuwar dake tsakanin Moddibo da malam Arɗo ya wuce zaton mutane.

Moddibo kuwa ɗan Murmushin dake ƙarawa fuskarsa kyau yayi kana yace.

“Ai dole dai kam”.

Dariya Malam Arɗo yayi yace.

“Dama gobe ka tabbatar lokacin shan ruwa yana yi na ganka, ba sai na kira ba ka gaishe da Jamilu kar ku
cinye min kati na”.

Ya ida maganar tare da katse kiran.

Murmushi M Jameel Yayi kana yace.


“Malam Arɗo ko?”.

Murmushi kawai Moddibo yayi yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi yake.

Cikin mintunan da baza su gaza biyar ba suka isa ƙofar katafaren gidan Hong M Jameel Yayi mai gadi ya
buɗe musu Anutse M Jameel ya cinna hancin motarsa gidan tare da yin parking a inda aka tana da danyi
Parking ɗin motoci.

Cike da nutsuwa suka nufi sashen Abban M Jameel, bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga tamfatsetsen
Falon nasa daya gaji da tsawuwa yana fitar da sanyayyan ƙamshi.

Tsaye suka hangosa yana gyara ɗaurin agogon hannunsa fuskarsa da damshi da alama Al,wala yayi.

Kallonsu yayi tare da sakar musu da murmushi kana yace.

“Ku shiga kuyi al,wala kunga muna shan ruwa sai mutafi masallaci”.

Kai suka gyaɗa sannan M Jameel ya nufi toilet dake Falon kana ya kalli Moddibo da faɗin.

“A.J kashi ga toilet ɗin ciki kayi al,wala”.

Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.

“A'a kashiga na ciki ni zan shiga wannan”.

Kallon Moddibo Abba yayi kana yace.

“Wato shi yashiga ɗaki na kai ba zaka shiga ba ko? To ai kaima ɗana ne kashiga babu komai Moddibo”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.

“Toh shikenan Abba”.

Sannan ya wuce Bedroom ɗin Abba ahankali ya saki murmushi ganin komai na Bedroom din tsaf-tsaf
akimtse Aransa yace ashe de J gadon tsafta yayi awajen Abba shima komai nashi tsaf-tsaf ajiyar zuciya ya
sauƙe tare da shiga toilet ɗin nan ma komai atsaftace Al'wala ya ɗaura kana ya fito atsaye ya samu M
Jameel da Abba Kallonsu Abba yayi kana yace.

“Ku ƙaraso mu isa dining”.

Kai suka gyaɗa tare da nufar dindin ɗin da aka ƙawata da kayan ciye-ciye na alfarma wani irin kwando ne
na kayan marmari ne kama daga, Inabi, Abarba, Ayaba, Kankana, Lemo, Ruman, Tuffa, Mangoro.

Sai kuma wasu Warmers masu kyau dake ɗauke da pride rice da yaji kayan lambu,sai daga ɗaya gefen
kuma wasu jug ne masu kyau ɗaya kindirmo ne mai sanyi adame ɗayan kuma kunun shinkafa ne sai
Flaks dake ɗauke da ruwan tea da kuma kofina daga gefensa kuma gongomin madara ne dana Bounvita
sai kulan ƙosai sosai dining din ya ƙawatu.

Anutse suka zauna akan kujeran Abba ya zauna daga ɓarin kudu Moddibo ya zauna daga ɓarin yamma
yana fuskantar gabar M Jameel kuwa daga ɓarin gabas ya zauna yana fuskantar yamma.

Anutse Moddibo ya ɗauki dabino guda bakwai ahannunsu idan yaci sai ya sanya ƙwallon ahannunsu na
hagu bayan yaci sai ya ɗauki inabi yaci M Jameel kuwa dabino uku yaci tare da apple haka ma Abba.

Sai.kuma suka sha kankana da inabi kana suka ɗan ɗaura da ayaba.

Kallon su Abba yayi cike da so da ƙaunarsu kana yace.

“Toh kuci abinci”.

Girgiza masa kai sukayi kana atare suka ce.

“A'a Abba sai mun dawo daga masallaci”.

Kai ya gyaɗa musu kana suka miƙe atare suka tafi masallaci suka idar da sallah bayan sun dawo M
Jameek ya ɗebi Pride rice Kaɗan da tsokokin kaza. Modibbo kuwa kindirmon da aka dama ya ɗiba a Cup
Abba kuwa chicken peper da pride rice shima ya ɗebi yana ci.

Fara cinsu babu daɗewa aka turo ƙofar aka shigo Idanun Hajiya Karima bai sauƙa ko ina ba sai kan
Moddibo dake riƙe da kofin kindirmon kana da plate ɗin da Abba ya sa mishi pepper chicken and
vegetables da fork a samansu.

Cike da tsanarsa ta watsa masa wani wulaƙantaccen kallo kana tace.

“Toh acire tsatsan haƙori anan, kaska raɓi mai jini wato ko zuwa shi kaɗai ya samu ya keɓe da mahaifinsa
ba za'a bari ya samu damar hakan ba ko?

Oh ni Kareeme tunda nake a duniya ni dai ban taɓa ganin mutum mai shegen nacin tsiya irin kaba, sam
baka da godiyar Allah ba zaka tsaya amatsayin ka ba shin kai wani irin Jarabebben mutum ne Aliyu?!”.

Cikin wani irin fushi da ɓacin rai Abba ya mike ahasale ya dubeta kana yace.

“Hajiya Karima mai kikeyi haka ne?

Wai meyasa ne ke baki da hankali ne? kinsan abinda kike faɗa kuwa!”.

Fuska ta ɓata kana tace.

“Toh Alhaji gaskiyane ya barka kaida ɗan ka kuhuta mana kuyi shawara acikin sirri”.
Afusace Abba ya katseta tare da faɗin.

“Me kike nufi shiɗin ba Uwa da Ubane suka haifeshi ba shima ɗana ne”.

Sheƙeƙe Hajiya Karima ke Kallonsa kafin cike da Isgilanci ta kallesa kana tace.

“Yaushe ka haifesa bamu da labari?,yaushe ka auri uwarsa har ka haifesa bamu sani ba?”.

Cikin tsananin fushi Abba yace.

“Kifita anan ki fita Karima bana son ganinki tun da ke kince baki da ɗa'a baki iya Mu'amala da mutane
arayuwarki ta duniya ba, bana son haka, Bana son haka kar ki sake yin haka na yi miki kashedi na ƙarshe
wannan shine last warning Hajiya Karima!, Kada ki sake yimin haka.

Domin kuwa koda Mahaukaci Jameel ya ɗauko ya kawo wannan gidan wallahi yafi min ke daraja, saboda
nasan koda mahaukacine Jameel zai nuna masa cewa ni mahaifinsa ne kuma na tabbata zai mutunta ni”.

Cikin fushi ya sauƙe ajiyar zuciya tare da furzar da Iska kana ya cigaba da cewa.

“Na tabbata ko Mahaukaci Jameel ya kawo gidan nan zai mutuntani, kuma zai ɗauke ni da daraja fiye da
yanda ke ki ɗaukeni ban isa da keba, misali ga yadda idan na baki umarni kike fatali dashi, ba zakiyi
amfani dashi ba.

Dan haka ko kin san Jameel ya fimin komai.

Jameel da kike gani shine Komai nawa a Duniya akan farin cikin Jameel ina iya yin komai dan haka tun
wurima ki kiyayeni!

Kifita idona in rufe Hajiya Karima!!.

Ki kiyayeni kada inci miki mutunci!!!”.

Ya ida mgnar tare da buga jikin kujerar dining ɗin kana yaci gaba da cewa.

“Na tabbata kare idan Jameel zai kawo gidan nan sai yamin biyayya fiye da yanda ke kike min biyayya.
Kare dai nasan idan Jameel zai kawo min gidan nan bazai tsaya yamin irin haushin da kike min ba!”.

Sai kuma ya watsa mata Kallon mai cike da fushi kana yace.

“Kare idan Jameel zai kawo gidan nan kare mai ɗa'a da biyayya zai kawo min ba karen da zai kunya ta
min baƙi na ba amma ke kullum baki da hankali. idan Jameel ɗan kine da kika haifa acikin ki zaki yi masa
haka ne?”.

Kasa cewa komai Hajiya Karima tayi sai huci da take tamkar zakanya.
M Jameel kuwa ƙasa yayi da kansa cike da jin daɗi karo na farko kenan da mahaifinsa ya burgesa a kanta
daya buɗewa Hajiya Karima wuta akan abinda ta keyiwa Moddibo domin kullum idan ta wulaƙanta
Moddibo sai sunbar gidan kafin yake mata faɗa akan ta daina, amma yau yaji daɗin faɗan da Abba yayi
mata agaban Idon Moddibo saboda Moddibo zaiji daɗi sannan zai san cewa yana da daraja da kuma
kima awajensu.

Moddibo kuwa kansa ya sunkuyar ƙasa da cike kunya sam baiji daɗin ɓatawan mata da Miji adalilinsa
ba, yayi dana sanin zuwa gidan, yasan cewa duk lokacin da yazo gidan sai yayi sanadin da za'a samu
hatsaniya, sannan ya riga daya sani tun yana yaro matar nan bata sonshi bata ƙaunar ganinsa da Jameel
sai dai ya fahimci ba wai shi ta tsana ba tana fakewa da guzma ne ta harbi karsana.

Cikin sanyi murya ya ɗago kansa tare da furzar da iska mai zafi kana yace.

“Abba kayi haƙuri dan Allah dan darajar Annabi”.

Juyawa Abba yayi ya kallesa kana ya ɗaga masa hannu da faɗin.

“Yi shiru ba maganar ka Aliyu barni da ita haka take yimin, ba kai kaɗai ba, duk baƙon da Jameel zai kawo
gidan nan sai taci masa zarafi, duk mutumin da zata gansa da Jameel saita nuna min ba mutumin kirki
bane!”.

Sai kuma ya juyo Afusace tare da kallonta har zuwa lokacin tana tsaye cike da ɓacin rai ya tsira mata
idanu kana yace.

“Mai Jameel ya tsare miki?, Jameel tun tasowar yana ƙarami biyayya yake miki bai taba Musa Miki ba
duk da kinzo kin samu yana da shekara goma sha huɗu na tabbata baki yiwa Jameel wahala ba amma
yana karramaki sannan yana mutuntaki kamar yanda yake mutunta mahaifiyarsa”.

Zazzafan iska ya furzar kana still muryarsa cike da ɓacin rai yace.

“Amma ke kullum baki da buri daya wuce kici masa zarafi, Idan kin zauna ki riƙa faɗa mun magana kinyi
zaton cewa bana son Jameel ne?.

Shin inada wani ɗa aduniya daya wuce Jameel ne?”.

Cikin tsananin fushi da ɓacin rai Hajiya Karima ta nuna kanta kana tace.

“Ni ka ciwa zarafi akan yaro ɗan maƙota dan yana abokin ɗan ka, sannan dan na faɗa maka gaskiya, kai
baka ga yadda yake liƙewa ɗan nakaba duk ya hana sa tattalin arziki sannan ya hanasa ya tara abin
kansa”.

Cikin wata fusatacciyar tsawa daya amsa ilahirin falon yace.

“Ki fice min anan Karima bana son ganinki”.


Afusace ta juya kamar zata tashi sama tana wani irin huci tare da jin tsanar Moddibo da M Jameel fiye da
komai arayuwarta!.

Anutse Abba ya juya ya kalli Moddibo kana cikin sanyi murya yace.

“Dan Allah Aliyu kayi haƙuri kada ka damu da abinda tayi maka, sannan bance ka ɗauki wannan
amatsayin wani mataki da zai hana ka zuwa gidan nan ba, aduk sanda kaga dama zaka zo”.

Murmushi yayi kana yace.

“Babu komai Abba ai ita mahaifiya ce agurin mu dan tayi mana haka ba zai zama wani aibu ba”.

Jinjina kai Abba yayi tare da cewa Ubangiji Allah ya al'barkaci rayuwarku”.

Atare suka amsa da.

“Ameen”.

Juyawa M Jameel yayi tare da kallon Moddibo Cikin sanyin murya mai cike da so da shaƙuwa ya numfasa
kana yace.

“Dan Allah A.J kayi haƙuri”.

Murmushi Moddibo yayi kana yace.

“Laa babu Komai J. Yanzu dai tashi muje mu bata haƙuri”.

Da sauri Abba ya kalli Moddibo kana yace.

“Baza ku bata haƙuri ba ku zauna kuci abinci”.

Kai suka gyaɗa sannan suka zauna baki ɗayansu, basu wani ci abincin kirki ba, domin ko kowa da irin
damuwar dake ransa, bayan sun kammala suka miƙe tare da yiwa Abba Sallama haƙuri Abba ya sake
bawa Moddibo.

Murmushi Moddibo yayi kansa aƙasa yace.

“Ayyah Abba Allah babu komai”.

Sannan suka juya har sun kai ƙofa Abba ya ɗan ɗaga sautin muryansa tare da cewa.

“Yau kam ba zamu kwana anan bane?”.

Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.


“A'a Abba idan mun kwana anan Innayi ita kaɗai zamu bari acan”.

Jinjina kai Abba yayi kana yace.

“Eh kam ya kamata gida babu namiji ba gida bane kuje”.

Godiya suka masa kana suka fice.

Suna cikin mota aka kira Isha'i kai tsaye masallacin da suke limancin suka nufa kamar ko yaushe
Moddibo ne yaja Sallar bayan sun idar sukayi Asham kana suka wuce gida.

Suna shiga gida kai tsaye sashen Innayi suka nufa zaune suka sameta riƙe da carbi ahannun Asma'u kuma
tana riƙe da Alkur'ani mai girma tana karatu.

Batare da sun ƙarasa shiga ba Moddibo yace.

“Innayi Barka da shan ruwa”.

Anutse ta kallesa kana tace.

“Yawwa yau ina kuka tsaya ne baku dawo da wuri ba, nace Asma'u ta kira min ku inji kuma ashe wayar
ba kati”.

Murmushi M Jameel Yayi kana yace.

“Ayya Innayi Abba ne ya kiramu wai muje mu sha ruwa acan shiyasa kika jimu shiru”.

Kai ta jinjina tare da kallon Moddibo tace.

“Fatan duk suna lafiya?”.

Kai Moddibo ya gyaɗa mata kana ya sake labulen tare da faɗin.

“Innayi akawo mana abinci”.

Ya ida mgnar tare da zama akan shimfiɗar dake barandar Asma'u Innayi ta ƙalla kana tace.

“Ɗauki abincin ki kai musu”.

Kai Asma'u ta gyaɗa sannan ta ɗauki lemun tsani ta yanka ta matsa kaɗan akai kana tayi slinzing ɗin
ƙwoyi kana ta zuba musu wadataccen man gyaɗa da kuma dakekken yajin barkono sai Cucumber da
Cabbage ta Kai musu.

Sosai suka Moddibo da M Jameel suka ci ɗan waken tare da 5alive, bayan sun kammala kai tsaye ɗakinsu
suka wuce tare da watsa ruwa, kana suka sake shiryawa tare da feshe jikinsu da turaraku masu daɗin
ƙamshi.
Cikin nutsuwa suka fito aharabar gidan suka samu Innayi da Asma'u sun fito buɗe bayan motor sukayi
suka shiga sannan Moddibo ya shiga mazaunin Driver yayin da M Jameel yashiga gefen mai zaman
banza, kai tsaye masallacin suka nufa har suka isa ƙira'a na tashi amotar suna parking Innayi da Asma'u
suka shiga sashen mata suka ma suka ƙara sa sashen su.

Yau ma kamar kullum gaba ɗaya cikin masallacin da harabar sa cike yake da ɗumbin jama'a cikin tsantsar
nutsuwar daya zame musu jiki suka nufi wajen zamansu cikin sanyi mai cike da kamala da kuma kamun
kai Moddibo ya ajiye System ɗin sa kana ya zauna tare da ɗan jingina bayansa da jikin kujeran ya lumshe
Idanunsa tare da motsa laɓɓansa alamar tasbihi Shikuwa M Jameel zaman microphone da aka dasa
masa ya gyara tare da buɗe System ɗin sa Lokaci ɗaya cikin masallacin ya gauraye da ƙamshin
sanyayyan turaren su yayin da hasken Fararen glob ɗin ya haskaka hasken farin fuskarsu na fitar da
sheƙin annuri yayin da baƙin sajensu ya kwanta luf-luf komai nasu kusan ɗaya yake tamkar tagwaye.

Cikin nutsuwa M Jameel ya lumshe Idanunsa tare da gyara zaman Microphone kana Yayi gyaran murya
cikin Sanyayyar muryarsa mai cike da kamala yayi gyaran murya kana yace.

_“Innalhamdulillah Nahmaduhu Wanastainuhu wanastaghfiru wa'nazubillahi billahi min shuriri anfusna


wamin sayyi ati a'amalina manyah dillahu fala hadiyala waman yudil fala mudillalah Wa'ash hadu Allah
ilahalillahu wahdahu lasharika Wa'ash hadu anna Muhammadu Abduhu warasulu Ya Ayyuhal lazina
amanut taƙullaha haƙƙu tuƙatihi wala tamu tunna illah wa'antum muslimun Ya ayyuhan nasu taƙu
rabbakummalazi halaƙakum min nafsi wahida wahalaƙa minha zaujuha wabassa min huma rijalan
kasiran wa Nisa'a wattaƙullahal lazi tasa aluna bihi wal arhama innalaha kana bikum raƙiba, Amma ba'ad
faya Ikhwatul musulmi Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu”_.

A tare jama'ar dake cikin masallacin suka amsa da.

“Wa'alaikum Salam warahmatullah wabarkatuhu”.

A hankali M Jameel ya fesar da sassayan numfashi tare da lumshe idanunsa kana a hankali yace.

“A yau muna sha huɗu ga watan Ramadan a cigaba da tafsirin Alkur'ani mai girma da muke acikin
masallacin mai Martaba sarki Bashiru acikin Suratu An-Nisa'i ayau zamu tashi akan aya ta Cassa'in da
huɗu wala Allah kuma bazai wuce da biyar zamu tsaya ba, sai kuma shekara mai zuwa idan Allah ya
bamu aron rai da lfyar”.

Sai kuma ya sauƙe numfashi kana ya cigaba da cewa.

“Tun daga kan aya na cassa'in da biyu muka shiga babi akan kashe ran mumini, da kuma hakkin ran
Muminai, ayau Insha Allah zamu cigaba, amman kafin nan zamuyi duba i zuwa kan dukkan ayoyin
Alkur'ani dake mgna kan ran muminai”.
A hankali ya buɗe kwayar idanunsa, sabida jin yadda masallacin ya cika da kabbara.

Gyara system ɗinshi yayi kana yace.

“Insha Allah ayau Aramma zai zaƙulo mana Ayoyin da Ubangiji yayi magana akan hakkin kashe ran
mumini, domin tunatar wa da kuma jan hankali da kuma fito da darajar ran ɗan Adam Dan kiyaye
lalacewar zamani da kuma tunatar da hakkin ran musulmi amatsayin ba komai ba”.

Cikin yanayin kamala ya juya tare da maida kallonsa kan Modibbo da idanunsa ke lumshe ajiyar zuciya
sauƙe kana yace.

“Aramma bamu ayoyin da Ubangiji yayi magana akan kashe ran mumini”.

Anutse Moddibo ya gyara zamansa tare da ɗan ture system ɗin sa gefe kana yayi gyaran murya cikin
sanyayyar sautin muryarsa ya fara kamar haka.

Surah Al-ma'idah Aya 32


‫َأ‬ ‫َأْل‬ ‫َأ‬ ‫َأ‬ ‫َأ‬
‫ِمْن ْج ِل َٰذِلَك َكَتْبَنا َعَلٰى َبِني ِإْس َر اِئيَل َّنُه َمن َقَتَل َنْفًس ا ِبَغْيِر َنْفٍس ْو َفَس اٍد ِفي ا ْر ِض َفَك َّنَما َقَتَل الَّناَس‬
‫َجِميًعا‬

Ya ƙare jan karshen ayar da fesar numfashinsa da ya riƙe domin fidda cikekken haƙin ko wanne harafi,

Yayin da Al'ummar Annabi dake cike a masallacin kuwa, sukayi sit suna masu samun cikekkiyar nitsuwa
ta mu'ijizan jin karatun Alqur'ani mai girma kenan.

M Jameel kuwa cike da raunin murya ya fara fassara ayar Allah madaukakin sarki nacewa-:

“Sakamakon haka ne muka wajabta akan 'ya'yan Isara'ila cewa, duk wanda ya kashe wata Rai ba tare da
ita Rai ɗin ta kashe wata ba, ko kuma yayi ɓarna a kan ƙasa (ta'addanci, Fashi da makami etc) toh kamar
ya kashe mutane ne gaba ɗaya na Duniya kuma ubangiji zai hukunta shi dai-dai da laifinsa”.

Shiru masallacin yayi baki ɗaya, kowa jiki nai a mace, yayinda manyan dottaɓai dake ciki kuwa, suka zuba
M Jameel da Modibbo ido suna nazartan yadda akayi akalar tasirin ya sauya daga kan Suratu An-Nisa'i ya
koma kan duk ayar da ke mgn kan kisan kai.

Shi kuwa M Jameel juyowa yayi ya kalli Modibbo tare cewa.

Aramma koma cikin suratul Al-ma'idah akwai ayar da Allah ke mgn kan rayuka”.

Cike da ƙwarewa da cikekkiyar hadda mai ɗauke da kaifin basira, Modibbo ya lumshe idanunsa da yakeji
suna cika da rauni cike da zaƙin murya ƙira'a mai sa nitsuwa ya kawo ayar

Surah Al-ma'idah Aya 33 ‫ِإَّنَما َجَز اُء اَّلِذيَن ُيَح اِرُبوَن الَّلَه َوَر ُس وَلُه َوَيْسَعْوَن ِفي اَأْلْر ِض َفَس اًدا َأن ُيَقَّتُلوا َأْو‬
‫َأْل‬ ‫اَل َأ‬ ‫َأ ُل‬ ‫َّل َأ َّط َأ‬
‫ُيَص ُبوا ْو ُتَق َع ْيِديِهْم َو ْر ُج ُهم ِّمْن ِخ ٍف ْو ُينَفْوا ِمَن ا ْر ِض‬.
Cike da nitsuwa ya dire ƙarshen ayar,
M Jameel kuwa gyara zamansa yayi tare da fara fashin baƙin.

“Allah madaukakin sarki nacewa-:

Lallai sakamakon waɗanda suke yaƙar Allah da Manzo nai, kuma suke yaɗa ɓarna a doron ƙasa
(ta'addanci, Fashi, ƙwamushe Garkuwa Da mutane etc), shine a kashe su, ko a giciye su”.

Sai kuma ya fesar da sassayan numfashi tare da lumshe idanunsa wanda tuni suke sheƙin ruwan hawaye,
murya cike da rauni yaci gaba da cewa.

“Ko a yanke Hannayen su da Ƙafafuwan su a saɓani (hannun hagu da ƙafar dama, ko kuma Hannun dama
da ƙafar Hagu), ko kuma a kore su daga Garin.”.

Zuwa yanzu shar-shar hawayensa ke kwaranya yayinda tuni muryarsa ke rawa, haka yasa da yawa
mutanen suke zubda hawaye.

Haka dai Modibbo ya rinƙa zaƙulo dukkan ayoyin Alkur'ani dake mgna kan ran mumini, M Jameel na
fassarawa, yayinda gaba ɗaya zuƙata jama'ar masallacin ya cika da rauni.

Kasan cewar gobe ne, Modibbo da M Jameel ɗin zasu wuce ƙasa mai tsarki, damin yin Umrah Ramadan,
yasa dole a ranar aka rufe tafsir ɗin. Bayan jero Addu'o'in wa al'ummar musulmi dama kasa baki ɗaya.

Washe gari ranar 15 ga watan Ramadan misalin ƙarfe tara na dara dai jirgi su Modibbo ya tashi daga
cikin Taraba zuwa ƙasa mai tsarki...!

Daga yauwa ɗin nan Laraba mun gama free page, in kina son ci gaban littafin SAKAYYAH to ki biya ki
karanta cikin aminci. Littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki
turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Ki biya ki karanta ba haƙƙin kowa a kanki.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

❤️❤️❤️

*SAKAYYAH*

_Page 17_

*LAST FREE PAGE*


_NA_

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*DAGA WANNAN PAGE ƊIN FREE PAGES SUN ƘARE, IN MA KIN SAKE GANIN LITTAFIN SAKAYYAH A WAJE
TO. NA SATANE NA ALLAH YA ISA ne, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal yar ki biya ki karanta cikin Aminci da
salama babu haƙƙin kowa kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar
biyanki ta WHATSAPP 09097853276 kiyiwa da Annabi in dai kin san kin sayane don ki fitarmin da littafin
na kiyi min mgn in mayar miki da kuɗinki. In kuma kin san zaki sayane dan ki fidda min littafina, wasu
Groups ɗin, kiyiwa Allah da Manzonsa ki bar kuɗinki na yafe cinikin bana buƙatar sa*

Alhamdulillah su Moddibo sun sauƙa lfy a ƙasa Mai Tsarki cikin ikon Allah Mabuwayi gagara Misali sunyi
Umarah sun samu goma shabiyar na watan acan cike da ɗumbin farin ciki.

Yau yakasance ranace ta Sallah angama azumi lfya. Al'ummar Musulmai na duniya sun cika da farin ciki
kowa kagani fuskarsa ɗauke da yalwataccen farin ciki, kana kowa yayi shiga ta haiba da kamala.

Alhamdulillah bayan an saƙƙo daga sallar idi ko wani gida kashiga zaka samesu cikin farin ciki da shiga ta
kamala kana da Lafiyayyan abinci.

Kamar yanda ko ina na faɗin duniya ya cika da farin cikin wannan ranan haka yakasance Agidan Lamiɗo.

Acan falon Mommy kuwa hallare suka gaba ɗayan su Khausar ce tsaye riƙe da waya ahanununta cikin
shiga ta alfarma da kamala wani rantsatstsen less ne Blue da ratsin fari ne ajikinta ɗinkin riga da skirt
yayin da skirt ɗin ya fitar mata da shape din ƙugunta rigan kuwa tayi ɗass ajikinta ma dai-dai-tan dukiyar
fulaninta sun cika fam yayin da tayi ɗaurin ƴar Minister ta zubo yalwataccen sumar kanta zuwa baya
daga gaban goshin kuwa ya kwanta luf-luf wuyanta maƙale da sarƙan Gwal da ɗan kunnensa kana
fuskarta ɗauke da simple make up daya sake ƙawata kyawun fuskarta.

Yayin da Raudat ma ke sanye cikin irin shigar dake jikin Khausar sai dai nata ɗinkin dogon riga ne.

Haiydar kuwa sanye yake cikin wata Bugaggiyar shadda Sky blue anyi masa ɗinkin samarin zamani rigar
ta tsaya iya gwiwarsa, kansa sanye da hula yalwataccen sumar irin na fulanin Usul yana kwance lib
aƙeyarsa haka ma Ramadan sanye yake cikin irin shigar Haiydar Yayin da Mommy ke sanye cikin Atanfa
mai Golden mai masifar kyau anyi mata ɗinkin riga da zani fuskarta ɗauke da simple make da Khausar
tayi mata.
Baki ɗaya falon wani sanyayyan ƙamshi yake fitarwa wanda ya haɗu da ƙamshin jikinsu.

Cike da tsantsar farin ciki Khausar dake ɗaukar su hoto ta juya ta kalli Mommy kana tace .

“Kuce Chesss”.

Dariya suka fashe dashi kana suka ce.

“Cheeessss”, Akuma dai-dai lokacin ta ɗauki hoton.

Sosai hoton yayi kyau kallo ɗaya zaka musu ka tabbatar da cewa suna cikin tsantsar farin ciki da
annushawa tare da nutsuwa.

Suna cikin hoton Hajiya Bunayya tashigo cikin shiga ta alfarma da kamala sosai tayi kyau.

Zama tayi bayan tayi Sallama Idanun ta akan Mommy tace.

“Barka da Sallah ƙanwata fatan anyi Sallah lafiya?”.

Murmushi Mommy tayi kana ta zauna kusa da ita tare da cewa.

“Ayyah Yaya ina shirin zuwa wajenki ma”.

Murmushi Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Ayyah babu komai nima cewa nayi bari na rigaki zuwa in samu ladan gaisuwar. Fatan munyi Sallah
lafiya?”.

Jinjina Kai Mommy tayi kana tace.

“Lafiya Lau Alhamdulillah Yaya Ubangiji Allah ya amshi ibadun da ayyukanmu na Al'khairai Allah ya nuna
mana na baɗin baɗaɗa da rai da lafiya”.

Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa kana tace.

“Ameen ya Allah Ƙanwata”.

Khausar kuwa kallo ɗaya tayi mata ta kawar da kai gefe.

Hajiya Bunayya kuwa kallonta ta mayar kan Khausar dake ɗaukar Haiydar, Ramadan, da Raudat hoto,
cike da makirci tayi wani murmushi kana tace.

“Khausar Barka da Sallah”.


Anutse Khausar ta juya ta kalleta babu walwala afuskarta muryarta ta saisaita kana tace.

“Yawwa Barka dai Ummah”.

Hajiya Bunayya ta mayar da kallonta kan Haiydar dake tsaye gefenta hannunsa ta kama tare da damƙa
masa key da murmushi afuskarta tace.

“Ga Barka da Sallah ka Babana”.

Zare ido Haiydar yayi tare da buɗe hannunsa ya kalli sabon key ɗin mashin dake cikin tafin hannunsa,

cike da tsananim farin ciki mara misaltuwa ya faɗa jikin Hajiya Bunayya tare da rungumeta cike happy ya
saƙi ƙara kana yace.

“Wayyo Ummah na Nagode. Allah ya saka da al'khairi. Allah yaƙara miki nisan kwana mai amfani. Allah
yarabaki da sharrin Mutum da Aljan, gaskiya nayi farin ciki kinyi surprise ɗina da kince sai bayan Sallah
da kwana biyu.

Cike da farin ciki tayi murmushin gefen baki kana tace.

“Ameen,Ameen Babana, Eyyyy dama sunce sai bayan Sallah da kwana biyu sai kuma suka kawo jiya da
daddare”.

Khausar kuwa cike da takaicin halayyar matar ta riƙa watsa mata harara wani irin haushin ta takeji,
aƙasan ranta kam cewa take shegiya muguwa aniyar ki ta biki da izinin Allah babu abinda zai samesa.

Mommy kuwa kallon Khausar dake bin Hajiya Bunayya da harara tayi kai ta girgiza tare da cewa.

“Khausar jeki ɗauko mana abinci a kichen ki kawo kin tsaya kin tsare mutane da ido baza ki iya taya ɗan
uwanki samun abin farin cikin da yayi ba”.

Zumɓura baki Khausar tayi tare da miƙewa batare da tace Komai ba tashiga kichen.

Haiydar kam Kallon Mommy Yayi kana yace.

“Mommy Ummah ku tashi nayi muku hoto”.

Miƙewa sukayi da murmushi afuskarsu Haiydar yashiga ɗaukar su.

Khausar kuwa fitowa tayi hannunta riƙe da Warmers dake ɗauke da soyayyun kaji ta ajiye a dining kana
ta koma ta sake ɗauko wasu Warmers ta ajiye.
Dai-dai lokacin da Mommy ke cewa.

“Yaya mun gode sosai Allah ya saka da alkhairi Agaskiya nayi farin ciki”.

Fuskar Khausar ta ɓata kana tace.

“Haba Mommy irin wannan godiyar sai kace wacce aka biyawa Kujeran Hajji”.

Kallonta Mommy tayi kana tace.

“Ai kujeran hajjin ne Khausar, mutumin daya so ɗan ka arayuwa har yayi masa alkhairi ai babu kamarsa
”.

Kai Khausar ta girgiza kawai aranta tace Mommy har yanzu baki san wacece wannan makirar matarba,
shiyasa kike yabonta wannan matar da kike gani tafi kwalba sharri afili kuwa cewa tayi.

“Hmmmm Allah ya kyauta”.

Murmushin da be wuce saman laɓɓaba Hajiya Bunayya tayi kana ta miƙe tare da cewa.

“Nikam zan wuce”.

Miƙewa Mommy tayi tare da cewa toh mungode Yaya Allah yaƙara girma da ɗaukaka”.

Ita kuwa Hajiya Bunayya ficewa tayi Yayin da Haiydar yabi bayanta zuwa sashen Lamiɗo.

yana shiga yace.

“Abba gashi Ummah ta siya min Mashin zan hau?”.

Kai Lamiɗo ya gyaɗa kana yace.

“Babu damuwa tun da kana son hakan, amma kafin nan sai an sake koya maka mashin ɗin na tsawon
wata biyu kafin ka fara hawa kai ɗaya kaga ai ka sake koya”.

Jinjina kai Haiydar yayi kana yace.

“Toh shikenan Abba babu Matsala ”.

Bayan sallah da kwana biyu jirginsu Moddibo ya sauƙa a Nigeria cike da farin ciki Moddibo, Innayi da M
Jameel Ummi suka dawo gida yayin da Hajja Nana ma ta sauƙa ta Ɓadamaye cike da farin ciki da kuma
murna.
**********

Ahaka rayuwa ta cigaba da tafiya komai yana tafiya dai-dai cikin ikon Allah Akwana atashi asaran mai rai,
sekonni na juyawa izuwa Mintuna, Mintuna na tafiya izuwa awanni.

Yayin da awanni ke juyawa izuwa kwanaki, kwanaki na tafiya izuwa Makonni.

Yayin da Mokonni ke juyawa izuwa Watanni. A hankali kuma watanni ke tafiya Izuwa shakara ko
shekaru...

Alhamdulillah su Khausar sunyi nisa kiwo aski yazo gaban goshi, yanzu suna shirye shiryen zana
jarabawar Ƙarshe na kammala secondary School WEAC and NECO baki ɗaya kansu ya ɗauki zafi basu da
wani lokaci saina karatu sosai suka maida hankalin su suna karatu tuƙuru domin fitowa da kyakkyawan
sakamako Inda yanzu ya rage saura Exam biyar ya rage su kammala Neco.

Khausar ce tsaye gaban Dressing mirror jikinta ɗaure da towel da tsawon sa ya kai gwiwarta,

Zuwa yanzu ko ina na jikinta ya cika fam, dukkan ƙirar girma maƙerin budurci ya ƙenƙesa matashi,
musamman Dukiyar fulaninta da kuma hips dinta da suka cika ƙugunta, yalwataccen sumar kanta irin na
Fulanin Usul ya sake tsawo da sansti.

Manyan Idanunta sun sake girma tare da lumshewa siririn dogon hancinta ya sake tsawo yayin da
madaidaicin bakinta ya sake tattarewa izuwa pich collor, yana yin ƙiranta kamar kolbar Coca cola Yayin
da Tsananin kamanninta da Kajol ya sake bayyana ayanzu tana da shekara goma sha tara a duniya.

Cikin sauri ta shafa Lotion ɗin ta tare da shafa powder sama-sama sai kuma ta shafa kwalli amanyan
Idanunta lipstick kaɗan ta shafa asaman laɓɓannta cikin sauri sauri ta sanya Uniform ɗin ta daya sha
guga tulin sumar kanta tayi acuci dashi kana ta feshe jikinta da turarukanta masu masifar daɗin ƙamshi
da sanya nutsuwa.

Cikin Sassarfa ta fito falo harara Mommy ta maka mata kana tace.

“Ke dai Khausar ba zaki canza ba kin girma amma kullum shiririta kike ƙarawa tun yaushe Ake jiranki, ga
Amina ma can tanata jira amma sai ɓata musu lokaci kike”.

Langwaɓar da kai Khausar tayi tare da riƙe kunnenta kana tace.

“Sorry Mommy”.

Fuska ta tsuke tare da ce wa. “Kin dai san Amina in ta gaji da jiran ki”.

Cikin ɗan sauƙe numfashi tace.


“Uhumm ai yaseen in ta gaya min mgn ramawa zanyi in banda asarama tun tuni yaci ace ta gama,
amman kullum taba cikin dakon aji har wai sai yanzu zamu gama tare”.

Mommy na juya zata fita tace.

“A'a ni bana son fitina”.

Ta ida mgnar tana fita,

Haka yasa ta biyo bayan Mommy da ɗan sauri yayin da ko wanni gaɓa na jikinta ke motsa wa baki ɗaya
alamun Budurci sun bayyana ajikinta ta ko wanni fanni ta zama cikakkiyar budurwa ƴar gayu First class.

Bayan motar ta buɗe ta shiga bayan ta ƙarasa wajen gani tayi duk Amina ta wani babbaje.

Kamar ba zata ce komai ba sai kuma tace.

“Ɗan matsamin in zauna”.

Kallon banza Amina ta watsa mata cikin ya mutse Fuska ta kalli Khausar kana tace.

“Keɗin har nawa kike da wannan wajen ba zai ishe ki ba?”.

Cikin juya ido tace.

“Kinsa cikakkiyar sura ta ƙasaitattun mata Allah ya min dole wurin bazai isheni ba tunda ba irin baki
bane”.

Cike da fusata Amina tace.

“Eh lallai yarinyar nan wuyanki ya kai yanka, amman dadin ta dai bada ɗuwawunki nake zamaba kuma
bada ƙugunki nake ɗaura zabi ba”.

Taɓeki tayi tare da juyawa ta kalleta.

Har kamar zata yi magana sai kuma ta fasa ganin yanda lokaci ke tafiya sannan ya Exam na Geography
zasuyi tasan muddin aka fara Moddibo na iya hukuntata baya ga haka ga kuma alamun yau akwai hadari
a garin wanda yau kimanin kwana tara kenan ba'ayin musu ruwan saman ba.

Gefen Haiydar ne ya matsa mata ta shiga kana Driver yaja suka tafi.

Suna Isa Khausar tayi saurin ficewa tare da nufar Hall da zasu zana Exam ta nufi Hall ɗin yayin da Iska mai
sanyi ya soma kaɗawa gari ya fara duhu suna cikin rubuta Exam ɗin hadari ya fara haɗa gangami sosai a
hankali gari ya fara duhu.

Basu wani ja lokaci ba suka kammala rubuta Exam ɗin atare Khausar da Asma'u suka fito.

Asma'u ma ta zama cikakkiyar budurwa komai na Budurci ya bayyana ajikinta.


Juyowa Khausar tayi ta kalleta ƙirjinta rungume da Questions da suka gama rubutawa, murmushi ta ɗan
yi kana tace.

“Asmeey ki gaida min Ummi dan Allah, wallahi nayi missing ɗinta, rabo na da ita fa ya kai wata biyu”.

Hararanta Asma'u liƙa mata kana tace.

“Ai baki da kirkine sannan babu saƙon ki da zan fada mata in da gaskene kizo”.

Ta ƙare mgnar tana mai ɗaga kanta ta kalli sama, ganin yadda gaba ɗaya garin ya rufa yayi duhu.

Da sauri Khausar ma ta fara juye-juye tana cewa.

“Yah Salam wannan hadari haka, ina Haiydar suzo mu tafi, kar ruwa nan ya rutsamu a nan.”

Murmushi Asma'u tayi tare da cewa.

“Allah yasa ya rutsa kin dai muga ta tsoro”.

Ta ida mgnar tare da yin murmushin mugunta dan tasan yadda Khausar ke masifar tsoron walƙiya da
tsawa.

“Ba Amin ba”.

Khausar ta faɗa tare da tura baki.

Ita kuwa Asma'u dariya tayi tare da jan hannun Bashir sukayi gaba saboda yanda hadarin ke sake
gangami ko ina yayi ɗib.

Murmushi Khausar tayi kana tace.

“Bashir dan Allah kagaida Ummi, dan naga yau mutuniyar Black Stomach take ji dashi”.

Asma'u na ƙoƙarin shiga mota tayi murmushi kana tace.

“Oho dai ance zuwa da kai ai yafi saƙo”.

Khausar kuwa murmushi tayi tare da bin bayansu ganin Haiydar yayi gaba.

Da ɗa sassarfa ta tashiga bayan motar ta zauna kusa da Haiydar tana ɗan kallon harabar makarantar da
duk aka watse sai mutane ɗaɗɗaya har malamai da alamun sun tattafi da sauri ta juya ta kalli Haiydar
kana tace.

“Ina Amina kuma?”.


hannu ya buɗe mata alamar bai sani ba, bata sake cewa komai ba,

ta lumshe idanunta tare da jingina bayanta da jikin Kujeran sassayan iskan hadarin dake bugawa na
ratsata.

Acan harabar makarantar kuwa Amina ce da Samira Sani ke tafiya.

Cikin taɓe baki Samira ta kalli Amina kana tace.

“Ni wallahi tunda nake ban taɓa kallon mutum Irin Moddibo ba ace mutum kamar dutse sam baya
fahimtar komai”.

Murmushi Amina tayi kana tace.

“Hmmm ke dai Samira bari M Jameel ɗin ma meyene, duk tsawon lokacin da muka ɗauka muna aiki da
maganin fa yanda yake wani shan min Ƙamshi”.

Harara Samira ta watsa mata cike da takaici tace.

“Amma Wallahi Amina baki da godiyar Allah ki dubi yanda mutumin nan ya fara sake miki, yana amsa
gaisuwar ki da fara'a, yana kula ki da ace nice nasamu wannan damar, awajen Moddibo ai dana godewa
Allah”.

Jinjina kai Amina tayi kana tace.

“Haka ne kuma amma gaskiya har yanzu sai mun sake sabon shiri akansu domin har yanzu Malam
Jameel yafi ji da wannan shegiyar yarinyar akaina”.

Da wannan hira suka isa jikin motar wani matsiyacin kallo Amina ta watsawa Khausar dake bayan mota
Idanunta alumshe cike da gadara da kuma Izzah ta ya mutse fuska kana tace.

“Iyeee ƙarfin hali yau naji Agola da ƙarfin hali, motar na gidan Ubankine da zaki shiga baya kiyi kane-kane
aciki, to ni kuma a ina zan zauna ji yanda kika tara ƙannenki kuka lafe abaya ku gaku ramukan kura ko
daga ke sai ƙannen ki, wai ma tukunna ni akanki zan zauna ne!? Da kika wani baza masaka-masakan
duwaiwaka”.

Ahankali Khausar ta buɗe Idanunta dake lumshe ta zuba mata su tana kallonta cike da mmki, amma ba
tace komai ba sai gyara zamanta da tayi tare da buɗa mata inda zata zauna.

Ya mutse fuska Amina tayi cike da jaraba da kuma gadara ta dubi inda Khausar ta matsa mata kana tace.
“Wannan wani irin iskanci ne da raini ne ko kuma ni sa'ar kice ke badan kinyi sa'ar Babanki ya mutu ya
bar uwarki tayi zawarci babana ya kwasa ba ai koda hanyar da nabi baki isa ki biba. Agola kawai mara
galihu ƴar matsiyata”.

Cike da ɓacin rai Khausar ta ɗago kanta babu walwala afuskarta ta kalli Amina tare da cewa.

“Wai Meyesa kike son zagina ne? Baga shi na gyara niki ba wannan ɗan ɗuwawun da kamar an ɗaurawa
kare zani me zai hana filin isarki, baki shigo kin zauna kinga wurin bai ishi tsamurarrun mauzanki da suke
kamar an matse lemon tsamiba kawai saboda kin saba da Akuyanci da kuma karnukan ci sai kin tsaya
anta masifa dake da raba hali, saboda ke Jaka ce baki san darajar mutane ba, zaki tsaya kina ta goranta
min akan wani Akwalar mota! To ki sani ni dai bazan zagi iyayenku ba musamman mahaifinki da yake
mumini uwarki kuwa zaginta ma asarane don ko zagi akan mai tsarki yake fatan a aikeshi”.

Harara Amina ta watsa mata kana Afusace tace.

“Eh koda Akwalar ce aiba Ubanki bane ya saya idan kuma Ubankine ya saya sai inji? koda yake nasan har
matsiyacin Ubannaki ya mutu bai taɓa mallakar irin wannan na kansa ba!”.

Cike da matsanancin ɓacin rai Khausar ke kallonta idan akwai abinda tafi tsana aduniya kana yake saurin
fusata ta shine zagin mahaifinta.

Azuciye ta sauƙa daga motar yayinda Haiydar da su Ramadan ma suka sauƙo,

cikin nuna Amina da yatsa tare da ƙanƙantar da idanunta kana tace.

“Kada ki sake zagin Ubana domin Ubana yafi ki daraja koda Agaban Ubangiji”.

A yatsine Amina ta watsa mata mugun kallo kana tace.

“An zage sa ƴar iskan yarinya mai hana ruwa gudu ƴar matsiyata”.

Cikin wani irin fushi Khausar ta ɗaga hannunta tare da kife Amina da wani irin azabebben mari hagu da
dama cikin nunuta da yatsa tace.

“Ki sake zagar min Uba kiga abinda zan gwada miki”.

Dafe kuncin Amina tayi cike da Mamaki take kallon Khausar kana tace.

“Ni kika mara Khausar?”.

Harara Khausar ta watsa mata da manyan Idanunta kana tace.

“An mare ki”.


Ahankali Habu Driver ya leƙo kansa tare da faɗin.

“Khausar kiyi haƙuri".

Sai kuma ya kalli Amina dake huci kana yace.

“Amina kema sam baki kyauta ba taya zaki zagi Ubanta ai duk Abinda zakuyi tsakaninku ne”.

Wani shegen kallo ta watsa masa Afusace tace.

“Habu ka rufe min baki ka fita Idona na zagi Uban nata idan taji haushi tabar mana gidan mu ta tafi gidan
Ubanta ƴar matsiyata ƴar jarababbu Angola ta bar nan garin ta koma can dajin nasu mana”.

Ta ida maganar tare da shiga motar taja murfin ta rufe da ƙarfi.

Sai kuma ta sauƙe glass ɗin motar tare da cewa “Haiydar, Ramadan, da Raudat ku shigo motar tunda ku
dai ta Ubanmu ne”.

Cikin takaici Haiydar ya girgiza kai alamar a'a su tafi.

Ita kuwa Khausar ciki takaici ta ɗaga Raudat da Ramadan ta sakasu cikin motar tare da nunawa Haiydar
ƙofar motar alamun ya shiga.

Murya a cushe yace.

“Toh kefa Adda Khausy”.

Cikin danne fushinta tace.

“Kada ka damu zan shiga Napep”.

Zai yi mgn tayi tayi saurin cewa.

“Dan Allah kada kace komai shiga kuje”.

Ta ƙare mgnar tana turashi ciki, dole ya shiga. Ita kuwa Amina tsaki taja tare da cewa.

“Dole su kam shiga ke kuma sai kije can kishiga naki na Uban”.

Kallon Habu tayi kana tace.

“Haba kaja motar mu tafi”.

Da mamaki Habu drive ya kalleta kana yace.

“Haba Amina taya zamu tafi mu barta anan dubi hadarin daya taso sannan babu kowa a haraban
makarantar ya za'ayi mutafi ne”.
Harara ta galla masa kana tace.

“Mu tafi kuma wallahi idan ka ƙi na rantse da Allah saina sa Ummah tasa akoreka”.

Ahankali Haiydar ya juya ya kalli Amina wanda tun da suka fara magana bai sa baki ba yace.

“Haba Addah Amina Meyesa haka Fisabilillah ai koma menene bai kamata ki hanata shiga mota ba dubi
hadari fa kuma kin san yadda take tsoron yanayin ruwan sama”.

Harara ta watsa masa kana tace.

“Rufe min baki an hanata ɗin rufe min baki ɗan Iskan yaro zaka nuna min ƴan Ubanci kenan ruwan ya
cinyata, ta mutuma kawai kowa ya huta”.

Da ɓacin rai Afuskarsa ya kalleta kana yace.

“Ni dai bazan nuna miki ƴan Ubanci ba, saboda bamu tashi da shiba, kuma wallahi idan na koma gida na
faɗawa Ummah ma ke kanki kinsan sai tayi miki faɗa”.

Dogon tsaki taja tare da cewa.

“Kayi sauri kada ƙuda ya rigaka”.

Jin haka yasa Haiydar yin shiru sai kuma ya kalli Amina tare da cewa. “Matsa min In ɗauki jakata bazan
iya tafiya in barta anan ba”.

Girgiza kai Khausar tayi kana tace.

“A'a Haidar kada ka ɗauka ka shiga dasu Ramadan ku tafi nima yanzu zan biyo bayanku”.

Amina kuwa kallon Habu Driver tayi kana tace.

“Mu tafi”.

Jin haka yasa Khausar jan marfin motar tare da rufewa kana tace.

“Pless dan Allah Haiydar zauna ku tafi, in Sha Allah babu abinda zai sameni”.

Dole ya zauba ba don ya soba,

Shi kuwa Habu ba yanda ya iya haka yaja motar ya tafi.

*Yar uwa littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan page ɗin na gama Free page, in dai kin ganshi a waje
to na satane, a Groups ɗina na sakayya ne ɗai ya halatta, 1k ne biya ki karanta cikin Salamah
0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA ban yafe ba a karanta min littafi ba'a biya ba in kin tura
kuɗin ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*
Khausar kuwa shiru tayi tare da bin motar da kallo har ya fice aharabar makarantar, ahankali ta juya ta
kalli cikin makantar babu ɗalibi ko ɗaya duk sun watse haka zalika ma Malamai duk sun watse shiru tayi
sai kuma ta ɗaga kanta sama ganin yanda hadari ya taso ga iska dake kaɗawa da ƙarfi.

Tamkar kazar da ƙwai ya fashewa aciki haka ta fara jan ƙafanta har ta fice acikin Makarantar tsayawa tayi
abakin titin koda zata samu Napep amma takai minti biyar babu abin hawan da yazo ya gifta sakamakon
hadari daya taso sosai a garin yasa dukkan ababe hawa tsagaita zirga-zirga tana nan tsaye har aka fara
ɗan yayyafi hakan yasa ta fara tafiya ahankali a gefen titin.

Ba tayi nisa da makarantar ba taji an buɗe gate ɗin makarantar da ɗan sauri ta juya, akan motar
Moddibo Idanunta suka sauƙa da sauri ta kawar da kanta gefe kana ta cigaba da tafiya.

Acikin mota kuwa Moddibo ne da M Jameel yayin da Moddibo ke Driving M Jameel na gefen me zaman
banza.

Kallo ɗaya Moddibo yayiwa bayanta ya ganeta, baki ya taɓe Aransa yace yau kuma wannan wani sabon
rashin kunya tayi musu suka sauƙeta, sai kuma ya ɗage kafarɗarsa alamun ita ta jiyo.

M Jameel kuwa sam bai ganeta ba saida suka gifta wajenta sannan yaga fuskarta.

Da mamaki ya furta.

“A'a Lelewal”.

Cikin sauri ya ɗaura hannunsa kan Moddibo tare da cewa.

“A.J tsaya Please dubi duk ɗalibai sun watse amma sai ita kaɗai mai ya tsayar da ita anan kuma ga hadari
baƙiƙƙirin dubi fa yanda garin yayi duhu ko Babba hadarin na bashi tsoro yakeyi!”.

Juyawa Moddibo yayi tare da Kallonsa cikin yanayin nutsuwarsa yace.

“To ina ruwanka da ita!?”.

Wara Ido M Jameel yayi kana yace.

“Ban gane ina ruwana da ita ba? ɗalibarmu cefa! sannan kullum a mota ake kawo su sannan zuwa ake
aɗauke su, kana mun ganta ba'a tafi da ita ba sannan ka duba ita kaɗai ce a layin nan dubi fa yanda layin
babu kowa”.

Kallon gefen Ido Moddibo yayi masa kana ya taɓe baki.

Da sauri M Jameel ya cigaba da cewa.

“Haba A.J ya za'ayi kace haka?”.

Moddibo kuwa juya idanunsa yayi kana yace.


“Toh Meye haɗin mu da ita? kasan Meye Uzurin daya tsayar da ita?

Sannan kasan Meye dalilin tsayuwarta! Wata ƙil ma wani bishiyoyin anguwar takeson hawa”.

Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.

“Ai koma mene sai mu tsaya mu tambayeta ko?”.

Kallonsa Moddibo yayi kana yace.

“Nifa bazan tsaya ba”.

Langwaɓar da kai M Jameel yayi kana cikin sanyin murya yace.

“Dan Allah A.J da darajar Annabi Muhammad (S.A.W) mu taimaki yarinyar nan.

Yanzu idan Asma'u ce zaka iya barin ta awajen nan ne?”.

Da sauri Moddibo ya kallesa kana yace.

“Asma'u kuma mai ma zai tsayar da ita anan mai zai haɗa ta faɗa da wasu har tayi musu rashin kunya su
sauƙeta amota, ai Asma'u baza ta kasance haka bama!”.

Sake Langwaɓar da kai M Jameel yayi kana yace.

“Amma kayi tunani ƴa mace ce ita ko addininmu ya koyar mana da kula dasu da kuma kula da al'amuran
daya shafesu A.J bai kamata ba na roƙe ka dan Allah ba danni ba kuma badan ita ba dan Allah da kuma
darajar Manzon mu kayi haƙuri ka tsaya! In ma bazaka ɗauketa ba, ni ka sauƙin bazan iya tafiya in bar
Khausy cikin wannan yanayin A.J bazan iya barin ta ananba”.

Ya ƙarashe mgnar cikin wata iriyar raunatacciyar murya mai fito da sirrin dake binne cikin zuciyarsa.

Hannu Moddibo ya sanya tare da dafe goshinsa alamar ya gaji da damuwar M Jameel ahankali yasanya
lallausan tafin hannunsa ya shafa sajensa ba tare da yace komai ba ya taka burki ya tsaya.

Yana mai kallon yadda M Jameel ya sauƙe numfashi.

Ganin ya tsaya ya sanya M Jameel sakin murmushi tare da buɗe motar ya fita cikin sassarfa da ɗan gudu
ya nufi inda Khausar take dan sun ɗanyi mata nisa kana ga yayyafin da aka fara da ƙarfi da kuma rugugi
alamar ana gaba da kecewa da ruwa mai ƙarfi.

Moddibo kuwa da kallo yabi M Jameel ta mirror motarsa.

Aransa yace Ohhh J ji yanda yake gudu kamar wani yaro ko ya gani a wannan ƴar nan har yake jinta cikin
zuciyarsa.

Khausar kuwa tana ganin M Jameel ta saki nannauyan Ajiyar zuciya tare da cewa.
“Yaya Jameel”.

Cike da kulawa ya kalleta tare da cewa.

“Lelewal mai yafaru yana ganki anan ke kaɗai, bayan baki ɗaya student's sun watse”.

Ahankali ta kallesa sai kuma tayi saurin lumshe Idanunta tare da cewa.

“Wallahi Yaya Jameel Amina ce ta hanani shiga motarsu yau kam masifa take ji dashi”.

Girgiza kai yayi tare da faɗin.

“Subhanallah gaskiya bata kyauta ba, maza zo ki shigo mota mutafi”.

“Toh”,tace tare da bin bayansa cikin sassarfa yayinda ko wanne gaɓa na jikinta ke motsawa.

Ɗan guntun tsaki Modibbo yaja, tare da kauda kansa daga kan madubin, ganin yadda suka wani jero da J
ɗinsa.

Suna isa wajen motar M Jameel ya buɗe mata bayan gefen da Modibbo yake tashiga, sannan shi kuma
ya zagaya ya shiga a hankali Khausar ta ɗaga kanta tare da kallon gaban motar ai kuwa idanunta suka
sauƙa akan Moddibo da batasan yana cikin motar Ba gashi ta zauna asaitin bayansa.

A kuma dai-dai lokaci ruwa ya kece tamkar da bakin ƙorya, key Moddibo yayi wa motar tare da figarta a
dan guje suka fara tafiya.

Kallon Moddibo M Jameel yayi kana yace.

“A.J kasan zamu biya ta gida ka sauƙe ni tun safe Abba ke kirana wai Inje Yana son magana dani muje ka
sauƙe ni”.

Kallon sa Moddibo yayi tare da cewa.

“Baza ka bari sai anjima ba?”.

Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.

“A'a muje dan Allah ka sauƙe ni saboda bansan me yake sona dashi ba yanata ne mana tun tuntuni”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.

“Toh naji”.

Yayi mgnar tare da haharan M Jameel ɗin,

Sannan ya cigaba da Driving ɗin sa.


Shi kuwa M Jameel murmushin yayi tare da ɗan mishi alamun zunɗe.

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan page ɗin na gama Free page, daga gobe in dai kinga littafin
SAKAYYAH a wani wuri to na satane, yar uwa ki biya 1k ne kacal ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin kowa a
kanki littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa kada ki karanta in baki biyaba 0661110170 GTBank AISHA
ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*

Khausar dake zaune abayan motar kuwa ƙanƙame jikinta tayi saboda yanda ɗumin motar ke ratsata sam
cikin motar babu sanyi da yawa ba kamar waje da iska ke kaɗawa ba.

Sanyayyar Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da gyara Questions peper dake hannunta ta sake rungumesu aƙirji
sai kuma ta gyara zaman wuyan hijabinta wanda har tattausan gashin gaban goshinta mai sansti ya
bayyana.

Baki ɗaya cikin motar a wadace yake da wani irin ni'imtaccen sanyayyan ƙamshi mai daɗin shaƙa yakeyi,
Ahankali Khausar ta maida kallon kan bayan Moddibo da take fuskanta sanye yake cikin ɗanyen Boyel
fari ƙal yasha guga sosai yayin da kansa ke sanye da hula zanna bukar wadataccen sumar ƙeyansa ya
kwanto lib-lib gwanin kyau sai sheƙi da ƙyalli yake zubawa.

Ƙeyar tasa ta zubawa ido sai kuma ta gallawa ƙeyar tasa harara tare da murguɗa masa baki.

Tana ɗago Idanunta suka sauƙa akan Idanun Moddibo ta madubin jikin motar yana kallonta cikin mugun
sauri tayi ƙasa da kanta zuciyar ta na mai bugawa da ƙarfin tsiya.

Moddibo kuwa Ƙoffa yayi tare da haɗa harshensa da hoƙorinsa ya fitar da wani sauti kana yace.

“Hmmmm!”.

Kallon sa M Jameel da Idanunsa ke lumshe yayi kana cike da kulawa yace.

“Ya dai A.J?”.

Shiru Moddibo ya masa tare da watsa masa Harara!.

Ware Ido M Jameel yayi tare da shafa sajensa kana yace.

“Ya dai kake ta harare-harare acikin mota!”.


Ƙin tanka masa Moddibo yayi ya cigaba da Driving ɗinsa tare da ƙara tsuke fuska.

Khausar kuwa shiru tayi sai kuma ta sake ɗago kanta ahankali ta kalli madubin ganin ya kawar da kansa
gefe yasa ta sake liƙawa ƙeyansa harara tamkar idanunta zasu manne bisa ƙeyar tasa, kana ta ɗago
hannunta na dama ta ɗan haɗe kan yatsun tare da buɗe su ta watsa masa alamar Jarabebbe!
Mayatacce!! Masifeffe!!! Fitinenne!!!! sai kuma ta sake watsa masa Harara tare da kai hannunta ƙeyarsa
kamar zata kai masa ronƙwashi.

A kuma dai-dai lokacin ya ɗago ya kalleta ta madubin.

Azabure taja baya tare da jinginar da bayanta da jikin kujeran zuciyarta na bugawa.

Cikin fushi Moddibo ya watsa mata mugun kallo tare da cewa.

“Anh zan karyaki wallahi kakkarya ki zanyi in watsar dake atiti inyi tafiyata, ƴar rashin kunya fitsararriya”.

Ita dai Khausar rumtse Idanunta tayi da masifan ƙarfi tare da sake rungume question peper ta aƙirji gam-
gam.

M Jameel kuwa daya ta kure jikinsa waje ɗaya idanunsa alumshe saboda sanyi da ake yayi saurin buɗe
idanunsa yayi tare da kallon Moddibo dake Driving tamkar bashi yayi maganar ba cikin tsaresa da Ido
yace.

“Ha'a wai mai yake faruwa a motar nan ne kake abubuwa iri-iri daga Harara, Ƙoffa, tsaki, tsuke fuska,
yanzu kuma sai cewa zaka kakkarya!,To waima wa zaka karya ne kam?”.

Cikin fushi Moddibo ya juya ya kallesa kana yace.

“Ai duk wanda zan karya ya sani!

Karya yarinyar nan zanyi fitsararriyar banza mara kunya idan kina sake kuskuren kallon min ƙeyata saina
gutsitsi-tsiraki na ƙwaƙule miki manyan mayatattun idonun ki masu kama da na yan maye na jefar! A titi
ko na samu salama”.

Lokaci ɗaya tsoro ya dirarwa Khausar jin wai zai Kakkarya ta ya ƙwaƙule mata ido cike da tsoro ta kuma
ƙara rumtse Idanunta tare da ta kure jikinta ajikin kujera ita kanta batasan dalilin da yasa yake mata
haka ba ita dai tasan da zata samu dama itama karyashin zatayi ta kuna tsitstsige gemunshi.

Akuma dai-dai lokacin suka isa ƙofar gidan su M Jameel Moddibo yayi Parking.

Ɓude Murfin motar M Jameel yayi tare da fita duk da ruwan da ake tsugawa bai hana sa saka kansa ta
cikin glass ɗin side da Khausar take ba, cikin ƙasa da murya yace.

“Lelewal be careful don't Misbehaving kinga bana nan yaseen kika mishi ba dai-dai a titi zai wurgaki ya
tafiyarsa”.
Kai ta gyaɗa masa cike da alamun tsoro sai taji kamar ta fita ta bisa.

Shikuwa M Jameel kallon Moddibo yayi tare da cewa.

“Toh Allah ya tsare Allah ya kaiku lafiya A.J Amana ce, dan amana A.J ka kularmin da ita”.

Daga haka ya juya da gudu ya nufi cikin gida zuwa lokacin duk ya jiƙe saboda yanda ruwan ke sauƙa da
ƙarfi.

Acikin motar kuwa lumshe idanu Moddibo yayi ba tare da yaja motar ba.

Khausar kam ƙasa da kanta tayi aranta tace wannan dai akwai bahagon mutum, fisabilillah yana kallon
yanda ake tsuga ruwa kamar da bakin ƙwarya amma yaja ya tsaya jifa yanda ruwan ke sauƙa.

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan na gama Free page, 1k ne kuɗin samun damar karantawa
0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, biya ki karanta cikin Aminci*

Sun kai kusan minti biyar ahaka ita batace komai ba, haka zalika shima baice komai ba banda sautin
ƙaran ruwa babu abinda ke sauƙa ɗago Idanunsa yayi dai-dai lokacin da itama Khausar ta ɗago Idanunta
ta kalli madubin cikin motar,

idanunsu ne suka sarƙafe cikin na juna.

Harara ya watsa mata kana cikin wata razananniyar murya da shi kansa bai san yana da ita ba yace.

“Uban me kike abayan mota koni.

Driver kine harda wani hakimcewar ki abaya a dole kega Sarauniya kin samu Driver!

Kifita idona fa, nifa ba J bane zan karya kifa”.

Cikin sauri ta buɗe bayan motar ta fita aranta tace Gwanda inyi yanda yake so dan yanda yake kiran zai
karya nin nan inda yazo da tsautsayi sai yajawa Mommy asarata, gaban motar ta buɗe ta shiga amma
duk da haka saida ta ɗan jiƙe sabida ruwan da ya fara ƙarfi, tana zama yaja motar suka tafi.

Akuma dai-dai lokacin ruwan ya sake kecewa da ƙarfin gaske tamkar da bakin ƙwarya ake tsuga ruwan.

Khausar kam lumshe Idanunta tayi aranta tace ya Allah ka kaimu gida lafiya ka rabani da wannan bawa
naka lafiya,
domin akwai rata tsakaninsu da gida sosai ahankali ta buɗe Idanunta ta kalli titin da yayi shiru babu
hayaniyar sai ƙugin motarsu da kuma yanda tayun ke fesar da Iska da ruwan kan kwalta fuuuu kana har
zuwa yanzu garin ɓakiƙƙirin yake duk da kuwa yadda ake sheƙa ruwan alamar har yanzu ruwan bashi da
niyyar ɗauke wa.

Suna cikin tafiya akayi wani irin walƙiya mai haske.

Da sauri Khausar ta rumtse idonta tare da furta.

“Bismillahi”.

A lokacin guda kuma ta sake buɗesu da sauri sabida

jin wani irin rugugi da akayi mai bada sautin rududuuu-duuuuhhh kana ga walƙiya daya haska da wani
irin sauri Khausar ta rungume jikinta waje ɗaya aranta tace.

_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakil Subhanal Lazi yusabbihul ra'adu bi
handihi wal Mala'ikatu min hiyfatin”._

Cikin tsananin tsoro tayi addu'ar domin arayuwarta babu abinda take masifar tsoro a damuna kamar
tsawa da walƙiya sam bata yarda ta haɗa ido da walƙiya da zaran taga za'a yi walƙiya zata rufe Idanunta
ta sunkuyar da kanta.

Shi kuwa Moddibo tafiya ya cigaba dayi yayin da titin yayi shiru babu hayaniyar komai sai bishiyoyi dake
rangaji ruwa na sauƙa akansu Sanyayyar iska mai cike da Ni'imah na kaɗasu baki ɗaya shaguna dake
gefen titin arufe suke baki daya garin babu hayaniya sai jefi-jefi suke hango Mutane.

Suna cikin tafiyar aka sake wani walƙiya mai masifar haske ja, alamun yanzu za'a ƙara kecewa da ruwa.

Atsorace cikin ɗaga sautin murya tace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.

Ta ida addu'ar tare da kife kanta akan gwiwarta yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa A ɗan juya kai
Moddibo yayi kalleta, domin shi kansa zuciyarsa ta harba sabida walƙiyar saida ta ɗauke masa ido
saboda yanda walƙiyar tazo da haske mai ƙarfin gaske sosai yaji tsoron walƙiyar amma sai yayi addu'a
aransa kana yana cigaba da tafiya bai tsaya ba.

Bayan walƙiyar ba daɗewa aka saki wata tsawa mai sautin rututuuuu alokaci ɗaya zuciyarsu ta buga
domin ji sukayi tamkar ƙasa zai tsage.
Atake wani matsananci tsoro ya sake lulluɓe Khausar yayin da jikinta yashiga rawa tamkar mazari kanta
ta kife acinyarta zuciyarta na cigaba da bugawa da masifan ƙarfi kana har zuwa lokacin kanta na sunkuye
akan ƙafafunta tun daga wannan rugugin.

Yayinda gaba ɗaya mazauna garin Gembu Mebila suke cike da taraddadi sabida bisa dukkan alamu yau
da tsawa da rugugin ruwan yake sauƙa.

Acikin haka ne aka sake walƙiya mai masifar haske irin walkiyar nan mai zuwa tamkar an watsa dogon
bulala koko tafiyar maciji,

Da masifar haske da tarsatsi yazo tamkar an watsa bulala Sharrrrrr sai kuma a take aka saki wata iriyar
tsawa mai masifar ƙarfi yabi yo bayansa wanda ke fitar da sautin felelelelelelelen da masifar karaji da
gigita dukkan bani adam

Cikin wani irin tsananin tsoro da gigita Khausar ta saki ƙara mai masifar sauti tare da furta.
_“Hasbunallahu wani'imal wakil. Subhanal Lazi yusabbihul ra'adu bi hamdihi wal Mala'ikatu min
hiyfatihi”._

Atake aka sake sakin wani walƙiyar haɗe da wata iriyar firgitacciyar tsawa mai masifar kara mai razana
dan adam dasa hanjin mutum kaɗawa.

Cikin tsananin tsoro da masifar gigita ta dari ta ɗago kanta a kiɗime ta afkawa jikin Moddibo yayin da
gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa shi kansa Moddibo wani irin tsoro ne ya kamasa saboda hasken
walƙiyar saida ya tsaga glass ɗin gaban motarsa tare da bada sautin ƙarararassss!!!.

Wani irin bugawa zuciyarsa keyi da masifar ƙarfe yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinsa ya ɗauki rawa ƙoƙarin
taka burki yake amma ya gagara saboda yanda ta takure jikinta ajikinsa ta kanainayeshi, bashida wani
kataɓus ɗin motsa wa, sabida yadda ta kife kanta afaffaɗan ƙirjinsa hannunta ɗaya na zagaye da bayansa
yayin da ta cusa hannunta na dama akan maransa.

Moddibo kuwa wani irin masifaffen rawa jikinsa ya farayi tamkar mazari yana wani irin tsuma ji yake
tamkar ana tsikara masa allurai ne agaba ɗaya ilahirin jikinsa lokaci ɗaya wani irin baƙon yanayi ya
ziyarcesa ga fargaban tsawar da har zuwa lokacin bai gama tsayawa ba.

Tsawan na tsayawa wani mai masifar rugugi ya sake sauƙa.

Wani irin masifaffen tsuma jikin Khausar keyi yayin da numfashinta ke fusga saboda tsananin tsoro Allah
ya sani tana masifar tsoton tsawa hakan yasa ta sake ƙanƙamesa tamkar zata tsaga jikinsa ta shige ciki.
Shi kuwa Moddibo baki ɗaya jikinsa tsuma ya shiga yi saboda yanda ta kanainayesa kar-kar-kar haka
jikinsa ke rawa yayin da baki ɗaya tsikar jikinsa ya miƙe daga tsakiyar kansa har zuwa babban yatsan
ƙafarsa yaji wani irin yanayi wanda bai taɓa jiba a iya tsawon rayuwarsa, sai yau kuma yanzu ya jishi.

Wani irin harba zuyarsa da sashi mafi daraja a jikinsa sukayi a tare da wani irin azaban ƙarfi.

Akuma lokacin aka sake sakin tsawa da walƙiya.

Ita kam Khausar cikin tsananin gigita da tsananin tsoro kana da ficewar hayyaci ta sake rungumesu tare
da sake tura hannunta ka maransa yayin da yatsun hannunta suka sauƙa akan cibiyar sa.

Tsawar da aka sake yine ya razana illahirin wani abu mai rai dake yankin Gembu,

yayinda hakan take a wurin Modibbo ma wani cikin rashin sanin makaman kamawa ya ya buɗe
hannayensa ya rungumeta da azaban karfi tare da taka burkin motar da ƙarfi wani irin sautin ƙuuuuuuu
motar tayi tare da cigaba da tafiya sabida tsantsin kwaltan da yayi sabida ruwan sama da kuma tsantsin
sabbin tayoyin da ƙyar ya samu motar ta tsaya a tsakiyar titin, sake Rungumeta yayi da masifar ƙarfe
kana ya cusa kansa atsakanin kafaɗarta da wuyanta.

Lokacin da aka kuma sakin wani irin rugugin nan da zakaji kamar ƙasa na amsawa.

Atake zuciyarsu ya buga da mugun ƙarfi tare da bada sautin dib-dab-dib-dab-difffh yayin da yake jin
wani irin masifaffen abu na tsirgar masa lokaci ɗaya lafiyarsa sa ta shaida mushi kasantuwarsa cikekken
Namiji.

Ita kuwa khausar tana jin yatsarta cikin ɗan hudan cibiyarsa amma tsananin tsoron da take ciki yasa ta
kasa fahimtar menene sai cusa kanta da ta kumayi a kirjinsa.

Shi kam Moddibo wani irin rungumeta yayi da masifar ƙarfi yana mai sakin wani irin amintaccen nish....!

*Free page sun ƙare daga wannan, ko kin ga littafin a wani wuri na satane, littafin SAKAYYAH na kuɗine
1k ne 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP
09097853276. Sai in saki a Group ɗin da nan kadai zanke posting*

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*


_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

*By*

*GARKUWAN MARUBUTA*

SAKAYYA

18
Rungume juna sukayu tamkar zasu shige cikin jikin junansu, yayin da ruwan sama kuwa ke cigaba da
sauƙa tamkar da bakin ƙwarya, kana ga walƙiya da tsawa dake cigaba da sauƙa.

Moddibo shi kam baki ɗaya ya burkice ya rasa tunaninsa, na wushin gadi, gaba ɗaya jinshi yake a wata
duniya ta da ban,

ga wani matsanancin tsoro daya lulluɓe sa kana ga wani baƙon yanayi da yake ji yana yawo agaba ɗaya
ilahirin ajikinsa, wani irin rawa lips ɗin sa keyi tamkar mai jin tsananin sanyi, ga kuma wani irin
azabebben buguwan da zuciyarsa keyi da masifaffen ƙarfi yana bada sautin dib-dab-dib-dab.

Haka zalika Khausar dake rungume dashi, itama haka zuciyarta ke bugawa,

sake ƙanƙamesa tayi da ƙarfi tana mai tura kanta afaffaɗan ƙirjinsa da bottle din gaban rigar suka buɗe,
hakan ya bawa fuskarta damar mannewa farar afaffaɗan ƙirjinsa dake ƙawace da tattausan gashi baƙi
mai sulɓi.

Wani irin fusga numfashinta keyi saboda tsananin tsoro da firgici da tashin hankali, haka yasa idan taja
numfashin sai ta ɗauki sekon talatin Kafin ya dawo.

Ko kaɗan Moddibo bai da wani kataɓus sabida yanayin da suka kasance a ciki, sake rungumeta yayi tare
da cusa kansa atsakanin wuyanta da kafaɗarta.

Daga can bayansa yake jiyo sautin ƙaran mota tana danna masa ɗiyyyyttt-ɗiyyyytttt, yasan shi akeyiwa
hon ɗin, amman sam baya jin zai iya koda kwakwaran motsine.

Shi kuwa mai motar dake bayansa, ganin shiru bai motsa bane, yasa ya ɗan ratsa ta gefensu ya fuce yana
dan leƙawa ganin ko lafiya kasancewar. Atsakiyar titin suke ganin babu wani alamun hatsari ko damuwa
yasa ya wuce.

Moddibo kuwa da ƙyar ya iya buɗe Idanunsa tare da ɗago kansa still ruwan ake sheƙawa zuwa yanzu
harda ƙanƙara yana jin yanda sautin ƙanƙarar ke sauka asaman motarsa fat-fat-fat ko kaɗan baya kallon
komai duk da kuwa gashi idanunnasa abuɗe suke, amman ina ganinsa ya ɗauke makanta ta meye gurbin
ganinsa, ya zama sam baya gani, kana ji yake jikinsa kamar shanyeyye.

Daƙyar ya iya ɗaga hannunsa tare da dafe kansa da yake jin wani irin jiri na fizgarsa tare da sarawa, da
sauri ya sake sunkuyar da kansa akan wuyanta kana ya sake rungumeta da ƙarfi baki ɗaya ya rasa wani
irin yanayi yake ciki.
Khausar kam sam batama san wani irin yanayi take ciki ba sam bata cikin hayyacinsa, hakan yasa ta sake
rungume Moddibo da ƙarfi,

Jin yadda take liƙewa a jikinsa ne, yasa shima ya saƙe yi mata wani irin amintaccen rugguma tare da
fesar da wani irin raunataccen numfashin yana mai shaƙan ƙamshin jikinta.

Itama sake rungumesa tayi cikin mawuyacin hali tana neman numfashi domin numfashinta na ƙoƙarin
ɗauke wa gaba daya tsananin tsoro da tashin hankali ya bayyana asaman fuskarta, duk da sanyi garin da
kuma yanda ake tsuga ruwa amma goshinta na na tsastsafo da zufa kana jikinta ya ɗauki ɗumi.

Cikin wani irin yanayi mai wuyar fassarawa da ficewar hayyaci Moddibo ya sake rungumeta yana jin
ɗumin jikinta kana yana mai furta.

“Hasbullahu wani'imal wakin, Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n La'ilaha Illah anta subhanaka Inni ukuntu
Minal Zhalimin, Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha”,Kana ya cigaba da karo to duk
wata addu'a da tazo bakinsa cikin fitar hayyaci, Allah ya sani kuma shine shaidarsa ya rasa yanayin da
yake ciki shin mutuwa zaiyi ne, koko kuma sumewa yake shirin yi,

domin jinsa yakeyi tamkar yana tafiya cikin sararin samaniya ne bisa gajumare,

ji yake tamkar fuka-fuki garesa ya kasa tantance shin mafarki yake ko kuma azahirance ne kana yakasa
tantance shin a sumen yake ko kuma amace yake, cikin rashin sanin madafa ya cigaba da karanto duk
wata addu'a da tazo bakinsa.

Yayin da numfashi Khausar ke cigaba da fusga,

adduo'i ya cigaba dayi cikin ikon Allah Albarkanci Adduo'i da yake da kuma zuciyar namiji dake da dakiya
yasa yafara dawowa hayyacinsa amma still Idanunsa basa gani mai kyau.

Ganinta kwance ajikinsa tana fuzgar numfashi yasanya shi sa. Lallausan tafin hannunsa ya tallabo
fuskarta tare buɗe manyan idanunsa da ƙyar dan har yanzu dishi-dushi yake gani, idanu ya tsirawa kan
goshinta daya tsats-tsafo da zufa, sai kuma ya rumtse idanun da karfi kana ya buɗesu tare da zura ido na
daƙiƙu bakwai sai kuma ya juya idanun zuwa kan wuyan hijabinta daya zame daga kanta zuwa kafaɗarta
yalwataccen sumar kanta mai tsayi da ƙamshi ya zuba agadon bayanta, yayinda saura kuma ya zuba
asaman fuskarta, kallonsa ya mayar kan fuskarta jin, yanda numfashinta ke fusga. Idanunsa ya mayar kan
ƙirjinta da sauri ya lumshe idanun sai kuma ya buɗesu, ganin yanda numfashinta ke hawa da sauka
alamun zata sume a ko wanne lokacin.

Ganin tana gab da sumewane ya sanyashi sun kuyar da kansa kaɗan, zuwa kan fuskarta kana ya ɗaura
lips ɗin da suke masifar rawan sanyi akan karan hancinta, lumshe manyan idanunsa da suka sauya launi
zuwa ja yayi, tare da fesa mata sanyayyan numfashinsa domin dai-dai ta mata nata numfashin, domin
duk da tsoron da kuma firgicin da yake ciki hakan, bai sanya numfashinsa ɗauke wa ba, kana yana kallon
fuskarta wanda akowani lokaci zata iya suma, sai kuma ya sanya hannu ya toshe hancinta tare da ɗaura
sanyayyan lips ɗin sa akan nata ya riƙa hura mata iskar bakinsa mai ɗumi da kamshi ceto rayuwa zuwa
gareta,

Wani irin dogon numfashi taja mai nauyi tare da fesar dashi da ƙarfi, cikin daƙiƙu kaɗan numfashinta ya
soma dawowa dai-dai kana duk abinda ke faruwa idanunta na lumshe.

Sannan har zuwa lokacin hannunta na kan mararsa, saman yatsarta na kan hudan cibiyarsa, sannu
ahankali numfashinta ya dai-dai ta sai dai har zuwa lokacin bata dawo hayyacinta ba, still kuma ruwan
ake cigaba dayi tamkar da bakin ƙwarya ita ko sai wani irin sakewa tayi tare da lafewa a jikinsa tana
shaƙar ƙamshinsa.

Shi kuwa Moddibo sannu ahankali ya fara dawowa hayyacinsa da nitsuwarsa.

Sake lafewa Khausar tayi ajikinsa tare da lumshe Idanunta domin ganin abun take kamar mafarki, ko
kuma mutuwa tayi tsaban masifar tsoron rugugin da take.

Shi kuwa Moddibo sannu ahankali cikin ikon Allah ya dawo hayyacinsa, kana har zuwa yanzu tsikar
jikinsa na tashi yayin da kansa ke juyawa jiri na ɗibarsa.

Ahankali ya sauƙe idanunsa akanta data manna a ƙirjinsa, yayinda tattausan suman kanta ya baje
aƙirjinsa, kallonta yakeyi kamar ya samu sabuwar halitta, kana aƙasan ransa ke mgnar zuci,

Wai yaya haka ne? Mekw faruwa? Wai ma waye ni?

Ya tambayi kansa da kansa,

Kaine Moddibo, sannan wannan Khausar ce kwance ajikika tana rungume dakai cikin yanayin da
ma'aurata ne kaɗai ya halatta su kasance ciki.

Wani sashi na zuciyarsa ya bashi amsa.

Lokaci ɗaya kuma jikinsa ya sake ɗaukar rawa far-far tamkar wanda ake sheƙa masa ruwan ƙanƙara lips
inshi kuwa, wani irin masifeffen tsuma sukeyi,

lumshe idanunsa yayi jin jikinsa babu kuzari kona misƙala zarratin, ji yake tamkar an zare masa lakar
jikinsa cikin sanyi da rashin kuzari dake tare dashi.

A hankali ya sake birkitota tare da ɗago kanta ya ɓanɓareta daga jikinsa gani yayi Idanunta alumshe.

Ita kuwa Khausar ji take tamkar cikin bacci take, ko kuma suma ta kasa fahimtar kalar yanayin
da dai take ciki,

Shi kuwa Modibbo kanta ya tallabe da hannunsa ɗaya yayin da ɗaya hannu yake ɗan marin fuskar yana
faɗin.

“Ke! Keh!!”.

Shiru bata motsaba, hakan yasa ya sake ɗan fizgo muryasa tare da faɗin.

“Khausar! Khausar!!”.

har zuwa lokacin tana rungume jikinsa

For the first time arayuwarsa da bakinsa yafara kiran sunanta.

Fuskarta yake ɗan yiwa ƙananan maruka ahankali kana cikin wata Sanyayyar murya mai cike da
tattausan lafazin yake fadin.

“Khausar!, Khausar!! Khausaaaar!!!”.

Lumshe idanunsa yayi shi kansa bai san yana da irin wannan raunataccen muryar ba, ya rasa
taƙamemmen yana yin da yake ciki, yayin da aƙasan ransa so yake ya mata faɗa da tsawa da masifar ta
sauƙa jikinsa, amma ya kasa kasancewar har zuwa lokacin bai gama dawowa cikin ainihin nutsuwarsa ba.

Kumatunta ya cigaba da ɗan mara yana faɗin.

“Khausar!, Khausar!!”.

A hankali kanta ya zame daga hannunsa ya tafi gefe luuuh kamar sumammiya.

Lokaci ɗaya zuciyarsa ta buga da ƙarfin gaske tare da jin tsinkewar zuciya ganin yanda Kanta yayi kamar
ta mutu!.

Cikin ɗaga sautin murya ya sake ɗan marin kuncinta tare da cewa.

“Khausar, *Lelewal*”.

Khausar kuwa still Idanunta na lumshe take Jin sautin muryar Moddibo na kiran sunanta kamar amafarki
ko kuma daga can sama.

Sai kuma ta sake jiyo sautin muryarsa da alamun kiɗima yake cewa.

“Ya salam Lelewal meya faru? me ya sameki?”.


Ahankali ya sanya hannunsa tare da ture hijabinta kana ya sanya hannunsa aƙirjinta wanda har yana iya
jin tudun caɓɓullen ta ahannunsa ji yayi ƙirjinta na bugawa da ƙarfi-ƙarfi.

Hannunsa ya cire tare da sunkuyar da kansa har suna shaƙar numfashi bakin juna, bakishin yakai kan
kunnenta kamar meyu mata raɗa yake faɗin.

“Lelewal tashi! Lelewal buɗe idonki!! Lelewal kalleni”.

Lumshe Idanunsa yayi akaro na barkatai tare da kai bakinsa cikin kunnenta kana cikin Sanyayyar murya
mai taushi yace.

*“Fattanah!”.*

Dogon numfashi taja tare da sauƙe nan-nauyan ajiyar zuciya tare da buɗe Idanunta sai kuma ta sake
runtsesu da sauri gani take tamkar har yanzu rugugin akeyi kana walƙiyar zai iya kashe mata Idanu.

Bayan kamar daƙiƙa ɗaya ta sake buɗe Idanunta still yana ronƙofe akanta yana shaƙar ƙamshin
numfashin dana gashinta dake baje.

Yayin da har zuwa yanzu hannunta ke cikin sa yatsunta guda uku nakan cibiyarsa tafin hannunta da
sauran yatsu biyun nakan ainihin mararsa ta danne.

Cikin wata sanyayyar murya ya tsira mata idanu tare da faɗin.

“Lelewal”,Ya faɗa still yana tallafe da kanta.

Buɗe Idanunta tayi sai kuma ta sake rufewa,

Akuma dai-dai lokacin Moddibo da itan duk suka gama dawowa cikin hayyacinsu tare da nutsuwar.

Cikin sauri tare da fushi

Moddibo ya kalleta a tsawace yace.

“Keee!!! Tafi can Mage uwar fitina tashi akaina ko in kakkaryaki”.

Ya dire mgnar cike da tsawa tare da yarfa mata mari da bayan hannunsa.

Shi kansa jin maganar yayi ta fito daga zuciyarsa kai tsaye kamar an fisgo a bakinsa.

Azabure Khausar ta buɗe Idanunta dake lumshe tare da janye jikinta daga nasa amma still hannunta na
kan cikinsa tana murza cibiyarsa.

Wani mugun kallo mai cike tarin kufula, takaici, tsuyan zuciya, da tarin ƙunci ya watsa mata firgitaccen
kallo. Ta da ɗaga hannunsa cikin wani irin masifeffen rawan jiki da gigitan yanayi yasanya tafin hannunsa
ya finciko hannunta dake kan cikin sa da masifar ƙarfi ya yarfa hannun nata har saida ta saki ƙara, dan ji
tayi kamar zai ɓalla mata hannun.

Shi kuwa a take kuma tsikar jikinsa ta mimmiki ta tashi.

Cikin tsananin tsoro da firgici Khausar ta janye jikinta kana ta koma ta mannu da jikin kujera tare da
rungume kanta a can gefen jikin kujeran motar tana mai jin raɗaɗin marin.

Moddibo kuwa da ƙarfi ya rumtse idanunsa sabida wani irin masifaffen har bawa da yaji zuciysrsa nayi
da masifar ƙarfi, lokaci ɗaya wani azabebben zufa ya wanke sa kana rawan da lips ɗinsa keyi ya tsananta
karkarwa yayin da har hakoransa ke rawa har suna bugun juna saboda wani masifaffen abu da yaji yana
yawo cikin kwanyar kansa, wani irin baƙon yanayi yaji ya taso masa da azaban ƙarfi, abinda bai taɓa jiba
atsawon shekaru.

Cike da dauriya da kuma fushi ya figi motar da gudu yayin da zuciyarsa ke wani irin azalzala idanunsa
kuwa har yanzu dishi-dishi suke gani sanna, sai wani irin rawa jikinsa da lips inda keyi, cikin mintunan da
basu gaza goma ba taji yayi Parking aƙofar gidansu.

Cikin tsananin tsoro da ruɗu ta buɗe murfin motar, cikin sauri ta fice batare data lura da ɗan kwalinta da
kuma hankief ɗin ta dake kan cinyar Moddibo ba.

Da ƙarfi yafi gi motar cikin mintuna kaɗan ya isa gidan yana parking ya fito.

Lokacin ɗaya ya jiƙe jikib saboda ruwan da ake cigaba dayi kamar da bakin ƙwarya.

Cak ya tsaya Atsakiyar gidan nasu, ruwan na sauƙa atsakiyar kansa saboda masifeffiyar baƙon yanayi da
yake ji ga kuma suya da raɗaɗin da zuciyarsa keyi, na firgicin saɓawa Ubangiji da yayi, tsoron Allah da
tarin damuwa ne ya sanya idanunsa fara zubda wasu irin zafafan hawaye masu ƙuna.

Rumtse idanun da yayi tare da furta.

“Astagfirullah wa,atubu ilaik, Ya Allah kaine mafi sanin zuciyata, Yah Allah ka gafarta min ya Allah ka
shafe min wannan zunubi, ya rabbi kada ka sake bani damar sake saɓa maka Yah Allah ka sani ban taɓa
aikata makamancin hakaba,”. Gaba ɗaya muryarshi rawa takeyi, yayinda idanunsa ke kwaranyar da
hawaye.

Duk da ruwan na dukansa amma ko kaɗan baiga alamar zaiji sauƙin abinda ke damunsa ba. ji yayi tamkar
ya ɗora hannunsa a ka ya rinƙa ihu da kururuwa. Duk da dauriyarsa kuwa, bai san sanda kuka ya kubce
masa, domin duk sauƙan ruwan akansa ji yake kamar ana ƙara rurumashi wutar fitina a jikinsa, ga kuma
ƙuncin zaciya da yake ji,

Har lau haƙoran sake dukan juna suke nusa bada sautin Ƙat-ƙat-ƙat baki ɗaya jikinsa rawa yake tamkar
mazari ahankali ya sunkuyar da kansa gani yayi yadda muhallin sa ya sake masifar nuna zalamarsa.
Cikin mawuyacin hali ya dafe kansa da hannunsa na hagu murya narawa yace.

“Wannan wace irin masiface? shin wannan wani irin abune mai wuyar jurewa me yake yafaru dani ne
wai? Shegiyar yarinya mai fitintinun al'amura, ya Allah ka isarmin da cutar dani da tayi, Yah Allah kaga ita
ta riskeni kaine shaida ni ban nufetaba, Allah ka isarmin kan wannan muguwar yarinya mai jikin zalumci
Astagfurullah”.

Ya ida maganar tare da fashewa da kuka, still dai yana tsaye acikin ruwan yana cigaba da dukansa, ganin
sam kuma abin nasa yaƙi nitsuwa ne yasa ya nufi hanyar sashensa domin sakarwa da kansa ruwan ɗumi
koda zaiji sauƙin abinda ke damunsa, abakin faradan Falon sa ya tsaya tare da zare rigar dake jikinsa
kana ya zame wandon ya shanya ya rage daga shi sai boxer Kai tsaye toilet ɗin sa dake cikin Bedroom
ɗinsa ya nufa yana shiga ya sakarwa da kansa ruwan ɗumi batare daya cire boxer ba yana tsaye ruwan
ɗumin ya cigaba da zuba akansa amma babu abinda ke yawo a idanunsa kamar lokacin daya rungumi
yarinyar ga wani masifaffen ƙamshinta da yake ji ajikinsa da ƙarfi ya matse jikinsa waje ɗaya kana cikin
tsanananin tsoron Allah ya ci gaba istigfari.

“Astagfurullah wa'atubu Ilaik ³ ya Allah na tuba kayafe min wannan abin da nayi. Ya Ubangijina na tuba”.

Kai kawai yake girgiza wa cike da tashin hankali mara misaltuwa daya rufe idanunsa babu abinda yake
hange face yanayin da suka kasance amota.

Acan ɓangaren Khausar kuwa da gudu ta shiga gida tare da wucewa Falon su.

Tsaye ta samu Mommyn ta cikin yanayin damuwa da tashin hankalin.

Mommy na ganinta ta saki ajiyar zuciya mai nauyi tare da cewa.

“Alhamdulillah Khausar kin dawo, gaba ɗaya hankalina ya tashi na kasa zaune na kasa tsaye, tunda
Haiydar ya dawo ya faɗa min yanda ku kayi da Amina!”.

Ida mgnar taba kallon yadda jikin Khausar ke ɗigar da ruwa ga wani rawa da jikinta keyi cikin jin ƙai da
tausayawa tace.

“Amina bata kyauta min ba. Wallahi Allah Amina bata taɓa yimin abinda ya ɓata min rai irin na yau ba,
ya za'a yi cikin wannan hadarin cikin wannan yanayin ta baro min ke a makaranta.

Yanzu waya dawo dake?”.

Cikin karkarwa na tsoro da sanyi ga kuma zogin mari tace.

“Uhhhmmm”.

Ita kuwa Mommyn cikin sanyi tace.


“Yanzun nan dama Abbanku nake jira? ya dawo dan baya nan na faɗa masa kina cikin makaranta. Yanzu
yana dawowa ne akan zai ɗaukeni muje can ɗin”.

Cikin sanyi da yanayin tsoro da kuma ruɗu Khausar ta dubi Mommy yayinda, jikinta ke rawa kamar zata
faɗi.

Kallonta Mommy tayi cike da tausayinta ta girgiza kai kana tace.

“Gashi na sani Khausar yanda kike rikicewa idan kikaji rugugi kike fita hayyacinki idan kika ga walƙiya
bare kuma kiji tsawa!.

Gashi yau kuma ruwan yazo da wasu irin tswawwaki masu ban tsoro.

Cikin rawan jiki ta sanya hannunta dake ta karkarwa ta janye Hijabinta kana ta kalli Mommyn Muryanta
na rawa tace.

“Yah Jameel ne ya kawo ni”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe kana tace.

“Kai Ubangiji Allah yayi masa albarka. Allah ya saka masa da mafi kyawun sakamakon”.

Kai Khausar ta gyaɗa still jikinta na tsuma tace.

“Ameen Mommy bari in cire kayana”.

Ta ida mgnar tare da wucewa Bedroom ɗin ta tana shiga ta kalli hannunta lokaci ɗaya ta sake shiga
sabon tashin hankali, cike da damuwa ta yarfe hannunta kana tace.

“Nashiga uku Ni Faɗimatuzzahara ina nasanya hannu na! Ni Batula?”.

Duk da cewa tana cikin tsoro amma tana sane da inda ya zaro hannunta kai tsaye toilet ta Wuce tare da
cire kayan jikinta ta sakarwa kanta ruwan ɗumi sabulu ta ɗauka ta mulke hannunta dashi kana ta shiga
gogawa ajikin tiles dake jikin bangon tana Girgiza Kai kana tana mai Furta.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Astagfirullah wa'atubu ilaik Subhanallah ya Salam Allah na tuba”.

Da ƙyar ta iya yin wankan ta fito bayan ta ɗaura alawalan tare da buɗe Siff ta ɗauki dogon riga na roba
baƙi ta sanya har zuwa lokacin jikinta na ƙamshin tularensa Sallaya ta shimfiɗa ta gabatar da Sallah kana
ta riƙe carbi tana hawaye da Istigfari.
Acan ɓangaren Moddibo kuwa bayan ya gama wanka al'wala ya ɗaura tare da fitowa har zuwa lokacin
zuciyar sa na tsaye alamar zai samu nitsuwa Siff ya buɗe tare da ɗaukar Boxes ya sa sai kuma ya tsaya
yana kallon kansa, ya tabbata idan yasa Jallabiya mutane zasu iya fahimtar halin da yake ciki wani dogon
tsaki yaja.

“Mitsssssssss!!! Yar iskar yarinya”.

tare da sanya hannunsa ya matse muhallinsa da ƙarfi wai ko zai masa biyayya cikin yanayin tashin
hankali ya kalli kuma sunkuyar da kansa tare da faɗin.

“Wai wannan wacce iriyar Masifa ce!?”.

Sake buɗe sabbin boxers ɗin sa dake cikin leda yayi ya ciro wani ƙarami wanda yake zaton zai masa
kaɗan shiyasa ma bai taba sakasu ba,

Cikin yamutsa fuska ya sanyashi,

sosai ya matsesa sai dai har zuwa lokacin al'amarin azimunne.

Wani boyel baƙi mai kyau ya ɗauka ya sanya kana ya feshe jikinsa da turarukansa cikin sanyin jiki ya fita
zuwa Masallaci ya gabatar da sallah Azahar.

A wunin wannan ranan dai baki ɗaya haka yayita agigice.

Acan gidan Lamiɗo kuwa Hajiya Bunayya ce zaune akan 3sitter yayin da Amina ke gefenta riƙe da kofin
shayi yana tururi.

Anutse Hajiya Bunayya ta juya tare da kallon Amina data kai kofin shayin bakinta kana tace.

“Amina yanzu ya kuke da Malam Jameel ne? nifa nagaji da wannan al'amarin kullum sai munga Abu
kamar yaci sai kuma kiga abu ya sake ta ɓarɓarewa!”.

Gyara zama Amina tayi tare da ajiye Cup ɗin tea kana tace.

“Hmmm ba gwara ma muba akan Samira Sani, sufa duk abinda suke kamar anshuka dusa shi Moddibo
na nan kamar Waliyyi baya fahimtar karatunta shu'umanci bare ya ratsasa kamar kurma baya ma
sauraronta bare kuma ya sake mata fuska”.

Ta gumi Hajiya Bunayya tayi tana cigaba da sauraren Amina.

Amina ta cigaba da cewa.


“Amma kinga gwara Ni dama Malam Jameel Yana da sauƙin kai sannan yanzu ya daina shash-shareni
idan na gaishesa yana Amsawa cikin sakin fuska da mutunci mun koma kamar da duk da dai dama haka
halinsa yake ga kowa”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.

“Kawai dai abinda nake gani Ummah kawai Abbah ya masa magana idan Abba ya masa magana kan
cewa Ina son sa bazai ƙini ba, saboda yana da kirki yana da mutunci da kawaici ko ba komai kuma gidan
dala yake domin nifa kuɗin mahaifinsa nafiso, badon kuɗin da suke da shiba, nafi son miji irin Modibbo
mishkili, ba sake fuska dan sunfi iya soyayya”.

Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta sauke tare da gyara riƙon wayarta kana tace.

“Anya Amina za'ayi hana kuwa? Ai gwara dai mujawo hankalinsa zaifi, kuma batun kuɗi yoh dama ai shi
mukewa bauta domin duk abinda nake kashewa a wurin boka ina lissafawa kina shiga daga ciki zaku
biyani”.

Kwaɓe Fuska Amina tayi kana tace.

“Kayya Ummah tun yaushe mukeyi amma abin baya wani kamasu gwara ma Malam Jameel Idan munyi
munga Abu ya kama kwana biyu sai kuma ya dawo baya kula har kata! anata ƙara lissafin kuɗin da zan
biya”.

Kai Ummah ta gyaɗa kana tace.

“Gaskiya dai kam in dai hakan zaiyi sai in faɗawa Mafaifinku yafi min kwanciyar hankali ma amma ko.
Abbanku baza mu fuskance sa kai tsaye haka ba dole sai anja hankalinsa akan maganar”.

Ta gumi Amina tayi tare da cewa.

“Toh Ummah acanza wani boka mana?”.

Saurin Kallonta Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Wani boka muke dashi da yafi wannan?,Duk aikin sai yace ana wasa dashi sannan aikin kuɗi yake
buƙata sosai kuma kinga Yanzu bani da kuɗi sosai Amina, kuma ai tunda muka canza boka Zurau wannan
duk aikin da yake min yana ci”.

Taɓe baki tayi tare da cewa.

“Gaskiya Ummah asamu ayi aikin nan idan muka samu nashiga gidansu zamu fanshe duk kuɗin da muka
kashe!”.

Jinjina kai Ummah tayi kana tace.

“Zanyi ƙoƙarin hakan in Allah ya yarda”.


Acan ɓangaren su M Jameel kuwa bayan ya shiga gida ya sauya kayansa zuwa blue jeans da farin t-shirt
mai dogon hannu kana ya gabatar da Sallah Azahar Yana idarwa ya nufi sashen Mahaifinsa zuwa lokacin
ruwa ya tsaya bakinsa ɗauke da sallama ya shiga kana ya zauna kusa da Abbansa.

Kallonsa Abba yayi bayan sun gaisa yayi gyaran murya tare da cewa.

“Dama batun Company Adamawa ne acikin kayayyakin da aka kawo muga ya yanayin ingancinsu akwai
atomfofi,

Gyaleluwa da kuma sauran kayayyakin ya kamata kaje”.

Jinjina kai M Jameel Yayi kana yace.

“Toh shikenan Abba yaushe ne tafiyar”.

Kallonsa Abbah yayi kana yace.

“Insha Allah tafiyar zai kasance idan kun gama jarrabawar ɗaliban ku da zasu gama makarantar bana
nasan zuwa lokacin hankalinka ya kwanta Asma'u da Bashir sun kammala Secondary School”.

M Jameel kuwa jingina kansa da jikin kujeran yayi tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Hakane kam Alhamdulillah yanzu kam na gama sun gullarsu Asma'u”.

Dai-dai lokacin da Hajiya Karima ta shigo falon Abba na cewa.

“Kaga yanzu shikenan tun da kagama da wannan shungullan gaba ɗaya duk abinda ya shafi shungullana
da kuma harƙoƙina, kasuwancina duk zan danƙasu ahannunka Babana.

Domin ni girma ya fara zuwa Inason hutu”.

Murmushi M Jameel Yayi kana yace.

“Toh shikenan Abba babu damuwa duk abinda kace shi za ayi da izinin Ubangiji”.

Murmushi Abba yayi har cikin ransa yake jin ƙaunar ɗan nasa saboda yanda yake masa biyayya ajiyar
zuciya ya sauƙe kana yace.

“Toh Nagode Allah yayi maka Albarka”.

Duk abinda suka tattauna Hajiya Karima na rakuɓe tana jin tattaunawar su Amaryan Abban Jameel Hajia
Turai ta shigo ganin Hajiya Karima atsaye yasa ta faɗin.

“A'a Lafiya kike tsaye anan Hajiya Karima?”.

Cikin sauri ta juya, sai asannan Abba da M Jameel suka juya suka ganta tsaye.
Murmushin da bai wuce saman laɓɓabanta ba tayi kana tace.

“Yanzu na iso ina gyara labule nai”.

Ita dai Hajiya Turai batace komai ba ta ƙarasa shiga falon kana Hajiya Karima tabi yo bayan suka cigaba
da hira.

Washe gari.

Cikin sanyin jiki da damuwa Khausar ta shirya cikin Uniform ɗin ta dake haska fatarta baki daya ta kasa
sakewa da zaran ta tuna inda ta sanya hannunta sai taji tashiga matsanancin tashin hankali.

Cikin sanyin jiki ta fita tare da nufar inda motarsu ke fake Amina ce tafito hannunta riƙe da lunchbox ɗin
Aminu dai-dai lokacin da Lamiɗo ya fito daga sashen Gimbiya Dadu da fuska a tsuke ya kalli Amina tare
da cewa.

“Banaso Amina kada ki sake yi min abinda kikayi jiya banaso haka ki kiyayeni! Ki kiyayeni!”.

Ƙasa tayi da kanta kana tace.

“Toh Abba kayi haƙuri”.

Sannan ta juya ta shiga, kana su Khausar ma suka shiga mota ko acikin mota Khausar jingina bayanta da
jikin kujera tayi tare da damƙe hannunta ahaka har suka isa makarantar.

Anutse ta fito ta tashiga hall da suke Exam kai tsaye bencin da number ta ke kai ta nufa tare da zama
kana ta dafe kanta ba jimawa Malam Isa ya shigo ya fara raba musu Booklet da questions na Economics.

Kallon Khausar data dafe kanta da hannu biyu yayi kana yace.

“Lelewal meke damunki?".

Da sauri ta ɗago kanta ta kallesa sai kuma ta girgiza kanta cikin sanyin murya tace.

“Ba komai Malam”.

Question peper ya ajiye mata kana ya cigaba da rabawa sauran.

Cikin mutuwar jiki Khausar ta riƙa yin amsarin Questions ɗin tun kafin a miƙa wa wasu Questions pepar
tuni ta gama Amsawa kwantar da kanta akan deks ɗin tayi tana godewa Allah daya sa basu da Exam din
Moddibo da batasan da idon da zata iya kallon sa ba.

Moddibo kuwa tunda yashigo makarantar ya wuce office ɗin su ya zauna cikin zullumi da damuwa.
Ahankali M Jameel ya fito daga class da yake teaching hannunsa riƙe da booklet ya nufi Office ɗinsu
bakinsa ɗauke da Sallama yashiga zaune ya samu Moddibo idanunsa na rufe kana lips ɗin sa na rawan
sanyi ahankali.

Booklet ɗin ya ajiye tare da zama gefensa kana yace.

“A.J meke damunka?”.

A hankali Moddibon Ya jujjuya idanunsa dake lunshe yayi kana ya Girgiza masa kai tare da cewa.

“Bakomai”.

Kallonsa M Jameel Yayi kana yace.

“Ya zaka ce min bakomai A.J ke faɗa min meke damunka ko dai baka da lafiya ne?”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da gyaɗa masa kai.

Cikin damuwa M Jameel yace.

“Toh meke damunka?,Ka faɗa min abinda ke damunka mana”.

Sai asannan Moddibo ya buɗe Idanunsa cikin raunin murya tamkar mai shirin fashewa da kuka yace.

“I don't know J I really don't know what's wrong with me WLH BAN SANIBA, BANSAN MEKE DAMUNA BA
J”.

Da Mamaki M Jameel ya kallesa kana yace.

“How A.J kamar ya bakasan meke da munka ba”.

Langwaɓar da kai Moddibo yayi cikin yanayin damuwa da tashin hankali ya kalli M Jameel daya tsaresa
da ido ya sauƙe Idanunsa ƙasa kana yace.

“Bansani ba J bansan meke damuna ba Na dai san bana jina dai-dai ina cikin ɗimuwa”.

Ya ida maganar yana mai lumshe idanunsa sam ya rasa taya zai fara faɗawa M Jameel yanayin da yake ji
ajikinsa.

Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe kana yace.

“To ko dai zazzaɓi ne?”.

Girgiza kai Moddibo yayi still cikin raunin murya yace.


“A'a”.

Ahankali M Jameel ya sake cewa.

“Toh ko Kanka ke ciwo?”.

Still Kai Moddibo ya sake Girgiza masa alamar a'a.

Numfashi M Jameel ya fesar kana yace.

“Toh ko dai cikin kane?”.

Nan ma kai Moddibo ya Girgiza kamar zai fashe da kuka.

Tagumin M Jameel Yayi kana yace.

“Toh meke damunka?”.

Lumshe idanu Moddibo yayi cikin sanyin murya mai rauni ya buɗe idanunsa tare da kallon M Jameel
daya tsaresa da Ido kana yace.

“J bana jina dai-dai ina jin kamar akwai wani abu da nake buƙata amma bansan menene ba”.

Murmushi M Jameel yayi kana yace.

“Toh me kake buƙata?”.

Girgiza kai Moddibo yayi tare da buɗe hannunsa kana cikin sanyin murya yace.

“Idont know J nima ban sani ba bansan me nake so ba amma inaji kamar akwai wani abu da ɗan Adam
yake buƙata acikin rayuwarsa wanda nima nake buƙatarsa kusa sani, daga jiya zuwa yau amma bansan
menene bane”.

Kallonsa M Jameel Yayi tare da kallon yanda idanunsa suka sauya launi zuwa Ja tun safe da suka zo ya
lura da hakan tamkar mai mayen bacci kana ya lura da yanda lips ɗin sa ke rawa sannan ya lura da yanda
bini-bini yake matse ƙafafunsa.

M Jameel na cikin Kallonsa. Moddibo yayi miƙa tare da matse ƙafafunsa kana lips ɗin sa suka shiga rawa
sai kuma ya runtse Idanunsa.

Murmushi M Jameel yayi kana yace.

“J kodai kana jin kana ɓuƙatar mace akusa da kai ne?”.

Lokaci ɗaya Moddibo yaji zuciyarsa ya tsinke da masifar ƙarfi ajiyar zuciya ya saki tare da kallon M
Jameel ji yake tamkar ya fashe da kuka ko zaiji sauƙin abinda ke damunsa sunkuyar da kai ƙasa yayi cikin
wata raunan'niyar murya mai sanyi yace.
“Ban sani ba J”.

M Jameel yace.

“Toh mutafi gida mana tunda na gama abinda nake kai kuma naga kamar baka da komai”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana ya miƙe tare da yin miƙa da ayau ya zame masa jiki domin baya minti goma
mai kyau sai yayi miƙa.

Kallonsa M Jameel yayi dan yanda yaga Modibbonsa ya tashi ta saman rigar duk da kuwa boxes biyu ya
saka duk dan ya suturta jikinsa ɗagowa M Jameel yayi tare da kallon fuskarsa yayi Murmushi.

Fita Moddibo yayi M Jameel yabi bayansa dai-dai lokacin da aka kira sallar Azahar acikin masallacin dake
makarantar.

bayan sun Idar suka fito suka shiga mota M Jameel ke driving yayin da Moddibo ke gefen mai zaman
banza idanunsa alumshe duk abin duniya ya Ishesa.

Suna isa gida M Jameel yayi Parking ya fita kai tsaye sashen Innayi ya wuce ya karɓa musu abinci
Moddibo kuwa cikin mutuwar jiki ya wuce sashen sa ya kwanta.

Ba jimawa M Jameel ya dawo hannunsa riƙe da Warmers da kuma Plate kwance ya samu Moddibo akan
3sitter yayi rub da ciki idanunsa akan ƙofar falon.

Ƙarasa shiga falon M Jameel Yayi tare da zama aƙasa kana ya kalli Moddibo da faɗin.

“Saƙƙo muci abinci idan muka gama sai muje kaga Dr”.

Girgiza kai Moddibo yayi cikin sanyayyar Murya yace.

“Bana jin yunwa bana son cin komai”.

Buɗe Warmer M Jameel Yayi tare da cewa.

“Toh Meyesa haka J?”.

Cike da raunin murya tamkar wanda ke shirin fashewa da kuka yace.

“Ban saniba nima”.

Dariya mara sauti M Jameel Yayi kana yace.

“A.J Na fahimceka fa kamar *Mace* kake buƙata acikin rayuwarka!”.

Cikin sauri Moddibo ya lumshe idanunsa jin suna tsats-tsafo wa da hawaye, miƙewa yayi tare da wucewa
Bedroom ɗin sa yana shiga yasa key ya rufe.
M Jameel kuwa jingina bayansa da jikin kujera yayi tare da fashewa da dariya harda riƙe ciki.

Moddibo kuwa yana kulle ƙofar ya juya ya kwanta ruf da ciki tare da lumshe idanunsa yayin da
ƙwaƙwalwar sa ta shiga tariyo masa moment da suka kasance acikin mota lokaci ɗaya Muhalinsa ya
shiga harbawa da ƙarfi tamkar zai fisge ya fito, yayin da lips ɗin sa suka shiga rawa har haƙoransa na
haɗuwa kar-kar-kar.

Batare daya shirya ba yaji hawaye suna bin kuncinsa shi kansa baisan meyake so ba bai san meke faruwa
dashi ba yakasa sanin yana yin da yake ciki ji yayi kawai yana kuka hawaye na bin kuncinsa yana
sheshsheƙa.

Miƙewa yayi cikin rashin sanin madafa shin ya zaiyi da wannan jarabar tun jiya yake fama da zaran ya
rufe Idanunsa yanayin da suka kasance da yarinyar ne yake gani.

M Jameel kuwa dambun shin kafa dayaji vegetables da soyayyen naman kaza dake tashin ƙamahi ya
zuba a Plate ya fara ci yana cikin ci ne wayarsa dake gefensa ya hau ruri.

Ahankali ya sanya hannunsa ya ɗauka Turkey Kawai ya gani babu Number.

Picking yayi tare da kaiwa kunnensa yana dariya yace.

“Yaushe kaje Turkey?”.

Murmushi Jalaludeen yayi kana yace.

“Na kusa kwana biyar acan ai”.

Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.

“Lallai dai kam yayi kyau ya gida”.

Gyaran murya Jalaludeen yayi tare da cewa.

“Lafiya wai meyasamu Aliyu ne”.

M Jameel na ajiye cokalin hannunsa yace.

“Nima kaina ban sani ba”.

Dariya Jalaludeen yayi kana yace.

“Mace ta fara shiga rayuwarsa kenan.

Aure fa yake da buƙata yana da ƙaƙƙarfan sha'awar da tuntuni na kwantar masa da shi”.
Zare Ido M Jameel Yayi kana yace.

“Auuu Jalaludeen kenan kaine ka maida mu waliyan dole?”.

Cikin sauri Jalaludeen yace.

“A'a Ni ban mayar daku mata ba, amma dai kawai nasan Aliyu nada ƙarfin sha'awa na masifa idan har
aka bar shi da wannan sha'awar zai iya zame masa masifa kana zai iya jefashi acikin damuwa gashi naga
burinsa a lokacin yayi ilimi mai zurfi, kuma in ka tuna a lokacin yana yawan fama da ciwon ciki”.

Dafe kunci M Jameel Yayi yana saurarensa.

Murmushi Jalaludeen Yayi kana ya cigaba da cewa.

“Tun haɗuwar mu na farko kafin ku fahimci wanene ni kafin ku fahimci komai akaina, kana tun kafin
afahimci wanene ni asan komai akaina na bashi abinda yasha wanda ya karyar masa da ƙarfin sha'awarsa
har yake ji kamar baya buƙatar mace acikin rayuwarsa”.

M Jameel ya gyara zamansa tare da cewa.

“Ikon Allah”.

Jalaludeen kuwa cikin yanayin su na can yaci gaba da cewa.

“Toh ajiya akwai abinda yafaru ko dai mace tashiga rayuwarsa ko dai akwai macen data kama jikinsa
wannan dalili yasa gaba ɗaya takarya alƙadarin abinda ke jikinsa!”.

Ajiyar zuciya M Jameel ya saki kana yace.

“Toh fa”.

Murmushi Jalaludeen yayi tare da faɗin.

“Kai kuma kwaɗayin ka ne ya kaika dana bashi maganin yana cikin sha kawai ka amshi kofin kasha
shiyasa kuka kasance atare haka amman ai kai naka ba kamar nashi bane ”.

Murmushi M Jameel Yayi kana yace.

“Amma dai gaskiya Jalaludeen baka da mutunci”.

Dariya Jalaludeen yayi kana yace.

“Nifa bance komai ba gaba ɗaya abinku lafiya lau yake kawai dai sha'awar ce na kwantar”.

Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.


“Toh yanzu shi kuma wannan ya za'ayi dashi dan yanzu wallahi ya tashi ya tafi ɗaki kamar zaiyi kuka”.

Murmushi Jalaludeen yayi kana yace.

“Kukan ma yakeyi yanzu”.

Ware ido M Jameel Yayi kana yace.

“Lallai dai kam maza sun gamu da aiki kenan”.

Jinjina kai Jalaludeen yayi tare da cewa.

“Gaskiya yanayin daya ke ciki ne awahale yake haka ya wuni jiya still haka ya kwana gashi kuma yau ma
ya wuni haka”.

Cike da tausayawa M Jameel yace.

“Toh yanzu ya za'ayi ?”.

Girgiza kai Jalaludeen yayi tare da cewa.

“Gaskiya ban sani ba dan bani da yanda zan mishi kawai abune daya zo masa babu yanda za'ayi haka
zaita rayuwa mafita ɗaya ne kawai yayi ƙoƙari yayi aure”.

Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da cewa.

“Ok zamu yi ƙoƙari muga mai ya dace tunda gashi dama duk abinda ya dace mun gama”.

Jinjina kai Jalaludeen yayi kana yace.

“Masha Allah amma yanzu ka samu ruwan ɗumi kasa masa laimun tsami yaji kana ka sanya zuma yaji sai
ka bashi yasha zai ɗan ji sauƙi”.

Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.

“Toh shikenan ba matsala mun gode”.

Sallama sukayi tare da katse kira.

Miƙewa M Jameel Yayi yashiga cikin kichen dake falon ya buɗe Flaks dake ɗauke da ruwan tea ya zuba a
Cup lemun tsami ya duba yaga babu rufe Cup ɗin yayi ya nufi cikin gadin ɗin gidan ya tsunko guda biyar
sannan ya dawo ya wanke tare da matse su duka acikin shayin kana ya buɗe kofin roban zuma yasa.

Fita yayi a kichen ɗin ya nufi Bedroom din Moddibo yayi Knowking ƙofar.
Dai-dai lokacin da Moddibo ya cire kayan jikinsa ka ya zura Jallabiya kasancewar boxers ya takure masa
jiki har yana jin mallakinsa na yimasa ciwo saboda yanda ya takuresa ya hanasa miƙewa cikin gajiyawa ya
mike ya cire boxes ɗin tare da cewa.

“Bari naga iya inda zaka tsaya uban ƴan zalamammu”.

Yayi maganar yana kallon jikin nasa daya miƙe ya tsaya acikin Jallabiyar.

Muryar M Jameel yaji yana cewa.

“A.J ka buɗe min ƙofar mana in baka magani”.

Daga ciki Moddibo ya buɗe masa ƙofar.

Kallonsa M Jameel Yayi sai kuma ya kalli yanda ya ɗaga rigar kawar da kai gefe yayi yana jin dariya na
neman kufce masa.

Kofin dake riƙe ahannunsu ya miƙa masa.

Cikin Sanyayyar muryarsa yace.

“J Me wannan?”.

M Jameel ya Kalli kofin kana yace.

“Kasha mana zaka ji sauƙin abinda ke damunka na fahimci meke damunka A.J”.

Moddibo bai sake cewa komai ba ya amshi Cup ɗin ya koma bakin gado ya zauna tare da kafa kansa ya
shanye tass kana ya ajiye kofin, cikin ikon Allah lokaci ɗaya yaji zufa ya fara sauƙa masa Atake yafara jin
abinda ke damunsa na sauƙa kaɗan-kaɗan amma still jikinai ɗin na nan amiƙe ahankali yaji lips ɗin sa ya
daina rawan zamewa yayi ya kwanta akan gadon yana sakin ajiyar zuciya akai-akai.

Acan gidansu Khausar kuwa zaune suke afalon Mommy suna cikin hira ka jiyo sallama.

Cikin sauri Haiydar ya ɗago kansa tare da cewa.

“Laaaaah....!

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki yar uwa
1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP
09097853276, sai in saki a Group na ɗin da zanke posting. Ko kinga littafin SAKAYYAH a waje na satane*
*By*

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYA

19

Miƙewa Haiydar yayi kana ya nufi ƙofar falon fuskarsa ɗauke da murmushi yace.

“Oyoyo Uncle Naseer”.

Khausar dake zaune kan 1sitter sanye cikin riga da baƙin wando Pencil da riga pinch color mai gajeren
hannu gaban rigar an rubuta Never Give Up manyan boobs ɗin ta sun cika gaban rigar yayin da bajejjen
ƙugunta ya baje acikin wandon, kanta sanye da hular Net baƙi gashinta ya zubo ta gefen wuya, a hankali
ta juyo ta kallesa tare da faɗaɗa fara'ar dake saman fuskarta kana tace.

“Laaa Uncle Naseer”.

Shi kuwa Naseer ido ya zuba mata yana sakar mata da wani irin shu'umin murmushi yayin da yashiga bin
ilahirin jikinta da kallo wani irin kallon Up and Down yake mata yana jin komai nata na kars burgesa
soyayyar ta na kuma ninkuwa a ransa.

Cikin wani irin salo kana still Idanunsa na kanta ya wani lumshe ido afili ya furta.

“Masha Allah Matata ta girma”.

Mommy dake zaune kan 3sitter tayi murmushi tare da cewa.

“Masha Allah Naseer mutanen India kwanan nan mukayi magana da Aunty Jameela kece min ka kusa
dawowa Ashe-ashe dawowa yazo ma”.

Murmushi yayi kana cikin yanayin zumuɗinsa yace.

“Aidai kam suma Surprised ɗin su nayi babu wanda yasan dawowana akwanan nan kawai sai ganina
sukayi”.

Cike da kulawa Mommy tace.


“Masha Allah sannu da zuwa ka iso”.

Raudat da Ramadan dake zaune suka mike tare da zuwa suka riƙe hannunsa,hannun Raudat ya riƙe tare
da ɗagata sama kana yace.

“Iyeee Baby Raudat Masha Allah an girma anyi kyau. Amma dai duk da haka Matas tayi miki wayau ta fiki
kyau”.

Murmushi Mommy dake zaune tayi kana tace.

“Haka dai kace”.

Ware ido yayi kana idanunsa akan Khausar yace.

“Allah kuwa Mommy dubi fa Khausi na tafita kyau”.

Khausar kuwa lallausan tafin hannunta tasa ta rufe fuskarta.

Sai kuma ta miƙe ta nufi kichen ta ɗauko drinks da Snacks sai kayan Friut tafi to masa dashi.

Har zuwa lokacin batayi magana ba sai dai da zaran sun haɗa ido zata sakar masa da ɗan guntun
murmushi kamar yanda shima yake sakar mata.

Haiydar kuwa da sauri ya saki hannun Naseer kana ya nufi sashen Hajiya Bunayya yana faɗin.

“Ummah,Ummah ga Uncle Naseer kizo ku gaisa".

Miƙewa Ummah tayi fuskarta ɗauke da murmushi Amina ma miƙewa tayi tana murmushi tabiyo
bayansu.

Cike da farin ciki Amina tace.

“Uncle Naseer mutanen India”.

Washe baki Naseer yayi domin shi mutum ne mai fara'a da son nuna shi wani ne, kana ga fafa da iyayi
baya ga haka yana da budeɗɗen ido da son holewa.

Ita kuwa Hajiya Bunayya kallonsa takeyi da murmushi afuskarta tace.

“Naseer sai ganinka mukayi babu sanarwar anyi karatu angama ka dawo Nigeria kenan?”.

Sha fa sumar kansa yayi yana shan Fruit da Khausar ta kawo masa yace.

“Wallahi kuwa Ummah nazo ganin Matata ce muyi aure in ɗauke ta mutafi.
Amma Ziyara nazo yi muku zan koma da matata, dan bazan iya zaman Nigeria ba”.

Murmushi Mommy tayi kana tace.

“Ayyah Naseer ai nan ma muna da waja-je masu kyau kodai India sunfi mu Weather mai kyau ne?”.

Girgiza Kai yayi tare da cewa.

“No Mommy bawai Weather mai daɗi ba kawai dai can ɗin zan samu aiki ne sannan gaskiya ni yanzu
bazan iya rayuwar Nigeria ba”.

Ya ida maganar yana ya mutse fuska cike da Iyayi.

Murmushin da bai wuce saman laɓɓaba Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Aikam dai kam yayi kyau Allah ya taimaka bari na koma ina aiki”.

Ta ida maganar tare da miƙewa dan Allah ya sani ya ƙona mata rai da batun ya aure Khausar su koma
India.

Amina kuwa siririn tsaki taja cike da jin haushin yanda Naseer ke Shish-shigewa Khausar ta miƙe tabi
bayan Hajiya Bunayya suka fice.

Bayan fitarsu Mommy ta miƙe tashiga Kichen Haiydar ma miƙewa yayi tare da ɗaukar Ramadan da
Raudat suka fita danmai yi musu lesson yazo.

Falon ya rage daga Khausar sai Naseer, Ahankali Khausar ta miƙe da niyyan barin falon cikin sauri Naseer
yace.

“Ohh My dear Wife Why are you going?”.

Murmushi Khausar tayi aranta tace Ohh Uncle Naseer sam bazai canza ba, wannan kalma ya riƙe ta tun
yarinta alokacin batasan ma'anarsa ba amma yanzu da zaran ya faɗa kunya take ji wai matarsa ko kunya
faɗa agaban su Mommy baya ji.

Anutse ta dawo ta zauna a inda ta tashi, cikin tsareta da Ido yace.

“Tunda baki gaisheni ba bari in gaishe ki”.

Cikin sauri tayi ƙasa da kanta kana tace.

“A'a Uncle Naseer ina yini ya karatu fatan ka dawo Lafiya?”.

Sumar kansa ya shafa kana yace.

“Karatu Alhamdulillah ya naki karatun??”.


Murmushi Khausar tayi kana tace.

“Alhamdulillah Uncle Naseer nan da kwana goma zamu gama Secondary school Insha Allah”.

Washe baki yayi yana binta da wani irin kallon yace.

“A'a Masha Allah Abu yayi kyau kenan abu zai tafi dai-dai yanda aka tsara”.

Murmushi tayi tare da sunkuyar da kanta ƙasa tana wasa da yatsun hannunta.

Ɗago kansa yayi tare da miƙewa ya koma kusa da ita.

Cikin wata narkakkiyar murya ya kalleta tare da cewa.

“Khausar ina fatan baki manta da maganar mu bako?”.

Murmushi tayi still ba tace komai ba sai ƙasa da tayi da kanta tana cigaba da wasa da yatsun hannunta”.

Shi kuwa Naseer sake narkar da muryarsa yayi tare da faɗin.

“My Khausi kinsan dai ina sonki, ke tawa ce inaji Ajikina Ubangiji ya halicce ki ne domin ni kaɗai kinsan
ina matuƙar ƙaunarki ina burin ki kasance matata ke ta dabance ina miki sahihiyar ƙauna bani da burin
daya wuce mu zamto ma'aurata in mori ni'imar da Allah ya halitta miki”.

Batare data ɗago kanta ba tace.

“Uhm”.

Shi kuwa wani narkar da fuska yayi tare da lanƙwasar da harshe kana yace.

“Meyesa ne komai nace sai kice Uhm?. Yanzu ke kanki bakya jin kina so kiyi Aure ne? aike kanki kin
girma kin kai matakin da akan kanki zaki buƙaci na miji atare dake musamman ma na miji irina wanda zai
iya gamsar dake tare da biya Miki duk kan buƙatunki ko ba haka bane?”.

Lokaci ɗaya Khausar ta kwaɓe fuska cikin yanayin rashin jin daɗi da kuma rashin tsammanin abinda ya
faɗa ta ɗago kanta tare da Kallonsa sai kuma ta kawar da kanta gefe fuska a tsuke.

Shiko sake narkar da murya yayi tare da tsira mata Idanu kana yace.

“Shifa rayuwar nan baya tafiya dai-dai dole sai ansamu dai-dai-to atsakanin halittar Namiji da mace,
rayuwar nan bata da wani daɗi idan har babu mace akusa da namiji, haka itama mace rayuwar bata
mata daɗi idan har babu Namiji akusa da ita, musamman idan anfara tafiya irin matakin shekarun kin
nan daga Sha tara, Ashirin, Ashirin da ɗaya,Asirin da biyar, Talatin,har zuwa talatin da biyar dole tana
buƙatar Namiji”.
Ya sake narkar da murya yana binta da wani shu'umin kallo yace.

“Muyi Aurenmu Khausar zaki ci gaba da karatunki a India sai kije kiyi karatunki acan”.

Ƙasa ta sake yi da kanta kana cikin yanayin ɓacin rai ta ɗago batare data yarda sun haɗa ido ba tace.

“Ni bana sha'awar zuwa India nafiso in zauna an ƙasata kusa da Mommy na bana buƙatar duk wani abu
da zai nesanta ni da ita da kuma ƙasata domin duk abinda India take dashi ai muma muna da shi harma
fiye da nasun”.

Cikin sauri ya sake Matsawa kusa da ita tare da sanya hannunsa zai kamata.

Da mugun sauri ta kauce ranta babu daɗi ta kallesa kana tace.

“Ya haka Uncle Naseer mai yasa zaka kama min hannu?”.

Ido ya lumshe yana jin sautin muryarta na ratsa shi sai kuma ya buɗesu akanta tare da cewa.

“Ohh My God wai Khausar har yanzu baki waye bane? me haka kamar ba ƴar zamani ba!? Dan na taɓa
ki ai bawani abu bane kada ki manta tun kina ƙarama ko su Abba sun sani ke mallaki nace idan Ubangiji
ya nufa”.

Fuska ta sake ɗaurewa kana cikin sauri tace.

“Toh kabari sai Ubangijin ya nufa kasamu. Shaidu sai inzama mallakin naka”.

Ta ida magarta tare da miƙewa tabar wajen.

Binta yayi da kallo bajejjen ƙugunta wanda duk takun da tayi sai sun motsa tamkar da gangan take
juyasu.

Dai-dai lokacin kuma Mommy ta fito daga kichen yana ganin ta ya miƙe tare da cewa.

“Mommy bari in isa wajen Yafendo Dadu”.

Shi ɗin ɗan ƙanwar Gimbiya Dadu ce,

Ya ida maganar tare da ficewa kai tsaye sashen Gimbiya Dadu ya nufa bakinsa ɗauke da Sallama ya shiga
falon.

Gimbiya Dadu dake zaune tana shan Fruit ta Washe baki kana tace.

“Nasiru lallai mutanen India masha Allah sannu da zuwa”.


Zama yayi daga gefenta yana murmushi kana yace.

“Yafendo fatan mun sameku lafiya?”.

Cike da farin ciki tace.

“Lafiya lau Nasiru ina ƴar Uwata ƴar Autanmu”.

Zamansa ya gyara tare da cewa.

“Tana lafiya tace in gaisheki”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Ayyah Ina Amsawa”.

Gyaran murya yayi tare da fuskantar Gimbiya Dadu kana yace.

“Yafendo na gama karatuna yanzu na dawo sannan na dawo da burin yin Aure. Ya maganar mu da
khausar tana nan dai ko?”.

Ajiyar zuciya mai nauyi Gimbiya Dadu ta sauke tare da lumshe Idanunta kana ta saki wani shu'umin
murmushi tare da kallonsa kana tace.

“Sosai ma kuwa maganar ku tana nan mai zai hanata da izinin Ubangiji maganar ku tana nan baka da
matar data wuce Khausar yau ɗin nan zan yiwa Abbansu maganar”.

Cike da farin ciki ya saki sanyayyar ajiyar zuciya kana yace.

“Kai Alhamdulillah Yafendo na naji daɗi”.

Murmushi kawai tayi shi kuwa miƙewa yayi bayan sun sake taɓa hira ya tafi.

Bayan kwana uku.

Ahankali Khausar ta sauƙa daga motar dake kaisu makaranta hannun riƙe da Raudat ta nufi ajinsu ta
kaita kana ta dawo tashiga ajinsu Lokacin har an fara raba booklet kallonta Malam Isma'il dake raba
Booklet ɗin yayi kana yace.

“Lelewal mai yasa kike son zuwa letti ne Exam ɗin ma baza ki fito da wuri ba?”.

Langwaɓar da kai Khausar tayi tare da cewa.

“Ayyah Malam ayimin afuwa”.


Harara Samira Sani dake bayan ta ta watsa mata cike da tsanar ta Asma'u dake gefen ta ta girgiza kai
domin ita dai ta rasa me. Khausar ta tsare musu suka tsaneta.

Khausar kuwa zama tayi Malam Isma'il ya bata Booklet da kuma Quatons peper Na Arabic da zasuyi yau
ma kamar kullum tun kafin a gama rabawa Khausar tashiga answering Questions ɗin cikin mintunan da
baza su gaza ashirin ba ta kammala.

Acan office ɗin Moddibo kuwa zaune yake ya jingina bayansa da jikin kujera yayin da ya ɗaura ƙafarsa
ɗaya kan ɗaya akan deks ɗin Idanunsa na lumshe.

Cikin sauri ya buɗe Idanunsa tare da jan dogon tsaki.

Domin da zaran ya rufe idanunsa babu abinda yake gani sai moment da suka kasance da yarinyar cike da
damuwa ya sauƙe numfashi kana aƙasan ransa yace.

“Na godewa Allah da yasa karatun yaran nan yazo ƙarshe kana naji daɗi da cewa sun gama Exam ɗina,
bazan sake shiga ajinsu ba”.

Da sauri ya runtse Idanunsa haka nan yake jin kunyar kansa da kansa ya rasa ta yanda zai fassara
al'amarin yasan tun farko yarinyar bata da kunya bare kuma wannan abu ya faru shin taya zai iya haɗa
ido da ita?.

Anan sashin su kuwa.

Atare Khausar da Asma'u suka fito daga Area class ɗinsu har zasu wuce suka hango M Jameel tsaye.

Abakin Office ɗin su Moddibo.

M Jameel ne tsaye ya jingina bayansa da jikin ƙofar yayin da Amina ke tsaye gefensa cikin iyayi da yauƙi
ta kashe murya tare da cewa.

“Malam sai gobe idan Allah ya kaimu zan dawo ko Principal ya dawo na amshi result ɗina”.

Anutse M Jameel ya juya ya kalleta tare da cewa.

“Ok Allah ya kaimu ki gaida gida”.

Sake karya murya tayi cikin tsaresa da ido tace.

“Toh gida zaiji Malam kaima ka gaida gida”.

Jinjina kai yayi batare daya sake kallonta ba yace.

“Gida zaiji”,Juyawa tayi tabar wajen.


Dai-dai lokacin da Asma'u da Khausar suka iso a tare Kallonsa Khausar tayi tare da cewa.

“Barka da rana Yah Jameel”.

Murmushi ya sakar mata kana yace.

“Yawwa Khausi bar ka dai yanzu kam an zama manyan ƴan mata ankusa agama Secondary school a huta
a shiga babin girma ko?”.

Jinjina kai tayi cikin jin daɗi ta kalli Asma'u kana tace

“Ai lallai dai kam bari kawai Yah Jameel jinmu nake tamkar ansaki tsuntsuwa daga sheƙarta.

Wani irin daɗi mukeji mun kusa mu rabu da rayuwar bauta rayuwar duka cin zali, kaɗe ɗan kwali, harara,
tsawa, hantara,”.

Kallon ta M Jameel Yayi tare da juya idanunsa zuwa office ɗin ya mata alamar Moddibo na ciki.

Cikin sauri ta sanya hannunta ta rufe bakinta tare da barin wajen bayanta Asma'u tabi tana ƙyalƙyala
dariya tare da cewa.

“Khausar ga Moddibo na miki magana wai kije”.

Dariya M Jameel yayi ganin

Cikin sassarfa Khausar ta fice daga wajen batare data yadda ta juya ba.

Moddibo kuwa na zaune a office duk Maganar da sukayi akunnensa da zaran sautin muryanta ya ratsa
kunnensa zaiji tsikar jikinsa ya tashi tamkar ana stikaresa da allura hakan yasa ya runtse Idanunsa da
ƙarfi kana yayi shiru.

Allah ne kaɗai yasan yana yin da yake ciki.

Khausar kuwa na fita wajen motarsu ta nufa ta samu duk su Amina su shiga ita kadai ake jira tana zama
Driver yaja suka tafi.

Asma'u kuwa na fita ita da Bashir mai Napep ɗin su ya iso ya ɗauke su suka tafi.

Washe gari da yamma bayan Khausar sun dawo makaranta misalin ƙarfe Uku ta fito cikin wata
Bugaggiyar shadda milk color anyi masa ɗinkin dogon riga da kuma zubi da akayi sa da Coffee zare
fuskarta ɗauke da light Make-up yayin da tayi ɗaurin Aysha Buhari ta zuba jelar gashinta ta gefen dama
dake fitar da sanyayyan ƙamshi kana ta yafa milk colour gyale akafaɗarta Hannunta riƙe da jaka Coffee
haka ma takalmin Half cover coffee color jikinta na fitar da sanyayyan ƙamshin tularen Balila da kuma
Sedection.

Kai tsaye Bedroom din Mommy ta nufa bakinta ɗauke da sallama tashiga ganin Mommy Bata ciki yasa ta
fito tare da nufar kichen.

Tsaye ta samu Mommy tana yanka albasa.

Mommy na ganinta tace.

“Har kin gama shiryawa?”

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Eh Mommy na gama shiryawa”.

Jinjina kai Mommy tayi tana cigaba da yanka albarsar tace.

“Idan kinje ki Gaishe da Ummin Asma'u”.

Kai ta gyaɗa tare da gyara rikon Handbag din ta kana tace.

“Insha Allah zata ji Mommy”.

Dai-dai nan suka jiyo Sallamar Naseer afalo, cikin sauri ta kalli Mommy sai kuma ta ɓata fuska lokaci ɗaya
ta nemi fara'ar dake fuskanta ta rasa.

Kallon mamaki Mommy tayi mata kana tace.

“Ya dai haka daga jin muryan sa kin wani tsuke fuska sai kace wanda yazo miki da wani mugun abu”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“Babu komai Mommy”.

Girgiza kai Mommy tayi tare da fita tana cewa.

“A'a wa nakeji kamar Naseer mutan India”.

Yana zaune kan kujera ya gyaɗa kai tare da cewa.

“Eh Mommy nine”.

Dai-dai lokacin da Khausar ta fito miƙewa yayi idanunsa akanta yace.

“Wooow Masha Allah”.

Sam ya mance da Mommy dake tsaye a wurin.


Gaba ɗaya imaninsa ya tafi gareta cike da zalama ya nufi Khausar tamkar zai rungumeta yana faɗin.

“Wowww my dear Wife you look so georoures, Fantastic, beautiful you look so Pretty”.

Khausar kuwa ganin yanda yake matsota zai Rungumeta yasa taja baya da sauri tare da cewa.

“Nagode.

Mommy kuwa kallon ikon Allah take ganin yanda baki ɗaya hankalinsa ya tafi kan Khausar da alama ya
mance da tana wajen.

Gyaran murya tayi tare da cewa.

“A'a Naseer ka zauna mana akawo maka abin taɓawa mana”.

Girgiza kai yayi da faɗin.

“A'a Mommy Nagode”.

Itako Khausar ɓata fuska tayi babu walwala atare da ita tace.

“Mommy na tafi".

Cikin sauri ya mike tare da bin bayanta kana yace.

“My dear Wife Ina Zakije?”.

Ataƙaice tace.

“Unguwa”,

Cikin yanayin zumuɗinsa yace.

“Bari in sauƙe ki”.

Mommy kuwa ita kanta rawan kansa ya bata tsoro ganin yanda yake nuna zalamarsa afili kamar kura
yaga ɗanyen Nama!”.

Da sauri Mommy ta kallesa tare da cewa.

“A'a Naseer ka bari basai ka kaita ba ai zata shiga Napep”.

Zare ido yayi tare da cewa.

“A'a Mommy na isa kamar ni ace Matata tashiga Napep no, impossible kamar Matar Naseer Ibrahim
ɗancanji amma ace Matata na hawa Napep Ina bai yiba bai yiba”.
Ita kuwa Mommy aranta tace Ohhh wannan yaro dai Allah yamasa kurari bawai basu da arziƙinba
mahaifinsa nadashi amman kurarinsa yafi kuɗin nasu yawa bashi da aiki sai cika baki.

Khausar kuwa tuni ta fice cike da takaicin zumuɗinsa.

Da sauri yabi bayanta yana cewa.

“My dear Wife ki tsaya mana let me drop you”.

Banza Khausar tayi masa tayi ficewar ta.

Kashe murya yayi tare da cewa.

“Dan Allah ki tsaya mai yasa kike yin haka?”.

Ba tare data juya ba kana cikin ɗaure fuska tace.

“A'a Uncle Naseer ka bari kawai zanje da kaina gidansu Asma'u nefa Napep ma zan shiga”.

Murmushi yayi kana yace.

“Yawwa muje kinga nima sai ingaishe da Umminta kinga dama na daɗe banga Asma'u ba yau ya kamata
mu gaisa”.

Khausar kam sake ɗaure fuska tayi tare da cewa.

“Yaya Naseer Allah da kabari kada in saka wahala nasan baza ka rasa abinyi ba”.

Langwaɓar da kai yayi tare da marairaice fuska kana ya karyar da murya tare da cewa.

“Please My dear Wife allow me to escort you kinsan dai Ina ƙaunarki sannan ina son kasancewa da ke
banaso kidinga nesanta kanki daga gareni”.

Siririn tsaki taja aranta kana tayi gaba abinta domin har ga Allah zalamarsa na bata tsoro.

Shi kuwa da sauri ya nufi Parking space tare da ɗaukar motarsa yazo ta gefenta tare da buɗe mata kana
ya karyar da murya tare da cewa.

“Please Wife to be kishigo mana”.

Dai dai lokacin da gate man ya buɗewa Lamiɗo da Gimbiya Dadu suka shigo bisa duk kan alamu daga
asibiti suke anje duba lafiyar Idonta dan bayan ta fito hannunta na riƙe da ledan magunguna da kuma
tambarin asibiti.

Gimbiya Dadu kuwa tun da ta sauƙa daga mota Idanunta nakan Khausar ta wani kafeta da Ido tare da
sake laɓenta na ƙasa.
Khausar kuwa cikin rawan jiki da tsinkewar zuciya tayi saurin koma wa bayan Naseer zuciyarta na
bugawa da mugun ƙarfi cike da tsoro take karanta duk wata addu'a da tazo bakinta.

Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa.

“A'a Nasiru ya dai ina zakuje kaida Mutuniyar taka?”.

Cikin yanayin zumuɗinsa da rawan kai ya shafa ƙeyarsa tare da cewa.

“Abbah zan kaita gidansu Asma'u ne dan banaso ta hau Napep”.

Jinjina kai Abba yayi kana yace.

“Yayi kyau Allah ya kiyaye hanya, Khausar sai kun dawo”.

Kasa cewa komai Khausar tayi still tana tsaye bayan Naseer zuciyarta na cigaba da tsinkewa ganin har
zuwa lokacin Gimbiya Dadu na Binta da ido burinta su haɗa Ido.

Gyaran Murya Lamiɗo yayi kana yace.

“Khausar shiga mota ku tafi”.

Cikin sauri tace.

“Toh Abba”.

Kana ta fito daga bayan Naseer tashiga gaban motar.

Kallon Gimbiya Dadu Naseer yayi kana yace.

“Yafendo sai mun dawo”.

Ya ida maganar tare da buɗe mazaunin Driver ya shiga kana yaja motar suka fice ahankali ya dai-dai ta
hancin motarsa suka hau kwalta.

Sai asannan ya juya ya kalli Khausar da fuskarta babu annuri kona misƙala zarratin zaman blutooth dake
kunnensa ya gyara ajiyar zuciya ya saki yana bin ilahirin jikinta da kallo hannunsa ya kai tare da
ranƙwafawa kanta zai riƙe yalwataccen sumar dake gefen wuyanta zai shinshina.

Cikin sauri Khausar ta kauce tare da watsa masa wani kallo.

Tsuke fuska yayi tare da marairaice murya kana yace.

“Haba My Wife mai yasa zaki min haka kibari mana in sinsina gashinki naji wannan Sanyayyar ƙamshin
da yake fita”.

Sake tsuke fuska Khausar tayi tare da tura ƙaramin bakinta kana tace.
“A'a nidai Yaya Naseer ka bari bana so”.

Langwaɓar da kai yayi kana cikin wata murya mai ɗauke da zallan shauƙi da sha'awa yace.

“Toh na bari ai yanda kike so haka za ayi hope dai kina sona?”.

Ƙasa tayi da kanta tana wasa da zara-zaran yatsun hannunta amma ba tace komai”.

Sake narkar da muryarsa mai ɗauke da zallan sha'awa kana yace.

“Dan Allah kice kina ƙaunata ko zanji daɗi kinsan na daɗe ina dakon soyayyarki azuciyata, Khausar kece
rayuwata bazan iya rayuwa idan babu keba kece muradin raina, kece fitilar dake haskaka rayuwata ina
miki sahihiyar ƙauna wanda bana yiwa kaina”.

Lumshe idanunsa yayi tare da kallon fuskarta zuwa ƙirjinta kana yace.

“Kece wacce zuciyata keda burin kasancewa da ita, kece farin cikina muddin ban mallakeki amatsayin
matata ba bazan taɓa samun nutsuwa ba, My Khausi saboda ke nadawo Nigeria ba dan keba wlh bazan
dawo ba.

Duk yawan kyakkyawawan matan dake India babu wacce ta burgeni ta kuma kwanta min arai sai ke duk
kyawunsu kallon maza nake musu!”.

Ita dai Khausar batace komai ba sai wasa da take da yatsun hannunta.

Naseer kuwa karyar da murya yayi tare da lashe lips ɗin sa kana yana binta da wani shu'umin kallo ya
lumshe Idanunsa tare da cewa.

“Khausar inada burin mallakar ki ke kaɗai ce zaki iya sarrafani, akan shimfiɗata sannan ke kaɗai ce zaki
iya bani farin ciki akan shimfiɗa ta”.

Lokaci ɗaya Khausar ta sake haɗe fuska cike da takaici tarasa Meyesa Naseer yake mata wasu irin
maganganu marasa kan gado.

Al'amarin Naseer yafi kama da irin mayaudaran mazan nan na zamani.

Shirune ya ratsa motar har suka isa ƙofar gidansu Ummi yayi Parking daga waje, Ahankali Khausar ta ziro
ƙafanta da suka sha jan lalle.

Dai-dai lokacin Asma'u ta iso.

Ganin Khausar yasa ta faɗaɗa fara'ar fuskarta kana tace.

“A'a Khausisi, Lelewal tawa”.

Murmushi Khausar ta sakar mata tare da gyara zaman gyalenta kana tace.
“A'a ina kika je?”.

Asma'u na gyara wuyan hijabinta ta kalli Khausar tare da cewa.

“Wallahi kitso naje”.

Jinjina kai Khausar tayi kana tace.

“A lallai dai kam”.

Juyawa tayi ɓangaren da Naseer ke tsaye ya zuba mata ido ɗauke kanta daga garesa tayi kana ta mayar
da kanta kan Asma'u tare da cewa.

“Asmeey ga Uncle Naseer”.

Sai alokacin Asma'u ta ganesa da murmushi afuskarta tace.

“Laa Uncle Naseer Mutanen India fatan kazo lafiya. Khausar tace min kadawo toh Allah yatemaka”.

Kai ya jinjina cike da Iyayi kana yace.

“Wallahi na dawo amma fa saboda My Khausi nazo, ana ɗaura mana aure kuma zan ɗauki abata
mukoma can”.

Murmushi Asma'u tayi tare da kallon Khausar da ta tsuke fuska kana tace.

“Toh Allah ya tabbatar mana da alkhairi”.

Da sauri ya amsa da.

“Ameen”.

Khausar kuwa hannun Asma'u ta riƙe zasu shiga gida.

Da sauri yace.

“Ya dai haka My Khausar ba zaki tsaya mu ɗanyi hira ba?”.

Ataƙaice ta girgiza masa kai tare da cewa.

“A'a”.

Shafa kansa yayi tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Toh ƙarfe nawa zaki koma gida sai inzo in ɗauke ki”.
Babu walwala atare da ita tace.

“A'a ba sai kazo ba Uncle Naseer zan koma”.

Wani irin zare ido yayi tare da girgiza kai kana yace.

“A'a My Khausi kar ki min haka.

Ni dai ki faɗa min ƙarfe nawa zanzo ɗaukarki”.

Ƙaramin tsaki taja aranta tare da cewa wannan mutumin ya fiye naci afili kuma juyawa tayi ta kallesa
tare da cewa.

“Toh ka dawo ƙarfe shida na Yamma”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan My Wife sai nazo”.

Ya ida maganar tare da shigewa motarsa yaja.

Bayan sun shiga cikin gida Khausar ta juya tare da kallon Asma'u kana tace.

“Ya dai naga kamar Ummi bata nan?”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh Ummi ta tafi gidan Innayi. Ni kaɗai ce sai Bashir dana bari yana mana gadin gidan shiyasa ma ana
gama min kitson na dawo.

Jinjina kai Khausar tayi kana tace.

“Ayyah yayi kyau”.

Kai tsaye Bedroom din Asmau suka shiga fridge Asma'u ta buɗe ta kawo mata drinks da Fruit.

Kallon Friut ɗin Khausar tayi tare da zabga ta gumi.

Zama Asma'u tayi daga gefenta cike da kulawa tace.

“Ya dai Khausar tunanin me kike?”.

Ajiyar zuciya Khausar ta saki tare cire gyalenta ta ajiye kana ta kalli Asma'u tare da cewa.

“Ni wallahi lamarin Uncle Naseer ya fara damuna”.

Asma'u na ninke hijabin data cire ta kalli Khausar tare da faɗin.


“Mai yafaru?”.

Ajiyar zuciya Khausar ta saki tare da lumshe Idanunta kana tashiga zayyanewa Asma'u abubuwan daya
yima tun daga zuwansa har yanzu daya kawota kana ta ɗaura da cewa.

“Asma'u Uncle Naseer yana bani tsoro abubuwan da yake gwada min sun fi kama dana mayaudara idan
yana wani abun tamkar yana da wani nufi akaina, sannan yana yawan nuna zalamarsa akaina, ya rinƙa
wani abu kamar maye!”.

Dariya Asma'u tayi tare da cewa.

“Wataƙil tsanananin son da yake miki ne kike ganin kamar haka, kinga tun kina ƙarama kamar da wasa
ya fara ce Miki matarsa har gashi girma yazo wataƙil tsananin soyayya ne sannan kinga ya zauna a ƙasar
da al'adun mu ba ɗaya dana suba kinga ƙasashen India wannan sai ahankali runguma da sumbata basu
ɗauke shi abakin komai ba may be shiyasa kike ganin yake miki haka kuma kinga ai ya riƙa dole zaiso
mace”.

Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da furzar da iska mai zafi kana tace.

“Anya kuwa Asma'u abin nasa is too hight ɗazun fa agaban Mommy saura kaɗan ya rungumeni saida na
kauce”.

Dafe kunci Asma'u tayi tare da kallon Khausar da fuskarta ke ɗauke da alamun damuwa kana tace.

“Toh tunda har haka ne ki kiyaye al'amarin sa”.

Ajiyar zuciya Khausar ta saki tare da lumshe Idanunta kana tace.

“Zan kiyaye insha Allah amma gaskiya ya fara bani tsoro baki ɗaya al'amarin sa azalamance yake”.

Jinjina kai Asma'u tayi tare da cewa.

“Amma duk da haka yana sonki”.

Kai Khausar ta gyaɗa kana ta buɗe Idanunta dake lumshe tace.

“Na sani Uncle Naseer na ƙaunata, amma kuma wani lokaci soyayyar tafi kama da Sha'awa”.

Girgiza kai Asma'u tayi tare da cewa.

“No Khausar kada ki fassara shi da haka, sannan kinga yanzu lokaci yayi da zaki bawa Uncle Naseer dama
kinga dama ga Maganar da Hajja Nana tazo da ita cewa kina gama Secondary school za ayi batun Aurenki
kinga yanzu munzo gangara koma ince mungama kawai”.

Shiru Khausar tayi tare da lumshe Idanunta tana jin wani iri azuciyar ta.
Asma'u ta cigaba da cewa.

“Sannan kin gani tayi miki maganar Yayanki Aliyu idan har baki amince da Naseer ba kika fitar dashi
amatsayin wanda kike soba dole Yaya Aliyu za'a liƙa miki, kuma kinga Yaya Naseer tunda ansan Asalin sa
sannan ansan komai nasa, kuma ke kanki kinsan yana masifar sonki”.

Ƙaramin tsaki Khausar taja tare da kallon Asma'u kana tace.

“Kayya Asma'u Asalin nasa har wani kyau gareshi!?

Mahaifiyarsa fa ƙanwar Gimbiya Dadu ce Uwar su ɗaya ubansa ɗaya, kuma duk ɗabi'u da hallayar
Gimbiya Dadu babu wanda mahaifiyarsa ta bari, sannan kuma shine ɗan Auta wajenta Ni Wallahi tsoron
su na nake ji wallahi nama fi tsoron mahaifiyarsan”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta cigaba da cewa.

“Amma shi Uncle Naseer bashi da matsala Saboda zuciya nason mai kyautata mata, shi kuma tun ina
ƙara ma yake nunawa kowa cewa. Ni ta da bance ni ta musamman ce awajensa, na ɗaukesa ne tamkar
wani sashina amma banjin Uncle Naseer awani mataki na daban sannan batun Yaya Aliyu kuwa gaskiya
saidai Hajja Nana tayi duk abinda zatayi, amma ni bazan Aure shiba babu ta yanda zanyi na aureshi”.

A hankali ta furzar da iska mai zafi daga bakinta kana ta kalli Asma'u da itama ita take kallo.

Idanunta ta lumshe cikin sanyi murya tace.

“Ni inaji azuciya ta ina da muradin da nake da ita na, musamman da nake buƙata inada muradin da nake
so Asma'u ina da wani abun da nake so, wanda ni kaina bansan menene ba.

Amma Uncle Naseer ba irin Nature da nakeso ajikin namiji yake dashi ba dama yanada ilimi Addini kamar
Yah Jameel ne to da ya tsarkaka, dama ace ɗabu'unsa irin na Yah Jameel ne da ya cikemib ko wanne
gurbi”.

Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe kana tace.

“Allah ko?”.

Tayi mgnar a fili yayinda zuciyarta ke saƙa wasu zantukan, ita kuwa Khausar kai kawai ta gyaɗa mata.

Cikin sauƙe numfashin Asma'u tace.

“Allah ya mana zaɓi mafi alkhairi dai”.

Cikin lumshe ida Khausar tace.

“Amin”.
Hira suka cigaba dayi, ƙarfe biyar dai-dai Khausar ta miƙe tare da ɗaukan gyalenta ta yafa kana ta kalli
Asma'u tare da cewa.

“Asma'u Ni zan tafi”.

Saurin Kallonta Asma'u tayi tare da cewa.

“Toh ba kince sai ƙarfe shida zaki tafi ba?,Kuma ina Uncle Naseer zai zo ya ɗauke ki!?”.

Baki Khausar ta taɓe kana tace.

“Guduwa zanyi kafin yazo ɗin dai, ai shiyasa nace masa shida kinga yanzu biyar zan tafi”.

Murmushi Asma'u tayi tare da cewa.

“Toh idan yazo fa?”.

Ka faɗa Khausar ta ɗage tare da taɓe baki kana tace.

“Sai kice masa na tafi”.

Ta ida maganar tana ficewa da sauri.

Asma'u tabi bayanta dan yi mata rakiya.

Misalin ƙarfe shida saura kwata Naseer yayi Parking aƙofar gidansu Asma'u tare da danna Hong.

Asma'u dake sauraran zuwansa ta sanya hijabi ta fita zaune ta samesa acikin mota kana tace.

“Bata daɗe da tafiya da taga iska ya taso”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Nagode”.

Kana ya figi motarsa yabar layin kai tsaye gidansu Khausar ya nufa lokacin daya isa ankira maghariba
direct masallaci ya wuce ya gabatar da sallah kana ya wuce gidan kai tsaye sashen Gimbiya Dadu ya
shiga.

Shigarsa ba daɗewa Haiydar ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama kana ya gaishesu tare da ajiye kulan
abincin Gimbiya Dadu.

Har ya juya zai fita.

Naseer ya kallesa tare da cewa.


“Please Haiydar kace da Khausi tazo zamuyi hira”.

Kai Haiydar ya gyaɗa kana yace.

“Toh Uncle Naseer sannan ya fita”.

Kai tsaye masallaci ya wuce sai Misalin takwas saura kwata ya koma sashen su bakinsa ɗauke da Sallama.

Khausar dake zaune kan 1sitter sanye cikin Neavy blue riga da wando na bacci mai santsi wanda ya sauƙa
har ƙasa rigar kuma mai hannun Spaghetti ne kanta sanye da hular Net jikinta na fitar da sanyayyan
ƙamshin tularen ta yayin da hannunta ke riƙe da wayar Mommy tana latsawa.

Da sauri Haiydar ya kalleta tare da cewa.

“Addah Khausar na manta ban faɗa miki ba, ɗazu kafin na wuce Masallaci Uncle Naseer yace. In faɗa
miki kije ki same shi a sashen Gimbiya Dadu yana son ganinki”.

Nanda nan Khausar ta canza fuska tare da cewa.

“A falon Gimbiya Dadu kuma!?”.

Harara Mommy ta watsa mata kana tace.

“Toh cin yeki Gimbiya Dadu za tayi ko kuma me Ni nalura wani shan ƙamshi kike yiwa Naseer fa, idan
kinsan bakya sonshi ki fito fili ki faɗa, sannan ki fito da wanda kike so, tun kafin kakar ki tazo ta
buwayemu da batun Aurenki.

Kinga dama ta ajiye target ne kina gama Secondary school magana ya ƙare za azo ayi miki aure”.

Ajiyar zuciya ta sauƙa kana ta cigaba da cewa.

“Idan kuma kinƙi baki da hujjar da zaki ƙi Auren Aliyu, dole kibi zaɓin ta dan haka ma gwara ki tsaida
zuciyarki kisan me kike ciki don in duniya duk zasu taru babu mahluƙin da zai hana batun wai kin gama
secondary School za'ayi miki aure, tunda har Hajja Nana ta rantse, dan haka gwara kawai ma ki tsaida
zuciyarki, ki fidda mijin da zai iya barinki kici gaba koda kinyi aure, kuma da fidda wanda kike sone, zamu
samu hujjar nuna mata kinada wanda kike son”.

A hankali Khausar ta janye idonta daga kallon Mommy kana tace.

“To amma ni gaskiya ba zanje.

Falon Gimbiya Dadu ba”.

Ɓata fuska Mommy tayi babu walwala atare da ita tace.


“Maza ki wuce kije idan ita kura ce to ta cinye ki”.

Miƙewa Khausar tayi badan ranta yaso ba sai dan ganin yanda Mommy ta ɓata rai yasa ta ɗauki hijabinta
dake fitar da ƙamshi sanya kana ta fice.

Acan ɓangaren su Moddibo kuwa zaune suke aɗakin Innayi shi da M Jameel bayan sun kammala cin
abinci Anutse ya miƙe tare da kallon Innayi da suke magana da M Jameel ya gyara tsayuwar sa tare da
cewa.

“Innayi saida safe”.

Kallon sa M Jameel da mamaki afuskarsa yace.

“Zaka je ka kwanta fa kace?”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Eh”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare da faɗin.

“Ok nima zan tafi gida”.

Ahankali Moddibo ya buɗe Idanunsa dake lunshe kana yace.

“Mu kwana anan mana tunda har ƙarfe takwas tayi”.

Girgiza kai M Jameel yayi tare da miƙewa kana yace.

“A'a ina so Inje gida”.

Kallon yanayin fuskarsa Moddibo yayi tare da cewa.

“Dan Allah mu kwana mana”.

Ataƙaice M Jameel yace.

“A'a tafiya zanyi”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauke tare da cewa.

“Toh shikenan ni zanje in kwanta”.

Ya Ida maganar tare da ficewa.

Da kallo Innayi da M Jameel suka bisa har ya ɓacewa Kallonsu.


Moddibo kuwa yana shiga falonsa yayi saurin yarfe hannunsa tare da jan tsaki tare da jan numfashi
kamar wanda yaci yaji lokaci ɗaya lips ɗin sa suka kama rawa cikin yanayin damuwa ya dafe kansa tare
da cewa.

“Ya salam³,Wannan wani irin al'amari ne meke mai wuyar ɗauka haka?”.

Cikin mutuwar jiki ya wuce kichen tare da ɗaukan Cup ya ɗauraye ya zuba ruwan Tea kana ya yanka
lemun tsami ya matse sannan ya zuba zuma ya kafa kansa ya shanye tass, ajiye Cup ɗin yayi ya fita zuwa
Bedroom ɗin sa yana shiga ya kwanta ko minti ɗaya baiyi da kwanciya ba yayi saurin miƙewa ya zauna
cikin sauri ya sake komawa ya kwanta tare dayin ruf da ciki cikin wani irin yanayi yasanya hannunsa duka
biyu ya danne mararsa saboda wani masifaffen harbawa da yakeyi.

Acan ɓangaren Gimbiya Dadu kuwa cikin sanyi jiki Khausar ta buɗe ƙofar falon tare da Sallama tana shiga
ta...!

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a
kanki littafin 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta
WHATSAPP 09097853276, kana in saki a Group ɗin da zanke posting nashi, yar uwa koda kinga LITTAFIN
SAKAYYAH A WAJE TO na satane, in dai kin san baki biya kadama ki karanta.*

*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son
k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman
lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun
matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa
ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki
tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones
dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da
tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da
ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda
ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya
wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka
kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.
Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki
da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp
in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta,
muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina
nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a
ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.

0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta
wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije
gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.

GARKUWAR MA'AURATA

*By*

*GARKUWAN MARUBUTA*

SAKAYYA

20

Tana shiga ta sauƙe numfashi ganin babu. Gimbiya Dadu, falon shiru ba kowa sai Uncle Naseer dake
zaune kan 3sitter yana riƙe da system akan cinyarsa da kuma wayarsa.

Yana ganinta yayi saurin rufe system ɗin kana ya zira wayarsa acikin aljihu tare da tsira mata idanu afili
ya furta.

“Wowww Masha Allah kinsha kyau My Dear”.

Batare da tace komai ba ta ƙara sa shiga falon tare da yiwa kanta masauƙi akan 1sitter.

Tsuke fuska yayi tare da zuba mata idanu kana yace.

“Meyesa ba zaki zauna akusa dani ba My Khausi?”.

Kallonsa tayi da lumsassun idanunta kana da alamun bacci acikin Muryanta tace.
“Unclr Naseer nan ma yayi”.

ta ƙarasa maganar tana mai lumshe Idanunta.

Ido ya tsira mata yana kallon yanda ta lumshe sexy Eyes ɗin ta miƙewa yayi tare da dawowa kusa da ita
ya zauna a hannun kujeran, yana shaƙan daddaɗan ƙamshin turarenta, Khausar kuwa jin alamu sa akusa
da ita yasa tayi saurin buɗe Idanunta dake lumshe kana ta miƙe da niyyan barin wajen.

Cikin hanzari ya sanya tafin hannunsa dake ɗauke da zoben azurfa ya riƙe nata yana binta da wani
mayataccen kallo.

fuskarta ta yamutsa cikin ɗaure fuska kana da rashin walwala tace.

“Me haka Uncle Naseer?”.

Langwaɓar da kai yayi tare da tsaida idanunsa cikin nata kana ya karyar da murya tare da faɗin.

“Guduna zakiyi?”.

Kai ta girgiza masa tare da lumshe Idanunta jin bacci na fusgarta kana tace.

“A'a ba gudunka nake ba kawai dai ai baidaceba”.

Karyar da muryarsa yayi tare da yi mata kallon Up and down kana yace.

“Toh ki zauna anan ni dodone, ko kuma cinye ki zanyi mai yasa kike min haka ne Khausar”.

Kai ta girgiza tare da gyara hijabinta kana tace.

“Bai dace bane Uncle Naseer haka baiyi ba ni ka sakar min hannu”.

Wani kallo ya watsa mata kana yace.

“Bazan sakar miki hannu ba”.

Ya ida maganar yana latsa mata hannu tare da yi mata tafiyar tsutsa.

Cikin fushi ta.

Fisge hannunta tare da galla masa harara kana tace.

“Ni gaskiya banason abinda kake min banaso sam”.

Ta Faɗa tare da juyawa zata bar masa falon.

Da sauri ya miƙe tare da shan gabanta kana ya durƙusa akan gwiwoyinsa tare dasa hannunsa duka biyu
ya riƙe kunnensa cikin wata. Sanyayyar murya mai cike da lallashi ya zuba mata ido tare da cewa.
“Na tuba dan Allah kiyi haƙuri, bazan ƙara ba Insha Allah, ki gafar ceni kinji My dear.

Dan Allah Dan darajar Annabi Muhammad (S.A.W) kiyi haƙuri ki koma ki zauna naji Ni zan zauna a ƙasa”.

Jin haka yasa ta saki ajiyar zuciya tare da komawa ta zauna.

Murmushin gefen baki ya saki tare da miƙewa ya zauna aƙasan Capet mai taushi dake malale Atsakiyar
falon tare da yin tagumi kana ya tsira mata Idanu, tare da saki ajiyar zuciya langwaɓar da kai yayi kana
yace.

“Khausar ina sonki, ya zanyi idan har kikayi fushi dani rayuwata ba zata yimin daɗi ba. Duniyar nan zata
yimin duhu matuƙar dai kikayi fushi dani, hankalina ba zai kwanta ba.

Kada ki mancefa na yarda nabi duk dokan da aka samin nacewa kada in sake inyi miki maganar soyayya
har saikin kammala Secondary school, ni Kuma na kammala karatuna”.

Ajiyar zuciya ya saki tare da fesar da numfashi kana yace.

“Bisa wannan sharaɗin aka hanani koda jin Muryan kine Koda na Kira Mommy mun gaisa baza ta baki
mu gaisa ba, haka nayi ta dakon soyayyarki azuciyata, duk tsawon shekarun nan da nayi a India ina
ɗauke da dakon soyayyarki Khausar, Ina son ki³ kinsan tsawon shekara shida ba wasa ba I miss you, I
really love you Matata, kece farin cikina kece sirrina kece duniya ta Khausar will you Marry me?”.

Ahankali tayi ƙasa dan kanta har ga Allah batasan mai zata ce dashi ba.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Khausar zaki Aureni!?”.

Lallausan tafin hannunta tasa ta rufe fuskarta batare data bashi amsa ba.

Shi kuwa Naseer murmushi ya saki kana yace.

“Nagode My Khausi”.

Domin shi duk azatonsa kunyarsa da kuma rufe fuskar da tayi sonsa take.

Cikin Sanyayyar murya mai taushi da kulawa ya kalleta kana yace.

“Kece Sirrina duk abinda zanyi aduniya dole ke sirrina ce, dake zanyi shi abubuwa biyu ne suka dawo
dani ƙasar nan Khausar,

akwai mahaɗin abinda ya dawo dani ƙasar nan sai kuma burin mallakar ki da fatan kasancewarki
mallakina na har abada”.
Cikin sanyin murya mai ratsa zuciyar duk wanda ya saurara tace.

“Uncle Naseer kace Ubangiji ya mana zaɓi msfi al'khairi, duk abinda muke so aduniya mu barwa Ubangiji
zaɓi kaji ko Uncle Naseer”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Naji Nagode amma ina da wata alfarma da nake so in nema awajenki shin zakiyi min shi?”.

Cikin sanyi da alamun bacci a idanunta tace.

“Eh Uncle Naseer in baifi ƙarfina ba zanyi maka shi”.

Gyara zamansa yayi tare da cewa.

“Kinyi alƙawari?”.

A hankali ta buɗe Idanunta sosai akansa kana tace.

“Toh ai ban sani ba yafi ƙarfina ko baifi ba”.

Langwaɓar da kai yayi tare da cewa.

“Baima fi ƙarfin kiba Khausar. Insha Allah bai fi ƙarfin ki ba zaki iya ba abune na kokuwa ko dambeba
sannan ba mugun abu da zai saɓawa Addinmu bane".

Ajiyar zuciya ta saki kana tayi murmushi tare da cewa.

“Allah dagaske!?”.

Ka ya jinjina mata kana yace.

“Eh dagaske”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan Uncle Naseer”.

Idanu ya tsira mata tare da faɗin.

“Kinyi alƙawari zakiyi min!?”.

Wara manyan Idanunta tayi tare da cewa.

“Bana so ina ɗauki al'ƙawari bansan kuma menene bane!”.

Cike da manufa ya karyar da murya tare da cewa.


“Ni dai nafi son kiyi min al'ƙawari, zaki te maki rayuwata, da kuma cigaban mu, da Kuma jin daɗin ki kinji
ko Khausar, saboda jin daɗina da jin daɗin ki nakeso muyi wannan abin kuma wannan sirrin mu ne
amatsayin ki na matata dan ko mahaifiyata bata san wannan sirrin ba!”.

Nan-nauyan ajiyar zuciya Khausar ta saki Idanunta akansa tace.

“Toh wannan wani irin sirrine ka faɗa min mana”.

Kai ya Girgiza tare da cewa.

“A'a har sai kinyi al'ƙawari zaki min abun zan faɗa miki”.

Girgiza kai tayi kana tace.

“Yaya Naseer bana so in maka al'ƙawarin da ban sani ba ko bazan iya ba”.

fesar da iska mai sanyi yayi tare da kallonta kana yace.

“Zama ki iya”.

Kallonsa tayi ganin yanda ya marairaice yasa ta saki Ajiyar zuciya tare da cewa.

“Toh shikenan sai nayi shawara”.

Da sauri ya kalleta tare da cewa.

“Shawara kuma da waye zakiyi shawara? bana faɗa miki siririn mu bane! Sirrina ne dani dake
kasancewar abu ɗaya zamu kasance, zaki kasance matata kuma uwar ƴaƴana kece zaki kasance ruwa
mai kashe min ƙishina”.

Sauƙe sanyayyar Ajiyar zuciya tayi tare da faɗin.

“Toh shikenan sai nayi tunani”.

Langwaɓar da kai yayi tare da cewa.

“Zuwa yaushe?”.

Shiru tayi alamar tunani sai kuma tace.

“Zuwa gobe ko jibi”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan ba damuwa Allah ya kaimu muyi hira mana”.


Marairaice fuska tayi kana tace.

“Ayyah Uncle Naseer bacci nake ji”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Toh shikenan muje inda rakaki”.

Batace komai ba tashige gaba yana biye da ita, tare da zubawa ƙugunta idanu saida ta shiga falo sannan
ya koma ya shiga motarsa ya wuce gida.

Acan ɓangaren Moddibo kuwa awannan dare haka ya kwana cikin mawuyacin hali saboda wani
azabebben yanayi dake damunsa sai. Wajajen ƙarfe uku da rabi wani irin bacci mai shegen daɗi ya
ɗauke sa.

Can cikin baccin nasa ya fara wani irin bahagon mafarki, ganinsa yayi tare da Khausar, suna kwance akan
gado ɗaya cikin wani irin ni'imtaccen bargo fari ƙal mai masifar taushi, kana babu komai a jikinsu yana
rungume da ita hannunsa na dama nakan yalwataccen sumar kanta mai ƙamshi da sheƙi yana shafawa,
yayin da ɗaya hannun ke kan caɓullenta yana murzawa.

Cikin Sanyayyar murya mai cike da shagwaɓa Khausar ta sakar masa wani irin narkekken kuka tare da
cewa.

“Tsoro nake ji nikam bazan iya ba Moddibo kabar ni bazan iya ba”.

Shi kuwa Moddibo karyar da murya yayi cikin tattausan murya mai cike da salama yake lallashinta.

Ƙarfe huɗu dai-dai ya farka sakamakon kiran sallar assalatu da akayi miƙa yayi tare da furta.

_“Alhamdulillahi lazi ahyana bada amatana wa'ilaihin nushur”_.

Kana ya tashi zaune yana kallin Boxes ɗinsa da ya bada damshi alamar yayi ta liking.

Cikin sauri ya furta.

“Ya Salam Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n nashiga Uku”.

Da sauri ya miƙe tare da dafe kansa kana yace.

“Innalillahi Wa'inna ilahi rajiu'n, shin wannan wace irin Masifa ce mai nacin tsiya da bibiyata, madadin
abin nan yayi baya kullum sai gaba-gaba yake yi, yanzu abin har yakai matakin mafarkin yarinyar nan
nakeyi wannan wace irin rayuwa ce? In banda ma rashin kunya da raini ya za'ayi yarinyar nan ta biyoni
har cikin bacci na”.
Sake kallon boxes sa yayi dan tabbatar wa still gani yayi zahiri ya jiƙe da yarinyar amafarki, cike da
tafasan zuciya ya shafa Dk ɗin sa dake bayyana zalamarsa duk da cewa yayi liking.

Amma bai nitsuba ba zama yayi abakin gado tare da dafe kansa da hannu biyu ji yake tamkar ya fashe
da kukan takaici.

“Tabbas da ace mafarki na zama gaskiya to da sai na sumar da yarinyar nan, ta yadda har abada bazata
sake zuwan min ba”. yayi mgnar a sama lips inshi.

Ahankali kuma sautin muryanta yashiga dawowa cikin kunnensa tana cewa.

“Tsoro nakeji bazan iya ba Moddibo”.

Wani dogon tsaki yaja kana cikin wani irin fushi ya miƙe tare da lumshe idanunsa tabbas badan amafarki
bane da sai yayi maganin yarinyar.

Toilet yashiga tare da wanka kana ya ɗaura Al'wala duk zuciyarsa babu daɗi bayan ya shirya ya tafi
masallaci.

Bayan kwana biyu kamar ko yaushe Anutse Khausar ce ta fara miƙewa kana tayi submitting ɗin Booklet
ɗin ta yayin da sauran ɗalibai ke cizon gindin biro sosai Exam ɗin Nahwun ya basu wahala ahankali.
Khausar ta fita tana lumshe Idanunta duk da cewa ta saba answering questions kafin abasu amsa amma
na yau ya wahalar da ita ajikin Up stair ta tsaya tare da ɗaura hannunta akan step ɗin sama kana ta zu
bawa farfajiyar makarantar Ido, sanyayyan iska na kaɗata tsayuwar ta da kamar minti biyar wata baƙar
mota tazo ta faka ta bada baya.

Cikin sauri ta zare Ido tare da kallon number motar cike da mamaki da al'ajabi ta mitsika Idanunta tare
da sake kallon number motar cikin rawan murya tace.

“Wannan Motar Again?”.

Tabbas wannan shine motar da tagani a Jauro Yaya a lokacin da suka tafi Rafi dasu Dija still, kuma aranan
aka kashe Baffa Umaru tabbas kamannin motar da kuma Number ba zasu taɓa ɓace mata ba to amma
mai yazo yi amakarantarsu.

Kallon motar ta sake yi still Yana tsaye cikin sauri ta fara taka step ɗin tana haɗawa bibbiyu har ta sauka
kana ta nufi gate.

Da sauri Baba Mai gadi ya miƙe tare da cewa.

“Khausar ina Zakije?”.


Kallonsa tayi tare da cewa.

“Saƙo zan amsa awajen masu wancan motar”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Kinsan dokar makarantar nan bata bari idan anshiga afita amma kina amsa ki dawo”,

Kai ta gyaɗa tare da ficewa shi kuma yabi bayanta.

Ahankali ta tsirawa number motar Idanu kana cikin sanyin jiki ta nufi motar.

Mutanen dake Cikin motar kuwa sam basu lura da ita ba saida taje gab dasu suka lura da kamar tana
leƙa su ne, kana ga dukkan alamu Idanunta na kan Plate number motar cikin sauri suka ɗaga glass ɗin
motar dake ƙasa.

Khausar kuwa cikin sauri ta nufi gaban motar dan ganin fuskokin su waye ne, mutumin dake zaune a
mazaunin Driver ne yayi saurin figar motar da mugun gudu suka tafi.

Cike da mamaki Khausar ta dafe kuncinta tare da cewa.

“Ha'a to meyesa haka?”.

Anutse ta juya bayanta jin Muryan Baba mai gadi na cewa.

“Toh ya kuma ba abinda suka baki suka ja mota da gudu haka suka tafi?”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da kallon Baba mai gadi kana tace.

“Agaskiya bansan suba fa, amma dai na taɓa ganin motar acan Rugar mu shiyasa yanzu na saƙƙo inga
shin wannan motar ce ko kuma watace, kuma na gane motar ita ɗin ce, kuma awannan ranan ma dana
gansu haka suka gudu”.

Kai Baba mai gadi ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh Allah yasa dai lafiya?”.

Nan-nauyan ajiyar zuciya ta saki tare da furzar da iska mai zafi daga bakinta kana tace.

“Ka kula gaskiya Baba mai gadi, ka kula duk sanda kasake ganin wannan motar ka faɗa min”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Toh shikenan amma ai kalar motoci da yawa taya zan gane wannan?”.
Sauƙe numfashi tayi tare da faɗin.

“Aina riƙe number”.

Bata jira cewarsa ba ta janyo biron dake kanta tare da yagar ƙasan Qautions paper ta rubuta masa
number tare da miƙa masa kana tace.

“Gashi ka riƙe duk sanda ka sake kallon tazo bakin makarantar nan, ka faɗa min ni ban yarda da motar
nan ba, dan ko can Rugar da suje adaren ranan akwai abinda ya faru”.

Ajiyar zuciya ta saki tare da rintse Idanunta kana ta cigaba da cewa.

“Haka nan naji na tsargi motar duk da bani da tabbaci sannan still yauma. Kaga tazo ta tsaya mana
abakin makaranta Indai tazo ka sake ganinta ka sanar min ko kuma ka sanarwa Malamai”.

Jinjina kai Baba mai gadi yayi tare da cewa.

“Toh shikenan insha Allah ”.

Kai ta gyaɗa tare da buɗe ƙaramin gate ta koma cikin makaranta tana koma suka haɗu da M Jameel na
ƙoƙarin zuwa office.

Da Mamaki M Jameel ya kalleta kana yace.

“Daga ina kike Khausar kaddai yanzu kika zo?”.

Kallonsa tayi tare da girgiza kai tayi kana tace.

“A'a tun ɗazu nazo na gama Peper nama shiyasa na fito”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“To mai kika je yi awaje?”

Murmushi tayi tare da cewa.

“Wani abu naje na ɗan duba?”.

Gyara tsayuwarsa yayi kana yace.

“Wani abu kika je dubawa bayan kinsan doka da ƙa'idar makarantar nan, in anshiga ba'a fita yanzu kiyi
laifi idan ansaki kaɗe ɗankwali kice rayuwar bauta kike baki da cikekken ƴanci ko?”.

Ƙasa tayi da kanta tare da cewa.

“A'a wata mota ce muka gani nida Baba Mai gadi”. Dai-dai lokacin kuma ta hango Moddibo ya fito daga
corridor da zai sada ka da office ɗin su zare ido tayi cikin sauri ta juya tare da hawa step ɗin class ɗinsu.
Murmushi M Jameel Yayi tare da girgiza kai Dramer Moddibo da Khausar na sanyashi nishaɗi.

Khausar kuwa na haurawa ta samu Asma'u ta fito tayi submitted Booklet din ta ba daɗewa kowa ya fito
sannan suka tafi.

Motar na parking Khausar ta fito dai-dai lokacin Mommy ta shigo tsayawa Khausar tayi har Mommy ta
ƙaraso kusa da ita.

Kallon ta Khausar tayi tare da cewa.

“Mommy daga ina haka naga kamar kin fita Unguwa?”.

Kai Mommy ta gyaɗa mata kana tace.

“Eh Khausar na fita Unguwa naje gidan Aunty Asiya ce yau ta haihu Allah ya sauƙeta lafiya”.

Wara Ido Khausar tayi cike da farin ciki tace.

“Laaaa Mommy Aunty Asiya ta haihu? Mai ta haifa Mommy?”.

Jinjina kai Mommy tayi tana tafiya tace.

“Ta haifi ƴa mace”.

Jinjina kai Khausar tayi tare da faɗin.

“Masha Allah bari nayi wanka naje na duba Baby”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.

“Ai dai kam ya kamata dama anats cewa wai yarinyar na kama dake”.

“Dani kuma Mommy?”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da zama akan 2sitter tana cire hijabinta tace.

“Eh toh da Raudat take kama Raudat kuwa kinga dake take kama shiryasa kowa ke cewa Jaririyar kamar
Khausar ²”.

Murmushin fuskarta ta faɗaɗa kana tace.

“Aikam bari nayi wanka Inje inga mai kama dani”.


Ta ida maganar tare da wucewa Bedroom akan beside drawer ta ajiye tarkacen hannunta kana ta cire
Uniform ɗin ta ɗaura towel tashiga toilet.

Tayi wanka tana fitowa ta zauna gaban Dressing mirrow tare da shafa Lotion ɗin ta, kana ta sanya dogon
rigar material Sky blue ta yane Kanta da baƙin gyale, sannan ta feshe jikinta da turaruka masu daɗin
ƙamshi ta fice.

Mommy dake zaune a falo ta kalleta tare da cewa.

“Khausar ko abinci fa baki ciba?”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“A'a Mommy sai na dawo”.

“Adawo lafiya”.

Anutse ta fita tafiya kaɗan tayi ta isa gidan mutum uku kawai ta samu aɗakin.

Kusa da Aunty Asiya dake mata murmushin ta zauna tare da cewa.

“Aunty Asiya ina baby?”.

“Gata nan”.

Ta faɗa tana nuna mata matar dake gefenta.

“Masha Allah, wata tana kama da niko? Allah ya raya mana”.

Murmushi Aunty Asiya tayi tare da faɗin.

“Ameen Khausar ga Baby”.

Da sauri Khausar ta karɓe ta tare da cewa.

“Bari inga mai kama dani”.

Ta faɗa tana zubawa Jaririyar Ido farace sol da ita ga wani yalwataccen gashi daya kwanta asaman
goshinta kana girar tama da yelwataccen gashi bakinta yayi pich da dogon Eyelashes.

Da sauri Khausar ta ɗago kanta da murmushi afuskarta tace.

“Aunty Asiya wallahi kam Baby kam tayi kyau Masha Allah”.
Jinjina kai Aunty Asiya tayi tare da cewa.

“Aikam dake take kama, wai Gimbiya Dadu tace idan kinzo kitso ina yawan kallonki shiyasa na haifi me
kama da ke”.

Baki Khausar ta taɓe tare da cewa.

“Uhm Ita kuma duk duniya akwai wanda yafi ta kallona ne?”.

Murmushi Aunty Asiya tayi, Khausar kuwa Jaririyar ta miƙa mata tare da miƙewa kana tace.

“Bari in tafi Aunty Asiya Allah ya raya”.

Karɓar Jaririyar Aunty Asiya tayi kana tace.

“Toh ki Gaishe da Mommy da gajiya”.

Amsawa Khausar tayi da cewa.

“Za taji” kana ta fice.

Bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon zaune ta samu Mommy a inda ta tafi ta barta kusa da Mommy ta
zauna da murmushi afuskarta tace.

“Wallahi Mommy Jaririyar muna kama nima naga kamar mu”.

Jinjina Kai Mommy tayi tare da ajiye wayarta kana tace.

“Nima gaskiya naga kamar ku sai naga kamar lokacin kina Jaririya, kuma haka Raudat ma take shiyasa
ake ganin kamar dake take kama”.

Veil dake kanta ta janye tare da cewa.

“Ai dai kam”.

Miƙewa tayi tare da cewa.

“Mommy bari na ɗauko abincina”.

Kai Mommy ta gyaɗa mata sannan ta wuce kichen ɗin.

Bayan kwana shida; Alhamdulillah a yau ne su Khausar suka rubuta Final Exam ɗin su cike da tsananin
farin ciki ko wanne ɗalibi ya fito daga hall da suka rubuta Exam ɗin, cikin tsanananin farin ciki Khausar ta
nufi jikin tap ɗin ruwa tare da buɗe wa ta cika wani ƙaramin Bocket kana ta nufi kan Asma'u dake tsaye.
Rungumeta tayi tare da sheƙa musu ruwan tace.

“Thank God My Asmeey Alhamdulillah yau mun taka matsayi na farko a fannin karatun mu”.

Cike da farin ciki Asma'u da jikinta ke ɗigan ruwa ta kalleta kana tace.

“Sosai kuwa Khausar mun godewa Allah”.

Baki ɗaya ɗaliban haka suka ringa jiƙa jikinsu da ruwa cike da matsanancin farin ciki kasancewar an
hanasu penday yasa suka shiga jiƙa jikinsu.

Khausar kuwa kallon Samira sani da itama jikinta ke jiƙe tayi tare da miƙa mata hannu kana tace.

“Assalamu Alaikum, Alhamdulillah yau kam abinda ya haɗa ya raba”.

Hannunta Samira Sani ta riƙe tare da murmushin gefen baki sai kuma ta watsa mata Harara dama can ba
wani haushin Khausar take jiba tunda Moddibo ba wani kulata yake ba sai dai yadda tafisu ƙwazone ke
bata haushi.

Acan ɓangaren Malamai kuwa baki ɗaya sun hallara a inda suka tanadar dan yin taro Moddibo ne kaɗai
baya wajen bayan duk ɗalibai sun hallara.

M Jameel ya miƙe tare da hura Microphone kana yace.

“Assalamu Alaikum warahmatullah Wabarkatuhu”.

Baki ɗaya Suka amsa da. “Wa'alaikum Salam warahmatullah wabarkatuhu”.

Yayi gyaran murya tare da cewa.

“Da farko amadadin dukkan malamai da shuwagabannin wannan Makaranta muna taya ɗaukakin
Ɗaliban wannan makaranta murnan kammala jarrabawar su na gama makarantar.

Allah ya bada sa'a Ubangiji ya baku ikon fitowa da sakamako mai kyau”.

Baki ɗaya wajen suka amsa da.

“Ameen”.

Tsayuwarsa ya gyara tare da cewa.

“Insha Allah shugaban makaranta zai bada Award da hannunsa ga dukkan ɗaliban da suka cancanta
Malam Bismillahi”.

Miƙewa Malam Arɗo yayi tare da karɓan Microphone ɗin kana yace.
“Ina taya ɗaukakin Ɗaliban wannan makaranta ta *AL,ANSAR Academic School* murnan kammala
karatun su na matakin farko Allah ya Albarkanci karatunki Ubangiji ya ɗauka ku aduk inda kuke”.

Baki ɗaya suka amsa da.

“Ameen”.

Gyaran murya yayi tare da cewa.

“Zamu miƙa award ga ɗilibar da tafi ko wacce ɗaliba.

Hazaƙa da tsafta”.

Baki ɗaya wajen sake nutsuwa yayi dan jin wacece wannan.

“Khausar Usman Abubakar Lelewal itace ɗalibar da tafi ko wacce ɗaliba Hazaƙa da kuma tsafta”.

Atake wajen ya kaure da kabarra masu taya ta murna irin su Asma'u da Aunty Ruƙayya nayi yayin da
masu baƙin ciki irinsu Samira da sauransu keyi.

Cike da nutsuwa Khausar ta miƙe tare da ƙara sawa ta amshi Award cike da tsananin farin ciki.

Gyaran murya Malam Arɗo yayi tare da cewa.

“Ɗalibar da tafi ko wacce ɗalibai Nutsuwa da biyayya itace Asma'u Ahmad”.

Cike da farin ciki Asma'u ta miƙe tare da ƙara sawa ta amshi Award ɗin ta haka aka kira sauran mutum
uku aka basu Award .

Cike da farin ciki Khausar ta koma gida kallo ɗaya zaka mata ka tabbatar da cewa tana cikin farin ciki
zaune take afalon hannunta riƙe da bowl na Fruit Salat.

Haiydar ne yashigo falon bakinsa ɗauke da Sallama kallon Khausar yayi tare da cewa.

“Addah Khausi Uncle Naseer yana kiranki afalon Abba”.

Murmushi tayi tare da ajiye bowl din Fruit Salat ɗin kana tace.

“A'a lallai kam ina zuwa”.

Murmushi Mommy dake zaune gefenta tayi tare da cewa.

“Yau kam Alhamdulillah gidan nan muna cike da farin ciki Khausar an gama Secondary school tare da
samun Award”.

Miƙewa tayi tare da cire hijabin Uniform da har zuwa lokacin yake jikinta wurgi tayi dashi tare da faɗin.
“Yau kam nayi hannun riga da Uniform daga yau nayi bye bye da uniform, shiyasa ko aiki banason aikin
da zai kasance min da Uniform, daga yau na wurgar da Uniform aduniya shiyasa Insha Allah Jenouelist
zan zama in dinga zaƙulo gaskiya aduk inda yake ”.

Murmushi Mommy tayi tare da cewa.

“Toh Allah ya taimaka Ubangiji ya cika miki burinki”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.

Ta faɗa tare da shigewa Bedroom kana ta cire Uniform ɗin ta tare da shiga toilet ta sakarwa kanta
shawer bayan ta gama wankan ta fito Lotion ta shafa tare da sanya doguwar rigar atanfa mai golden
kana tayi ɗaurin ture, ta feshe jikinta da turarukanta masu daɗin ƙamshi kana ta fice. Jikinta na fitar da
sanyayyan ƙamshin kai tsaye falon Abba ta nufa bakinta ɗauke da Sallama.

Lumshe Idanu Naseer dake zaune kan 2sittee yayi tare da zuba mata idanu yana shaƙan daddaɗan
ƙamshin turaren yace.

“Congratulation My Khausi yau kin gama makarantar ki, nayi matukar farin ciki abubuwa na tafiya yanda
ya kamata”.

Murmushi Khausar tayi cike da farin ciki ta jinjina masa kai.

Ahankali Naseer ya ɗauko Flowers dake jikin wata leda anyi wrapping ɗinsa tare da ɗauko kwalin waya
iPhone tare da tarin Choculate ya miƙa mata.

“Ga gift ɗin Graudion ɗin ki”.

Wara Ido Khausar tayi tare da kallon Uban gift ɗin cike da tsanananin farin ciki ta ɗago manyan Idanunta
tare da kallon sa kana tace.

“duka wannan na wane?”.

Kai ya jinjina mata tare da faɗin.

“Yes My Wife duka naki ne”.

Langwaɓar da kai tayi kana tace.

“Mommy ta hanani riƙe waya tace sai na gama Secondary school duka ko lokacin da muke Ss duk abinda
zanyi da waya tace sai dai in karɓi nata yanzu kuma kaga”.

Saurin katseta yayi tare da cewa.


“Ai me ai kun gama kin manta yau kukayi final Exam”.

Jinjina kai tayi tare da cewa.

“Eh haka ne fa Uncle Naseer”.

Murmushi yayi tare da faɗin.

“Kada kice komai kawai kice Allah yamin Albarka, ya mallaka min ke Insha daɗin zama dake”.

Shiru tayi tare da ƙasa da kanta tana wasa da yatsun hannunta.

Miƙewa yayi daga kan 2 sitter da yake zaune ya dawo gabanta ya zauna aƙasan rock ɗin daya mamaye
ɗakin kana cikin narkar da murya yace.

“Naga yau kina cikin farin ciki?”.

Kai ta gyaɗa masa tare da cewa.

“Sosai ma kuwa Uncle Naseer”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da narkar da murya kana yace.

“Nima ki sani cikin farin ciki mana”.

Tana wasa da yatsun hannunta ta ɗago kanta tare da cewa.

“Toh me kake so in yimaka?”.

Karyar da murya yayi tare da faɗin.

“Ki cika min alƙawarin da kika ce zaki yimin, kince sai kinyi shawara nan da kwana biyu amma yau kusan
kwana goma kenan da yin maganar mu kullum idan na tambayeki, sai kice baki yi tunani Ba dan Allah
yau dai kiyi min”.

Cike da farin cikin kammala karatun ta da kuma nasaran data samu ta kallesa tare da cewa.

“Nayi alƙawari Uncle Naseer duk abinda kake so zanyi maka matuƙar bai saɓawa addinin Musulunci ba”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da gyara zamansa kana yace.

“Naji daɗi My Khausi, Khausar ɗina ina sonki My life is nothing without you, you are my World”.

Kallonsa kawai take Amma batace Komai ba.


Ahankali ya sanya hannunsa acikin aljihu tare da ciro wani farin ƙyalle fari ƙal yana fitar da wani irin
ƙamshi mai masifar hawa kai tare da birkita lissafi, ƙyallen ya miƙa mata ba tare da ta karɓa ba ta tsaida
Idanunta akansa kana tace.

“Wannan kuma na menene?”.

Langwaɓar da kai yayi tare da cewa.

“Ki karɓa mana”.

Girgiza kai tayi tare da faɗin.

“Toh ka faɗa min na menene sai na karba”.

Marerece Murya yayi kana yace.

“Ki karɓa mana zan faɗa miki ai ba dai kinyi al'ƙawari ba?”.

Kai ta gyaɗa tare da karɓa..

Murmushi yayi tare da shafa sajensa kana yace.

“Ki shin shina ƙamshin mana”.

Kai ta girgiza tare da jan siririn tsaki asaman laɓɓanta kana tace.

“Haka ma yayi dan inajin ƙanshin yana hawa kai!”.

Zama ya gyara tare da cewa.

“Allah ko?”.

Matsar da ƙyallen tayi daga jikinta saboda irin ƙamshin da yake fitarwa mai masifan hawa kai.

Anutse ta ɗago manyan Idanunta dake lumshe ta kallesa tare da cewa.

“Toh Uncle Naseer mai zan maka da wannan ƙyallen?”.

Matsowa kusa da ita yayi har gwiwan ƙafarsa na taɓa yatsun ƙafa ta cikin wata siga ya karya murya tare
da faɗin.

“Khausar kinyi min al'ƙawari ko?”.

Kai ta gyaɗa tare da cije lips ɗin ta kana tace.

“Eh nayi al'ƙawari”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon ƙofan falon kana yace.


“Kuma na faɗa miki cewa sirrine tsakanin mu dake”.

Kallon farin ƙyallen tayi tare da juyawa ta kallesa kana tace.

“Eh nasani”.

Sauƙe numfashi yayi tare da fesar da iska daga bakinsa kana yace.

“Sannan kinsan na faɗa miki cewa ci gaban mu ne. Ni dake da kuma ƴaƴan da zamu haifa?”.

Jinjina kai tayi tare da cewa.

“Eh nasani ka faɗa min mana”.

Langwaɓar da kai yayi tare da narkar da murya kana yace.

“Zan faɗa miki amma da farko ina so ki.

Sirrinta min dan nasan duk duniya babu wanda zan roƙa ya min inba keba”.

Aƙage ta kallesa tare da faɗin.

“Toh ina jinka ka faɗa min menene?”..

Kallon fuskarta yayi tare da sakin ajiyar zuciya kana ya sunkuyar da kansa.

Idanu Khausar ta zuba masa tare da kallon yanda ya sunkuyar da kansa ƙasa sannan tace.

“Ka faɗa kawai”.

Ɗago kansa yayi cikin sigar rauni yace.

“Kinyi al'ƙawari ba zaki faɗawa kowa ba ko?”.

Jinjina kai tayi tare da cewa.

“Nayi al'ƙawari bazan faɗa ba”.

Sauƙe Ajiyar zuciya yayi tare da faɗin.

“Kin tabbata?”.

Aƙage ta gyaɗa masa kai batare da tace komai ba dan tagaji da wannan tambayar tasa.
Iska ya furzar daga bakinsa kana yace.

“Khausar nasan dai tuntuni kin daɗe da fara period ko?”.

Cikin sauri tayi ƙasa da kanta cike da mamaki da kuma kunyar tambayarsa.

Ya shafa ƙyeyarsa tare da karyar da murya kana yace.

“Ya kikayi shiru?”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“Babu komai”

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da tsira mata idanu kana yace.

“Ki faɗa min gaskiya tsakanin ki da Allah nasan dai kin daɗe da farawa?”.

Ƙin cewa komai tayi sai ƙasa data sake yi da kanta.

“Ki faɗa min gaskiya kiyi haƙuri na haɗa ki da Allah”.

Still Nan ma shiru tayi Zuciyarta na bugawa.

Zama ya gyara tare da faɗin.

“Nasan dai kin fara tabbas”.

Ataƙaice ta gyaɗa masa kai.

Zare Ido yayi tare da cewa.

“Yauwa Alhamdulillah

kin fara period din ko?”.

Kai ta gyaɗa fuskarta babu walwala tace.

“Eh”.

Sajensa ya shafa tare da cewa.

“Alfarma to nakeso kiyi min”.

Gyara zamanta tayi tare da ɗago kanta kana tace.


“Toh wace iriyar alfarma ce zanyi maka?”.

lumshe idanunsa yayi tare da buɗe su akanta kana yace.

“Bance ki bani kuɗi ba, ban kuma ce kibani ranki, ko lafiyarki ba, kuma bance ki mallaka min kanki ba,
kawai abinda nake so ki sammin Period ɗin ki”.

Atsorace ta zare Idanunta tare da ɗago kanta kana cike da mamaki tace.

“In san maka Period Kuma Uncle Naseer? Kamar yaya ban gane ba”.

Tayi mgnar jikinta na rawa kana ta miƙe cike da tsoro tana ja da baya.

Da sauri ya ɗaga mata hannunsa cikin sassauta murya yace.

“Karki manta fa kinyi al'ƙawari zaki sirranta min maganata, kuma shiyasa na faɗa miki dan nasan cewa
zaki siririn ta min ki zauna mana kiji”.

Ya ƙare mgnar yana kuma yin mgnar zuci.

“Wannan yarinya sirri baya kamata da wuri, duk da ta shaƙi ƙamshin turaren nan amman ga yadda take
min gardama”.

Yayi mgnar cikin ƙoƙon zuciyarsa dan baiyi zaton zata iya musa mishiba.

Ita kuwa Khsusar kallonsa tayi jikinta na rawa ta girgiza kai tare da faɗin.

“Toh ai ban fahimci mai kake nufi bane! wannan wace iriyar magana ce? me hakan yake nufi kenan?”.

Marerece Murya yayi da alamun damuwa yace. “Dan Allah dan darajar Annabi Muhammad (S.A.W) kiyi
shiru kar kuyi magana da ƙarfi kiyi magana ahankali zaki fahimceni”.

Lokaci ɗaya tashin hankali ya bayyana afuskarta cike da tsoronsa tace.

“Toh mai zanyi maka?.

Kai ya langwaɓar tare da karyar da kai tamkar mai shirin fashewa da kuka yace.

“Nasan kina Period”.

Cikin fusata da yanayin tsoro tace.

“Ni ka daina maimaita min wannan maganar”.

Matsota yayi tare da cewa.


“Dole in maimaita Miki wannan maganar tunda abinda nake sone kuma kikayi al'ƙawarin zaki yimin!”.

Girgiza kai tayi still jikinta na rawa tace.

“A'a ai ko al'ƙawari idan abu yafi ƙarfin ka ba zaka yiba zaka janye sa”.

Cikin sauri ya kalleta tare da cewa.

“No baifi ƙarfin kiba Khausar bafa cewa nayi kiyi min komai ba, idan Period ɗinki yazo kika fara kawai
zaki ɗauki ƙyallen ne sai kisa shi agabanki madadin kisa Pad Idan yayi awa ɗaya sai ki cire kisa min aleda
zanzo in karɓi abuna shine kawai abinda nake so Khausar abinda kaɗai nake sofa”.

Ya ida maganar cikin yaudara murya tamkar zai fashe da kuka.

Ya cigaba da cewa.

“Kuma kada ki manta al'ƙawari kika yimin kuma baifi ƙarfin ki ba sannan ba kanki nace kibani ba”.

Cike da mamaki take Kallonsa cikin yanayin damuwa da alamun tsoro ta zare Idanunta kana tace.

“To me zakayi dashi Uncle mai zaka yi dashi wannan wani irin abune?, Wannan wace iriyar magana ce
zaka ce min haka Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.

Cikin sauri ya riko tsintsiyar hannunta tare da Marerece fuska kana yace.

“Ki yiwa Allah da Annabi ki nutsu Khausar kar ki manta cewa kinyi min al'ƙawari.

Kuma wallahi idan kika faɗawa wani zan miki abinda ba kiyi tsammani ba!”.

Cike da fushi da kuma tsoro tace.

“Toh me zaka yimin tukunna?”.

Karyar da murya yayi tare da saurin dai-dai-ta nutsuwarsa kana yace.

“Zanyi fushi dake”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da sakin murmushi har tayi zaton ko wani mugun abu zai mata tura
madaidaicin bakinta tayi tare da cewa.

“Nidai gaskiya banyi al'ƙawari ba Uncle tsoro nakeji, amma tukunna mai zaka yi dashi?”.

Ɗan hararanta yayi tare da cewa.

“Ke dai me ruwanki? Maganin abu zanyi da shi maganine ance sai na samu Period ɗin zanyi maganin?”.

Kallonsa tayi still zuciyarta na cigaba da tsinkewa tace.


“Wani irin maganine wannan wanda saida period ɗin mace za'ayi shi?”.

Wani irin kallo ya watsa mata kafin ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.

“Magani ne kawai nace miki magani zan haɗa amma kamar baki yarda dani ba inada matsala ne ke dai in
Zaki yimin in samu lafiya in kuma baza kiyi min ba shikenan dama can aikinsa inada ciwon kai ko?”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da jinjina kai kana tace.

“Eh nasani toh shine ake cemin saina samu yanzu idan kika samin a farin ƙyalle, da daddare in zan
kwanta ne zangoga shi asaman goshina ance insha Allah daga ranan na rabu da shi kenan”.

Sanyayyar Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da lumshe Idanunta kana tace.

“Tsakaninka da waye?”.

Ahankali yace.

“Tsakanina da Allah Wallahi dagaske na faɗa miki. My Khausi Magani zan haɗa kuma kinsan duk sanda
ciwon kan nan ya tashi kamar zan mutu”.

Khausar kuwa jinjina kai tayi tare da sauƙe ajiyar zuciya kana tace.

“Toh shikenan ba damuwa insha Allah zanyi maka”.

Ta faɗa tare da juyewa ta fice bayan ta dauki ƙyallen.

Tun da Khausar ta koma ɗaki ta rasa meke damunta baki ɗaya ƙamshin ƙyallen na damunta ahankali ta
buɗe drawer ta ɗauki leda ta jefa ƙyallen aciki sannan tasake saka wani ledan saida ta ninka masa laida
biyar sannan ta fita bakyard ta ajiye sai asannan ta samu nutsuwa baki ɗaya ƙamshin ɗaga mata hankali
yake.

Bayan kwana biyu Ya kama yau ne ake sunan Aunty Asiya misalin ƙarfe goma Mommy, Hajiya Bunayya,
Amina, Raudat, Ramadan duk suka tafi sunan Aunty Asiya gidan ya rage saura Khausar ita kadai
kasancewar. Mommy tace da ita dai idan ta dawo zata je dan kada abar gidan.

Khausar dake zaune a Bedroom ɗin ta tayi saurin miƙewa jin muryan Asma'u afalo atare Asma'u da
Haiydar suka shigo falon da alama daga koyon Machine ya dawo saboda hannunsa dake riƙe da ƙaton L,
kwanciya yayi akan 3sitter tare da kunna TV bayan sun gaisa da Asma'u, Khausar kuwa cike da farin ciki
ta rungume Asma'u.

Ahankali Asma'u ta janye jikinta daga na Khausar kana tace.

“Ya naji gidan shiru kamar ba kowa?”.

Kai Khausar ta jinjina cikin sanyin murya da alamun damuwa atare da ita tace.

“Eh babu kowa sunje gidan Aunty Asiya yau sunanta, nima so nake inyi wanka sai Inje in duba su.
Mommy nake jira baya ga haka ma jikina duk amace yake”.

Ta ida maganar lokacin da suka shiga ɗakin ƙaramin fridge dake ɗakin Khausar ta buɗe tare da ciro Friut
ta ɗauki Plate akai ta zuba mata kana ta ajiye mata agabanta.

Cike da kulawa Asma'u tace.

“Khausar ya dai na ganki Asanyaye kamar akwai abinda ke damunki?”.

Girgiza kai Khausar tayi tare da cewa.

“Babu komai Asma'u kici Fruit”.

Kallonta Asma'u tayi tare da girgiza kai kana tace.

“A'a Taya zan sha Friut baki faɗa min abinda ke damunki ba?".

Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da faɗin.

“Wallahi Asma'u wani Abu ke damuna, yake kuma bani tsoro nasha faɗa miki al'amarin Uncle Naseer.

Yana bani tsoro kince ba haka ba ko to kinji abinda ya faɗa min kwanaki”.

Atake ta kwashe dukan yanda sukayi da Naseer ta faɗa mata“.

Atsorace Asma'u ta dafe ƙirjinta tare da cewa.

“Kai Khausar kada ki yarda ki sanya Period ɗinki akan wannan ƙyallen ki bashi muka san mai zaiyi dashi
ke har kin yarda dashi”.

Girgiza kai Khausar tayi cike da damuwa ta langwaɓar da kai kana tace.

“Nasan yana da ciwon kai, amma baki ɗaya ban yarda cewa maganin ciwon kai zaiyi dashi ba”.

Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe kana tace.

“Gaskiya kar ki yarda ki kiyaye”.


Cike da damuwa Khausar tace.

“Toh yanzu ya zamuyi?”.

Gyara zama Asma'u tayi tare da faɗin.

“Gaskiya dai kam Khausar kada ki yarda kisa jininki akan wannan ƙyallen, hakan ma bazai yuba mukasan
me yake nufi dashi, kika san me zaije ya aikata dashi ai haka baza ta yuba?”.

Lumshe idanu Khausar tayi kana tace.

“Toh shikenan ai dama bazan saba”.

Mommy ce tashigo tare da ɗaga labulen bayan tayi sallama.

Amsawa suka yi kana cike da ladabi Asma'u ta gaishe da Mommy.

Cikin sakin fuska Mommy ta amsa tare da tambayarta yasu Umminta.

Kallon Khausar Mommy tayi tare da cewa.

“Khausar ki ɗauki Plate da Spoon ki Kai gidan Aunty Asiya”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh”,Juyawa Mommy tayi ta fice.

Miƙewa Khausar tayi tare da cewa.

“Asma'u muje ki rakani”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare da miƙewa direct kichen ta nufa ta tare da ɗaukar Plate da Spoon suka fita kai
tsaye gidan Aunty Asiya suka nufa.

Ahankali Asma'u ta zubawa raguna biyu dake rataye a coumpund ɗin ido, da alama na suna ne duk
angama gyarasu an cire kayan cikinsu ana jiran su tsantsame.

Har suka shiga cikin gidan suka kai Plate ɗin baki ɗaya hankalin Asma'u na kan ragunan dake coumpund
ɗin bayan sun fito Asma'u ta kalli ragunan cikin sanyin murya ta kalli Khausar tare da cewa.

“Khausar ga dama ta samufa”.

Da sauri Khausar tace.

“Wacce damar”.
Cikin yin ƙasa da murya Asma'u tace.

“Dauko ƙyallen nan zamuyi muzo musaka jinin wuyan ragon nan”.

Jinjina kai Khausar tayi cike da gamsuwa tace.

“Ƙwarai kuwa Asma'u muje mu ɗauka”.

Cikin sauri suka fice cikin sa'a koda suka shiga basu samu Mommy a falon ba tana toilet. Haiydar kuwa
baya nan kai tsaye backyard suka nufa Khausar ta ɗauki ƙyallen a inda ta ajiye sannan ta since.

Da sauri Asma'u ta kawar da kanta gefe jin yanda ƙamshin jiki ya bugeta.

Cikin ya mutse fuska tace.

“Kai Wannan wani irin ƙamshine mai tada hankali ba daɗin ji”.

Baki Khausar ta taɓe kana tace.

“Hmm nima dai haka naji”.

Ahankali suka juya suka fita kai tsaye gidan sunan suka nufa Baba Mai gadi dake zaune yace da.

“Hajiya Khausar ya gida?sai yanzu kika leƙo?.

Murmushi tayi tare da cewa.

“A'a ɗazu ma nazo bamu ganka bane”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Ayyah wataƙil na zagaya ne”.

Cikin sa'a babu kowa a coumpund ɗin kallon Khausar Asma'u tayi cikin ƙasa da murya tace.

“Kinga mai gadi na kallonmu sai munje dai-dai wajen ragon zan durƙusa kamar takalmina ya tsinke ke
kuma saikiyi saurin daddalan jinin ajiki”.

Kai Khausar ya gyaɗa suna isa wajen Asma'u ta tsugunna tana taɓa ƙafarta.

Khausar kuwa cikin sauri ta matsa jikin ragunan ta ciro ƙyallen cikin leda sannan ta manna ƙyallen ajikin
wuyan ragon dake ɗigar da jini kaɗan-kaɗan sannan ta sake dan dala tayi haka har sau uku ajikin wuyan
ragon cikin sauri tace.

“Asamu'u nayi mu tafi”.

Miƙewa Asma'u tayi suka nufi ƙofa,Baba mai gadi yace.

“Ya dai Asma'u ta kalmin tsinkewa yayi ya kuka tafi baku shiga ba?”.
Murmushi Asma'u tayi tare da cewa.

“A'a kawai dai na ɗan gurɗene naji ƙafar na yimin ciwo sannan mun manta ɗauko abinda Mommy ta
aiko mu mukawo”.

Daga haka suka fice daga gidan.

Kai Baba ma gadin ya jinjina musu,

Tare da juyowa, cikin gidan,

Wani irin zazzaro idanu waje yayi cike da tsanani tsoro da mamaki Baba Mai gadi ya buɗe baki da ido da
hanci duka gani, cikin raguna biyu dake rataye ɗaya ya ɓace ɓat......!

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a
kanki littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar
biyanki ta WHATSAPP 09097853276,*

*By*

*GARKUWAN MARUBUTA*

SAKAYYA

21

Cikin tsananin tsoro da mamaki Baba mai gadi ya juya gabas da yamma,r kudu da arewa acikin
coumpund ɗin gidan amma babu mutum babu dalilin mutum, cikin tsananin kaɗuwa da ganin wannan
abin al'ajabin yace.

“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n. Cikin abinda bai wuce second ɗaya ba ace babu rago babu dalilinsa,
kuma abu ayanke bawai da ransa ba bare ace ya gudu”.

Cikin kaɗuwa ya nufi cikin gidan tare da cewa.

“Ya Ilahi mai ya faru”.

Duk ya burkice ganin abin yake tamkar mafarki dai-dai lokacin da mai gidan ƙanin Lamiɗo yake fitowa.

Aruɗe Baba mai gadi yace.


“Alhaji ragunan biyu suna ɗaure amma yanzu naga ba ɗaya”.

Kallon Mamaki Alhj Musa ya masa tare da cewa.

“A'a ragunan biyu yanzu kuma babu ɗaya ƙafa ragon yake dashi Malam Idi?.

Aruɗe Malam Idi yace.

“Wallahi tallalahi Alhj da gaske yanzu-yanzu ragonan yana nan amma yanzu ya ɓace babu shi babu
dalilinsa”.

Tsayuwa Alhj Musa ya gyara tare da cewa.

“Toh ragon ƙafa zaiyi ina zai shiga?”,.

Malam Idi daya gama shiga tashin hankali yace.

“Wallahi da gaske Alhj”.

ya faɗa tare da juyawa ya fice daga gate ɗin ganin su Khausar basu yi nisa ba yasa ya saki Ajiyar zuciya
tare da cewa.

“Khausar!, Khausar!! Kuzo”.

A tsorace Khausar da Asma'u suka jiyo atare kana suka haɗa baki wajen faɗin.

“Ya dai Baba mai gadi”.

Hannu ya ɗaga musu tare da cewa.

“Kuzo dai”.

Cikin rawan jiki da tsoro Khausar tace.

“Lafiya?”.

Cikin ƙasa da murya Asma'u tace.

“Mun shiga uku kad dai ya gane?”.

Da ƙarfi Khausar ta haɗiye wani abu mai ɗaci tare da cewa.

“A'a Insha Allahu ma bai gane ba”.

Suna isa bakin gate ɗin yace.

“Khausar kushigo”.

Ƙara sa shiga sukayi zuciyar su na bugawa da mugun sauri.


Kallonsu Baba mai Gadi yayi tare da kallon Alhj Musa kana yace.

“Dan Allah dan Annabi ba ragunan biyu suna nan ba, har kuka tsaya kusa dasu suna ɗaure ba?”.

Atsorace Khausar ta gyaɗa masa kai kana Muryanta na rawa tace.

“Eh”.

Da sauri Baba mai gadi ya sake kallon wajen tare da cewa.

“Kawai ina zaune fa kamar abin wasa kamar amafarki kamar a Tv naga rago ɗaya ya ɓace”.

Khausar da jikinta ya fara rawane tace.

“Ya ɓace kuma?”

Cikin tashin hankali Asma'u da Idanunta sukayi zuru-zuru ta dafe ƙirjinta tare da faɗin.

“Ya ɓace kuma dai?”.

Jinjina kai Baban mai gadi yayi tare da cewa.

“Wallahi kuwa kun fita kenan ina juyawa naga ragon nan ya ɓace Khausar abin nan abin mamaki fa ina
kuma kun gansu?”.

Shi dai Alhj Musa na tsaye ya harɗe hannunsa aƙirji yana sauraransu cike da al'ajabi.

Cikin tsananin tsoro mamaki da al'ajabi da kaɗuwa gami da kiɗima Khausar ta kalli Alhj Musa kana tace.

“Wallahi kuwa Baba ƙarami muma munga ragunan nikam mafa akusa dasu na tsaya. Innalillahi wa'inna
ilahi rajiu'n yau mun shiga uku Meye faru ya akayi haka?”.

Jin hayaniya yasa mata dake cikin gida suka fara fitowa suna tambayar abinda yafaru duk wanda yaji
rago ya ɓace sai yashiga cikin mamaki da al'ajabi.

Baba mai Gadi da abin ya tsaya masa arai ya kalli mutanen dake wajen tare da cewa.

“Wallahi ganin Idona ragon nan ya ɓace ɓat kamar a Film kuma babu kowa a farfajiyar gidan Khausar
suna fita abin ya faru ina juyawa naga sun ɓace ɓat!”.

Atsorace Khausar ta jinjina kai tare da cewa.

“Wallahi kuwa Muma yanzu muka gansu mun samu ragu nan nan aɗaure”.

Ana haka Mommy tashigo nan ta samu labarin rago ya ɓace nan suka shiga jajantawa.

Khausar kuwa hannun Asma'u taja suka fice bayan sun fita Asma'u ta juya ta kalli Khausar tare da cewa.
“Khausar”.

Juyawa Khausar tayi tare da haɗiye wani abu mai Masifar ɗaci tace.

“Asma'u”.

Asma'u taja dogon numfashi kana tace.

“Khausar da kece zaki ɓace fa. Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n”.

Khausar kuwa da jikinta yake rawan jitayi Idanunta sun ciko da hawaye cike da alhini tace.

“Asma'u mun shiga uku”.

Cike da rawan jiki suka ƙarasa gida kai tsaye ɗakin Khausar suka nufa tare da zama a ƙasa Capet ɗin duk
sunyi zuru-zuru dasu kallo ɗaya zaka musu kasan cewa suna cikin ɗimuwa da tashin hankali mara
misaltuwa.

Cikin rawan murya Khausar ta kalli Asma'u tare da cewa.

“To yanzu kam Uncle Naseer me yake nufi dani? Dama tsafi zaiyi dani, kenan Uncle Naseer ma tsafi ne
Asma'u? ba kingani ba dama ni sam ban yarda da shiba, tsoronsu nake dama Gimbiya Dadu ya take
bare kuma ƙanwarta mun shiga uku dama tsafi zaiyi dani Asma'u shikenan da kashe ni suke sonyi?”.

Cikin raunin murya Asma'u tace.

“Khausar wannan abin ya gigita ni na rasa ta yanda zan fassara shi”.

Ta gumi sukayi yayin da zuciyarsu ta cigaba da bugawa tsoro da tashin hankali ya bayyana atare dasu
lokacin ɗaya zazzaɓi ya fara dirarwa Khsusar.

Ba jimawa Mommy ta dawo kai tsaye ɗakin Khausar ta shiga tana cewa.

“Ohhh Allah mai iko an duba fa ƙasa da sama babu ragon nan babu dalilinsa an duba ko ina babu shi ya
ɓace!”.

Murya na rawa Asma'u tace.

“Mommy muma fa mun gansu”.

Mommy kuwa ahankali ta maida kallonta kan Khausar da jikinta ke rawa duk ta ruɗe cike da kulawa
tace.

“Khausar ya dai?”.

Kuka Khausar ta fashe dashi tare da yarfe hannu kana tace.


“Mommy zan faɗa miki Mommy zan faɗi gaskiya”.

Kallon Mamaki Mommy tayi mata kana tace.

“Meya faru Khausar?”.

Cikin kuka sosai Khausar tace.

“Allah Mommy Zan faɗi”.

Zama Mommy tayi gefensu kana tace.

“Wai meke faruwa ne Asma'u”.

Cikin ƙoƙarin tsaida hawayen Khausar ta riƙe hannun Mommy acikin nata, kana ta zayyane mata duk
yanda sukayi da Naseer da kuma shawarar da Asma'u ta bata sannan ta ɗaura da cewa.

“Mommy kuma nice ɗazun na dandala ƙyallen akan wuyan ragon, har muka ji tsoro kar Baba mai gadi ya
ganmu kuma Allah wanda na shafawa ƙyellen ne ya ɓace”.

Aruɗe Mommy ta saki salati tare da sanar da ubangiji.

_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n. Hasbunallahu wani'imal wakil. La'ilah ha Illah anta subhanaka Inni
kuntu Minal Zhalimin. Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha_. Ohh Khausar am nashiga
uku wannan rayuwa har ina Khausar kin tabbatar?”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Wallahi tallahi Mommy da gaske ne”.

Ta faɗa tare da cusa hannunta ƙarƙashin gado ta ciro mata ƙyallen data ajiye da niyyar idan Naseer yazo
zata bashi”.

Cikin raunin murya tace.

“Mommy kingani Mommy kin gani ko wallahi shine ƙyallen”.

Jinjina kai Mommy tayi tare da kallon ƙyallen da ƙamshinsa ke bugun kanta kana tace.

“Nashiga Uku ni Aysha wannan masifa har ina?”.

Asma'u kuwa ta gumi tayi ganin abin take tamkar almara.

Khausar na share hawaye tace.

“Mommy ina dai yanzu kin gani kinga zahiri Mommy inaga yanzu kam zaki iya yarda su Mayu neko?”.
Girgiza kai Mommy tayi cike da jimami da kuma al'ajabi ta kalli Khausar tare da cewa.

“Toh su sukayi ko shi Allah am nashiga uku ba'a shaidar halin ɗan mutum”.

Girgiza kai Asma'u tayi kana tace.

“Nikam wallahi Uncle Naseer ya bani Mamaki duk da rawan kansa ban taɓa zaton zai aikata irin wannan
abin ba”.

Ta gumi Khausar tayi duk abin duniya ya isheta Hausawa sunyi gaskiya da suka ce Mutum mugun Icce.

Ganin yanda suka ruɗe da al'amari yasa Mommy dai-dai ta nutsuwarta tare da cewa.

“Kar ku damu ku cigaba da addu'a domin addu'a takobin mumunice, sannan kada ku faɗa wa kowa
wannan maganar ya zama sirri atsakanin mu”.

Sai kuma ta maida kallonta kan Asma'u kana tace.

“Asma'u Allah ya miki al'barka, kin cika ƙawar kirki duk inda ake neman ƙawar arziki kin kai.

Allah Ubangiji ya Al'barkanci rayuwar ku ya kuma kare ku aduk inda kuke”.

Haɗa baki sukayi wajen faɗin.

“Ameen”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe kana tace.

“Wannan magana ya zama sirri atsakanin mu, kada ku fadawa kowa daga. Ni sai ku sai kuma Ubangijin
daya halluccemu shi kuma Naseer zamu ga manufarsa.

Za muga iya gudun ruwansa sannan daga yau Khausar koda ya kira ki baza ki sake zuwa inda yake ba ko
dai kina son shi!?”.

Zaro ido Khausar tayi cikin sauri ta shiga yarfe hannun tare da Girgiza kai kana tace.

“Allah Mommy bana sonshi, na tsane shi bani bashi har abada, me zanyi da matsafi ni dai bana sonshi
Wallahi bana sonshi”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da kallon su kana tace.

“Toh shikenan ki kwantar da hankalin Allah ya tsare ku ya muku zaɓi da maza na gari, wannan ma ai
addu'a ce tasa asirinsa ya tonu Allah ya ƙara tsaremu baki ɗaya ku kara riƙo da addu'a in sha Allah duk
sharrin mai sherri sai dai yaga gadon bayanmu”.

Atare suka amsa da.


“Ameen”.

Haka dai akayi suna aka watse kowa na al'ajabi da ta'ajjadin ɓacewar ragon suna.

Acan gidansu Moddibo kuwa M Jameel zaune tare da Innayi Moddibo kuwa na tare da Malam Arɗo bai
dawo ba.

Anutse M Jameel ya ɗago kansa tare da kallon Innayi dake zaune ta tanƙwashe ƙafafunta cikin sanyin
murya yace.

“Innayi”.

Ahankali ta ɗago kanta tare da cewa.

“Na'am”.

Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe kana yace.

“Innayi ni ko badan kar kice ina bincikar ki da tuhumar kiba.

Da zance da Allah Innayi ina ne asalin ƙasar ku tunda nan dai garin naji labarin zuwa kuka yi dan Allah
Innayi ki faɗa min inane asalin garinku sannan, wai kwata-kwata mahaifin A.J bashi da dangi ne? Sannan
Ina dangin Mahaifiyarsa”.

Ido Innayi ta tsira masa tana jin bugun zuciyarta na ƙawura.

M Jameel kuwa cigaba yayi da cewa.

“Sannan dan Allah kiyi haƙuri kada ranki ya ɓaci shin ke kakarsa ta wajen auwace ko kuma kakar sa ta
wajen Uba ne?”.

Kallonsa kawai Innayi keyi tana jijjiga ƙafarta.

Ajiyar zuciya M Jameel ya saki kana yace.

“Dan Allah Innayi ki faɗa min ina son insan wannan abin kada ki ƙi faɗa min ke ta wani gefe ne kika
kasance.

Kaka agaresa sannan kuma akwai abubuwa da dama da suke ɗaure min kai ina so insan su Innayi, idan
har baki faɗa min suba Wallahi zan rayu da ƙumfa dan Allah ki faɗa min kada in mutu baki faɗa min ba”.

Sanyayyar Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da kallon M Jameel kana tace.

“Aaa to mutuwan nan Kam Jamilu am ai tana kan kowa, sannan ni tsohuwa ma ban ce kar in mutu ban
faɗa muku ba, sai kaine zaka ce kar ka mutu ban faɗa maka ba!”.
Langwaɓar da kai yayi tare da karyar da murya cikin son karya logonta da batun zai mutu dan yasan bata
son jin hakan yace.

“Ni dai ki faɗa min”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“Jamilu bana son tone-tone ne Jamilu abar kaza cikin gashinta fa yafi, sannan kuma babu amfanin tone-
tone da faɗe-faɗe!”.

Zamansa ya gyara tare da cewa.

“Innayi Ni dai inaso shi tone-tonen nan da faɗe-faɗen nan ina so afada min waye ne A.J Ina son insan
Abu akan Abokina kuma Aminina ina so insan komai akanshi”.

Sauƙe numfashi tayi tare da kallon M Jameel kana tace.

“Toh nayi maka al'ƙawari ni kuwa zan sanar maka da komai in. Allah ya yarda zan faɗa maka abinda ya
sawwaka duk da cewa bakomai zan faɗa maka ba”.

Jinjina kai yayi kana yace.

“Toh Innayi nagode amma ranan yaushe zaki faɗa min”.

Shiru tayi alamar tunani sai kuma tace.

“Duk ranan dana shirya zan faɗa maka sai kazo kai kaɗai”.

Jinjina kai yayi tare da cewa.

“Toh shikenan Innayi Nagode sosai”.

Bayan sun sake taɓa hira ne ya mata Sallama ya tafi.

Da daddare Misalin ƙarfe takwas Naseer ya shiga gidansu bayan yaje ya gama sharholiyarsa kai tsaye
falon mahaifiyarsa ya nufa zaune ya samu Mahaifiyarsa da Yayunsa mata guda biyu dawowarsu daga
gidan sunan kenan basu daɗe ba.

Zama yayi tare da gaishesu suka amsa cikin sakin fuska.

Aunty Hindu ce ta kallesa tare da cewa.

“A'a yau fa mun ga abin al'ajabi agidan Yaya Musa kawai ragon suna ya ɓace bat.

Ni dai gaskiya ban yarda da mai gadin nan ba da ƙyar idan bashine ya sace ragon ba yazo yana ihu da
kururuwa wai rago ya ɓace rago zai ɓace shi tsuntsune ko abin tsafi ne?”.
Dariya Naseer yayi tare da kallon Addar tasa kana yace.

“Atoh ku dai bin ciki mai gadin nan rago zai ɓace haka nan ba dalili ne”.

Aunty Larai tace.

“Atoh abin dai akwai abin dubawa”.

Miƙewa Naseer yayi tare da miƙa yace.

“Bari na shiga ciki na watsa ruwa”.

Kallonsa Aunty Hindu tayi kana tace.

“Bari muje ka bani tsaraba ta da yake baka da kirki tunda kazo ba kaje gida na ba Naseer”.

Zaro ido yayi kana yace.

“Wallahi ranan naje Aunty Hindu akace min wai kinje kitso yara basu faɗa miki ba?”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Ai kuwa sun faɗa min ba shakka na tuna toh muje ka ban tsara bata”.

Ta faɗa tare da miƙewa gaba yayi tabi bayansa har suka shiga tsarerren falon nasa da komai na ciki ash
colour da baƙi ne Bedroom ya wuce Aunty Hindu kuma ta zauna aɗaya daga kujerun cikin falon tana
jiransa.

Naseer kuwa yana Shiga Idanunsa suka sauƙa akan yankekken rago Atsakiyar gadonsa Atsorace yaja
baya cikin kiɗima da ruɗewa ya dafe kansa tare da furta.

_“Innalillahi Wa'inna Ilahi rajiu'n”_

Aunty Hindu kuwa jin Muryar sa Aƙiɗime yasa ta miƙe da sauri ta isa Bedroom ɗin Idanunta bai sauƙa ko
ina ba sai kan ragon.

Dafe ƙirjinta tayi tare da cewa.

“Innalillahi ragon anan kuma?”.

Cikin sauri Naseer ya sanya hannunsa tare da rufe mata baki kana yace.

“Na roƙe ki Aunty Hindu Dan Allah ki rufa min asiri kada ki faɗa kada kiyi maganar”.

Cike da mamaki da kuma tsoro tace.

“Toh kenan Naseer kaine ka saci ragon?”.


Kallonta yayi tare da cewa.

“Kamarya in saci rago kamar wani almajiri. nima ganin sa kawai nayi akan gadona kamar yanda kika
gansa”.

Harara ta watsa masa tare da kallon ragon dake kan gadon kana ta kallesa tare da cewa.

“Kai ka sace mana in ba Haka ba Naseer menene?”.

Wani shegen kallo ya watsa mata da alamun ɓacin rai atare dashi yace.

“Ba sacewa nayi ba idan ma satar zanyi ba zan saci mai raiba!? Ko ni matsiyacine da bazan iya saya ba, ko
mun rasa wadatane a gidan”.

Sai kuma ya saki Ajiyar zuciya tare da dai-dai ta Muryar sa yace.

“Kawai dai akasi aka samu?”.

Cikin rashin fahimta tace.

“Kamar ya akasi aka samu?”.

Ƙugunsa ya riƙe da hannunsa biyu tare da furzar da Iska mai zafi daga bakinsa kana yace.

“Kawai an ɓata min aikina ne?”.

Cikin rashin fahimta tace.

“Aiki kamar ya?”.

Dafe kansa yayi alamun gajiya kana yace.

“Na haɗa ki da Allah da darajar Manzonsa, ni kar kiyi min tonon silili da tereren ban kaɗa dan Allah ki
haɗiye wannan maganar ƴar uwa ki rufa min asiri wannan magana tsakanin mu ne kawai kin gansa
magana ya ƙare”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da faɗin.

“Toh ka faɗa min menene sirrin?”.

Girgiza kai yayi tare da cewa.

“Ba zaki iya ɗauka ba”.

Kallonsa tayi kana tace.


“Ka faɗa min menene bazan iya ɗaukar ba?Abinda nasani Naseer idan ma maita ce duk mun tsotsa fa!”.

Sake ɗaure fuska yayi kana yace.

“Maita ku kuka tsotsa ni dai bana maita amma ina abin da yafi maita!”.

Zaro Ido tayi tare da cewa.

“Menene?”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe kana ya sake kallon ragon lumshe idanunsa yayi tare da cewa.

“Bokana ne ya bani laƙani idan nayi aiki da al'adan mace zanyi kuɗi zanyi arziƙi mai tarin yawa da yake ba
kisan kai bane shiyasa na bayar”.

Cije labɓansa na ƙasa yayi kana yace.

“Sannan kuma duk yarinyar data saka min jininta zan zo in same ta akan gado na”.

Furzar da iska mai zafi yayi daga bakinsa kana yace.

“Aunty Hindu ina fama da matsala tun da nadawo ƙasar nan ban samu nayi Sex ba. Ina dame ina cikin
tsananin buƙatar Mace, toh kinga Khausar kuma ina sonta sannan nasan cewa nizan aureta shiyasa na
bata mahaɗin maganin da aka bani ƙyallen akan ta samin jininta kinga da ita zanzo in samu akan gado
madadin ragon nan".

A hankali ya numfashi kana ya cigaba da cewa.

“Kinga zanyi Sex ɗina da ita baza ta hanani ba kana nasan.

Ni zan aureta shiyasa ban damu ba jini kuma ba wani abu zai mata ba kawai dai in Anyi amfani da jinin
zanyi arziƙi ne, zan shiga cikin manyan Yara na wannan ƙasar sai dai kiji ƙanin ki ya zama yaro da kuɗi
abokin manya, kije Makka kije Madina inkai ki Dubai in kaiki India kije duk ƙasar da kike so afaɗin
duniya”.

Cike da takaici Aunty Hindu tayi Ƙwaffa tare da cewa.

“Shegiyar yarinya ta ɓata mana aiki, ai wannan yarinyar da kake gani dama ba a abin arziƙi da ita, kai dai
ka dage kana sonta ne amma da wata yarinya ka samu wawuya sai ta saka maka amma wannan da
shegen wayo kamar dila, kaga duk yanda akayi jinin ragon ta saka ajiki tunda dai kaga rago ne yazo maka
kan gado”.

Jinjina kai yayi tare da cewa.

“Wallahi kuwa”.
Dafa kafaɗar sa tayi tare da cewa.

“Kada ka damu zan nema maka yanda zakayi kayi aikin nan”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Toh shikenan Aunty Hindu.

Amma fa muyi taka tsantsan tunda mukayi na farkon nan ya wargaje ina tsoro ko kuma kawai ma zanje
in samu Bokan nawa ya canza min sabon salon aiki”.

Kallon sa tayi tare da cewa.

“Amma kana ganin hakan zai yi?”.

Kai ya jinjina mata kana yace.

“Sosai ma dama ya bani zabi biyu ne akwai wanda za'ayi amfani da jini, sannan idan inaso akwai wanda
za'ayi amfani da Sparm ɗina amma matsalar nan duk yaran garin basu waye bane dake ba wani babban
gari bane ba zaiyi kaje ka hakewa yarinya ba kuma ma anfiso na matata toh akwai kuma na maciji sai dai
shi sai Bayan anyi aure ne, kuma yafi muni shiyasa bana sonshi amman gsky zaifi bada manyan kuɗaɗe”.

Cije lips ɗinsa yayu tare da cewa.

“Da zan samu nayi Sex ai zan iya saka Sparm ɗina ayi aiki da shi dan boka yace anfi son sama amma nace
ayimin dana Period ɗin saboda zanci riba bibbiyu kinga zan samu in kashe ƙishin dake damuna, zan samu
inyi da Khausar tunda Ni zan aureta, sannan kuma mahaɗin arziƙi na zaiyi”.

Ajiyar zuciya Hindu ta sauƙe kana tace.

“Shikenan kaci gaba da gwadata idan ta yarda da lallami in kukayi sex din ai shikenan”.

Jinjina kai yayi tare da cewa.

“Toh zan gwada hakan”.

Atake awajen ya ɗauki ragon yakai kichen sannan ya daddatsa yasa abako kana ya miƙawa Aunty

Hindu ya ce.

“Ki tafi dashi”.

Dariya tayi tare da cewa.

“Wato dai munci banza”.

Murmushi yayi kana yace.


“Eh sosai ma munci banza, to mun isa mu fita da ragon munce mun sameshi adakina ne, aikinga
asirinmu zai tonu".

Jinjina kai Hindu tayi kana tace.

“Hakane”.

Kai tsaye gidanta ta nufa da ragon zata gyara musu kamar yanda yace.

Wayewar garin Laraba baki ɗaya Jama'ar

Garin Gembu sun tashi da lumshi tun ranan da akayi ruwa tamkar da bakin ƙwarya da kuma rugugi ba
asake yin ruwa ba kusan Makonni biyu kenan garin ya zamana har sun fara ɓuƙatar ruwa duk da irin
sanyin da ake musu amma garin ya fara ɗumi ga hadari daya haɗu baƙi asama sai dai babu ruwa sai
Sanyayyar Iska mai sanyi da ratsa jiki da ake surarawa.

Acan ɓangaren Khausar kuwa cikin shiri ta fito daga Bedroom ɗin ta cikin riga da wando na Pakistan daga
saman rigar atsuke take yayin da daga ƙasanta kuwa abuɗe take wando kuwa Pencil ne sosai kayan suka
amsheta sai ya fito tamkar Kajol yayin data ɗaura Maroon ɗin hijab har ƙasa jikinta na fitar Sanyayyar
ƙamsin turaren Oud Ma'arup bakinta ɗauke da Sallama tashiga Bedroom ɗin Mommy.

Anutse Mommy ta ajiye Carbin dake hannunta kana tace.

“Har kin shirya?”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh Mommy”.

Ajiye Carbin Mommy tayi tare da kallonta kana tace.

“Khausar ki kula koda Ummin Asma'u bana so ku faɗa wa abinda ya faru”.

Kai Khausar ta gyaɗa kana tace.

“Toh Mommy ni dai nasan da ƙyar idan Asma'u ta faɗa wa Ummin ta amma idan ma ta faɗa mata
shikenan dan nasan Ummi koda ta faɗa mata babu matsala”.

Jinjina kai Mommy tayi tare da ciro 1k A pose ɗin ta tace.

“Ga Kudin transport”.

Amsa Khausar tayi tare da faɗin.

“Nagode”.

Kana ta fice.
Tana fita ta tari A dai-dai-ta Sahu ta shiga tafiyar minti ashirin da biyar ne ya kaisu gidansu Asma'u.

Anutse ta sauƙa tare da bashi kudin kana ta tura ƙaramin gate ɗin gidan tashiga tare da nufar falon
bakinta ɗauke da sallama tashiga Ummi dake zaune a falo ta faɗaɗa Murmushin fuskarta tare da cewa.

“Khausar sannu da zuwa”.

Cike da ladabi Khausar ta tsugunna tare da cewa.

“Ina Yini Ummi?”.

Murmushi Ummi tayi tare da faɗin.

“Lafiya lau Khausar yasu Hajiya Aysha dasu Haiydar?”.

Khausar ta amsa da.

“Lafiya ƙalau suna gaisheki”.

Jin muryan Khausar yasa Asma'u dake Bedroom din Ummi tana gyara fitowa da murmushi afuskarta
tace.

“Fattanah”.

Miƙewa Khausar tayi tare da wurga mata Harara kana tace.

“Ai wannan sunan na barwa wanda ya liƙa min shi amakaranta sai dai kuma ya sawa wata amma ba dai
niba abi wani sarkin”.

Dariya Asma'u tayi kana tace.

“Ai Suna linzami tunda wasu ma idan za'a kwana ana ce musu Khausar basu sani ba sai ance Fattanah
kinga, kuwa Yaya Moddibo ya sanya miki suna ya biki ko ba ragon suna”.

Taɓe baki Khausar tayi kana suka shiga ɗakin Ummi atare suka gyara ko ina tare da jona bona suka sa
turare.

Bayan sun gama gyara ko ina suka koma ɗakin Asma'u.

Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe cikin ƙasa da murya tace.

“Asmau'u kin faɗa wa Ummi Maganar?”.

Girgiza kai Asma'u tayi tare da cewa.


“Wallahi ban faɗa mata ba Khausar ai Mommy ta gargaɗe mu”.

Jinjina kai Khausar tayi tare da kallon Asma'u kana tace.

“Asmeey kin kuwa san har yau Naseer bai sake zuwa wajena ba sannan bai sake yi min magana ba.

Kuma wayar daya bani akwai sim card da komai da komai amma har yanzu bai sake kira na ba”.

Girgiza kai Asma'u tayi tare da faɗin.

“In dai bai miki maganar ba kada kiyi masa. waya kuma kima ajiyeta kawai dan kuɗin san nan bama asan
na menene ba, kana bamusan me yake nufi dake ba”.

Tagumi Khausar tayi har yanzu abin na mugun bata mamaki koda wasa bata taɓa tsammanin Naseer zai
mata haka ba.

Asma'uce ta riƙe Hannunta kana tace.

“Waya sani ma ko Lalata yayi niyyar yi dake yanda ragon nan ya ɓace wataƙil ke ki ɓace tema ma
aɗakinsa za'a sameki yayi rapping ɗinki”.

Lumshe idanu Khausar tayi kana ta buɗe su akan Asma'u tare da sauƙe Ajiyar zuciya kana tace.

“Haka ma Mommy na tace kuma kinga ta karɓe wayar ma sannan ta tura asiya min waya acikin Taraba
wayar da yafi wacce ya kawo min ma za'a siya Min”.

Muskutawa Asma'u tayi kana tace.

“Yama fi miki nima Ya Jameel yace zai siya min waya”.

Wara Ido Khausar tayi cike da farin ciki tace.

“Kice mun kusa muyi waya mu daina Aron na su Ummi”.

Jinjina kai Asma'u tayi kana tace.

“Ai dai Lallai kam munji daɗin mu”.

Acan ɓangaren Moddibo kuwa a hankali ya fito da motarsa daga gidan Malam Arɗo ya dai-dai-ta hanci
motarsa akan titi cikin nutsuwa yake driven yayin da ƙira'ar ke tashi acikin suratul Muminin cikin,
Sanyayyar sautin muryarsa yake bin ƙira'ar dai-dai ƙofar gidan su M Jameel yayi parking tare da ciro
wayarsa yayi dearling number M Jameel Amma har ya katse ba ayi Picking ba sake kira yayi still ba amsa
ajiye wayar yayi tare da buɗe Murfin motar kana ya fita mai gadi naganin sa yayi saurin miƙewa hannu
Moddibo ya bashi suka gaisa ahankali Moddibo yace.

“J yana ciki ne”.

Cike da girmamawa mai gadin ya girgiza kai tare da cewa.

“A'a” godiya Moddibo ya masa kana ya shiga motarsa kai tsaye gidan Ummi ya nufa da tunanin ƙila
Jameel na can bayan yayi Parking ya fito Anutse ya shiga Falon bakinsa ɗauke da Sallama.

“Ummi dake zaune tana Azkharul masa ta ɗago kai tare da faɗada fara'ar dake fuskarta kana tace.

“Babana sannu da zuwa”.

Cikin yanayin nutsuwarsa da kuma sanyinsa yace.

“Ummi ina yini”.

Ta amsa da.

Lafiya tare da tambayar Innayi

Kansa a ƙasa yace.

“Duk suna lafiya Ummi J fa?”.

Zama Ummi ta gyara tare da cewa.

“Tun shekaran jiya da kuka zo ai be sake zuwa ba amman dai nasan in sha Allah yau zaizo”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauke kana yace.

“Ayyah ni kuma tun safe da muka rabu bamu haɗu bane shiyasa nazo nan, naje can gidan Abba ma baya
nan nayi tsammanin ma yazo nan wataƙil ko suna tare da Innayi”.

Shiru Ummi tayi alamar tunani kana tace.

“Eh to wataƙil ma yana can”.

Jingina kai Moddibo yayi kana yace.

“Ni na kira ma baya ɗagawa”.

Hannu Ummi ta miƙa tare da ɗaukar wayarta kana tace.

“Bari na gwada”.

ta faɗa tare da dearling.


Cikin sa'a yana shiga M Jameel Yayi picking tare da Sallama.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe kana tace.

“Ina kake ne?”.

Anutse M Jameel yace.

“Ummi ina wajen Innayi ce muna hira”.

Kallon Moddibo tayi tare da faɗin.

“Aikuwa ga Moddibo yazo neman ka”.

Dariya M Jameel Yayi kana yace.

“Rabu dashi Ummi be nemeni agida ba ya tafi maƙota yana nema na”.

Kallon Moddibo dake sakin ajiyar zuciya Ummi tayi kana tayi murmushi tare da cewa.

“Ai dai kam”.

Moddibo kuwa kallon Ummi yayi bayan ta katse wayar yace.

“Toh Ummi bari na tafi tun da yana gida kam”.

Jinjina kai Ummi tayi kana tace.

“Toh ba matsala Moddibo Nagode bari na kawo maka abin taɓawa”,

Ta faɗa tare da miƙewa kichen tashiga tare da ɗauko masa Alkaki da dambun naman kaza ta ajiye masa
acikin wasu roba masu kyau.

Amsa yayi da faɗin.

“Nagode Ummi”.

Sannan ya juya har ya isa ƙofan Falon Ummi tayi saurin cewa.

“Yawwa Babana tsaya dan Allah ka ajiye min yarinyar nan agida”.

Ta faɗa tare da juyawa ta nufi ɗakin Asma'u tare da cewa.

“Khausar ina yanzu zaki tafi ga Maghariba ta kawo kai?”

Daga ciki Khausar ta ɗan daga sautin muryanta tare da cewa.

“Eh Ummi yanzu zan tafi”.


Kai Ummi ta gyaɗa tare da juyawa kana tace.

“Toh ki fito Yayanki ya sauƙe ki tunda dai dole sai yabi ta titin unguwar ku”.

Murmushi Khausar tayi tana ƙoƙarin sanya hijabinta tace.

“Yaya Jameel ko?”.

Cikin sauri ta fito falon Cak ta tsaya ganin Moddibo nanda nan ta nemi fara'ar dake fuskanta ta ta rasa.

Hannunta Ummi ta riƙe kana tace.

“Yawwa Babana ka sauƙe min ita agida kasan ƴaƴa mata bama so suna kaiwa dare awaje”.

Shiru Moddibo yayi tun lokacin da Ummi ta ambaci sunan Khausar ya nemi nutsuwarsa ya rasa sam
baya.

Son wata alaƙar da zai haɗa sa da yarinya.

Jin yayi shiru Ummi ta kallesa tare da cewa.

“Ya dai Babana ko dai da matsala ne?”.

Girgiza kai yayi kana cikin sanyin murya yace.

“A'a”.

Still tana riƙe da hannun Khausar tace.

“Toh dan Allah kayi haƙuri ka sauƙeta aƙofar gidansu Lamiɗo”.

Jinjina kai yayi tare da faɗin.

“Toh shikenan Ummi”.

Sannan ya fice.

Har jikin mota Ummi da Asma'u daketa murmushin mugunta suka raka Khausar.

Anutse Moddibo ya buɗe mazaunin Driver ya shiga Khausar kuwa cikin tsinkewar zuciya ta buɗe gaban
motar ƙiran Rang Rover tashiga cikin sauri ta lumshe Idanunta jin wani ƙamshi mai daɗi daya ratsa
hancinta ne yasata lumshe ido, ahankali ta tukure jikinta waje ɗaya.

Moddibo kuwa motar yaja.

Hannu Ummi ta ɗaga musu tare da cewa.

“Toh Allah ya kare Babana Nagode Allah Yamaka albarka”.


Asma'u kuwa murmushi kawai ta saki ganin yanda Khausar tayi tsuru-tsuru tamkar za'ace ƙyat ta arta da
gudu.

Tunda suka shiga motar babu wanda yace da ɗan Uwansa komai kowa da irin tunanin da yake Aransa
kana ga abin hawa da suke giftawa da ɗan gudu kasancewar maghariba ta gabato Ahankali Khausar ta
juya tare da satan kallon sa gudun kada tayi laifi awajen sa yace bata gaishesa ba yasa cikin sanyin
murya tace.

“Malam ina yini”.

Banza yayi da ita kamar bai jiba.

Cikin sanyin Murya ta sake cewa.

“Malam ina yini”.

Still banza ya mata.

Lumshe Idanunta tayi akaro na uku kana tace.

“Malam ina yini”.

Still ƙin tanka ta yayi ya cigaba da Driving ɗinsa.

Ƙawar da kai gefe Khausar tayi tare da watsa masa Harara kana ta murguɗa baki asaman laɓɓanta tace.

“Ai dai nafita hakki ko awajen Allah”.

Shi kuwa Moddibo tunda wannan abin yafaru atsakaninsu yasa yake jin haushin Yarinyar gani yake
tamkar idan suka haɗu zata rainasa kana yana ganin yanayin da suka kasance Amafarki kamar ta sani.

Cikin dakekkiyar murya yace.

“Idan kika sake tura min bakin nan, zan tsike lips ɗin in watsawa karnuka”.

Tsit tayi kamar bata cikin motar, mamaki kawai takeyi ya akayi yasan ta murguɗa mishi baki, domin ko ta
inda take bai kallaba.

A haka dai sukaci gaba da tafiya.

Suna cikin tafiya wata Trailer tazo ta hannun damar su yayin da wata ƙaramar mota ke gefen hagunsu
daga gabansu kuwa mai Napep ne duk ajere suke tafiya Trailer dake gefen damar su ya yanko ta gefensu
tamkar zai hau kansu cikin sauri Moddibo ya karkatar da kan motar zuwa hagunsa cikin rashin sani ya
gogawa motar dake hagunsa cikin sauri ya juya akalar motar zuwa gaba nan ma ya bugi mai Napep dake
gabansu gaba ɗaya abun ya faru a lokaci ɗaya kamar ƙibtawar ido.
Cikin tsananin tsoro da kiɗimar ganin accident na Shirin faruwa yasa Khausar ƙwalla ƙara tare dasa
hannunta kan hannun Moddibon ta damƙe fam tare da faɗin.

“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n, Ɗiyyyyttt-ɗiyyyytttt”,Tayi ƙaran tare da hayewa jikin Moddibo ya zama
na duka rabin jikinta na kansa kana ta ƙanƙame hannunsa tare da manna kanta adamten sa na dama.
Har lau kuma Ɗiyyyt-Ɗiyyyyyyt take cewa kamar itace motar.

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙin na kanki, 1k ne kacal
0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276
sai in saki a Group na inda nake posting littafin. In dai baki biya sis kada ki karanta min littafina, kuma in
kin gashi a wasu wuraren ma na satane, na Allah ya isa.*

Cikin sauri mai Napep ɗin ya ƙara gudu wancan motar tabi bayansa,Cikin ikon Allah ya zamana babu
wanda yaji ciwo Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe yana sakin numfashi baki ɗaya ya gama Imagine zai haw
kan mai Napep ɗin nan, baki ɗaya zuciyarsa ta tsinke.

Khausar kuwa numfashi ta shiga saukewa akai-akai tare da sake manna kanta ajikin damtsen hannunsa.

Ahankali ya juya ya kalli yanda rabin jikinta ke kansa cikin wata Sanyayyar murya mai cike da wani irin
yanayin salo yace.

“Sake ni”.

Wannan shine karo na biyu arayuwarsa da yaji yayi amfani da irin wannan murya wanda shi kansa bai
san daga inda ya samo shi ba.

Ita kuwa cikin sauran tsoron tayi lamo a jikinsa.

Buɗe idanunsa yayi da kyar murya a harɗe yace.

“Zaki kasheni fa”.

Haka nan taji raunin muryar da yayi mgn da ita har tsakiyar kanta.

Cike da tsoro da kuma sanyin jiki ta janye jikinta daga garesa kana ta sauƙe ajiyar zuciya cikin rawan
murya tace.

“Ni dai ka sauƙe ni anan zan shiga Napep”.


Harara ya watsa mata kana ya cigaba da Driving ɗin sa batare daya tanka taba yana isa ƙofar gidansu
yayi Parking cikin sauri ta buɗe Murfin motar ta fita Shikuwa kai tsaye gida ya nufa, zuwa lokacin har
anfara kiran sallar maghariba yana Parking ya fito cikin nutsuwa ya nufi sashen sa tare da wucewa
yashiga toilet kana ya ɗaura alwala ya fito dai-dai lokacin da M Jameel ma ya fito daga ɗaya ɗakin da
alamun shima alwala yayi.

M Jameel na Kallonsa ya zuba masa ido yana murmushi kana yace.

“No wonder A.J Ashe ƙwarjininka ba halitta kaɗai bace gadone jinine mai ƙarfi ke yawo a jikinka”.

Anutse Moddibo ya juya tare da kallon M Jameel daya tsaresa da Ido kana yace.

“Meye kake kallona haka?”.

Murmushi M Jameel Yayi kana yace.

“Ina kallon kane tamkar...!

*Al'bishirunku Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku


ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.

Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce,
akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna
uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin
yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace
ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa
bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore
ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar
gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san
hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa
tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.
Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan
mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina
mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka
yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke
taimakawa (sex hormones 😍) dinki.

Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu
tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?

Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da
ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa
domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.

Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?

Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar
amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin
mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar
mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,

Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke
mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.

Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta
akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.

Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*

Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne
masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na
daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka
ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar
da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari
maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276
domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA
ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba
Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.
Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
😘

*(GARKUWAR MA'AURATA)*

*By*

*GARKUWAN MARUBUTA*

SAKAYYA

22

Cikin sauri Moddibo ya katsesa tare da cewa.

“Kana kallona kamar me?”.

Murmushi M Jameel yayi tare da shafa sajensa kana yace.

“Ina kallon ka kamar Ayu uban Jarababbun duniya”.

Harara Moddibo ya watsa masa tare da cewa.

“Mtssss kai dai baka da aikin yi”.

Ya ƙare mgnar tare da yin ƙasa da kansa yana kallon yanda Jallabiyar, lumshe Idanunsa yayi lokaci ɗaya
tsikar jikinsa ya tashi cije labɓansa na ƙasa yayi kana yaja siririn tsaki tare da komawa Bedroom ɗin sa
buɗe durowarsa yayi tare da ɗaukar boxes ya sanya kana yaƙara dogon wando sannan ya fito still. Yana
jin tudun A ɗin sa M Jameel na ganin fitowarsa ya juya suka fice kai tsaye Masjid suka nufa tare da
gabatar da Sallar Maghariba basu fita ba sai da suka idar da Sallar Isha'i sannan suka fito.

Bayan sun isa bakin gate M Jameel ya nufi jikin motarsa dake fake Kallonsa Moddibo yayi kana yace.

“A'a Baza mushiga muci abinci ba?”.

Cike da kulawa M Jameel yayi murmushi tare da cewa.

“Aini naci tunda zafinsa, kasan tun yaushe muke tare da Innayi kuwa? tun bayan sallar la'asar muna tare
fa sai da aka kira maghariba nashigo nan nayi alwala”.
Wara Ido Moddibo yayi kana yace.

“Iyee gulmar me kuka yi?”.

Murmushi M Jameel yayi tare da faɗin.

“Ta faɗa min komai ta faɗa min duk kan abinda baka sani ba”.

Gyara tsayuwa Moddibo yayi tare da harɗe hannunsa aƙirji kana ya juya ya kallesa tare da cewa.

“Kamarya abinda ban sani ba?”.

M Jameel kuwa murmushi yayi tare da cewa.

“Zuwa yanzu nafi ka sanin kan ka ma nafi ka sanin wanene kai duk yanda kasan kan ka to yanzu na fika
sanin kan ka”.

Lumshe idanu Moddibo yayi tare da shafa sashensa kana ya buɗe idanun nasan tare da kallon M Jameel
yace.

“Iyeeeeh toh zo ka fesa min mana tunda angumtsa maka na hannun damana”.

Tsayuwa M Jameel ya gyara tare da cewa.

“Sirrine sai da nayi al'ƙawari bazan fesa maka ba kafin ake fesa min”.

Moddibo kuwa murmushi yayi tare da shafa sajensa kana yace.

“Toh yanda kayi lallaɓa nima zanje inyi lallaɓan afaɗa min”.

Cikin dariya M Jameel yace.

“Toh kaje ka gwada sa'arka, amma yanzu kam kasani bana cikin duhu”.

Taɓe baki Moddibo yayi kana yace.

“Iyyeeee wato gulmana nema kuka tayi”.

Agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa ya kalla ganin da ɗan sauran lokacin salla ne ya juyo ya kalli
Moddibo tare da faɗin.

“Ba wani gulmarka da muka tayi na dai faɗa mata cewa kana ɓuƙatar aure yanzu”.

Cikin sauri Moddibo ya juya tare da watsa masa Harara Dariya M Jameel yayi tare da buɗe motarsa
yashiga mazaunin Driver key yayi wa motar tare da saita hancin motar ya fara tafiya.

Shi kuwa Modibbo da ƙafa ya nufi masallacin.

A hanya ya tsaya yayi salla kana ya ƙarasa cikin gidan.


Parking aharabar gidan cike da nutsuwa ya fito tare da nufar falon bakinsa ɗauke da sallama ya shiga.

Ahankali yake bin cikin falon da kallo batare daya shiga ba cikin hasken fari gloves ɗin da suka haska
falon kana da murmushi afuskarsa yace.

“Ina Umminaaaa?”.

Ummi dake zaune kan 3sitter idanu ta zuba masa batare da tace komai ba.

Malam Ahmad dake zaune kan 1sitter ya kalli M Jameel dake tsaye ƙofar falon tare da cewa.

“Ƙara so mana Jamilu”.

Juyawa yayi ya kalli Ummi kana yace.

“Kin tsaresa da ido kuma baki ce masa ya shigo ba”.

Murmushi M Jameel yayi tare da cewa.

“Ummi nayi kyau ko?”.

Jinjina kai Ummi tayi still Idanunta na kansa tace.

“Sosai ma Babana”.

Murmushi yayi tare da Wara ido kana yace.

“Iyyeee naji daɗina yau kuma nine Babanki ko da yake Baban miji ai baba ne?”.

Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana yace.

“Sosai ma”.

Ummi kuwa still Idanunta na kanshi.

Bashir daya fito daga Bedroom ne ya kalli Ummi kana ya kalli M Jameel data tsirawa Idanu matsawa kusa
da Ummin yayi tare da cewa.

“Yaya Jameel wallahi Ummi na sonka kamar me”.

Sai asannan Ummi ta ɗauke Idanunta daga kan M Jameel ta mayar kan Bashir tare da yi masa daƙuwa
kana tace.

“Haka naka Bashiru”.

Asma'u data fitowarta kenan daga Bedroom tayi murmushi tare da zama gefen M Jameel.

Miƙewa Malam Ahmad yayi tare da nufar ɗakinsa bayan sun gaisa da M Jameel.
Kallon Asma'u M Jameel Yayi tare da cewa.

“Asmeey”.

Cike da ladabi ta ɗago kanta kana tace.

“Na'am Yaya”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da cewa.

“Zuwa yanzu kaso 85% cikin 100% na nauyin ku dake araina nake tunawa 85% sun sauƙa min saura
shabiyar nake tunawa 15% ɗin nan kuma sune manya masu wuya”.

Ajiyar zuciya yauƙe tare da cewa.

“Ina so inga kinyi karatu kin gama, sannan na miki zaɓi da miji na gari Mumini, Salihi, Mai tsoron Allah,
na Aura masa ke, sannan na danƙa masa Amanar ki.

Hakazalika Ina so inga Bashir ya gama karatunsa ya fara aiki ta yanda ko bana kusa zai kula da Ummin
mu ba zata nemi komai ta rasaba”.

Cikin yanayin damuwa Asma'u tayi ƙasa da kanta lokaci ɗaya Idanunta suka ciko da hawaye yayin da taji
zuciyarta yana masifar bugawa da ƙarfi Allah ya sani in ta tuna zatayi aure ta rabu da Unminta tanajin ba
daɗi.

Cikin raunin murya tace.

“Bare ma Yah Jameel kai zaka yiwa Ummi komai kafin mu”.

M Jameel kuwa murmushi yayi tare da kallon Asma'u kana ya cije labɓansa na ƙasa tare da lumshe
idanunsa yana sauraron bugun zuciyarsa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da buɗe idanunsa akan Asma'u kana
yace.

“To ai ita rayuwar dama ta gaji haka watarana ayi farin ciki watarana ayi baƙin ciki!”.

Girgiza Kai Bashir yayi tare da kallon M Jameel cikin yanayin tsinkewar zuciya ya gyara zamansa tare da
cewa.

“Yah Jameel Meyesa kake karyar mana da zuciya ne!?”.

Girgiza kai M Jameel Yayi tare da kallonsu wani irin tausayinsu da kuma ƙaunarsu na ratsa dukkan
zuciyarsa, bashi da wani ƙunci a rayuwarsa fiye da yadda ya kasance baya tare da Umminsa da ƙannensa
a inuwa ɗaya, ciwon sakin mace ba iya kanta kawai yake tsayuwa ba, har kan ƴaƴan data haifa yake
shafa.

Iska mai zafi ya fesar daga bakinsa kana yace.


“Ba karya zuciya bane Bashir burina ne, akan ku inaji kuma har yanzu akwai kason da ban idaba,

sabida ban zaɓawa Asma'u mijin aure a shine babban abinda yafi damuna sannan kai kuma kagama
makarantar ƙuruciya ce sai jami'a gidan kazo nazo”.

Numfashi yaja tare da fesarwa Idanunsa nakan Bashir yace.

“Acan ne ake samun tarbiyya daban-daban da halayyar al'ummar matasa kashi-kashi ina tunanin kada
ginin da mukayi nida Ummi wani yaje yayi yaɓe akai ya lalata kyakkyawan gini da kyakkyawan tubalin da
mukayi maka”.

Da sauri Bashir ya jujjuya kai tare da cewa.

“In sha Allah haka bazai faruba”.

Cikin jin sanyi yace.

“Bashir kayi min al'ƙawarin zaka kasance nagari, kayi min alƙawarin zaka kasancewa Ummi farin cikinta”.

Lokaci ɗaya hawaye suka cika idanun Bashir cike da tsoron kalaman Yayan nasa.

Cikin wata razananniyar murya ya kalli M Jameel da Idanunsa ke lumshe kana yace.

“Nayi maka al'ƙawari Yah Jameel Nayi alƙawari zan kasancewa Ummi ɗa nagari zan kasance me share
mata hawaye, zan kasance mai sata farin ciki idan Allah yayi duniya dan Manzo (S.A.W) ”.

A hankali ya ɗaga idanunsa tare da kallon Ummi da ta tsirawa M Jameel idanu cikin wani irin yanayi ko
ƙyaftawa bata yi ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.

“Zan kasance mai sata farin ciki, nayi alƙawari Ummi ba zata taɓa shiga ƙunci ko damuwa ba in dai a kai
nane in sha Allah”.

Ahankali M Jameel ya maida kansa jikin kushin ɗin ya jingina kana ya miƙe ƙafafunsa tare da riƙe hannun
Bashir aciki nasa kana ya cije lips ɗin sa.

Ummi kuwa wani irin sanyi jikinta da zuciyarta keyi cikin wani irin yanayi ta zubawa M Jameel Idanu.

Anutse M Jameel ya buɗe Idanunsa dake lumshe ya sauƙe akan Ummi Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da
furzar da iska daga bakinsa kana yace.

“Ummi ya dai kike kallona haka kamar na ƙarshe!?”.

Cikin saurin Ummi ta dafe ƙirjinta daya buga da ƙarfin gaske cikin raunin murya irin na wanda ke gab da
zub da hawaye ta kallesa karo na farko arayuwarta data fara kiran sunan sa tace.

“Haba haba Jamilu”.


Cike da mamaki ya ɗago idanunsa da suka sauya launi ya kalleta, Asma'u ma da sauri ta kalli Ummi haka
ma Bashir karo na farko kenan arayuwar su da suka ji Ummi ta kira M Jameel da sunan sa.

Ummi kuwa lokaci ɗaya wasu hawaye masu masifar zafi suka fara bin kuncinta Shar-shar.

Cikin yanayin tashin hankali M Jameel ya sauƙa tare da ƙara sawa gabanta ya durƙusa tare da riƙe
hannun ta cikin sanyin murya yace.

“Ummi kiya femin Ummina kiya femin kada ki zubar da hawayenki akaina Ummi me nayi miki!”.

Damƙe hannunsa Ummi tayi cikin raunin murya da alamun tashin hankali tace.

“Meyesa kake zuwa kake karya mana zuciya nida ƙannenka, kasani ayanzu kaine Inuwata kaine mafakar
da muke samu nida ƙannen ka muke fakewa. Meyesa wasu lokutan idan kazo kake min wasu maganganu
masu wuyar fahimta”.

Ta ida maganar hawaye nabin kuncinta.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da yin murmushi yayin da Idanunsa ke sheƙi kana yace.

“Toh Ummi inada ikon canza ƙaddarata ce? Idan son samu ne Ummi zan kasance me Kula dake har iya
ƙarshen numfashi na, kuma zan kasance me saki acikin farin ciki da walwala har numfashina na ƙarshe”.

Girgiza kai Ummi tayi still Hawaye nabin fuskarta tace.

“Ko yanzu ka sanya ni farin ciki duk kan wani farin ciki da jin daɗi ka bani shi Jamilu”.

M Jameel kuwa cike da mamaki ya ɗago Idanunsa dake jiƙe da ruwan hawaye yace.

“Ummi me kika ce?”.

Cikin Muryan kuka tace.

“Jamilu nace”.

Kallonta yayi cikin rawan murya yace.

“Ummi Meyesa?”.

Hawaye na zuba daga idanunta yayin da jikinta ke tsuma tace.

“Toh me zance maka? Kana tunanin bana jinka araina ne? Kana zaton bana jinka ajikina ne?
Ban taɓa ganin wani ɗa kafin kai bafa Jamilu, kaine ɗana na farko tsatsona, jinina, mallakina, kafin inga
Asma'u da Bashir da dai abu ya sameka a ace ina da ikon canza ƙaddara da zan dawo dashi kaina, domin
nasan ko bayan raina zaka kula da ƙannen ka fiye da yanda zan kula da su”.

Sauƙe ajiyar zuciya tayi tare da share hawaye masu zafin gaske da suka zubo mata kana tace.

“Kaga ma min komai Jamilu, kayi min komai Jamilu. Ubangiji Allah Yamaka albarka Allah Ubangiji ya rufa
maka asiri duniya da lahira Allah yasa kagama da duniya lafiya”.

M Jameel kuwa sake Matsawa jikin Ummi yayi tare da ɗaura kansa akan cinyarta hawaye masu zafin
gaske suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar.

Ganin haka yasa Asma'u dake gefe ita hawaye suka shiga bin kuncinsa.

Kusa da Asma'u Bashir ya matsa tare da sanya hannu ya shiga share mata hawayen cikin raunin murya
yace.

“Kiyi haƙuri Asma'u kada kiyi kuka kinga zaki ƙara karyarwa Ummi zuciya”.

Kai ta gyaɗa yayin da hawaye suka cigaba da zubowa daga Idanunta cikin sheshsheƙan Kuka tace.

“Ka gani fa Yah Jameel ma kuka ya keyi”.

Jin haka yasa M Jameel da Idanunsa ke jiƙe da hawaye ya ɗago kansa tare da sakar mata da murmushi
kana yace.

“Hmmm Asma'u kinsan meyake sani kuka?”.

Kai ta girgiza still Hawaye na bin kuncinta.

Lumshe Idanunsa yayi tare da taune lips ɗin sa kana yace.

“Kada kiyi kuka saboda ke baki da abinda zai saki kuka”.

Cikin sheshsheƙan kuka ta kallesa still hawaye na zuba daga Idanunsa cikin wata raunan'niyar murya
tace.

“Toh Yah Jameel me yake saka kuka Idan muna da iko zamu raba ka dashi”.

Girgiza kai yayi tare da rintse idanunsa kana yace.

“Ba zai rabu ba Asma'u tun tasowa ta aduniya bayan shekara goma sha huɗu bani da damuwar data
wuce ganin Ummi bata gidan mahaifina, hankalina yana tashi akan hakan, kuma ina tunanin hakane
badan faɗa da ƙaddararta ba, a'a saidai inajin maraici inajin kewar ta, inajin ciwon rashi mahaifiyata a
cikin gidanmu, ina so ko yaushe Idan na tashi naga Ummi kusa dani haka zalika idan zan kwanta ya zama
naje gareta taimin addu'a muyi saida safe”.

lumshe idonsa yayi yana mai jin wani irin yanayi azuciyar kana ya buɗe su tare da cewa.

“Ina so kafin naje na kwanta akowani dare in ganta kafin naje nayi bacci ina jin kamar nayi rashin komai
na duniya da Ummi bata kusa dani ina jin mai zan mata na sauƙe hakkinta na uwa akaina”.

Shafa kansa Ummi tayi still hawaye nabin fuskarta kana cikin raunin murya tace.

“Toh wai meye rage da bakayi min ba? Ka kaini Makka, Ka kai ni Madina ka gina min kyakkyawan muhalli
ka zuba min Kyakkyawan kayan ƙawa, ka riƙe cina shana suturata jinyata nawa dana ƙannen ka harma
mijin da nake tare dashi har maƙotan dake tare dani baka barsu sun zubda hawayeba kanai musu
dukkan abin buƙata”.

A hankali ta danne kukan dake ƙoƙarin sufce mata kana tace.

“Jamilu har maƙota nafa kagama yi musu komai”.

Murmushi M Jameel yayi still Hawaye na bin kyakkyawar fuskarsa kana yace.

“Har yanzu ban gama ba Ummi, sai dai ki tayani da addu'a Allah yasa in gama Allah yabani ikon
gamawa”.

Sai kuma ya maida kallonsa kan Asma'u dake zubda hawaye har zuwa lokacin take kuka kana ya maida
kallonsa ga Ummi yace.

“Ina Son inga na Aurar da Asma'u sannan inga Bashir ya zama babban mutum magidanci kafin wannan
lokacin Ummi *INA SON INYI AURE”*.

Cikin sauri Ummi ta ɗago Idanunta dake jiƙe da hawaye ta kallesa kana tace.

“Me kace Jamilu?”.

Ɗago kansa yayi tare da kallonta kana ya jinjina mata kai tare da cewa.

*“Ummi ina so inyi Aure”.*

Cike da mamaki Ummi ke kallon aranta tace tunda nake arayuwarta Jameel bai taɓa faɗa min magana
makamancin haka ba”.

Sake Kallonsa tayu akaro na barkatai kana tace.

Babana kaine? Kai da bakinka kake ce min kana so kayi Aure?”.

Jinjina kai yayi tare da faɗin.


“Ummi ina so inyi Aure in ɗaukeki ku dawo gidana dake da Malam sannan Asma'u da Bashir duk mu
zauna tare dasu duk sanda gari ya waye na dawo gidana in ganki Kusa dani mu zauna afalonki ki bamu
tea musha Idan dare yayi kafin na kwanta nazo na zauna afalonki ki bani Tea nasha”.

Sauƙe ajiyar zuciya yayi tare da lumshe idanunsa kana ya buɗesu tare da cewa.

“Sannan nayi hira da ƙanne na. Ina son haka Ummi shiyasa nake so nayi Aure Insha Allah Ummi zanyi
Aure zanyi Aure”.

Ummi kuwa cike da mamaki da kuma jin daɗin kalamansa tayi yalwataccen murmushi kana tace.

“Haka naka”.

Da sauri ya rufe idanunsa tare da cewa.

“Ummi ni ɗin?”.

Cikin shafa kansa tace.

“Eh kai ɗin, wato dan kana son ka sanarmin zakayi aurene, sai kabi ka kashe min jiki, ka zauna ka tasani
gaba harda kukanka, ko gaisawafa baka bari kunyiba, ashe du mgnar auren ce ke tsaburarka”.

Murmushi Asma'u da Bashir sukeyi cike da jin daɗi,

Shima M Jameel murmushi yakeyi tare da sunkuyar da kansa cike da alamun kunya.

Ita kuwa Ummi numfashin jin dadi ta fesar tare da cewa.

“Allah ya yarda Babana Ubangiji Allah ya nufa. Allah ya Al'barkanci rayuwar ka Allah ya nufa. Allah ya
rufa maka asiri Allah ya maka kyakkyawan tanadi agidan Aljanna ya kuma yima zaɓi da mace ta gari”.

Murmushi yayi cike da jin daɗin Addu'ar ta ya shafa sajensa tare da cewa.

“Ameen Ummina”.

Asma'u da Bashir kuwa dariya sukayi suna jin ƙaunar Yayan nasu, miƙewa yayi tare da yiwa Ummi
Sallama kana ya fice bayan tayi masa Allah ya tsare.

Kai tsaye gidansu ya nufa cikin nutsuwa yake Driving har ya isa gida bayan yayi Parking ya fito atsaye ya
hango Abbansa akan barandar sashen sa ya goya hannunsa abaya.

Ganin Abba yasa ya nufesa Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da kallon sa kana yace.

“Babana daga ina haka kake?”.


Langwaɓar da kai M Jameel yayi tare da sanyaya muryarsa kana yace.

“Abbah daga gidan Ummina nake”.

Numfashi Abbah ya fesar kana ya kalli agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa tare da cewa.

“Babana kalli fa yanzu ƙarfe sha ɗaya da rabi Meyesa baka tsoro ne”.

Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da kallon Abba kana yace.

“To Abba tsoron me Mutum zaiji, duk guduna fa bazan guji ƙaddarata ba haka zalika duk saurina
ƙaddarata ta fini sauri, kana duk hamzarina da kuma ɓuyana ƙaddarata tafini sanin inda nake”.

Jinjina kai Abba yayi kana yace.

“Duk da haka bana so Babana, duk inda kake indai ƙarfe sha ɗaya yayi ka kwana awajen, ba wani abin ni
na amince ma nasan ba baza kwana alalaceccen waje ba ko kuma inda zai jaza min magana”.

Cike da ladabi ya jinjina kai kana yace.

“Toh Abbana”.

Kansa Abba ya shafa yace.

“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ka Allah yatsareka da duk kan abinƙi”.

Murmushi yayi tare da faɗin.

“Ameen Abbana”.

Kana ya juya ya nufi ɗakinsa.

Acan gidan Lamiɗo kuwa Hajiya Aysha ce zaune da ƴaƴanta acikin falon su.

Ramadan dake zaune gefen Khausar ya ɗago kai tare da kallon ta kana yace.

“Addah Khausi ke kam kin huta da zuwa makaranta”.

Murmushi Khausar tayi tare da kallon Ramadan kana tace.

“Yanzu zan fara wani ai Ramadan”.

Ya mutse fuska yayi kana ya kalli Mommy dake zaune kan 2sitter yace.

“Mommy na”.

Ahankali Mommy ta ɗago kanta tare da cewa.


“Na'am Ramadan ɗina”.

Langwaɓar da kai yayi tare da marairaice murya kana yace.

“Ayyah Mommy am gobe abarni kar Inje makaranta mana”.

Kallonsa Mommy tayi tare da cewa.

“Toh Meyesa Ramadan?”.

Kai ya Girgiza kana ya marairaice murya tare da cewa.

“Mommy nidai kawai bana son zuwa Makarantar nan”.

Hankalinta ta mayar kansa kana tace.

“A'a Babana ba yadda za'a yi haka ace baka son zuwa makaranta. Ai yanzu ka fara zuwa ma”.

Araunace ya kalli Mommy tare da cewa.

“Dan Allah Mommy Gobe kawai.

Na goben nan dan Allah Mommy na kada Inje Mommy na goben nan kawai kada abarni Inje makaranta
kada inje”.

Girgiza Kai Mommy tayi cike da kulawa tace.

“A'a Ramadan ya za'a yi inbarka ba kaje makaranta ba ai bazai yuwu ba dole ne kaje makaranta kam”.

Jan zuciya yayi tare da dafe kuncinsa kana yace.

“Mommy shikenan kin yarda in tafi?”.

Jinjina masa kai tayi tare da cewa.

“Na yarda mana kaje”.

Miƙewa yayi daga wajenta ya koma kusa da Khausar tare da riƙe Hannunta cikin yanayin roƙo ya
langwaɓar da kai tare da marairaice murya yace.

“Addah Khausy ki tayani bawa Mommy haƙuri gobe kada Inje makaranta kice tabarni gobe kar Inje
makaranta mu zauna da ita bana son zuwa makarantar nan Addah Khausi bana so ki faɗawa Mommy”.

Khausar kuwa Kallonsa ta riƙa yi har ya kai ƙarshe, ajiyar zuciya ta sauƙe tare da riƙe tafin hannunsa
acikin nata kana tace.

“Toh Ramadan tun daga yanzun ka kana primary 3 sannan kace bakason zuwa makaranta Primary mafa
yanzu kayi rabin gamawa ai Ramadan ka fara da wuri”.
Araunace Ramadan ya kalleta tare da cewa.

“Yanzu Addah Khausi zaki bari inje”.

Cikin rashin ɗaukar maganarsa da muhimmanci Khausar tace.

“Eh Sosai ma”.

Haiydar dake kwance kan 3sitter ya ɗago kansa tare da kallon Ramadan kana yace.

“Eh dolenka. Dolenka ma kaje”.

Sai kuma ya maida kallonsa kan Mommy dake kallon Ramadan kana yace.

“Allah Mommy Idan aka sakewa Ramadan ma bazai yi karatu ba”.

Tura baki Ramadan yayi tare da sake hannun Khausar ya koma jikin Mommy kana yace.

“Mommy ki faɗa masa ƙoƙarin da nake a hadda ai yasani ko.

Gasa akaje ni nake zuwa mana na ɗaya a sate ɗin mu”.

Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa.

“Na sani Ramadan kana ma da kokari kawai dai da kake cewa kar abari kaje gobe abarka ka hutane bai yi
ba. Idan ka tuna ma gobe Laraba ne idan kaje gobe jibi Alhamis zaka huta gata Friday shima zaka huta
kaji ko Ramadan”.

Girgiza kai yayi still Idanunsa akan Mommy yace.

“Ayyah Mommy ni Banason zuwa ki barni mana”.

Khausar ne ta kallesa cike da mamaki tace.

“Ohh Ni Khausar yau kam naga ikon Allah da nacin yaro”.

Taɓe baki Haiydar yayi tare da cewa.

“Rabu dashi duk zai gama kuma dole gobe sai yaje makaranta”.

Acan Bedroom ɗin Hajiya Bunayya kuwa kwance take akan makeken gadonta daya ji shimfiɗa na alfarma
kana kunnenta maƙale da babbar waya ta gyara kwanciyarta tare da cewa.

“Nama gama ɗaukar wannan matakin in Allah ya yarda in dai wannan anyi angama ya wuce Babban
shima Insha Allah za asan abinda za'a yi akai”.
Daga ɗaya ɓangaren Hajiya Lami dariya tayi kana tace.

“Da dai yafimiki in ba Haka ba kina gani ƴaƴan ki zasu zama bayi, dan da zaran sarautar nan ta fita
ahannun ku kinyi bankwana da ita ƴaƴan ki kuwa sun zama tamkar ba ƴaƴan Sarauta ba, duk da cewa
Masarautar ba wata babba bace ai baka so ya wuce kaba ya fita ahannunka!”.

Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta sauƙe kana tace.

“Hakane”.

Murmushi Hajiya Lami tayi tare da faɗin.

“Kinga ai Gimbiya Fadeela ta cikin Taraba Aminiya tace duk iya ƙoƙari tanayi dan ganin sarauta ya zauna
ahanununta ke kanki kinsani ai ina faɗa miki saboda iya na cinka iya samun abin ka”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Hakane ai ma duk na gama shi in faɗa miki”.

Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauƙe kana tace.

“Ai haka yafi kam kada ki tsaya kallon ruwa kwaɗo ya miki ƙafa”.

Dariya Hajiya Bunayya ta sheƙe dashi kana tace.

“Kede ki bari zaki sha kallo”.

Hira suka sake taɓawa daga haka Hajiya Bunayya ta katse kiran.

Washe gari.

Da safe baki ɗaya yaran aka shirya su cikin Uniform Bayan Khausar ta gama shirya Ramadan cikin
Uniform ɗin sa tamiƙe ta shiga kichen dan ɗauko masa Lunch box ɗin sa.

Ramadan kuwa yana ganin fitan cikin sanɗa ya fice daga sashen nasu zuwa sashen Hajiya Bunayya ya
ɓoye.

Khausar kuwa kai tsaye Bedroom ɗin su ta nufa bakinta ɗauke da Sallama Cak ta tsaya ganin Ramadan
bai ciki ƙara sawa ciki tayi tare da kiran sunan sa amma shiru toilet da Wadrope ta buɗe still baya ciki.

Cikin sauri ta fito tare da nufar Bedroom ɗin Mommy kana ta kalli Mommy dake zaune gefen gado tace.
“Mommy na gama shirya Ramadan da Raudat kuma ga Raudat amma banga Ramadan ba har munje
wajen mota bamu gansa ba”.

Miƙewa Mommy tayi tare da cewa.

“Ikon Allah to ina kuma yashiga?”.

Buɗa hannu Khausar tayi da faɗin.

“Allahu A'alam”.

Falon suka fito tare da duba ko ina amma baya nan.

Kallon Khausar dake leƙa bayan Kushin Mommy tayi kana tace.

“Khausar jeki duba ɗakin Haiydar ko yaje ya ɓuya acan yau, Bansan meke damun Yaron nan ba tun jiya
baya so ayi masa batun zuwa makaranta abinda bai taɓa yi ba”.

Taɓe baki Khausar tayi kana tace.

“Iyayi mana Mommy daga anyi masa wasa shikenan ya ɗauka”.

Ta ida maganar tare da fita zuwa ɗakin Haiydar.

Abakin ƙofan ta tsaya tare da ɗan ɗaga sautin Muryanta kana tace.

“Ramadan kafito fa?”.

Shiru ba amsa jin haka yasa ta buɗe ƙofar ɗakin tashiga shiru ba kowa da mamaki take kallon ko ina dake
kimtse tsaf har toilet ta ɓude still baya ciki siririn tsaki taja tare da ficewa ta koma sashen Mommy.

Ƙugunta ta riƙe da hannu ɗaya kana ta kalli Mommy dake tsaye tace.

“Mommy ban gansa ba fa”.

Girgiza kai Mommy tayi tare da faɗin.

“Toh kije ki duba sashen Ummanku ko yaje ya ɓuya acan kinsan itama zata iya ɓoyesa”.

Kai Khausar ta gyaɗa kana ta juya ta fice.

Bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon zune ta samu Hajiya Bunayya akan 1sittee.

Kallon ta Khausar tayi tare da cewa.

“Ummah Ramadan yazo nan?”.


Murmushi Hajiya Bunayya tayi tare da gyaɗa kai kana tace.

“Eh gashi nan yazo ya ɓuya wai yau baya son zuwa makaranta”.

Ƙwaffa Khausar tayi kana tace.

“Aikuwa dole sai yaje”. ta faɗa tare da wuce Bedroom Kana tace.

“Wallahi Ramadan kafita idona”.

Jin muryan Khausar yasa Ramadan miƙewa tare da hawa can karshen gadon Hajiya Bunayya kana ya
ɗaga sautin muryansa tare da cewa.

“Dan Allah Ummah ki hanasu kice yau dai kawai subarni kada Inje makaranta”.

Murmushi Hajiya Bunayya tayi tare da haɗa hannunta biyu waje ɗaya kana tace.

“Dole sai kaje maza ka fito ka tafi nikam kasan bazan hanaka zuwa makaranta ba, Ramadan dole zaka
je”.

Dai-dai lokacin Sulaiman ya fito tare da faɗin..

“Ikon Allah yau Ramadan da kanka kake cewa baka son zuwa makaranta duk ƙoƙarin kan nan?”.

Shi dai bai ce komai ba Khausar na ƙoƙarin za gayawa gefen gadon ta riƙo sa yayi saurin ɗirƙa ta ɗaya
side ɗin gadon ya fice waje da gudu.

Dafe kai Khausar tayi tare da bin bayansa yana cewa.

Ramadan kazo mu tafi Sulaiman duk sun shiga mota saura kai ka ɗai ake jira”.

Shi kuwa Ramadan sashen Mommy ya nufa da gudu yana shiga ya ɓuya abayan Mommy.

Muryarsa na rawa tamkar wanda ke shirin fashewa da kuka yace.

“Mommy dan Allah kar inje”.

Hararansa Mommy tayi kana tace.

“Sai kaje Meyesa ba kason zuwa Ramadan ka faɗa min dalili”.

Rau-rau da idanunsa yayi kana yace.

“Ni dai bana so bazan jeba Mommy”.


Dai dai nan Khausar ta shigo kansa ta nufa tare da miƙa hannunta da niyyar kamasa tayi saurin damƙe
maranta tare da rintse Idanunta kana tace.

“Wayyo Allah na!”.

Cike da kulawa Mommy ta kalleta tare da cewa.

“Yau kuma ciwon cikin ki ko?”.

Kai ta gyaɗa mata cikin sanyi murya ta kalli Ramadan kana tace.

“Ramadan kazo mana kai kaɗai fa ake jira”.

Maƙale kafaɗa yayi dai-dai nan suka jiyo hong ɗin mota cikin sanyin murya Khausar tace.

“Mommy kin jifa shi kaɗai ake jira zasuyi letti fa Allah zaija idan sunje azanesu kinsan, Moddibo ba
ruwansa ko yara sawa yake aci ƙaniyarsu!”.

Ta ida magansr tare da miƙa hannu da niyar janyo sa.

Cikin sauri Ramadan ya sake Matsawa baya tare da riƙe ƙafafun Mommy tare da fashewa da kuka kana
cikin raunin murya yace.

“Mommy dan Allah kice abarni ni dai yau bana son zuwa makaranta bana so Mommy dan Allah ki barni”.

Mommy kuwa Kallonsa tayi lokaci ɗaya taji jikinta yayi masifar sanyi janye ƙafafunta tayi tare da Kallonsa
kana tace.

“Kai Ramadan wai meyesa bakason zuwa makarantar?”.

Cikin kuka sosai yace.

“Ayyah Mommy dan Allah yau ɗin nan kaɗai ki barni kada Inje makaranta nafi so yau In wuni ina kallonki
kina kallona”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“Ramadan kaje yau kaga gobe idan Allah yakai mu Alhamis ne baza kaje makaranta ba zamu wuni agida
juma'a ma zamu wuni tare kaga har Asabar ma baza ka jeba”.

Girgiza kai yayi still hawaye na bin Fuskarsa yace.

“Mommy ni dai bana so”.

Miƙewa Khausar tayi tare da kama hannunsa tana jansa shima hannun Mommy ya riƙe yana kuka
Khausar na jansa yana jan Mommy da ƙar ta fincike sa suka fita kana ta sanya shi amota tana kallon
Haiydar dake hararan Ramadan tace.
“Gashi ku tafi”.

Kana ta juya ta koma ci.

Da yake shi Haiydar haddan safe suke zuwa na maza.

Kusa da Mommy ta zauna tare da riƙe mararta tana yarfe hannunta kana ta runtse Idanunta tare da
faɗin.

“Wayyo Cikina ciwo Mommy!”.

Mommy kuwa jikinta ne yayi sanyi kallon Khausar dake riƙe da marar ta tayi tare da cewa.

“Ke tashi kijeki ɗauko min Yarona, bana so yau abar minshi kada yaje makarantar nan, tunda tun jiya da
daddare yake Matsawa kada abarshi yaje nima raina baya so kawai abarshi ya dawo yafi min tashi ki
ɗauko min ɗana”.

Ahankali Khausar ta ɗago tare da kallon Mommy kana cikin sanyin murya tace.

“Ayyah Mommy cikina ya kama bazan iya ba kuma Mommy meyesa zaki biye mishi?”.

Girgiza kai Mommy tayi tare da cewa.

“Khausar naji kawai bana so ya tafi ɗauko min shi”.

Dai-dai lokacin kuma suka ji Girinirin alamun an rufe gate Kallon Mommy Khausar tayi kana tace.

“Toh Mommy kin jin anrufe gate sun tafi”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da lumshe Idanunta kana tace.

“Toh shikenan Allah ya tsare Allah ya dawo dashi lafiya”.

Khausar kuwa Ameen tace tare da kwanciya akan 3sitter still Hannunta na dafe saman maranta.

Kallonta Mommy tayi cike da kulawa tace.

“Yau kuma cikin ki yau nawa ga wata ne?”.

Ahankali Khausar ta buɗe Idanunta tare da cewa.

“Yau Sha biyar Mommy”.

Jinjina kai Mommy tayi kana tace.

“To aima kusan saura kwana huɗuma Period ɗinki yazo date ɗin da saura?”.
Kai Khausar ta gyaɗa tare da matsa saman maranta kana tace.

“Eh Mommy haka dama yake min kafin kwanakin su cika yana min yawan ciwon ciki”.

Numfashi Mommy ta fesar kana tace.

“Allah dai ya sawwaƙa kije ki haɗa ruwan zafi da zuma kisha”.

Ahankali Khausar ta motsa laɓɓanta tare da faɗin.

“Toh”.

Kana ta yunƙura zata tashi tayi saurin komawa saboda yanda cikin ya murɗa.

Ganin haka yasa Mommy ta miƙe tare da zuba mata Zuma da ruwan zafi akofi ta kawo mata amsa tayi
tasha tare da gyara kwanciyar ta akan kujeran tana jin ciwon na sauƙa ahankali Mommy kuwa zaman ta
ta gyara akan kujeran tare da lumshe Idanunta...

Acan mota kuwa bayan sun isa bakin makarantar Amina dake baya ta kalli Driver tare da cewa.

“Malam Habu ka sauƙe su ba sai mun shiga cikin gate ba sai ka wuce ka kaini unguwar Waziri gidansu
Samira Sani”.

Anutse Malam Habu ya juya ya kalleta kana yace.

“In dai shigar dasu kinga Yara ne ba zasu iya tsallaka wa daga kan titin nan ba bare yanda motoci suke
wucewa”.

Wani kallon ta watsa masa tare da cewa.

“Yau suka fara zuwa makarantar kuma ga Haiydar ai zai riƙe su”.

Kai Malam Habu ya gyaɗa tare da sauƙe su kana yaja motar ya tafi.

Haiydar kuwa juyawa yayi tare da ɗaukar Raudat kana ya juya da nufin zai riƙe hannun Ramadan kawai
ya hangosa Atsakiyar titin Aminu kuwa tuni ya tsallaka.

Kamar daga sama wata baƙar mota jeep ta taho aguje.

Cikin tsananin tashin hankali da ruɗu Haiydar yace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Ramadannnn”.

Motar kuwa da mugun gudu tazo tare da nufar kan Ramadan...!


*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a
kanki littafin 1k ne 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta
WHATSAPP 09097853276*

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._
sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,
😘

*By*

*GARKUWAN MARUBUTA*

SAKAYYA

23

*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son
k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman
lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun
matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa
ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki
tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones
dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da
tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da
ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda
ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya
wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka
kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki
da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp
in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta,
muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina
nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a
ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.

0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta
wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije
gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.

GARKUWAR MA'AURATA

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta, cikin Aminci domin ko kin gashi a wasu wuraren
toh na satane na Allah ya isane, Yaseen kuwa wlh na Allah ya isan ne duk ƙanƙatar haƙƙina ban yafeba,
yake yar uwa mai tsoron Allah da kikaye haƙin wani ki biya 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU
GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, sai in saki a Group ɗin, ku kuma
masu fitar da littafina ki da Allah, Allahu Rabbi ya isarmin wahalata da nasha kusan tsawon shekara ina
rubutu. Dan ki biya 1k kudin karatu kike fitarwa mutun sama da ɗari, toh yadda kika tozarta min
kasuwanci ne kema Allah ya haɗaki da mai miki fiye da abinda kikayi min, kuma ki sani wlh ban yafeba*

23

Gaban motar ne ya bugi Ramadan, kamar gilmawar walƙiya ya faɗi agefen kwaltan.

Akuma dai-dai lokacin motar Moddibo da M Jameel ya tsaya awajen cikin sauri M Jameel ya buɗe motar
tare da fita yana cewa.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”. kana ya nufi inda Ramadan ke kwance.

Moddibo kuwa kansa ya dafe tare da rintse idanunsa.

Akuma dai-dai lokacin Malam Isa,Malam Ahmad da malam Sa'id suka ƙara so Kasancewar lokacin ne
Malamai suka fara zuwa wasu ma ko Parking basuyi ba.

Motar daya bige Ramadan kuwa ko tsayawa bai yiba ya ɗiba aguje.

Aminu kuwa cikin tsoro da tashin hankali ya juya tare da kallon Ramadan dake kwance yayin da M
Jameel ke tsugunne kansa zuwa lokacin tuni Ramadan ya suma ɗagosa M Jameel yayi tare da ɗan buga
kuncinsa yana cewa.

“Ramadan! Ramadan!!”.
Amma ko motsa wa baiyi ba alamar babu nunfashi atare dashi.

Cikin sauri Malam Arɗo ya fito daga cikin makaranta kasancewar ɗaya daga cikin Malaman yashiga ya
sanar masa an samu hatsari awaje.

Moddibo kuwa cikin sauri yayi wa motar key tare da ƙoƙarin bin bayansu ganin basu da niyyar tsayawa
yana ƙoƙarin gilmawa M Jameel ya ɗaga masa hannu tare da faɗin.

“A.J ka tsaya mu ɗauke sa mu kaisa asibiti”.

Jin haka yasa Moddibo fasa bin bayan motar kana ya tsirawa bayan motar Ido ya tsaida ganinsa kan
number burki ya taka.

M Jameel kuwa cikin sauri ya ɗauko Ramadan ya sanya shi cikin motar ya tada suka nufi asibiti, Malam
Arɗo kuma motar Malam Isa suka shiga tare da kallon sauran Malaman dake tsaye kana yace.

“Malam Isma'il ku shiga ciki”.

Kana Malam Isa yaja motar suka tafi.

Haiydar kuwa har zuwa yanzu ya kasa buɗe Idanunsa saboda tsananin tsoro da tashin hankali ji yake
yana buɗe idanunsa zai ga ƙwaƙwalwar Ramadan abaje akan kwalta hakan yasa ya runtse Idanunsa kana
ya sanya hannunsa duka biyu ya dafe kansa yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinsa ke rawa.

Raudat kuwa kuka take tamkar ranta zai fita yayin da take yarfe hannunta tare da bubbuga ƙafarta tana
cewa.

“Wayyo Ramadan ina za ku kaisa Meyesa mesa Wayyo Ramadan ɗina!”.

Malam Isma'il ne ya ƙara so kusa da Haiydar tare da riƙe hannunsa ganin yanda jikinsa ke rawa kana
yace.

“Haiydar buɗe idon ka”.

Girgiza kai Haiydar yayi still cikin Muryan kuka yace.

“A'a tsoro nakeji in buɗe ido na inga ƙwaƙwalwan Ramadan akan kwalta”.

Girgiza kai Malam Isma'il yayi tare da cewa.

“Babu komai babu abinda ya sameshi beji ciwo ba motar ce ta bigesa ya koma gefe amma bata bi ta
kansa ba!”.
A hankali ya buɗe Idanunsa da sauri kuma ya sake ware su ganin babu kowa sannan Ramadan ma baya
nan cikin rawan murya ya kalli malam Isma'il tare da cewa.

“Ina Ramadan ɗin?”.

Kallon titin Malam Isma'il yayi tare da faɗin.

“Malam Jameel da Moddibo sun tafi kaishi asibiti sannan Malam Arɗo yabi bayansu yanzu kutafi cikin
makaranta ka kwantar da hankalinka kaji?”.

Girgiza kai Haiydar yayi yace.

“Ya za'ayi kace in kwantar da hankalina kansa yafashe ko?

ya karye ko? Ko dai ya mutu ne?.

Cikin sa ya fashe ko? Kan kare sa akayi akwalta ko!?”.

Duk alokaci ɗaya ya jero masa tambayar.

Girgiza kai Malam Isma'il yayi kana yace.

“Wallahi babu abinda ya sameshi kawai dai tsoro ne idan mutum bai taɓa accident ba dole tsoro zai sa
ya suma kaje kashiga cikin makarantar maza kushiga ciki”.

Dai-dai lokacin kuma ɗalibai suka fara zuwa cikin rarrashi Malam Isma'il yace.

“Ku shiga ciki”.

Raudat kuwa kuka ta riƙa yi tana yarfe hannu tsugunna wa Malam Isma'il yayi ya ɗauketa suka shiga
cikin makarantar kana ya shiga bawa Haiydar ƙarfin guiwa.

Acan ɓangaren su M Jameel kuwa suna isa Hospital ɗin aka karɓi Ramadan tare da kaisa Emergency
Room.

Atake aka fara bashi temakon Gaggawa kasancewar akwai ƙwararrun Likitoci cikin ikon Allah beji wani
rauni ba sai karaya daya samu aƙafarsa na hagu.

Cikin mintunan da baza su gaza talatin ba ya farfaɗo tare da fashewa da kuka kana ya buɗe Idanunsa
tare da cewa.

“Wayyo ƙafata Addah Khausi Ƙafata, Wayyo Addah Khausi Ƙafata”.


Ahankali Moddibo dake gefensa ya matsa tare da riƙe hannunsa kana yace.

“Sorry Ramadan kayi haƙuri kayi shiru kaji”.

Cikin kuka sosai Ramadan ya kallesa tare da cewa.

“Mommy na Malam akaini wajen Addah Khausi.

Ina Addah Khausi na Ƙafata ciwo yake min zafi?”.

Ya ida maganar yana jujjuya kai yayin da gaba ɗaya zufa ya wanke masa ilahirin jikinsa Musamman
saman goshin sa amma babu hawaye a Idanunsa yayinda ƙafansa ya sake kamar roba ya langwaɓe.

Cike da rarrashi da kuma tausayawa Moddibo yace.

“Kayi haƙuri zai daina insha Allah”.

M Jameel kuwa magunguna da abubuwan da za'ayi ɗauri Dr ya rubuta masa kana ya ya fice tsaye ya
samu malam Arɗo maƙale da waya akunnen da alama da Lamiɗo yake magana.

Cikin yanayin jimami ya gyara zaman wayar akunnensa tare da cewa.

“Wallahi kuwa akwai yaron wajenka da mota ta ɗan kuskuresa yanzu haka ma muna asibiti”.

M Jameel ne ya gyara tsayuwar sa tare da harɗe hannunsa aƙirji kana ya lumshe idanunsa.

Cikin sauri Malam Arɗo yace.

“A'a ka kwantar da hankalin ka Mai Martaba baiji wani ciwo ba.

Dan Allah dan Annabi ka kwantar da hankalin ka”.

Ganin Malam Arɗo ya katse kiran yasa M Jameel cewa.

“Malam wai batun ɗauri ne ƙafarsa ta karye to yanzu ance za'a yi masa ɗauri”.

Jinjina kai Malam Arɗo yayi kana suka fita da M Jameel.

A can Gidan Lamiɗo kuwa tun bayan tafiyarsu Ramadan Makaranta Mommy ta kasa miƙewa taje ta
gyara ɗakin mijin nata.

Duk da kuwa cewa itace da girki baki ɗaya jikinta Asanyaye yake bata da wani kuzarin kirki yayin da
Khausar ke kwance gefenta har zuwa lokacin hannunta na dafe da maranta.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da furzar da iska mai zafi daga bakinta kana ta yunƙura da niyyar
miƙewa dai-dai lokacin Lamiɗo ya shigo bakinsa ɗauke da sallama.

Yana shiga idanunsa akan Mommy tare da cewa.

“Aysha!, Aysha”.

Cikin sanyin murya da mutuwar jiki Mommy tace.

“Na'am”.

Sai da yayi ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa tare da cewa.

“Zo muje ki rakani?”.

Kallon Mamaki Mommy tayi masa tare da faɗin.

“Ina zamu je?”.

ƙasa yayi da kansa kana yace.

“Ke kam zoki rakani wani waje mana”.

Atake zuciyarta ya tsinke ƙirjinta ya buga da masifar ƙarfi kana tace.

“Rakiya kuma ina kuma zamuje. Mai Martaba ka faɗa min?”.

Ta ƙara sa maganar tare da kallon ƙwayar idanunsa da take iya hango tsantsar tashin hankali da
damuwa.

Cikin rawan murya tace.

“Meyesa mu Ramadan”.

Jin abinda tace yasa Khausar dake kwance tayi saurin miƙewa Atake Idanunta suka cika da ruwan
hawaye lokaci ɗaya tsoro ya rufeta!.

Cikin dakiya Lamiɗo yace.

“Babu Abinda Ya samu Ramadan ke kam zoki rakani”.

Cikin yanayin sadaukar wa Mommy ta kallesa kana tace.

“Dan Allah ka faɗa min Meya samu Ramadan ɗina!”.


Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da cewa.

“Kizo mu tafi mana”.

Miƙewa Khausar tayi cikin rawan murya dan tuni hawaye suka wanke mata fuska kana tace.

“Dan Allah Abba inzo mu tafi”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.

“Eh”.

Cikin sauri ta sanya dogon hijabinta dake fitar da sanyayyan ƙamshin ta fita, shima Lamiɗo fita yayi
sashen Hajiya Bunayya ya nufa yana kirata kasancewar shi kansa be san waya samu hatsari acikin ƴaƴan
nasa ba Haiydar, Aminu, ko Ramadan.

Mota suka shiga Khausar na gaba Lamiɗo Gimbiya Bunayya da Mommy suna baya.

Lokaci ɗaya hankalin Mommy ya sake tashi ganin sun nufi hanyar asibiti cikin tsanananin tashin hankali
tace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n dan Allah Mai Martaba ka faɗa min me yasamu Ramadan ɗina?”.

Girgiza kai yayi tare da kallonta kana yace.

“Nima kaina ban sani ba Aysha babu yanda muka iya da hukuncin Ubangiji”.

Hajiya Bunayya kuwa ƙasa tayi da kanta cikin tsananin farin ciki da jin daɗi ta saki murmushi aranta tace
Alhamdulillah burina ya cika in. Allah ya yarda yau ankawar min da Haiydar da Ramadan na huta dole
inƙara musu kuɗi me tsoka yanda zasuji farin ciki na kawar min da ƴaƴa biyu maza ɗin nan shikenan Mai
martaba bashida wani ɗa Namiji sai Aminu dole Aminuna shi zai gaji sarauta.

Ahankali ta ɗago kanta Idanunta cike taf da ruwan hawaye ta kalli Lamiɗo tare da cewa.

“Innalillahi Wa'inna ilahi rajiu'n. Mai martaba mai yafaru?”.

Cikin yanayin damuwa yace.

“Ni kaina ban sani ba ance min dai ɗana Namiji ne amma ban sani ba Aminu ne...”.

Aruɗe Hajiya Bunayya tasa hannu ta dafe ƙirjinta tare da cewa.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ɗaya-ɗayan nawa”.

A hankali ya fesar da iska daga bakinsa kana yace.


“Kuma ban sani ba ko Haiydar, ko Ramadan ne ban sani ba sai mun shiga”.

Mommy kuwa lumshe Idanunta tayi tare da faɗin.

_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan min ha”_.

Suna isa suka fito bayan Driver Yayi parking Malam Arɗo na ganin Lamiɗo yayi saurin miƙewa tare da isa
inda suke kana yace.

“Sannunku da zuwa Mai Martaba”.

Khausar kuwa tun da suka fito take kuka baki ɗaya jikinta ya gama bata Ramadan ne kuma ya rasune.

Batare da Lamiɗo ya amsa Barka da zuwan da yake masa ba yace.

“Acikin ƴaƴana waye ne yasamu hatsarin?”.

Malam Arɗo ya gyara tsayuwar sa tare da cewa.

“Ƙaramin ne”.

Ƙasa daure wa Khausar tayi kuka ta fashe dashi tare da faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Mommy Ramadan ne,

sai da yace kada yaje makaranta yau kawai abarshi kada yaje kamar yasan me zai faru dashi na nace dole
na muka turashi”.

Mommy kuwa kasa daure wa tayi hawaye masu zafi suka shiga zubo mata.

Dai dai lokacin M Jameel ya dawo daga sayo magungunan a Pharmacy dake cikin Hospital ɗin.

Kallon Malam Arɗo Lamiɗo yayi kana yace.

“Ku kaimu ciki”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare dayi musu Jagora kasancewar Mai matarba ne da iyalansa yasa aka barsu
suka shiga.

Suna Shiga idanun Khausar ya sauƙa akan Moddibo dake Rungumeta da Ramadan yana lallashinsa.

Ramadan na kallonta ya fashe da sabon kuka tare da cewa.

“Adda Khausi ƙafata Addah Khausi zoki riƙe min ƙafata”.


Kallonsa ya mayar kan Mommy tare da cewa.

“Mommy ancire min ƙafata ko? Bana jinta a jikina”.

Sai kuma ya kalli Lamiɗo daya zuba masa Idanu cikin matsanancin kuka yace.

“Abbah Ƙafata, Ƙafata”.

Kallonsa ya mayar kan Hajiya Bunayya ya langwaɓar da kai amma baice komai ba.

Hajiya Bunayya kuwa kallon Moddibo tayi jikinta na tsuma tace.

“Ina Haiydar kadde shi yana mutuware?, Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.

Ido Moddibo ya zuba mata tare da tsaida idanunsa acikin nata abinda ba ɗabi'arsa bace ba kuma
al'adarsa bace haɗa ido da mutum amma haka nan ya tsinci kansa da tsaida idanunsa akan matar yana
kuma nazartan ta.

Cikin yanayin ɓacin rai M Jameel ya juya ya kalleta tare da cewa.

“Haba Hajiya wannan wani irin kalma ne ya za ayi kice yana mutuware?”.

Hannu tasa tare da share hawayen fuskarta kana tace.

“To ina yake? Ina Haiydar Allah sarki babban ɗan mu wanda zai gaji Mahaifinsa a sarauta Wayyo
Haiydar”.

Malam Arɗo da shigowarsa kenan ya kalleta tare da cewa.

“Haiydar na nan lafiya yana makaranta yana karatu kana suna cikin kulawa!”.

Da sauri Ta haɗiye wani abu mai masifar ɗaci tare da cewa.

“Toh Ina Aminuna?”.

Cike da kulawa malam Arɗo yace.

“Shima yana cikin ƙoshin lafiya wannan ne kaɗai Accident ɗin ya faru dashi”.

Lokaci ɗaya wani masifaffen ɓacin rai da baƙin ciki ya mamaye zuciyarta cikin ranta tace Haiydar bai
mutu ba sannan shima wannan karayane ka ɗai?”.

Tsaban zancen zuci dake cinta saida kalmar Karaye ne kaɗai ya fito fili.
Atare Khausar da Moddibo suka kalleta jin abinda tace wannan ɗin ma Karaye ne kaɗai Moddibo ya
maimaita kalmar Aransa.

Khausar kuwa kwallon ta tayi tare da tsareta da ido tana sake maimaita kalmar aranta.

Malam Arɗo ya kalli Lamiɗo tare da cewa.

“Mai Martaba karaya yasamu dama akan za'a yi masa ɗauri ne saboda Andu basa gaba ɗaya baiji wani
ciwo ba Karayane da Allah ya ƙadarta toh insha Allah yanzu za'a yi masa ɗauri”.

Jinjina Kai Lamiɗo yayi tare da cewa.

“Mun gode Allah ya saka da alkhairi”.

Cike da damuwa Malam Arɗo yace.

“Dan Allah kayi haƙuri akasani ne, tsautsayi aka samu wanda baya wuce ranan sa mai motar kamar da
gayya yayi ko tsayawa bai yiba ya gudu baki ɗaya abin yazo da akasani ne bamu taɓa samun irin wannan
akasin abakin makarantar ba”.

Girgiza kai Lamiɗo yayi tare da cewa.

“Bakomai Malam Arɗo ai babu yanda muka iya da ƙaddara ko agadon Mahaifiyarsa yake idan Allah ya
ƙadarta zai karye dole ya karye Waman Ƙadarallahu Haƙƙa ƙadrihi”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa tare da cewa.

“Haka ne kam”.

Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe tare da faɗin.

“Amma bana son ɗaurin asibiti zamu koma dashi gida ayi masa na Gargajiya”.

Jingina kai Malam Arɗo yayi tare da cewa.

“Toh shikenan Babu matsala”.

M Jameel ya Kalli Ramadan cike da tausayawa kana yace.

“Toh Mai Martaba Allah ya ƙara sauƙi”.

Kana ya miƙa masa ledan maganin daya sayo yace.

“Gashi magunguna ne na rage zugi da zafin ciwo koda ɗaurin gidan za'ayi masa za ayi amfani dasu”.

Karɓa Lamiɗo yayi tare da faɗin.


“Toh angode”.

Kana ya sanya hannu acikin aljihu ya ciro wayarsa tare da kiran number Malam Bala mai ɗauri.

Katse wayar yayi bayan sun gama mga, juyawa yayi ya kalli Hajiya Bunayya da Mommy kana yace.

“Mutafi to”.

Sai kuma ya juya ya kalli Khausar dake kuka hadda sheshsheƙa yace.

“Haba Addah Khausi kiyi haƙuri mana ai sai ki ƙara tayar masa da hankali shi yana kuka yana kiran ki
sannan kema kina kuka ki bashi ƙarfin gwiwa mana”.

Kai ta gyaɗa tare da Matsawa kusa dashi still Moddibo na riƙe dashi bakin gadon ta ƙara sa Moddibo
kuwa saurin lumshe idanunsa yayi.

Ita ko Khausar cikin kuka ta kalli Ramadan tare da cewa.

“Kayi haƙuri Ramadan da mun sani da baka je makarantar nan ba tun jiya kake cewa baza kaje ba kana ta
roƙon Mommy kada kaje”.

Kallonta ta mayar kan Mommy tare da faɗin.

“Dan Allah Mommy duk sanda yaron nan ya sake cewa ba zaije makaranta ba kada abarshi yaje tun jiya
yake ta roƙo yau ɗaya abarshi ya huta kamar yasan abinda zai faru dashi”.

Kasa cewa komai Mommy tayi ɗan ita kaɗai tasan yanda zuciyar ta ke mata.

Khausar kuwa ahankali ta tsugunna akan Ramadan ganin yanda goshinsa ke tsats-tsafo da zufa ta ɗago
lallausan tafin hannunta tare da mannawa agoshin sa ta yarfe masa zufan.

Ahankali Moddibo ya tsirawa tafin hannunta Idanu cikin wani irin yanayi sannu Ahankali tsikar jikinsa ya
fara tashi lumshe idanunsa yayi kana ya tuna lokacin da Amafarki ta sanya Lallausan tafin hannunta tana
shafa Sajensa, ɗan juya hannunta ya buɗe Idanunsa da suka sauya launi tare da kallon hannunta yanda
take shafa goshin Ramadan ɗin cikin nutsuwa yasa yaji wani abu mai masifar ƙarfi ya tsirga masa tun
daga kan yatsan ƙafansa har zuwa ƙwaƙwalwar kansa lokaci ɗaya... ɗin sa ya harba da ƙarfin gaske cikin
sauri ya cije lips ɗin sa tare da lumshe idanunsa yana kiran Sunan Allah Aransa.

M Jameel ya juya ya Kalli Moddibo da Idanunsa ke lumshe kana yace.

“Mu tafi ko?”.


Kai ya gyaɗa tare da yunƙurawa ya ɗauki Ramadan dake ta faman kuka Khausar ta kauce gefe tana sakin
ajiyar zuciya.

Anutse Moddibo ya juya ya fita kana suma suka fice daga ɗakin zuwa harabar asibitin yana isa jikin
motar ya samu har Lamiɗo yashiga gaba kana Mommy tashiga baya cikin sauri Hajiya Bunayya tace.

“Kawo shi nan in riƙe shi”.

Banza Moddibo yayi tamkar baiji me tace ba haka nan zuciyarsa ke raya masa Mommy ce mahaifiyarsu
saboda kammani kana ga yanda Khausar ke kiran sunan Mommy akai-akai haka ma Ramadan yasa ya
fahimci itace Mahaifiyarsu.

Buɗe bayan motar yayi tare da kallon Mommy da hankalinta ke tashe ahankali ya ɗago Ramadan tare da
ɗaura mata shi akan cinyarta.

Cikin sanyayyar muryarsa mai cike da kamala nutsuwa da ladabi da kuma ƙwarjini yace.

“Mommy dan Allah kada ki tada hankalin ki. Insha Allah zai samu lafiya ki cigaba dayi masa addu'a”.

Jinjina kai tayi tare da cewa.

“Nagode Allah ya saka maka da alkhairi Ubangiji ya Albarkanci rayuwar ka nagode”.

Kansa a ƙasa ya amsa da.

“Ameen Allah ya sawwaƙa”.

Sannan ya rufe musu mota.

Driver yaja suka tafi kana Moddibo da M Jameel suka shiga motarsu suka tafi.

Sannan Malam Arɗo da Malam Isa suka shiga mota suka tafi.

Ahankali Moddibo ke Driving yayin daya tsirawa titin Idanu,M Jameel dake gefe ya sauƙe ajiyar zuciya
tare da cewa.

“Kai Allah ya gyara wannan al'amarin Ubangiji Allah ya ƙara tsarewa ya kare gaba!”.

Anutse M Jameel ya juya ya kalli Moddibo jin bai amsa addu'ar tasa ba cike da kulawa yace.

“Ya dai? A.J meyafaru ne kayi shiru? Ina ta magana ba reply?”.


Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da furzar da iska mai zafi da kallon M Jameel kamar wanda aka
fisgo maganar daga bakinsa yace.

“Wannan Accident ɗin shiryeyyene!”.

Zare ido M Jameel Yayi tare da cewa.

“Kamar ya shiryeyyene?”.

Ƙaramin tsaki Moddibo yaja kana yace.

“Akwai abinda ban gamsu dashi ba amma babu komai insha Allah zamuyi bin cike saboda na ɗauki
number Motar Allah dai yabawa yaron nan Lafiya”.

Sauƙe numfashi yayi tare da fesar da iska daga bakinsa kana yace.

“Kaga yanda mahaifiyarsa tashiga tashin hankali amma matar nan da suka zo da ita hmmmm”.

Sai kuma yayi shiru tare da faɗin.

_“Astagfirullah Wa'atubu Ilaik ³_”.

A hankali ya numfasa tare da cewa.

_“Azzanna zambu walau kana haƙƙun,_

Allah kagafar ta min Allah kaya femin munana zato dana yi mata”.

Kallon M Jameel Yayi kana yace.

“J bangamsu da yanayinta ba”.

Jinjina kai M Jameel yayi tare da cewa.

“Sosai ma nima na lura da wani yanayi atare da ita amma dai Astagfirullah Allah mun tuba”.

Har suka shiga makarantar ba wanda ya sake magana Moddibo na Parking ya fita.

Acan gidan Lamiɗo kuwa bayan sun isa Lamiɗo ya riko Ramadan aka kafadarsa Already mai ɗaurin yazo
kai tsaye sashen sa ya nufa dashi cikin sauri Mommy ta tsaya daga gefensa cikin raunin murya tace.

“Mai Martaba akaishi wurina kawai aje amasa acan”.

Kallon ta Lamiɗo yayi kana yace.

“Aysha aje amasa awaje na kawai ni yakamata inyi jinyarsa tunda yaro na miji ne”.

Girgiza kai tayi kana cikin sanyin murya tace.


“Zaka bar uzurorin kane ai ƙaramine zan iya yi masa komai yanzu da Haiydar ne zaka iya cewa zai fi ƙarfin
indinga ɗaga sa ko kuma yi masa wani abu”.

ta faɗa Idanunta na zubar da hawaye

Jinjina kai Lamiɗo yayi tare da cewa.

“In dai har kina so in Samu ƙarfin gwiwa kidena zubar da hawaye kin san Banason ganin hawayen ki”.

Khausar kuwa tuni ta bar wajen.

Bayan sun shiga falon Mommy Malam Bala ya ɗaura ƙafar cikin tsanananin azaba Ramadan ke kuka
saboda zafi da raɗaɗi daya ke ji miƙewa Mommy tayi tashiga Bedroom ɗin tana hawaye cike da
tausayinsa Khausar ma miƙewa tayi ta shige Bedroom ɗin ta yana sheshsheƙa ba zata iya juran Kallonsa
cikin ciwo ba Lamiɗo kuwa riƙe sa yana rarrashin sa bayan angama ɗaurin Malam Bala ya basu
magunguna da za'a shafa ledan da M Jameel ya bashi ya ɗauko tare da ɓalla masa maganin ya bashi
sannun ahankali Ramadan ya fara sakin Ajiyar zuciya nan da nan bacci ya ɗauke sa miƙewa Lamiɗo yayi
ya kwantar dashi akan 3sitter kana ya nufi Bedroom ɗin Mommy.

Hajiya Bunayya kuwa ganin ba kowa afalo yasa ta sanya hannunta abakin zaninta tare da ciro wayarta
kana tayi dearling wani Number tana Jin anyi picking tayi ƙasa da murya tare da cewa.

“Ya haka? Shima wanda kuka buge ɗin karaya ne fa kaɗai!?”.

A kuma dai-dai lokacin Khausar ta fito daga Bedroom ɗin ta jin falon yayi shiru ta ɗago manyan Idanunta
da sukayi ja ta kelleta.

Cikin basarwa Hajiya Bunayya tace.

“Wallahi Allah ya taƙaita karaya ce kaɗai toh Nagode”.

sannan ta katse wayar.

Jinjina kai Khausar tayi tare da Kallon ta babu walwala atare da ita tace.

“Hmmm Mai rabon ganin baɗi dai zai gani koda ana kamawa ana sawa aturmi ana kirɓawa, kana zakaran
da Allah ya nufa da cara ko ana ga muzuru ga shaho sai yayi”.

Hararan ta Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.

“Ni tsiyata dake kin cika habaici da zaurance gaki Bafulatana amma kamar ba haushiya”.

A kuma dai-dai lokacin Mommy da Lamiɗo suka fito daga Bedroom ɗin suna murmushi Mommy na
Kallon Hajiya Bunayya tace.

“Yaya keda Khausar dai”.


Murmushin yaƙe Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.

“Ai lallai dai kam”.

Kallon Lamiɗo Mommy tayi kana tace.

“Yayi bacci”.

Jinjina kai yayi tare da cewa.

“Eh kafin ya tashi ya kamata adafa masa kaji ahaɗa da maganin da Bala ya bada yana tashi sai abashi
yaci”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da karɓa, Khausar ta kalli Mommy tare da faɗin.

“Mommy kawo inje in dafa masa ainaga kamar akwai sauran kaji a fridge kana ta wuce kichen ɗin”,

Jinjina kai Mommy tayi tare da miƙa mata.

Acan Makaranta kuwa Haiydar na ganin Moddibo da M Jameel sun shigo ya miƙe da sauri tare da riƙe
hannun Raudat da har zuwa lokacin take kuka kana ya nufi wajensu.

Cikin sanyun muryan yace.

“Malam ya jikin Ramadan?”.

Cike da kulawa Moddibo ya kallesa cike da tausayi ya riƙe hannun Haiydar acikin nasa tare da cewa.

“Bakomai fa ya samu lafiya karaya ne kaɗai Abbanku yaje ya ɗauke sa ankoma dashi gida za ayi masa
ɗaurin gida ka kwantar da hankalin ka Haiydar ba komai insha Allah”.

M Jameel kuwa Raudat ya ɗauka tare da kallon Moddibo kana yace.

“Ita wannan kam Malaman su sunce ba tayi karatu ba sai kuka”.

Ahankali Moddibo ya juya ya kalleta baki ɗaya fuskarta yayi ja Idanunta sun kumbura kana jikinta ya
ɗauki zafi cikin sanyin murya yace.

“Kiyi haƙuri Hassan ɗinki yana lafiya babu abinda ya sameshi zaki koma ki same shi agida cikin ƙoshin
lafiya Insha Allah”.

Kallonsa tayi tare da cewa.

“Da gaske!?”.

Kai ya gyaɗa mata.


“Toh zamu koma gida yanzu”.

Ta faɗa tare da fashewa da kuma hadda sheshsheƙa.

Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da kallon Moddibo kana yace.

“Ina ganin ya kamata abarsu su koma gida dan yau ɗin nan ko sun zauna bawani karatu zasuyi ba ga
Haiydar dake Babba ma baki ɗaya agigice yake bare ita yarinyar sai kuka take duk jikinta yayi zafi”.

Jinjina kai Moddibo yayi idanunsa akan Raudat yace.

“Eh hakan yayi sai su koma gida kawai”.

M Jameel na Kallon Haiydar yace.

“Bari akira gida sai aturo Driver yazo ya ɗauke ku”.

Kai Haiydar ya gyaɗa kana ya nufi Office ɗin Malam Arɗo ya sanar masa nan Malam Arɗo ya kira Lamiɗo
babu daɗewa Driver yazo ya ɗauke su.

Suna isa gida Raudat ta fice da gudu tare da shiga falon Idanunta ya saƙa akan Khausar dake zaune gefen
Ramadan tana bashi kazar da already ta gama dafawa shi kuwa yana amsa yana ci Zugin ƙafar yayi sauƙi
Sosai sai abinda ba arasa ba da gudu Raudat ta shiga tare da ƙara sawa ta rungume kan Ramadan cikin
sauri ya ɗaga mata hannunsa na hagu tare da nuna mata ƙafar sake sa tayi tare da komawa gefensa ta
zauna kana tace.

“Ya ƙafan ka?”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Da sauƙi”, Langwaɓar da kai tayi kana tace.

“Allah ya ƙara sauƙi sannu³”.

Haiydar kuwa zama yayi agefensa tare da rintse idanunsa hawaye masu zafi suka zubo masa ahankali ya
buɗe Idanunsa tare da sauƙe su akan Mommy kana yace.

“Mommy tamkar gimmawar walƙiya haka naga motar nan tazo ta bugi Ramadan sanda yayi sama kafin
ya faɗo Mommy banyi tsammanin kansa ba zai fashe ba”.

Khausar dake cirewa Ramadan ƙasusuwa ajikin kazar ta ɗago kanta tare da miƙawa Ramadan tsokar
kana ta mayar da kallon ta kan Haiydar tace.

“Allah ne ya kare Haiydar saboda addu'ar mahaifiyarmu saboda haka Ubangiji zai ci gaba da kare mu
yana mana katangar ƙarfe da magauta!”.
Da sauri Mommy dake cirewa Raudat Uniform ta ɗago ta kalleta kana tace.

“Khausar wasu magautan kuma wannan ai ƙaddara ce wacce ta riga fata”.

Murmushi mai ciwo Khausar tayi kana tace.

“Hmmm Mommy kenan”.

Acan ɓangaren Hajiya Bunayya kuwa bayan tashiga ɗaki zaune ta samu Amina hannunta riƙe da Tuffa
tana ci,

Amina na kallonta tace.

“Mommy ba abinda ya sameshi ko?”.

Ƙwaffa Hajiya Bunayya tayi tare da zama kana cike da takaici tace.

“Ai shi Haiydar ba abinda ya sameshi ko ƙwarzani bai yiba. Ramadan ne kaɗai ya bugu ba wani na arziƙi
ba Karayane kaɗai”.

A kufule ta ajiye Mayafinta tare da kallon Amina data tsareta da ido kana tace.

“Na kirasu munyi magana dasu sannan na nuna musu ɓacin raina sai suka ce wai abinda yasa haka
saboda lokacin Malamai sun fara zuwa idan suka tsaya za'a iya kama su”.

Ya mutse fuska Amina tayi kana tace.

“Ai dai kam sai ahankali”.

Hannu tasa tare da ɗaukar Ayaba a Plate dake gaban Amina kana tace.

“Ɗazu bayan kin dawo ina kika tsaya dana shigo ban ganki bane?”.

Murmushi Amina tayi tare da cewa.

“Ina side ɗin Gimbiya Dadu nida Uncle Naseer”.

Wara Ido tayi kana tace.

“Allah ko?,Ni dai Amina da zaki yarda sannan badan Masifar Son da yake yiwa wannan shegiyar Khausar
mai kama da sadaka Yallanba yanda yaron nan ya samu cigaba da arziƙi ga kuma arziƙin da Iyayensa suke
dashi da kin haƙura da Jameel din Nan duk da kuwa arziƙin da Mahaifin sa yake dashi”.
Ƙwaffa Amina tayi tare da cewa.

“Nifa Mommy Ina son Uncle Naseer kuma Ina son Malam Jameel saboda gaba ɗayan su suna da kuɗi
kuma dama Ni ko Malam Jameel saboda kuɗin sa nake son sa”.

Sai kuma tayi saurin cewa.

“Yawwa Ummah ni kuwa Akwai Aure atsakanin mu Uncle Naseer?”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da ajiye ɓawon Ayaba kana tace.

“Sosai ma kuwa Akwai Aure atsakanin ku ko a musulunci ya halatta”.

Kai Amina ta gyaɗa tare da faɗin.

“Ummah kiga yanda yake kashewa yarinyar nan kuɗi kinga wayar daya siya mata kuwa wayar kusan
dubu ɗari huɗu da hamsin kinga siye-siye tunda kinga Malam Jameel Anyi anyi aka mashi awajen Boka
an kasa tunda shi wannan yana da riƙo da Ibada shi kuma wannan shgirigirbaune za'ayi saurin kamashi”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.

“Hakane fa Amina nima na fara wannan tunanin ga abu mai sauƙi sawa zamuyi asa ya tsani Khausar ɗin
ya soki shidama in anyi auren bazaku wuce wata uku ba anan zaku tafi india”.

Murmushi Amina tayi kana tace.

“Eh kuma wannan abu mai sauƙi ne duk da masifar son da yake yiwa Khausar tun tana ƙarama amma
yau ɗin nan tun da muka zauna tsawon zaman mu ya sake min fuska kamar zai iya maraba da duk abinda
naje masa dashi”.

Cikin jin dadi ta saki wani murmushi tare da cewa.

“Tun da muka zauna yau ko yawan kiran sunan Khausar da yake yau be yawaita ba Ummah”.

Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta sauƙe kana tace.

“Bari zamu duba mu gani sannan zamuyi magana akai ai ɗazun muka rabu da Jameel da wannan ɗan
banzan Moddibon ko yaushe ka gansa da Jallabiya kamar ɗan Larabawa”.

Dariya Amina ta fashe dashi kana tace.

“Aini shiyasa Samira Sani ke bani mamaki da take son Moddibo me yake dashi meya mallaka komai fa
idan kika ganshi dashi sai dai idan Malam Jameel ne ya bashi kullum yana nan acikin Jallabiya bashi da
kayan daya wuce Jallabiya ko motar da yake hawa daga kin gani kinsan mahaifin Malam Jameel ne ya
saya mishi”.

Ta gumi Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Ikon Allah shi kuma haka yake ashe se Uban faɗin rai kamar ɗan ƙaruna saboda arziƙi yana abu kamar
mai rawani gashi da uban kwarjini”.

Tsaki Amina taja kana tace.

“Ko sutura kika gansa dashi sai dai in Malam Jameel ne yasaya mishi saboda duk yawanci kayansu iri
ɗaya ne na rasa Meyesa Samira Sani take son shi koda yake inaga tsabar kyansa da ƙwarjinsa take so”,

Sai kuma ta gyara zamanta tare da taɓe baki kana tace.

“Inba hakaba me abin so ajikin talaka faƙiri komai sai aboki ya masa, arayuwa gashi ba kuɗiba se shegen
jijji da kai da taƙamar banza da ɗan karen ƙasaita”.

Dariya Hajiya Bunayya tayi tare da kallon Amina kana tace.

“Nima kaina abin ya ban dariya Amina da Hajiya Lami tazo tana ta haukan bin bokaye akansa yaron da ko
wa'azin sa kake kallo yana cikin Jallabiya da Hirami kamar rainon Saudi”.

Dariya Amina tayi kana ta taɓe baki tare da faɗin.

“Ai dai kam ni dai mai ruwana su suka sani mu dai yanzu mun canza shekarar mu daga kan Malam
Jameel zuwa Uncle Naseer”,

murmushi ta saki tare da kallon Hajiya Bunayya kana tace.

“Idan kuma za'a tayi akansu su biyun muna raba ƙafa da duk wanda yazo tun da duka Iyayen su nada
arziki kuma suma suna dashi duk kansu babu wanda yayi karatu aƙasar nan ko wannensu mijin nunawa
sa'a ne da zaran na auri ɗaya daga cikinsu zan zama big Girl acikin garin nan”.

Acan ɓangaren Gimbiya Dadu kuwa Uncle Naseer ne zaune akan 2sitter hannunsa riƙe da wayarsa yana
latsawa Gimbiya Dadu na zaune kan Sallaya tunda ta idar da maghariba bata motsa ba suna taɓa hira
jefi-jefi.

Cike da nutsuwa Lamiɗo yayi sallama ya shiga, tare da miƙawa Uncle Naseer hannu sukayi Musabaha
kana ya gaishe da Gimbiya Dadu.

Cikin sanyin Murya Lamido ya kalli Gimbiya Dadu kana yace.

“Ɗazu fa Ramadan ya gamu da hatsari ya karye”.


Da sauri Uncle Naseer ya ɗago kansa kana yace.

“Subhanallah³ ikon Allah”.

Gimbiya Dadu ma cikin sauri ta ɗago kanta tare da kallon Lamiɗo cikin yana yin damuwa tace.

“Subhanallahi bari idan na idar da Sallar Isha'i zanje in duba sa”.

Miƙewa Uncle Naseer yayi tare da cewa.

“Bari naje na dubasa”.

Ya faɗa tare da ficewa.

Kai tsaye sashen Mommy ya nufa bakinsa ɗauke da Sallama Ahankali Idanunsa suka sauka akan Khausar
dake zaune gaban Ramadan kallon falon yayi yaga ba kowa sai su kadai.

Ahankali Khausar data ji Sallamar sa ta juya ta kallesa.

Cike da duniyan ci ya sakar mata da mayaudariyar murmushi kana ya kashe mata ido ya wani langwaɓar
da kai tare da Shagwaɓe fuska kana yace.

“Ya dai Matas?”.

Shiru Khausar tayi tare da yin ƙasa da kanta cike da mamakinsa aranta tace Uhmmm Uncle Naseer da
tsaurin Ido duk abinda ya aikata ashe zai iya zuwa inda nake.

Cikin rashin damuwa ya matsa kusa da ita idanunsa akan Ramadan yace.

“Ayyah Ramadan sorry Allah ya sawwaƙa³”.

Kai Ramadan ya gyaɗa kana yace.

“Ameen Uncle Naseer”.

Hannun Ramadan ya riƙe tare da cewa.

“Me kakeso in kawo maka”.

Kallonsa Ramadan yayi tare da cewa.

“Komai ma ka siya min ina so Uncle Naseer ”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.


“Toh Autan Mommy”.

Ahankali Naseer ya juya ya kalli Khausar da Idanunta ke kan Ramadan ya narkar da murya tare da faɗin.

“Mommy fa?”.

Kamar ba zata ce komai ba sai kuma tace.

“Ta shiga ciki tana Sallah Isha'i ne”.

Jinjina kai yayi kana yace.

“Ayyah Allah ya bashi lafiya”.

Ta lumshe Idanunta tare da cewa.

“Ameen ya Allah”.

Ahankali ya juya gareta tare da gyara zamansa akan rock ɗin kamar yatsun hannunsa zasu taɓa yatsun
Ƙafarta.

Ya karyar da kai tare da sanyaya muryarsa kana yace.

“My dear yau kusan kwana uku kenan koda naki ra wayar ki bata shiga idan wani laifi na miki sai ki faɗa
min laifina in baki haƙuri duk da cewa ina da yaƙinin bani nayi miki laifa kece kikayi min laifin, gashi ke
kuma baki iya bada haƙuri bako”.

Saurin Kallonsa Khausar tayi tare da maimaita bani nayi miki laifi ba aranta.

Kamar yasan tunanin da take ya jinjina kai tare da narkar da murya kana yace.

“Yes My Khausi Kece kika yi min laifi amma baza kiban haƙuriba to naji na amshi laifina.

Ni zan baki haƙuri duk da cewa kin ɓata mana aiki”.

Sai kuma ahankali ya juya ya kalli ƙofar Bedroom ɗin Mommy kana ya kalleta duk ya koma kalar tausayi
kana yace.

“Kin ɓata mana aiki My Khausi baki damu da rayuwata ba ke baki damu da in mutu ko ina rayu ba abinda
na faɗa miki ai ba jini kawai ake buƙata ba tunda ba Jinin mutum kawai ba jinin ma na Period ɗin mace
magani za'a haɗa min”.

Ta gefen ido ya saci kallonta tare da fesar da numfashi kana yace.


“Amma kika je kikayi min abinda bashi bane, Wallahi kin yimin muguwar fahimta wallahi ba wani abu
bane saboda yanda kika ɓata kikasa na dabba shiyasa aka samu akasin da aka samu”.

Anutse Khausar ta ɗago manyan Idanunta dake cike da mamaki ta tsaida su akan sa.

Ganin kallon data ke jifansa dashi yasa ya dake tare da langwaɓar da kai kana ya marairaice murya tare
da cewa.

“Wallahi na rantse miki da Allah My Khausi gaskiya nake faɗa miki ki yarda dani”.

Still Ido Khausar ta zuba masa aranta tace Ohhh lalle Uncle Naseer baya tsoron Allah ya aikata abu
sannan yazo yana rantsewa da girman Allah saboda baisan girman Allah ba.

Hannun Ramadan ya riƙe acikin nasa tare da sake Matsawa gabanta kana yace.

“Na rantse miki da Allah My Khausi ban aikata abinda kike zargina ba wallahi tallahi ai babu wani abu
sama da Allah?”.

Wani irin kallo ta watsa masa tare da Kallonsa kana tace.

“Ni dai awajena da duk wani Muminin duniya babu wani abu sama da Allah.

Amma awajen matsafi yana da abu da yake ganin zai bashi abu sama da Allah yana da dodon tsafi! Kuma
dama yawan rantsuwa a mgn ai masiface”.

Zare Ido Uncle Naseer yayi cikin yanayin ruɗewa ya kalleta tare da cewa.

“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n Khausar!, Khausar!!, Khausar!!! Nine matsafi?, Hasbunallahu wani'imal
wakil, ya Salam Khausar Ashe dama kallon da kike min kenan?. Kai cona da wannan zargi da matar
aurena take min”.

Lokaci ɗaya jikin Khausar yayi masifsr sanyi kallon fuskarsa tayi taga duk yanda ya wani susuce aranta
tace To Uncle Naseer ko dai dan naji tsoron abin ne amma kayi haƙuri na zarge ka akan abinda baka
aikata ba.

Uncle Naseer kuwa jin bata ce komai ba yasa ya sake narkar da murya tare da cewa.

“Sam ban taɓa zaton zaki yimin irin wannan mummunar fahimtar ba, My dear koda ace ina tsafi tasirin
soyayyarki ba zaisa inyi tsafi dake ba shin idan nayi tsafi dake dawa zan rayu? kece rayuwata My life is
nothing without you Khausi”.
Dai-dai lokacin Mommy ta fito daga Bedroom.Jin motsin fitowarta yasa Uncle Naseer ya juya tare da dai-
dai-ta nutsuwarsa kana yace.

“Mommy ya mai jiki ashe abinda yafaru Allah ya sawwaƙa”.

Ba yabo ba fallasa Mommy tace.

“Ameen mun gode”.

Kana ta nufi kichen tare da cewa.

“Khausar zo muje mu ƙara sa aiki”.

Ahankali Khausar ta kalleta tare da cewa.

“Toh”.

Mommy kana ta miƙe idanu ya zuba mata har ta ɓacewa Kallonsa.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da miƙewa ya fita.

Acan ɓangaren Moddibo kuwa Anutse suka fito daga masallaci bayan sun idar da Sallar Isha'i suka nufi
gida suna shiga coumpund ɗin M Jameel ya tsaya.

Anutse Moddibo ya juya ya kallesa tare da cewa.

“Ya dai J”.

Lumshe idanu M Jameel Yayi kana cikin sanyin Murya yace.

“A.J muje wajen Ummi mana nayi missing ɗin ta”.

Kallonsa Moddibo yayi kana yace.

“Kai J ina yau da safe ma kafin muje makaranta sai da muka biya?”.

Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.

“A.J Ina son ganinta ne wallahi A.J inajin zanyin Aure kwanan nan”.

Cike da Mamaki Moddibo ya juya ya kallesa kana yace.

“Aure J?”.

Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.


“Eh zanyi Aure”.

Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.

“Toh babban magana J wannan magana ce mai girma ai mushiga daga ciki muyi ta”.

Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.

“A'a mushiga mota dai muje muyi ta agidan Ummi”.

Wara Ido Moddibo yayi tare da saurin kallon M Jameel kana yace.

“J baka da kunya agaban Ummi?”.

Murmushi M Jameel Yayi tare da faɗin.

“A.J ni kake cewa bani da kunya ba gwara niba cewa nayi inason Aure, kaifa jikinka ne ya nuna kana son
Aure na riga dana fadawa Innayi na faɗa mata komai na kuma zaɓa maka matar da zaka aura ma”.

Cike da mamaki Moddibo ya juya ya kallesa tare da sakar masa da murmushi kana ya shafa sajensa tare
da cewa.

“Iyeee sannu Babana”.

Dariya M Jameel Yayi kana yace.

“Ayaaa kana wasa ne?, Wallahi da gaske nayi maka zaɓin mata kuma na faɗawa Innayi sannan ta aminta
da hakan kana na shaida mata cewa A.J ɗina yana ɓuƙatar Aure”.

Juyawa Moddibo yayi ya kallesa tare da Matsawa kusa dashi kana ya ɗan mari fuskarsa.

M Jameel kuwa dariya ya fashe dashi wanda ya bayyanar da Fararen haƙoransa kana ya shiga tsinkar
fulawar dake wajen yana sunsunawa tare da watsa su sama ga hasken farin wata da da gloves ɗin ya
haska wajen.

Moddibo kuwa idanu ya zubawa M Jameel yana sakin murmushi akai-akai wani irin amintaccen kyau M
Jameel ya masa fuskarsa kuwa sheƙi da ƙyalli takeyi more especially gishinsa, lumshe idanu Modibbo
yayi kana Aransa yace.

“Masha Allah J kayi kyau sosai baka taɓa yin kyau irin na yau ba”.

M Jameel kuwa still dariyar ya cigaba dayi yana mai buɗe hannayensa tare da cewa.

“Allah ko A.J nayi kyau, kace inje amaryata ta ganni”.


Ahankali Moddibo ya sauke Ajiyar zuciya tare da cewa.

“Au ashe mgnar ta fito fili.”

Cikin sakin yalwataccen murmushin da yasa kyawawan haƙoransa bayyana ya gyaɗa mishi kai.

Shi kuwa Modibbo a hankali yace.

“Sosai ma kuwa J kayi kyau, fara'a nayi maka kyau idan kana dariya kana kyau sosai”.

Ahankali M Jameel ya ɗago ya kallesa still Yana cigaba da dariyar yace.

“Ai kaima in zaka yi fara'a haka yana maka kyau A.J”.

Girgiza kai Moddibo yayi har zuwa lokacin da murmushi afuskarsa yace.

“Bazan iya dariya yanda kake yi haka ba J”.

Wara Ido M Jameel Yayi kana cikin dariyar yace.

“Zaka iya A.J”.

Harɗe hannunsa yayi a ƙirjinsa tare da ɗan jingina da jikin mota, kana ya zubawa M Jameel ɗin idanu
yana kallon yadda yaketa dariya har maƙolloton wuyanshi yana ɗan haurawa sama kana ya yi ƙasa,
sannan haƙoransa nata sheƙi.

Innayi ce ta fito daga sashen ta tare da kallon M Jameel kana tace.

“A'a Jamilu yau mai ya maka daɗi haka?”.

Cikin dariya sosai ya kalli Moddibo kana ya nuna masa saitin Dick ɗin sa da ido.

Da sauri Moddibo ya sunkuyar da kansa tare da kallon inda M Jameel ya nuna da sauri ya lumshe
Idanunsa ganin yanda Dick ɗinsa ke miƙe tun ranan da abin ya faru tsakanin sa da Khausar har yau Dick
ɗin sa bai sake kwanciya ba koda na second ɗaya sam yaƙi kwanciya ya koma Normal yanda yake cikin
dabara ya sanya ƙafarsa ɗaya agaba ɗaya abaya ya matse cinyarsa kana ya cije lips ɗin sa.

Wani sabon dariya M Jameel ya fashe dashi tare da riƙe cikinsa kana ya kalli Innayi tare da cewa.

“Wayyo Allah cikina hahahaha khhykhy Innayi wai dan nace masa na zaɓa masa mata shine yake cewa,
nine Babansa kuma na faɗa masa akan na faɗa miki cewa wallahi Aure yakeso ya girma yanzu shine yake
wata magana Innayi ki faɗa masa bana zaɓa masa mata ba?”.

Murmushi Innayi tayi kana tace.


“Sosai ma”.

Moddibo kuwa sajensa ya shafa tare da kallon su kana yace.

“Iyeee kune ma masu tsara min rayuwata toni nace muku ina bukatar aure ne?”.

Still cikin ƙyelƙyala dariya sosai M Jameel yace.

“Ai bai sai kafaɗa da bakin ka ba A.J dama ai body language ɗabi'ar kace to ganganar jikinka ta faɗa min
kana son Aure”.

Moddibo kuwa cikin sauri ya juya tare da nufar mota jin M Jameel na Shirin tona masa asiri batare daya
juya ba yace.

Toh kazo mu tafi Innayi bari muje gidan Ummi”.

Kai Innayi ta gyaɗa da murmushi afuskarta tace.

“Toh Allah ya tsare”.

Bayansa M Jameel yabi tare da buɗe motar yashiga har suka isa gidan da zaran M Jameel ya Kalli
Moddibo zaiyi dariya shi kuwa Moddibo sai ya sakar masa da murmushi.

Suna isa Moddibo yayi Parking suka fita akan baranda suka hango Ummi hannunta riƙe da kayan shanya
da alama akan igiya ta ɗebosu, ƙara sawa Moddibo yayi kana yace.

“Ummi kawo in karɓa miki”.

Miƙa masa yayi.

Cike da so M Jameel yace.

“Umminaaa”.

Kallonsa Ummi tayi tare da ƙara sa shiga falon ya suka biyo bayan ta atare.

Akan capet Ummi ta zauna tare da jingina bayanta da jikin kushin kana ta miƙe ƙafafunta ahankali
Moddibo ya zauna daga gefenta tare da ajiye kayan wankin ganin kayanta ne yasa ya fara ninkewa.

M Jameel kuwa ahankali ya kwanta tare da ɗaura kansa akan cinyar Ummi kana ya ɗaura ƙafa ɗaya kan
ɗaya kana ya lumshe Idanunsa tare da cewa.

“Ummina kenan”.
Ahankali Ummi ta juya ta kalli Moddibo kana ta mayar da kallonta kan M Jameel sai kuma ta ɗaga kanta
ta kalli haɗeɗɗen agogon dake manne abango kana ta sauƙe Idanunta ƙasa tare da cewa.

“Ayana yin garin nan da yake ga alamun yau akwai hadari sannan baku zo da wuri ba dubi time fa har
kusan 8:30 kodai zamu kwana ne?”.

Murmushi M Jameel Yayi tare da ɗago kai ya kalleta kana ya langwaɓar da kai tare da cewa.

“Ummi dana fi kowa farin ciki ace yau gani gaki muna kwana gida ɗaya”.

Juyawa yayi ya kalli Moddibo kana yace.

“Shiyasa ma nake faɗawa A.J nifa Aure zanyi”.

Cikin sauri Ummi ta juya ta kallesa kana cike da Mamaki wannan shine karo na biyu da yake faɗa mata
Kalmar yana son Aure Girgiza kai tayi kana tace,

“Jamiluuuu”,Ta faɗa kai tsaye ta rasa Meyesa acikin kwanakin take kiran sunan sa kai tsaye.

Dariya M Jameel ya fashe dashi sosai yake ƙyalƙyala dariya harda kaɗa ƙafa.

Asma'u da Bashir kuwa jiyo sautin dariyar sa yasa suka fito daga Bedroom tare da zama daga gefensu
cike da girmamawa suka gaishesu atare.

Ahankali ya kalle tare da sakar musu da murmushi kana yace.

“Ƴan ƙanne na”.

Sai kuma ya juya ya kalli Ummi dake murmushi kana yace.

“Wallahi Ummi dagaske aure nake so”.

Wara Ido Asma'u tayi cike da farin ciki ta kalli M Jameel kana tace.

“Kai Alhamdulillah gaskiya munji daɗi”.

Murmushi M Jameel yayi kana yace.

“Aikam dai Asma'u munji daɗin mu zan ginawa Ummina da Malam side ɗin su na musamman in saka su
acikin”.
Sai kuma ya numfasa tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Sannan ingina miki ɗakin ki in zuba miki kayan masu kyau sannan Bashir ma ingina mishi side dinsa da
ban da daddare kafin inyi bacci inzo inyi hira da Ummina inganta ta ganni kana kullum idan gari ya waye
daga na dawo daga masallaci in biya inga Ummina ta ganni kana ta bani shayinta mai daɗi Insha”.

Cike da jin daɗi Asma'u ta kallesa kana tace.

“Allah yasa Yah Jameel”.

Lumshe Idanunsa yayi kana yace.

“Hmmmm!”.

Kansa Ummi tashafa cike da ƙaunarsa tace.

“Ameen”.

Moddibo kuwa ahankali ya zuba musu Idanu yana kallon su cike da burgewa.

Ummi kuwa ahankali take shafa kan M Jameel kana tace.

“Kai ko kunya baka ji ƙato da kai kazo ka kwanta min akan cinya na!?”.

Ta ƙarashe maganar tana shafa yalwataccen sumar kansa.

Murmushi yayi kana yace.

“Uhmmm Ummina idan ban ɗaura kaina akan kiba to akan wa zan ɗaura? Abinda ma ya kusa ƙare wa
hmm”.

cikin sauri tace.

“Ya kusa ƙare wa kamar ya!?”.

Murmushi yayi kana yace.

“Idan nayi Aure mana ai shikenan na samu sabon cinya”.

Girgiza kai Moddibo yayi tare da kallon M Jameel kana yace.

“Mtssss J Allah ya shiryeka”.

Miƙewa M Jameel Yayi tare da kallon Ummi kana yace.


“Ummi nida A.J rana ɗaya za muyi Aure, nida Innayi mun zaɓa mishi mata, amma sai idan nazo ni kaɗai
zan faɗa miki sai mugama magana tsakanina dake”.

Wara ido Ummi tayi tare da kallon Moddibo kana tace.

“Allah ko”.

Kai ya gyaɗa mata yana dariya ganin hararar da Moddibo ke wurga masa kana yace.

“Eh”.

Sha ɗaya saura suka yiwa Ummi Sallama kana suka tafi suna isa gida suka shiga falon M Jameel har ya
juya da niyyar shiga ɗakinsa da yake kwana ya fasa yabi bayan Moddibo.

Ahankali Moddibo ya juya ya kallesa tare da cewa.

“Ya dai J?”.

Murmushi M Jameel Yayi kana yace.

“Yau tare zamu kwana”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana ya wuce ciki.

Tunda Moddibo ya fito daga toilet ya zauna agefen gado tare da dafe kansa da hannu biyu har yanzu bai
janye yayinda Jameel kuwa ke ciki.

Ahankali M Jameel ya fito daga toilet ɗin.

Yana mai tsane suman kanshi da mini towel Idanunsa suka sauƙa akan Moddibo daya dafe kansa da
hannu biyu.

Cike da kulawa yace.

“A.J ya dai?”.

Ahankali Moddibo ya ɗago kansa.

M Jameel kuwa kallon yanda Idanunsa suka kaɗa suka jawur yayi kana lips ɗin sa na rawa yayin da jikinsa
ke ɓari kamar mai jin sanyi.

Cikin sauri M Jameel ya matsa kusa dashi kana yace.

“A.J ya dai?”.
Cikin yanayin damuwa da raunin murya Moddibo ya kallesa kana ya miƙe tare da yin wani irin fitinenne
miƙa Atake A ɗin sa ya Miƙe tsaye baki ɗaya jikinsa rawa yake idanunsa sun kaɗa sunyi jawur tuni lips ɗin
sa ke rawa tamkar mai jin zazzaɓi.

Wani irin tausayinsa ne ya kama M Jameel Cike da tausayawa yace.

“A.J ya dai?”.

Cikin yanayin tashin hankali Moddibo ya Girgiza masa kai kana cikin raunin murya yace.

“J ga halin danake c....!

*Littafin SAKAYYAH dai na kuɗine 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin aminci 0661110170 GTBank AISHA
ALIYU GARKUWA.*

*By*

*GARKUWAN MARUBUTA*

SAKKAYA

24

Cikin raunin murya ya yarfa hannun sa kana yace.

“Ga halin da nake rayuwa a ciki fa, gani fa J”.

Cikin sanyin murya M Jameel yace.

“A.J na faɗa maka koda ace bakinka bai furta kana son Aure ba jikin ka ya gama nunawa har yaushe
zamu cigaba da zama ahaka?”.

Cikin sanyi ya lumshe idanunsa tare da buɗe su akan Moddibo kana yaci gaba da cewa.

“A.J dole sai munyi auren nan Auren nan shine cikan farin cikinmu gaba ɗayan mu.

A.J buri na ba zai taɓa cika ba idan har banyi Aure na riƙe Ummi da ƙanne naba farin cikina ba zai cika”.
Sai kuma ya sauƙe Ajiyar zuciya tare da kallon yanda gaba ɗaya ilahirin jikin Moddibo ke rawa har
haƙoran sa na haɗuwa kana yace.

“Sannan kaima burin ka bazai cika ba zuwa yanzu yaci ace Innayi ta huta da wasu abubuwa da zaran kayi
aure zata huta da aikace-aikace cikin gida idan kayi aure Itama ta huta koda girki ne sai dai agirka abata”.

Yarfe hannun Moddibo yayi cikin wani irin yanayi mara misaltuwa yace.

“Taya zan fara abin yana damuna fa J inaji kamar inyi ta kuka”.

Miƙewa M Jameel Yayi kana ya nufi kitchin tea ya haɗa masa da lemun tsamin kana ya fito.

Bakinsa ɗauke da Sallama yashiga direct Moddibo ya nufa tare da miƙa masa Cup ɗin da faɗin.

“Kasha”.

Runtse idanu Moddibo yayi cikin raunin murya tamkar mai shirin fashewa da kuka yace.

“Gaba ɗaya kullum ina rayuwa cikin shan ruwan zafi da lemun tsami gaba ɗaya nafara jin alamun Ulcer
zata kamani saboda lemun tsamin nan abin ya fara isata zanje inga likita may be zasu bani wani abu da
zan dinga sha inji sauƙi”.

Jinjina kai M Jameel yayi kana yace.

“Eh hakan yana da amfani kayi ƙoƙarin zuwa kaga Dr”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da damƙe ƙasan maransa kana yace.

“Uhmmm abin yana damuna fa wallahi yau tsawon kwanaki kenan gaba ɗaya ban sake samun kwanciyar
hankali ba baki ɗaya D ɗina yaƙi kwanciya da zaran dare yayi nayi sallama da kwanciyar hankali da
nutsuwa kenan gwara da rana abin baya tsananta min”.

Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe kana yace.

“Za muyi ƙoƙari muga mun haɗu da likita sannan ka yawaita azumi kamar yanda kakeyi da”.

Kallonsa Moddibo yayi cikin raunin murya yace.

“J dama can inayin azumi amma yanzu abin ne ya faskara koda nayi azumin karyewa yake shiyasa na
daina yi”.

Cikin tausasawa M Jameel ya miƙa masa kofin hannunsa kana yace.

“Kayi haƙuri kasha wannan abin insha Allah zaka ji dama-dama”.


Ba musu ya amsa tare da kafa kansa ya shanye tass kana ya janye kofin daga bakinsa ya koma ya zauna
yana sakin ajiyar zuciya Atake zufa ya fara wankesa nan da nan yaji bacci na fusgarsa kwanciya yayi tare
da addu'a cikin minti biyar bacci ya ɗauke sa.

Sai asannan M Jameel ya saki Ajiyar zuciya tare da kwanciya ba jimawa bacci ya ɗauke sa.

Shi kuwa Moddibo can cikin baccinsa ya hangosa kwance akan Mashahurin gado na alfarma.

Yayi irin kwanciyar nan na rabi a jingine ya jingina bayansa da jikin kan gadon yayin da Khausar ke tsaye
tana shafa masa lallausan tafin hannunta agoshinsa.

Ahankali ya ɗago idanunsa ya kalleta wani irin Arnen rigan baccine ajikinta wanda da kaɗan tsawonsa ya
wuce cinyarta yayin da daga sama rigar less ne yana hango saman nipples ɗin ta daga ƙasan rigar kuwa
Net me santala-santalan cinyoyinta farare masu taushi sun bayyana.

Cikin yanayin sanyinsa ya ɗago hannunsa na dama ya riƙe nata da take shafa goshinsa dashi kana ya ɗan
miƙa da niyyar fisgota zuwa jikinsa da sauri ta ɗan ja baya tare da girgiza masa kai kana cike da wani salo
ta jujjuyawa masa yatsarta manuniya tare da faɗin.

“Laaaa,Laaaa”.

Ahankali yayi ƙasa da kansa tare da ɓata fuska kana ya sake kai hannunsa da niyyar Fisgota jikinsa cikin
sauri ta sake kaucewa tare da juya masa yatsarta fuskarta na ɗauke da ƙayataccen murmushi daya
bayyanar da jererrun fararen haƙoranta tace.

“Laaa,laaaa”.

Moddibo kuwa ahankali ya zuba wa ƙirjinta Ido,Ita kuwa khausar ganin yanda ya zubawa waje ɗaya ido
yasa ta maida Idanunta wajen gani tayi baki ɗaya idanunsa nakan ƙirjinta ɗin ta kallonta ta mayar
fuskarsa gani tayi ya buɗe bakinsa kaɗan lips ɗin sa sunyi ja suna rawa alamun yana jin sanyi kana
idanunsa sun kaɗa sunyi ja tamkar wanda ke mayen bacci, Khausar kuwa murmushi take sakar masa
daga tsayen da yake Ahankali ya zaro harshensa ya juya alamun tazo still. Kai ta girgiza tare da maƙale
kafaɗa kana ta juya ta nufi ƙofa yayin da ko wanne sassan jikinta ke kaɗawa musamman Bajejjen
ƙugunta da dukiyar fulaninta cikin sauri Moddibo ya yun ƙura tare da bin bayanta ita kuwa tana fita ta
rufe ƙofar tana ƙyalƙyala dariya.

Baya ya koma tare da dafe D ɗinsa Akuma dai-dai lokacin ya farka daga bacci kansa ya dafe tare da jan
siririn tsaki kana ya miƙe tare da shiga toilet ya sakarwa kansa ruwan ɗumi yakai minti talatin atsaye
ruwan na sauƙa akansa lips ɗin sa na rawa yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinsa ke ɓari kana har zuwa
lokacin D ɗin sa bai kwanta ba da zaran ya lumshe idanunsa Kyakkyawan suranta keyi masa yawo acikin
ƙwayar Idanunsa.

Washe gari.

Anutse M Jameel Yayi parking motarsa aharabar Makarantar kana ya buɗe gefen Driver ya fito yayin da
Moddibo ya buɗe gefen mai zaman banza ya fito cikin shigarsa as Usual Jallabiya yayin da jikinsu ke fitar
da sanyayyan ƙamshin tularen Oud Kareem Kai tsaye office ɗin Malam Arɗo suka shiga bakinsu ɗauke da
Sallama.

Cikin nitse Malam Arɗo dake duba wani littafi ya ajiye tare da ɗago kai fuskarsa ɗauke da murmushi kana
cike da girmamawa suka gaishe sa ya amsa cikin sakin fuska kana yace.

“Ya labarin yaron nan mai jiki?”.

Gyara zama Moddibo yayi kana yace.

“Muma abinda muka zo mu tambaye ka kenan”.

Jinjina kai yayi tare da cewa.

“Eh toh ni banje ba gaskiya amma nakira mahaifinsa yace.

“Da sauƙi sai dai basuyi bacci ba amma yanzu da safen nan dai ya samu bacci”.

Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.

“Da ma ai sai ahankali Allah ya sawwaƙa”.

“Ameen ”. Cewar Modibbo

Gyaran murya M Jameel ya ɗanyi kana ya kalli Malam Arɗo tare da motsa laɓɓansa alamar mgn sai kuma
yace.

“Hmmm Malam”.

Sai kuma yayi shiru.

Ahankali Malam Arɗo ya ɗago kai tare da kallon sa kana yace.

“Ya dai Jamilu ka faɗa mana”.


Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe Kana yace.

“Nifa na gama karantarwa Amakarantar nan”.

Cike da mamaki Malam Arɗo ya ɗago kansa tare da kallon sa kana yace.

“A'a Jamilu wannan wace iriyar magana ce?”.

Numfashi M Jameel ya fesar tare da cewa.

“Zancen gaskiya ne”.

Cikin yanayin damuwa Malam Arɗo ya Girgiza kai kaina yace.

“Wannan magana bata yimin daɗi ba ya haka Moddibo kayi masa magana”.

Moddibo da kansa ke ƙasa ya ɗago ahankali tare da kallon Malam Arɗo kana yace.

“Harni ɗin ma ai”.

Cike da tsanananin mamaki Malam Arɗo ya kallesa kana cikin gaskiya da gaskiya yace.

“Aikuwa baku isa ba”.

Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.

“Aikuwa Ni dai gaba ɗaya na gama abinda nazo yi amakarantar nan gaskiya.

Dama tun farko ban ɓoye maka ba batun ƙannena ne sannan yanzu sun gama”.

Sai kuma ya lumshe idanunsa tare da sauƙe numfashi kana yace.

“Sannan yanzu Mahaifina yana ɓuƙatar in temaka Masa a harƙan Kaauwancinsa ban sani badai A.J ko
shi zai cigaba”.

Cikin sauri Moddibo ya kalli M Jameel kana yace.

“J kasani nazo makarantar nan ne domin in tayaka tarbiyyan tar da ƙannen ka saboda ƙannenka ƙanne
nane”.

Jinjina kai M Jameel Yayi kana yace.

“Tabbas na yarda na kuma aminta amma bayan wannan kuma fa?”.

Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.

“Babu komai J”.


Jinjina kai M Jameel Yayi yace.

“Na yarda A.J”.

Shi dai malam Arɗo Kallonsu kawai yake cikin rashin sanin abin cewa.

M Jameel ya kallesa tare da cewa.

“Malam kaga mun gama abinda ya kawo mu makarantar nan sannan muna da abin yi kaga har A.J
Mahaifina yana so mu taimaka masa aharƙan kasuwancinsa sannan baya ga haka shi A.J yana so zai
koma Jami'atul Madina saboda za'a bashi gurbin karantarwa acan”.

Cikin mutuwar jiki malam Arɗo ya jinjina kansa kana yace.

“Ba kuzo min da labari mai daɗi ba yaran nan kun karya min da gwiwata kun sakar min da ƙwarin
gwiwata duk wani comfedance ɗina kun kwaye min shi”.

Fesar da iska mai zafi yayi tare da dafe kansa kana yace.

“Makarantana ta cigaba amma acikin shekaru shida da kukayi karantarwa aciki tayi cigaban da gaba ɗaya
jahar Taraba ma baki ɗaya babu makarantar data cigaba irinta bare ace nan Gembulan Membila babu
makarantar da tayi sunan nawa”.

Kai ya jujjuya kana yace.

“Babu makarantar dake da haziƙan ɗalibai kamar Makaranta na, kana nasan kune ƙashin bayan wannan
nasarorin, amma rana tsaka kuzo min da wannan labarin banji daɗin sa ba bana son jin hakan kar kuyi
min haka jikokina”.

Ahankali Moddibo yayi ƙasa da kansa cikin sanyin murya yace.

“Toh ya zamuyi komai ka gani arayuwar nan yana da ƙa'ida, sannan yana da lokaci kana mun faɗa maka
dama”.

M Jameel ne ya ɗago kansa dake sunkuye yana lalata wayars tare da kallon Malam Arɗo daya zabga ta
gumi kana yace.

“To ai iya lokacin kenan Ni dai bayan wannan lokacin bani da Wani lokacin da zan iya ƙarawa”.

Saurin Kallonsa Moddibo yayi kana ya girgiza kai tare da cewa.

“Nima bani da lokacin da zan iya ƙarawa anan nima ina da abubuwan da zanyi ayanzu”.

Cikin sanyin murya da alamun damuwa Malam Arɗo ya janye tagumin da yayi kana yace.
“Bazan iya sauraron maganar ku ba wannan maganar agida ya kamata muyi ta in kuma albashinku ne
yayi kaɗan in ƙara muku mana”.

Miƙewa Modibbo Yayi kana yace.

“Ni dai nagana karantarwa Amakarantar nan babu wani lokacin daya rage min dazan karantar batun
ƙarin albashi kuwa kai kanka kasan ba haka muke ba”.

Yana gama faɗa ya fice.

Hararansa Malam Arɗo yayi cike da ƙaunarsu har cikin ransa yake jinsu kana yace.

“Ai dama kai ɗan fadi ba'a tambaye ka bane”.

Dariya M Jameel yayi kana yace.

“Ai gaskiya ne”.

Murmushi M Jameel yayi tare da bin bayan Modibbo.

Kai tsaye inda sukayi Parking motarsu suka nufa M Jameel yashiga mazaunin Driver Moddibo ya shiga
gefen me zaman banza kai tsaye gidan Abban M Jameel suka nufa.

Suna isa suka fito daga motar kai tsaye falon suka shiga Abba dake zaune kan kujera ya buɗe musu
hannu tare da faɗaɗa Fara'ar fuskarsa.

Fuskarsu ɗauke da ƙayataccen murmushi suka nufesa M Jameel ya nufi gefen damansa Moddibo kuwa
gefen hagunsa ya nufa rungumesu yayi tare da faɗin.

“Alhamdulillah yanzu dai buri ya cika hankali ya kwanta kun gama karantarwa awannan makarantar”.

Jinjina kai M Jameel yayi tare da cewa.

“Sosai ma Abba yanzu ma haka daga can muka fito mun isarwa da Malam Arɗo ƙudirina”.

Cikin sauri Moddibo ya kallesa kana yace.

“Ƙudirun mu dai”.

Jinjina kai M Jameel Yayi kana yace.

“Hakane”.
Cike da so Abba ya sauƙe Ajiyar zuciya kana yace.

“Sosai nake ɓuƙatar temakon ku acikin harƙan kasuwanci na saboda kuna da ilimi akan harƙan
kasuwanci sannan yanzu ni girma ya fara zuwan mun ina da ɓuƙatar hutu akan wannan zirga zirga daga
wannan ƙasar zuwa wannan kasar ɗin ina son hutawa”.

Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Insha Allah Abba matukar ina raye zaka huta sannan zan kula da Company ka kamar yanda kake kula
dashi koma fiye da haka”.

Jinjina kai Abba yayi kana yace.

“Na sani na gamsu”.

Dai-dai lokacin da Hajiya Turai ta shigo.

Ahankali Abba ya sake su kana yace.

“Toh ku zauna”.

Kai suka gyaɗa kana suka zauna akan 1-1sitter Abba kuwa miƙewa yayi tare da shiga Bedroom ɗin sa
kana ya ɗauko wasu manyan files ba daɗewa ya fito hannunsa riƙe dasu kana ya fito ya zauna.

Anutse ya juyo ya kalli Moddibo kana yace.

“Moddibo”.

Cike da ladabi yace.

“Na'am Abba”.

Gyaran murya Abba yayi kana ya kalli files ɗin hannunsa tare da cewa.

“Ina so ka zama shaida tsakanina da ɗana akwai shiya yanki da nake so in Ware na mallakawa Jamilu na
halak malak koda bayan raina wannan mallakin sa ne baya cikin tumunin gado”.

Cikin sanyin murya Moddibo ya kallesa kana yace.

“Bayan ni ba ɓuƙatar kanemi wani shaida

Saboda kasancewa ta da J atare musamman ma yanzu dake tunanin zaka samu cikin kasuwanci”.

Girgiza kai Abba yayi kana yace.


“Moddibo akwai wata shaida bayan Allahu Subhanahu wata'ala ne?”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana yace.

“Babu”.

Juyawa Abba yayi tare da ɗaukar files dake gefensa ya buɗe tare da ciro wasu takardu aciki kana ya kalli
Moddibo tare da cewa.

“Wannan takardun Company na Marroco ne na mallakawa Jamilu su duniya da lahira na bashi”.

Kallonsa ya mayar kan M Jameel kana yace.

“Kuma akwai kuɗaɗe na musamman da nake so in baka dan tafiyan tar da Company to amma yanzu bani
da tsuran kuɗi a ƙasa Jamilu dan ko hajji ma bana mutun takwas kaɗai na biyawa, ko su Hajia Kareema
da kuɗinsu suka biya”.

M Jameel kuwa kasa cewa komai yayi sai murmushi da yake saki akai-akai tare da tsirawa Mahaifin nasa
Ido.

Ganin yanda M Jameel ke sakin murmushi akai-akai yasa Abba sakar mishi da murmushi kana yace.

“Ina so in haɗa maka da tsuran ruwan kuɗi amma yanzu gaskiya bani da ruwan kuɗi ahannuna saboda
kwanan nan nagama gina Company na Katsina sannan kuma nasiya wani fili anan za'a gina gidan Mai
shiyasa ya zama bani da ruwan kuɗi da yawa ahannuna”.

M Jameel kuwa Anutse ya ɗago kansa fuskarsa ɗauke da murmushi kana ya kalli Abba tare da cewa.

“Uyummm”,

Abba kuwa faɗaɗa fara'ar fuskarsa yayi.

Ahankali Moddibo ya saki murmushi yana kallonsa cike da burgewa kana yana kallon yanda da zaran M
Jameel Yayi murmushi Maƙolloton sa ke sama da ƙasa.

Cikin dariya sosai M Jameel ya Kalli Moddibo kana yace.

“A.J”.

Moddibo daya kasa daina Kallonsa yace.

“Na'am”

Murmushi M Jameel yayi tare da faɗin.


“Ga duniya ta samu amman ba lokacin cinta”.

Cikin wani irin yanayi Moddibo ya zuba masa Ido amma baice komai ba.

Abba kuwa kallon M Jameel tare da shafa kansa yayi kana yace.

“Duniya kuwa ai bata gama samuwa ba Jamilu har saina yi maka Aure tukunna dan duk jin daɗin duniya
idan mutum bashida Aure rageggene amma in tambaye ka mana ya batun Aure?”.

Dariya M Jameel ya fashe dashi tare da buga hannunsa na dama akan cinyarsa kana yace.

“Uyummm Abba mun kusa yin Aure”.

Murmushi Abba yayi kana yace.

“Toh ina surukan nawa suke?”.

Gyara zama M Jameel Yayi tare da kallon Abba yace.

“Toh na dai zaɓawa A.J kam nayi masa mata”.

Saurin Kallonsa Moddibo yayi yace.

“Abbah haka yaketa cewa wai shida Innayi sun zaɓa min mata yanzu da girmana wai J da Innayi ce zasu
zaɓa min mata”.

Dariya Abba ya ƙyalƙyale dashi Idanunsa akan Moddibo yace.

“A'a wannan tsakanin ku ne”.

Hajiya Turai dake ƙoƙarin shiga tuntuni ta fasa ta tsaya daga jikin ƙofar tana sauraron duk tattaunawa da
suke Hajiya Karima kuwa na cikin ɗaya daga cikin Bedroom ɗin Abba yayin da take ji tamkar zuciyarta zai
fashe saboda baƙin ciki da takaici yadda ya ware kadara mai girma zai bawa Jameel kamar shine kaɗai
ɗansa.

Girgiza kai Moddibo yayi tare da Hararan M Jameel kana yace.

“Uyummm lallai kam”.

Murmushi M Jameel Yayi Yana Kallon Moddibo yace.

“Allah Abba da gaske na faɗawa Innayi na yiwa A.J mata na zaɓa masa wacce zasu dace”.
Kai Abba ya gyara zamansa tare da faɗin.

“To wacece”.

Girgiza kai M Jameel Yayi tare da cewa.

“Abbah Asirri zan zo in faɗa maka”.

Cikin sakin fuska Abba yace.

“A lallai dai kam yayi kyau kai kuma fa?”.

Ƙasa da kai M Jameel Yayi sai kuma ya sake ɗago kansa tare dasa yatsarsa manuniya kan kuncinsa yayin
da yasa sauran yatsun kuna kan gemunsa alamar tunani kallon Abba yayi kana yace.

“Hmm zanyi Aure kam Abba amma kalar matar da zan Aura ta musamman ce.

Kuma fa ni ba mace daya zan aura ba”.

Saurin Kallonsa Moddibo yayi cike da Mamaki yace.

“Toh mata nawa zaka Aura?”.

Murmushi M Jameel Yayi tare da wara ya tsun hannun ya nuna masa kana yace.

“Huɗu zan aura Sunnah zanyi”.

Abba kuwa murmushi yayi tare da cewa.

“Hmmm Jamilu ko kunya baka ji”.

Langwaɓar da kai yayi tare da Shagwaɓe murya kana yace.

“Abba idan ban faɗa maka ba wazan faɗawa ai shiyasa nake faɗa maka saboda kashirya kashe kuɗi kana
ka sake neman kuɗi da wuri naji kana cewa babu kuɗi a ƙasa”.

Numfashi ya fesa kana yaci gaba da cewa.

“Abbah matar da zan Aura fara ce ƙal mai kyau domin kyakkyawa ce mai yalwataccen gashi gata da
tsafta gata da ƙwarjini da tarin ilimi”.

Wara Ido Moddibo yayi kana yace.

“Kamanta kace huɗu zakayi sauran kuma ya suke?”.


Kallonsa M Jameel Yayi kana yace.

“Duka haka suke”.

Atare suka sanya dariya dukan su cikin dariya Abba yace.

“Lalle kace za'asha biki”.

Jinjina kai M Jameel Yayi kana yace.

“Sosai ma Abba za'a asha biki kam”.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“aifa kam za'a sha shagali”.

Numfashi mai nauyi M Jameel Yayi tare da wara ido yace.

“A'a Abba bikin sunna za'a yi ace kamar bikin Malam Jameel da Sheik Moddibo ana raƙashewa ai girma
ya faɗi”.

Dariya Abba yayi kana ya jinjina kai tare da cewa.

“Eh kayi gaskiya”

Gyara zama M Jameel Yayi tare da shafa sajensa yace.

“Walima mai zafi zamuyi Abba ayi na mata ayi na maza sannan akawo min mata na ka faɗawa A.J shi
tashi ɗaya ce rak ko kishiya ban amince yayi mataba”.

Ahankali Moddibo yashafa sajensa. Yana Kallon yanda M Jameel ke sakin murmushi.

Abba kuwa takardun ya ɗauka tare da miƙewa M Jameel yace.

“Kayi sign anan”.

Karɓa M Jameel Yayi tare da cewa.

“Toh shikenan Abba”.

Sannan yayi Sign”.

“Na mallaka makasu Ubangiji shine shaida da kuma abokin ka sannan akwai wasu ma amma basanan
suna Katsina sai anturo minsu in baka kasa hannu”.
Kasa tsaida murmushinsa yayi cike da ƙaunar Mahaifin nasa yace.

“Abbah Nagode Allah ya ƙara girma”.

Jingina kai Abba yayi yace.

“Ameen”.

Bayan sun ci abinci suka idar da Sallar La'asar suka yiwa Abba Sallama suka tafi.

Bayan kwanaki Alhamdulillah jikin Ramadan yayi sauƙi kumburin ma yafara raguwa yana cin abinci sosai
kana yana shan magunguna Mommy da Khausar na kula dashi sosai yanda ya kamata.

Da yammacin Alhamis Hajiya Bunayya da Hajiya Lami ce zaune agaban Boka Kar'uzu cikin jinjinawa
Hajiya Bunayya ta ɗaga hannunta na dama tare da kallon boka Kar'uzu tace.

“An gaida Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye shaiɗani Uban
Shaiɗanu”.

Cikin wata sandararriyar murya mara daɗin amo ya kece da wata mahaukaciyar dariya tare da cewa.

“Kuna so ku canza sheƙa ko?,”.

Cikin sauri Hajiya Bunayya ta gyaɗa masa kai,

Da ƙarfi ya sake kece wa da wata mahaukaciyar dariya kana yace.

“Aikuwa gashinan yaron shi da kansa yana ta batun Aure”.

Cike da zaƙuwa Hajiya Bunayya tace.

“Wani yaron kenan Boka?”.

Cikin daga sautin murya yace.

“Shi Jamilun kuma akwai Naseer yashigo cikin lamarin ku”.

Da sauri Hajiya Bunayya ta gyaɗa masa kai kana tace.

“Eh”.

Ya sake kece wa da wata razananniyar dariya kana yace.


“Wa kuka fi so aja muku hankalinsa Naseer hankalinsa zaifi saurin Jawuwa amma shima yana da buri
akan ku kuma har kwanan gobe yana son Khausar”.

Zare Ido Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Wani irin buri Boka”.

Da sauri Boka Kar'uzu yasa fankacecen hannunsa ya bugi ƙasa tare da wasu rubutu akai kana ya ɗago
kansa ya kalleta tare da cewa.

“Toh burinsa zai iya tafiya ƙarƙashin Aure ne amma”.

Hajiya Bunayya kuwa aƙage tace.

“In dai burinsa a ƙarƙashin Aure ne ai babu matsala ajawo mana hankalinsa tunda shi wancan kace
samun shi zai mana wuya tunda gashi tsawon shekara biyu cess har ana ƙoƙarin cika na uku amma abin
ya gagara ko ya kagani?”.

Wata ƙwarya mai ɗaure da layu ajiki ya ɗago tare da kaiwa bakinsa yayi wasu surutan tsafi kana yace.

“Za'a maida aikin kan Naseer jan hankalin Naseer ba zai yi wuya ba tun da dama shima yana da buƙatar
ku wannan aikin naku ganemmene kada ku damu zan danne son Khausar a ransa zan cire mishi
sha'awarta”.

Hajiya Lami data zabga Uban tagumi ta kalli Boka Kar'uzu kana tace.

“Toh Ni kuma ya batun aikin mu?”.

Kallonta yayi tare da fashewa da wata mahaukaciyar dariya kana yace.

“Batun aikin ku³ ”.

Jinjina kai tayi kana tace.

“Eh batun aikin mu boka Kar'uzu”.

Kallonta yayi tare da lashe dagargajejjen laɓɓansa yace.

“Ki turo min ƴar ki idan har kina son aikin da kuke buƙata ya kan kama duk dare tazo mu kwana har
tsawon darare bakwai”.

Aƙiɗime Hajiya Lami ta dafe ƙirjinta kana tace.

“Duk dare?”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Yanda zan fasa budurcinta zan sake mayar mata yanda koya Aureta zai sameta amatsayin budurwa”.

Da ƙyar Hajiya Lami ta haɗiye wani yawu mai masifar ɗaci kana tace.

“Boka ya za ayi haka kuma?”.

Ya watsa mata wani kallo da munanan Idanunsa kana yace.

“Sai na kusanceta da ruwan maniyyina da nata zan haɗa inyi aikin da za'a ja Hankalinsa ya dawo gareta
dama na faɗa miki akwai aikina ƙarshe da muke da tabbaci akai amma mai tsanane idan kinga zaki iya ki
turo ƴarki magana ta ƙare”.

Cikin sanyin murya da alamun damuwa tace.

“Toh boka zanyi shawara”.

Cikin wata razananniyar tsawa yace.

“Tashi ku tafi sai naji daga gareki yanzu zanyi baƙi ɗan busurungu mai ƙiran kwaɗi zai ƙaraso da
tawagarsa maza ku ɓace ƙananun La'anannu kafin ƙarasowar sa”.

Cikin rawan jiki suka fice.

Acan ɓangaren Khausar kuwa Adaren Alhamis da ciwon ciki ta kwana duk ba tayi wani ishesh-shen bacci
ba.

Washe gari Juma'a bayan an saƙƙo Sallar Juma'a Moddibo ne zaune amota cikin shigar Voyel Sky blue
anyi masa ɗinkin zamani kansa sanye da hula Zanna bukar wadataccen sumar kansa daya sha gyara ya
zuba ta ƙyeyarsa yayin da jikinsa ke fitar da sanyayyan ƙamshin tularen Oud Kareem idanunsa alumshe
kana yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi.

Yayin da M Jameel ke gefensa yana Driving cikin irin shigar Moddibo.

Anutse M Jameel ya Kalli Moddibo kana yace.

“A.J muje gidan Lamiɗo mu duba jikin Ramadan, kaga ko Jiya ma saida Malam Arɗo ya kira ya tambaya
munje mun duba jikin yaron”.

Buɗe Idanunsa dake lunshe yayi kana yace.

“Muje kuma gwara dai ya turo mana number sa”.

Girgiza kai M Jameel Yayi yace.


“A.J muje zuwan yafi mutunci, tunda yaron nan kusan ahannun mu suka je suka karɓesa a asibiti sannan
muna daga cikin Malaman makarantar, sannan tunda kaga Malam Arɗo ya matsa muje kamar ya
wakilcemu ne akai”.

Ya sauƙe numfashi tare da cewa.

“A.J muje kafa san yanda falalar duba mara lafiya yake kada ka manta da hadisin dake cewa”.

_“Izamaridal Abdah Ausafara Kutibalahu misla ma kana ya'ama muƙiman sahiha”_.

Cikin sauri Moddibo yace.

“Naji muje”,

Murmushi M Jameel yayi tare da juya akalar motar zuwa Unguwar su Lamiɗo suna isa M Jameel ya
Danna hong cikin sauri mai gadi ya leƙo Idanunsa suka sauƙa akan wata ɓaƙar Rang-Rover yana shyning
ganin haɗuwar motar yasa ya koma ciki ya buɗe musu gate Anutse M Jameel yayi Parking a inda aka
tanadar dan Parking motoci kana ya buɗe motar ya fito ahankali Moddibo ma ya buɗe side da yake ya
fito.

Cikin sauri mai gadin ya ƙara so kusa dasu cike da girmamawa yace.

“Sannun ku da zuwa”.

Atare suka amsa da yawwa.

M Jameel na gyara zaman haɗeɗɗen agogon diomond dake ɗaure atsintsiyar hannunsa yace.

“Mai Martaba na ciki?”.

Kai mai gadin ya gyaɗa kana yace.

“Eh yana nan ɗazu ya shigo”.

Jinjina kai M Jameel Yayi kana yace.

“Ayi mana sallama dashi ace masa Malaman su Haiydar ne sun zo duba jikin Ramadan ne”.

Cike da girmamawa mai gadin yace.

“To bari Inje in faɗa musu sannunku da zuwa”.

Ya faɗa tare da nufar sashen Maimartaba Lamiɗo.


Acan side Mommy kuwa Khausar ce kwance Atsakiyar gadonta yayin da take murƙususu cikin
mawuyacin hali.

A falo kuwa Mommy ce ke bawa Ramadan magani bayan ta gama bashi ta wuce Bedroom din Khausar.

Cike da tausayawa Mommy tace.

“Sannu Khausar Allah ya sawwaƙa”.

A hankali Khausar ta ɗago Idanunta dake jiƙe da ruwan hawaye ta gyaɗa mata kai.

Girgiza kai Mommy tayi cike da tausayinta kana tace.

“Amma kinsha maganin?”.

Still Kai Khausar ta gyaɗa jikinta na fidda zufa sai murƙususu take.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauke sannan tace.

“Wannan Abu yayi yawa duk sanda zakiyi Period sai kin ta fama da ciwon ciki Khausar muje asibiti”.

Girgiza kai Khausar tayi cikin yanayin azaban ciwon da mararta ke yimata ta kalli Mommy tare da faɗin.

“Nikam bana so Mommy Idan munje asibiti mu cewa Dr me ya kawo mu Mommy kibani.

Zuma da ruwan zafi Insha”.

Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.

“Toh shikenan”,Sannan ta fice kai tsaye kichen ta nufa ta buɗe Flaks ta zuba ruwan zafi a Cup kana ta
zuba zuba mai yawa aciki tare da zuba dakekken citta kaɗan ta gauraya sannan ta koma ɗakin har zuwa
lokacin tana ta murƙususu har ta dawo bakin gadon tana daf da faɗowa.

Cikin sauri Mommy ta tare ta zuwa jikinta kana ta gyara mata kwanciyar ta cike da damuwa tace.

“Khausar zaki faɗi kijiwa kanki ciwo ko kuma ki karye ki sake samun wani aikin ga Ramadan ma bai warke
ba”.

Kasa cewa Komai Khausar tayi sai hawaye wani dake bin wani yayinda hannun damanta ke kan maranta.

Haiydar kuwa daga bakin ƙofar ya tsaya cike da tausayawa yace.

“Sannu Addah Khausy Allah ya sawwaƙa”.

Ya faɗa tare da ficewa cike da tausayinta.


Mommy kuwa ɗaga Khausar tayi tare da zaunar da ita kana ta miƙa mata kofin tace.

“Gashi maza ki kafa kanki ki shanye”.

Amsa tayi jikinta na rawa kamar mazari ta kafa kanta kat-kat-kat ta shanye.

Lokaci guda wani zufa yashiga wanke mata jiki still mararta na damƙarta hannunta na hagu tasa ta
damƙe cikin nata tare da sunkuyar da kanta yayin da jikinta yashiga rawa kar-kar-kar.

Cike da tausayawa Mommy ta shafa kanta kana tace.

“Sannu Khausar am Allah ya sawwaƙa abin nan yana wahalar dake nikam abin nan yafara damuna”.

Miƙewa Khausar tayi daga durƙuson da tayi duk ta burkice.

Ahankali Haiydar ya juya cike da tausayinta ya nufi kichen ya ɗibi ɗan wake a Plate sannan ya zuba
Cabbage da Cocumber sannan ya fito ya zauna agefen Ramadan dake kallon Cartoon ya fara ci duk ya
zuzzubar a ƙasa ajiye Plate ɗin yayi tare da janyo System ɗin Mommy yana kallon Musabaƙar da akayi a
Saudi wanda Nigeria ce tazo na ɗaya.

Khausar kuwa jin cikin na lafawa yasa ta ɗago kanta tare da kallon Mommy kana cikin sanyin murya tace.

“Mommy yunwa nake ji”.

Murmushi Mommy tayi kana tace.

“Ohh ni Aysha wani abu sai Khausar mutun na ciwo amma baya fasa cin abinci sai ma ƙaruwa”.

Cikin tale Baki tare da rumtse ido tace.

“Mommy ga ciwo gaba cin abinci ai sai mutum ya mutu”.

Jinjina kai Mommy tayi kana tace.

“A lallai sai mutum ya mutu kam”.

Cikin sauri ta miƙe tashiga toilet da kallo Mommy tabi bayanta.

Tana shiga toilet ɗin taga Period ɗin ta yazo drawer ta ɓude ta ɗauki Pad ta Sanya kana ta gyara jikinta
ta fito abakin toilet ɗin ta tsaya tare da riƙe ƙugunta ta kalli jikinta riga da wando ne ajikinta tun na bacci
sai dai suna da duhu da taushi kana rigar nada gajeren hannu kanta sanye da hular sanyi mai tambarin
*K* a gaban goshi ta tura tulin sumar ta aciki ahankali ta fita falon kasancewar har zuwa lokacin cikin bai
daina ciwo ba saidai yayi sauƙi akan 1sitter ta zauna tana facing Haiydar.

Kallon Haiydar tayi cikin Muryanta dake rawa tace.

“Ka kalli yanda ka ɓata wajen nan gaba ɗaya ɗazu fa na share duk da ciki na na ciwo, haka na gama gyara
ko ina kalli fa Haiydar yanda duk ka ɓata kuma baza ka iya gyarawa ba”.

Ahankali Haiydar ya kalleta yace.

“Haka kike idan baki da lafiya duk ki gigita mu tausayinki ya kama mu idan kin ji sauƙi bakin ki da masifar
ki duk ya cika mu yanzu kinga na tashi ne ban gyara ba?”.

Kanta ta ɗago tare da watsa masa harara still tana damƙe da maranta tace.

“Ai ko baka tashi ba yanzu idan muka yi baƙi fa kaci sannan kabar Plate ɗin awajen kaja system ka fara
game kome kake oho ni ban sani ba”.

Girgiza kai yayi kana yace.

“Dan Allah Addah Khausar kiji da kanki ki ƙyaleni baki san abinda nake ba, bance ki share ba kiji da kanki
Allah ya sawwaƙa”.

Da sauri ta rintse Idanunta tare da damƙe cikinta saboda murɗawa da yayi kana ta shiga jujjuya kanta
hakan yasa hular dake kanta rabi ya zame gashin goshinta ya bayyana.

Acan Falon Lamiɗo kuwa mai gadi na sanar dashi Malaman su Ramadan ne yace ashigo dasu juyawa mai
gadi yayi ya fita kana babu daɗewa ya dawo Moddibo da M Jameel na biye dashi.

Lamiɗo na ganinsu ya faɗaɗa fara'ar dake fuskar sa cike da mutumtaka da kuma dattako yace.

“Sannun ku da zuwa”.

Ido M Jameel ya zubawa falon Komai na cikin falon na tsarin sarauta ne acikin ransa yace wato dai duk
ƙanƙantar Masarauta sai ka samu kayan sarauta aciki sosai tsarin falon ya burgesa ganin wasu manyan
tuntun jikin bangon anyi tambarin masarautar ajiki.

Cikin sakin fuska yace.

“Marabanku ku iso ku iso”.

Naseer dake hakimce akan 1sittee yana danne danne waya ya ɗago kansa tare da cewa.
“Sannun ku da zuwa”.

Cike da kamala M Jameel da Moddibo suka zauna akan 2sitter kana cike da girmama suka ce.

“Ina yini Allah rene ya mai jiki?”.

Still da murmushi afuskarsa yace.

“Alhamdulillah Jiki da sauƙi zuwa yanzu kam yana iya motsa ƙafar mai gyaran ma yace randa ya cika
kwana goma za'a fara tsayar dashi ƙafa kan yayi sauƙi kumburin ya saɓe duka”.

Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.

“Masha Allah Allah ya ƙara sauki”.

Kishin giɗa Lamiɗo yayi kana yace.

“Ameen”.

M Jameel kuwa kallon agogon hannunsa yayi tare da gyara zaman hular kansa yace.

“Malam Arɗo yace mu gaishe sa da jiki”.

Jinjina kai Lamiɗo yayi kana yace.

“Kai aikuwa Nagode Nagode sosai”.

Kallon Naseer dake danne-dannen waya Lamiɗo yayi kana yace.

“Yawwa Naseer kaisu falon Aysha su duba Ramadan da jiki”.

Kai Naseer ya gyaɗa tare da faɗin.

“Toh”,Kana ya miƙe tare da Kallonsu yace.

“Bismillah muje”.

Kallo ɗaya Moddibo ya masa ya ɗauke kansa.

Bayan sun fito coumpund ɗin Naseer ya kallesu cikin yanayin zumuɗi da son gwaninta yayi gyaran murya
tare da cewa.

“Nan inda muka fito shine side ɗin Mai Martaba.

Wancan na ɓarin Kudu shine Sashen Gimbiya Dadu mahaifiyar Mai Martaba.

Ni kuma yayar Mahaifiyata ce da mahaifiyar Mai martaba da mahaifiyata Uwarsu ɗaya Ubansu ɗaya”.
Sheƙeƙe M Jameel ya kallesa kana aransa yace.

“Toh kuma waya tambayesa ko kuma waya nemi ƙarin bayani bare ya kama yi mana dogon Inroducing”.

Moddibo kuwa baki ya taɓe abinda ba ɗabi'arsa ba yau shiyake ji dan wani mugun haushin yaron yakeji
har ƙasan ransa.

Uncle Naseer kuwa cikin yanayin zumuɗi da nuna asan cewa shi wani ne yace.

“Wancan kuma shine Sashen Hajiya Bunayya Uwar gidan mai Martaba”.

Jinjina kai M Jameel Yayi kana yace.

“Masha Allah”.

Dai-dai lokacin suka isa sharshen Mommy.

Atake Uncle Naseer ya faɗaɗa fara'ar dake fuskarsa kana yace.

“Nan kuma shine Side ɗin Surukata Hajiya Aysha Amaryar Mai Martaba”.

Wara ido M Jameel Yayi kana yace.

“Iyeee Surukar ka kuma?”.

Jinjina kai Naseer yayi tare da faɗin.

“Eh surukata”.

Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.

“Eh lallai dai kam zaka Auri ƴarta kenan?”.

Gyaɗa kai Uncle Naseer yayi tare da kallon M Jameel kana yace.

“Eh Khausar ai matata ce”.

Atake Fara'ar dake fuskar M Jameel ya gushe lokaci ɗaya ya ɓata rai tare da tsuke fuskansa wanda har ya
kasa ɓoyewa ya bayyana afuskar sa hakan yasa yayi banza dashi Moddibo kuwa baki ya taɓe.

A takaice M Jameel yace.


“Ok”.

Suna hawa step ɗin Naseer ya fara shiga falon bakinsa ɗauke da sallama Dai-dai lokacin da Mommy ta
kawo wa Khausar Plate ɗin ɗan wanke da dafeffen ƙwai guda uku sai, Cocumber, Cabbage, Tomatoes,
albasa agefe sai roban yaji agefe ga kuma man ainihin ƙarago yana ƙamshi.

Mommy na ajiye mata ta jiyo muryan Uncle Naseer,Anutse ta ɗaga kanta kana tace.

“A'a Naseer kaine?”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Eh Mommy tare da baƙi nake Malaman su Ramadan ne suka zo duba sa da jiki”.

Miƙewa tayi tare da cewa.

“Aaaa sannun su da zuwa maraba ka iso dasu”.

Khausar kuwa Maggi ta dauƙa tare da marmasawa akai kana ta ɗauko Cabbage, tomatoes, albasa,
Cocumber ta zuba akai sannan ta yaryaɗa mai tare da dumbuzo yaji da yawa ta zuba kana ta gauraya
gefe ta ajiye cokalin, ganin ta ajiye cokalin yasa Haiydar Matsawa kusa da ita kana yace.

“Ya Inzo muci ne?”.

Hararansa tayi kana tace.

“Banaso”.

Murmushi yayi tare da faɗin.

“Naga kin ajiye cokalin gefe ne”.

Tana sake barbaɗa yajin tace.

“Aikasan bana cin ɗan wake da cokali ci da hannu yafi daɗi kuma ba yanzu kagama cin naka ba duk ka
ɓata mana falo ba gashi yanzu anyi baƙi ba duk ka ɓata falon”.

Girgiza kai Haiydar yayi tare da cewa.

“Toh Aunty Masifatu naji bakyaso ai akwai wani zan saka”.

Baki ta taɓe kana tace.

“Oho dai”.
Ta ƙare mgnar da murguɗa mishi baki kana ta cigaba da cin ɗan wakenta saboda masifaffen yunwar da
take ji baki ɗaya jikinta rawa yake rabonta da abinci tun wanda taci daren jiya dan yau da sai yanzu
zatayi breakfast saboda ciwon cikin.

Dai-dai lokacin M Jameel ya shigo falon Moddibo na biye dashi.

Atake sanyayyan ƙamshin tularensa ya ratsa hancinta.

Kallo ɗaya Moddibo yayi mata yayi saurin rintse idanunsa tare da kiran sunan Allah aransa babu abinda
ya faɗo masa arai face yanayin da suke kasance acikin mafarkan sa.

Ahankali Mommy ta gyara lullubin dake kanta kana tace.

“Sannun ku da zuwa”.

Murmushi suka yi tare da zama akan 2sitter ya zamana suka facing Ramadan dake kwance kan 3sittee
Uncle Naseer kuma na zaune gefen Haiydar.

M Jameel kuwa kallon Khausar yayi da murmushi afuskarsa yace.

“A'a ya dai Lelewal”.

Anutse Khausar ta ɗago kanta tare da kallon M Jameel cikin yanayin damƙar da cikinta ya fara tace.

“A'a Yah Jameel sannun ku da zuwa”.

Murmushi yayi kana yace.

“Sannu Lelewal lallai kam ashe dai kema irin Asmeey ce bubbuga rumbu ne”.

Marairaice fuska tayi tare da Shagwaɓe fuska kana tace.

“Wallahi Yah Jameel tun jiya banci komai ba yauma tun da safe banci komai ba yunwa nake ji”.

Sai kuma ta juya ta kalli Haiydar cikin bada izinin tace.

“Katashi ka ɗauki Plate ɗin nan tun da ka gama ka shiga dashi kichen”.

Moddibo kuwa ɗago kansa yayi tare da kallon inda Mommy ke zaune cike da ladabi da kuma nutsuwa
yace.

“ina yini”.
Kallon sa Mommy tayi tare da cewa lafiya lau ya ƙoƙari?”.

Kansa a ƙasa yace.

“Alhamdulillah ya mai jiki?”.

Kallon Ramadan daya zubawa Catoon da ake ido tayi kana tace.

“A jiki da sauƙi Alhamdulillah”.

Ramadan kuwa kallon Moddibo yayi kana yace.

“Malam Moddibo ina wuni”.

Murmushi Moddibo ya ɗanyi tare da kallon sa kana yace.

“Ramadan ya ƙafa?”.

“Da sauƙi Malam yanzu kam har ina iya motsa ƙafar”.

Ya faɗa tare da jijjiga ƙafar yana murmushi.

Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.

“Masha Allah”.

M Jameel dake gefe ya miƙe tare da matsawa kusa dashi kana ya kalli ƙafar tare da cewa.

“A Masha Allah”.

Khausar kuwa ahankali ta juya ta kalli Moddibo da bakinsa ke motsa wa alamar tasbihi kana ya ɗan
lumshe idanunsa sai dai baiga ma rufewa ba cikin tura baki tace.

“Malam ina yini”.

Yana jinta ya mata banza.

Sake tura madedecin bakinta tayi kana tace.

“Moddibo Ina yini”.

A hankali Moddibo ya ɗago kansa gani yayi duk hankalin Mommy na kan Khausar ajiyar zuciya ya sauƙe
kana ataƙaice yace.
“Lafiya”.

M Jameel kuwa kallon Khausar yayi tare da cewa.

“A'a Khausar babu tayi ne”.

Girgiza kai tayi kana tace.

“A'a Malam akwai bari akawo muku”.

Kallon Mommy dake magana da Uncle Naseer tayi kana tace.

“Mommy akawo musu”.

Cikin sauri M Jameel ya Girgiza kai yace.

“A'a nikam wasa nake Alhamdulillah Mommy wallahi aƙoshe muke”.

Mommy data miƙe tace.

“Allah bari akawo muku”.

Dariya yayi tare da shafa sajensa kana yace.

“Alhamdulillah Mommy wallahi aƙoshe muke”.

Khausar kuwa ahankali ta cigaba da cin ɗan wakenta lokaci ɗaya cikinta ya murɗa da masifan ƙarfi cikin
tsananin azaba ta runtse Idanunta tare da damƙe cikinta da hannunta na hagu Atake Idanunta suka kaɗa
sukayi ja jikinta yashiga rawa yayin da gaba ɗaya zufa ya tsats-tsafo agoshinta.

Cike da damuwa Mommy ta matsa kusa da ita kana tace.

“Sannu Khausar am Allah ya sawwaƙa”.

Uncle Naseer ma Matsawa Yayi kamar zai riƙe hannunta ya marairaice murya tare da cewa.

“Sorry My dear”.

Cike da kulawa M Jameel ya Kalli Mommy kana yace.

“Mommy me yake damunta?”.

Cikin yanayin damuwa Mommy ta kalli Khausar dake murƙususu dafe da cikinta kana tace.

“Wallahi ciwon ciki take fama da shi kwananan duka tun jiya da daddare ya tsananta gashi har yau haka
ta tashi dashi”.
Girgiza kai yayi tare da cewa.

“Subhanallah Allah ya sawwaka”.

Khausar kuwa sosai ta haɗa zufa yayin da hannunta ɗaya ke damƙe da yaji data ɗebo.

Moddibo kuwa kai ya Girgiza kana aransa yace.

“Ba dole tayi ciwon ciki ba irin wannan yajin da take ci kamar tsohuwar Mayya”.

Sai kuma ya kalli Naseer dake dafe da kujeran da take yana mata sannu siririn tsaki yaja aƙasan ransa
kana yayi ƙasa da kansa.

M Jameel kuwa warin harara mai cike da tsana ya watsawa Unclee Naseer, tare da cizon lip inshi na
ƙasa.

Kwafa yayi kana ya maida kansa wurin Khausar kallonta yake cike da tausayawa kana yace.

“Subhanallah sannu Allah ya sawwaƙa Amma Mommy to kuje Asibiti mana”.

Kallon M Jameel Mommy tayi tace.

“Wallahi na faɗa mata amma Khausar bata son batun allura bata son batun magani duk sanda zance
muje asibiti sai tace in bari zata samu sauƙi”.

Wani irin rawa jikin Khausar yake banda murƙususu babu abinda take baki ɗaya jikinta zufa yake fitarwa
tuni hular dake kanta ya zame yalwataccen sumar ta data tura ciki ya zubo har gadon bayanta kana ya
rufe mata fuska cike da tausayawa, Mommy, Uncle Naseer, M Jameel keyi mata sannu.

Haiydar kuwa kallon yanda duk ta fice hayyacinta yayi girgiza kai yayi tare da miƙewa kana yace.

“Idan ciwo ya damƙeki ki zama abin tausayi yana sake ki kuma ki dame mu da jaraba bari dai in ɗauki
Plate ɗin nan in Kai kichen kafin ki dawo hayyacinki ki fara min bala'i”.

ya Ida mgnar tare dasa hannunsa, da nufi matsar da plate ɗin ɗan wakenta.

Yana janye plate din ya matsar gefe.

Dai dai lokacin Khausar ta fara sauƙe ajiyar zuciya jin ciwon cikin ya fara lafawa,

sannun ahankali ta fara maida numfashi yayin da Idanunta ke cike da ruwan hawaye hannu ta sanya da
niyyar janyo Plate ɗin ta da Haiydar zai matsar gefe cikin sauri ta riƙe cikin muryan kuka tace.

“Kabani ɗan wakena”.


ta faɗa tare da janye Plate ɗin.

Da sauri Haiydar ya sakar mata plate din tare da nufar kitchen yana dariya.

Ita kuwa Khhausar numfashin ciwo ta fesar tare da ɗaura plate ɗin kan cinyarta kana ta damƙo yaji ta
barbaɗa aka ɗauwaken da yaji mai da vegetables da ƙwai din takai bakinta.

M Jameel da yake gabanta ya janye tagumin da yayi tare da yin dariya kana yace.

“Lallai kam yau ga mai ciwo anan”.

Murmushi Haiydar daya fito kitchen yayi kana ya kalleta tare da cewa.

“Haka take ni mamaki nake ban taɓa ganin irin Addah Khausar ba”.

Ya maida kallonsa kan M Jameel kana yace.

“Ka ganta ko Malam Jameel wallahi tana ciwo kamar zata mutu amma tana cin abinci”.

Ɗago kai Khausar tayi tare da makawa Haiydar Harara kana tace.

“Kana gani jikina har rawa yake yunwa kamar zai kasheni toh ga yunwa ga ciwo in banci abinci ba in
mutu kenan kakeso!?”.

Ta ida maganar tare dasa hannunta aroban yajin ta ɗebo.

Cikin ɗaga murya da tsawa Moddibo yace.

“Ki daina cin yajin nan ya isa haka ai shima dole yasa miki ciwo dubi yanda kike cin yajin nan kamar
Mayy”.

Sai kuma yayi shiru tunawa da yayi agaban Mahaifiyarta yake.

M Jameel kuwa juyawa yayi ya kallesa tare da sakin murmushi Aransa yace.

“Toh saboda yi kenan wai Gawa da gatsinai agaban uwarta ma sai ya mata Masifa”.

Uncle Naseer kuwa kasa motsa wa yayi duk inda Khausar tayi zai bita da ido yana mata sannu.

Girgiza kai Moddibo yayi shikam ganin yanda take cin barkonon ne yake bashi mamaki.

M Jameel kuwa abin ne yake bashi dariya ga hawaye shaɓe-shaɓe afuskarta kana ga hannunta ɗaya
acikin robar yaji ɗaya kuma riƙe da mararta.
Murmushi yayi kana yace.

“Ikon Allah lalle ana mutane daban-daban aduniya ga ciwo ga kuka ga cin abinci wani idan yayi ciwo ai
baya iya cin abinci”.

Murmushi Mommy tayi Idanunta akan Khausar dake kai lomar ɗan wake tace.

“Haka take tun tasowar Khausar tana ƙarama bata taɓa tayi ciwo ya hanata cin abinci ba ka ganta nan
haka take ko zazzaɓi tayi bata fasa cin abinci”.

Dariya Uncle Naseer yayi kana yace.

“Ai haka shine dai-dai kinga zata ji sauƙi ta wani ɓangaren”.

M Jameel kuwa murmushi yayi idanunsa akan Khausar yace.

“Aikam taji daɗinta nikam idan nayi ciwo abinci shi zan fara tsana”.

Kai Haiydar ya gyaɗa kana yace.

“Ai haka ma aka sani Indai mutum bashida lafiya Indai ciwon Allah da Annabi ne kuma ciwon gaskene
karya ci abinci wani lokacin ma dai ba ciwon gaske bane taya za'a yi mara lafiya yaci abinci?”.

Khausar kuwa ɗago kai tayi cikin Muryan kuka ta kalli Haiydar kana tace.

“Ai dai Allah ya sani ciwona na gaskene taya za ayi banci abinci ba”.

Jinjina Kai Moddibo yayi tare da taɓe baki Aransa yace.

“Wannan ta fiye Shagwaɓa da sangarta ba abin ya maketa ba”.

Ahankali Moddibo yace.

“Allah ya sawwaƙa Mommy bari mu tafi”.

Ya faɗa tare da miƙewa kana ya ciro dubu goma a aljihunsa ya ajiyewa Ramadan shima M Jameel dubu
goma ya ajiye masa kana yace.

“Gashi Asiya masa Sweet”.

Murmushi Mommy tayi kana tace.

“Ayyah kun shiga ɗawainiya mun gode”, Murmushi sukayi tare da ficewa cikin sauri Mommy tashiga
kichen ta ɗauki Warmers ta zuba musu ɗan wanke da ƙwai da kuma vegetables ɗin ta bawa Haiydar yabi
bayan su Moddibo ya kai musu”.
Bayan kwana biyar Alhamdulillah jikin Ramadan yayi sauƙi sosai har ya fara takawa nan da kwana uku
za'a since ɗaurin sosai Khausar da Mommy ke bashi kulawa cikin ikon Allah kuwa ƙafar ta warke babu
wani ciwo sai abinda ba'a rasaba.

Acan Falon Hajiya Bunayya kuwa zaune take yayin da Uncle Naseer ke zaune kan 1sitter Anutse Amina ta
fito cike da kwarkwasa ta zauna ahannun kujeran kana ta narkar da murya tare da cewa.

”Uncle Naseer mai kuma kake so?”.

Ɗago kansa yayi tare da tsira mata ido kana yace.

“Me kuma nake so?”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Eh mana Uncle Naseer faɗa min me kake so”.

A sakarce ya saki murmushi kana yace.

“Idan na faɗa miki abinda nake so zaki yarda da cewa ina son shi?”.

Kai ta gyaɗa tare da tsira masa idanu.

Idanunsa ya sanya acikin nata kana ya narkar da murya tare da cewa.

“Toh ke nake so”.

Cike da mamaki ta zare ido kana ta rufe fuskarta tare da cewa.

“Kaji Uncle Naseer Kai da ga Khausar ɗin ka waya ke kuma batun Amina?”.

Cikin tsira mata ido yace.

“Ha'a to Khausar ai naji cewa.

Kakarta tayi mata zaɓin miji kinga shiyasa za'a nuna mana cewa ita ba tamu bace amma tunda ke
tamuce ai shike nan”.

Sai kuma ya maida kallonsa kan Hajiya Bunayya dake sakin murmushi kana yace.

“Hajiya za'a bani ita ko?”.

Ya ida maganar cikin salon yaudara da marairaice wa.


Hajiya Bunayya kuwa cike da farin ciki da jin daɗi tayi dariya kana tace.

“A'a mai zai hana ai kaima mai bada ita ne da kai da kaya duk mallakar wuya ne Naseer”.

Cike da farin ciki da kuma jin daɗi Hajiya Bunayya ta miƙe tare da shiga Bedroom ɗin ta tana shiga ta ciro
wayarta cike da farin ciki ta lalumo Number Boka Kar'uzu ta kira.

Yana ɗagawa ta fashe da dariya cike da farin ciki tace.

“An gaida Boka Kar'uzu La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye tsinanne Uban tsinannun Boka
aiki yaci”.

Wata mahaukaciyar dariya ya kece dashi kamar an tada lalataccen Injin Markaɗe yace.

“Ai kaɗan ma tukunna kika gani aiki zai cigaba da tafiya kamar yanda ake buƙata, shaf zan mantar dashi
Khhausar ko mgnarta zai daina yi. kashe waya Sarkin Wadannin aljanu zai kawo min ziyara”.

Cikin sauri ta katse wayar tare da kiran wayar Hajiya Lami tana Picking tace.

“Hajiya Lami aikin boka yaci yaron nan yanzu muna zaune Afalo yace yana son Amina”.

Cikin jimami Hajiya Lami tace.

“Ohhh kukam kunji daɗi mukam yanzu ya zamuyi?”.

Gyara kwanciya Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Ya kuma zakuyi dan boka yace ƴarki taje tayi kwana bakwai Meye kike jira keda kinsan mukam mu yayi
amfani damu bare kuma ƴaƴanmu ki turata taje tayi kwana Bakwai”.

Shiru tayi alamar tunani sai kuma tace.

“Idan yaso sai kice wa mahaifinta za taje gidan ƙanwarki tayi sati, ko kuma ki turo min ita nan idan yaso
duk dare sai na kaita da kaina ta kwana da safe idan an kai yara makaranta sai insa Driver ya ɗaukota
tunda shima Ni yake yiwa aiki”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.

“Wallahi kuwa Hajiya Bunayya haka za ayi ”.

Gyara kwanciya Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Ai dai kam hakan za'a yi”.

Kana suka katse wayar bayan sun tsaida magana kan Samira Sani zata zo.
Acan ɓangaren M Jameel da Moddibo kuwa zaune suke afalon Ummi tana zaune kan 1sitter yayin da M
Jameel ya jingina kansa ajikin cinyar Ummi suna hira.

Ahankali Ummi ta ɗaga kanta tare da kallon agogo dake nuni da sha ɗaya saura kallonta ta mayar kan M
Jameel kana tace.

“Jamilu”,Anutse ya kalleta tare da cewa.

“Na'am Ummina”.

Cikin sanyin murya tace.

“Ka tashi ku tafi dare yayi fa”.

Miƙewa daga jikinta yayi kana yace.

“Toh Ummi gaskiya kam dare yayi bari mu tafi”.

Anutse Moddibo ya mike tare da cewa.

“Ummi sai da safe”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Allah ya ta kaiku lafiya”, Atare suka amsa da. “Ameen”kana suka fita.

Suna fita dai-dai ƙofar gidan Ummi suka ga wani irin...!

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a
kanki littafin 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA*

*By*

*GARKUWAN MARUBUTA*

SAKAYYA

25
*Al'bishirunku Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku
ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.

Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce,
akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna
uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin
yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace
ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa
bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore
ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar
gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san
hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa
tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan
mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina
mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka
yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke
taimakawa (sex hormones 😍) dinki.

Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu
tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?

Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da
ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa
domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.

Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?

Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar
amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin
mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar
mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,

Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke
mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.

Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta
akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.
Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*

Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne
masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na
daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka
ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar
da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari
maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276
domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA
ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba
Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA


😘

*(GARKUWAR MA'AURATA)*

25

Suna fita suka ga gari yayi shiru ga wani irin hadari daya haɗu baƙiƙƙirin, sanyayyar iska mai sanyi da
ratsa jiki yana kaɗawa alamun wata ƙil hadarin ya watse ne ko kuma ya sako ruwa, wani irin lumshe
idanu Moddibo yayi tare da cije labɓansa na ƙasa cikin sauri ya shiga mota M Jameel yashiga maza
mazaunin Driver yaja suka tafi suna isa gida aka fara yayyafi still yau ma ɗakin Moddibo M Jameel
yashiga ya kwanta nan da nan bacci ya ɗauke sa.

Moddibo kuwa tunda ya kwanta yake juyi ahankali ya miƙe ya zauna idanunsa cike da ruwan fitina da
zaran ya lumshe Idanunsa kyakkyawar suranta daya gani amafarkine ke masa yawa kana idan ya buɗe
lokacin da suka kasance amota ne yake masa gezo zama yayi Atsakiyar gadon D ɗinsa ya shiga harbawa
da masifar ƙarfi tamkar zai tsinke lokaci ɗaya jikinsa ya ɗauki rawa yayin da lips ɗin sa suka shiga rawa
har haƙoransa na haɗuwa suna bada sautin Ƙat-ƙat-ƙat kana Idanunsa sun kaɗa sunyi jawur tare da
ƙanƙancewa kallo ɗaya zaka masa kasan yana cikin tsananin buƙatar kasancewa da.
Mace da ƙyar ya miƙe yashiga toilet tare da sakarwa kansa ruwan sanyi duk da kuwa sanyin da ake
agarin amma tamkar ƙarawa yake cikin mawuyacin hali da yanayin buƙatuwa ya fito tare da kwanciya
rub da ciki cikin wahalallan hali bacci ya ɗaukesa.

Bayan kwanaki biyar sosai kafar Ramadan yayi sauƙi har ya fara takawa ahankali sosai Mommy da
Khausar da kuma Lamiɗo sukayi farin ciki ganin babu wata matsala.

Aɓangaren Uncle Naseer kuwa abubuwa suna tafiya kamar yanda ya tsara baki daya ya maida hankalinsa
da nutsuwarsa kan Amina yana nuna mata zallar so tare da yimata duk wani abinda take so yayin da
acan ƙasan ransa kuwa soyayyar Khausar na nan kamar yanda yake yana da burin ta kasance matar.

Aurensa kana yana jin

yana son ya haɗa shimfiɗa da ita yana so yaji shin ya ɗanɗanonta yake, domin itace mace ta farko daya
fara so tare da ƙulafacin ɗanɗanar zumanta ita kaɗai duk da cewa yayi Sex da mata kala da ban da ban
bai taɓa sanun cikakkiyar nutsuwa da kwanciyar hankali ba, yanaji awajen Khausar ce kaɗai yake da ya
ƙinin zai samu irin wannan nutsuwar da yake buƙata, duk wani tsarinsa yana yine dan ganin ya samu ya
ɗanɗanin zumanta tare da kawar da ƙishinsa akanta.

Aɓangaren su M Jameel kuwa sun sake samun malam Arɗo da batun barinsu makaranta amma fir
malam Arɗo yaƙi amincewa sam baya so ma suzo masa da batun yayin da M Jameel da Moddibo suka
rage zuwa makarantar domin sukanyi kwanaki uku ko huɗu ba suje ba wani zubin ma har satin ya ƙare
baza sujeba kasancewar sun riga da sun faɗa masa cewa sun ajiye aikin.

Baki ɗaya sun mai da hankali da nutsuwar su akan abinda suka sa gaba na batun aikin da zasu fara a
Company Abban M Jameel.

Abba kuwa kasancewar yanzu damuna ne yasa ya maida baki ɗaya hankalinsa da ragowar kuɗin
hannunsa akan noma musamman nomar Auduga da ake masa saboda yana amfani dashi a
Companyn',sa na Marrocco yana buga manyan zannuwan gadaje sallayoyi da jallabiyoyu na mata da
maza riguna na alfama da dai sauransu.

Wata ranar Litinin tun safe garin Gembu suka tashi da ruwan sama tamkar da bakin ƙwarya sai daf
Azahar ruwan ya tsaya gari yayi sanyi Sanyayyar iska na kaɗawa yayin da bishiyoyi ke rangaji tamkar zasu
karye ko wanni magidanci yana farin ciki da kasancewar wannan Weather mai cike da Ni'imah da kuma
sanya shauƙi.
Acan ɓangaren Moddibo kuwa da yammaci misalin ƙarfe biyar M Jameel ne zaune aka 2sitter yayin da
Moddibo ke kwance akan 3sitter yayi rub da ciki idanunsa alumshe.

Anutse M Jameel ya ɗago kansa daga kan system tare da kallon Moddibo cikin yanayin shaƙuwa da
ƙaunar junansu yace.

“A.J muje gidan Ummi mana”.

Cikin Yanayin buƙata da tsananin sha'awar dake addabarsa ya damƙe ƙasan mararsa waye wan garin yau
yasha ruwan lipton da lemun tsami har ya godewa Allah amma ko kaɗan abinda yake ji bai raguba hakan
yasa ya kasa furta komai.

Jin kamar bai jiba yasa M Jameel sake maimaitawa.

Ahankali Moddibo ya ɗago Idanunsa cikin raunin murya da yanayin harbawan da ɗin sa keyi kana
muryarsa Asanyaye ya kalli M Jameel tare da cewa.

“J bazan iya ba Wallahi bazan iya ba”.

Ya faɗa yana lumshe Idanunsa ajikinsa yana jin tamkar idan ya miƙe ɗin sa zai tsinke baki ɗaya ya rasa
inda zai sanya ransa yaji daɗi ji yake tamkar ya ɗaura hannunsa akai yaita zunɗuma ihu koda zaiji sanyin
Aransa baki ɗaya lips ɗin sa rawa suke idanunsa sun sauya launi zuwa ja jijiyoyin goshinsa sun tashi yayin
da goshinsa ke tsata-tsafo da zufa.

M Jameel kuwa lura da yanayin da yake ciki da yayi yasa ya miƙe tare da nufar kichen kamar ko yaushe
ruwan Tea da lemun tsami da kuma zuma ya haɗa masa kana ya fito ya miƙa masa tare da cewa.

“Gashi kasha”.

Ba musu Moddibo ya sanya hannu ya karɓa domin baya cikin yanayin da zai iya musa masa ahankali
yakai kofin bakinsa tare da kafa kai ya shanye saboda yanda yake ji ajikinsa.

Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe kana cikin sanyin murya yace.

“Tun da kasha ka kwanta Insha Allah zaka ji sauƙi bari zanje gidan Ummi anjima zan dawo bazan daɗe
ba”.

Kai Moddibo ya gyaɗa masa still Idanunsa alumshe M Jameel kuwa key mota ya ɗauka tare da ficewa kai
tsaye gidan Ummi ya nufa.

Yana isa yayi Parking Cike da nutsuwa ya buɗe Murfin motar ya fita tare da duba agogon dake ɗaure
atsintsiyar hannunsa dake nuni da ƙarfe 5:15 lumshe idanunsa yayi kana ya buɗe tare da nufar cikin
Falon bakinsa ɗauke da Sallama shiru falon ba kowa sai dai komai akimtse kana ga ƙamshin tularen wuta
dana Room freshner dake tashi, Murmushi yayi Aransa yace.

“Allah sarki Ummina ba dai tsafta ba”.

Numfashi ya fesar tare da nufar kichen inda yake jiyo motsinta.

Tsaye yasame ta a kichen ta tuƙa tuwo tana kwashewa aleda cike da so da ƙauna yace.

“Ummina”.

Juyawa Ummi tayi fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi ta kallesa kana tace.

“A'a yaushe kashigo?”.

Yana ƙara sa shiga kichen ɗin yace.

“Yanzu Ummina”.

Juyawa Ummi tayi tare da leƙa bayansa”.

Dariya yayi kana yace.

“Nasan wa kike nema ai”.

Murmushi tayi kana tace.

“Eh to ai ban gan shi bane naga Hussain banga Hassan ba”.

Cikin sanyin murya yace.

“Yana gida Ummi yau yana ɗan jin zazzaɓi ne shiyasa bamu zo tare ba”.

Girgiza kai Ummi tayi cike da tausayawa tace.

“Subhanallah Ubangiji ya bashi lafiya Allah ya sawwaƙa mishi”.

Ahankali M Jameel yace.

“Ameen”.

Kana ya matsa jikin kular yana ƙoƙarin budewa yace.

“Ummina yau me kika girka mana ne?”.

Murmushi tayi kana tace.

“Tuwo ne”.

Wara ido yayi tare da cewa.


“Miyar me za kiyi mana Ummi?”.

Tana ƙoƙarin wanke nama ta kallesa kana tace.

“Miyar taushe zanyi”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“A to asamana nama da yawa”.

“Toh Babana za'a saka”.

Ta ida maganar tare da ɗaura naman akan gas kana ta yanka albasa tare da sanya Maggi, citta kamafari
ta rufe.

M Jameel kuwa Attaruhu, Albasa,Tattasai ya haɗa ya wanke tare da gyarawa kana ya ɗauko blander ya
zuba.

Kallonsa Ummi tayi kana tace.

“Ka bari fa da yaji kada yashiga Idon ka”.

Kai ya girgiza tare da cewa.

“A'a Ummi kibari in tayaki nima yau na samu ladan da Asma'u ke samu dana iyama ni zan miki girkin
nan”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Ai dai kam hakan ma Nagode yayi Allah yayi albarka Ubangiji ya tsareka daga sharrin duk kan abinƙi
kuma ai kafin Asma'u samun lada in sha Allah”.

Kallonta yayi kana yace.

“Ameen Ummina”.

Ummi kuwa buɗe tukunyar tayi tare da zuba mai kana ta zuba jejjegen da M Jameel Yayi a blander.

M Jameel dake gyara kifi banda ya juya ya kalli Ummi tare da cewa.

“Ummi ya yau naji gidan Shiru ina Asma'u da Bashir”.

Tana ɓare Maggi tace.

“Sunje gidan Goggon su takwarar Asma'u”.

Kai ya gyaɗa kana yace.


“Ayyah shiyasa yau naji gidan shiru sun barki ke kaɗai to Malam fa?”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Ai dai kam Malam kuma yaje wata rugar Fulani nan kusa amma sai gobe zai dawo acan zai kwana”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Ashe dai yauma kam zan ta yaki ɗebe kewa gidan nan”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Ai dai kam ko zamu kwana ne?”.

Ahankali ya juya ya kalleta tare da cewa.

“Da nafi kowa farin ciki Ummina ace zan kwana gida ɗaya dake”.

Murmushi Ummi tayi batare da tace komai ba.

Ana kiran sallar maghariba suka gama dai-dai lokacin kuma Asma'u da Bashir suka dawo atare, alwala M
Jameel Yayi kana Bashir ma yayi hannun Bashir ya riƙe suka tafi masallaci su kuma sukayi alwala tare da
gabatar da Sallah.

M Jameel kuwa koda suka idar da Sallah basu dawo ba saida sukayi Isha'i sannan suka fito.

Asma'u kuwa Anutse ta fito daga Bedroom bayan ta idar da sallah kusa da Ummi ta zauna kana tace.

“Ummina Ayyah yau aiki ke kaɗai”.

Kallonta Ummi tayi kana tayi murmushi tare da cewa.

“Ina kuwa nayi aiki Ni kaɗai Yayanku yazo ya tayani yau shiya mana miya ma”.

Wara ido Asma'u tayi tare da sakin murmushi kana tace.

“A lallai kai ashe yau zamu sha miyar Yaya kenan”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin.

“A sosai kam zaku sha miyar Yaya Jameel”.

Atare M Jameel da Bashir suka shigo tare da zama.


Gnin shigowarsu yasa ta miƙe tashiga kichen kular tuwon ta ɗauko kana ta koma ta ɗauko Plate-plate ta
dawo Ummi ce ta karba ta sakawa M Jameel kana ta zuba masa miya agefe sannan ta zubawa Asma'u da
Bashir.

Ahankali M Jameel ya kalli Ummi kana ya kalli Asma'u da Bashir sai kuma ya kalli tuwon Ajiyar zuciya ya
sauƙe tare da cewa.

“Toh Ummi muci tare mana musamu ladan cin abinci tare”.

Ɗagowa Ummi tare da kallon sa kana tace.

“Kuma dai”.

Cikin wani irin yanayi ya gyaɗa mata kai kana yace.

“Allah kuwa Ummi”.

Kallonsa ya mayar kan Asma'u tare da cewa.

“Asmeey jeki ɗauko Tray babba ki kawo mana”.

Kai Asma'u ta gyaɗa kana tace.

“Toh Yaya Jameel”,.

Sannan ta miƙe ta shiga kichen ɗin ta ɗauko Babban faranti ta fito dashi tana ƙoƙarin juyewa yace.

“Kawo in zuba mana”.

Murmushi Asma'u tayi tare da faɗin.

“Yah Jameel da kan ka kabari zan zuba mana”,

Girgiza kai yayi kana yace.

“A'a Asma'u kawo in zuba mana bana so ki wahalar da kanki”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Laaa Yah Jameel ka jika Allah zanyi mana”.

Lumshe Idanunsa yayi tare da saurin dafe ƙirjinsa kana ya buɗe Idanunsa tare da Kallonsu ɗaya bayan
ɗaya tare da cewa.

“No Asmeey ki bari in zuba mana kaɗai”.

Saurin Kallonsa tayi tare da miƙa masa Plate ɗin.


Murmushi yayi tare ɗaukar Plate ɗin tuwon ya zuba musu akan babban farantin kana ya ɗauka ya ajiye
musu Atsakiyar su tare da kallon Bashir yace.

“Ɗauko Mana drinks”.

Kai Bashir ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh”,Kana ya miƙe ya ɗauki Plate ya ɗebo drinks da swan water ya ajiye musu.

Ya zauna sai ya zamana M Jameel da Ummi na facing juna Asma'u da Bashir ma na facing juna sai ya
zama sunyi Cycle plate din na tsakiyar su.

Ummi kuwa shiru tayi tare da zubawa M Jameel Ido Batare da tace komai ba kana tana jin wani irin
yanayi mara misaltuwa azuciyarta wanda takasa sanin na menene hakanan ta tsinci kanta da Kallonsa
acikin kwanakin nan.

Ahankali M Jameel ya janyo kular miyar tare da ƙara musu namar da bandan kifi kana fuskarsa ɗauke da
murmushi yace.

“Hayya kuci yau zakuci miyar da baku taɓa ciba irinta ba dan ni nayita ko Ummi?”.

Ya faɗa tare da ɗago kai sai yaga baki ɗaya Idanun Ummi na kansa faɗaɗa Murmushin fuskarsa yayi tare
da cewa.

“Kai Ummina ya dai?,Ai gaskiya na faɗa”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.

“A gaskiya ka faɗa kam”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Toh Ummi kici mana”.

Dariya Ummi tayi tare da girgiza kai kana tace.

“A'a kai da kayi dai ka fara ci muga result ɗin da fuskarka zai bayar kafin mufara ci”.

Wara ido yayi tare da kallon Asma'u da Bashir da suma Kallonsa suke,

“Toh ɗan Auta fara ɗana mana muji”.

Kai Bashir ya gyaɗa kana ya gutsiri loma ɗaya yakai bakin sa lumshe ido yayi tare da haɗa yatsunsa
hannu biyu alamar jinjina kana yace.

“Kai amma miyar tayi daɗi gaskiya Yah Jameel na baka Award”.
Murmushi Ummi tayi tare da kallon M Jameel da Yayi wani irin kyau na ban mamaki tamkar wanda aka
sanya shi a inji aka sake ƙenƙesashi ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.

“Uyummm toni nayi bashi ba”.

Dariya M Jameel Yayi wanda ya bayyanar da Fararen haƙoransa kana yace.

“Toh na yarda Ummi mu duka biyu mukayi”.

Murmushi Asma'u tayi tare da kallon M Jameel kana tace.

“Aikuwa Yaya Kayi ƙoƙari sosai amma muci kada yayi sanyi”.

Kai suka gyaɗa atare kana lokaci ɗaya suka sanya hannunsu akan tuwon tare da kai tuwon bakinsu
lokaci ɗaya suka kalli juna tare da sakin murmushi.

M Jameel kuwa murmushi ya saki tare da lumshe Idanunsa kana yace.

“Ina ma ace zamu kasance ahaka ko yaushe mu riƙa zama tare nuna cin abinci atare da nafi kowa farin
ciki”.

Asma'u da takai nama bakinta ta kallesa kana tace.

“Yah Jameel zamu kasance atare mana Insha Allah”.

Kai ya Girgiza tare da cewa.

“Dole wataran fa zan barku sai dai ku zauna ku uku kuci abinci ba tare dani ba”.

Cikin sauri suka kallesa Bashir yace.

“A'a Yaya Jameel mai yasa zakace haka insha Allah zamu kasance atare”.

Ummi kuwa Kallonsa kawai take.

Murmushi M Jameel Yayi tare da kurɓan drinks kana yace.

”Dole wataran zan barku zanyi tafiya gari mai nisa wanda zan kasance Ni kaɗai acan batare da kuba
nasan zanyi kewar ku kamar yanda zakuyi nawa tunda Abba ya dage dole zan koma Marrocco”.

Kai suka gyaɗa tare da sauƙe ajiyar zuciya kana suka ci gaba da cin abinci batare da wanin su ya sake
magana ba sai dai lokaci zuwa lokaci yakan kallesu tare da sakin murmushi.

Wayar M Jameel ne ya karaɗe wajen da ruri ahankali ya ɗauka tare da sakin murmushi kana yayi Picking
tare da Sallama.

Daga ɗaya ɓangaren kuwa cikin sanyin murya Moddibo yace.


“J ina ka tsaya na jika shiru ko abinci banci ba, sannan kasan bani da lafiya ko dai har yanzu kana gidan
Ummi ne?”.

Murmushi M Jameel Yayi tare da gyara zaman wayar akunnensa kana yace.

“Ayyah sannu A.J Please kaci abinci sannan ka sake shan maganin dana haɗa maka Insha Allah ina
hanya”.

Lumshe idanu Moddibo yayi tare da sakin ajiyar zuciya kana.

“Toh shikenan sai kazo kace ina Gaishe da Ummina”.

Murmushi M Jameel Yayi tare da kallon Ummi dake sauraron duk abinda suke faɗa kana yace.

“Zata ji”,daga haka ya katse kiran.

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.

“Ohh ina ga dai wannan ko kunyi Aure gida ɗaya zaku zauna bakwa iya minti talatin batare da kunga juna
ba ko kuma kunji muryan juna”.

Murmushi M Jameel Yayi kana yace.

“Ai dai kam dole watarana arabu”.

Jinjina kai Ummi tayi,tana murmushi kana suka cigaba da cin abincin.

Bayan sun cinye tuwon farantin M Jameel ya Kalli Ummi tare da cewa.

“Ummi aƙara mana yau ina jin daɗin abinci ina so inci³ incika cikina dan ban sani ba sai kuma yaushe zan
sake ci”.

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.

“A'a to ai ko yaushe ma kakeso ai zaka zo kaci”.

Lumshe Idanunsa yayi tare da buɗe su akan Ummi kana yace.

“Toh Ummi kwanan nan zamu fara batun aikin nan kinga in dan na tafi Marocco ai bazan dinga samun
ciba”.

Kai ta jinjina tare da faɗin.

“Ai in dai nan da ne ba nisa bane dashi idan ya kama sai inmaka miya da komai duk zan aika maka dasu
idan yaso saika na sawa a fridge”.

Murmushi Yayi tare da cewa.


“Hmmyyym Ummina Allah ya ƙara miki nisan kwana mai amfani Allah ya barmu tare”.

Jingjna kai tayi tare da faɗin.

“Ameen Babana Allah ya ƙara maka nisan kwana inga har jikokin ka”.

Murmushi yayi tare da kallonta kana yace.

“Hmmm Ummina kenan.

Kin ko san in sha Allah ƴata ta farko sunanki zan samata,

Na kuwa tabbatar zata ga soyayya ko ƙuda bazan bari ya taɓa ta ba”.

Kallonsa Ummi tayi tare da cewa.

“Jamiluuu na”.

taja sunan tana murmushi haka nan take jin daɗin kiran sunan sa.

Bayan sun kammala cin abincin Asma'u ta miƙe tare da tattare Plate ta Kai kichen M Jameel kuwa da
kansa ya mike ya ɗauki kular abincin ya kai kichen Ummi kuwa Kallonsa ta riƙa yi cike da so.

Bayan ya ajiye ya fito, woje ya nufa yana cewa

“Bari in ɗauko abu a mota".

Toh Ummi tace kana ta meda hankali kan tv.

Jim kaɗan da fitar da ya shigo riƙe da kwalayen waya masu kyau.

Ƙirar Samson, kana ya dawo ya zauna gefen Ummi Asma'u da Bashir suka zauna daga gefensa gyaran
murya yayi tare da fuskantar Asma'u kana yace.

“Ga woyoyinku nan Asma'u yau dai na cika alƙawarin ko”.

Cikin tsananin jin dadi Bashir ya ruggumshi, yayinda Asma'u kuwa Ummu ta ruggume.

Cikin son juna suka rinƙayi mishi godiya tare da fatan al'khairi.

Murmushin jin dadi yayi tare da shafa kan Bashir kana yace.

“Asma'u yanzu ke wani irin makaranta kike so?”.

Murmushi tayi tare da cewa.


“Yah Jameel duk makarantar da ka zaɓa min ina sonta ina farin ciki da ita”.

Jinjina kai yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya kana yace.

“Zan kuwa zaɓa miki wanda ya dace dake Insha Allah naga keda ƙawarki kusan ra'ayin ku ɗaya ko
yaushe amman wannan karon an samu akasi ita Jenouelist take fata naga ke kuma likitanci kike son
karanta”.

Kallon Bashir yayi tare da cewa.

“Kai kuma wani irin Makaranta kake so?”.

Murmushi Bashir yayi kana yace.

“Duk wanda ka zaɓa min Yaya”.

Lumshe idanu M Jameel Yayi tare da cewa.

“Insha Allah kuwa zan zaɓa maka ina ganin Law zaka karanta zaifi dacewa da kai”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana ya tsira musu ido tare da cewa.

“Asma'u”.

Kanta ta ɗago tare da cewa.

“Na'am Yaya”.

Anutse ya kalleta cikin yanayin nutsuwarsa da alamun rashin wasa yace.

“Kinga ke ƴa macece ita rayuwar duniyar nan duk i da ƴa mace ta tsinci kanta ta tsare mutuncinta da
darajar ta shine abu mafi daraja ki kiyaye tarbiyyar da muka sha wahalar baki nida Ummi kada ki kunya
tamu kada kisa ta baƙin ciki”.

A hankali ya sauƙe numfashi tare da gyara zamansa kana yace.

“Saboda ke ƴa macece ke mukafi taraddadi akan ki kinga yanzu ga Bashir amma bana ta raddadi akansa
kamar ke mace”.

Asma'u kuwa ƙasa ta sakeyi da kanta batare da tace komai ba sai wasa da yatsun hannunta da take yi.

lumshe idanunsa yayi kana yace.

“Burina da fatana inga mun kasance gida ɗaya muhalli ɗaya wallahi akanki da Bashir da kuma Ummin mu
yasa nake so inyi Aure inga muna tare”.

Sai kuma ya kalli Bashir da shima yayi ƙasa da kansa kana yace.
“Ina so inga lokacin tafiyarku makarantar kana inga lokacin dawowan ku a idona sannan insan kalar
mutanen da kuke mu'amala dasu".

Sai kuma ya juyo ya kalli Asma'u cikin yaƙini yace.

“Na yarda da ƙawancen ku da Khausar saboda tana da tarbiyya duk da kuwa tana da rawan kai”.

Numfasa yayi tare da kallon ta kana cikin raunin murya yace.

“Asma'u ki kula da rayuwarki sannan kisan irin mutanen da zaki dinga alaƙa dasu idan kuma har Aure
kike so Asma'u ki faɗa min idan yaso idan kikayi aure sai ki cigaba da karatun ki agidan mijinki kada ki
ɓoye min ki faɗa min komai ki ɗaukeni tamkar ƴar Uwarki mace”.

Cike da kunya Asma'u tayi ƙasa da kanta tare da girgiza kanta kana tace.

“A'a Yah Jameel nikam karatu zanyi”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Kin tabbatar ba Aure kike so ba sannan babu wanda kike so?”.

Cike da kunya ta girgiza masa kai tare da faɗin.

“Yaya Jameel Ni kuma wazan so kuma babu wanda ke zuwa gurina”.

Dariya M Jameel Yayi tare da kallonta kana yace.

“Mun shiga uku Ummi kadde ƙanwar tawa baƙin jini take dashi?”.

Murmushi Ummi dake aikin Kallonsu tayi tare da faɗin.

“Ba wani baƙin jini kawai dai dake tana kiyaye kanta ne babu wanda ke kawo mata wargi”.

Jinjina kai yayi tare da dai-dai-ta nutsuwarsa kana yace.

“Toh shikenan Asma'u tun da dai kin bani tabbacin karatu kike so daga nan harki kai digir-gire ki gama
har ki taka duk kan matakin da kike so nayi al'ƙawarin zan taimaka miki da duk kan ƙarfina da kuɗina
muddin ina numfashi zan tsaya miki”.

Kallon Bashir yayi tare da cewa.


“Sannan kai kuma Bashir zaka karanci fannin Law tunda kana da ilimin addini ina da yaƙinin zaka tsaya
akan gaskiya duk runtsi duk wuya kada Kabi bayan ƙarya ka kasance mai al'ƙawarin da rikon amana
aduk inda ka tsinci kan ka”.

Jinjina kai Bashir yayi kana yace.

“Yah Jameel Insha Allah Nayi alƙawari zan kasance ayanda kake fata”.

Hira suka cigaba dayi sosai irin wanda suka ɗauki tsawon lokaci basuyi irin saba wanda har dare yaraba
basu lura ba.

Ahankali Ummi dake murmushi ta daga kanta Idanunta suka sauka akan agogon dake manne abango
wanda ke nuni da ƙarfe sha biyu da minti goma,Cikin sauri ta kalli M Jameel tare da cewa.

“Jamilu”.

Anutse ya ɗago ya kalleta tare da cewa.

“Na'am Ummina”.

Ta sauƙe ajiyar zuciya tare da Kallonsa kana ta sake kallon agogon zuciyarta na bugawa tayi saurin dafe
ƙirjinta kana tace.

“Ka kalli time fa”.

Cikin sauri M Jameel ya juya Kalli agogo tare da kallon Ummi kana...!

Cikin sakin fuska yace.

“Ummi yau anan zan kwana”.

Cike da mamaki Ummi ta juya ta kallesa, domin tunda Allah yasa tayi aure agidan mahaifin Asma'u bai
taɓa kwana ba, sai dai yakan zo aduk sanda yaga dama, a hankali ta sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.

“Anan zaka kwana?”.

Kai ya jinjina tare da faɗin.

“Eh zan kwana Ummina”.

Kallon Ummi Bashir yayi cike da farin ciki ya langwaɓar da kai kana yace.

“Ayyah Ummi ki barshi kinga yanzu ma dare yayi ki gani fa sha biyu hadda kwata dare fa ya riga da yayi
nisa”.

Cikin sanyin murya me ɗauke da farin ciki Asma'u tace.


“Gaskiya dai kam mu kwana kawai Yah Jameel, yau nayi matuƙar farin ciki zamu kwana agida ɗaya Allah
ya nuna mana ranan Aurenka mu kasance atare na har abadan”.

Murmushi M Jameel yayi tare da shafa sajensa kana ya tsira musu ido tare da lumshe idanunsa, a hankali
ya sauƙe ajiyar zuciya kana yace.

“Asmeey zamu kasance atare in sha Allah zanyi Aure kana zaku kasance gida me kyau da na al'farma da
kwanciyar hankali, ni kaina bansan kamannin gidan ba amma na sani gida ne mai masifar kyau da ɗaukar
hankali zan riska in sha Allah”,

Sai kuma ya sauƙe numfashi tare da lumshe idanunsa kana yaci gaba da cewa.

“Wanda kowa ke burin samu, in Sha Allah zan sameshi, domin inaji ajikina na kusa isa wannan gidan
kafin ku iso zan kasance cikin farin ciki amma idan ina tare daku zanfi farin ciki na zai fi nin kuwa”.

Cikin yanayin sanyin jiki ya tsira musu ido su duka ukun.

Ummi kuwa idanu ta zuba masa ko ƙyaftawa ba tayi wani irin yanayi takeji azuciyarta, wanda takasa
tantance na menene.

Asma'u kuwa murmushi tayi tare da Kallonsa kana tace.

“Yaya Jameel Allah ya baka mace ta gari wacce zata kula da Ummin mu tamkar yanda kake kulawa da ita
sannan ta ƙaunace mu tamkar yanda kake ƙaunar mu”.

Murmushi yayi kana ya lumshe idanunsa tare da cewa.

“Insha Allah Asmeey matar da zan Aura, macece wacce ta fito daga babban gidane masu tarbiyya da
kamala, wacce zata riƙe Ummina daku tamkar Iyayen ta da kuma ƙannenta”.

Sai kuma ya numfasa tare da tsira mata ido.

Kai Asma'u ta gyaɗa murya cike da jin daɗi tace.

“Ni kuwa Yah Jameel Nayi maka al'ƙawarin zan kasance mata tamkar yar uwa Aminiya yadda kake fata
har ma fiye da haka”.

Sassayan numfashi ya fesar kana yace.

“Alhamdulillah Asmeey idan kika min haka ko a ina na kasance zanyi al'fari dake sannan zanyi farin ciki”.

Sai kuma ya maida kallonsa kan Bashir tare da cewa.

“Yauwa kai kuma Bashir”.


Anutse ya ɗago kansa tare da faɗin.

“Na'am Yah Jameel”.

cikin sanyin murya yace.

“Bashir ka maida hankalin ka akan karatun ka, kada ka biyewa aboka nan banza kasan dawaye ya dace
kayi abota kada ka biyewa matan banza da abokan baza kada kasa Ummi tayi Allah wadai da halayyar
ka”.

Ƙasa da kai Bashir yayi yayin da Ummi kuma shiru tai tana mai jin daɗin Nasiyyar da yake wa ƙannensa.

A hankali ya numfasa kana yaci gaba cewa.

“Bashir aikin Law aikine mai matuƙar daraja da muhimmanci sai dai wasu sun ɓata aikin da cin hanci da
rashawa da tauye haƙƙin masu gaskiya, da tozartasu, ina so kamin alƙawari kai zaka kasance mutum mai
adalci da karamci akan aikinsa wanda duniya za tayi al'fahari da kai sannan Ummina tayi farin ciki da
rayuwarka”.

Sai kuma ya ɗanyi shiru yana kallon yadda Bashir ke gyaɗa masa kai alamar nasihar na ratsashi, cikin
yanayin lallashi da jan hankali yaci gaba.

“Dan Allah Bashir kada ka bari adalilinka Al'umma su la'anci Ummina suyi Allah wadai da haihuwarka da
tayi”.

Cikin rawan murya Bashir yace.

“In sha Allah zan zama yanda kake da buri har ma fiye da haka Yah Jameel”.

Lumshe Idanu M Jameel Yayi tare da shafa sajensa kana cikin sanyin murya yace.

“Nagode Bashir tabbas ko bayan ba nan Idan ka kasance mutumin kirki zanyi farin ciki, sannan ka kula
min da Ummina da Asma'u kada ka bari hawayen baƙin ciki ya zubo daga idanunsu ni dai burina kayi min
wannan al'ƙawarin”.

Jinjina kai Bashir yayi tare da cewa.

“Nayi maka alƙawari Yah Jameel Ummi da Asma'u baza su taɓa baƙin ciki dani ba, kullum zan saka su
farin ciki sannan zan kasance mai riƙon alƙawari aduk inda na tsinci kaina”.

Murmushi M Jameel Yayi Idanunsa alumshe yace.

“Alhamdulillah³ Allah na gode maka”.

Anutse ya juya ya kalli Ummi data tsira musu Ido kana cikin sanyin murya yace.
“Yauwa Ummina faɗamin me kike buƙata ko kuma kike so arayuwar ki nayi miki?”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe kana tayi murmushi tare da cewa.

“Toh ni kuma meya rage arayuwa wanda baka yimin ba Jamilu?

Ai ni kam kayi min komai sai dai Ubangiji Allah ya maka albarka Allah yabaka ƴaƴan da zasu yi maka
biyayya”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Ameen Ummina amma yanzu baki da wata damuwa ko buƙata?”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Bani da wani damuwa ko buƙata aduniya Jamilu, domin kafin na buƙaci komai ma kiyi min”.

Hannunsa biyu ya ɗaga sama tare da faɗin.

“Alhamdulillah Allah Nagode maka ya Ubangijin Allah ka bani damar da duk ɓuƙatar da mahaifiyata take
dashi kafin ma ta buƙata nayi mata shi”.

Murmushi tayi kana tace.

“Ameen Ubangiji Allah ya maka albarka Allah ya rufa maka asiri duniya da lahira Allah yasa ƴaƴan ka su
ramamaka abinda kayi mana”.

Still Fuskarsa ɗauke da murmushi yace.

“Ameen ya Allah”.

Ummi kuwa ahankali ta daga kanta gani tayi har ƙarfe uku kallonta ta mayar kansu kana tace.

“Yanzu yaranan baza ku tashi kuje ku kwanta ba ku dubi time fa”.

Atare Asma'u da Bashir suka ce.

“Toh Ummi am gaba ɗaya yau bama jin baccin ma”.

Murmushi M Jameel Yayi kana yace.

“Ai dai kam”,

Ummi kuwa murmushi tayi kana suka cigaba da hira.

Jin ankira Sallar ƙarfe huɗu yasa Ummi kallon su tare da faɗin.

“Toh yanzu kam mutashi muyi alwala muyi nafillah mu rufe wannan daren da roƙon Ubangiji”.
Bayan duk sunyi Al'wala ne suka dawo falo duk suka shimfida Sallaya sukayi nafila raka'a huɗu-hudu.

M Jameel kuwa acikin sujjadar ta ƙarshene yace.

“Ya Allah katsare min Mahaifiyata da ƙannena Ubangiji ka zama gatansu anan duniya da lahira ya Allah
ka tsaresu daga sharrin abin ƙi Ubangiji ka inganta rayuwar Asma'u da Bashir ya Allah ka tabbatarwa da
A.J na al'khairi a cikin samun mace tagari wacce zata kula da ɗawainiyarsa ya Allah kabiyawa duk
musulmi ɓuƙatar su na Alkhairi”.

Ko wannensu haka ya dinga addu'a saida aka kira Assalatu kafin suka miƙe Shida Bashir suka tafi
masallaci Asma'u da Ummi kuwa anan suka Idar da Sallah.

Bayan sun dawa daga masallaci M Jameel ya kwanta akan 3sitter Ummi Atake Bacci mai daɗi ya ɗaukesa.

Ummi da Asma'u kuwa kichen suka shiga tare da soya musu soyayyen dankali da ƙwai kana suka tafasa
ruwan tea da yaji citta da kanumfari sai kuma tayi musu ɗumamen tuwon jiya, ganin yadda yaketa zuba
tururine yasa Asma'u tas hannun da nufin buɗe murfin tukunya, zafin da taji ya ratsa ƴan yatsunta ne
yasa ta saki karfin ya faɗi ƙasa tare da bada ƙara.

Cikin sauri Ummi ta kalleta kana cikin ƙasa da murya tace.

“Kai Asma'u kiyi a hankali mana kada ki tashi yayan ku, bakiga jiya bai samu bacci ba”.

Murmushi Asma'u tare da gyaɗa mata kai kana tace.

“Toh Ummi”.

Har misalin ƙarfe tara M Jameel bai far kaba Ummi kuwa toilet tashiga tayi wanka bayan ta shirya ta fito
falon har zuwa lokacin M Jameel na bacci ahankali ta zauna agefensa tare da tsira masa idanu tana
kallon yanda yake baccin cikin kwanciyar hankali tamkar yana murmushi kyawun fuskarsa ya sake
nunkuwa fiye da ko yaushe.

Asma'u data fito daga kichen ta kalli Ummi kana ta saki murmushi tare da cewa.

“Kayyy Ummi irin wannan kallon sai kace kin samu TV ”.

Sai asannan Ummi ta ɗauke Idanunta daga kansa ta mayar kan Asma'u tare da yi mata daƙuwa.
Murmushi Asma'u tayi kana tace.

“Ai gaskiya ne”.

Bashir daya shigo Bedroom din yayi dariya kana yace.

“Gsky dai Ummi kwanan nan kina yawan kallon Yah Jameel ko dan yafi mu kyaune?”.

Wara ido tayi tare da sakin murmushi kana tace.

“Waya faɗa maka yafi ka kyau ai kafisa”.

Murmushi yayi kana yace.

“Ummina kin dai faɗa min inji daɗi ne kawai”.

M Jameel kuwa cikin bacci yake jiyo hiransu sama-sana ahankali ya motsa.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da kallon sa kana tace.

“Toh katashi kayi Breakfast. Idan yaso sai ka koma baccin”.

Cikin sauri ya buɗe Idanunsa tare da Kallon Ummi kana yace.

“Uhmmm Ummi sai anjima”.

Kansa ta shafa kana tace.

“A'a tashi kaci abinci, bana son bacci da yunwa Babana”.

Hannunta ya riƙe kana yace.

“Naji daɗina Ummina ta kirani da Babana Abbana ya kirani da Babana”.

Miƙewa yayi ya zauna tare da cewa.

“Ummina banyi wanka ba sannan banyi brush ba ba zan iya Breakfast ba”.

Girgiza kai Ummi tayi tare da faɗin.

“Aikam dai gashi tun ɗazu na bawa Bashir kuɗi ya sayo maka Brush kafin ka tashi ga Brush ga Maclean
kayi”.

Miƙewa yayi kana ya ɗauka, toilet dake falon yashiga ya wanke bakakinsa.

Asma'u kuwa tun shigansa toilet ta Miƙe tankwaso musu kayan Breakfast ɗin yau ma kamar jiya haka
atare sukayi Breakfast ɗin.

A hankali ya kai kofin tea bakinsa sai kuma yayi sauri ajiye cup din jin wayarsa ta hau ruri Asma'u dake
kusa da wayar ta miƙa masa karɓa yayi tare da sakin murmushi kana yayi Picking tare da cewa.
“Assalamu Alaikum A.J”.

Daga ɗaya ɓangaren Moddibo ne yace.

“J yana jika shiru gashi Innayi ta haɗa mana Breakfast na kasa ci ni kaɗai”.

Murmushi M Jameel yayi tare da kallon Ummi, Asma'u,da Bashir kana yace.

“A.J gani tare da Ummina da Asma'u da kuma Bashir muna Breakfast tray ɗaya kamar yanda mukayi jiya,
ina jin farin ciki inaji kamar wani gurbi na cike wanda ban samu damar cike saba tsawon shekaru”.

Lumshe idanu Moddibo yayi kana ya gyaɗa kansa tabbas ya fahimci farin cikin da M Jameel ke ciki ajiyar
zuciya ya sauƙe tare da cewa.

“Shikenan hakan yayi kyau bawa Ummina mu gaisa”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare da miƙawa Ummi wayar.

Cike da so Ummi tace.

“Babana na ƙwace maka Amini ko?”.

Murmushi Moddibo yayi wanda take iya jiyo sautin sa kana cike da ladabi yace.

“Ayyah Ummina bakomai ai kawai ina kewar sa ne Ina kwana?”.

Murmushi tayi tare da faɗin.

“Lafiya Lau ya Innayi?”.

Ahankali yace.

“Tana lafiya tace agaishe ki”.

Daga haka sukayi sallama tare da katse kiran Bayan sun kammala Breakfast ɗin Asma'u ta tattare
kwanikan kare da kaiwa kichen kana ta dawo ta gyara wajen.

M Jameel kuwa jingina kansa da guiwar Ummi yayi kana suka cigaba da hira cike da tsananin ƙaunar
junansu...!

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci 1k ne kacal 0661110170 GTBank
AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*
SAKAYYA

26

Acan ɓangaren gidan Lamiɗo kuwa Ramadan ya fito daga Bedroom da gudu kai tsaye Bedroom din
Mommy ya nufa afalo suka ci karo da Hajiya Bunayya wani irin kallo tabisa dashi dai-dai lokacin da
Khausar ta fito sanye cikin riga da skirt na less ɗinkin ya zauna ɗas ajikinta kana ta sanya Blue Black hijabi
mai Facemaks jikinta na fitar da sanyayyan ƙamshin turaren Oud Ma'aruf fuskarta ɗauke da simple
Make-up.

Cak ta tsaya tare da kallon Hajiya Bunayya data tsirawa Ramadan idanu ganin tsayuwar Khausar yasa
Hajiya Bunayya sakin murmushi tare da cewa.

“Ikon Allah Ramadan ƙafa tayi sauki sosai”.

Sai kuma ta juya tana cewa.

“Ki cewa Aysha ankawo kayan tazo ta gani ta zaɓa mana”.

Girgiza kai Khausar tayi tare da kallon Ramadan dake cewa.

“Addah Khausi ƙafana tayi sauƙi”.

Murmushi tayi tare da shafa kansa kana tace.

“Alhamdulillah Ramadan amma ka daina wannan gudun har yanzu ƙafanka baiyi ƙwari ba”.

Kai ya gyaɗa mata kana yabi bayanta zuwa Bedroom ɗin Mommy bakinsu ɗauke da sallama.

Ƙara sawa Ramadan yayi tare da faɗawa jikin Mommy kana yace.

“Mommy ƙafana yayi sauƙi badan Addah Khausi tace kar inyi gudu ba da nayi kin gani”.

Murmushi Mommy tayi tare da shafa kansa kana tace.

“Masha Allah mun godewa Allah, ka riƙa bi ahankali insha Allah zaiyi sauki”.

Khausar na murmushi tace.

“Mommy zanje gidan su Asma'u”.


Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.

“Toh Allah ya kiyaye ki gaishe su amma kada ki daɗe Allah ya tsare”.

Kai ta gyaɗa kana ta fice.

Tare da Sallama ta ɗan tura ƙofar Falon.

Tana shiga Idanunta ya sauka akan M Jameel dake zaune kan 2 sitter murmushi ta sakar masa kana tace.

“Laa Yah Jameel”.

Murmushin ya maidamata tare da faɗin.

“A'a Lelewal kece yau agidanmu?”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Eh mana Yah Jameel na kawowa Ummi ziyara ne kuma nayi kewar Asmeey”.

Wara ido yayi tare da cewa.

“Iyeee Lelewal wato wariya zaki nuna min ni bakiya kewata ba? Rabona dake tun randa kuka karkare
makaranta fa”.

Rufe fuska tayi tare da cewa.

“Kai Yah Jameel nayi mana, duk makarantar ma nayi missing ɗinta da kowa nata”.

Murmushi yayi kana cikin yanayin fara'arsa yace.

“Yanzu naji bayani amman harda Modibbo kinyi kewarsa?”.

Da sauri ta tura baki tare da cewa.

“Kewar masu sona nayi banda maƙiyana”.

Dariya mai sauti yayi tare da cewa.

“Maƙiyi kuma, kai a'a kam Lelewal”.

Ita dai Khausar juyawa tayi ta kalli Ummi

kana tace.

“Ummi ina yini?”.

Cike da kulawa Ummi tace.


“Lafiya lau ya Ramadan da ƙafa?”.

Gyara zama Khausar tayi kana tace.

“Yaji sauƙi Ummi yanzu yana takawa ko ina”.

Atare suka ce Masha Allah Ubangiji Allah ya ƙara sauƙi”.

Murmushi tayi kana tace.

“Ameen”.

Kana suka ci-gaba da hira wanda duk mafi yawan hiran nasiyya M Jameel yake musu kan sukula da
rayuwar duniya kana suka sance masu riƙe al'ƙawari tare da kare mutuncin su.

Ganin rana ya fara yasa Asma'u ta kalli Khausar tare da cewa.

“Khausy mushiga kichen muyi girki”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da miƙewa ta cire hijabinta tabi bayan Asma'u abakin ƙofar ta tsaya tare da
juyawa falon kana cike da kulawa tace.

“Yah Jameel mai za'a dafa maka?”.

Murmushi yayi kana yace.

“Duk abinda kika dafa min Khausar ina so zanci”.

Jinjina kai tayi tare da sakar masa da murmushi kana tace.

“Toh shikenan Yah Jameel Insha Allah zanyi maka abinda zaka so da izinin Ubangiji”.

Khausar na shiga kichen suka fara aikin cikin nutsuwa da ƙwarewa Dambun shinkafa da yaji Vegetables
suka Atake kichen ɗin ya gauraye da ƙamshi Warmers me kyau ta ɗauka ta zuba masa kana ta ɗauki
Bowl ta haɗa masa Fruit Salat mai sanyi sannan ta ɗaura Ababban faranti ta fito.

Kallon M Jameel dake hira da Ummi tayi kana tace.

“Yah Jameel gashi na kawo maka”.

Wara ido yayi kana fuskarsa ɗauke da murmushi yace.

“Wai Lelewal duka Ni kaɗai?”.

Kai ta gyaɗa masa kana tace.


“Eh aina Malamina ne yanzu ma zan gasa maka nama gashin tukunya”.

Jinjina kai yayi tare da cewa.

“Lallai Khausisi naji daɗina na dafa tudu biyu ga Malami sannan kuma yaya saura cikon tudun dafawa na
uku”.

Murmushi tayi tare da zama gefensa kana tace.

“in sha Allah in akwai na huɗuma duk zaka taka Yaya Jameel”.

Yana sa Fruit Salat abakinsa ya lumshe Idanunsa kana ya kalli Khausar tare da cewa.

“Uhm Yummmy na daɗe bansha Fruit salat mai daɗi irin wannan ba Lelewal da alama dai na musamman
ne”.

Asma'u data fito daga kichen ta wara ido kana tace.

“Kai Yah Jameel har nawa?”.

Kai ya jinjina mata tare da sanya dariya kana yace.

“Iyee sosai ma Asmeey nifa yau komai jinsa nake na daban, girkinma tun tuni yake cika min hanci da
ƙamshi”.

Kallon yanda yake dariya Khausar tayi wanda har ya bayyanar da Fararen haƙoransa kana idanunsa
alumshe haskensa ya sake bayyana kana sajensa sunyi luf-luf suna sheƙi.

Ajiyar zuciya ta sauƙe still Fuskarta ɗauke da murmushi tace.

“Yah Jameel kaima yau na da banne kyawunka ya sake nunkuwa tamkar Balarabe”.

Bashir da Asma'u kuwa haɗa baki sukayi wajen cewa.

“Wallahi kuwa Muma duk akwanakin nan haka muke kallonsa”.

Wara ido yayi still Yana Shan Fruit Salat ɗin yace.

“Uhm ko dai dan na kusa Aure ne yasa kuke kallon kyawuna”.

Saurin Kallonsa Ummi tayi tare da cewa.

“Sai kace gobene auren.

Murmushi yayi tare da faɗin.

“Uyumm Ummina”.
Sai kuma ya maida Kallonsa kan Khausar tare da cewa.

“Lelewal zaman gida ya kusa ƙarewa ko?”.

Kai ta jinjina tare da cewa.

“Eh Yah Jameel Insha Allah result ɗin mu na fitowa za'a samomin Admission”.

Jinjina kai yayi tare da cewa.

“Masha Allah, haka muke fata, ku dai kiyaye ku tsare mutuncinku a duk inda kuka riski kanku”.

“Insha Allah Yah Jameel na maka alƙawari zan kasance fiye da hakan ma”.

Kallon Asma'u Ummi tayi tare da cewa.

“Kawo mana abincin muci”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare da miƙewa ta zuba musu ababban faranti Khausar kuwa drinks ta kwaso musu.

Kana suka zauna kallon Ummi M Jameel yayi tare da langwaɓar da kai kana yace.

“Ummi ya aka cire ni adangi gaskiya nima ajuye muci tare”.

Murmushi Khausar tayi tare da cewa.

“Toh Yah Jameel bari na zuba mana”.

Ta faɗa tare da juye nasa akan faranti kana suka zauna tare da sanya farantin Atsakiyarsu Ummi da
Khausar na facin juna Asma'u da M Jameel na facing juna haka suka gama cin abincin cike da nishaɗi.

Suna gamawa ana kiran sallar Azahar M Jameel ya Miƙe tare da shiga toilet ya ɗaura alawala kana ya
nufi masallaci Asma'u da Khausar kuwa wajen suka gyara tare da kwashe kwanukan suka kai kichen kana
suka wuce Bedroom ɗin Asma'u suka ɗaura alwala tare da gabatar da sallah bayan sun idar suka fito
zuwa falo.

Bayan an isar da salla.

M Jameel yana shigowa ya kalli Ummi dake zaune kan 2sitter kana yace.
“Toh Ummi zan tafi ina jin jikina aɗaɗɗaure tun jiya da daddare fa rabona da wanka ji nake kamar nayi
wata banyi wanka ba”.

Cikin sauri Khausar ta miƙe tare da cewa.

“Yawwa Yah Jameel dan Allah ka sauƙeni agida Mommy tace kar in daɗe”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh Lelewal muje mana”.

Kai ta gyaɗa tare da riƙe hannun Asma'u kana suka fita.

Ummi kuwa haka nan ta tsinci kanta da ɗago kai ta zuba masa Ido batare da tace komai ba.

Ahankali ya kalli Ummi ganin shi take kallo yace.

“Ya dai Ummina?”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da girgiza masa kai kana tace.

“Bakomai ba zaka bari sai anjima ba?”

Girgiza kai yayi tare da cewa.

“Um-um Ummi ina so in tafi sauri nake”.

Cikin sanyin murya tace.

“Toh saurin me kake?”.

Langwaɓar da kai yayi kana yace.

“Toh Ummi banyi wanka bafa ba kuji na fara tsami ba?”.

Wara ido Asma'u tayi tare da sanya dariya kana tace.

“Ƙamshi dai kake Yah Jameel”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Gwara dai Inje inyi wanka”.

Dai-dai lokacin wayarsa ta hau ruri yana cirowa yaga Moddibo murmushi yayi tare da kallon Ummi kana
yace.
“Kinga fa Moddibo na kira na yanzu zaice ko Breakfast baiyi ba yana jirana, haka yake dake cin abinci bai
damesa ba idan bana nan sai yace yana jirana, yaita takura min da kira idan kuma ina nan yaƙi ci”.

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.

“Toh yanzu tafiya zaka yi?”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Eh Ummi”.

Cikin sanyin murya tace.

“Toh ka kira Baban nawa yazo nan kuci abincin”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Ummi zan tafi Insha Allah da yamma zan zo musha hiran mu”.

Sai kuma ya matsa kusa da ita tare da ranƙwafawa kanta ya kai bakinsa dai-dai kunnenta kana yace.

“Ummi sai anjima da daddare zanzo insha Allah musha hiran mu sannan in faɗa miki matar da zan Aura
da kuma matar da na zaɓawa A.J na”.

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.

“Toh shikenan Babana Allah ya kai ka lafiya ya dawo min da kai lafiya Ubangiji Allah yama SAKAYYAH da
mafificin Aljanna”.

Murmushi yayi tare da durƙusawa agabanta cike da jin daɗin Addu'ar ta yace.

“Ameen Ummina Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.

Ummi kuwa hannu ta sanya acikin sumar kansa tana shafawa kana tace.

“Allah ya rufa maka asiri duniya da lahira Allah yasa kagama da duniya lafiya Allah yasa Aljanna ce
makomarka Allah ya tsareka da dukkan sharrin abinƙi Ubangiji ya raba ka da sharrin mai sharri”.

Tafin hannunta ya riƙe kana yace.

“Allah ya amsa addu'o'in ki Ummina, shiyasa nake da yaƙinin cewa duk abinda ya sameni, na tabbata
ƙaddarar ce da Ubangiji ya rubuta minne amma addu'ar ki ba zai taɓa bari wani mummunan abu
yasame niba Nagode sai dai in daga Allah ne”.

Bashir daya shigo kuwa Ido ya zuba musu yana kallon yanda Ummi ke sanya masa albarka tare da
adduo'i shi kuma yana Amsawa da Ameen.

Da sauri ya isa ya durƙusa gefen yayan nashi tare da cewa.


“Ayi addu'o'in damu”.

Murmushin Ummi tayi tare da shafa kansu,l.

Asma'u da Khausar kuwa tuni suka fita suna jira ganin shiru bai fito bane yasa Khausar leƙawa Falon kana
tace.

“Yah Jameel baza mutafi ba. Mommyna fa tace kada in wuce Azahar”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Gani nan zuwa Lelewal”.

Kai Khausar ta gyaɗa kana suka cigaba da hira da Asma'u.

M Jameel kuwa fita yayi har ya isa baranda sai kuma yayi baya tare da leƙawa falon kana yace.

“Ummi yau ba rakiya ne ko dan bamu zo da Babanki bane?”.

Ummi kuwata

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da Kallonsa kana tace.

“Na'am Jamilu”.

Langwaɓar da kai yayi kana yace.

“Ummi yau dai dan ban zo da Babanki ba ba rakiya”.

Murmushi tayi tare da faɗin.

“Toh muje in rakaka Babana”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh Nagode”.

Sannan suka fita afalon kai tsaye jikin motarsa ta nufa ta buɗe masa.

Murmushi yayi tare da shiga kana ya maida kallonsa kan Bashir tare da cewa.

“Bashir yau dai na ƙwace maka fadar ka”.

Murmushi Bashir yayi tare da kallon M Jameel kana yace.

“Ba komai Yah Jameel na bar maka lokacin kane ai”.

Ahankali Ummi ta tura Murfin motar tare da rufewa.


M Jameel kuwa Ido ya zubawa Ummi ta ɗan tsakanin glass din Motar batare daya jaba Itama Ummi
Idanu ta zuba masa tare da juya masa hannun alamar ya dai?.

Sauƙe glass ɗin motar yayi tare da sanya babban yatsan sa acikin bakinsa yana ɗan ciza farcen a hankali.

Cikin tsare sa da ido tace.

“Ya dai?”.

Sauke glass ɗin motar yayi tare da zuba mata Ido.

Girgiza mata kai yayi still baice komai ba.

Matsawa jikin Glass din tayi kana tace.

“A'a wai meye haka?”.

Ƙasa cewa komai yayi still Idanunsa na kanta.

Sunkuyawa jikin Glass din Motar tayi kana tace.

“Ya dai?”.

Ahankali ya lumshe idanunsa tare da jan dogon numfashi kana ya fesar cikin rawan murya yace.

“Ban sani ba Ummi”.

Da mamaki tace.

“Baka sani ba kuma?”.

Kai ya gyaɗa mata still ya tsansa na bakinsa.

Cike da kulawa tace.

“Toh me kake so?”.

Juyawa yayi ya kalli faɗin ilahirin gidan nasu kana ya kalli Asma'u da Bashir sai kuma ya dawo da
Kallonsa kan Ummi kana yace.

“Ummi ku nake so”.

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.

“Kai ko Jameelu ba'a rabaka da zolaya”.

Ta faɗa tare da kallonsa tsakiyar idanunsa ga mmkinta sai taga still baiyi murmushi ba kamar yanda ya
saba ba.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.


“To ko dai ka manta wayar kane?”.

Hannu ya sanya tare da shafa aljihun gaban rigarsa still yatsansa na cikin bakinsa yana gyatsawa a
hankali kana yace.

“Um-um Ummi ban manta wayata ba gashi a aljihuna”.

Cikin yanayin damuwa da jinƙai irin na mahaifa tace.

“Toh Meye ne?”.

Kanshi ya ɗaura a kan hannunta dake kan glass ɗin motar, tare da lumshe idanunsa kana ya janyo tafin
hannunta ɗaya ya kife akan goshinsa tare da buɗe lumsassun idanunsa da suke sheƙi, shiru yayi kamar
mai nazari.

Sai ya kuma lumshe idanu.

Khausar dake gefe tayi dariya tare da cewa.

“Kai Yah Jameel bisa dukkam alamu dai yau kam Shagwaɓa kake ji dashi?”.

Ahankali ya buɗe idanunsa dake lumshe batare daya juya ba kana cikin raunin murya yace.

“Uhm Lelewal baza ki gane ba”.

Murmushi tayi kana tace.

“Yah Jameel zan gane mana gashi yau Shagwaɓa kake yiwa Ummi”.

Ummi kuwa sun kuyowa kansa tayi sai taga ya kuma lumshe idanunsa yayi shiru Kamar mai tunani
hannunta dake goshinsa ta ɗago tare da cewa.

“Menene? Shin wai meke damunka? Me kake son faɗa min mana?”.

Cikin sanyin murya yace.

“Ummi”.

Sai kuma yayi shiru.

Ahankali ya buɗe Murfin motar ya fito tare da jan hannunta suka nufi cikin falon kana ya kalli su Asma'u
tare da cewa.

“Ku jirani”.

Da kallo Khausar, Asma'u da kuma Bashir suka bisu, amma babu wanda yace komai kowa da tunanin da
yake Aransa.
Suna shiga falon ya zaunar da Ummi kan 1sitter kana ya durƙusa agabanta cikin raunin murya yace.

“Ummi ba abinda kikeso in miki?”.

Cikin raunin murya tace.

“Meyesa kake hakane, shin wai idan ina da ɓuƙatar abu, bani da kaina nake kiran ka in faɗa maka ba
Jameelu?”.

Araunane ya kalleta tare da cewa.

“Ummi ki tuna dai! ba abinda kike so in miki kada damar ta wuceni fa Ummi? Ki tuna dai”.

Ya ƙare mgnar yana murza tafin hannunsa kan rumfa sawunta

Saurin Kallonsa tayi kana tace.

“Kamar ya damar ya wuce ka Jameelu?

Na faɗa maka bana ɓuƙatar komai”.

Cikin raunin murya yace.

“Toh bani wayar ki Ummi”.

Ahankali ta miƙa masa wayarta dake hannun kujeran karɓa yayi tare da shiga text messages ɗin ta, ya
duba Alart gani yayi duka-dudu kudin dake ciki baifi dubu ɗari biyu da hamsin da biyar ba.

Kallonta yayi kana yace.

“Ummi kina da buƙatar kuɗi”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“Ga kuɗi kuma mai zanyi dasu?.

Me zanyi da kuɗi komai fa kai kakeyi min Jamilu”.

Girgiza kai yayi tare da zaro wayarsa acikin al'jihunsa Atake yayi charking balance tare da cewa.

“Nima bani ba kuɗi da yawa acikin account ɗina”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.

“Ta yaya kuɗi zai zauna acikin account ɗin ka Jamilu nasan ka haka Allah yayi ka kana da yawan kyauta
zaka bawa wannan ka bawa wancan”.
Girgiza kai yayi tare da cewa.

“Allah yabamu mu bayar Ummi”.

Jinjina kai tayi tare da cewa.

“Ameen”.

Atake ya Mata transfer million ɗaya zuwa account dinta.

Kana yace Ummi ga Million ɗaya na miki transfer”.

Cikin sauri ta kallesa kana tace.

“Me zanyi dasu Jameelu?”.

Hannunta ya damƙe acikin nasa kana yace.

“Ummi duk abinda kike so kiyi dashi, tunda kin ƙi ki faɗa min abinda kike buƙata ina ji kamar akwai
nauyin da ban gama sauƙewa ba gani nake kamar kinada wata buƙatar”.

Ya ida maganar muryarsa na rawa sosai sai kuma ya kama gwiwoyinta da hannu kana ya kife kansa akan
cinyarta.

Cikin sanyayyar murya mai cike da rauni yace.

“Ummi”.

Ummi kuwa cikin sanyin murya tace.

“Na'am”.

Still muryarsa na rawa yace.

“Idan akwai abinda na miki kiya femin”.

Cikin sauri ta kallesa kana tace.

“Wai Jameelu Meyesa kake yin haka ne?.

Wai meyesa?”.

Girgiza kai yayi tare da faɗin.


“Ai ɗa baya rasa laifin da yake yiwa Mahaifiyar sa, ko babu abinda na miki a yanzu, ai kin ɗauki nauyin
cikina tsawon wata tara da kwanaki tara, kin sha wahalar naƙuda kafin ki haifeni, kinsha jidalin rainona,
nayi miki kashi nayi miki fitsari na miki tumɓuɗi da amai, na hanaki bacci a lokacin da kowa ke bacci

Ummi kiya femin domin wannan ma shine babban abin neman yafiya ga iyaye, idan kuna akwai abinda
na miki yayin kuruciya da girma da kuma yayin rarrafe wata ƙil har cizonki nayi yayin shayarwa dan Allah
da Manzonsa duk ki yafe min, kiyi min aikin gafara”.

Ya ƙare mgnar cikin wani irin raunataccen muryar mai rawa.

Kai ta girgiza kana cikin raunin murya tace.

“Ba kayi min komai ba kuma na yafe maka duniya da lahira na yafe maka komai na raunin cewa ko da
haihu da rainonka bayan haihuwa, duk na yafe maka shi tun kafin yau”.

Wasu irin tagwayen numfarfashi masu nauyi ya rinƙa sauƙe tare da cewa.

“Alhmadulillah Ummina ngd matuƙa.”

Ita kuwa Ummu cikin sarƙewan murya taci ga da cewa..

“Meyesa kake min irin wa'annan abubuwan bana sofa”.

Dariya yayi kana yace.

“Toh Ummi dan ɗa yanemi yafiyar Uwarsa sai yazama laifi?”.

Girgiza kai tayi tare da Kallonsa kana tace.

“Toh ni babu abinda ka min ka tashi mu tafi Allah yayi ma sakayya da mafifiyaciyar Al'jannah mai cike da
ƙololuwa ni'ima tashi muje in rakaka”.

Ta faɗa tare da miƙewa kana ta riƙe hannunsa kamar yaro haka suka fito kana ta buɗe masa murfin
motar tace.

“Toh kashiga Allah yayi maka al'barka”.

Kai ya gyaɗa tare da shiga.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.

“Toh kaje Ubangiji Allah ya maka albarka Allah ya tsareka Allah ya rufa maka asiri Ubangiji ya maka
sakayya da mafi kyawun abin sakamako Allah yatsare min kai Allah Ubangiji ya Albarkanci rayuwar ka
Allah ya azurtaka da arziki mai albarka da yara na gari”.

Murmushi yayi tare da cewa.


“Ameen ya hayyu ya ƙayyum Ummina”.

Ya ida maganar tare da zuba mata Ido.

Asma'u kuwa ita ma shiru tayi tare da zuba masa Idanu tana kallon yanda yake kallon Ummi.

Khausar kuwa Kallonsa tayi kana tace.

“Yah Jameel gaskiya zan tafi idan kai ba zaka tafi ba”.

Kallonta yayi kana yace.

“Toh mutafi Lelewal baki sani bane duk saurin da kikeyi nafi ki sauri fa bakisan inda zanje bane fa
shiyasa”.

Tura baki tayi kana tace.

“Yah Jameel Ina zaka je”.

Murmushi yayi tare da kallon Asma'u da Bashir kana yace.

“Ku kula da kanku sannan ku riƙe kada ku manta da alƙawarin da kuka min ga amanar Ummi na kafin na
dawo”.

Murmushi sukayi tare da gyaɗa masa kai kana suka ce.

“Insha Allah Yah Jameel Allah yatsare sai kadawo.

Murmushi kawai yayi tare da jan motar suka fita saida Ummi taga motar ya ɓacewa kallonta kafin ta
sauƙe ajiyar zuciya ta koma cikin gida Asma'u da Bashir na biye da ita.

Acan mota kuwa Anutse M Jameel ke Driving kana ahankali ya juya ya kalli Khausar data tsirawa tiri
idanu kana ya sauƙe numfashi daga zuciyarsa ya fara tunanin Maganar da zai mats kana cikin sanyin
murya yace.

“Lelewal”.

Juyawa tayi ta kallesa tare da cewa.

“Na'am Yah Jameel”.

A hankali ya furzar da iska kana a hankali cikin tattausan lafazin yace.

“Inne mi alfarma awajen ki mana?”.


Anutse ta kallesa kana tace.

“Toh Malam Jameel Allah yabani ikon yin duk al'farman daka ke so awajena”.

Cikin jin daɗi ya buɗe idanunsa dake lumshe ya kalleta kana yace.

“Kinyi alƙawarin duk abinda nake nemi al'farmar zaki yimin?”.

Kai ta gyaɗa masa kana tana wasa da yatsun hannunta tace.

“Na sani malam Jameel baza ka sani yin haramtaccen abu ba sannan baza ka sani yin abinda yafi ƙarfi
naba kuma kafi ƙarfin neman alfarma ko wani abu awajena ina hana ka saidai ka bani Umarni Yah Jameel
faɗa min me kake so inyi maka? Kai tsaye bani umarnin kawai ni kuwa in cika maka umarninka da sauri”.

Jinjina kansa yayi still Yana driving Cike da nutsuwa kana yace.

“Alhamdulillah naji daɗin Lelewal Thanks".

sai kuma yayi gyaran murya tare da juyowa ya kalleta, itama shi take kallo ganin yadda fuskarsa ta koma
alamun daga can cikin ƙahon zuciyarsa abinda zai faɗa ɗin zai fito cikin yanayin neman al'farma cikin
iyawa da ƙwarewa ya juya harshe zuwa sahihin Larabci mai cike da Kekkyawan lugga ya fara mgn da
larabci yayinda itama Khausar ta juya harshen zuwa larabcin.

Aƙalla sunyi magana daya ɗauki tsawon minti goma sha biyar, kafin suka koma magana da yaren Hausa
Inda M Jameel ya ƙare maganar da cewa.

“Nagode Khausar Nagode Nagode Lelewal Ubangiji Allah ya miki albarka”.

Khausar kuwa cikin wata raunan'niyar murya tayi ƙasa da kanta yayin da ruwan hawaye suka cika
kwarmin Idanunta kana tace.

“Ameen”.

Ahankali M Jameel ya cigaba da Driving kana Yana cigaba da yi mata nasiyya akan rayuwa.

Ahankali Khausar da Idanunta ke kan madubin side ɗin da take ta juya tare da kallon M Jameel kana
tace.

“Yah Jameel kamar wannan motar binmu fa take”.

Kai ya gyaɗa mata kana cikin sanyin murya yace.

“Eh nima na lura da haka Khausar tun ɗazu ma”.

Jinjina kai tayi tare da cewa.


“Toh Yah Jameel ka rage gudu mugani mana muga kodai mudin suke bi”.

Kai ya gyaɗa tare da rage gudun still sai motar dake bayansu itama ta rage gudun.

Ahankali M Jameel ya cigaba da Driving yayin da still motar ke bin bayansu.

Suna isa wani babban super market M Jameel ya kalli Khausar da hankalinta ke kan motar kana yace.

“Bari mushiga cikin Super Market ɗin nan mugani idan ma mu suke bi ai zasu tsaya”.

Suna Parking suka fita tare da shiga cikin Super Market din M Jameel ya ɗiba mata turaruka tare da
Choculate da sweet da kuma Biscuits yana tsinta yana faɗa mata wasu kalamai da larabci, duk da dai ba
ji nake amman yadda fuskarta ke nuna kalaman masu nauyi ne yake sanarmata.

Kana kamar kimanin minti talatin da shigarsu suka fito ga mamakinsu sai suka ga wannan motar ta faka
agefen nasu kai tsaye suka shiga motar M Jameel ya mata key ita ma wannan motar sai akamata key aka
tayar sunbi ta bayan motar idanun Khausar ya sauƙa akan Motar tana kallon fuskar mutanen ciki, duk da
nesa ne ta gane cewa mutanen ne da ta gani Arugar Jauro Yaya sannan itace abakin makarantar su kana
taga still Motar ta cigaba da binsu.

Lokaci ɗaya tsoro da damuwa ya shigeta cikin yanayin tsoro ta kalli M Jameel tare da cewa.

“Yah Jameel Motar nan mu take bi”.

Jinjina kai yayi tare da faɗin.

“Nima naga alama amma watakila arashi ake samu sunyi”.

Kai ta gyaɗa still zuciyarta na cigaba da bugawa da masifar ƙarfi suna cikin tafiya motar ta ɓacewa kallon
su.

Anutse M Jameel ya Kalli Khausar kana yace.

“Kin gani kawai arashi ake samu may be suma zasu shiga Super Market ne sannan hanyar mu ɗaya
shiyasa haka”.

Murmushin yaƙe Khausar tayi kana tace.

“Haka ne kam”.

Aranta kuwa cewa tayi to kodai mutanen sun gane ta ganeta ne shiyasa suke bibiyar rayuwarta wata ƙil
ita suke son su kasheta kana ta raya dole idan ta koma dole ta faɗawa Mommy.
Anutse M Jameel ya juya tare da kallon Khausar data zurfafa cikin tunani kana yace.

“Lelewal muje mu gidan su Moddibo ki gaishe da Kakarmu”.

Da sauri ta dafe ƙirjinta tare da cewa.

“Gidansu Moddibo kuma?”.

Murmushi M Jameel yayi kana yace.

“Babu abinda zai miki Khausar”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“Nikam ina tsoro Yah Jameel. Abu kaɗan ya fara masifa ko agidan mu ma faɗa yake min bare kuma naje
gidansu”.

Cikin sanyin murya M Jameel yace.

“Nayi miki alƙawari ko hararanki ba zai yiba, Insha Allah bare kuma ya miki faɗa zai miki maraba, ki yarda
dani”.

Kai ta gyaɗa kana cikin sanyin murya tace.

“Toh shikenan”.

Suna isa gidan yayi Parking a coumpund din farkon kana ya fita cike da nutsuwa yake tafiya tana biye
dashi a baya, a kuma dai-dai lokacin da Moddibo ke kokarin fitowa daga falonsa, cikin sassarfa ya
nufeshi.

Shi kuwa Modibbo wani irin sassayan numfashi ya fesar tare da tsaida idanunsa kan J ɗinsa.

Shi kuwa M Jameel murmushi mai cike da farin ciki yayi tare ƙara sawa wurin Modibbo rungume shi yayi
da ƙarfi.

Wanda haka yasa shima Modibbo yayi masa wani irin amintaccen

runguma mai cike da son juna a tare suka sauƙe ajiyan zuciya cikin sanyin sauti Modibbo yace.

“J nayi fushi da kai”.

Cikin sanyin Muryan M Jameel yace.

“Kada kayi fushi dani A.J idan kayi fushi da J ɗin ka dawa zaka sulhunta”.

Cikin sanyin Murya Moddibo yace.


“J ka tafi gidan Ummi ka barmu mu kadai agidan, sam gidan nan ba daɗi idan baka nan shiru baki ɗaya
gidan bai mana daɗi ba”.

Murmushi M Jameel yayi kana a hankali yace.

“A.J Rungumeka da nayi alfarma nake nema awajenka.

Saboda muyi maganar sirri akwai baƙuwar da nazo da ita dan Allah dan darajar Annabi A.J ko hararanta
kada kayi”.

Sai kuma ya sauƙe numfashi tare da cewa.

“Ayyah A.J ka tayani cika al'ƙawarin dana ɗauka dan Allah kada ka tozar tamu ka tuna ba haushe yace
baƙonka Annabin ka sannan Annabi Muhammad (S.A.W) yace duk wanda yayi imani da Allah da rana ta
ƙarshe to ya girmama baƙon”.

Kai Moddibo ya jinjina kana yace.

“Toh J naji dama ya za'ayi na tozarta matar da J na zai aura har abada bazanyi hakaba?”.

Hararansa M Jameel yayi tare da faɗin.

“Kai dai kayi min al'ƙawari koma wacece ai zaka ganta”.

Kai kawai Moddibo ya gyaɗa.

Tare da cewa.

“Nayi al'ƙawari”.

Ahankali M Jameel ya sakeshi tare da matsawa.

Da sauri Moddibo ya ɗan yi gefe da kansa lokacin da idanunsa suka sauka akan Khausar da Idanunta ke
ƙasa tana wasa da yatsun hannunta.

Khausar kuwa cikin wata Sanyayyar murya mai cike da rauni ta kawar da kanta gefe tare da cewa.

“Ina yini”.

Kamar yanda ta kawar da kai gefe haka shima ya kawar tare da faɗin.

“Lafiya”.

Daga nan ya juya yayi gaba.


Khausar da M Jameel suka jera atare zuwa sashen Innayi bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga.

M Jameel kuwa cikin yanayin sa yace.

“Innayi ga baƙuwa na kawo miki ku gaisa”.

Daga cikin Innayi tayi murmushi tare da cewa.

“Sannun ku da zuwa ko dai matar ce ka kawo Min?”.

Murmushi mai sauti yayi kana yace.

“Ehahea lallai Innayi kenan ke dai ga tanan ku gaisa dama zan wuce da ita gida ne.

Kuma A.J nata kirana shiyasa nace bari na fara zuwa nasan idan bai ganni ba wataƙil hankalin sa bazai
kwanta ba”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauke kana yace.

“Hmmm Yayi maka kyau da kazo a gaggauce ai da sai ka ajiyeta kafin kazo”.

Murmushi M Jameel yayi tare da cewa.

“Ai kawota nayi ta gaida Innayi kuma bamu gama tattaunawa da itaba”.

Taɓe baki Moddibo yayi ba tare da yace komai ba.

Khausar kuwa ahankali ta tsugunna tare da Gaishe da Innayi.

Kallonta Innayi tayi kana tace.

“A'a wannan ai kamar na ganeki kamar ƙawar Asma'u ko?”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da sakin murmushi kana tace.

“Eh nice Innayi”.

Jinjina kai Innayi tayi tare da cewa.

“Yasu mamanki?”.

Cike da nutsuwa Khausar tace.

“Duk suna lafiya”.


Ƙoƙarin miƙewa Innayi tayi kana tace.

“Bari akawo miki abin taɓawa”.

Cikin sauri Khausar ta girgiza kai tare da cewa.

“Nagode Innayi yanzu daga gidan Ummi nake ta cika min cika na da abinci”.

Saurin kallonta Moddibo yayi jin yanda take magana Anutse kamar ba ita ba baki ya taɓe tare da mgnar
zuci.

“Ganta kamar gaske haka take da nitsuwa”.

M Jameel kuwa kallon Innayi yayi kana ya juyi ya kalli Khausar yace.

“Mu tafi ko”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh”.

kana tayi gaba M Jameel da Moddibo suka fito atare a hankali suke tafiya, a hankali lips ɗin M Jameel na
motsawa alamun mgn yakeyiwa Modibbo, shi kuwa Modibbo kai kawai yake jinjina mishi tare da tsaresa
da ido, a haka har suka isa bakin motar Moddibo da kanshi ya buɗe masa gaban motar ya shiga kana
yace.

“Dan Allah kazo kada ka barni. Ni kaɗai sam bana jin daɗin gidan”.

Murmushi M Jameel yayi tare da yiwa motar key kana yace.

“A.J ka jika randa akace babu nifa?”.

Cikin sauri Moddibo ya rumtse idanunsa da karfi, sai kuma ya buɗe su da sauri ya kallesa tare da cewa.

“Jhhhh”.

Ya ja sunan a cikin maƙoshinsa.

Murmushi M Jameel yayi tare da jan motar,

Shi kuwa Modibbo hannunsa ya harɗe a ƙirji yana kallonsa har suka tafi.

Kai tsaye unguwar su Khausar suka nufa suna tafe yana tsokanarta, a haka har suka isa yana isa yayi
Parking ta fita tare da yi masa godiya kana tayi cikin gida.
M Jameel kuwa Anutse ya juya akalar motarsa kai tsaye gidansu ya nufa yana isa yayi Parking tare da fita
kai tsaye sashen Abban sa ya nufa yan shiga sukayi ta hira har La'asar tayi, atare suka je masallaci suka
gabatar da sallah kana bayan su. Idar ya fito ya nufi Sashen sa yashiga bai sake fita ba sai da akayi
Maghariba kana ya nufi masallaci bai fito ba sai da aka Idar da Isha'i sannan yana dawowa ya nufi sashen
Abbansa lokacin shima Abbah bai dade da dawowa daga masallaci ba.

Cikin lumshe ido yace.

“Abba zanje wajen Moddibo za muyi magana”.

Jinjina kai Abba yayi tare da cewa.

“Allah ya tsare amma idan dare yayi ka kwana a can bana son tafiyar daren nan, kasan duniyar nan babu
gaskiya”.

Kai M Jameel ya gyaɗa kana ya fice yana murmushi.

Motarsa ya shiga da addu'a kana yayi Hong mai gadi ya buɗe masa ya hau kan titi yana maiyin
murmushin, wayarsa ya zaro, whatsApp ya shiga kan number'n Moddibon ya kusa kai.

Cikin sakin murmushin yayi mishi voice ɗin 1 mitune And 33 second

Ba zato ba tsammani yaji an sako hannu daga bayansa an ɗaura masa bindiga akai kana cikin wata
magautacciyar murya akace kana juyawa zan fasa maka ƙwaƙwalwar kai da sauri ya saki wayar tasa ta
faɗa kan cinyarsa garin ta sule ɗin ne kuma yatsarsa ma nuniya tayi sending din voise ɗin nasa da sauri
ya ƙara taka motar jin mutumin ya ɗana kunaman bindigar yana cewa.

“Maza mu tafi kada kayi min gardama dan ko motsi kayi zan fasa kanka...!

Dan-dan yanzufa aka fara labarin ku biyuni, da kekkyawar yaƙini da ƙarfin zuciya.

*By*

*GARKUWAN MARUBUTA*

SAKAYYA

27
*Al'bishirunku Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku
ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.

Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce,
akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna
uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin
yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace
ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa
bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore
ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar
gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san
hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa
tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan
mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina
mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka
yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke
taimakawa (sex hormones 😍) dinki.

Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu
tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?

Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da
ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa
domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.

Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?

Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar
amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin
mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar
mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,

Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke
mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta
akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.

Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*

Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne
masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na
daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka
ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar
da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari
maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276
domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA
ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba
Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA


😘

*(GARKUWAR MA'AURATA)*

27

Acan Falon Moddibo kuwa zaune yake akan 2sitter hannunsa riƙe da Kofin Tea yana sha time to time zai
ɗaga kansa tare da kallon agogon dake manne abango ahankali ya gyara zamansa tare da kurɓan tea
dake tiriri ya lumshe idanunsa tare da buɗe su akan agogon cinyarsa ya matse da ƙarfi har saida yaji
jikinsa na rawa, ƙara matse jikinsa yayi sabida yadda yake jin M ɗinsa na miƙewa yana harbawa cike da
zalama, ɗan gajeren tsakiya yaja, cikin sanyin murya a fili yace.

“J har yanzu baka dawo ba”.

Yayi mgnar kamar Jameel ɗin na gabansa.

Sai kuma ahankali yasa hannunsa tare da laluɓar wayarsa a aljihun sa na hagu da dama jin babu yasa
yaja siririn tsaki tare da miƙewa cikin wani irin masifeffen kasala da sanyin jiki mai kashe ilahirin gaɓɓai
ya nufi bedroom ɗinsa a kuma lokaci ɗaya zuciyarsa ta buga tare da tsinkewa da masifaffen ƙarfi, da ƙyar
ya iya ɗaga ƙafarsa na dama kana ya taka ya shiga Bedroom tare da furta.

“Hasbunallahu wani'imal wakin”.

Jin yanda zuciyarsa ke cigaba da bugawa cikin yanayin tsinkewar zuciya da sanyin jiki ya ɗauki ƙaramar
wayar tasa, kana ya dawo falon ya zauna tare da shiga Call log zai kira M Jameel sai kuma kiran Malam
Arɗo yashigo wayar sa.

Zubawa screen ɗin wayar ido yayi tare da jan siririn tsaki kamar ba zai ɗaga ba sai wata zuciyar tace ka
ɗaga mana kasan menene Uzirinsa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da picking.

Acan ɓangaren Ummi kuwa zaune take a falonta kan kujera 3sitter tayi ta tagumi da duka hannunta biyu,
kana ta tsirawa waje ɗaya Idanu yayin da ƙirjinta ke bugawa da masifar ƙarfi zuciyarta na tsinkewa yana
bada sautin dif-dif-dif lokaci ɗaya taji wata muguwar kasala na rufe mata jiki haka nan take jin zuciyarta
na tsinkewa.

Jiki a mace Asma'u ta fito daga kichen hannunta riƙe da Plate ƙara sawa falon tayi Idanunta akan Ummi
data zabga tagumi ta zauna akan 1sitter tare da cewa.

“Ummi har yanzu baki kwanta ba?”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana ta gyaɗa mata kai tare da cewa.

“Eh Asma'u ban kwanta ba”.

Cike da kulawa Asma'u ta ɗaga kanta tare da kalli agogo, tare da cewa.

“Ummi kalli fa har sha ɗaya ta wuce me kikeyi afalo ke kaɗai shiru ga Abban mu yashiga tun ɗazu”.

Lumshe Idanu Ummi tayi still zuciyarta na tsinkewa kana tace.

“Babu”.

Numfashi Asma'u ta fesar tare da ajiye cokalin dake hannunta tace.

“Toh Ummi ko dai baki da lafiya ne?”.

Kallonta Ummi tayi tare da girgiza kai.

“Lafiyata ƙalau Asma'u”.

“Ayyah Ummi am to mai yasa baki kwanta ba kin zauna shiru ke kaɗai dubi yanda kika yi tagumi da
hannu duka bibbiyu”.
Cewar Asma'u.

“Ban sani ba Asma'u ba wai bani da lafiya ba amma ina jin jikina wani iri bai min daɗi ba ina jin zuciyata
na tsinkewa sannan ga wata kasala data rufe ni”.

Ido Asma'u ta zuba mata kamar mai son gane wani abu sai kuma tace.

“Toh Ummi ki riƙa maimaita Hasbunallahu wani'imal wakin mana kuma may be rashin bacci ne kinga jiya
kwana mukayi muna hira ba kisamu kinyi wadataccen bacci ba, sannan yau da safe ma baki samu kinyi
wani ishesshen bacci ba”.

Gyara riƙon da taiwa plate ɗin tayi kana taci gaba da cewa.

“Har yanzu ma baki samu kinyi Ummi, kiyi ƙoƙari kije ki kwanta Insha Allah zakiji dama dama”.

Kai Ummi ta jinjina tare da cewa.

“Toh ki maida Plate ɗin kichen idan kin gama sannan ki rufe ƙofar kichen ɗin kana kizo ki rufe mana
ƙofan falon”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh”.

Ta mike tare da ajiye Plate din ta kife Sauran abincin sannan ta rufe ƙofar tare da murza mukulli ta dawo.

Still zaune ta samu Ummi tayi tagumi.

Cike da kulawa tace.

“Ummi kije ki kwanta dan Allah kiyi baccin”.

Ahankali Ummi ta ɗago ta kalleta tare da sauƙe ajiyar zuciya kana tace.

“Toh kije Insha Allah yanzu zan kwanta”.

Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta wuce Bedroom ɗin ta Ummi kuwa kasa tashi tayi ahankali ta lumshe
Idanunta tare da komawa ta kwanta akan kujeran still zuciyarta na cigaba da tsinkewa tana mai
maimaita kalmar Hasbunallahu wani'imal wakin aƙasan ranta.

Acan ɓangaren Moddibo kuwa yana Picking call ɗin yakai kunnensa tare da cewa.

“Assalamu Alaikum”. cikin sanyin murya M Arɗo ya gyara zaman wayar akunnensa tare da cewa.

“Wai yanzu yaran nan tsakanin ku da Allah kun bar batun karantarwa Amakarantar nan kenan?”.
Anutse Moddibo ya lumshe Idanunsa kana ya buɗe su cikin yanayin kasala da tsinkewar zuciyar da yake
ji ya gyara zamansa tare da cije lips ɗinsa na ƙasa yace.

“Toh ka asamsa Sallamar da nayi maka mana Before ka fara ƙorafi da zakayi”.

Girgiza kai Malam Arɗo yayi tare da cewa.

“Toh Wa'ailaikum salam kune ai baki ɗaya kuke son caza min kai, baki ɗaya satin nan yashiga har ya fita
amma baku zoba toh gashi yau jumma'a gobe Asabar za akoma shiyasa nace bari na kira ku kada ace
baku zoba”.

Iska mai zafi Moddibo ya fesar daga bakinsa tare da shafa sajensa kana ya lumshe idanunsa tare da
cewa.

“Gaskiya baza mu zoba”.

Asanyaye Malam Arɗo yace.

“Toh meyesa”.

Muskutawa Moddibo yayi tare da gyara zaman wayar akunnensa kana yace.

“Ai mun riga da mun gama yi maka magana kayi haƙuri kawai ”.

“Amma kunsan ina son koyar wanku Amakarantar nan ina jin dadin zama daku sannan ɗaliban ma suna
jin daɗin koyarwanku, makaranta na ya cigaba adalilin kune kada kuyi min haka”.

“Malam kayi haƙuri da akwai Uzurin da yake gaban mu, wanda yafi wannan na tabbata badan wannan
Uzurin ba babu dalilin da zaisa mubar koyar wa Amakarantar”.

Cikin sanyi murya Malam Arɗo ya sauƙe Ajiyar zuciya kana yace.

“Toh shikenan tunda abin ya zama haka dole in sawa zuciyata haƙuri amma kusa marmin wasu Malamai
masu Hazaƙa, duk da nasan da wuya asamu kamar ku tabbas nasan nayi rashin zaƙaƙuran Malamai
kamar ku”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana cikin sanyin murya yace.

“Toh ba matsala zamu yi kokarin hakan”.

Cikin sanyi Malam Arɗo yace.

“Toh Nagode saida safe”.

kana ya katse wayar.


Moddibo kuwa cikin sauri zuciyarsa ya cigaba da bugawa yana bada sautin dif-dab-dif-daf ahankali ya
ɗago wayar da niyyar kiran M Jameel cikin wani Irin yanayi ya dafe saitin ƙahon zuciyarsa jin yanda yake
bugawa da azabebben ƙarfi yana cigaba da bada sautin dif-dif-dif rintse idanunsa yayi still hannunsa na
dafe da saitin ƙahon zuciyarsa.

Acan ɓangaren Gimbiya Bunayya kuwa har Misalin ƙarfe sha biyu da minti biyu na dare Uncle Naseer da
Amina na zaune akan 2sitter suna hira.

Yayin da ita kuma ke kwance a Bedroom ɗin ta kunneta maƙale da waya tana Magana da Hajiya Lami.

Murmushi Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.

“Hajiya Lami ni dai yanzu Alhamdulillah buƙata ta biya hankalina ya kwanta, yanzu batun soyayyar Amina
da Naseer ya kankama yayi zurfi”.

Atake fara'ar dake fuskanta ya gushe ta mike ta zauna tare da cewa.

“Yanzu kuma hankalina ya koma kan ƴaƴan wannan shegiyar matar mai kama da Mayyar wannan yaro
mai ƙwala-ƙwalan ido daya karye nake son kawar dashi tun da shi wancan mai kama da Brolas ɗin
Uwarsa ta shayar dashi saɓani, tunda kinga wannan hatsarin ma shi na shiryawa abi takansa amma, ba'a
samu babban ba akabi takan ƙaramin”.

Sai kuma ta sauƙe numfashi tare da jan dogon tsaki kana tace.

“Dole saina koma na samu boka Kar'uzu da maganar ayi duk abinda za ayi nikam Haiydar shine babban
matsala ta tunda shi Ramadan shine ƙarami akan Aminu, babu yanda za ayi Aminu na raye aɗauki
Sarauta abawa Ramadan dole dai sai ɗana ɗin dai”.

Cikin sauri Hajiya Lami ta katseta tare da cewa.

“Kul-Kul Hajiya Bunayya kada kiyi la'akari da wannan ƙaramin tunanin naki, ba kiji Malam Bahaushe na
cewa ɗan hakin daka raina shike tsole maka Ido ba?.

To ki rufa wa kanki asiri ki kawar dasu duka biyun hankalinki ya kwanta ki samu nutsuwa da salama
aranki”.

Kana ta saki wani murmushi tare da cewa.

“Kinga idan kika gama dasu ɗaya ce zaki samu nutsuwa akanta itace Raudat da kuma Khausar.

Kinga Khausar kuwa ba ƴar gidan bace babu yanda za ayi agola tavi gadon Sarauta koda na mijine bare
kuma mace. Raudat kuwa ƙarama ce kuma mace.
Amman Haiydar da Ramadan dai kaudasu, da kike batun Ramadan shine ƙarami a kan sulaiman, sau
nawa manyan Yayu ke zaune ake bawa ƙannen su Sarautar, ni dai shawarar da zan baki yanda zaki gama
da Haiydar haka zaki gama da Ramadan”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da gyara zaman wayar akunnenta kana tace.

“Haka ne fa kuma aini duk wannan tunanin bai zo min ba, atunanina idan na kawar da Haiydar
shikenan”.

Girgiza kai Hajiya Lami tayi tare da faɗin.

“A'a tsaya kallon ruwa kwaɗo ya miki ƙafa, har kina wani batun shine ƙaramin akan Aminu ai ba'a
wannan zancen kima rufawa kanki asiri, kigama dasu gaba ɗaya to asannan hankalin zai kwanta, ki samu
nutsuwa anan ne zaki tabbatar sarauta ahannun Aminu take, ke kuma kin zama Gimbiyar Gembulan
Matar sarki Uwar sarki amma muddin ƴaƴan wancan koɗaɗɗiyar matar na nan keda Saurauta saidai
hange daga naisa”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi cike da gamsuwa kana tace.

“Aikuwa hakane Nifa duk wannan tunanin bai zomin ba shiyasa nake alfahari dake ƙawata.

Insha Allah zanje muyi magana da boka Kar'uzu asan yanda za'a ɓullowa lamarin”.

Kai Hajiya Lami ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh nima Insha Allah gobe idan muka je zan faɗa masa ya tsaida rana da Samira zata fara zuwa wajensa
suyi satin, tunda dai yace idan ya kusance tama zai mayar mata da budurcinta ai shikenan”.

Atare suka sheƙe da dariyamai cike da farin ciki da annushawa kana Hajiya Bunayya tace.

“Ai dai haka yafi shiyasa na yarda da aikin Boka Kar'uzu kamar yankan wuƙa dan sha yanzu magani yanzu
ne tun yaushe muke bin boka bursunu tsawon shekaru ba biyan buƙata sai asaran kuɗi”.

Jinjina kai Hajiya Lami tayi kana tayi mata Sallama suka katse wayar.

Aɓangaren Abban M Jameel kuwa tsaye yake ajikin window falonsa ya tsirawa harabar gidan Ido tun
bayan fitar Motar M Jameel ya kasa motsa wa daga wajen.

Hajiya Karima data fito daga Bedroom ɗin sa ta dubesa cike da kulawa tace.

“Ya dai Alhj tun tuni kana tsaye ana ka gaza motsa sama da awa biyu kenan tun bayan fitar motar
Jameel kake tsaye lafiya kuwa?”.

Cikin wani irin yanayi ya lumshe idonsa.


Haka nan yaji ruwan hawaye na tsats-tsafo masa a hankali ya sauƙe ajiyar zuciya tare da furzar da iska
kana yace.

“Haka nan dai narasa me nake tunawa awajen nan”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da dafa bayansa kana tace.

“Toh kazo ka zauna mana”.

Girgiza kai yayi tare da fesar da numfashi kana cikin sanyi murya yace.

“Ina ga ko dan garin dana gani da alamun hadari ne ko yaya ne ban sani ba”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh kadawo ka zauna dan Allah tsayuwar tayi yawa”.

Kai ya gyaɗa lokaci ɗaya yaji wani irin masifaffen rauni mai haɗe da bugun zuciya ya rufe sa Atake yaji
Idanunsa na tsats-tsafo da ruwan hawaye masu ɗumi yayin da zuciyarsa ya cigaba da tsinkewa jikinsa na
mutuwa tamkar ana zare masa laka cikin sanyi jiki yaja ƙafafunsa da yaji sunyi masa mugun nauyi ya
zauna akan kujera tare da kwanciya akan 3sitter kana ya lumshe Idanunsa.

Cike da kulawa tace.

“Ya dai lafiya kuwa kashiga ciki mana?”.

Girgiza kai yayi still zuciyarsa na cigaba da bugawa yayinda muryarsa ke ɗauke da rauni yace.

“Please Karima ki barni in kwanta inaji kamar kaina na ciwo”.

Cikin sauri tace.

“Alhj kad dai BP kane?”.

Girgiza kai yayi still Idanunsa na lumshe yace.

“A'a ba BP na bane bari dai mu gani”.

Zama tayi daga hannun kujeran kana tace.

“Toh kasha maganin ka kuwa?”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Eh sosai ma yan zun nan kafin Jameelu ya fita ya bani nasha”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh ƙwarai kuwa hakane toh Allah ya sawwaƙa”.


Ahankali yace.

“Ameen”, Miƙewa tayi tare da shiga Bedroom ɗin sa ta kwanta.

Ɓangaren Moddibo kuwa har Misalin sha biyu da kwata yana zaune dafe da ƙirjinsa dake cigaba da
bugawa ahankali ya ɗago kansa tare da shafa gefen wayarsa haske ya bayyana tare da nuna masa ƙarfe
12:15 afili ya furta.

“Har yanzu J bai zoba”.

Yayi mgnar tare da shiga Call log yayi dearling number M Jameel amma ga mamakinsa sai yaji Swich off.

Cikin yanayin damuwa ya dafe kansa tare da cewa.

“Ikon Allah lafiya kuwa wayar J arufe?”.

Kallonsa ya mayar kan babbar wayarsa tare da ɗauka kana ya fito da ɗaya number M Jameel ya kira
Shima still Swich off.

Miƙewa tsaye yayi ido a lumshe yace.

“Ha'a ya wayar J akashe kuma dai J baya kashe wayarsa, to amma mai yafaru yau wayarsa akashe toh
me yake faruwa bayan ya faɗa min yau zai dawo!?”,l.

Yayi maganar cikin zulumi

“Ya ilahi ya mujabat da'awati, to kuma ko kafin J ya fito sai da ya kirni yace zaije wajen Abba ya sallame
sa sannan yazo amma kuma har yanzu bai zoba”.

Atake wata zuciyar tace kasani ko yazo suna tare da Innayi suna can suna ƙus-ƙus atake ya amince da
abinda zuciyarsa ya raya masa cikin mutuwar jiki ya nufi ƙofan falonsa tare da buɗewa.

Wani sanyayyan iska ya hurasa ahankali ya ɗaga kansa sama gani yayi hadari ya fara haduwa sai walƙiya
dake haskawa can ƙasa alamun yanzu hadarin ya fara, garin ya danyu duhu sakamakon rashin wuta ga
kuma hadarin,

ahankali yabi sararin samaniyar da kallo ganin yanda hadarin yayiwa garin zobe kana aƙasan ransa yace
to kodai wannan hadarin ne ya hana J zuwa sai kuma yace to kodai yana ɗakin Innayi ya faɗa yana taka
step ɗin ahankali.

Cikin sauri Innayi ta haske masa ido da touch light mai masifar haske cikin han zari ya Janye hannuunsa
dake danne da J ɗinsa ya tare Idanunsa dashi saboda hasken touchlight daya haska masa ido.

Cike da kulawa Innayi tace.


“Moddibo ya dai lafiya ina zuwa Atsakiyar adaren nan?”.

Ahankali ya sake sakƙowa daga kan step ɗin tare da jingina bayansa da jikin filan barandarsa, kana
hannunsa na dama na kan flowes dake gefe yace.

“Kece fa kike ganinsa tsakiyar dare ne, dudu shabiyu da rabi ne fa yanzu”.

Kallonsa tayi tare da cewa.

“Tsakiyar dare ne mana Moddibo yanzu fa ƙarfe shabiyu harda rabi ai tsakiyar dare ne, to amma me
kafito yi lafiya dai ko?”.

Cikin sanyin murya yace.

“J ne har yanzu bai zo ba kuma ya fito akan zai zo ma ya kirani awaya kan cewa yanzu zai shiga wajen
Abbansa ya masa saida safe ya fito, kuma har yanzu bai iso ba sannan nata kiran layukan sa basa shiga”.

Ya ida maganar akasalance.

Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da cewa.

“Toh dan bai zoba Moddibo ai ba abin tashin hankali bane, kaga yanayin wannan hadarin daya haɗu zai
iya hanasa zuwa wataƙil daya shiga wajen Abban nasa zaice dare yayi kuma ga hadari ya bari sai gobe”.

Da sauri ya katseta da cewa.

“To ai Innayi wayarsa bata shiga fa”.

Saurin Kallonsa Innayi tayi tare da cewa.

“Ka kira layinsa duka?”.

Kai ya jinjina mata.

“Eh na kira layukansa duka fa basa shiga”.

Cikin yanayin bacci ta kalli Moddibo tare da sakin hamma kana ta aro Jarumtaka tare da cewa.

“To ko dai network ne?”.

Lumshe Idanunsa yayi tare da Girgiza mata kai kana yace.

“A'a ba network bane cemin akeyi akashe kuma fa Innayi J baya kashe wayarsa, ko zai kwanta komai
yaya kuma nasan wayar J baya rasa caji”.

A hankali Innayi ta rufe idonta jin kamar tsinkewar zuciya ya ziyarci ta.

Amma sai ta daure kana tace.


“To amma kaga jiya ma kace min wajen Umminsa ya kwana to ko dai yauma yaje canne ne ya kashe
wayarsa dan kada kayi ta kiransa?”.

Jinjina kai yayi tare da faɗin.

“Ok ba mamaki fa bari na kira Ummi”.

Cikin sauri Innayi ta kallesa tare da cewa.

“Aƙarfe ɗaya saura zaka kirasu?”

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Eh Innayi in dai har wurin Ummi yake nasan yanzu zasu ganshi kamar takwas na dare ne, saboda nasan
yanzu suna hira ba suyi bacci ba.

Kai Innayi ta gyaɗa tare da gyara tsayuwar ta kana tace.

“Toh shikenan ka kira”.

Dearling number Ummi yayu.

Acan ɓangaren Ummi kuwa kwance take yayin da idanunta ke lumshe cikin tsananin tsinkewar zuciya da
kasala jin rurin wayarta yasa ta miƙe firgice cikin yanayi sanyi sanya hannunta na dama ta janyo wayar
tare da ƙurawa screen ɗin Ido sunan Moddibo ke yawo.

Cikin sauri tare da rawan jiki tayi Picking call ɗin tare da kaiwa Kunnenta batare data amsa Sallamar daya
mata ba tace.

“Babana Lafiya?”.

Cikin ƙoƙarin danne damuwarsa yace.

“Ummi lafiya ya naji kamar kin razana?”.

Ahankali ta koma ta jingina bayanta da jikin kushin ɗin tare da lumshe idanunta kana cikin wata
raunan'niyar murya mai cike da kasala da tsoro ta fesar da numfashi tare da cewa.

“Gaba ɗaya ma ai. Arazanen nake Babana”.

Moddibo kuwa cikin kasala da mutuwar jiki ya yaja numfashi tare da fesar wa kana yace.

“To Ummi me yafaru?”.


Buɗe Idanunta dake lumshe tayi tare da dafe ƙirjinta da still yake bugawa kana tace.

“Ban saniba amma gaba ɗaya ina jina wani irin gani nan dai kamar mara lfy, kuma ba zance ga abinda
yake damuna kai tsaye ba”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.

“Toh amma Ummi lafiyar ki lau?”.

Kai ta gyaɗa masa kamar yana gabanta kana tace.

“Lafiya ta ƙalau,Amma Babana lafiya ka kira yanzu?”.

Numfashi ya sauke tare da lumshe idanunsa kana ya sake jingina bayansa da jikin step ɗin tare da cewa.

“Eh lafiya lau babu komai dama zan tambayeki ne ko dai J yazo yana wurinki ne munyi dashi tun ɗazu
akan zai zo har yace min gashi ya fito amma zai sallami Abbansa ne kawai ya taho”.

Sai kuma ya lumshe idanunsa tare da cijan lip ɗin sa na ƙasa kana yace.

“Amma har yanzu be taho ba, inata jiran sa ko ƙofar gida bamu rufe ba, shiyasa nace bari na kira koya
biya wajenki, da yake jiya ma nan ya kwana!?”.

Rumtse ida nunta tayi da masifar ƙarfi k cikin wani azabebben tsinkewar zuciya da faɗuwar gaba ta buga
hannunta na dama aƙirji tare da cewa.

_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n. Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan min_

bai zo ba kuma yace maka zai zo?

Abbansa kaɗai zai Sallama?”.

Gyaɗa kai Moddibo yayi tamkar yana gabanta kana cikin raunan'niyar murya mai cike da sanyi yace.

“Eh Ummi”.

Cikin wani irin yanayi na taraddadin zuciya da rauni Ummi tace.

“Ya Ubangiji Allah ka dubeni da Idon Rahma. Ya Allah ka tsare wannan bawan naka, aduk inda yake
Alfarman Annabi da Alkur'ani”.

Jin salatin da kuma yanayin da Ummi tayi Magana cikin firgici ya farkar da Asma'u, Bashir da Malam
Ahmad Aruɗe Asma'u ta miƙe tare da dafe kanta da taji yayi masifar sarawa ta sauƙa daga kan gadon.
Acan ɗakin Bashir kuwa Hasbunallahu wani'imal wakin ya furta tare da sauƙa ƙasa kusan atare suka fito
falon ko wannensu zuciyarsa na bugawa da kaso tamanin cikin ɗari.

Moddibo kuwa cikin sanyu da ruɗu yace.

“Ameen ya Allah Ummi ameen ya rabbil Izzati”.

Cikin zulumi Ummi ta runtse Idanunta kana tace.

“Amma Babana ka kira Abbansa mana”.

Numfashi Moddibo ya fesar tare da kallon Innayi data tsaresa da ido cikin yanayin razani yace.

“Eh Ummi nayi tunanin kiran Abbansa amma sai nace bari na fara kiranki tunda jiya yazo na, sannan
Ummi nasan J baya kashe wayarsa rashin shigar wayarsa nema yafi damuna!”.

Girgiza kai Ummi tayi yayinda ruwan hawaye masu masifar ɗumi suka cika kwarmin Idanunta kana cikin
raunan'niyar murya tace.

“Tabbas baya kashewa ka kira Abbansa kaji”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Eh dama zan kirasa amma Innayi tace ko Abbansa ne ya hanasa zuwa ganin hadari”.

A hankali tace.

“Anya?,Ka kira sa dai”.

“Amma yanzu dare baiyi ba Ummi”.

Cikin sauri tace.

“A'a ka kira Babana ka kira Abbansa ɗin duk yanda kukayi ka kirani ka sanar min”.

“Toh”.

Moddibo yace kana ya katse kiran.

Asma'u da Bashir kuwa zuru-zuru sukayi da ido domin suna iya jiyo sautin muryar Modibbo.
Durƙusa wa Asma'u tayi tare da toshe bakinta kana tashiga.

Girgiza kanta tare da cewa.

“Ya Allah kada ka jarabcemu da abinda baza mu iyaba ɗaukaba Allah ka tsare Yaya Jameel aduk inda
yake ya Allah kada ka bari wani abu na cutarwa ya sameshi”.

Cikin raunin murya Ummi ta kalleta Atake taji wasu hawaye masu masifar ɗumi sun zubo kuncinta.

Ahankali Malam Ahmad da jikinsa yayi masifar sanyi ya ƙarasa kusa da Ummi.

Moddibo kuwa yana katse kiran ya shiga contact tare da fito da Number Abban M Jameel.

Kana ya Kalli Innayi cikin sanyin murya mai cike da tashin hankali yace.

“Kin gani ko Innayi baya can. J baije gidan Ummi ba. Innayi ina J ya tafi bayan yasanar dani cewa zai
taho”.

Lokaci ɗaya wani masifaffen tsoro da tashin hankali ya ziyarci Innayi wanda ta kasa ɓoyewa har hakan ya
bayyana asaman fuskarta dake nuni da tsantsar ruɗu.

Cikin dakiya da kuma nuna masa babu komai insha Allah ta gyara tochligt dake hannunta kana tace.

“Ka dai kira Abbansa muji wataƙil yana can tare dashi hadarin ne ya hanasa fitowa”.

Kai ya gyaɗa mata tare da dearling number Abban M Jameel yana jin yanda zuciyarsa ke cigaba da
bugawa da masifar ƙarfi yana bada sautin dif-dumm-dif dumm.

Abba dake kwance kan 3sitter Idanunsa arufe bacci ya fara fusgarsa yaji suwwan wayarsa Atsakiyar
kansa afirgice ya miƙe tare da zama kana ya duba screen ɗin wayar nan yaga sunan Moddibo na yawo
cikin rawan jiki yayi Picking.

Atare Abba da Moddibo sukayi Sallama.

Ahankali Moddibo ya sauƙe numfashin tare da ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa kana yace.

“Wa'alaikum Salam Abba”.

Cikin yanayin firgici da ruɗu Abba ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.

“Na'am Aliyu ya akayi?”.

Numfashi Moddibo ya fesar kana yace.

“Lafiya Abba”.

Kai Abba ya gyaɗa tare da jingina bayansa da jikin kushin kana yace.
“Ya gida kowa lafiya dai?

Jameelun yaƙara so yana lafiya ko?”.

Lokaci ɗaya zuciyar Moddibo ya buga da masifar ƙarfi kana yayi saurin dafe ƙirjinsa tare da cewa.

“Abba baya gidane”.

Wani irin azabebben bugawa zuciyar Abba yayi kana yace.

“A'a bakwa tare ne tun 10:15 ai ya sallameni yace min zai taho wurinka”.

Moddibo kuwa da sauri ya rumtse idanunsa tare da dafe jikin step ɗin yana mai jin kansa na masifar
sarawa tamkar zai rabe gida biyu cikin raunin murya yace.

“Abba tun ƙarfe 10:15 ya fita kuma yace wajena zai zo? Abba tun ɗazu fa nake jiransa ko ƙofar gida
bamu rufe ba har yanzu J bai zoba sannan fa nata kiran layukan basa shiga”.

Cikin tsananin razani da tsinkewar zuciya Abba ya miƙe tsaye kana yace.

“Aliyu mai kace?”.

Araunane Moddibo da Idanunsa ke juyawa ya dafe kansa kana cikin sanyin murya yace.

“Abba na yita kiran layinsa baya shiga”.

A ruɗe Abba ya miƙa tsaye tare da cewa.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n to lafiya Aliyu?”.

Girgiza kai Moddibo yayi tare da gyara tsayuwar sa kana yace.

“Toh Abba kuma yace waje na ɗin zai taho?Abba J bai zoba bafa”.

ya ida maganar cikin raunin murya mai cike da tsantsar tashin hankali.

Atake zufa ya wanke wa Abba jiki duk da iskar dake kaɗawa d ƙarfi ya haɗiye wani abu mai ɗaci kana
yace.

“Ko dai gidan Ummin sa yaje”.

Da sauri Moddibo ya girgiza kansa muryarsa na rawa yace.


“Um-um Abba baya can yanzu nayi waya da Ummi itace ma tace in Kira ka Dan ni Ina tunanin dare ma
yayi bazan kira ba”.

Cikin tsinkewar zuciya Abba ya nufi ƙofar falon Hajiya Karima da sautin muryansa ya farkar da ita tayi
saurin fitowa daga Bedroom ɗin Aruɗe ta kallesa kana tace.

“Lafiya Alhj?”.

Girgiza kai Abba yayi tare da cewa.

“Jameelu ba agansa ba wai baije wajen Moddibo ba sannan baije wajen Umminsa ba”.

Da sauri ta dafe ƙirjinta kana tace.

“Ba agansa ba kuma gashi yanzu ƙarfe ɗaya”.

Kasa cewa komai Abba yayi ya nufi ƙofa da sauri.

Tare da cewa.

“Miƙo min key mota”.

Cikin sauru tabi bayansa tare da Kallonsa ganin Gajeren wando da single ne kaɗai ajikinsa yasa tace.

“Toh yanzu ina zaka je adaren nan??”.

Cikin raunin murya yace.

“Karima ina zanje kike tambaya ta? Jameelu na fa baya gidansu Aliyu sannan baya gidan Umminsa to ina
Jameelu yaje kinsan waye Jameelu da in dai baya nan yana gidansu Aliyu ko gidan Umminsa tabbas da
akwai abinda yake faruwa”.

Cikin sauri ta juya tare da komawa Bedroom ta dauƙa Masa Jallabiya da key mota kana ta sanya hijabinta
ta fito tare da miƙa masa.

Karba yayi yana tafiya yana saka jallabiyar kana ya nufi inda Motarsa yake ya shiga cikin sassarfa tabi
bayansa yana shiga mazaunin Driver itama tayi saurin buɗe gefen mai zaman banza ta Zauna.

Kallonta yayi tare da cewa.

“A'a ki koma”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“A'a Alh ya za'ayi in barka ka tafi kai kaɗai muje dai”.


Kai ya gyaɗa batare da yace komai ba ya figi motar.

Suka tafi bayan mai gadi ya buɗe masa ahankali ya fara bin hanyar Yana dudduba gefen titin kana cikin
sanyin murya yace.

“To ko dai motarsa ta samu matsale ne?”.

Girgiza kai Hajiya Karima tayi kana tace.

“Idan ma motarsa ta samu matsala Alh ai saidai ya kira akawo masa wata”.

Kai ya jinjina still Yana cigaba da Driving ɗin yayin da zuciyarsa ke cigaba da bugawa da kaso Cassa'in
cikin ɗari suna cikin tafiya har suka isa gidan su Moddibo.

Moddibo dake tsaye coumpund ɗin har zuwa lokacin ya gagara koda ƙoƙƙwaran motsi yayi saurin kallon
gate ɗin ganin hasken mota Itama Innayi dake tsaye tayi saurin bin wajen da kallo zuciyarta na cigaba da
bugawa.

Cikin sauri tare da rauni yace.

“Toh waye wannan ko dai motar J ne?”.

Ya faɗa tare da nufar gate ɗin Innayi kuwa ido ta zuba masa har ya buɗe gate.

Moddibo kuwa yana buɗe gate din idanunsa suka sauƙa akan motar Abba.

Cikin sauri ya ƙarasa jikin motar tare da cewa.

“Abba kaine?”.

Jinjina kai Abba yayi asanda ya ƙarasa fita daga motar kana cikin raunin murya yace.

“Eh Nine Aliyu ina tsammanin Jameelu yana nan to idan ba nan ba ina Jameelu zai je adaren nan.

Amma anya ka bin cika baya gidan Umminsa ba wasa take mana ba?”.

Girgiza kai Moddibo yayi cikin mutuwar da jiki da rauni yace.

“A'a Abba baya can tunda nayi magana da Ummi kuma yanzu da muka gama waya da kai ma na kirata
nace baya can itama kuka fa takeyi”.

Cikin ruɗu da rashin sanin madafa Abba yace.

“Toh kazo muje can ɗin mu duba may be ko motarsa ta ɓaci ahanya can ya nufa”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da faɗin.

“To bari in ɗauki motata dan nasan Innayi ma bazata zauna ita kaɗai agida ba”.

Ya faɗa tare da shigewa cikin gida kai tsaye falonsa ya nufa ya ɗauki key sannan suka fito da Innayi acikin
motar.

Motar Modibbo ce ta shiga gaba na Abba na biye da ita tuƙi kawai Moddibo yake amma baki ɗaya baya
cikin nutsuwarsa.

Acan gidan Ummi kuwa tunda Moddibo ya sanar mata M Jameel baya gidan Abba hankalinta yayi
masifar tashi ta fito coumpund ta tsaya tana kuka yayinda Asma'u da Bashir ke taya ta cikin tsanananin
kaɗuwa.

Cikin rarrashi da nasiyya Malam Ahmad ke tausanta dasu Asma'u.

Cikin sauri Ummi ta ɗaga kanta ganin hasken motoci abakin gate ɗin gidan su.

Aruɗe ta kallesa tare da cewa.

“Ka kalli hasken mota Malam ko dai Jameelu ne?”.

Cikin sanyin murya yace.

“Ki kwantar da hankalin ki Fatima dan Allah ki nutsu Insha Allah babu komai, ba abinda zai samu
Jameelu”.

Kai ta girgiza kana tace.

“A'a to ai naga hasken mota ne”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da riƙe hannunta ganin yanda ta firgice kana yace.

“Toh bari naje na duba naga ko waye ne”.

Kai ta girgiza kana cikin raunin murya tace.

“A'a to muje dai”.

Kai ya gyaɗa tare da yin gaba kana tabi bayansa Malam Ahmad na buɗe ƙaramar ƙofa yaga motar
Moddibo daf da bakin gate Dai-dai lokacin Moddibo ya buɗe Murfin motar ya fito.

Cikin sauri Ummi ta kallesa tare da leƙa motar dake bayansa kana tace.

“Babana”.
Cikin sanyin murya yace.

“Na'am Ummi J bai zo nan ba dagaske?”.

Cikin muryan kuka ta girgiza kai kana tace.

“A'a bai zo bafa Babana idan yazo ya za ayi in ɓoye muku”.

Cikin mutuwar jiki Abba ya buɗe Murfin motar tare da fita kana ya kalli Ummi da hawaye ke bin kuncinta
yace.

“Fatima”.

Saurin Kallonsa Ummi tayi tare da cewa.

“Abban Jameel”.

Cikin yanayin tashin hankali yace.

“Da gaske Jameelu bai zoba?”.

Kai ta gyaɗa Masa still Hawaye na bin kun cinta tace.

“Bai zoba kuma nata kiran wayoyinsa basa shiga”.

Cikintashin hankali da ruɗu suka haɗa baki wajen furta.

_“Innalillahi Wa'inna Ilahi rajiu'n Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha”_.

Cikin sanyi Moddibo ya kalli Abba da idanunsa suka sauya launi saboda tashin hankali kana yace.

“Abba mu koma ta hanyar gidaku mu duba ko dai motarsa ta samu matsala ne ko kuma yayi hatsari
ne?”.

Kai suka gyaɗa cikin sauri Ummi ta juya tare da kallon Moddibo kana tace.

“Bari na ɗauko hijabina muje tare”.

Bata jira jin abinda zasu ce ba ta juya da sauri ta koma tare da ɗaukan hijabinta ta fito coumpund ɗin
kallon Asma'u da Bashir tayi wanda har zuwa lokacin suna cikin ruɗani, cikin Muryan kuka tace.

“Asma'u ku kula da kanku zamu duba hanya ko Allah zaisa mu gansa”.

Cikin sauri Asma'u tace.

“Ummi zamu biku”.

Girgiza kai Ummi tayi tana tafiya tace.


“A'a ku zauna kada ku fito”.

Daga haka ta fice Malam Ahmad na ƙoƙarin ɗauko mota Moddibo yace.

“Ummi kuzo ku shiga motata kawai”,

Kai ta gyaɗa kana tashiga bayan motar kusa da Innayi.

Malam Ahmad kuwa a gaba, kana suka fara tafiya koda da irin tunanin da yake Aransa duk wani inda
suke tunanin mota zai iya maƙalewa ko kuma hatsari sun duba amma babu M Jameel da motarsa babu
dalilinsa har unguwar su Abba suka koma amma still Babu shi babu dalilinsa.

Cikin yanayin gajiyawa da ɗimuwa Abba ya buɗe Murfin motar ya fito kana Moddibo da sauran ma duk
suka fito.

Cikin raunin murya me nuni da razani Abba yace.

“Gashi mun biyo har nan ma amma baya nan, to mu gwada zuwa asibiti mu duba ko dai yayi hatsari ne
ko yaya”.

Cikin raunin murya Moddibo ya Girgiza kai kana yace.

“Abba hatsari kuma? Ai da hatsari ne da munga mota kuma da ankira mu”.

Kafin Abba yace wani abu Innayi ta kalli Moddibo tare da cewa.

“Eh muje dai asibitin saboda Kore shakku”.

Jinjina kai sukayi tare da shiga motar kana suka nufi Asibitin.

Ahankali Moddibo ya kalli Innayi kana yace.

“Toh wani asibitin zamuje kin san dai bawasu manyan asibiti muke dasu ba”.

Cikin sanyi malam Ahmad yace.

“Mu fara zuwa babban asibitin idan yaso sai mu duba sauran daga baya”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da nufar babban asibitin Abba na biye dasu.

Suna isa suka tarar da gate din asibitin arufe kasancewar har biyu tayi,sauran asibitin suka shiga
zagayawa amma ko wanne arufe in sun buga an buɗe musuma in sun shiga bashi ba lbrinsa.

Cikin han zari Abba ya cewa Moddibo su nufi Private hospital ɗin Abba haka kuwa akayi.
Suna isa Moddibo ya sauƙa tare da nufar cikin Hospital kana ya tambayi Norse dake aiki ko M Jameel
yazo suka ce a'a juyawa yayi ya shiga motar kana suka ci-gaba da nemansa.

Wasa gaske fa babu Jameel ba dililinsa ba motarsa, gaba ɗaya sun shiga ruɗu da zulumi gamida tsoro.

Misalin ƙarfe uku hankalin su ya kai ƙololuwa wajen tashi baki ɗaya sun cika da damuwa zuwa wannan
lokacin sun tabbatar ba lafiya domin M Jameel baya yawo sannan Gembulan ba wani babban gari ne da
keda charking point ba bare su kai report.

Moddibo kuwa banda tasbihi da kiran sunan Allah babu abinda yake Aransa yayin da kasala da mutuwar
jikinsa ke ƙaruwa fiye da farko kana ga hadarin da zuwa yanzu yayi gangami asama da alamar ruwa na
gab da sakƙowa, dan tuni aka fara yayyafi.

Abba kuwa tunda suka fito a asibiti ya kifa kansa ajikin motar zuciyarsa na bugawa da masifaffen ƙarfi
cikin raunin murya yace.

“Acikin wannan daren ga hadari na kira layukan Jameeluna duka basa shiga a wannan yanayin ina Jamilu
na ya shiga”.

Cikin raunin murya mai cike da karaya Modibbo ya fesar da numfashi mai zafi kana yace.

“Yanzu acikin daren nan ina J yake?.

Wani hali yake ciki?.

Wani irin yanayi yake cikin a wannan daren da kuma hadarin da yake tasowa ina J ɗina yake!?”.

Cikin ƙarfin hali Malam Ahmad ya numfasa kana yace.

“Insha Allah ba komai mu bari muga zuwa safiya abinda Ubangiji zai yi”.

Cikin tsanananin rauni Ummi ta kife kanta da jikin kujeran Motar kana ta fashe da wani Marayan kuka
mai gunji”.

Cikin damuwa da kuma tausayawa Abba ya juya tare da kallon Malam Ahmad kana yace.
“Malam ku tafi gida kaima Moddibo ku koma gida da Innayi kada ruwan nan ya saƙƙo muna nan duk
inda ya kamata mu duba mun duba baya nan bari mu gani zuwa safiya”.

Girgiza kai Moddibo yayi Araunane yace.

“Abba ya za ayi mu koma mu shiga cikin gida mu samu mafaka bayan bamu san halin da J yake ciki ba.
Abba ina kake tunanin zamu koma mu samu nutsuwa acikin wannan yanayin bayan bamu san ina J yake
ba!?”.

Kallonsa Abba yayi cike da rauni yace.

“Toh Aliyu ina zamuje mu duba?, Duk inda ya kamata mu duba mun duba sannan wayoyinsa basa shiga
wannan shine babban tashin hankalina mu koma gida muyi alwala mu sanar wa Ubangiji halin da muke
ciki Aliyu”.

Jinjina kai sukayi atare cike da gamsuwa da abinda yace sam tashin hankali da ruɗanin da suke ciki yasa
sun kasa samun nutsuwar da zasuyi addu'a.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.

“Toh Abba”.

Sannan suka shiga mota Abba yaja ya nufi gidansu cikin tashin hankali da ɗimuwa yayin da Hajiya Karima
ke kuka Abba kuwa ko da kallonta ya gagara yi bare kuma ya iya lallashin ta.

Ya yinda Moddibo ya nufi gidan Ummi babu abinda ke tashi acikin motar banda sheshsheƙan Kukan
Ummi ta rasa shin wani irin tunani zata yi shin ina Jameelunta yake awannan tsohon daren Akuma irin
wannan lokacin.

Moddibo kuwa cikin tsananin damuwa da zulumi da macewar jiki ya cigaba da Driving har ya isa kofar
gidan yayi Parking.

Fita Malam Ahmad yayi Ummi ma ta sauƙa suka nufi cikin gidan.

Ganin hasken mota yasa Bashir miƙewa da sauri tare da buɗe ƙaramin gate ɗin.

Cikin sauri Asma'u da har zuwa lokacin take zaune ta ɗago kanta tare da miƙewa ta riƙe hannun Ummi
kana tace.

“Ummi Ina Yaya Jameel Ummi kunga Yah Jameel?".

Cikin sanyi Ummu ke jujjuya mata kai.

Ita kuwa a ɗimauce tace. “Ummi to ina yashiga awannan daren dubi hadari fa wani hali yake ciki?”.
Girgiza kai Ummi tayi tare da fashewa da kuka kana tace.

“Ban saniba Asma'u Bansan inda Jameelu na yake ba, bansan halin da yake ciki ba Asma'u zuciyata zafi
take jinake tamkar kaina zai rabe gida biyu!”.

Aruɗe Asma'u tace.

_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha_, nashiga uku Yah
Jameel”.

Cikin sauri Malam Ahmad ya riƙe hannun Asma'u ganin kamar bata hayyacinta kana yace.

“Subhanallah Asma'u da iliminki kike kirawa kanki shiga uku kada ki sake haka Addu'a ya kamata mu
masa kunji ko?”.

Kallonsa ya mayar kan Bashir kana yace.

“Kuzo mushiga muyi masa addu'a ayanzu ba kuka Jameelu yake da buƙata daga wajen muba face
adduoi”.

Kai suka gyaɗa sannan ya sake hannun Asma'u ya riƙe na Ummi Bashir kuma yarike hannun Asma'u suka
shiga ciki kai tsaye ko wannensu toilet yashiga ya ɗaura Al'wala kana ya fito suka shimfiɗa Sallaya tare da
fara jera nafillah suna roƙon Allah daya fitar da M Jameel aduk halin da yake ciki.

Moddibo kuwa suna isa gida yayi Parking tare da rufe ƙofar kana ya wuce falonsa yayin da Innayi ma
tashige sashen ta yana shiga kai tsaye toilet dake falon ya shiga ya ɗaura alwala kana ya fito ya shimfida
Sallaya cike da nutsuwa ya fara Sallah kana duk sujjadar da zaiyi sai ya roƙi Ubangiji ya kare J ɗin sa aduk
inda yake”.

Baki ɗaya su haka suka raya wannan daren cike da bautar Ubangiji tare kuma da rokon Allah daya
bayyanar da M Jameel kana Allah yaraba sa da duk kan sharrin Mutum da Aljan.

Bayan an kira Assalatu Moddibo ya fito ya nufi masallaci ana idar da sallah kai tsaye gidan Abba ya nufa.

Yana isa kiran Ummi na shiga wayarsa ciki. Sanyin jiki ya ɗaga wayar tare da kaiwa kunnensa kana yayi
Sallama.

Cikin dashashshiyar murya Ummi ta amsa Sallamar sa kana tace.

“Babana ya labarin Jameelu na?”.

Cikin sanyin murya yace.

“Ummi nima gashi yanzu nazo wajen Abba naji ko ya dawo gida”.
Dai-dai lokacin Abba ya buɗe gate ya fito ganin Moddibo tsaye yasa ya isa wajensa ahankali Moddibo ya
zare wayar daga kunnensa bayan yace anjina zai kirata.

“Aliyu dama yanzu zanje wajenka”.

A hankali Modibbo yace.

“Abba to yanzu ya zamuyi”.

Numfashi Abba ya fesar tare da cewa.

“To mu tafi police station Jiya Baki ɗaya ba muyi tunanin zuwa can ba”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana suka shiga motarsa yaja Abba kuwa jingina da jikin kujera yayi baki ɗaya
zuciyarsa ta tushe ya rasa wani irin tunani zaiyi yayin da Idanunsa suka tsats-tsafo da ruwan hawaye.

Moddibo kuwa Driving yake amma baki ɗaya baya fahimtar komai ko gilmawar mutum ya gani sai yaga
kamar J ɗin sane.

Suna isa yayi Parking atare suka fito daga motar tare da shiga station din Dpo dake ƙoƙarin fita yayi
Murmushi tare da cewa.

“Alh Bashiru maidala Barka da zuwa kaine da kan ka?”.

Jinjina kai Abba yayi kana cikin sanyin murya yace.

“Na kawo report ne ɗana Jameelu ne bamu ganiba”.

Cike da mamaki da kuma al'ajabi Dpo da sauran folisawan suka ce.

“Ɗan ka Jameelu kuma?”.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“Eh tun jiya ba agansa ba kuma babu motarsa sannan akira layukan sa basa shiga”.

Cike da jimami Dpo yace.

“Subhanallah Alhj mai yasa baku kawo report tun dare ba!?”.

Numfashi Abba ya fesar kana yace.

“Yanayin hadari ne sannan baki daya hankalin mu baya Jikin mu sai mukayi tunanin bari muyi addu'a mu
kaiwa Ubangiji kukan mu”.

Daga nan yayi miki bayanin dukkan abinda ke tafiya.


Kai Dpo ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan Alhj insha Allah yanzu zamu kira hedquater mu na cikin Taraba afaɗa musu halin da ake
ciki”.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“Toh shikenan mun gode”.

Moddibo kuwa tun da suka shiga ya jingina da jikin bango Ya Lumshe Idanunsa yana motsa laɓɓansa
alamar tasbihi bai ce komai.

Wunin wannan ranan baki ɗaya haka gidaje uku sukayi sa cikin zullumi,fargaba da kuma tsantsar tashin
hankali Moddibo kuwa duk bayan minti biyu sai ya kira Number M Jameel aƙalla daga Jiya da daddare
zuwa yau ya kira wayarsa yafi sau ɗari.

Acan ɓangaren Ummi ma haka yakasance bini-bini zata kira layin sa amma amsar ɗaya ake basu shine
Switch off.

Haka zalika Abba time to time zaiyi try number M Jameel amma akashe Wunin wannan ranan baki ɗaya
sunyi zuru-zuru dasu kallo ɗaya zaka musu kasancewa suna cikin tsananin tashin hankali da ɗimuwa duk
inda ya kamata su nema ko su bincika duk sun nema sun bincika amman ba lbri.

Abba kuwa zama yayi afalonsa tare da kira duk wani danginsa ko kuma abokin arziki ko zaiji Jameelu yaje
amma kowa amsa ɗaya yake basa baije ba.

Haka zalika Ummi baki ɗaya ta kira danginta ko M Jameel yaje amma suma dai amsar ɗaya ce baije ba.

Wunin wannan ranan har dare babu M Jameel babu labarin sa zuwa wannan lokacin tsananin tashin
hankali da ruɗun da suke ciki ba zai misaltuba.

Da daddare Misalin ƙarfe goma Moddibo ne zaune a falon Abba kansa aƙasa yayinda idanunsa suka kaɗa
sukayi ja jawur kana jijiyoyin kansa sun tashi sunyi ruɗu ruɗu rabonsa da bacci tun daren shekaran jiya
haka zalika yauma koda runtsawa ne yakasa kana ya sanya duka hannunsa biyu ya dafe kansa dashi zuwa
lokacin baki ɗaya ya kasa control ɗin kansa kife kansa yayi ajikin kujera tare da fashewa da kuka mai
gunji.

Cikin wata raunan'niyar murya mai cike da karkarwa yace.

“Abba ina J yake? Abba ina J ya tafi ya barni Abba wani hali J yake ciki?”.
Hajiya Karima ce tashigo falon bakinta ɗauke da Sallama tare da kallon Moddibo dake kuka tamkar
ƙaramin yaro lumshe Idanunta tayi tare da cewa.

“Haba Aliyu kuka kuma kai da ya kamata ka tausashi Mahaifinsa sannan kuma ka zauna zakuyi ta kuka
atare kenan?”.

Karo na farko kenan arayuwar data yi masa magana cikin taushin lafazi.

Ahankali Moddibo ya ɗago kai ya kalleta still yana kuka yace.

“Aunty Karima ina J yake Ina J ɗina yashiga ya barni?”.

Cikin rauni Abba ya ɗago idanunsa da hawaye ke zuba Akuma dai-dai lokacin wayar Abba ta ɗauki ruri
yana ɗagawa yaga number ce ba suna sai ya mayar ya ajiye.

Kallonsa Moddibo yayi tare da faɗin.

“Abba waye ne?".

Ciki Sanyin Abba ya kalli wayar kana yace.

“Numbar ce ba suna”.

Cikin muryan kuka Moddibo yace.

“Toh Abba ka ɗaga mana ko za'a faɗa mana anga J ne”.

Cikin sauri Abba yayi Picking call ɗin tare da cewa.

“Assalamu Alaikum”.

Daga ɗaya ɓangaren cikin wata bauɗaɗɗiyar murya aka amsa da.

“Wa'alaikum Salam kaine Alhaji Bashiru Maidala mahaifin Malam Jameelu?”.

Cikin sauri Abba ya gyaɗa kai tare da miƙewa tsaye kana yace.

“Eh nine mahaifin Jameelu”.

Cikin sauri Moddibo ya miƙe tsaye,

itama Hajiya Karima cikin sauri ta miƙe tsaye.

Gyaran murya yayi kana yace.

“Toh Jameelu yana wajen mu”.

Cikin rawan baki Abba yace.

“Jameelu yana wajen ku yana cikin halin lafiya? To a ina kuke?”.


Kai tsaye yace.

“Eh gashi ma kaji muryarsa”.

Ya faɗa tare da miƙawa M Jameel wayar.

Cikin sauri Abba yace.

“Jameelu”.

M Jameel kuwa cikin wata raunan'niyar murya me cike da galabaita da tashin hankali kamar wanda yayi
kuka yana sauƙe ajiyar zuciya yace.

“Abbana”.

Cikin rawan jiki da rauni Abba yace.

“Na'am Jameelu Meye sameka?,Aina kake?”.

Ajiyar zuciya mai nauyi M Jameel ya sauƙe cikin rauni da yanayi wahala yace.

“Abba nima ban sani ba bansan inda nake ba Abba ina A.J”.

Cikin muryan kuka Abba ya kalli Moddibo da jikinsa ke rawa kana yace.

“Gashinan".

Ahankali M Jameel dake sakin ajiyar zuciya yace.

“Abba ka bashi wayar”.

Miƙawa Moddibo wayar Abba yayi cikin sauri Moddibo ya amsa tare da mannawa akunnensa kana Yace.

“Jyyyyyy”,yaja sunan cike da taraddadi.

Fesar da numfashi M Jameel Yayi tare da cewa.

“AJ”.

Cikin yanayin rauni da tausayawa ya lumshe idanunsa tare da cewa.

“J ina kake?”.

Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.

“AJ ban sani ba bansan inda nake ba, ban san ida suka kawoni ba”.

Cikin sauri aka Fisge wayar daga hannun M Jameel kana cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya akace.

“Ka bawa mahaifinsa waya”.


Ahankali kuma cikin sanyi Moddibo yace.

“Waye kai ina J yake?”.

Cikin wata razananniyar tsawa yace.

“Kabawa mahaifinsa waya ba da kai muke son magana ba?".

Moddibo kuwa Girgiza kai yayi kana yace.

“Toh me kuke so ku faɗa min ko mameye”.

Cikin sauri Abba ya janye wayar daga kunnensa tare da sa wayar a handsfree kana yace.

“Gani mahaifin Jameelu".

Daga ɗaya ɓangaren mutumin yace.

“Jameelu yana hannunmu bawai mun sace sa dan mu kashe sa ko wani abu bane amma idan kuka yi
mana taurin kai zamu iya kash”...

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki
0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP
09097853276*

*By*

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYA

28

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki littafin
1k kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP
09097853276, sai in saki a Group ɗin*

28
“Idan har kana son rayuwar ɗanka to.

Kabi sharaɗin mu kabi tsarinmu, sannan kabi dukkan dokokin, muddin kana so Jameel ya rayu idan kuma
ka kuskura kayi mana taurin kai kayi mana gardama kan sharuɗan da muka ginda ya maka to zakaga
abinda zai biyo bayan gardama”.

Cikin tsanananin kaɗuwa Abba ke girgiza kai yayin da bakinsa ke rawa ya gaza furta komai.

Cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya mutumin ya cigaba da cewa.

“Dama kai tsaye mu aikin kashe sa aka bamu. Toj amma saboda nagartansa da mutuncinsa yasa mukaji
bama buƙatar kashe Malam Jameelu munfi ɓuƙatar abada kuɗi musakeshi domin shi Jameelu na
kowane, kauda irinsu a doron kasa asarace data shafi, dukkan al'umma, dan haka kabi sharuɗanmu mu
sakeshi salamun-salaman ya dawo hannunku hankali kwance, idan kuma ka kuskura kayi mana gardama
duk da na gartan Jameel zamuyi abinda muma ranmu bai soba!”.

Cikin tsanananin tsoro da tashin hankali Abba ya dafe ƙirjinsa da hannu ɗaya kana yace.

“Innalillahi.

Dan Allah ku faɗa min koma me kukeso zan baku bazan muku gardama ba da Izinin Ubangiji”.

Cikin wata kakkausar murya mutumin yace.

“Bayan kai wanda mu kejin sa agefenka kada ya mana gardama domin shine Amininsa Moddibo”.

Girgiza kai Abba yayi still jikinsa na rawa kana muryarsa cike da rauni yace.

“Ba zaiyi gardama ba”.

Gyaran murya Mutumin yayi kana yace.

“Kasa amsa kuwwa shima Moddibo yaji abinda ake magana akai”.

Kai Abba ya gyaɗa still muryarsa na rawa yace.

“Nasa, nasa, nasa”.

Cikin bada umarni mutumin yace.

“Ku nutsu ku zauna ku jini”.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“Toh”.
Gyara murya mutumin yayi cike da isa yace.

“Baku zauna ba nasan atsaye kuke”.

Atare Abba, Moddibo da Hajiya Karima suka zauna Araunane Abba yace.

“Toh mun zauna wallahi”.

Kai Mutumin ya gyaɗa tare da faɗin.

“Yayi kyau sharaɗin mu na farko da zamu ƙidanya muku idan ka bishi Jameel ya rayu idan kuwa baka
bishi ba Jameel ya mutu wannan shine sharaɗi na farko kuma shine mafi tsauri”.

Ajiyar zuciya kawai Moddibo ke sauƙewa zuciyarsa na cigaba da bugawa da masifar ƙarfi.

Mutumin ya cigaba da cewa.

“Sannan yanzu rayuwar Jameel yana hannunka da kai da Amininsa da kuma mahaifiyarsa da ma sauran
Makusantan ku, idan kuka mana gardama kamar kuna wasa da rayuwar Jameel ne”.

Atare Moddibo da Abba suka haɗa baki wajen cewa.

“Meye kuke buƙata menene sharaɗin naku?”.

Kai Mutumin ya gyaɗa kana yace.

“Sharaɗin namu shine wannan maganar kada ku yarda kada ku kuskura koda agigin bacci koda amafarki
kusa hukuma acikinta!”.

Moddibo kuwa ƙirjinsa ne ya buga cikin sauri ya dafe kansa da hannunsa biyu tare da kifa fuskarsa ajikin
kushin kana ya furta.

“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n”.

Cikin ƙasa da murya Abba ya runtse Idanunsa tare da cewa.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin”.

Cikin tsawa mutumin yace.

“Zaku faɗa kenan!?”.

Da sauri Moddibo ya girgiza masa kai dake kife akan kushin kamar yana gabansa kana yace.

“Ba zamu faɗa ba wa kowa ba, mudai fatan mu J ya kasance cikin ƙoshin lafiya, kada ku cutar dashi”.

Taɓe baki Mutumin yayi kana yace.


“Kada ku yarda kada ku kuskura ku sanya hukuma aciki”.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana yace.

“Ba zamu faɗa ba da izinin Ubangiji zamu bi sharaɗin ku.

Amma sai dai kafin ma ku kiramu mun kaiwa hukuma maganar amatsayin Jameel ya ɓata tunda mun
kwana babu shi sannan mun wuni babu shi toh munje wajen hukuma amma bawai munje amatsayin
mun kai ƙorafi akan ku bane”.

Jinjina kai Mutumin yayi tare da taɓe baki kana yace.

“Toh wannan sharaɗine Idan hukuma sun dawo dan suna nan kamar Mayu, daga sunji babu mutum idan
sun sake kawo kansu kada kuce mun nemi kuɗi awajenku”.

Yarfe hannu Hajiya Karima tayi tare da girgiza kai ta ƙurawa Abba Ido tamkar shike maganar.

Cikin bauɗaɗɗiyar murya Mutumin ya cigaba da cewa.

“Muddin kana son ran Jameel to.

Kayi shiru da bakin ka idan mun kafa maka sharaɗi na biyu ko kuma mun faɗi abinda mukeso kun bayar
to Jameel zai dawo amatsayin ɓata yayi sannan ba sace sa akayi ya dawo ba”.

Abba kuwa buɗe idanunsa dake lumshe yayi kana yace.

“Insha Allah zamu bi sharaɗin ku amma yanzu mai kuke so ku faɗa min”.

Cikin sauri ya janyo wayar tare da kallon screen ɗin jin ɗit-ɗit-ɗit alamar an kashe.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da rintse idanunsa da karfi kana yace.

“Innalilahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin”.

Moddibo kuwa da still hannunsa ke dafe akansa yana taune lip ɗin sa na ƙasa babu abinda ke fita
abakinsa face kalmar Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n.

Hajiya Karima kuwa Girgiza kai kawai take tare da yarfe hannu kana tana mai maimaita kalmar
Hasbunallahu wani'imal wakin ta juya tare da kallon Abba da idanunsa suka kaɗa suka yi jawur sannan
tace.

“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n wannan wani irin zamani Allah ya kawo mu kenan ƴan Kidnapping ne
suka ɗauke Jameelu”.
Lokaci ɗaya Moddibo ya sake dafe kansa da karfin yana cigaba da taune lip ɗin sa na ƙasa.

Girgiza kai Hajiya Karima tayi kana ta cigaba da cewa.

“Amma Alhj wannan sharaɗin nasu zancene na banza ina muke da yaƙinin zasu iya kare Jameelu ba zasu
cutar da shiba ba gwara mu faɗawa hukuma ta shiga cikin maganar nan ba”.

Cikin sauri Moddibo ya ɗago kansa daga jikin kushin wanda sai alokacin ya samu damar hakan hannunsa
biyu ya haɗe waje ɗaya alamun roƙo kana ya runtse Idanunsa da ƙarfi ya shiga.

Girgiza kansa muryarsa na rawa yace.

“A'a,a'a,a'a Aunty Karima kiyi wa Allah da Manzonsa kada ki sako hukuma acikin maganar nan Wallahi
kina sa hukuma zasu iya yiwa J komai kiyiwa Allah kada kisa hukuma aciki kiji abinda suka faɗa mana”.

Abba kuwa jujjuya kai ya shiga yi kana idanunsa akan Hajiya Karima yace.

“Karima ban yarda ba ban yafe ba wannan maganar ya fita muddin kinaso Jameelu na ya dawo kada ki
faɗawa hukuma wannan maganar”.

Kai ta gyaɗa cike da damuwa.

Kallon wayarsa Abba yayi tare da cewa.

“Yanzu bari na sake kiransu naji me suke buƙata”.

Ya faɗa tare da dearling number amma swich off”.

Ɗagowa Abba yayi tare da kallon Moddibo kana yace.

“Aliyu Wayar akashe”.

Cikin sauri Hajiya Karima tace.

“Ai dama zaiyi wuya yashiga ya za ayi ya shiga ai ba zai taɓa shiga ba”.

Daga Abba har Moddibo babu wanda yace komai Allah ne kaɗai yasan abinda suke ji aransu.

Dai-dai lokacin Hajiya Turai ta shigo bakinta ɗauke da Sallama kusa da Hajiya Karima ta zauna Idanunta
sun kaɗa sunyi jawur har sun kumbura alamar tayi kuka ta gaji Idanunta akan Abba tace.

“Alhj har yanzu babu labarin Jameelu”.


Kafin Abba yace wani abu Hajiya Karima tayi saurin cewa.

“Yan zun nan ƴan Kidnapping sun Kira su suka ɗauke sa!”.

Cikin sauri Hajiya Turai ta dafe ƙirjinta tare da cewa.

“Hasbunallahu wa niimal wakil Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n,Ƴan Kidnapping kuma Alhj!?”.

Girgiza kai Abba yayi sai kuma ya riƙe tafin hannunta kana yace.

“Ki zauna”.

Ba musu ta tazauna jikinta na rawa saboda tashin hankali da take ciki.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana ya maida kallonsa kan Hajiya Karima tare da cewa.

“Wannan maganar daga mu sai mu iya mu nan kada ku kuskura maganar nan ta fita iya mu nan ban
amince ba kuma ban yafe ba daga ke har Karima ban amince ku kai maganar nan kunnen hukuma ba,
duk wacce takai abakin igiyoyin auren ta duka saboda sun sa sharaɗin idan na yarda hukuma ta shiga
zasu kashe min Jameelu”.

Ya ida maganar cikin raunin murya.

Kai Hajiya Turai ta girgiza cikin Muryan kuka tace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n in sha Allah ba zamu faɗa ba Alhj yama za ayi mu faɗa ai wannan ba abin
faɗa bane!”.

Hajiya Karima ma cikin sauri ta girgiza kai kana tace.

“Insha Allah ba zamu faɗa ba, zamu kiyaye”.

Moddibo kuwa har zuwa yanzu yana dafe da kansa da hannu biyu still Idanunsa aruntse.

Ahankali Abba ya kira sunan sa tare da cewa.

“Aliyu”.

Araunane Moddibo ya ɗago idanunsa da sukayi Jawur kana sun kumbura ga lip ɗin sa na ƙasa sunyi ja
kana ya ɗan kumbura.

Cikin rauni ya kalli Abba tare da cewa.

“Na'am Abba”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.

“Aliyu ya zamuyi?”.

Zazzafafar ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da cewa.

“Abba sai dai mu jira kiran su na biyu muji mai suke buƙata magana ce dai na kuɗi atanadi abinda suke
bukata a ajiye tun wuri”.

Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh Aliyu amma yanzu ya zamuyi da mahaifiyarsa inaga kada ka faɗa mata halin da ake ciki”.

Moddibo kuwa kallon Abba yayi kana ya girgiza kansa tare da cewa.

“Abba kar afaɗa mata kuma? Ai gwara tasan cewa J yana raye, domin zuciyar Ummi zata iya bugawa da
idan ba afaɗa mata ba gwara in Faɗa mata tasan cewa J yana raye tasan cewa munyi magana da shi naji
muryansa, kaima kaji muryan J fa yanda muka yi magana dashi ƙilan sun dake shi!”.

Ya faɗa cikin raunin murya.

Runtse Idanu Abba yayi da ƙarfi hawaye masu zafin gaske suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar.

Moddibo kuwa still Idanunsa na runtse ya gagara buɗewa har zuwa yanzu yana jin muryan M Jameel na
cewa A.J bansan inda nake ba ban san ina nake ba.

Cikin rauni ya ɗago kansa muryarsa na rawa yace.

“Abba kaji fa J cewa yake baisan inda yake ba Abba ina suka kaisa ina suka cusa sa”.

Dafa kansa Abba yayi kana yace.

“Aliyu duk yanda za ayi idan ka faɗawa Fatima kada ta faɗawa kowa, sannan ka kiyaye yanda zaka faɗa
mata kada hankalinta ya tashi!”.

Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.

“Abba ba zata faɗawa kowa ba idan na faɗa mata halin da ake ciki”.

Jinjina kai Abba yayi tare da cewa.

“Toh shikenan Aliyu ka kula”.

Kai Moddibo ya gyaɗa dai-dai lokacin kiran Ummi ya shigo wayar Moddibo kallon Abba yayi kana yace.

“Abba ka gani ko kirana ma take yi yanzu kafin na wuce gida ma saina biya wajenta”.
Cike da rauni Abba yace.

“Toh shikenan tashi kaje Aliyu gashi kaima har ƙarfe goma na dare yayi tsoro nakeji, jiya a irin ya wannan
lokacin suka ɗauki Jameelu”.

Runtse Idanu Moddibo yayi tare da miƙewa kana ya yiwa su Hajiya Turai sallama ya fita har kofar gida
Abba ya rakasa sai da yaga tashin motarsa kafin ya koma cikin gida zuciyarsa na zafi.

Cikin sanyin jiki yayi parking kana ya fita ƙaramin ƙofar ya tura ya shiga A baranda ya hango Ummi,
Asma'u da Bashir Idanun Ummi da Asma'u sun kaɗa sunyi Jawur dasu kana sun kumbura.

Bashir kuwa cikin dauriya kasancewar sa namiji yasa ya riƙe hannun Asma'u dake kuka tare da cewa.

“Ummi ki kwantar da hankalin ki da izinin Ubangiji ba abinda zai samu Yah Jameel Allah zai tsaresa aduk
inda yake Asmey ki daina kuka dan Allah”.

Girgiza kai Asma'u tayi cikin Muryan kuka tace.

“Bashir taya zamu iya tsaida hawayen mu bayan bamu san halin da Yah Jameel ke ciki ba!?”.

Cikin rauni Ummi ta ɗago kanta Idanunta ya sauƙa akan Moddibo dake shigowa Iska na kaɗa sa duk yayi
sauya cikin sauri Ummi ta miƙe jikinta na rawa ta nufesa tare da cewa.

“Babana”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana ya zuba mata Ido cike da tausayawa ganin kamar
bata cikin nutsuwarta ƙarasawa kusa da ita yayi tare riƙe hannunta kana suka zauna agefen barandar
cikin sanyin yace.

“Ummi”.

Kallonsa tayi tare da cewa.

“Na'am Babana ya labarin Jameelu na”.

Sunkuyar da kansa yayi tare da cije labɓansa na ƙasa wanda zuwa lokacin sunyi masifar ja kana sun
kumbura yayin da Idanunsa ke tsats-tsafo da ruwan hawaye sai dai sun gagara zubo wa.

Ahankali ya ɗago kansa tare da damƙe hannun Ummi na dama acikin nasa kana yace.

“Ummi munyi waya da J”.

Cikin sauri Ummi ta zaro Idanunta duka waje kana tace.

“Kayi waya da Jameelu”.

Kai ya gyaɗa mata hawaye masu zafi suka zubo akuncinsa.


Kallonsa Ummi tayi tare da faɗin.

“Kayi waya da Jameelu Babana kuma kana kuka!?”.

Moddibo kuwa kallonta yayi cikin ƙoƙarin tsaida hawayen sa yace.

“Ummi anyi Garkuwa Da shine”.

Cikin matsanancin tashin hankali Asma'u ta ɗaura hannunta akai tare da cewa.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.

Ta dire addu'ar tare da komawa ta zaun.

Ita kuwa Ummu wani irin zazzafan numfashi ta fesar tare runtse idanu kana ta buɗe su akan Moddibo
cikin dan sassaucin tashin hankali da take ciki tace.

“Toh ai ba komai Babana kawai Abbansa yayi ƙoƙarin haɗa kuɗi da suke buƙata a basu, su sako mana shi.

Alhamdulillah tunda yana raye, domin ai wannan abune da ya zama ruwan dare, tunda su dai in an basu
abinda suke so basa kisa.”

Sai kuma ta lumshe idanunta wasu sirran hawaye suka gangaro mata cikin raunatacciyar murya tace.

“Waya sace min Jameelu na!? Waya sacemin farin ciki na!?

Waya ɗauke min jin daɗina!?

Waya ɗauke min Garkuwana da gatana!?

Wayake son yimin shamaƙi da bangona majinginata!?”.

Moddibo kuwa hannunta ya riƙe acikin nasa kana yace.

“Ummi dan Allah ki daina kuka addu'a zakiyi masa kamar yadda kikace abinda suke so kawai za'ayi musu,
sun kuma gargaɗemu kada asa hukuma a cikin mgnar, sai muyi ƙoƙarin kiyayewa”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da share hawayen ta amma still wasu na zubowa.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da zayyane mata duk yanda sukayi.

Atare Asma'u, Ummi,da Bashir suka sauƙe nannauyan numfashi.

Kallon Moddibo Ummi tayi kana tace.

“Babana basu faɗi nawa suke so bane?”.


Kai ya girgiza tare da cewa.

“Ummi basu faɗa ba tukunna sharaɗin su na farko suka bamu kada ayarda a faɗawa hukuma”.

Ajiyar zuciya mai haɗe da jan zuciya Ummi ta sauƙe still tana hawaye tace.

“Ba zan faɗa ba Insha Allah bazan faɗa ba Babana.

Ba zan faɗa ba”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da cewa.

“Ummi ki cigaba da addu'a Insha Allah babu abinda ya gagari Ubangiji kuma Insha Allah tunda suka fara
kira zasu sake kira su faɗi abinda suke so sai ayi ƙoƙari amusu abinda suke so”.

Jinjina kai tayi kana tace.

“Insha Allah gobe zanje gidan su muyi magana da Abbansa idan Malam ya bari”.

Dai-dai lokacin Malam Ahmad ya shigo cike da tausayawa yake Kallonsu kana yace.

“Nama bari Fatima na bari Allah ya tsaresa ya kuma bayyana sa aduk inda yake”.

Atare suka amsa da Ameen.

Miƙewa Moddibo yayi kana yace.

“Ummi zan tafi gida”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Toh Babana Allah ya kiyaye”.

Ameen ya amsa sannan ya juya ya fice cikin mutuwar jiki.

Yana isa gida yayi Parking tare da fitowa ya rufe ƙofar kana ya shiga falon baki ɗaya abubuwan sun ca
kuɗe masa ga rashin bacci rabonsa da bacci tun daren shekaran jiya ga tashin hankali da damuwa baki
ɗaya zulumi sun mishi rubdugu ya fita hayyacinsa sai alokacin ya tuna baki ɗaya wayewar garin yau baiyi
wanka ba cikin kasala ya nufi toilet din sai dai baya tunanin zai iya yin wanka, al'wala ya ɗaura kana ya
fito tare da shimfiɗa darduma ya fuskanci alƙibla cike da nutsuwa ya shiga gabatar da nafillah aduk
lokacin da ya kai goshinsa kasa (Sujjada)Sai ambaci J dinsa, raka'a huɗu yayi bayan ya idar ya ɗauki
Alkur'ani mai girma kana ya fara karantawa Acikin Suratul An-Nisa'i har Misalin ƙarfe 2:00am yana
karatun idan ya karanta wani aya sai M Jameel ya faɗo Masa arai kana ya tuna da wasu lokutan idan
yana karatu yazo wajen Ayar azaba saiya rufe Kur'anin ya Rungume kana yaita kuka idan kuma yazo
wajen Ayar Rahma sai yaita sakin murmushi kana yana cigaba da karatun.
Ahankali Moddibo ya runtse Idanunsa tare da Rungume Kur'anin aƙirjinsa idanunsa sun kaɗa sunyi jawur
dasu kana sun kumbura saboda tashin hankali da yake ciki har aka kira Assalatu Moddibo bai rintsa ba.

Haka zalika ɓangaren Abba ma ya kwana ba tare daya rintsa ba acikin kwana ɗaya da yini duk ya canza
yayi zuru-zuru dashi.

Washe gari da safe:Misalin ƙarfe 8:00am Abba ne zaune afalonsa ya ƙurawa wayoyinsa Idanu koda
motsin kirki ya gagara baki daya hankalin sa nakan wayarsa.

Cike da ladabi mai gadi yayi Sallama ɗagowa Abba yayi ya kallesa kana ya amsa masa Sallamar.

Cike da tausayawa mai gadin yace.

“Alhj ga baƙi awaje”.

Numfashi Abba ya fesar kana yace.

“Su waye ne?”.

Tsayuwa mai gadin ya gyara kana yace.

“Hukumar ƴan sanda ne wai daga Taraba suka zo”.

Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh ka shigo dasu”.

Kai mai gadin ya gyaɗa kana ya fice yace su shiga.

Dai-dai lokacin Moddibo yazo Parking motarsa Yayi kusan atare suka shiga ƴan sandan mutum biyar na
gaba shi Kuma yana bayansu.

Bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga wajen zama Abba ya nuna musu bayan ya amsa Sallamar su.

Moddibo kuwa gefensa ya nufa ya zauna cikin mutuwar jiki da damuwa.

Gyaran murya ɗaya daga cikin ƴan sanda yayi kana Idanunsa akan Abba yace.

“Sunana Asp Mahmud Adam Shani daga rundunar ƴan sandan jahan Taraba masu bincike akan abinda
ya shafi ɓatan mutane da kuma kisan kai kana da fashi da makami ina fatan zaku bamu haɗin kai.

Mun samu kirane daga nan ƙaramin Headquarter din mu”,'.


Sai kuma ya sauƙe numfashi tare da kallon Moddibo da yayi ƙasa da kansa kana yana motsa laɓɓansa
alamar tasbihi yake.

Kana ya cigaba da cewa.

“Mun samu masaniya Kan cewa Jameel ɗan Alhj Bashiru Maidala ya ɓata shiyasa nazo da kaina inji
ba'asin maganar sannan muga ta inda ya kamata mu fara da taimakon Allah da kuma baya nan da zaku
bamu zamuyi nasara wajen gano inda yake”.

Jinjina kai Abba yayi tare da rintse idanunsa kana ya fesar da numfashi tare da sunkuyar da kansa ƙasa
hawaye masu zafi suka zubo masa.

Cike da tausayawa Asp Mahmud Adam Shani yace.

“Alhj ka kwantar da hankalin ka kayi min duk kan bayanin da zan gane saboda yanda zamu kula da aikin
da kuma abinda ya kamata ayi akai”.

Jinjina kai Abba yayi tare da ƙoƙarin hana hawayensa zuba kana ya daure yace.

“Jameelu nine mutum na ƙarshe da yayi sallama dani ya fita ina tsaye ajikin window har ya fita bayan
fitarsa na kai kimanin awa ɗaya da rabi ina tsaye ajikin window, Bayan nan kuma duk cikin mu babu
wanda yayi magana da Jameelu domin ya fita akan zaije wajen Abokinsa amma bai isa ba”.

A hankali ya fesar da zazzafan iska tare da taune lip ɗin sa na ƙasa tare da kallon Asp Mahmud Adam
Shani kana yace.

“Adaren Abokinsa yazo domin rashin samun layinsa da bai yiba”.

Jinjina kai Asp Yayi kana yace.

“Eh anyi min wannan bayanin daga Headquarter din mu na Nan Inspector Ayuba Garba kumo ya sanar
dani komai to amma daga ɓatansa zuwa yanzu babu wanda ya kira ka!?”.

Cikin sauri Abba ya Girgiza masa kai kana yace.

“A'a babu".

Ido Asp ya zuba masa kana yace.

“A'a Alhj Bashir dan Allah kada kuce zaku bi sharuddan ire-iren mutane masu garkuwa da mutane, idan
har akwai wanda ya kira ka ya maka barazana ko kuma ya nemi wani abu ka faɗa mana ko kuma ka bami
number da suka kira Insha Allahu Jameelu zai kuɓuta sannan zai rayu da izinin Ubangiji zamu tsera tar
dashi”.

Moddibo kuwa cikin sauri ya kalli Asp zuciyarsa na bugawa da masifar ƙarfi ya Girgiza kai tare da cewa.

“Babu wanda ya kira ai da akwai wanda ya kira zamu sanar daku sannan mu ma da hankalin mu zaifi
kwanciya ma, mun san cewa yana raye”.
Ido Asp ya tsira musu kana yace.

“Anya kuwa anya babu wanda ya kira ku!?”.

Cikin sauri Moddibo ya gyaɗa kai kana cikin ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa yace.

“Babu wanda ya kira tashin hankalin mu kenan”.

Abba ya karɓi maganar da cewa.

“Da har ankira Asp Mahmud da ace ankira kamar yanda kake zaton ƴan Kidnapping ne kuma sun buƙaci
kuɗin ai da tuntuni nayi muku bayani sannan idan yakama da in basu kuɗi zasu dawo min da Jameelu na
da tuni na bayar an dawo min da Jameelu na!”.

Anutse Asp ya gyara zamansa kana cikin sauri yace.

“Alhj na roƙe ka dan Allah koda ankira ance kuɗi ake buƙata kada ka basu, kawai ka bamu Number
sannan kayi mana bayani shine abinda muke bukata amma ana temakamu sune sannan ana ƙara basu
ƙarfin gwiwa dayi musu abinda suke so shiyasa suke ƙara yin abinda suke su ɗin”.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da jingina bayansa da jikin kujeran kana yace.

“Insha Allahu zanyi ƙoƙari duk abinda ake ciki zan sanar muku Nagode sosai musamman tattakin da kayi
daga Taraba zuwa nan”.

Dai-dai lokacin Hajiya Karima tazo Idanunta akan Asp Mahmud Adam Shani da sauran Folisawan Kallonta
ta mayar kan Abba kana tace.

“A baƙi mukayi ne sannun ku da zuwa”.

Asp dake rubutu awata ƙaramar takarda yace.

“Yawwa”.

Kana ya cigaba da rubuce-rubucen sa.

Kallon Abba Hajiya Karima tayi tare da kallon Moddibo da idanunsa ke lumshe haƙoransa uku na sama
na kan laɓɓansa na ƙasa numfashi ta fesar kana ta ƙara sa kusa da Abba da har zuwa lokacin bayansa ke
jingine ajikin kujera tace.

“Alh ga Hajiya Fatima mahaifiyar Jameel ta iso”.

Ahankali Abba ya ɗago kansa kana cikin sanyin murya yace.

“Kice ta iso”.
Kai ta gyaɗa tare da juyawa ta fita ba jimawa ta shigo Ummi na biye da ita Ahankali Ummi ta ƙara sa kusa
da Moddibo ta zauna Hajiya Karima ta juya ta fice cike da tausayawa Moddibo da Abba ke kallonta ganin
yanda Idanunta suka kumbura sukayi jawur sun ƙanƙance.

Anutse Asp ya ɗago kansa tare da kallon Ummi kana yace.

“Wannan ce mahaifiyarsa?”.

Kai Abba ya gyaɗa tare da faɗin.

“Eh itace”.

Atausashe Asp ya gyara zamansa tare da cewa.

“Sannu Mmn Jameel Ubangiji Allah ya bayyana sa ya kuma tsaresa aduk inda yake, ki kwantar da
hankalinki in sha Allah zamuyi iyakar iyawarmu zamu samoshi a duk inda yake”.

Kai ta gyaɗa cikin muryanta daya dishe da kuka tace.

“Ameen ya Allah”.

Miƙewa Asp Yayi kana yace.

“Alhj to bari mu tafi amma dan Allah duk abinda ake ciki a faɗa mana”.

Kai Abba ya jinjina tare da cewa.

“Toh Insha Allah”.

Bayan tafiyarsu Ummi ta juya tare da kallon Abba cikin raunin murya tace.

“Alhj har yanzu basu sake kira ba!?”.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“Fatima har yanzu basu kira ba”.

A raunace ta sanya gefen hijabinta tare da share hawayen da suka zubo mata kana tace.

“To idan sun sake kira duk abinda suke so dan girman Allah kataima keni kaceci rayuwar Jameel kayi
musu”.

Girgiza kai Abba yayi idanunsa na tara ƙwalla yace.


“Fatima ba sai kin roƙeni kin haɗa Ni da Allah ba, idan har banyi musu abinda suke so andawo min da
Jameel ba menene amfanin dukiyata?”.

Sai kuma ya runtse Idanunsa kana ya cigaba da cewa.

“Jameel yafi min komai aduniyar nan zan iya sadaukar da duk dukiyata domin ceton rayuwar Jameel
insha Allah zanyi iya bakin ƙoƙarina wajen ganin ya dawo”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.

“Toh shikenan Nagode Ubangiji Allah ya kuɓutar dashi Allah yasa su faɗi abu mai sauƙi kada su faɗi
abinda yafi ƙarfin mu Allah ya tsaresa Allah yasa yana cikin ƙoshin lafiya”.

Atare Moddibo da Abba ke Amsawa da Ameen cike da tausayawa.

Kallon Abba tayi kana tace.

“Bari na tafi gida”.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“Toh shikenan”.

Cikin sanyin murya Moddibo yace.

“Ummi muje in kaiki gida”.

Kai ta gyaɗa kana ta miƙe.

Suka fita da kallo Abba ya bisu cike da tausayawa.

Moddibo kuwa yana ajiye Ummi agida kai tsaye makarantar Malam Arɗo ya nufa yana isa yayi Parking
tare da fita ya nufi harabar makarantar iska na kaɗa shi kai tsaye Office din malam Arɗo ya Murɗa
handle din ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama.

Anutse Malam Arɗo dake duba wani littafi ya ɗago kansa tare da sauƙe Idanunsa akan Moddibo ganinsa
cikin wani irin yanayi yasa yayi saurin miƙewa tare da riƙe hannun sa kana yace.

“Moddibo ya dai?”.

Kai Moddibo ya Girgiza cikin sanyin murya yace.

“Bakomai”.

Kujera Malam Arɗo yaja masa ya zauna kana shima ya koma mazauninsa.
Cike da kulawa Malam Arɗo yace.

“To ina ƴan biyun naka?”.

ƙasa yayi da kansa tare da runtse Idanunsa kasancewar sa ba mai saurin kuka ba ya tabbata da ace yana
da saurin kuka da zaran an ambaci sunan J ɗin sa zaiyi kuka ko hakan zaisa ya samu sassaucin abinda
yake ji Aransa ya sake damƙe lip ɗin sa da ƙarfi wanda zuwa lokacin ya sake kumbura kana yayi ja sai
sheƙi yake.

Ido Malam Arɗo ya tsira masa kana yace.

“Ya dai Aliyu mai yake faruwa da Jameelu tun jiya da yamma naji ana raɗe-raɗin wai ba agansa ba nayi ta
kiran wayarka baka ɗauka sannan shi kuma idan na kirasa akashe ina Jameelu da gaske ne babu shi!??”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da ɗago kansa still yana taune da lip ɗinsa kana cikin raunin murya yace.

“Babu J”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace.

“Na sani Aliyu ka nutsu ka dawo hayyacinka Aliyu na sani babu Jameelu sannan na gaskata tunda har
naga kai kaɗai kazo nan na tabbata do min idan anganka tamkar anga wata ne dole za'aga zara”.

Ya faɗa tare da miƙewa ya dafa kafaɗar sa.

Runtse Idanu Moddibo yayi

“Yanzu ya ake ciki?”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da shafa ƙirjinsa dake bugawa da ƙarfi kana yace.

“Nima kaina ya kulle a duniya bansan me zanyi ba bansan ya zanyi na ganni da J ba?”.

Dafa kafaɗar sa Malam Arɗo yayi cike da tausayawa yace.

“Toh yanzu wani mataki aka ɗauka akan lamarin!?”.

Cikin raunin murya yace.

“Babban matakin da aka ɗauka shine addu'a da faɗawa Ubangiji abinda yake faruwa”.
Jinjina kai Malam Arɗo yayi tare da faɗin.

“An ɗauki mataki mai kyau, da girma wanda ya dace da dukkan Musulmi yanzu mu shiga cikin
makaranta mu faɗawa yara su tayamu da addu'a Ubangiji Allah ya tsare malam Jameelu ya kuma
bayyana sa aduk inda yake”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da miƙewa kana yace.

“Toh Nagode Allah ya saka da alkhairi”.

Hannunsa Malam Arɗo ya riƙe bayan ya mike suka fita kai tsaye bangaren ƴan primary suka fara shiga
Ajinsu Ramadan da Raudat yaran na ganinsa suka miƙe cike da farin ciki suna cewa Moddibo Moddibo
Kusan a tare Raudat Ramadan da wasu ɗalibai uku suka ce Moddibo ina Malam Jameel munyi kewar ku
bakwa zuwa.

Lumshe Idanunsa da yaji suna masa zafi da zaran an ambaci sunan J ɗin sa zuciyarsa zata buga da
masifar ƙarfi tsayuwar sa ya gyara agaban ajin tare da cewa.

“Ina ɗaliban Malam Jameel?”.

Baki ɗaya yaran suka ɗaga hannu suna tsalle tare da cewa gamu nan Moddibo ina yake munyi kewarsa
bakwa zuwa yanzu, dan Allah kace yazo muna san ganinsa.

Kasa furta komai Moddibo yayi hakan yasa ya jingina bayansa da jikin bango yayi ƙasa da kansa yasan
yanda J ɗin sa ke son Yara da kuma wasa da su wanda a ra'ayinsa baison koyar da yara amma saboda
yanda J ɗin sa ke son Yara Yasa yake shiga koyar musu ganin haka yasa Malam Arɗo yayi gyaran murya
Atake duk yaran suka nutsu tare da tsirawa Malam Arɗo ido.

A hankali Malam Arɗo ya sauƙe tare da faɗin.

“Kuna jina?”.

Kai suka gyaɗa masa.

Ya sauƙe numfashi tare da cewa.

“To zaku yiwa Malam Jameel din ku addu'a Allah ya bayyana shi?”.

Aruɗe yaran suka ce Malam Jameel ya ɓata ne?."

Kai Modibbo ya gyaɗa musu cike da damuwa.

Cikin zare ido Raudat tace.

“Malam Jameel din mu ya ɓata kuma to ina yaje?”.


Ramadan kuwa miƙewa yayi tare da zuwa gaban blackboard ɗin cikin yanayin damuwa sosai ya riƙe
hannun Moddibo da har zuwa lokacin Idanunsa ke lumshe yace.

“Moddibo ina Malam Jameel ɗin mu yaje dan Allah ka kira wayansa kace ya dawo Muna so sa”.

Kasa cewa komai Moddibo yayi sabida zulumi.

Gyaran murya Malam Arɗo yayi tare da cewa.

“Kuyi masa addu'a Allah ya bayyana shi idan kunyi sallah kuyi addu'a Allah ya bayyana Malam Jameel
sannan ku faɗawa iyayenku suma suyi masa addu'a Allah ya karesa ya kuma dawo dashi cikin aminci da
salama”.

Hawaye Ramadan ya fara zubdawa tare da cewa.

“Toh Malam zamuyi masa addu'a zan faɗawa Mommy da Addah Khausina suma zasuyi masa addu'a
Allah zai dawo dashi”.

Ahankali Moddibo ya shafa kansa tare da cewa.

“Yawwa Ramadan kuyi masa addu'a ayanzu babu abinda Malam Jameel yake buƙata awajen mu face
addu'a”

Cikin rauni sosai yaran suka ce zamu yi masa.

Cikin sanyin jiki Malam Arɗo da Moddibo suka fita zuwa bangaren Secondary bayan sun fita anan suka
shiga ɓangaren na naziri saida suka gama zagaye ko wani aji suna sanarwa Ayiwa Malam Jameel addu'a
Ubangiji Allah ya bayyana shi cikin tashin hankali ɗalibai suka shiga masa addu'a.

Bayan sun fito Moddibo ya nufi hanyar gate

Cikin kula malam Arɗo yace.

“Moddibo baza ka shiga office din ku ba?”.

Kai ya girgiza tare da cewa.

“Um-um bazan shiga ba zan tafi bazan iya zama babu J ba”.

Ya faɗa tare da ficewa yashiga motarsa kai tsaye gidan Abban M Jameel ya nufa bayan yayi Parking ya
fito tare da shiga falon bakinsa ɗauke da Sallama A inda ya fita yabar Abba anan ya dawo ya sameshi
zaune still wayarsa na gabansa ya zubanusu Ido da alama tun bayan fitarsa ko motsawa baiyi ba.
Ahankali Abba ya ɗago kai tare da zuba masa ido cike da tausayinsa baki ɗaya ya rame ya canza idanunsa
sun sake girma da ja kana idanunsa sun faɗa, Ahankali Moddibo ya ƙaraso ya zauna agefensa aƙasan
Capet Cike da tausayawa Abba yace.

“Aliyu ba kayi wanka ka sauya kaya ba”.

Siririn tsaki Moddibo yaja tare da yin ƙasa da kansa kana yace.

“Abba har yanzu basu sake kira ba!?”.

Kai Abba ya Girgiza tare da cewa.

“Har yanzu basu sake kira ba gani nan ina zaune tamkar gadin waya nake sai tsumayin kiransu nake
amma basu kira ba, amma yanzu ka samu kaje kayi wanka ka samu kaci abinci”.

“Abba banajin yuwa”.

“Ya zamuyi Aliyu idan kaima baka ci abinci ba ai faduwa zakayi. Insha Allah addu'ar mu bazai bar Jameelu
ya ta gayyara ba”.

Sai ya kuma maida kallonsa kan Hajiya Karima data shigo wacce ita ma baki ɗaya tayi sanyi ahankali
yace.

“Ki zubawa Aliyu sbinci”.

Kai ta gyaɗa tare da nufar dining ta ɗauki Plate ta zuba masa jollof fice da yaji bushesh-shen kifi da
namar kaza ta kawo masa.

Moddibo kuwa hannu ya daga mata alamar kada ta ajiye masa ganin ta ajiye yasa ya maida kansa jikin
kushin ɗin ya jingina tare da lumshe idanunsa yace.

“Ina ma ace tare suka ɗauke Ni da J da yafi min farin ciki ina rayu dashi aduk inda yake duk halin da yake
ciki ace muna tare wallahi da yafi min farin ciki akan rabani da Jameel da sukayi”.

Kallonsa Abba yayi cike da tausayawa wannan shine karo na farko arayuwar sa da yaji Moddibo ya kira
Complete sunan M Jameel cikin raunin murya yace.

“Toh ya zamuyi Aliyu ka daure kaci abinci”.

“Abba ba zan iya cin abinci ba”.

Cikin rarrashi Abba yace.


“Haba Aliyu ka naso kasake sa kamu cikin damuwa ne rashin cin abinka dai dai yake da yiwa kan ka illah,
wanda bazan so hakan ba dan Allah ka daure kasa wani abu acikin ka”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.

“Toh Abba abani tea”.

Miƙewa Hajiya Karima tayi ta nufi dining kana ta haɗa masa tea cup ɗaya ta kawo masa ahankali ya
karba tare da kaiwa bakinsa da ƙyar ya iya shan rabi ya ajiye Cup ɗin.

Abba bai tilasta shiba dan shima akaran kansa yasan ba zai iya saka komai acikin sa ba baya ga tea ɗin da
yake sha dan raya kai, cikin sanyin murya yace.

“Aliyu kaje ɗakin Jameelu kayi wanka ka sauya kaya”.

Girgiza kai yayi cikin rawan murya yace.

“Abba bari in je gida saboda nabar Innayi ita kaɗai tun safe sannan na barta cikin damuwa”.

Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh Aliyu ka gaisheta”.

Yana isa gida yayi Parking tare da wucewa Bedroom ɗin sa, kai tsaye toilet ya shiga tare da sakarwa
kansa ruwan sanyi sai alokacin ya lura da Dick ɗin sa daya kwanta luƙui tamkar bai taɓa tashi ba
tsanananin fargaba da tashin hankali da yake ciki yasa ya kasa tantance shin shi ɗin wani irin halitta ko
kuma wanne irin jinsi ne shin shi ɗin namiji ne ko mace baisan matsayin da yake ba bare kuma ace
sha'awa baki daya Dick ɗin sa ya kwanta tamkar babu wani abu mai suna sha'awa daya taɓa ji cikin sanyi
Jiki ya gama wankan tare da fitowa ya shirya cikin Jallabiya kana ya fesa turare kai tsaye sashen Innayi ya
nufa.

Misalin ƙarfe 5:00pm da wasu Mintuna bayan antaso Amakaranta motarsu Ramadan na shiga harabar
gidan tayi Parking Ramadan ya ɓude tare da ficewa da gudu.

Acan falo kuwa Mommy da Khausar ce zaune suna kallon TV cikin tashar Nat geo well Suna kallon
namomin daji Ramadan ya shigo tare da zama gefen Khausar kana ya langwaɓar da kansa tare da cewa.

“Addah Khausi”.

Hankalinta na kan wasu irin halittun ruwa tace.

“Na'am Ramadan”.

Cikin muryan rauni yace.


“Addah Khausi wai Malam Jameel ya ɓata”.

Cikin sauri ta kallesa tare da riƙe hannunsa kana cike da mamaki tace.

“Malam Jameel ya ɓata kuma!?”.

Kai ya gyaɗa mata kana yace.

“Eh Addah Khausi Moddibo da Malam Arɗo su suka shiga ajinmu suka faɗa mana Malam Jameel ya ɓata
ba asan inda yake ba”.

Cike da mamaki da kuma al'ajabi Khausar tace.

“Ha'a wace iriyar magana ce wannan Malam Jameel ya ɓata ba'a san inda yake ba!?”.

Mommy kuwa cike da mamaki take kallon Ramadan kana tace.

“Ramadan ka tabbatar kuwa?”.

Kafin yace wani abu Raudat ta shigo da kuka fuskarta jage-jage da hawaye kana ta zauna kusa da
Mommy tare da cewa.

“Wallahi Mommy wai ya ɓata!”.

Da sauri Mommy ta ɗauki wayarta dake hannun kujera kana tace.

“Gashi kiramin Umminsa”.

Amsar wayar Khausar tayi still da mamaki atare da ita tace.

“Eyyy aikuwa Jiya naga miss call ɗin Asma'u bana wajen daga baya kuma da nazo ina ta kiranta bata ɗaga
ba”.

Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya ta shigo sanye da hijabi har ƙasa kana ta zauna kusa da Khausar dake
laluɓo number Ummi ya zama na sun sa Ramadan Atsakiya kasancewar kujeran 2sitter ne.

Bayan Mommy ta amsa Sallamar ta tace.

“Hajiya wai kinji abinda yaran nan suke faɗa wai Malam Jameel ya ɓata!”.

Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh dama baki ji bane aini tun jiya da yamma Aminu ke faɗa min wai yaji Amasallaci ana cewa ayi addu'a
Allah ya bayyana ya kuma tsaresa ashe dama ba kiji ba?”.
Kai Mommy ta.

Girgiza fuska cike da damuwa tace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Wallahi ban jiba Subhanallah ya Salam Ubangiji Allah ya tsaresa”.

Hajiya Bunayya kuwa ahankali ta saci kallon Mommy sai taga idanunta nakan Khausar data maƙala waya
akunnenta cike da dabara ta sake murza turaren dake hannunta kana ta fito dashi ta ɗaura akan
Ramadan tana shafa masa aranta kuwa fari fess tana cewa Alhamdulillah wannan turaren dai na samu
na shafa masa saura kuma gobe in faɗawa Boka Kar'uzu na shafa masa turaren.

Khausar kuwa jin Asma'u tayi Picking call ɗin yasa cikin sauri tace.

“Asma'u”.

Cikin wata dashash-shiyar murya mai cike da rauni Asma'u tace.

“Na'am Khausar”.

Cikin alamun damuwa Khausar tace.

“Asma'u wai me nake ji?”.

Cikin muryan kuka Asma'u tace.

“Khausar an sace Yah Jameel yau kwana biyu kenan kusan na uku ba Yaya Jameel ba labarinsa”.

Atsorace Khausar ta dafe hannunta aƙirji kana tace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ansace Yah Jameel Kuma?”.

Kai Asma'u ta gyaɗa hawaye na bin kuncinta tace.

“Eh”,

Cikin sanyin murya tace.

“Ubangiji Allah ya bayyana shi aduk inda yake Allah ya fito mana dashi”.

Ameen Asma'u ta amsa tare da katse kiran.

Kallon Mommy Khausar cikin tashin hankali tace.

“Mommy wallahi da gaske an sace sa”.


Girgiza kai Mommy tayi tare da cewa.

“Ya Salam wallahi bamu sani ba barin idan Abbanku ya shigo zan tambaye sa muje muyi wa Umminsa
jaje Ubangiji Allah ya bayyana shi Allah ya tsaresa aduk inda yake”.

Khausar kuwa kasa tsaida hawayen ta tayi cikin Muryan kuka tace.

“Ameen Mommy Ameen ya hayyu ya ƙayyum Allah ya bayyana Malam Jameel har kwana biyu kuma!?”.

Ta gumi Hajiya Bunayya tayi tare da marairaice fuska kana tace.

“Hakane kam wannan duniyar ta zama abin tsoro idan kana fama da talauci ka banu idan kayi wadata
ɓarayi da ƴan Kidnapping su hanaka kwanciyar hankali da nutsuwa Allah dai ya kyauta”.

Ta faɗa tare da miƙewa ta fice ranta fess.

Baki ɗaya Wunin wannan ranan haka Mommy da Khausar suka yita cikin jimami da fargaba musamman
Khausar ta gagara tsaida hawayen ta.

Moddibo kuwa yana fita daga sashen Innayi mota ya shiga tare da nufar gidan Abba yana isa ana kiran
maghariba tare da Abba suka shiga Masallaci suka gabatar da sallah.

Acan ɓangaren Mommy kuwa bayan an idar da sallar Isha'i ta sanarwa da Lamiɗo suna san zuwa yiwa
Ummi jaje nan yace ba damuwa ta kira Khausar da Hajiya Bunayya su fito bayan sun fito da kansa yayi
Driving ɗinsu zuwa gidan Ummi.

Bayan sun isa.

Mommy ce agaba sai Khausar sai kuma Hajiya Bunayya bakinsa ɗauke da Sallama suka shiga dai-dai
lokacin kuma maƙotansu suka fito.

Zaune suka samu Ummi kan 2sitter tana riƙe da Kur'ani Idanunta sun kumbura sun ƙanƙance yayin da
Asma'u ke zaune gefenta hannunta riƙe da Carbi.

Cikin sauri Khausar ta ƙarasa kusa da Asma'u tare da riƙe hannun ta kana tace.

“Asma'u da gaske wai dagaske ansace Yah Jameel!?”.

Cikin zubda hawaye Asma'u ta gyaɗa mata kai kana tace.


“Khausar da gaske ansace Yah Jameel tun randa kikazo ya maida kin nan, har yanzu babu labarin sa
yanzu kusan dare na uku kenan za ashiga”.

Khausar ma cikin zubda hawaye ta damƙe hannun Asma'u tare da cewa.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.

Kallon Ummi Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.

“Ayyah Ummin Jameel Ashe abinda ya faru kenan toh Ubangiji Allah ya tsare Allah ya bayyana shi”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin.

“Ameen ya Allah Nagode”.

Mommy kuwa kafaɗar ta ta dafa kana tace.

“Ba komai Ummin Jameel kiyi haƙuri ki daina kukan nan ki riƙa yi masa addu'a Insha Allah Ubangijin zai
bayyana shi”.

Cikin sauri Ummi ta share hawayenta kana tace.

“Nagode Mommyn Khausar Nagode³”.

Cike da tausayawa Mommy ke sake ƙarfafa mata guiwa.

Ahankali Khausar ta juya tare da kallon Ummi cikin Muryan kuka tace.

“Ummi Allah ya bayyanar da Yah Jameel insha Allah ba zasu samu nasarar cutar da shiba zamu tayi masa
addu'a Allah ya karesa”.

Miƙewa Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Bari mutafi Alhj na jiran mu awaje yace a gaidaki".

Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.

“Nogeda Allah ya saka”.

Sannan suka fita a coumpund suka haɗu da wasu matan sun shigo yiwa Ummi jaje bayan sun koma gida.

Baki ɗaya Khausar ta kasa nutsuwa kafin ta kwanta taje tayi alwala kana ta ɗauki Kur'ani tana ta karatu
tare da tawassali dashi da niyyan Ubangiji ya bayyana M Jameel aduk inda yake.
Misalin ƙarfe goma na dare kamar lokacin da aka dauke M Jameel Moddibo dake gefen Abba ya miƙe da
niyyar tafiya Akuma dai-dai lokacin wayar Abba dake gabansa ta hau ruri.

Atare Abba da Moddibo suka kalli wayar cikin sauri Abba yayi Picking call ɗin tare da kaiwa Kunnensa.

Daga ɗaya ɓangaren akace Alhj Bashiru mahaifin Jameel ko!?”.

Cikin sauri Abba ya gyaɗa kai tare da cewa.

“Eh nine nayi ta kiran layinku baya shiga”.

Cikin fusatacciyar murya Mutumin yace.

“Dama ce maka mukayi idan ka kira zai shiga?”.

Girgiza kai Abba yayi tare da faɗin.

“A'a to menene sharaɗin ku na biyu kaga ban faɗawa kowa ba!”.

Cikin bauɗaɗɗiyar murya Mutumin yace.

“Kuɗin fansa zaka biya shine sharaɗin mu na biyu”.

Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.

“To nawa kuke buƙata?”.

Kai tsaye mutumin yace.

“Milion ɗari biyu”.

Atsorace Abba ya dafe hannunsa aƙirji kana ya zare ido cikin tsanananin firgici yace.

“Milion ɗari biyu!?”.

Atare Hajiya Bunayya da Moddibo da maganar ya dakesu suka haɗa baki atare wajen cewa.

“Milion ɗari biyu?”.

Cike da gadara Mutumin yace.

“Toh idan ba zaka bada ba sai ka shirya karɓan gawar ɗan ka!”.

Cikin sauri Abba ya Girgiza kai tare da cewa.

“Kuyi hakuri dan Allah dan darajar Annabi kada ku kashe wayar”.

Cikin Yanayin ɓacin rai Mutumin yace.


“To ai mun riga mun faɗa muku abinda ake buƙata idan ka shirya gobe zamu sake kiran ka muji ko ka
shirya”.

Yana gama fadar haka ya katse kiran...!

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYA

29

*LITTAFIN SAKAYYAH NA KUDINE KO KIN GANSHI A WASU WURAREN DA BA CIKIN GROUPS NA DANA
BUƊE NA SAKAYYAH BAto na satane, 1k ne kacal kuɗin littafin SAKAYYAH yar uwa ki biya ki karanta cikin
Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min
shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, kiyiwa Allah da Manzonsa ku dena fidda min littafina, in dai
kin san kin sayane dan ki turawa wasu, dan Allah ki gaya min in mayar miki da kuɗinki🙏🏻🙏🏻Dan Allah
nace ba dan niba*

29

Moddibo kuwa cike da mamaki da tsoro ya maimaita 200 Millions asaman laɓɓansa, he can't believe or
imagine zasu iya tambayar wannan maƙudan kuɗin how cames kidnapper zasu tambayi kuɗin fansa
kamar sun sace ɗan shugaban ƙasa.

Rintse idanunsa yayi tare da cije labɓansa na ƙasa lokaci ɗaya jijiyoyin kansa suka tashi sukayi ruɗu-ruɗu
dasu.

Dafe kuncin Hajiya Karima tayi da hannunta duka biyu kana ta kyale baki tare da cewa.

“Ohh Allah ya kawo mu wani zamani ka haifi ɗa sannan wasu ƙartin banza da wofi su saka kasa ke sayan
sa bafa Millions biyu ba, Ba ashirin ba, Ba hamshin ba, Ba ɗari ba, har Millions ɗari biyu sai kace abin
Masifa ko dan sunyi zaton Jameel ɗan Aliko ɗan Gwate ne, shi, ka haifi ɗa kasha wahalar ciyar dashi
shayar dashi tufatar dashi biya masa makaranta sannan ace ka sake siyan sa”.
Dafe kai Abba yayi da duka hannunsa biyu baki ɗaya ilahirin jikinsa rawa yake kar-kar-kar tamkar mazari
yayin da idanunsa suka kaɗa sukayi jawur tamkar garwashi.

Dai-dai lokacin Hajiya Turai tashigo baki ɗaya tayi zuru-zuru da ita. Idanunta sun kaɗa sunyi jawur dasu
ganin halin da Abba ke ciki yasa tace.

“A'a Alhj Lafiya Subhanallah”.

ta faɗa tare da nufar Bedroom ɗin sa ta da buɗe drawer ta ɗauko naganinsa ganin alamar hawan jinjinsa
ne ya tashi tare da manna waya akunnenta bayan kamar second uku tace.

“Hello Dr Muktar dan Allah kazo yanzu ina ganin kamar hawan jinin Alhj ne ya tashi”.

Cikin raunin murya Abba ya ɗago kai ya kalleta tare da cewa.

“A'a ki bari ba sai Dr yazoba, ki bani maganin kawai”.

Kai ta gyaɗa kana cikin sauri ta zuba masa ruwa a glass cup ta miƙa masa tare da bara masa maganin
karɓa yayi ya afasu abakinsa ya haɗiye.

Sannu a hankali ya fara maida numfashi sama-sama yana jin bugun zuciyarsa tare da sarawan da kansa
keyi ya fara raguwa amma still hannunsa na dafe da kansa.

Ɗago Idanunsa yayi tare da kallon Moddibo daya zuba masa Idanu kana ya kalli gefen damansa Hajiya
Turai ce durƙushe Idanunta cike da hawaye lumshe idanunsa yayi kana ya shiga tunani kwata-kwata
kuɗin dake cikin account ɗinsa tsuran kuɗi, gaba da baya Million Sha biyu ne wanda yake tunanin da sun
cika Ashirin zai bawa M Jameel saboda ya habɓaka Company daya bashi, da ƙarfi ya sake rintse idanunsa
tare da dafe kansa tuno wa da yayi acikin Million Sha biyu ma akwai cikon kudin hajji nashi da na
matansa da zai cika ta, baki ɗaya tunaninsa ya tushe ina yasan zai fara kai kadaransa asiya masa su cikin
gaggawa kuma da daraja sannan abashi kuɗin cikin tsanananin tashin hankali yace.

_“Ya Ilahi ya lillahi ya mujibud da'awati ya hayyu ya ƙayyum bi rahma tika astaghisu lahaula wala
ƙuwwata illa billahil aliyul azim”_.

Abin da yake maimaitawa kenan asaman laɓɓansa.

A hankali Moddibo ya matsa kusa dashi cike da tausayawa yace.

“Colm down Abba ka nutsu ka kwantar da hankalin ka everything will be fine by the grace of Allah”.

Cikin sauri Abba ya riƙo tsintsiyar hannun Moddibo tare da cewa.

“Aliyu Why should I find 2 hundred Millions?”.

Aliyu mai zan fitar in sayar dashi cikin gaggawa in Samu kuɗi?.
Aliyu bani da ko Million ashirin acikin account ɗina,kaji kuɗin da suka kira fa”.

Kallonsa kawai Moddibo keyi cike da tausayinsa Cikin raunin murya Abba ya cigaba da cewa.

“Aliyu kwanan nan na cire kuɗi na siya filin nan kuma shima gaba ɗaya filin dana siyeshi 25 Million ne da
ace suna nan kaga kuɗin akwai ɗan gwaɓi ahannu na”.

Sai kuma ya sauƙe numfashi tare da sake damƙe hannun Moddibo acikin nasa kana yace.

“Ina da kadaran da zan iya sayarwa amma ta yaya awani lokaci zan samu ace ansiya se anbani kuɗina
sannan na wane”.

Kasa ƙara sa maganar yayi kawai saiya janye hannunsa dake cikin na Moddibo ya rufe fuskarsa yana mai
furta.

_“Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha Hasbunallahu wani'imal wakin La'ilaha Illah anta
subhanaka Inni kuntu Minal zhalimin”_.

Hajiya Karima dake dafe da kuncinta ta ɗago kai tare da kallon Abba kana tace.

“Alhj ai dole dama za ayi ciniki dasu idan yaso sai anemi ragi”.

Moddibo kuwa kai ya girgiza tare da kallon ta kana yace.

“Idan da ace sunzo mana da sauƙi da kuma Imani acikin zancen zamu iya hakan amma fa kiga yanda idan
sunyi magana sai su yanke mana kiran baza su tsaya suji ta bakin muba sai sun kwana ɗaya ko biyu kafin
su sake kiran mu”.

Da ƙarfi ya runtse Idanunsa tare da cije labɓansa na ƙasa kana ya cigaba da cewa.

“Basa tunanin shin wani irin yanayi ko hali zamu kasance aciki ba yaya zamuyi, da wannan kuɗin da suka
kira”.

Ya ida maganar cikin raunin murya.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.

“Nima abinda nake tunani kenan idan nace musu babu zasu iya yiwa Jameel Illah”.

Girgiza kai Moddibo yayi tare da cewa.

“Abba kar ma kace musu babu sai muyi ƙoƙari duk yanda zamuyi mu haɗa kuɗin nan muyi ƙoƙari mu
basu”.

Ahankali Abba ya furta.

“Ya Salam”.
Hajiya Turai kuwa cikin matsanancin kuka ta kalli Moddibo kana ta maida kallonta kan Abba tare da
cewa.

“Ai abayar ɗin yafi Alhj duk wani abinda kake dashi ka sashi akasuwa kawai asamu asayar akarɓo Jameel
meye fi maka Jameel aduniyar nan Alhj, kawai asayar da komai akai musu kuɗin akarɓo shi”.

Cikin sauri Hajiya Karima ta kalli Hajiya Turai kana tace.

“Kamar ya asaida komai Hajiya Turai kifayi tunani akan abinda kike faɗa idan aka sayar da komai muku
mu murayu aya kenan?”.

Sai kuma ta maida kallonta kan Abba kana ta cigaba da cewa.

“Alhj ya za ayi ɗauki irin wannan maƙudan kuɗin amulmula abasu kaga idan wa'annan ƴan Kidnapping
din da suka kinnafe Jameelu sunji dadi an basu abinda suke so to wasu kuma ai sauran ƴaƴan zasu zo su
kwashe”.

Ta ida mgnar tare da sauke numfashi kana ta cigaba da cewa.

“Suma sauran ƴaƴan sai aje a kinnafesu su kuma idan kuɗin da za'a fanshe su bai rage ba ya za ayi kenan.

A gaskiya wannan ba shawara bace ace za aɗauki wannan maƙudan kuɗin abasu sai kace ba asha
wahala wajen ne mansu ba”.

Ahankali Moddibo ya ɗago kumburarrun Idanun sa ya kalli Hajiya Turai dake dafe da ƙafaɗan Abba tana
sharɓan kuka kana ya maida kallonsa kan Hajiya Karima data zabga tagumi.

Girgiza kansa yayi.

Sosai hankalin Abba yayi masifar tashi yama rasa wani irin tunani zaiyi Aransa ya gaza tantance abin
cewa.

Sannu a hankali idanunsa suka fara lumshewa jikinsa ya saki baya yaja tare da gyara kwanciyarsa akan
3sitter tare da lumshe idanunsa Atake Bacci ya ɗauke sa sabida magungunansa da Hajia Turai ta bashi
yasha sun jiƙa sunbi jininsa.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da miƙewa kana yai musu sai da safe tare da ficewa yashiga motarsa
kai tsaye gidan Ummi ya nufa.

Awaje yayi Parking motarsa kana ya fita iska na kaɗa ko wani sashe na jikinsa ahankali ya murɗa handle
din ƙofar ya tura bakinsa ɗauke da sallama ya shiga.

Idanunsa suka sauƙa akan Ummi dake zaune kan Sallaya hannunta riƙe da Carbi yayin da Malam Ahmad
ke zaune gefenta yana rarrashin ta.
Ganinsa yasa Ummi ta ajiye carbin dake hannunta kana ta maida hankalinta kansa,Anutse Moddibo ya
ƙara sa tare da miƙawa malam Ahmad hannu sukayi musabaha kana ya koma ya zana agaban Ummi.

Jin Sallamar sa yasa Asma'u da Bashir suka fito daga Bedroom tare da zama gefe da gefen Ummi ya
zamana sun sashi a tsakiya kana cikin raunin murya suka gaishesa atare zuwa lokacin shima Bashir kuka
yake sosai duk yayi zuru-zuru.

Ahankali Ummi ta zubawa Moddibo Idanu kana cikin sanyin murya tace.

“Babana ya akayi sun sake kira?”.

Kai ya gyaɗa tare da sun kuyar da kansa ƙasa kana yace.

“Eh”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.

“Me suke buƙata?”.

Still Kansa na ƙasa yace.

“Ummi kuɗi suke so”.

Numfashi ta fesar kana tace.

“Kuɗi suke so?”.

Kai ya gyaɗa amma bai ce komai ba.

Cikin tsira masa ido tace.

“Kuɗi kamar nawa suke so?”.

Cikin rauni ya kalleta kana ya kalli malam Ahmad, Asma'u da Bashir ya fesar da numfashi tare da cewa.

“Ummi kuɗin suna da yawa kuɗin da suke buƙata sun wuce zatonmu”.

Gyara zama tayi kana tace.

“Toh Meye amfanin kuɗin mahaifinsa?, Meye amfanin kuɗin Babansa?,Menene amfanin duk tattalin da
yake yi!?”.

Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.

“Ummi kuɗin sun wuce tunanin mai tunani!?”.

Ɗa gowa Ummi tayi tare da tsira masa ido kana tace.


“Kamar nawa suke buƙata Babana?”.

Cikin raunin murya da alamar sarewa Moddibo yace.

“Ummi har Million ɗari biyu suke buƙata”.

Cikin wani irin yanayi mai cike da rauni, tsoro, mmki Ummi taja ajiyar zuciya kana ta maida kanta ta
jingina da jikin kujeran da Malam Ahmad ke zaune tare da lumshe Idanunta kana Muryanta na rawa
tace.

“Ƙarya sukeyi ba kuɗin suke so ba so suke su kashe min Jameelu lallai Mahaifinsa mai arziƙi ne amma be
kai matakin da za'a matsesa lokaci ɗaya ace ya fito da Million ɗari biyuba, kawai dai yaudarace suke
mana anya ma Jameelu yana raye kuwa?”.

Cikin sauri Moddibo ya girgiza mata kai kana yace.

“Yana raye Ummi ina ji ajikina J yana raye kuma na faɗa miki munyi magana dashi”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“Yau da suka kira kunyi magana dashi?”.

Shiru yayi yana kallonta amma baice komai ba.

Kallonsa Ummi tayi cikin muryan kuka tace.

“Babana ka faɗa min gaskiya tsakanin ka da Allah yau kunyi magana dashi?”.

Girgiza mata kai Moddibo yayi tare da faɗin.

“Ummi ba muyi magana dashi ba, amma naji muryan J ƙasa-ƙasa yana cewa Abba abasu duk abinda suke
so”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da rintse idanunsa kana tace.

“Babana ka tabbatar gaskiya kake faɗa min?”

Jinjina kai Moddibo yayi kana cikin sanyin murya yace.

“Wallahi Wa rabbul Khaba Ummi naji muryan J ƙasa. yana magana bawai sun bashi bane amma naji yana
magana”.

Kuka Asma'u da Bashir suka fashe da shi atare kana lokaci ɗaya suka haɗa baki wajen cewa.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ya Allah ka kuɓutar da Yah Jameel Ubangiji kada ka basu ikon cutar dashi
ya Allah kaine gatanmu Yah Jameel shine ka wakilta da isar mana gatanmu ya Allah ka karesa da
karewaka”.

Numfashi Malam Ahmad ya fesar kana cike da tausayawa yace.

“Asma'u ba kuka ya kamata kuyi ba addu'ar mu Jameelu ke buƙata idan kuna kuka ya kuke so Ummin ku
tayi?”.

Cikin sheshsheƙan Kuka Asma'u tace.

“Abba Yah Jameel fa Yah Jameel yana cikin mawuyacin hali Abba kaji fa maƙudan kuɗin da suke buƙata
Abba ya za'ayi mu samu irin wannan kuɗin mu karɓo Yah Jameel Abba Ina tsoron kada su cutar mana
dashi”.

Girgiza kai Malam Ahmad yayi cikin sanyin murya yace.

“Insha Allah da izinin Ubangiji babu abinda zai samu Jameelu, ko wani bawa da kalar tashi ƙaddaran tun
kafin a haifi Jameelu Ubangiji ya zana masa ƙaddaransa muyi masa addu'ar Allah ya sauƙaƙa mana zafin
ƙaddararsa”.

Jinjina kai Moddibo yayi yana jin wani irin azabebben zafi aƙirjinsa.

Kallon Moddibo Malam Ahmad yayi kana yace.

“Moddibo mai Yakamata ayi acikin wannan al'amarin!?”.

Moddibo da kansa ke ƙasa ya ɗago ya kallon Malam Ahmad a hankali yace.

“Malam abinda yakamata kawai afara cuku-cukun neman kuɗin nan sai muga abinda zai kasance”.

Girgiza kai Ummi tayi still tana jingine da jikin kujera tace.

“Babana ina zamu samu kuɗin nan Million ɗari biyu fa da ace Million biyu suka ce koni kaina ma zan
bada su”.

Ta faɗa tare da ɗaukar wayarta tayi checking balance kana tace.

“Gashi yanzu anan ina da Million ɗaya da dubu ɗari huɗu da hamsin da ɗaya sannan kuma ba matsala
gobe in Allah ya kaimu zan tafi cikin.

Taraba zan kai gwala-gwalaina”.


Sai kuma ta ɗan tsaya, jin numfashin ta na yankewa, da ƙarfi ta fizgo numfashin tare da cije labɓanta na
ƙasa hawaye cike da Idanunta murya na cike da rauni ta cigaba da cewa.

“Zan saida su inga nawa zan samu ajikinsu zan haɗa harda na Asma'u sannan, motata itama zan saidawa
muga nawa zan samu awurina”.

Jingina kai Malam Ahmad yayi kana cikin sanyin Murya yace.

“Har gidan nan ma asashi a. Kasuwa asayar dashi”.

Kallonsa Moddibo yayi tare da girgiza kai kana yace.

“A Malam ayi haka”.

Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana yace.

“Asiyar Moddibo menene Jameelu baiyi mana ba aduniyar na, kasancewar sa atare damu shiyafi mana
komai”.

Ahankali Ummi ta ɗago kanta tare da tsira masa ido hawaye na bin kuncinta ta sani fili dai filinsa ne
halalinsa mallakinsa, amma baki ɗaya ginin dake ciki Jameel ne ya musu bayan yasa an buge tsohon ginin
taɓon.

Girgiza kai tayi cikin rauni tace.

“A'a ba sai anyi haka ba bari muga abinda Mahaifinsa zai samu”.

Girgiza kai Malam Ahmad yayi tare da kallon Asma'u da Bashir da har zuwa lokacin suke kuka a hankali
ya fesar da numfashi tare da cewa.

“Ni dai na sadaukar da wannan gida ga.

Jameelu wallahi na yafe masa shi duniya da lahira na amince asa shi akasuwa muddin za a samu masu
siya, to asa shi akasuwa mu samu muga aƙalla dai awajen mu ace an samu Million goma kuɗin zaifi
gwaɓi”.

Sun kuyar da kai ƙasa Ummi tayi hawaye masu masifar zafi suka zubo mata.

Hannunta Moddibo ya riƙe cikin sanyin murya yace.

“Ummi dan Allah ki daina wannan kukan idan kina kuka muku ma ya zamuyi Ummi babu abinda J ke
buƙata awajen mu face addu'a ganin ki awannan yanayin naya sake raunatamana zuciya”.

Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana yace.


“Sosai ma wannan kukan da kike Fatima saidai ya haddasa miki wani ciwon amma babu amfanin da zaiyi
dan Allah ki daina ki cigaba da yi masa addu'a. shi kansa ba zaiso ace kina masa kuka ba”.

Kai ta gyaɗa tare da share hawayen ta kamar yarinya kana tace.

“Na daina Insha Allah zan cigaba da yimasa addu'a Ako da yaushe”.

Saida Moddibo ya tabbata ta daina kukan kafin ya mata sallama ya fice cike da tausayinsu Driving yake
ahankali har ya isa gida yayi Parking kana ya fito ya rufe gate din tare da wucewa sashen Innayi bakinsa
ɗauke da sallama.

Kwance ya samu Innayi cikin Yanayin damuwa gefenta da Radio tana sauraro wanda ɓatan M Jameel ake
sanarwa.

Miƙewa tayi ta zauna tare da amsa Sallamar sa kana tace.

“Moddibo ya labarin Jameelu?”.

Cikin sanyin murya yace.

“Innayi sun sake kira ɗazu”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.

“Toh kunyi magana dashi yana cikin ƙoshin lafiya?”.

Girgiza mata kai yayi kana yace.

“A'a Innayi bamuyi waya dashi ba amma bisa duk kan Alamu J baya jin daɗin zaman wajen can”.

Ahankali Innayi ta jingina bayanta da jikin bango kana ta matsar da Radio gefe tare da cewa.

“Dama Moddibo ya za ayi yaji daɗin zaman wannan wajen. kasan yanayin da yake ciki ai dole bazai ji
daɗin zaman wannan wajen ba amma me suke buƙata?”.

“Innayi kuɗi suka nema”.

“Kuɗi suka nema to aisai abasu aje a karɓe shi”.

“Innayi kuɗin da suka nema na fitar hayyacine!”.


“Kuɗi har nawa suka nema? Da zai zama na fitar hankali”.

Dafe goshinsa yayi kana yace.

“Innayi Million ɗari biyu suka nema kuma cikin ƙanƙanin lokacin fa”.

Ita kam Innayi baki ɗaya lissafin ta sincewa yayi jin maƙudan kuɗin tama rasa nawane, kallon Moddibo
tayi tare da cewa.

“Dubu ɗari biyu?”.

Kai Moddibo ya Girgiza tare da cewa.

“A'a ba dubu ɗari biyu bafa Million fa Million ɗari biyu”.

Daga kanta sama tayi alamar tunani sai kuma ta kallesa tare da cewa.

“Million biyu?”.

Still girgiza mata kai Moddibo yayi kana yace.

“A'a Million ɗin goma, ashirin, hamsin, ɗari, ɗari da hamshin har ɗari biyu”.

Dafe kirji tayi kana tace.

“Million ɗari biyu?”.

Jinjina mata kai Moddibo yayi.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“Ban gane lissafin ba Aliyu”.

Lips ɗinsa duka biyu ya cije a lokaci guda kana yace.

“Ba zaki gane lissafin ba Innayi kuɗi ne masu tarin yawa suke nema”.

Cikin sanyin murya Innayi ta jujjuya kanta kana tace.

_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin Layukalliful nafsi illa wusɗaha_

Toh yanzu mai Baban nasa yace?”.

“Innayi Abbansa bashi da wannan kuɗin a ƙasa kwanan nan dama ya gama yi mana ƙorafi bashi da kuɗi”.
Lumshe idanu Innayi tayi kana tace.

“Ya Salam ya Ubangiji Allah ka dube mu da idon rahama, ya Allah ka yayemana ya Allah ka sauƙaƙa mana
ya Allah ka tsare Jameel ka kare mana shi, Allah ka tseratar da wannan bawan naka”.

Cikin sanyin murya Moddibo yace.

“Ameen”.

Kallon second biyar zuwa bakwai Innayi ta yiwa Moddibo kana tace.

“To amma kai Moddibo mai kake ganin zakayi akai?”.

Still hannunsa na dafe akansa yace.

“Innayi akwai kuɗi awajena zan tattara su in haɗa su muga nawa za'a samu awajena”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Yafi kam”.

Bayan sun sake tattauna ne Moddibo ya miƙe tare da yi mata Sallama kana ya nufi Sashen sa ahankali ya
tura Murfin Kofar shiga tare da mayarwa ya rufe.

Kana ya jingina bayansa da jikin da kofar tare da rintse idanunsa sautin murya M Jameel ya farayi masa
kai-komo AJ bansan idan nakeba,

Lumshe danunsa yayu zuciyarsa na bugawa da masifar ƙarfi yana bada sautin dif-dif-dif cikin sauri ya
buɗe Idanunsa jin muryan M Jameel na yawo a kansa yana cewa A.J A.J Kallon kan 3sitrer kurui ji yake
kamar zaiga J dinsa a wurin, cikin raunin murya yace.

“J Why are you?, Zuciyata zata fashe ya Allah kaji ƙaina ya rabbil Izzati ka dawo da J garemu cikin aminci
da salama ya Allah kada ka bawa waɗɗanan azzaluman daman cutar dashi”.

Ya kai 15 minutes yana mai jero Addu'o'in cike da rauni, kafin ya miƙe kamar wanda aka mitsina ya nufi
Bedroom ɗin sa kai tsaye toilet ya shiga ya watsa ruwa kana ya ɗaura alwala ya fito ya kwanta bisa
gadonsa yayi rigingine duk da yasan cewa da wuya bacci ya ɗauke sa amman ya lumshe idonsa domin
yau kwana uku rabon da ya samu wani wadataccen bacci sai wani irin azabebben ciwon kai da yakeji
tamkar kansa zai rabe da ga wani irin sarawa da yakeyi yana bada wani irin sauti mara daɗi gau-gau-
gau!.

A hankali ya bude idon sai kuma yayi saurin

Lumshe Idanun sabida sarawa da kan yayi masa.


Cikin zazzaƙan muryansa mai cike da rauni ya fara raira ƙira'ar Suratul Yusuf hawaye masu ɗumi suka riƙa
fita daga idanunsa suna shiga kunnensa cikin wannan yanayin da cikar Sa'adatu da karatun Alqur'ani
mai girma ya samar masa, wani irin kiɗimemmen baccin da bai shirya masa ba ya sace sa.

Acan cikin baccin sa kuwa zaune ya hangosa akan wata.

Tattausan shimfiɗa cikin wani masha'hurin falo mai masifar kyau da ƙawa.

Sai dai kima yana ta dariya hartada karketawa, yayinda idanunsa kuma sunyi jawur jikinsa na rawa jin.

A hankali ya fara jujjuya kansa yana mai ci gaba da dariyar ya juyo kansa gabansa, jin alamar tafiya tare
da wani ƙamshi daya ratsa hancinsa yasa ya ɗaga manyan idanunsa da sukayi luhu-luhu ya sauƙe
ganinsa akan Khausar dake zuwa garesa cikin wata iriyar ƙasaitacciyar shiga, ido ya zira mata ko ƙebtawa
bayayi har ta isa garesa, a hankali ta zauna gefensa.

Tare da tsira masa manyan Idanunta masu haske wanda ke ciki da ruwan hawaye kana ta miƙa masa
wani hankief fari ƙall mai masifar ƙamshin turare.

Ƙin karba yayi saima lumshe idanunsa da yayi wanda sai lokacin ya samu wasu irin tafasassun hawaye
suka samu damar kwaranyowa, hakan yasake kawar da kansa gefe tare da sakin sheshsheƙa.

Ahankali Khausar ta matsa gabansa har suna shaƙan nunfashin juna kana ta sanya hankief ɗin ta shiga
share masa hawayen cikin wata Sanyayyar murya mai cike da nutsuwa da kuma rauni tace.

“Yah Jameel Addu'ar mu yake buƙata ba kuka ba idan kai kana kuka.

Toh Ni kuma ya zanyi addu'a za muyi masa kaji ko Abu J”.

Ta ida mgnar da kiransa da sunan da ta raɗa masa, tare da faɗawa jikinsa ta fashe da sassayan kuka dai-
dai lokacin kuma ya farka.

Kansa ya dafe tare da miƙewa ya shiga toilet ya ɗaura al,wala kana ya dawo ya shimfiɗa Sallaya ya fara
nafillah yana cigaba da yiwa M Jameel addu'a.

Ba tare da yabi ta kan mafarkinba, domin yanzu kam idan da sabo ai yaci ace ya saba da yawan ziyarar
kutse da nacin da Khaisar keyi masa cikin rayuwar baccinsa.

Washe gari Ummi ta tattara baki ɗaya Sarkoƙi, ta da ɗan kunnen zobe da awarwon Gwal nata dana
Asma'u ta shirya ta tafi Tarata.

Tana isa kai tsaye babbar kasuwar su ta wuce kana tashiga shagon saida gwala-gwalai ta bayar aka
gwada cikin sa'a ta samu sunyi farashi sosai kasancewar Manyan Sarƙoƙine nata dana Asma'u wasu nata
tun tana gidan Abban Jameel ne, suka haɗa mata kuɗin ta Naira Million biyu da dubu ɗari huɗu da
hamsin sukayi mata transfer dinsu.

Daga nan gidan kai tsaye gidan Ƙawarta Hajiya Salma Wanda mijinta ke saida Motoci yawanci awajensa
M Jameel ke siyan mota ko kuma can zawa.

Mai A dai-dai-tan na sauƙeta ta miƙa masa kudinsa kana ta shiga cikin tangamenen coumpund ɗin daya
tsaru kai tsaye ciki ta nufa tare da Knowking ɗin ƙofar kana ta murɗa handle ɗin tashiga bakinta ɗauke
da sallama.

Hajiya Salma dake zaune akan kujera ta miƙe cikin sauri kana tace.

“Hajiya Fatima sannu da zuwa ga wajen zama”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.

“Yawwa Nagode”.

Sannan ta zauna tare da sakin Ajiyar zuciya.

Bayan sun gaisane.

Cikin sanyin murya Hajiya Salma tace.

“Ayyah Hajiya ashe ga abinda ya faru da ɗana Jameel kuwa?”.

Cikin yanayin sanyin ɗaya zamewa Ummu jiki, ta gyaɗa mata kai tare da cewa.

“Ummm bari ke dai Hajia Salma duniya tayi min zafi”.

Cikin tausayawa Hajia Salma tace.

“Ba komai in sha Allah, kada ki damu Hajia Fatima.

Ubangiji Allah ya bayyanar da Jameel aduk inda yake Ubangiji ya karesa daga sharrin mai sharri”.

Cikin sanyin Murya Ummi tace.

“Ameen ya Allah ameen ya hayyu ya ƙayyum”.

Cike da tausayawa Hajiya Salma tace.

“Wallahi Koda wasa banji ba sai ɗazu da safe Alhj na duba jarida ya gani shine yake sanar min”.

Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.


“Allah sarki ai yanzu anshiga kwana na huɗu kenan.

Uhmmm dama nazo kiyiwa Alhj Abdallah magana ne akan ya duba motata ya siya”.

Ajiyar zuciya Hajiya Salma ta sauƙe kana tace.

“Ubangiji Allah ya tsare Malam Jameel aduk inda yake”.

ta faɗa tare da shigewa ciki tsaye ta samu mijin nata yana ƙoƙarin fita Kallonsa tayi kana tace.

“Alhj Hajiya Fatima ce ta zo mahaifiyar Malam Jameel”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Ikon Allah muna shirin zuwa kuma sai gata”.

Ya faɗa tare fitowa a tare, a inda Hajiya Salma ta barta anan suka sameta tayi ta gumi.

Ahankali Ummi ta ɗago jai tare da cewa.

“Alhj Abdallah ina kwana ya gida”.

Zama yayi kana yace.

“Lafiya lau Hajiya ashe kuma ga abinda ya faru da Malam Jameel”.

Kai Ummi ta gyaɗa kana cikin sanyin murya tace.

“Eh”.

Ajiyar zuciya Alh Abdallah ya sauƙe kana yace.

“Wallahi bamu da labari sai ɗazu ina karanta Jarida na gani nake faɗawa Salma tace itama bata da labari
dake akwai wani fitar gaggawa daya kamani nace idan nadawo zan kaita da yamma ta gaishe ki”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da gyada kai kana tace.

“Allah sarki dama Motata ce nazo ka tura adauƙa maka ka ga lafiyarta zan saidata in zaka siya”.

Ɗagowa yayi tare da kallonta kana yace.

“Motar da Malam Jameel ya siya miki nan?”.

Kai ta gyaɗa masa tare da cewa.

“Eh shi”.

Zaman hular kansa ya dan gyara kana yace.

“Amma ai motar bata daɗe ba Hajiya Fatima”.


Kai ta gyaɗa Muryanta na rawa tace.

“Eh bata daɗe ba Uzurin gaggawa ne ya kama Ni shiyasa zan siyar”.

Jinjina kai yayi tare da cewa.

“Aikam dama mota ce mai kyau sannan bai daɗe da sayanta ba za tura yaro yaje ya ɗaukota kuma yanzu
mugama magana tunda abu na gaggawa ne”.

Cikin sanyin murya tace.

“Tun baka gani ba”.

Girgiza kai yayi tare da faɗin.

“Baki da matsala Indai wannan ne zan baki Million shida”.

Cikin sauri Ummi tace.

“Alhj har Million Shida kuma dama motar yana da tsada kenan?”.

Kai ya gyaɗa mata tare da zaro wayarsa acikin aljihu kana yace.

“Eh dama Million biyar ne haka ya siyeta toh nasiyeta biyar ɗin kamar yanda ya siya sannan Million
ɗayan kuma na bada nawa gudunmawar Ubangiji Allah ya bayyana Malam Jameel”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa.

“Ameen ya rabbil izzati, ngd Matuƙa".

Da sauri ta kalleshi jin yana cewa.

“Ki bani account number ki zan miki transfer”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da kiramasa number's ɗin.

Atake ya mata transfer.

Miƙewa tayi tare da yi masa godiya sosai kana ta fito, har ƙofa Hajiya Salma ta rakata kana ta Wuce.

Kai tsaye tashar motar Gembila ta nufa, tana zuwa kuwa tayi sa'a mutun ɗaya ya rage, haka yasa ta shiga
motar ta tashi.

Alhamdulillah sun isa Gembila lfy.


A hankali Ummi ke tafiya tana jin wani irin sanyi a ranta tare da Comfedance ga Million ɗaya da dubu
ɗari huɗu da dake account ɗinta ga kuma Million biyu da dubu ɗari huɗu da hamsin na Sarkoƙi kana ga
Million Shida na mota ya zama tana da tsuran kuɗi ahannunta har Naira Million tara da dubu ɗari takwas
kenan.

A hankali ta sauƙe wani zazzafafar ajiyar zuciya kana ta nufi gida.

Acan ɓangaren Moddibo kuwa ya haɗa duk wasu kuɗaɗe dake hannunsa ya samu Million huɗu da dubu
ɗari biyu da hamshin kai tsaye gidan Ummi ya nufa yana Parking ɗin motarsa mai A dai-dai-tan sahu na
ajiyeta atare suka shiga falonta.

Suna shiga Bayan sun gaisa Ummi tashiga Alart massage tare da miƙawa Moddibo wayarta tare da cewa.

“Babana ka kalli kuɗi sunyi gwaɓi”.

Amsar wayar yayi tare da Kallon Alart massage ɗin kuɗin kana ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.

“Masha Allah kuɗi sunyi gwaɓi bari na haɗa dana wajena”.

Kallonsa Ummi tayi haka nan taji hawaye na ciko mata kwarmin Idanunta.

Cikin sanyin murya Moddibo yace.

“Ummi na wurina na bashi da yawa Million huɗu da dubu ɗari biyu da hamsin ne”.

Cike da tausayinsa tace.

“Toh Allah ya biya. Babana Allah yabamu yanda zamuyi Ubangiji ya saka maka amma ka rage wani abu
aciki ka samu na kashewa”.

Girgiza kai yayi cikin raunin murya yace.

“Ummi wani abu zan rage idan ina da abinda yafi wannan zan ɗauka in bayar akarɓo J naje. nayi magana
da dillalai gidan mu na sashi akasuwa in dai za'a samu siyansa akan lokaci.

Cikin sauri Ummi ta kallesa tare da cewa.

“Gidan ku kuma Babana!?”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.

“Ummi Meye amfanin gidan mai zamuyi da gidan babu wani farin ciki acikisa.

Muddin J baya nan fa wanne farin ciki zamuyi. kuma komai da muka rasa zamu iya samu idan J ya dawo
gare mu”.
Jinjina kai Ummi tayi, Account number dake wayarsa ya fito dashi ya mata transfer kuɗin tare da miƙa
mata wayar karɓa tayi ta duba Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da kallon kuɗin Naira Million goma sha huɗu
kenan cib.

Numfashi ta fesar tare da kallon Moddibo kana tace.

“Alhamdulillah Babana kuɗi sun cika Million goma sha huɗu bari muje gidan Abban sa tare”.

A hankali yace.

“Amma Ummi ki bari sai gobe muje wataƙil yau ba zasu kira ba sai goben, amma ni yanzu idan nafi ta
zanje wajen Abba muji nawa aka samu awajensa”.

Kai ta gyaɗa cikin sanyi tace.

“Toh shikenan Babana Allah yasa muji al'khairi”.

Kai ya gyaɗa tare da miƙewa kana yace.

“Amin.

Toh shikenan bari naje yanzu”.

Ya faɗa tare da ficewa.

Kai tsaye gidan Abba ya nufa bayan yayi Parking ya fito tare da shiga Falon bakinsa ɗauke da Sallama.

Abba dake zaune kan 2 sitter ya jingina bayansa da jikin kujera ya amsa masa Sallamar cike da tausayinsa
ya zuba masa yana ganin yadda yake tafiya duk ya faɗa acikin kwanaki huɗu ya rame yayi shafal.

Ƙara sawa Moddibo yayi tare da zama gefensa kana yace.

“Abba ina yini ya kuma haƙurin rayuwa?”.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da cewa.

“Alhamdulillah Aliyu ya wajen su Innayi?”.

Kansa a ƙasa yace.

“Lafiya lau Abba basu sake kira ba ko?”.

Girgiza kai Abba yayi tare da fesar da numfashi kana ya runtse Idanunsa cikin sanyin murya yace.
“Basu sake kira ba Aliyu”.

Jinjina kai Moddibo yayi tare da cewa.

“Toh yanzu Abba kuɗi kimanin nawa aka samu awajenka?”.

Abba kuwa ahankali ya zame daga kan kushin ɗin ya zauna akan capet tare da fuskantar Moddibo kana
yace.

“Aliyu na tattara duk abinda yake wajena kana duk wanda nake binsu bashi na tattarasu sannan na nemi
temakon bashi duk wanda zan nemi temakonsu sunban bashi baki ɗaya kuɗin dana samu awajena
Million hamsin da shida ne, iya adadin kudin dake hannu na kenan, duk ta inda zan buga na buga
Aminaina ƴan uwana duk na nemi temako awajen su wasu sun bani kyauta wasu kuma aro na buga
shine Million hamsin da shida”.

Jinjina kai Moddibo yayi tare da cewa.

“Toh Abba kuɗi dai sun ɗanyi gwaɓi gashi awurin Ummi an samu Million Sha uku yanzu kenan muna da
Million Saba'in dai-dai a ƙasa.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana yace.

“Alhamdulilah kuɗi sun fara taruwa Amma ɗari biyu fa suka ce gashi ko ɗari cikekke bamu samu ba”.

Cikin raunin murya Moddibo yace.

“Abba bari mugani idan sun sake kira sai mu rokesu su rage mana idan sun tallafa sun tausaya mana ko
bashin banki ne zamu ci sai mu ƙara akai kuɗin ya cikata”.

Kallon sa Abba yayi tare da jinjina kai kana yace.

“Toh shikenan ba laifi Allah yasa mu dace”.

Ameen Moddibo ya amsa kana suka cigaba da hira har Misalin ƙarfe goma.

Abba najin ringing din wayarsa Yayi saurin zabura tare da picking kana yayi Sallama.

Daga ɗaya ɓangaren cikin bauɗaɗɗiyar murya mutumin yace.

“Alhj Bashiru ka haɗa kuɗin?”.

Cikin raunin Murya Abba ya gyaɗa kansa kana yace.

“Kuyi haƙuri bawan Allah dan Allah kuyi haƙuri wallahi kuɗin nan da kuka faɗa babu su awajena kwata
kwata babu”.
Daga ɗaya ɓangaren mutumin ya juya tare da kallon M Jameel dake zaune a ƙasa kana cikin wata
dakakkiyar murya mutumin yace.

“Da alama dai mahaifinka baya sonka”.

Jin muryan mutumin agefe yasa Abba saurin cewa.

“Don Allah ku bani inji muryarsa”.

Cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya Mutumin ya wurga wa M Jameel wayar kana yace.

“Gashi kaji muryan sa”.

Cikin sauri M Jameel ya cafke wayar tare da kaiwa Kunnensa kana cikin sanyin mai cike da rauni mai tada
hankalin ɗan Adam cikin murya mai cike da galabaita yace.

“Abbana”.

Cikin sauri Moddibo ya karɓi wayar a hannun Abba kana yasa a handsfree tare da danna record.

Cikin raunin Murya M Jameel yace.

“Abba kabasu kuɗin Abba dan Allah ka basu abinda suke so ka fitar dani awannan wajen mana Abbana”.

Runtse Idanu Abba yayi kana yace.

“Babana zan fitar da kai ina nan ina har haɗawa kuɗin insha Allah zan fitar da kai amma Jameelu duka-
duka kuɗin da muka haɗa anan Million Saba'in ne su kuma sunce Million ɗari biyu suke so”.

Cikin wata raunan'niyar murya mai cike da masifaffiyar galabaita da neman jin ƙai M Jameel yace.

“Abba a saida motocina duka sannan aduba ɗakina akwai kuɗi amma bai cika Million biyu bama dan
Allah ahaɗa Abba abasu azo a karɓe ni”.

Cikin rauni ya runtse Idanunsa da hawaye suka cika kana yace.

“Abba bana son zaman nan babu daɗi ba Ummina ba A.J sannan kaima ba kai wuri ba daɗi dan Allah
Abba ka basu duk abinda suke so kazo ka karɓe ni ku saida komai nawa a haɗo kuɗin”.

Kai Abba ya gyaɗa tare da ƙoƙarin hana hawayen sa zubowa kana yace.

“Babana Insha Allah zan zo in karɓe ka koda raina suke so zan basu amadadin ranka”.

Modibbo kuwa tuni wasu irin hawaye masu masifar zafi ke kwaranyo mishi tamkar mace.
Fisge wayar sukayi daga hannun M Jameel kana cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya Mutumin yace.

“Toh kaji dai abinda ɗan ka ya faɗa zamu baka dama ta karshe”.

Cikin sauri Moddibo da idanunsa ke rintse ya buɗe tare da cewa.

“Dan Allah! Dan Allah!! Dan girman Allah!!! dan darajar Annabi Muhammad (S.A.W) badan muba kamar
yanda kuka ce J nada mutunci da kamala toh dan Allah saboda wannan kamalar tasa ku rage mana kuɗin
zamu yi muku duk kan biyayya amma ku faɗa mana abinda zamu iya kawo wa”.

Daga ɗaya ɓangaren shiru mutumin yayi ba tare da yace komai ba kana bai katse kiran ba.

Cikin raunin murya Moddibo yace.

“Dan Allah kuyi haƙuri ku rage mana Insha Allah ba zamuyi gardama ba, amma kuɗin hannun mu munyi
munyi sun kasa kai adadin da kuke buƙata mu samu su kai adadin da kuke buƙata wannan shine
matsalar mu ku temaka ku ragar mana”.

Ajiyar zuciya mutumin ya sauƙe tare da cewa.

“Wannan Moddibo ne ke magana ko?”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana cikin sanyin murya yace.

“Eh”

Cike da gadara Mutumin yace.

“Toh shikenan ku bada Million ɗari da hamsin”.

Cikin raunin murya Moddibo yace.

“Mungode amma dan Allah ba zaku ƙara rage mana ba?”.

Cikin wata razananniyar tsawa Mutumin yace.

“Dan ubanka dan ka samu na zabge Million hamshin.

Atake to wallahi acikin Million ɗari da hamsin Naira biyar ba zamu rage ba kuma wallahi idan ku ka
yarda kuka sake yi mana batun ragi kuɗi to wallahi akan ran Jameel domin kuɗi ne dai mu ki ya rayu ko
ya mutu zamu samesu”.

Cikin tsanananin tsoro da kaɗuwa Moddibo ya dafe ƙirjinsa yayin da kansa ya sara da masifan ƙarfi.

Cikin tsawa Mutumin ya cigaba da cewa.

“Yanzu Moddibo gashi kayi magana dashi na ƙarshe wanda ko bacci yake yana kiran sunan ka gashi kayi
magana dashi dan wataƙil shine maganarka na ƙarshe kenan dashi matukar dai baku haɗa kuɗin nan ba
ku kasake yi mana batun ragin kuɗin to kayi magana dashi na ƙarshe kenan”.
ya faɗa tare da wurgawa M Jameel wayar.

Cikin sauri M Jameel ya cafke wayar tare da maƙalawa akunnensa kana cikin raunin murya yace.

“A.J”.

Cikin sauri da zaƙuwa Moddibo yace.

“J ina kake?”.

Girgiza kai M Jameel Yayi tare da cewa.

“A.J ban san inda nake ba ina Ummina!?”.

Runtse Idanu Moddibo yayi tare da taune lips ɗinsa kana yace.

“Tana lafiya J?”.

Cikin sanyin Murya M Jameel yace.

“J ka tabbata?”.

Cikin raunatacciyar murya yace.

“Na'am”.

jin haka yasa yaci gaba da cewa.

“Kace mata kada tayi kuka tayi ta min. Addu'a A.J ina sonka Ina son Ummina Ina son Abbana Ina Son
Asma'u Ina son Bashir”.

Da sauri Moddibo ya dafe ƙirjinsa dake harbawa da masifan ƙarfi cikin raunin murya M Jameel ya cigaba
da cewa.

“A.J Ina son Khausar tashigo rayuwar mu”.

Cikin tsanananin rauni Moddibo yace.

“Na sani J nasan kana son mu muma muna sonka, kuma in sha Allah duk zamu kasance a tare, zata shiga
rayuwarka J zan mutunta abinda kakeso J”.

Girgiza kai M Jameel Yayi still cikin raunin murya yace.

“Ngd A.J in kayi haka kayi min komai, kayiwa Ummina magana idan akwai wani abu a hannunta ta bayar
ahaɗa azo a karɓeni awajen nan dan Allah katemaka min”.
Araunane Moddibo yace.

“Insha Allah J zan taimaka da duk kan iyawa ta da kuma duk kan damata J koda ace da raina ne zan
fanshi ranka da rayuwarka Insha Allah zamu fito da kai”.

Jinjina kai M Jameel yayi tare da faɗin.

“Nagode Nagode A.J ina maka fatan al'khairi acikin rayuwarka ga Amanar Ummina, Asma'u, Bashir,Abba
da.... ka kula dasu kafin in dawo sannan kada ka mance batun Kh”...

Fisge wayar akayi daga kunnensa tare da katsewa.

Dafe kai Moddibo yayi cikin wani irin azabebben rauni ya fashe da matsanancin kuka tare da miƙewa
batare da yace komai da Abba ba ya fice yana fita ya shiga motarsa tare dayi mata key.

Kana ya ciro wayarsa tare da dearling number Ummi tana ɗagawa murya a raunace yace.

“Ummi”.

Cikin sanyin murya tace.

“Na'am”.

Cikin ƙoƙarin hana kansa kuka yace.

“Ummi munyi waya da J yanzu”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe kana tace.

“Dagaske Babana?”.

Kai ya gyaɗa kamar tana gabansa.

Cike da tsoro Ummi tace.

“Babana to Meyesa kake kuka?”.

Fashewa yayi da kuka kana cikin sheshsheƙa yace.

“Ummi ina kukan rashin J akusa dani ne Ummi wanda suka sai motarki Alhj Abdallah kice ya tura Azo
aɗauki motocina da na J duka azo asiya ahaɗa kudin duka”.

Numfashi Ummi ta fesar tare da rintse idanunta kana tace.

“Sunƙi ragewa ko?”.


Girgiza kai yayi tare da cewa.

“A'a Ummi sun rage mana Million hamsin akai yanzu ya zama Million ɗari da hamsin suke buƙata”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa.

“Toh Alhamdulillah wataƙila zamu iya cin nasara".

Cike da rauni Moddibo yace.

“Insha Allah Ummi da izinin Ubangiji”.

Ya faɗa tare da katse kiran jin wani kuka na neman kufce masa.

Kai tsaye hanyar gida ya nufa ba abinda ke yawo acikin kunnensa face sautin Muryar J ɗinsa yana isa gida
yayi Parking tare da rufe musu gate.

Kai tsaye sashen Innayi ya nufa yana isa ya zauna abakin baranda tare da riƙe kansa da hannu duka biyu,

Kana ya fashe da wani irin kuka mai masifar ciwo a zuciya.

Wani irin azaban zogi yaji zuciyarsa na masa hadi da zafi da raɗaɗi yayin da wani masifaffen rauni ya
lulluɓesa.

Innayi da bacci ya fara fisgarta ne, ta miƙe da sauri jin kamar sheshsheƙan Kukan Moddibo kana ta fito
tare da Kallonsa yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ya ɗauki rawa cikin sanyin murya tace.

“Ya dai Moddibo lafiya kuwa mai ya faru da Jameelu?”.

Cikin matsanancin kuka yace.

“Innayi ya zamuyi taya zanyi in.

Samu in taimaki J duk kan tattalina ya ƙare babu abinda zan samu in saida cikin gaggawa.

Zan saida tsohuwar motar da kika siya min da wannan sabuwar da kuma na J duka za'a siyar sannan
Innayi nasan koda an siyar dasu duka, kuɗin ba zasu ciki Million ɗari ba”.

Sai kuma ya kife kansa bisa guiwowinsa ya sake fashewa da sabon kuka kana yace.

“Innayi sunce idan muka sake neman ragi akan kuɗin kamar mun nemi akashe J ne”,.

Jingina kansa yayi jikin fillan dake gefenta tare da fashewa da matsanancin kuka hadda sheshsheƙa.
Cikin Sanyin jiki Innayi ta zauna kusa dashi batare da tace yayi shiri ko kuma ya daina kukan ba, domin ta
tabbata duk abinda yasa Moddibo kuka ba ƙaramin abu bane, kana idan har bai yiwa wannan abin kuka
ba to mai zai yiwa kuka arayuwarsa.

Moddibo kuwa kuka ya cigaba da yi tamkar ransa zai fita har shidewa yake.

A ƙalla ya ɗauki Mintuna masu tsawo yana kuka kafin ahankali ya ɗago kansa tare da kallon Innayi kana
yace.

“Innayi”.

Cikin sanyin murya tace.

“Na'am Moddibo”.

Cikin Muryansa daya dishe da kuka yace.

“Innayi ta wace hanya ce wace damace wane daliline kike samu kike mana duk kan buƙatun
rayuwarmu?

Innayi in dai har adana kuɗi kikayi in dai har basu ƙare ba Innayi ki fito mana dasu ki taimakeni aceci J
dashi”.

Jinjina kai tayi kana tace.

“Moddibo gaba ɗaya tattalin da mukayi na zaman rayuwar mu awannan yanki awannan gari a wannan
ƙasar anje matakin da gaba ɗaya tattalin namu yazo ƙarshe sabida lokacin komawa muhalli ya kusan
cimmmana”.

Sai kuma ta kalli Moddibo da har zuwa lokacin hawaye ke bin Fuskarsa kana tace.

“Na tanadi komai ne domin sanin cewa muna da bukatar su kama daga karuntaka, ci, sha, Jinya, sutura.

Da dai sauransu to yanzu kuma lokaci ya tafi rayuwa ta juya abubuwa sun tafi baki ɗaya tattalin namu
yayi ƙasa tsadan rayuwa ya cinye kaso mafi tsoka”.

Numfashi Moddibo ya fesar kana yace.

“Innayi koma wani irin tattaline shin babu ragowa ne ko kaɗan ne?”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Akwai ragowa”.

Cikin kuka yace.


“Menene amfanin ragowan duk tattalin arzikin da kike dashi matukar dai ba zai fito atemaki J ɗina da
shiba Jamelunki fa ya fito daga inda yake fa”.

Ya ƙare mgnar cikin ƙunan rai, domin gani yake kamar ma duk duniya ba'a damu da J ɗinsa ba.

Ita kuwa Innayi cikin tafiya wani sashi nazarin Jinjina kai tayi tare da cewa.

“Bashi da amfani Indai bazan fito dashi ba, amma bari na fito dashi amma yanzu ka fara yin shiru
tukunna kana kayi min al'ƙawarin cewa bazaka tambayeni komaiba akan duk abinda zaka gani”.

Kai ya gyaɗa mata kana yace.

“Innayi muga abinda zan fara samu awajenki tu kunna zanfi jin sanyi, ni yanzu a duniya babu tambayar
da ke bakina daya wuce ina J yake , wanne hali yake ciki”.

Sai kuma ya fesar da zazzafan numfashi tare da cewa.

“Wallahi Allah ji nakeyi tamkar naje na zauna abakin masallacai inyita bara asamu ahaɗa kudi in cikata in
karɓo J Innayi ya zanyi”.

Cike da rauni Innayi tace.

“Ba zakayi bara ba Moddibo Bari muga abinda Allah zai mana”.

Kai ta gyaɗa tare da jan hannunsa suka nufi bayan ɗakinta inda randunan ƙasa ke ajiye.

Kallon Moddibo da har zuwa lokacin hawaye ke zuba a idanunsa tayi kana tace ɗaga min randan nan”.

Sauri kallonta yayi kana ya Kalli randan ƙasan tare da cewa.

“In ɗaga miki randa kuma?”.

Ba tare data kallesa ba tace.

“Kada kayi min musu idan na baka Umarni kabi”.

Kai ya gyaɗa cikin sanyin yace.

“Toh”.

Tare da ɗaga randan ya matsar gefe.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.

“Toh ɗaga fantekar”.

Kai ya ɗaga tare da matsar da fantekar dake cike da ƙasa gefe.

Yana janye fantekar yaga ƙasan wajen alailaye.


Ahankali Innayi ta zauna agaban wajen Moddibo kuwa cikin sanyi jiki ya durƙusa agefenta.

Itako Innayi hannunta ta sanya ta fara tono ƙasan dake wajen ganin duhu agarin yasa Moddibo sanya
hannunsa acikin aljihu ya ciro wayarsa tare da kunna tochligt ya haska mata inda take tonawan.

Innayi kuwa ahankali ta cigaba da tono ƙasan bayan ta gama kwashe ƙasan ya rage sauran wasu manyan
duwatsu ahankali ta ciresu duka.

Cike da mmki Moddibo ya tsaida idanunsa akan fafakekken rami an lailayeshi da siminti yana rufe da
murfin tukunya kamar na lamba uku, da ɗan ƙarfi ta ɗago Murfin tukunya.

Cikin sauri Moddibo yayi saurin rintse idanunsa da karfu sakamakon wani haskene mai masifar sheƙi
daya ɗauke masa idanu daya kashe masa idanu,

A hankali ya kuma saƙe buɗe inadunsa, da sauri ya mitso ganin yadda cikin ramin ke sheƙi da ƙelƙeli mai
ɗauke ido yake fitowa daga cikin ramin, acan ƙasan ramin kuwa cike yake da ƴan ƙananan sulallan gwala-
gwalai wanda basu fiye yawa ba sosai hasken ya ɗauke masa idanu saboda hasken wayarsa daya haske
cike da tsanananin mamakin ya sunkuyo tare haska cikin ramin da kyau kana ya sanya tafin hannunsa
acikin ramin ya ɗebo guda huɗu tabbas sulallan Gwalne...!

Littafin SAKAYYAH na kuɗine ko kin ganshi a wani wurin na satane. Ki biya ki karanta cikin Aminci 1k ne
kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYA

30

*Littafin SAKAYYAH dai na kuɗi ne ba free book bane 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin Aminci kada ki
karanta na sata na Allah ya isa. 0661110179 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar
biyanki ta WHATSAPP 09097853276 sai in saki a Group ɗina*

30
Acikin tafin hannunsa ya ɗebo sulallan Gwal ɗin da wasu yan guntu-guntun sanduna tare da birbiɗin
yashin kana ya shiga jujjuyasu, ahankali ya maida kallonsa kan Innayi data gyaɗa masa kai alamar ya fito
dasu hannunsa ya zura acikin tukunyar yashiga kalato salullan wanda na ainihin Gwalne aƙalla sun kai
guda ashirin, karkaɗe yashin yayi tare da fitowa dasu kana ya ɗaura su akan rigarsa tare da gyara zaman
sa abakin ramin ya tsura mata Ido Innayi ma ido ta zuba masa ganin yanda ya zauna yasa tashiga maida
yashin ta rufe ramin kana ta sanya duwatsun ta rufe tare da tura fantekar kan ramin kallon Moddibo
dake binta da kallo tayi kana tace.

“Ɗaura min randan nan akai”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe still Idanunsa na Kanta cikin sanyin murya yace.

“Innayi wannan kamar Gwal?”.

Kai ta gyaɗa masa kana tace.

“Eh Gwal ne”

Still ba tare daya motsa ba ya sake kallon Gwal ɗin kana yace.

“Ina kika same su Innayi?”.

Girgiza masa kai tayi kana tace.

“Wannan ba lokacin tambayar ina nasamu gwala-gwalai bane. Moddibo lokacine daya kamata ace ka
lissafa su muga adadin su kana musan nawa za'a samu mu haɗa mu karɓo Jameelu yanzu tashi mubar
wajen nan mushiga ɗaki kaga dare ya tsala”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.

“Toh”,Kana yabi bayanta tare da tsira mata idanu cike da ɗumbin mamaki tare da tarin tuhuma ahankali
ya sake kallon sulallan Gwal ɗin dake haɗe da waɗanan sanduna guntaye aciki asaman laɓɓansa yayi
sallama tare da shiga ɗaki.

Wutan ɗakin Innayi ta kunna Atake haske ya zagaye ɗakin bayan Moddibo ta ratsa tare da rufe kofar
ɗakin kana ta dawo kusa dashi ta tsaya tare da sanya hannunta ta tsistsince ƴan guntulayen sandar ta
shiga haɗawa kasancewar akwai wajen haɗawa ajiki Moddibo kuwa Idanu ya zuba mata cike da mamaki.

tana cigaba da haɗawa ga mamakinsa sai yaga ya zama sanda irin wanda manyan Limamai ke riƙe wa
suna tafiya dashi sanda ce mai masifar kyau da tsari wacce da ka gani kasan mai tsadace.

Kallonsa Innayi tayi tare da cewa.


“Wannan sanda ce samansa inda ake riƙewa ne kaɗai keda Gwal sai kuma ƙasan sa inda ake dogara wa
amma wannan bazan baka shiba saboda ba zaiyi daraja sosai ba. Saboda ahaɗe yake da sanda kana
sandar kuma bazan siyar ba, sulallan dai zaka haɗa ka duba sai dai sunzo mana alokacin da bashine ba
saboda sulallan baki ɗaya sun ƙare”.

Ido kawai Moddibo ya zuba mata still da shock atare dashi.

Innayi ta cigaba da cewa.

“Baki ɗaya nauyin karatunka.

Cin mu, shan mu, suturar mu, tun kana ƙarami da duk wani abinda ya kama su nake ɗauka in siyarwa
Alhaji Hashim mai sayan gwala-gwalai shiyasan farashin sulallan duk yanda suke zan faɗa masa adadin
da suke yazo ya siya muyi lissafi muga nawa za'a samu”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan”.Yayi mgnar tare da lumshe idanunsa, baki ɗaya damuwarsa asamu kuɗin bawai
tunaninsa ya tambayi ina tasamu gwala-gwalan nan ba sannan bashida kuzarin da zai iya tambayar ta,
sandar na menene, kana bashi da ƙarfin zuciyar jin mai yasa baza asayar da sandar ba, ayanzu burinsa
bai wuce asamu ahaɗa kuɗaɗen akarɓo J ba.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon Innayi kana yace.

“Toh zan tafi dasu ɗakina”.

Kai ta gyaɗa masa kana ya miƙe ya fita yana jin confidence da farin ciki yasan Gwal nada daraja duk da
cewa ƴan ƙananun sulallane amma yasan da izinin Ubangiji zasuyi daraja.

Acan gidan Abba kuwa bayan tafiyar Moddibo Hajiya Karima ta kalli Abba daya zurfafa acikin tunani kana
ta ɗan ya mutse Fuska tace.

“Alhji wai yanzu baza ka sake ƙara neman ragi ba? yanzu sai ka ɗauki Million ɗari da hamsin ka basu mai
kake tunanin zai faru gaba idan sunji daɗi za'a sake ɗaukan ƴaƴanka ne fa!”.

Anutse Abba ya ɗago kansa tare da kallonta kana cikin sanyin Murya yace.

“Karima to me kike tunani?”.

Ba yabo ba fallasa tace.

“Ka nemi ragi”.

furzar da iska mai zafi yayi still Idanunsa na kanta kana yace.

“Karima kamar baki ji me yace ba, cewa fa yayi muddin aka nemi ragi akan rayuwar Jameel”.
Cikin sauri tace.

“Bafa za'a kashe Jameel ba, kawai Alhj idan zaka nemi ragi ka nemi ragi, sai kace baka sha zafin neman
kuɗin ba zaka ɗauka agabtale ka basu kamar ba kasan darajar suba, amma babu yanda zaka ɗauki
wannan maƙudan kuɗin ka bayar akan Jameelu!”.

Cike da mamaki Abba ya kalleta kana cikin ɗaga sautin murya yace.

“Karima to idan ban bada kuɗi akan Jameelu ba akan wa kike so in bayar? Shin Karima anya Karima?”.

Wani irin kallo ta masa kana cikin sauri tace.

“Anya me?”.

Dai-dai lokacin Hajiya Turai ta shigo baki ɗaya ta hargitse babu walwala afuskarta ta kalli Hajiya Karima
kana tace.

“Ai dai kam abin nata da mamaki, idan bai ɗauki kuɗi ya bayar akan Jameelu ba akan wa kike so ya
bayar?”.

Sai kuma ta maida kallonta kan Abba da idanunsa ke lumshe kana tace.

“Aini Alhj naga ƙoƙarin ku ma da har kuka iya neman ragin da suka rage muku, kuma ai sunyi ƙoƙari ni
dai anawa tunanin kada ku kuskura kada ku sake yin batun ragin wasu kuɗin, suje su kashe mana yaro
abanza idan aka kashesa mai son sa keda asara wanda bai sonsa kuma bai damu ba”.

Ta ida maganar hawaye na ciko kwarmin Idanunta.

Hajiya Karima kuwa wani kallo ta watsa wa Hajiya Turai tare da cewa.

“To mekike nufi?”.

Taɓe baki Hajiya Turai tayi kana tace.

“To ai gaskiya ne duk mai son Jameelu ba zai so ace za'a sake neman ragi ba”.

Taɓe baki Hajiya Karima tayi tare da watsa mata kallon banza kana tace.

“Kenan kina nufin Ni bana son Jameelu?”.

Hannu Hajiya Turai ta buɗe kana tace.

“A'a wannan ke ki kafaɗa da bakin ki amma dai shawaran da kika kawo ba shawara me kyau bace”.
Hannu Abba ya ɗaga musu tare da kallon Hajiya Karima dake kumfar baki kana yace.

“Bana son hayaniya ya isheku.

Dan Allah kubarni inji da abinda ke damuna”.

Kai Hajiya Turai ta gyaɗa tare da tsuke bakinta alamun itama ba hayaniyar take soba.

Cikin sanyi ta kalli Abba tare da cewa.

“Alhj ga Million biyu a Account ɗina zan bayar ahaɗa”.

Wani shegen kallo Hajiya Karima tabi Hajiya Turai dashi kana cikin taɓe baki tace.

“Hmmm munafurci dai da neman gindin zama haddasu kaza acikin cin danƙo”.

Cikin sanyi Abba yace.

“Nagode Turai Allah ya saka da alkhairi ayanzu kyauta koda na Naira biyar aka bani ita ina buƙatar ta,
xansa acikin tumunin kudin da za'a karɓo Jameel”.

Cikin sauri Hajiya Karima tace.

“Nima Allah ya bani in bayar”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Ameen”.

Juyawa tayi ta fice Hajiya Turai kuma ta zauna gefensa tana sake tausansa.

Acikin kwanaki biyu Moddibo ya saida gwala-gwalan da kuma motocinsa dana M Jameel Yayi total ɗin
kuɗin sun kama Million ashirin da biyar ya turawa Abba cikin account ɗin sa Alhamdulillah yanzu akwai
Million casa'in da biyar acikin account ɗin Abba Aɓangaren Abban ma yana cigaba da fafutuka ganin ya
samu kuɗi.

Acikin kwanakin baki ɗaya abubuwa sun kankama baki ɗaya sun sake maida hankalinsu kan neman kuɗin
suga sun samu sun haɗa yau ya kama kwanan M Jameel goma kenan awajen Kidnappers din kana yau
kwana biyu rabon Abba da Moddibo suyi waya da M Jameel Misalin huɗu na yamma Moddibo ya bar
gidan Abba ya nufi gidansu bayan sun sake tattauna wa.

Acan ɓangaren Boka Kar'uzu kuwa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami ce gurfane agabansa cikin wata
sandararriyar murya Boka Kar'uzu ya kece da wata mahaukaciyar dariya tare da jujjuya gashin dake
wangamemen tafi hannunsa kana ya ɗago kansa tare da Kallon Hajiya Bunayya da jajayen Idanunsa da
suka tara kwantsa yace.

“Kin tabbatar gashin yaron ne dai ko?”.

Cike da ƙwarin gwiwa Hajiya Bunayya ta jinjina masa kai tare da faɗin.

“Tabbas na tabbatar Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye
tsinanne Uban tsinannun wannan gashin kan Ramadan ne domin dana shafa turare na shafa kansa
bayan na fita naga gashi ya manne ahannu shine na tattare na kawo maka kamar yadda ka umarceni.

Wata mahaukaciyar dariya. Boka Kar'uzu ya sheƙe dashi wanda yasa bukkan da suke ciki ya hau girgiza
cike da jin daɗin kirarin data masa yace.

“Hhhhh magana ta ƙare Ƙaramar la'ananniya me kafirar zuciya aiki ya riga yayi anwuce babinsa saura na
Babban”.

Girgiza kai Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.

“Agama da batun Ramadan ɗin kafin ayi na Haiydar to babu matsala wannan ba damuwa bace”.

Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauƙe kana tace.

“Ni kuma Boka yanzu Abban Samira na nan amma nanda sati biyu masu zuwa zai tafi aikin Umrah,
shiyasa nayi shiru da batun zuwan Samira nan mu bari sai mahaifinta ya tafi kaga ba kowa agida da
banaso daga gidan Hajiya Bunayya arika zuwa ana daukan ta saboda sa idanawa. Amma Alhj na tafiya
idan ya kama ma ta dawo gidan ka idan kuma kaine ma zaka rinƙa kwana idan gari ya waye ka dawo to
duk daya”.

Wata dariya mai masifar ƙara Boka Kar'uzu ya kece dashi kana buga ƙafarsa na hagu wanda baki daya
ƙura ta buke wajen kana yace.

“Hhhhh saishi Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye tsinanne
Uban tsinannun shaiɗani Uban shaiɗanu babu wata matsala da zaran ya tafi zan zo Ni da kaina dan zamu
fi sakewa agidan naku acan ma zan tare in ragargaji sabon budurci”.

Kai Hajiya Lami ta gyaɗa tana murmushi kana tace.

“Yanda kake so haka za'ayi”.

Daga nan suka miƙe suka fita ta baya kamar yanda suka shigo suka nufi gida ransu fari soll musamman
Hajiya Bunayya.
Acan ɓangaren Khausar kuwa sanye ta fito cikin hijabi maroon mai facemaks kafadarta rataye da jaka
fari sol jikinta na fitar da sanyayyan ƙamshin turaren Oud Ma'aruf cikin yanayin sanyin ta da tun ɓatan M
Jameel bata dawo dai-dai ba ta kalli Mommy dake zaune kan 2sitter kana tace.

“Mommy zan tafi”.

Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.

“To kice ina gaida Ummi”.

Kai Khausar ta gyaɗa cike da nutsuwa ta fita tare da sanya Platshoe fari Anutse ta nufi coumpund ɗin
dai-dai lokacin da Amina da Uncle Naseer suka shigo hannunsu sarƙafe da juna kallo ɗaya Khausar ta
musu ta kawar da kanta gefe kana ta lumshe Idanunta.

Ido Uncle Naseer ya zuba mata tare da shafa kansa kana cikin sakin fuska yace.

“A'a Khausi ina zuwa da yamma nan?”.

Batare data sake kallon inda suke ba kana cikin sanyin murya tace.

“Zanje gidan su Asma'u ne”.

Langwaɓar da kai yayi kana yace.

“Ai haka dai maganar bata haɗa muba Khausar, ashe wai Malam Jameel aka sace Agaskiya garin nan ya
fara bada tsoro bari muje na kaiki in jajantawa Ummi”.

Girgiza kai Khausar tayi kana tace.

“A'a kabari kawai”.

Cikin sauri Amina ta watsawa Khausar harara kana ta maida kallonta kan Uncle Naseer Shima ta
hararesa.

Uncle Naseer kuwa ganin kallon da Amina ke jifansu dashi yasa ya ware idonsa tare da sakar mata da
lallausan murmushi kana yace.

“Ohh Baby Colm down mu nayin Auren mu zan ɗauke ki mu gudu mubar ƙasar nan, kafin muma
Akinnafemu tunda kinga anfara tsincr ƴaƴan masu kuɗi an ɗauke Malam Jameel next target ɗin su ni za'a
ce za'a saɓe ko ke, kafin ma su ankara zamu gudu abinmu.

Dariya Amina ta ƙyalƙyale dashi tare da manna kanta ajikin damtsen hannunsa.

Khausar kuwa cikin sauri ta kawar da kanta gefe tare da lumshe Idanunta.
Ahankali Uncle Naseer ya ɗago kansa tare da tsura wa Khausar Ido tabbas soyayyanta acikin jininsa yake
har yau har gobe zuciyarsa na muradin Khausar, itace burinsa Kawai zai Auri Amina ne domin cikar
Burinsa amma Khausar itace muradinsa.

fesar da iska mai sanyi yayi yana jin wani irin yanayi agame da ita kana yace.

“Khausi jirani in ɗauko sakon Uwaniyona inzo in kaiki?”.

Da sauri Amina ta janye kanta dake manne adantsensa kana tace.

“Ka kaita kuma?”.

Kai ya gyaɗa tare da yimata raɗa akunne yace.

“Yes My dear wife ai jaje ne".

Ashagwaɓe ta girgiza kai tare da cewa.

“Gaskiya Ni dai Uncle Naseer bana so ka tafi ka barni”.

Shafa fuskarta yayi kana yace.

“Bafa daɗewa zanyi ba”.

Khausar kuwa cike da takaicin abinda sukeyi tace.

“A'a Uncle Naseer ka bari ganan Haiydar ma zai kaini da mashin ɗinsa”.

Kai ya gyaɗa still Idanunsa na kanta yace.

“Ok”.

Dai-dai lokacin Haiydar ya fito daga sashen Abbansu hannunsa riƙe da key mashin dinsa.

Kallon Uncle Naseer da Haiydar yayi da murmushi afuskarsa yace.

“Uncle Naseer yau dai Addah Khausy ta yarda in jata amashin ɗina”.

Cikin alamun so Naseer yace.

“To ayi a hankali dai banda fifita”.

Dariya Haiydar yayi tare da cewa.

“Uhmm aikam zata sha fifita”.

Murmushi Uncle Naseer yayi tare da cewa.


“Dan Allah ka jata ahankali kada kayi mana asara”.

lumshe Idanunta tayi baki ɗaya bata da wani kuzari ɓatan M Jameel yayi masifar ratsata hakan yasa ko
magana bata fiye yiba daga Um-sai Um-um.

Haiydar kuwa mashin ya ɗauko tare da ɗaukar ta suka fice kana Amina da Uncle Naseer suka shiga ciki.

Haiydar na isa kofar gidan Ummi yayi Parking ahankali Khausar ta sauƙa tana gyara zaman hijabinta kana
atare suka shiga cikin Falon Ummi bakinsu ɗauke da Sallama.

Ummi dake zaune riƙe da carbi ahannunta Asma'u da Bashir na zaune gefenta suka Amsa Sallamar.

Cike da ladabi Haiydar ya gaisheta tare da sake yi mata jaje kana suka gaisa da Bashir tukunna suka fice
atare.

Khausar kuwa cike da sanyin tace.

“Ummi ki kwantar da hankalin ki insha Allah yaya Jameel zai bayyana babu abinda zai sameshi da izinin
Ubangiji addu'a mu bazai tafi abanza ba".

Jinjina kai Ummi tayi cikin yanayinta kamar mara lafiya tace.

“Ameen ya Allah”.

Cikin sanyin murya Asma'u da Muryanta ya dishe da kuka tace.

“Babbar matsalar mu yau kwana biyu kenan Basu sake kira ba gashi baki ɗaya kuɗin Million Casa'in da
biyar aka samu aka haɗa”.

Kallonta Khausar tayi tana cire hijabinta tace.

“Haka dai kika cemin jiya har yanzu kuɗin basu haɗuba”.

Kai Asma'u ta gyaɗa mata kana tace.

“Basu haɗu ba Khausar damuwar dake damunmu kenan wlh, baki ɗaya hankalinmu ya kasa kwanciya sai
dai Yah Modibbo yace Abba ya nemi bashin banki amman sunce yau ko gobe zai samu kuɗin”.

Cikin sanyin murya Khausar tace.

“Insha Allah kuɗin zasu haɗu da izinin Ubangiji Allah ya karesa ya tsare lafiyarsa”.

Atare suka amsa da Ameen.

Shiru Khausar tayi tare da tallafe kuncinta kana ta kalli Ummi da Asma'u sai kuma ta fesar da numfashi
kana buɗe jakarta tare da kwaso ƴan kunnaye da sarƙa da kuma zobe kala biyu da alamun nata dana
Mommy ne, hannun Ummi ta kama tasasu a ciki kana ta rufe hannun Ummin tare da cewa.
“Gashi inji Mommy na, tace Dan girman Allah da Manzonsa kada ki ƙi karba Ummi dan Allah kada kice
komai a saidashi a haɗa kuɗin.

Cikin tsananin jin dadi Ummi ta kalli girman Gwal ɗin musamman na Mommy wanda a ƙalla shi kadai zai
iya kai one Million da yan ɗori.

Hawaye na tsiyayo mata tace.

“Bazan ƙiba Khausar kicewa Mommynki ngd matuƙa ubanji yayi mata sakayya da gidan al'janna mai
girma”.

Cikin sanyi duk suka amsa da Amin.

Cikin sanyi Khausar ta fesar da numfashin kana a hankali tace.

“Amma Ummi Meyesa ba asa Police acikin maganar ba?”.

Cikin raunin murya Ummi tace.

“Sunce muddin Akasa police acikin maganar to abakin ransa”.

Cikin sauri ta dafe ƙirjinta tare da cewa.

“Innalillahi akan ransa kuma?”.

Kai Asma'u ta gyaɗa Tare da cewa.

“Kuma batun kuɗi ma da suka ce da farko Million ɗari biyu sukace yanzu ya zama Million ɗari da hamsin
saboda ragin da aka nema to yanzu sunce muddin aka sake neman ragi akan ransa”.

Aruɗe Khausar ta rintse Idanunta tare da cewa.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.

Sai kuma ta juya tare da kallon Ummi cikin sanyin murya tace.

“Ummi kinsan wani abu?”.

Kai Ummi ta girgiza kana tace.

“A'a”.

Lumshe idanu Khausar tayi tare da cewa.

“Ummi ranan da Yah Jameel ya mai dani gida da muna tafiya munga wata mota tana ta binmu abaya”.

Sai kuma tayi shiru alamar tunani ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.
“Ummi shine fa dama nace da za'a faɗawa hukuma zan iya bada number Motar saboda na zargi motar
duk inda mukayi motar na biye damu wataƙil da hukuma zasu shiga za'a iya kama wa anda suka sace Yah
Jameel, domin tun fitar mu motar ke bibiyanmu har saida muka kusa gidanmu suka daina binmu”.

Cike da mamaki Asma'u tace.

“Kai Khausar?”.

Kallonta Khausar tayi tare da gyaɗa mata kai kana tace.

“Wallahi kuwa Asma'u amma lokacin bamu kawo komai aranmu ba shima kuma Malam Jameel Bai kawo
komai ransa ba”.

Girgiza kai Ummi tayi kana tace.

“Toh ya zamuyi idan an faɗa zai zama matsala zasu kashesa tunda sunce basu yarda afaɗa wa hukuma
ba shiyasa dole muyi hakuri”.

Jinjina kai Khausar tayi kana cikin sanyin murya tace.

“Toh shikenan Ummi Insha Allah zamu cigaba da yiwa Yah Jameel Addu'o'i Allah ya bayyana shi”.

Jingina kai Ummu tayi tare da cewa.

“Yawwa shine abinda ya dace Allah yabamu Sa'a”.

Wunin wannan ranan haka Khausar tayi ta rarrashin Asma'u da Ummi kana tana sake basu ƙwarin gwiwa
kan cewa da izinin Ubangiji M Jameel zai dawo bayan Sallar sala'sar ta koma gida tana isa gida daga
bakin.

Barandarsu ta jiyo sautin kukan Ramadan cikin sauri ta cire takalminta tare da shiga falon bakinta ɗauke
da Sallama.

Cike da damuwa ta sauƙe Idanunta akan Ramadan daya kifa kansa kan cinyar Mommy cikin rauni da
raɗaɗin ciwo yake jujjuya kansa akan cinyar Mommy kana yana cewa.

“Mommy Kaina ciwo!,Mommy Kaina zai fashe!”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe Cike da damuwa tace.

“Subhanallah Ramadan yau tun safe kake ta cemin kanka na ciwo to meke faruwa ne na baka magani
kasha abanza ko dai in kira Abbanka ne akai ka asibiti?”.

Cikin tsanananin ciwo ya Girgiza mata kai yayi kana cikin Muryan kuka yace.

“Mommy ni dai Banason allura aƙara min magani kar kaina ya fashe”.
Khausar kuwa cikin sauri ta cire hijabinta kana ta ƙara sa kusa dashi tare da ɗaura tafin hannunta akan
goshinsa lokaci ɗaya zafi ya ratsa tafin hannunta har ƙananan jijiyoyin kansa sun tashi suna harbawa
cikin sauri ta kalli idanunsa gani tayi sun kaɗa suyi jawur dasu kana yanayin su ya koma kamar ajuye.

Saurin kallon Mommy dake jera masa sannu tayi kana tace.

“Subhanallah gaskiya Mommy akaishi Asibiti”.

Cikin sanyin murya Mommy ta kalli Ramadan dake ta juyi kana ta kalli Khausar dake cikin damuwa ta
fesar da numfashi tare da cewa.

“Nima nace aikai shi asibiti amma yace baya Son allura da zaran nace akaisa saiya sa kuka”.

Girgiza kai Khausar tayi kana ta sake shafa goshinsa da yayi masifar zafi cike da damuwa tace.

“Mommy yaushe za'a biye masa jifa yanda kansa yayi zafi kamar wuta”.

Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.

“Bari akwai maganin da Abbanku yace zai sayo masa yanzu bari idan ya kawo za'a bashi idan Allah yasa
ya samu sauƙi shikenan idan kuma abin be lafa ba dole sai mutafi asibitin”.

Jinjina kai Khausar tayi tare da cewa.

“Toh shikenan Allah ya bashi lafiya Allah kuma ya dawo da Abba lafiya”.

Mommy na shafa kan Ramadan tace.

“Ameen”.

Acan ɓangaren Abban Jameel kuwa ahankali ya miƙe tare da kallon wayarsa kana ya sauƙe Ajiyar zuciya
tare da nufar toilet domin ya watsa ruwa baki daya baya jin daɗin jikinsa bakinsa ɗauke da addu'a ya
shiga toilet din kana ya fara wanka.

Hajiya Karima dake zaune afalon kasancewar itace da girki tayi saurin kallon wayar Abba dake ruri
miƙewa tayi tare da isa kan 3sitter ganin number babu suna yasa tayi saurin picking tare da kaiwa
kunnenta tace.

“Assalamu Alaikum”.

Ba tare da mutumin ya amsa Sallamar taba yace.

“Ina Mahaifin Jameelu?”.

Da sauri ta gyara zaman wayar akunnenta tare da cewa.


“Me kuke so ku faɗa min nice mahaifiyarsa”.

Cike da gadara Mutumin yayi gyaran murya kana yace.

“Dashi muke son magana, muna son muji shin kuɗin mu sun haɗu ne?.

Zamu faɗa masa inda za'a ajiye kuɗin sannan kuma da inda za'a zo akarɓi Jameel”.

Hajiya Karima kuwa cikin ƙasa da murya tace.

“Haba bayin Allah kuji tsoron Allah mana.

Yanzu fisabilillah ina zamu samu Million ɗari da hamsin wannan aiba rayuwa bane duk da cewa
Mahaifinsa mai kuɗi ne ina zai samu wannan uban kuɗin acikin ƙaramin lokaci kawai dai ku temaka ku
rage idan ku akayi wa haka ya zakuji? Gwara dai ana rage mugunta”.

Dai-dai lokacin da Abba ya fito daga wankan batare daya gama ba jin alamar muryan Hajiya Karima na
magana ƙasa².

Yana fitowa ya Fisge wayar ahannunta tare da mannawa akunnensa dai-dai lokacin da mutumin ke
magana cikin tsanananin fushi da gadara yace.

“Ok haka ma kuka ce. Wato wasa da mu ku keyi kun maida mu bamusan abinda muke ba, toh Insha
Allah daga yau har gaban Abadan baza mu sake kiran kuba. Alhj Bashir ya maka kyau duk irin halarcin da
gargaɗin da muka maka baka jiba har kuna sake neman ragi”.

Cikin tsanananin kaɗuwa, ruɗu, da tashin hankali. Abba ya girgiza kai kana cikin raunin murya yace.

“Dan Allah da m...”.

Kafin ya ƙarasa yaji ɗit-ɗit-ɗit alamar sun kashe kiran.

Cikin wani irin yanayi ya zauna tare da sake kiran layin yaji akashe Aruɗe ya shiga fito da sauran numbers
din su yana kira amma baki ɗaya Switch off.

Kansa ya dafe da hannunsa na dama yayin da hannunsa na hagu ke riƙe da wayar.

Cikin wani irin fushi ya miƙe tare da kallon Hajiya Karima dake tsaye azabure ya ɗaga hannunsa tare da
kife ta da mari kana ya sake watsa mata wani gigitaccen marin da saida taga gilmawar taurari cikin wani
irin fushi ya cigaba da yarfa mata maruka gefen hagunta da damanta.

Muryarsa na rawa yace.

“Karima na saki acikin wannan maganar tunda aka fara. Meyesa zaki ɗauka min waya. Karima kin cuceni.
Wallahi Karima duk wani abinda ya faru da Jameelu kece sanadi kece kika ja ke kika cutar min da
rayuwar ɗana”.
Da sauri ya dafe ƙirjinsa dake wani irin zafi kana ya ɗago ya kalleta da idanunsa da suka sauya launi zuwa
tsantsar tashin hankali kana yace.

“Karima haka nayi dake kina gani ɗazu akan idonki na dawo daga Taraba naje na karamo kuɗi na sake
karɓan bashin banki 50 millons yanzu ruwan kuɗi ahannuna Million Ɗari da arba'in da biyar ne Million
biyar ne kaɗai ya rage kuma nasan da izinin Ubangiji ba zasu gagara ba zan nemosu amman shine zaki
nema min ragi”.

Hajiya Karima kuwa kuncinta ta dafe tare da sun kuyar da kanta ƙasa tana mai cike da taraddadi.

Cikin rauni da fusata Abba ya cigaba da cewa.

“Saboda bake kika haifi min Jameelu ba shine zaki salwantar da rayuwarsa, yanzu da ɗan da kika haifa a
cikin kine zaki masa irin wannan abin? Karima kin cutar da rayuwata cuta mafi muni, muddin wani
mummunan abu ya faru da Jameelu na bazan taɓa yafe miki ba”.

Cikin zubda hawaye Hajiya Karima tace.

“Haba Alhj wallahi ni ba haka nake nufi ba, kafahimceni tunda naga wancan karon ma da aka nemi ragin
ai sun rage shiyasa nace barin ne mamaka sauƙi”.

Dai-dai lokacin Moddibo ya shigo falon idanunsa suka sauƙa akan Abba da jikinsa ke rawa idanunsa sunyi
Jawur tamkar zai tsats-tsafo da hawayen jini yayin da numfashinsa ke seizing.

Cikin sauri Moddibo ya ƙara sa tare da riƙe Abba kana ya zaunar dashi akan kujera cikin sanyin murya
yace.

“Abba mai ya faru?”.

Kasa cewa komai Abba yayi baki ɗaya baya cikin hayyacinsa numfashinsa sai kai koma yake cikin rauni da
ficewar hayyaci yace.

“Karima kin cuceni Meyesa zaki min haka. Meyesa zaki ƙuntata min ta wannan hanyar!?”.

Cikin sauri Hajiya Turai ta shigo ganin halin da Abba ke ciki yasa kai tsaye ta wuce Bedroom ɗinsa tare da
ɗauko masa magani kana ta kira Dr Muktar ya ɗagawa tace.

“Dan Allah Dr maza kazo jikin Alhj ya tashi gaba ɗaya ma numfashinsa sama yake yi”.

Da Ok Dr ya Amsa kana ta katse kiran tare da fitowa da magani ta ɓare tare da miƙa masa.

Cikin azabebben rawan da jikinsa keyi ya ture hannunta tare da cewa.


“Ba zan shaba Karima kin cuceni kin cutar da rayuwata, kin datse min farin cikina. Meyesa haka Karima
duk abinda ya samu Jameelu Karima kece sanadi idan wani abu ya samu Jameelu Karima kece sanadi!”.

Ganin alamar baya cikin nutsuwarsa yasa Moddibo cewa.

“Dan Allah Abba ka kwantar da hankalin ka”.

Girgiza kai Abba keyi yana cewa.

“Karima kin cuceni kin cutar da rayuwata kin katse min farin cikina”.

Zama Moddibo yayi kana cikin sanyin murya ya shiga Furta.

_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakil Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli
khairan minha La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin la haula Wala ƙuwwata Illah
billahil aliyul Azhim”_.

Ahankali Abbah yafara bin bakinsa yana karato adduo'in tun yani yi Aransa har yafara afili.

Hajiya Turai kuwa number Dr Muktar ta sake Kira yana ɗagawa tace.

“Dr kayi sauri dan Allah ina katsaya har yanzu baka zoba kuma na faɗa maka jikin Alhj ya tashi gashi mun
basa magani yaƙi sha”.

Cikin sauri Dr Muktar yace.

“Gani nan na fito dama yanzu zan wuce asibiti amma yanzu na kusa gidanku ma ina ƙara so wa”.

Cike da damuwa tace.

“Toh shikenan sai kazo dan Allah kayi sauri”.

Ta ida maganar tare da katse kiran kana ta juya ta fice.

Moddibo kuwa ciki sanyi ya riƙe hannun Abba tare da cewa.

“Abba dan Allah kayi haƙuri ka cigaba da Addu'a”.

Kai Abba ya gyaɗa kana ya cigaba da maimaita adduo'in but still ɓarin da jikinsa keyi bai dai naba saima
ƙaruwa da yake.

Dai-dai lokacin da Dr Muktar yayi hong mai gadi ya buɗe masa kana cikin sauri ya fito daga motar
hannunsa riƙe da fest aid box Hajiya Turai dake Safa da marwa a coumpund ɗin ta masa jagora zuwa
ɗakin suna shiga Dr Muktar ya zauna kan 1sitter kana ya buɗe Aidbox ɗin sa tare da gwada Bp Abba.
Cikin sauri ya kalli Abba tare da cewa.

“Subhanallah jinin Alhj ya hau sosai na faɗa muku ku daina kawo duk wani abu da kuka san zai ɓata
masa rai, ko kuma tayar masa da hankali”.

Ya faɗa tare da ciro sirinji kana yace.

“Alhj bari nayi maka allura baki ɗaya damuwa yayi masa yawa”.

Ajiye sirinji Dr Muktar yayi kana ya balli magunguna ya miƙa masa tare da cewa.

“Alhj gashi kasha”.

Girgiza kai Abba yayi cike da rauni yace.

“A'a bazan shaba”.

Asanyaye Dr Muktar yace.

“Ayyah Alhj dan Allah kasha mana”.

Girgiza kai Abba yayi tare da cewa.

“A'a bazan shaba menene amfanin rayuwata matuƙar dai bazan iya temakon Jameelu na ba.

Meye riban cigaba da rayuwata matukar Jameelu na baya tare dani?”.

Cikin sauri Moddibo ya Girgiza kai tare da cewa.

“Subhanallah Abba kada kace haka kada zafin damuwa yasa mu kaucewa lissafin hankali da na
Musulunci Abba kayi addu'a dan Allah ka karɓi maganin kasha Abba. shin yakakeso nayi idan har kaima
ka faɗi ciwo ya kwantar da kai”.

Cikin tausayawa ya kalli Abba idanunsa cike da ruwan hawaye kana yace.

“Abba na tabbatar ko da J na nan bazai yi farin ciki da haka ba Abba dan Allah kayi haƙuri kasha
maganinka, ganinka cikin dauriya shike bani ƙarfin gwiwa Abba bazan so ganin wani mugun abu yasa
Meka ba. Idan har wani abu ya sameka Abba ya zanyi da rayuwata!?”.

Ya ida Maganar tare da miƙawa Abba maganin karɓa Abba yayi tare da kaiwa bakinsa ya haɗiye miƙewa
Dr Muktar yayi kana yace.

“Alhj bari a maka Allura”.

Kai Abba ya gyaɗa kana Dr Muktar ya masa bayan ya masa ya juya ya fice.
Sannu Ahankali Abba ya fara maida numfashi kana ya jingina bayansa da jikin kujera ahankali
numfashinsa ya fara dai-dai-ta Atake zufa ya shiga tsats-tsafo masa agabaki ɗaya ilahirin jikinsa.

Moddibo kuwa ganin haka yasa ya miƙe ahankali tare da ɗaukan remote ɗin AC ya kunna kana ya dawo
ya zauna agefensa.

Matsawa kusa da Abba Hajiya Turai tayi kana ta ɗauki hankief ta shiga goge masa zufa,

cikin sanyin murya tace.

“Sannu Alhj Ubangiji ya sawwaƙa maka, ka kwantar da hankalin ka insha Allah babu abinda zai samu
Jameelu sai al'khairi”.

Kallonta yayi amma baice komai ba.

Moddibo ma ahankali ya dawo kusa dashi ya zauna kana cikin sanyin murya yace.

“Abba ka kwantar da hankalin ka insha Allah babu abinda zai samu J Abba yanzu fa abinda ya kawoni da
mukayi waya kace ansamu kudin kwata kwata Abba yanzu fa Million biyar ne ya rage akan kuɗin da
muke nema ai abu yazo ƙarshe insha Allah babu abinda zai samu J,

Kuma ma kafin inzo nayi waya da Ummi tace akwai wasu gwala-gwalai guda biyu gobe zata kaisu Taraba,
da akan yau zata kaisuma to dare yayi, ta kuma cemin in sha Allah zasu iya kai two million.

Kajifa alamomin nasara Abba meye zai tayar maka da hankali!?”.

Ahankali Abba ya ɗago jajayen Idanunsa tare da kallon Moddibo kana ya kalli Hajiya Turai sai kuma ya
maida kallonsa kan Hajiya Karima dake tsaye cikin rauni ya nuna ta da yatsa kana yace.

“Karima ce nashiga wanka suka kira.

Karima ta ɗauka wai tana musu maganan ragin kuɗin nace ta nema min ragi ne?

Tabarni mana Jameelu ba ɗana bane ai zan fashi ɗana amma Meyesa Karima zata min haka!?”.

Moddibo kuwa cikin wani azabebben tsinkewar zuciya ya riƙe kansa tare da cewa.

“Innalilahi wa'inna ilahi rajiu'n.

kika nemi ragin kuɗi kuma Aunty Karima amma gaskiya baki kyauta mana ba”.

Cikin tsananin tsoro da fargabar abinda hakan zai haifar yaci gaba da cewa.
“Amma gaskiya baki kyauta manaba, ai wannan mugunta ne an saki ne ko kuma annemi wani temako
awajenki fisabilillahi? wallahi kin cutar damu wannan shine cuta mafi muni da kika mana bayan kinji
gargaɗin da sukayi”.

Ya ƙarashe mgnar cikin raunin murya yana jin zuciyarsa na wani irin zafi da karaya.

Cikin sauri Hajiya Turai ta kalli Hajiya Karima tare da Girgiza kai cike da takaicin halayyar ta tace.

“Idan har ba tayi haka ba ai bata cika Yadukko ba, ai dama baka sanin mai sonka da gaskiya sai kashiga
wani hali, wasu kuma burinsu su samu hanyar da zasu musguna wa rayuwarka suke nema”.

Kallon Hajiya Turai Hajiya Karima tayi kana ta kalli Abba da Moddibo cikin Muryan kuka tace.

“Agaskiya ni anyi min bahaguwar fahimta nima Ina son Jameelu tamkar ɗa yake awajena fa, ke Hajiya
Turai da kike wannan maganar nida ke waya fara zama da Jameelu ne?”.

Banza Hajiya Turai tayi da ita tana jin wani irin takaicin abinda ta aikata aranta.

Sannu Ahankali bacci ya fara fisgar Abba saboda magani da Alluran da aka masa nan take Bacci ya ɗauke
sa kwanciya Moddibo ya gyara masa akan kujeran kana ya miƙe tare da ɗaukar key ɗin motarsa
zuciyarsa cike da rauni damuwa da tashin hankali duk sun bayyana afuskarsa.

Yana fita yashiga motarsa tare da yimasa key yayin da hawaye suka cika kwarmin Idanunsa Driving yake
yana sake try numbers din da suke kira kasancewar duk lokacin da suka kira saiya yi copy amma baki
ɗaya Swich off.

Ahankali ya fito da Number M Jameel kana Yayi dearling cikin ikon Allah yaji wayar tashiga tana ringing
lokaci ɗaya ya shiga cikin matsanancin farin ciki afili ya furta.

“Yau kuma wayar J tana shiga”.

Cikin sauri ya juya akalar motarsa zuwa gidan Ummi kana ya Parking awaje tare da buɗe gate ya shiga
coumpund ɗin yana cewa.

“Ummi! Ummi!! Ummi!!!”.

Ummi dake tsaye Atsakiyar falo tayi saurin fitowa tare da cewa.

“Na'am Babana me yafaru?”.

Cike da walwala yace.

“Ummi wayar J ɗina yana shiga yau”.

Cike da farin ciki Ummi ta ware ido kana tace.


“Wayar Jameelu yana shiga?”.

Kai Moddibo ya gyaɗa still da murmushi afuskarsa ya gyaɗa mata kai kana yace.

“Wallahi yana shiga Ummi bari ma kiji”.

Ya faɗa tare da dearling number M Jameel aikuwa ya shiga ya fara ɗut-ɗut-dut cikin Sauri ya samata
akunne da sauri Asma'u da Bashir dake Bedroom suka fito jiyo sautin su Ummi cikin farin ciki.

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.

“Bari in Kira nima".

Ta ida maganar tare da dearling number kasancewar wayar na hannunta still ya shiga yana ringing.

Cikin sanyi ta juya ta kalli Moddibo tare da cewa.

“Babana to ya baya ɗauka kuma?”.

Cikin wani masifaffen tsinkewar zuciya da tsoro Moddibo ya kalleta cikin ƙoƙarin ɓoye tsoronsa yayi
Murmushi tare da cewa.

“A'a Ummi Insha Allah tunda har wayarsa tana shiga zai ɗaga mu cigaba da kira da izinin Ubangiji zai
ɗaga Agaskiya Ummi yau naji sanyi”.

Murmushi Ummi haram Asma'u, da Bashir.

“Har naji hankali na ya dan kwanta wayar J ɗina ya shiga, kinga farko kafin mu rasa shi kiran wayarsa
muka fara rasawa Ummi, yanzu kuma Insha Allah mun samu kiran wayarsa shi zamu ƙara samu next da
izinin Ubangiji”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.

“Ameen”.

Cikin jin sanyi Asma'u tayi murmushi kana tace.

“Alhamdulillah wayar Yah Jameel ya shiga gaskiya munyi farin ciki”.

Malam Ahmad daya fito daga wanka ya fito coumpund ɗin fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace.

“Alhamdulillah Asma'u maza kawo musu abinci suci tunda mun samu wayar Jameelu ya shiga maza kawo
musu abinci”.

Moddibo kuwa kallon Malam Ahmad yayi kana yace.


“Nikam ma Malam baki ɗaya cikina ya cushe baki ɗaya farin ciki ya cika min cikana”.

Murmushi Ummi tayi kana tace.

“Nima cikina ya cika baki ɗaya farin ciki nake ji”.

Jinjina kai Malam Ahmad yayi tare da cewa.

“Dan Allah ku zauna kuci abinci wayarsa muka fara rasawa yanzu kuma wayarsa muka faru samu insha
Allah shi ma zamu sameshi nan kusa ”.

Dai-dai lokacin Asma'u tazo ta ajiye musu abincin.

Tun ɓatan M Jameel sai yau Ummi da Moddibo sukaci abinci mai nauyi acikinsu duk da ba dayawa suka
ciba.

Miƙewa Moddibo yayi kana yace.

“Ummi bari naje in faɗawa Innayi ta tayamu farin ciki”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin.

“Aikam dai gwara kaje”.

Ficewa yayi tare da tafiya Driving yake Cike da farin ciki har ya isa gida yana zuwa ya shiga sashen Innayi.

Innayi dake ki shimfiɗe ta miƙe kana tace.

“Alhamdulillah Moddibo naga kana cikin farin ciki da alama akwai labari mai daɗi?”.

Kai ya gyaɗa still Fuskarsa ɗauke da murmushi yace.

“Innayi wayar J ɗina ya shiga yau”.

Kai Innayi ta gyaɗa tare da cewa.

“Alhamdulillah gaskiya munyi farin ciki. Allah ya bayyanar mana dashi”.

Ameen ya amsa tare da wucewa sashen sa cike da farin ciki yana shiga ɗaki ya kira layin Malam Arɗo.

Malam Arɗo na dagawa yace.

“Malam Alhamdulillah yau wayar J ɗina yashiga a cigaba da taya mu da addu'a a masallacai da
makarantu”.

Cike da farin ciki malam Arɗo yace.

“Masha Allah da izinin Ubangiji zai fito Insha Allah zamu cigaba da addu'a”.
Awannan daren haka Moddibo Ummi, Asma'u Bashir malam Ahmad da Innayi suka kwana cike da farin
cikin shigar wayar M Jameel.

Yayin da Aɓangaren Abba ya kwana cikin taraddadi da tashin hankali koda ya farka tsakiyar dare kuka
yayi ta yi yayin da Hajiya Karima ke kuka tana basa haƙuri kana tana cewa bada niyya tayi ba.

Aɓangaren gidan Lamiɗo ma haka Khausar da Mommy suka kwana azaune da Ramadan da kansa ke
masifar ciwo da zaran an bashi maganin da Lamiɗo ya kawo yasha ciwon zai ɗan lafa jimawa kaɗan kuma
zai sake tashi tsakiyar dare ya farka ya riƙa kuka dole Ummi ta kira Abba ya kawo masa magani cikin ikon
Allah yana sha ciwon kan ya lafa.

Washe gari; Moddibo, Malam Arɗo, Ummi Innayi duk wani makusancin M Jameel na cikin farin ciki kana
duk wanda ya kira wayarsa zai shiga sai dai ba aɗagawa Wunin wannan ranan haka Moddibo yayi yana
kiran layin M Jameel still ba amsa.

Zuwa yamma jikin Moddibo ya fara sanyi da lamarin ganin yana kiran wayar M Jameel baya shiga lokaci
ɗaya tsoro ya fara kamashi hankalinsa ya tashi Misalin ƙarfe goma na dare yana gidan Abba zaune sun
kira Jameel kuma sama da sau ashirin kuma duk kiran yana shiga, sau dai ba'a ɗagawa, su kuma
masatan basu kiraba.

Yayin da idanun Abba ke kumbure alamar har yanzu jinjinsa bai sauƙa sosai ba.

Cikin mutuwar jiki Moddibo ya koma gida kai tsaye sashen Innayi ya nufa bakinsa ɗauke da Sallama ya
shiga.

Innayi dake zaune riƙe da carbi ta amsa masa cikin raunin Murya yace.

“Innayi”.

Kallonsa tayi cike da kulawa kana tace.

“Na'am”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana cikin sanyin murya yace.

“ Innayi hankalina ya soma tashi wayar J yana shiga ba'a ɗauka sannan mutanen nan basu sake kira ba”.

Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da cewa.

“Ba komai Moddibo Insha Allah ka kwantar da hankalin ka”.


Girgiza kai yayi kana yace.

“Anya kuwa Innayi?”.

Cikin bashi ƙwarin gwiwa tace.

“Ba komai Insha Allah ka cigaba dayi masa addu'a da izinin Ubangiji zai fito yanzu idan sun sake kira kuce
musu an samu kuɗin Insha Allah Million biyar bazai gagara ba koda a masallatai anemi temako za'a
samu su haɗu”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Toh Innayi Allah yasa su kira ɗin dan yanzu kam ma cikon Million ukune”.

Cikin jin daɗi Innayi tace.

“Alhamdulillah Allah ya bamu sa'a”.

Amin yace

Sanna ya miƙe ya koma sashen sa cike da damuwa. Washe gari jin sauran kuɗin da ake buƙata, Lamido
ya bawa Mommy da kanta ta kaiwa Ummi su sau dai sam basu kuma kiraba.

Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya yau kusan kwana ki shida kenan duk lokacin da aka kira wayar M
Jameel zai shiga sai dai ba'a ɗauka.

Yayinda Ramadan kuwa ke kwana da azabebben ciwon kai idan aka bashi magani yasha ciwo ya lafa
anjina kaɗan kuma ya sake dawowa.

Ga ɗaya Mommy da kwausar sun shiga damuwa, sun kai asibiti har cikin Taraba anyi hoton kan da duk
wani gwaje-gwaje amman babu wani ciwo dake kansa, dan da farima likitocin sunyi zaton brain cancer
ne.

baki ɗaya yaron ya fita hayyacinsa saboda tsananin ciwon kai.

Yau kimanin kwana shida kenan da aka fara samun wayar M Jameel na shiga.

Washe garin rana ta bakwai.

Da safe bayan an idar da Sallar Asbah Moddibo na fita a masallaci ya kira wayar M Jameel.

Cike da mmki tsoro ya janye wayar a kunnenshi sabida jin ance masa Switch off.

cikin mutuwar jiki ya nufi gidan Ummi yana shiga ya samu Ummi zaune akan Sallaya hannunta riƙe da
Carbi.
Cike da ladabi ya gaisheta kana cikin sanyin murya yace.

“Ummi”.

Kallonsa tayi tare da cewa.

“Na'am Babana”.

Cikin raunin murya yace.

“Ummi na kira wayar J ɗina baya shiga”.

Ahankali Ummi ta jingina kanta da jikin kujeran falon kana tace.

“Nima na kira wayan Jameelu na baya shiga bansan Meyesa ba Allah yasa al'khairi ne”.

Cike da sanyi Middibo yace.

“Amin ya Allah in sha Allah ba komai Ummi”.

Cikin raunin murya Ummi ta lumshe Idanunta tare da cewa.

“Hmmm,Hmmm Ubangiji Allah yabamu ikon cinye jarrabawar da zai jarabce mu”.

Cikin sanyi Moddibo yace.

“Ameen”.

Miƙewa Moddibo yayi kana yace.

“Ummi bari naje gidan Abba naji koshi ya kira ya shiga”.

Kai Ummi ta gyaɗa Muryanta cike da rauni tace.

“Toh”.

Cikin sanyin jiki zuciya cike da karaya Moddibo ya nufi gidan Abba yana shiga coumpund ya ga Abba na
ƙoƙarin shiga falo dawowansa daga masallaci kenan.

Ƙara sawa Moddibo yayi tare da miƙa masa hannu sukayi musabaha kana cikin sanyin murya Moddibo
yace.

“Abba wayar J ɗina baya shiga”.

Ahankali Abba ya sunkuyar da kansa hawaye masu zafi suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar kamar
ƙaramin yaro baki ɗaya ya rame cikin raunin murya yace.

“Aliyu dama wayar Jameelu da kira yake shiga. Wani sanyi ne dama hankalina ya tashi tun jiya nake kiran
wayar baya shiga, dama ni banyi farin ciki da shigan wayar Jameelu ba. Aliyu inaji Ajikina kamar akwai
wani abu da bamu san menene ba jikina na bani ko ina Jameelu na yaje baya cikin walwala na rasa tudun
dafawa”.

Cikin sauri Moddibo ya runtse Idanunsa zuciyarsa na bugawa da masifaffen ƙarfi kana cikin raunin murya
yace.

“Abba insha Allah J yana cikin ƙoshin lafiya mu cigaba da masa addu'a amma nima baki ɗaya hankalina
yayi masifar tashi”.

Cikin rauni da tsanananin tashin hankali suka ci-gaba da tattaunawa.

Acan gidan Lamiɗo kuwa Mommy, Khausar da Lamiɗo basu rintsaba a wannan daren.

A kan Ramadan suka kwana yanata kuka baiyi bacci ba.

Washe gari Bayan an idar da sallan Asbah Hajiya Bunayya ta shigo falon Mommy ahankali Ramadan dake
kuka ya miƙa mata hannu kana cikin wata raunan'niyar murya mai cike da wahala yace.

“Ummah! Ummah! Kaina zai fashe kaina zai faɗi Wayyo Allah na Kaina! kaina”.

Baki daya jijiyoyin kansa sun tashi sunyi ruɗu ruɗu dasu yayinda idanunsa sukayi ja.

Cike da tausayawa Khausar ta ɗaura tafin hannunta na dama akan goshinsa Idanunta cike da ruwan
hawaye kasa riƙe hawayen ta tayi jin yanda kan ke harbawa da masifar ƙarfi.

Kuka sosai Ramadan keyi kana cikin tsananin radaɗin ciwo ya riƙo hannun Mommy kana yace.

“Wayyo Mommy Kaina zai fashe. Mommy Kaina Wayyo zan mutu Mommy Zan mutufa”.

Wani irin miƙa Ramadan yayi tare da cewa.

“Momyyyyy zan mutuuuu”.

Cikin sauri Lamiɗo da yanzu ya shigo ya karɓesa ganin yanda idanun yaron suka juya da sauri ya fara ɗan
bubbuga kumatunsa yana cewa.

“Ramadan! Ramadan!”.

Wani irin juyawa Idanun yaron yayi tare da wulƙitawa kana yaja dogon numfashi....!

*Zuwa yanzu dai mun gama ratsa tsakiyar labari babi-babi na zaren na dab da fara warware wa.*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*
SAKAYYAH

31

*Littafin nan dai ba free book bane, na kuɗine ko kin gashi a wasu wuraren da ba Group na da ake biya
insa mutum, littafin 1k ne kacal in sha Allah zaki karanta shi daga forko har ƙarshe akan 1k kacal
0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276
ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki yar uwa*

31

Lamiɗo kuwa cikin yanayin, tausayi da jinƙai da ƙauna mai haɗe da taraddadi da tsoro, ya sanya tafin
hannunsa na dama ya tallafo, fuskar Ramadan ya juya gefe da gefe ga mmkinsa gaba ɗaya uwayan
yaron ya koma lagob-lagob cikin yanayi da kiya da son aro Jarumtaka ya runtse Idanunsa tare da
maimaita kalmar Hasbunallahu wani'imal wakil. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n.

Cikin sauri Hajiya Bunayya dake zaune ta buga hannunta aƙirji tare da kallon Lamiɗo daya zubawa
Ramadan ido tace.

“Mai Martaba ya rasu ko?”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da ɗago ido ya kalleta kai ya girgiza mata batare da yace komai ba.

Da sauri Mommy dake tsaye tayi baya tare da zama da ɓas akan kujeran dake bayanta, baki ɗaya jikinta
ya saki Atake ta fara Maimaita kalmar.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin”,ta faɗa hawaye na bin kuncinta Shar-
shar.

Khausar kuwa juyawa tayi ta kalli Hajiya Bunayya kana ta mayar da kanta kan Mommy da hawaye ke bin
kuncinta ahankali ta sake maida kallonta kan Lamiɗo da yayi shiru yana jan yatsun Ramadan alamar yana
dai-dai-tasu.

Cikin wani irin yanayi tace.

“Abba mu tafi dashi asibiti,Abba mu kaisa asibiti”.


Jujjuya kai Lamiɗo yayi kana yace.

“Khausar ki nutsu”.

Kallon Hajiya Bunayya da Idanunta ke kan Ramadan yayi yace.

“Hajiya Bunayya kama khausar ki zaunar da ita”.

Mommy kam tana zaune akan kushin babu abinda take maimaitawa face kalmar Innalillahi still hawaye
na bin kuncinta.

Ganin haka yasa Lamiɗo fesar da numfashi kana ya miƙe tare da ɗaukar Ramadan awuyansa ya fice.

Da sauri Khausar ta miƙe tare da bin bayansa tana cewa.

“Abba inzo mu tafi Asibitin ne!?”.

Tsintsiyar hannunta Hajiya Bunayya ta riƙe tare da gyara zamanta tace.

“Khausar ki nutsu mana ki dawo ki zauna?”.

Kai khausar ta girgiza cikin rawan murya tace.

“Ki sake ni zamu tafi asibiti ne kiga Ramadan fa”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da faɗin.

“Ki zauna mana ba kiji Abbanku yace ki zauna ba.

Kai ta gyaɗa cikin wani irin yanayi ta koma ta zauna.

Lamiɗo kuwa yana fita kai tsaye sashen Gimbiya Dadu ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama zaune ya samu
Gimbiya Dadu afalon.

Ganinsa Rungume da Ramadan yasa cikin sauri tace.

“Ya dai lafiya Lamiɗo meke faruwa?”.

Cikin sanyin murya yace.

“Ramadan ne fa ki duba min shi”.

Kai ta gyaɗa tare da Matsawa gaban Ramadan dake kwance ƙasan ɗakin yatsunta biyu ta kai saitin
hancinsa sannan ta riƙe jijiya hannunsa kallon Lamiɗo tayi cike da mamaki tace.

“Ha'a bashi da rai ai ajikinsa?”.


Araunane Lamiɗo ya ɗago idanunsa da suka kaɗa sukayi jawur jijiyoyin kansa ya tashi cikin raunin murya
yace.

“Nima dai kamar haka na gani ahannuna na ya cika kamar babu rai atare da shi.

Jinjina kai Gimbiya Dadu tayi cikin rawan murya tace.

“Tabbas ba Rai atare dashi Ramadan ya rasu fa”.

Ta ida maganar tare da ɗago hannunsa ta juya sangalam duk ta inda ta juya sai ya tafi luuuu zai fadi kana
ga bakinsa dake aɗan buɗe idanua kafe.

Ahankali Lamiɗo ya sunkuyar da kansa akan Ramadan hawaye masu ɗumin gaske suka shiga zubo masa
asaman kincinsa, suna ɗiga kan fuskar Ramadan tal-tal yayinda jinkinsa ya shiga tsuma.

Gimbiya Dadu kuwa bayanta ta jingina da jikin kujeran cikin sanyin murya tace.

“Allah sarki Ramadan ashe dai ciwon kan nan na ɗauka ne? Ciwo lokaci ɗaya!?”.

Akuma dai-dai lokacin Uncle Naseer ya shigo falon ganin yanayin da suke ciki ne yasa ya zauna gefen
Gimbiya Dadu tare da cewa.

“A Lafiya meke faruwa?”.

Ahankali Gimbiya Dadu ta ɗago kai tare da Kallonsa tace.

“Wallahi Ramadan ne Allah ya masa rasuwa!”.

Arazane Uncle Naseer ya Kalli Gimbiya Dadu tare da kallon Ramadan dake kwance cikin wani irin yanayi
yace.

“Ha'a wani irin magana ne Gimbiya Dadu ya zakice Ramadan ya rasu!? Ko ke Dr ce ya za ayi kice ya rasu
taya kika gane hakan?”.

Kallonsa ya mayar kan Lamiɗo daya zubawa Ramadan ido kana yace.

“Yah Lamiɗo mu kaisa asibiti”.

Kallonsa Lamiɗo yayi tare da Girgiza masa kai still Idanunsa na nan ja jawur ruwan hawaye na kwance
acikinsu yayinda jikinsa ke cigaba da tsuma zuciyarsa na harbawa da masifan ƙarfi.

Uncle Naseer kuwa hannu yasa a aljihu tare da ciro wayarsa yayi dearling number family Dr su yana
ɗagawa yace dan Allah yazo ya duba yaro agida Dr ya amsa da toh.
Bayan minti 16 minute Dr yazo bayan ya duba ya tabbatar musu da Ramadan ya rasu kimanin minti
talatin da suka wuce.

Sai asannan Uncle Naseer ya yarda kana ya raka Dr ya tafi yana dawowa.

Sashen Gimbiya Dadu ya hadu da Lamiɗo ya fito da Ramadan Rungume akafaɗarsa bayansa yabi Lamiɗo
kuwa kai tsaye Falonsa ya nufa yana shiga ya kwantar da gawar Ramadan Atsakiyar ɗakin kana ya cire
masa suturar jikinsa ɗen oh foɗimo.

Cikin rauni da tsinkewar zuciya ya nufi ɗakin Mommy a inda yabar Mommy zaune anan ya dawo ya
sameta still Idanunta na zubar da hawaye masu zafi da ƙuna a zuciya.

Khausar dake gefenta ta kalleta tare da cewa.

“Mommy Meye faru me yasamu Ramadan?”.

Ahankali Mommy ta janyota jikinta tare da kwantar da ita akan cinyarta kana ta sanya hannunta akanta
tana shafawa cikin sanyin murya mai cike da rauni tace.

“Khausar muyi haƙuri Ramadan kam ya tafi ya barmu.

Ubangiji Allah yajiƙan sa Allah ya masa rahma Allah yasa mai cetone”.

Cikin tsananin tashin hankali Khausar ta fashe da matsanancin kuka me tsuma zuciya yayin da ta shiga
girgiza kanta kallon Mommy tayi Muryanta na rawa tace.

“Mommy Ramadan kike cewa ya rasu!? Mommy wannan wani irin magana ne!?

Dan Allah Mommy kice mafarki nake Mommy kice ba gaskiya bane!”.

Girgiza kai Mommy tayi still Hawaye na bin fuskarta amma ta gaza furta komai.

Cikin sauri Khausar ta toshe bakinta jin wani matsanancin kuka ya taho mata.

Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe tare da ƙarasawa cikin falon ya zauna kusa da Mommy, kasancewar akan
3sitter take.

Cikin sanyi murya yace.

“Khausar kiyi haƙuri kinji ko?”.

Kallonsa tayi da jikaƙƙun Idanunta kana tace.

“Abba da gaske wai Ramadan ya rasu!?”.


Nunfashi Abba ya fesar tare da jinjina mata kai yace.

“Da gaske ne Khausar ya muka iya da hukunci Ubangiji, dama shi ya bamu Ramadan kuma shi ya
karɓesa, kiyi haƙuri ki daina kukan nan kinji ko!?”.

Girgiza kai tayi tare da sake fashewa da matsanancin kuka mai gunji.

Dafa kanta Lamiɗo yayi cike da tausayawa yace.

“Kiyi haƙuri yanzu ma Naseer ya kira Dr yazo ya dubasa sannan ya tabbatar min da cewa ya rasu!”.

Cikin wani irin yanayi mai cike da ruɗu Khausar ta miƙe da gudu tare da shiga Bedroom ɗinta ta faɗa kan
gado tare da sakin marayan kuka.

Lamiɗo kuwa bayan ya sake rarrashin Mommy tare da bata haƙuri da kuma nuna mata muhimmanci
tawakkali da haƙuri ya mike ya fita.

Bayan angama shirya Ramadan an masa wanka an suturtasa yanda addinin Musulunci ya tsara aka kaisa
gidansa na gaskiya.

Bayan andawo Lamiɗo da ƴan Uwansa da kuma Abokan arziƙi aka zauna zaman Makoki.

Wunin wannan ranan haka Mommy da Khausar suka yini cikin alhini da jimamin rashin Ramadan Hajiya
Bunayya kuwa sosai tayi farin ciki sai dai kallo ɗaya zaka mata ka fuskanci mutuwar ta shigeta domin
ayanda take nunawa tafi Mommy damuwa wani abin ma Mommy ke tausarta tana bata haƙuri.

Washe gari Khausar ce zaune a ƙasa Mommy na Kan kujera gabansu Kuma kayan Breakfast ne.

Cikin sanyin murya Mommy ta kalli Khausar tare da cewa.

“Khausar ki matso kici abinci”.

Girgiza kai Khausar tayi tare da kallon Mommy da kumburarrun Idanunta kana cikin sanyin murya tace.

“Mommy ba najin yunwa”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da rintse Idanunta kana tace.

“Khausar ki matso kici abinci bana son haka zamuyi fushi da abinda Ubangiji ya jarabcemu da shine Allah
daya halicci Ramadan yafimu son sa shi ya bamu Ramadan kuma shi ya ɗauke mana shi!”.

Wasu hawaye masu masifar zafi ne suka zubowa Khausar akuncinta cikin matsanancin kuka tace.

“Mommy shikenan!, Shikenan Ramadan ya tafi baza mu sake Kallonsa ba shikenan mun ransa shi har
abada. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.
Kallonta Mommy tayi still Idanunta cike da ruwan hawaye Akuma dai-dai lokacin wayarta ya ɗauki ruri.

Kallon screen ɗin wayar tayi nan taga sunan Hajja Nana na yawo.

Cike da ladabi tayi Picking tare da kaiwa kunnenta tace.

“Hajja ina yini?”.

Daga ɗaya ɓangaren Hajja Nana tace.

“Lafiya lau ina Khausar!?”.

Cikin sanyin murya Mommy ta kalli Khausar da hawaye ke zuba a Idanunta kana tace.

“Gata nan”,

“Toh ki bata wayar”, cewar Hajja Nana ta.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da miƙawa Khausar wayar.

Amsa Khausar tayi cikin Muryan kuka tayi sallama.

Cike da kulawa Hajja Nana tace.

“Ke kuma lafiya ya naji muryanki haka kukan me kike!?”.

Cikin sheshsheƙan kuka Khausar tace.

“Hajja Nana Ramadan ɗin mune ya rasu”.

Hajja Nana kuwa cikin sauri tace.

“Innalillahi Wa'inna Ilahi rajiu'n Ayyah Allah sarki Ubangiji Allah ya jiƙansa da rahma Allah yasa
maicetone ai bamu da labari bamu sani ba bawa Mommy naki”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da miƙewa Mommy wayar.

Jin Mommy ta amshi wayar yasa Hajja Nana cewa.

“Wai ashe Ramadan ya rasu!?”.

Kai Mommy ta gyaɗa kana cikin sanyin murya tace.

“Eh Wlh”.

Ajiyar zuciya Hajja Nana ta sauke tare da cewa.

“Ikon Allah Meye sameshi haka?”.

Numfashi Mommy ta fesar tare da gyara zaman ta kana tace.


“Wallahi ciwon kai ne mako ɗaya”.

Cikin sanyin murya da tausayawa Hajja Nana tace.

“Allah sarki Allah ya gafarta masa Ubangiji yasa maicetone! Dama yanzu Malam Liman zai shigo
Gembulan Insha Allah zan biyo shi muzo”.

Jinjina kai Mommy tayi cikin sanyin murya tace.

“Toh Allah ya kawo ku Lafiya mungode sosai”.

Bayan Mommy ta kashe wayar ta kalli Khausar data zubawa kayan Breakfast Ido Cike da tausayawa ta
shiga lallashinta.

Acan gidan Ummi kuwa Moddibo ne zaune afalon ya tsurawa waje ɗaya Idanu yayin da Ummi kanta ke
ƙasa hawaye zira-zira baki ɗayan sun zurfafa acikin tunanin da suke Asma'u ta fito daga kitchen cikin
mutuwar jiki ta tsugunna kusa da Ummi kana cikin sanyin murya tace.

“Ummi”.

Ahankali Ummi ta ɗago Idanunta dake zubar da hawaye kana cikin sanyin murya tace.

“Na'am”.

Lumshe idanu Asma'u tayi tare da faɗin.

“Ummi yanzun nan mukayi waya da Khausar tace in gaisheki”.

Kai Ummi ta gyaɗa cikin sanyin murya tace.

“Ina Amsawa”.

Asma'u kuwa cikin raunin murya tace.

“Ummi wai Ramadan ya rasu fa”.

Cikin sauri Ummi ta ɗago kanta dake ƙasa ta kalli Asma'u shima Moddibo cikin sauri ya kalli Asma'u
zuciyarsa na cigaba da bugawa da masifar ƙarfi.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe cikin raunin murya tace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n yaushe ya rasu!?”.


Gyara zama Asma'u tayi cikin sanyin murya tace.

“Shekaran jiya fa take cemin randa tazo bayan ta koma ciwon kan ya fara mishi, sunyi ta sintirin asibiti a
banza, tace shekaran jiya kuma haka aka kwana dashi haka jiya da Asbah ma ya tashi dashi washe gari da
safe bayan sallar Asbah ya rasu sai bayan Azahar akayi jana'izar sa!”.

Girgiza kai Ummi tayi tare da fesar da numfashi kana tace.

“Allah sarki rayuwa Ayyah Aysha ta ɗanɗani Mutuwa mai zafi da raɗaɗi mutuwar ɗa akwai ciwo Allah ya
masa rahma Allah yasa maicetone”.

Cikin sanyin murya Asma'u tace.

“Ameen Ummi”.

Jinjina kai Ummi tayi tare da cewa.

“Insha Allahu zanyi ƙoƙari muje”.

Moddibo kuwa ahankali ya buɗe Idanunsa dake lumshe ya kalli Ummi tare da cewa.

“Allah yajiƙan sa da rahma, shine yaron da Mota ya buge ko?”.

Kai Asma'u ta gyada tere da cewa.

“Eh shine”.

Cije lip ɗinsa na ƙasa yayi tare da cewa.

“Allah sarki kwanansa na gaba alokacin Allah ya gafarta masa”.

Cikin sanyi murya Ummi tace.

“Ameen”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.

“Ummi bari in tashi Inje wajen Abba naji ya ake ciki muji daga Jiya zuwa yau ko sun kira”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan”.

Cikin sanyin jiki ya miƙe tare da ficewa kai tsaye gidan Abba ya nufa.

Bayan ya isa gidan ya shiga falon Abba nan ya samu Dr Muktar zaune zama gefen Abba yayi bayan sun
gaisa Moddibo ya sauƙe numfashi kana cikin sanyin murya yace.

“Abba har yanzu basu kira ba”.


Kai Abba ya gyaɗa masa tare da rintse Idanunsa kana yace.

“Basu kira ba Aliyu bansan me mutanen nan suke nufi da muba”.

Tagumi Moddibo da Abba sukayi duk sunyi jugum-jugum dasu.

Misalin ƙarfe biyu da rabi na rana Hajja Nana da Malam Liman suka iso gidan Lamiɗo bayan sun gama
gaishe-gaishe suka zauna har aka Idar da La'asar Lamiɗo ya shigo tare da kallon Hajja Nana kana yace.

“Hajia ki fito malam Liman yana jiranki”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh gani nan fitowa”.

Kallonta ta mayar kan Mommy dake jan Carbi kana tace.

“Yanzu kam ba abinda zance miki, ta'aziyya muka zo miki amma Insha Allah kwanan nan zan dawo kan
batun Khausar”.

Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa.

“Toh shikenan Nagode Hajja Nana Allah ya saka da alkhairi”.

Miƙewa Khausar tayi tare da bin bayan Hajja Nana jikinta sanye da dogon hijabi har ƙasa yayin da
hannunta ke riƙe da wayarta Idanunta sunyi luhu-luhu dasu suna fita coumpund ɗin taga Malam Liman
acikin mota amazaunin Driver.

Wara kumburarrun Idanunta tayi kana cikin sanyin murya tace.

“Iyeee lallema tsohon nan ashe ka iya mota?”.

Murmushi malam Liman yayi tare da gyada mata kai kana yace.

“Eyyy sosai ma kuwa dama lokacin da kikaje ai mota ta talalace ne shiyasa ankaita wajen gyara to wata
aka sake siya min”.

Murmushi tayi kana tace.

“Ashe kunji daɗi ƙauyenku akwai mota”.

Jinjina kai yayi da murmushi afuskarsa yace.

“Hadda ke ai acikin ƙauyen ya zaki cire kanki?”.


murmushi tayi cikin yanayin sanyin tace.

“ai Lallai dai kam to Allah ya tsare muku hanya”.

Ta faɗa tare da komawa cikin falon Ummi.

Kallon Hajja Nana Malam Liman yayi bayan ya dai-dai-ta motar akan kwalta yace.

“Addah Nana za muje gidan Malam Arɗo wannan ɗaliban nawa”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh ba matsala muje mana”.

Jinina kai Malam Liman.

bayan sun isa gidan malam Arɗo yayi Parking tare da isa falon baƙinsa wanda ke harabar gidan bakinsu
ɗauke da Sallama.

Daga ciki malam Arɗo wanda ke zaune tare da Moddibo ya amsa tare da basu Izinin shiga.

Bayan angama gaishe-gaishe Malam Arɗo yace.

“Lafiya Malam Liman yau ziyarar yamma”.

Cikin jimami Malam Liman yace.

“Wallahi ɗan gidan Mai martaba Lamiɗo ne ya rasu shine muka zo Ta'aziyya”.

Jinjina kai Malam Arɗo yayi tare da faɗin.

“Bashakka hakane ai yaron ɗalibin mune, wallahi ni lokacin da akayi jana'izar nasa banji ba amma Insha
Allah zanje ta'aziyya da izinin Ubangiji”.

Kai Malam Liman ya gyaɗa tare da gyara zamansa kana yace.

“Wallahi kuwa rasuwa abin tausayi wai ciwo dare ɗaya ya tsananta”.

Girgiza kai Malam Arɗo yayi da alamun damuwa atare dashi yace.

“Ayyah haka fa kwanaki mota ta bigeshi abakin Makarantar mu fa. Yaron ya samu karaya wannan
bugewan ba wanda yayi tunanin zai warke Allah sarki ashe ajalin nakusa”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da cewa.


“Haka fa rayuwar take ciwon Ajali lokacin ɗaya zai shige mutum sai dai kaji ance babu shi saidai fatan
Allah yasa mu cika da Imani”.

Baki daya suka amsa da Ameen banda Moddibo daya zubawa ƙasan ɗakin Idanu da alama ya zurfafa
acikin tunanin da yake.

Ahankali Malam Liman ya juya tare da kallon Moddibo kana ya maida kallonsa kan Malam Arɗo tare da
cewa.

“A'a Malam Arɗo wannan jikan namu dashi kaje kwanakin baya ko?”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa tare da kallon Moddibo da har zuwa lokacin kansa ke ƙasa yace.

“Eh jika nane kuma Malamine Amakaranta na”.

Murmushi Malam Liman yayi tare da faɗin.

“Ayyah Masha Allah Yayi kyau amma lafiya na ganshi haka baki ɗaya ya canza ko bada shine ku kaje
Jauro yaya kwana kiba”.

Cikin sanyi malam Arɗo ya gyaɗa kai kana yace.

“Eh da shine mukaje”.

Cike da mamaki Malam Liman yace.

“Amma lafiya kuwa?”.

Numfashi Malam Arɗo ya fesar tare da Girgiza kai kana yace.

“Ina kuwa lafiya wannan zamani da Allah ya kawo ku. Malam Liman kai dai Ubangiji ya rufa mana asiri”.

Anutse Malam Liman ya gyara Alkyabbar dake jikinsa kana yace.

“Amin ya Allah".

Kana ya ɗaura da cewa.

“Amman Meke faruwa?”.

Gyara zama Malam Arɗo yayi tare da fuskantar Malam Liman cikin sanyin murya yace.

“Akwai wani Amininsa Yaron Alhj Bashir mai Dala Jameelu da aka sace baki ɗaya abin ya fitar mana
hayyaci mun rasa wani irin tunani zamuyi ma acikin wannan al'amari”.

Cikin sauri Malam Liman yace.


“Sunhanallah”.

Cike da damuwa Malam Arɗo ya gyara zama tare da zayyane musu duk abinda ke tafiya yanda aka
sacesa da kuma yanda akanemi kuɗin fansa kana da yanda suka daina jin labarinsa kwata kwata.

Girgiza kai Malam Liman yayi kana yace.

“Subhanallah”.

Ya faɗa tare da maida kallonsa kan Moddibo wanda shima adai-dai lokacin ya ɗago Idanunsa da suka
kaɗa sukayi jawur baki ɗaya fuskarsa tayi fayau ya rame.

Cike da tausayawa Malam Liman yace.

“Amma yanzu baku da labarin sa!?”.

Girgiza kai Moddibo yayi kana cikin raunin murya yace.

“A'a bamu da labarinsa yau kusan kwana goma sha biyu kenan bamu da labarinsa, sannan wayarsa bata
shiga suma kuma sun daina kiran mu abinda yafi komai tayar mana da hankali kenan, bamusan Inda J
yake ba”.

Malam Liman kuwa Anutse ya fesar da nunfashi cike da tausayinsa kana ya gyara zamansa tare da cewa.

“Bakomai Insha Allah za muyi addu'a da izinin Ubangiji duk inda yake a faɗin duniyar nan Ubangiji zai
bayyana shi”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da Gyara zamansa Malam Liman ya cigaba da cewa.

“Da Iznin Ubangiji Allah zaiyi dalilin da za'a ganshi zan baka addu'a'o'in idan har zaku jure kuyita yi da kai
da mahaifiyarsa da kuma Mahaifinsa, to za ayi nasara kuma nima zan tayaku”.

Cikin sauri Moddibo ya sauƙe Ajiyar zuciya tare da cewa.

“Munaso Malam ai addu'a'u Saiful mu'uminun ce ita addu'a itace makamin bawa dama ita muke tayi
ai”.

Kai Malam Liman ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan zan baka adduo'i Insha Allah da izinin Ubangiji Allah zai bayyana shi, aduk inda yake
afaɗin duniyar nan sai dai walau ko araye ko amace amma Ubangiji zai bayyana shi insha Allah za'a ga
walallanilansa”.

Cikin sanyi Moddibo yace.


“Mun gode Malam”.

Cike da nutsuwa da kamala Malam Liman ya fara bashi Adduo'i Moddibo kuwa cikin sauri ya ɗauki jotter
da biro ya fara rubutawa wasu da yawa daga cikin Adduo'in Moddibo ya sansu wasu kuma baisan suba
sabida shi ilimi kogine faɗi gareshi. sosai ya riƙa faɗa masa adduo'in Moddibo kuwa yana rubuta
adduo'in yana bitar su yasan da izinin Ubangiji idan ya zauna na awa biyu yayi research ɗinsu zai
haddace su.

Bayan Malam Liman ya gama bawa Moddibo adduo'in Hajja Nana ta saki ajiyar zuciya kana tace.

“Toh Ubangiji Allah ya karesa Allah ya bayyana sa aduk inda yake”.

Cikin sanyi murya suka amsa da Ameen.

Kallon Malam Liman Hajja Nana tayi tare da faɗin.

“Ai wannan Jikanmu ne ka tuna ƙawata Innare?”.

Kai Malam Liman ya gyaɗa mata tare da cewa.

“jikanta ne?”.

Jinjina kai Hajja Nana tayi tace.

“Eh shine”.

Murmushi Malam Liman yayi tare da faɗin.

“A Masha Allah Yayi kyau”.

Ita kuwa maida kallonta kan Moddibo tayi wanda gaba ɗaya ya zubawa takardan adduo'in ido kana tace.

“Idan ka koma ka gaishe min da ita yau kam bazan samu zuwa ba yanzu ma munyi yamma”.

Kai ya gyaɗa kana cikin sanyin murya yace.

“Toh mun gode Allah ya saka da al'khairi Insha Allah zataji”.

Miƙewa Hajja Nana da Malam Liman sukayi tare da yi musu Sallama suka tafi Moddibo kuwa yana fita
daga gidan Malam Arɗo kai tsaye gidan Abba ya wuce Bayan sun gaisa Abba yayi shiru tare da tsirawa
waje ɗaya ido gabansa da magunguna da alamar bai daɗe da gama shaba.

Ahankali Abba ya maida kallonsa kan Moddibo da yaga yayi mugun rama ya sake zama wani so silent duk
da dama can bamai yawan magana bane amma yanzu shirun yayi yawa.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da faɗin.


“Aliyu kaga yanda ka koma kuwa ka dawo kamar wanda yayi shekara yana jinya”.

Kallon Abba Moddibo yayi tare da sakin murmushin da yafi kuka ciwo kana ya sunkuyar da kansa ƙasa
tare da cewa.

“Abba”.

Still Idanun Abba na kansa yace.

“Na'am”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.

“Insha Allah Abba inaji Ajikina J ɗina ya kusa bayyana”.

Numfashi Abba ya fesar tare da sakin murmushi na alamar jin daɗi kana yace.

“Allah yasa haka Aliyu”.

Ahankali Moddibo ya amsa da Ameen kana yace.

“Abba ya zun nan akwai wani malami da muka haɗu dashi agidan malam Arɗo ko Malam Arɗo da kansa
wajensa yake zuwa ɗaukan darasi ya bani adduo'i masu tarin yawa”.

Sai kuma ya lumshe idanunsa tare da cije Lip ɗin sa na ƙasa kana yace.

“Adduo'in da nake ji ajikina insha Allah Ubangiji zai amsa mana, gashi ya bani adduo'i da dama yace mu
riƙa yi dani da kai da Ummi. Insha Allah duk inda J yake afaɗin duniya Allah zai bayyana mana shi za muji
labarinsa aduk inda yake”.

Murmushi Abba yayi tare da faɗin.

“Mungode ƙwarai Allah yasa adace”.

“Ameen yace kana yaci gaba da cewa.

“Kyansa ma mu ƙara harda Azumi amma dama Ni tuntuni ina Azumin Abba kaima ka gwadayi.

In Sha Allah ni zan shiga itiƙafi na tsawon kwanaki uku Insha Allah”.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“Toh shikenan Moddibo Allah ya temaka”

Nan Moddibo ya bawa Abba adduo'in kana ya tafi kai tsaye gidan Ummi ya nufa itama ya bata Adduo'in
cikin sanyin murya tace.
“Toh Babana Insha Allah zanyi”.

Kai ya gyaɗa kana ya fice kai tsaye gida ya nufa yana isa sashen Innayi ya wuce sannan ya mata bayanin
duk abinda ya faru tare da bata Adduo'in da Malam Liman ya bayar kana ya faɗa mata saƙon gaisuwar
da ƙawarta ta bata.

Kana ya gyara tsayuwar sa tare da cewa.

“Toh zan shiga 'itiƙafi a ɗaki”.

Jinjina kai Innayi tayi da faɗin.

“Toh me dame kake bukata?”.

Girgiza kai yayi kana cikin sanyin murya yace.

“Bana buƙatar komai Akwai Friuts a Fridge sannan akwai kayan tea kuma azumi zanyi”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh Allah yatemaka Allah ya bada sa'a.

Ameen ya amsa tare da nufar Bedroom ɗinsa.

Yana shiga yaja ƙofa ya rufe tare da nufar toilet ya ɗaura alawala yana fitowa ya zauna bisa salla ya
fuskanci gabas.

Ya fara rera karatun Al'ƙur'ani sai karfi ɗaya ya fara jero Adduo'i yanayi yana kuka.

Sai ƙarfe uku ya kwanta ƙarfe huɗu dai-dai ya farka yasha tea da fruits Washe gari ya tashi da Uzumi
haka ya yini da azumi yaita Adduo'i da karatun Alkur'ani idan dare yayi haka zaita nafilfili sai karfe uku zai
kwanta ƙarfe huɗu zai tashi yayi Sahur haka ya cigaba da rayuwa har tsawon kwanaki uku aɗaki yana
fadawa Ubangiji bukatarsa Aɓangaren Abba ma haka ya ɗauki tsawon kwanaki uku yana bautar Ubangiji
haka Ummi ma baki ɗaya ta miƙawa Ubangiji lamuranta.

Yau ya kama kwana na huɗu kenan ahankali Moddibo ya fito daga falonsa tare da tsayawa abakin
farandar.

Innayi dake tsaye ta zuba masa ido lokaci ɗaya taji hawaye na zubo mata ganin yanda yayi wani masifar
ramewa idanunsa sunyi luhu-luhu dasu yayinda sajensa ya cika fuskarsa kasancewar gashi mai santsi da
laushi yasa sai sheƙi yake fuskarsa nan tayi fayau sai sheƙi take alamun a ɗan kumbure take sabida
yawan kuka da rashin isasshen bacci.

Lumshe Idanu Innayi tayi hawaye masu zafi suka zubo ganin kamar daga jinya ya tashi.
Moddibo kuwa ahankali ya ɗaga kai ya kalleta jin yandata tsaresa da ido.

Cikin rawan murya tace.

“Moddibo kaga yanda ka dawo kuwa?”.

Murmushi mai ciwo yayi tare da Girgiza kansa cikin sanyin murya yace.

“Innayi bari na tafi wajen Ummi”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh baka tsaya kaci abinci ba”.

Girgiza kai yayi kana yace.

“A'a Innayi na ƙoshi”.

Kallonsa Innayi tayi Idanunta cike da ruwan hawaye tace.

“Dan Allah Moddibo ka tsaya kaci wani abu dubi yanda ka dawo fa”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.

“Toh shikenan Innayi ki bani tea”.

Cikin sauri ta hado masa tea ta kawo masa karɓa yayi yasha bayan yasha ya fita kai tsaye gidan Ummi ya
nufa bakinsa ɗauke da Sallama ya shiga falon.

Ummi na ganinsa tayi saurin miƙewa tare da fashewa da kuka mai cike da rauni.

Moddibo kuwa cikin sauri ya ƙarasa kusa da ita tare da riƙe tafin hannunta kana cikin raunin murya yace.

“Ummi meyafaru Ummi kuka kuma?”.

Cikin zubda hawaye ta kallesa tare da cewa.

“Babana abubuwan sun haɗu sunyi min yawa acikin kwanaki Ukun nan Ba Jameelu na sannan kai ɗinma
da nake gani inji sanyi na daina ganinka. Babana kaga yanda kadawo fa”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Ummi Insha Allahu in Allah ya yarda hawayen mu ya kusa daina zuba inaji Ajikina J yana kusa damu”.

Numfashi ta fesar tare da cewa.

“Allah yasa hakan Babana dubi yanda ka dawo fa kamar wanda aka sallamo daga asibiti kana tafiya Iska
na ɗibarka”.
Sai kuma ta maida kallonta kan Asma'u data zabga tagumi tana binsu da kallo baki ɗaya itama ta rame ta
sake zama shiru.

Cikin sanyin murya tace.

“Asma'u kawo masa abinci yaci”.

Kai ya Girgiza Asanyaye yace.

“Ummi bana jin yunwa”.

Cikin sauri da sanyi Ummi tace.

“Zafa kaci abinci matuƙar kana son hankalina ya kwanta to kaci abinci Babana”.

Cikin sanyi yace.

“Toh Ummi”.

Ahankali Asma'u ta fito hannunta riƙe da Plate ɗin dambun shinkafa dayaji Vegetables ya na fidda
ƙamshi da soyayyan naman kaza akai da kwalin exotic.

Agabansa ta ajiye masa kallon Ummi yayi ganin yanda ta tsare da ido tana zuba masa, ahankali ya fara
cin abinci duk da yana jin cikinsa ya cushe yaci ya kai rabi kana yasha lemon Kaɗan.

Ture Plate din yayi kana yace.

“Ummi bari Inje gidan Abba”.

Kai ta gyaɗa da fadin. “Adawo lafiya”.

Moddibo na fita kai tsaye gidan Abba ya nufa yana isa ya shiga falon bakinsa ɗauke da Sallama Atare
Abba da Malam Arɗo dake zaune suka amsa masa cikin sanyi Moddibo ya nufi gefen Abba ya zaune tare
da Gaishe su.

Kallon Moddibo Malam Arɗo yayi kana yace.

“Moddibo yau kwana uku bakai babu dalilinka sannan wayarka bata shiga shine nace bari inzo tambayi
Abban Jameel ko lafiya kaddai wanda suka ɗauki Jameelu ne suka ɗauke mana kai”.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.

“Nima da ban ganshi ba gaba ɗaya hankalina ya tashi duk da cewa nasan yana gida lafiya amma rashin
ganinsa ya sake tayar min da hankalin rashin ganin Jameelu na”.

Cikin sanyin murya Malam Arɗo yace.


“Toh Allah ya bayyana shi Alhj Ubangiji Allah ya bayyanar dashi aduk inda yake!”.

Cikin rauni Moddibo ya kalli Abba tare da cewa.

“Abbah basu kira ba atsawon kwana ki ukun nan”.

Girgiza kai Abba yayi da faɗin.

“A'a basu kira ba Aliyu kuma ga wayar Jameelu na ta daina shiga, yanzu sannan suma sun daina kira”.

Moddibo kuwa ahankali yace.

“Bakomai Abba Insha Allah Allah zai bayyana shi akan al'khairi Alfarman Annabi da Alkur'ani”.

Atare suka amsa da Ameen Hajiya Turai ce tashigo bakinta ɗauke da sallama bayan sun gaisa da malam
Arɗo ta kalli Moddibo da faɗin.

“Moddibo kwana biyu shiru gashi babu wani labarin Jameelu Ubangiji dai Allah ya bayyana mana shi”.

Cikin sanyin murya suka amsa da Ameen kana ta juya ta fice.

Kallon Moddibo Malam Arɗo yayi kana yace.

“Moddibo muje ka rakani wani waje mana”.

Kallonsa Moddibo yayi da faɗin Ni kuma?”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa masa kana yace.

“Eh”.

Girgiza kai Moddibo yayi cikin sanyin murya yace.

“A'a kayi haƙuri ni kam babu inda zanje”.

Kallon Moddibo Abba yayi kana yace.

“Aliyu kaje ka rakasa mana”.

Gyara zama Malam Arɗo yayi tare da faɗin.

“Kuma ta'aziyya ne ma zai rakani, gidan Lamiɗo tunda akayi rasuwar yaron nan yau wuni na biyar kenan
ban samu naje ba, kuma kaima ya kamata kaje amatsayin ka na Malaminsu”.

Shiru Moddibo yayi tare da sunkuyar da kansa ƙasa.


Ahankali Abba yace.

“Aliyu kuje mana zama waje ɗayan nan ma bashi da daɗi”.

Girgiza kai Moddibo yayi cikin sanyin murya yace.

“Abba ni dai banason zuwa”.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe da faɗin.

“Kuje mana Aliyu Ubangiji Allah yasa zuwan ya zama alkhairi”.

Cikin sanyin murya yace.

“Ameen”.

Sannan ya miƙe Malam Arɗo na biye dashi suka fita.

Acan gidan su Khausar kuwa Lamiɗo ne zaune afalon tare da wasu baƙi guda biyu da suka zo daga
Taraba Alhj Ibrahim da Alhj Musa suka zo yi masa ta'aziyya sai kuma Uncle Naseer dake gefe.

Mai gadi ne ya shigo bakinsa ɗauke da sallama kana yace.

“Ranka ya daɗe ga Malam Arɗo da Malam Moddibo Malaman su Ramadan sunzo”.

Kai Lamiɗo ya gyaɗa tare da faɗin.

“A'a kace su shigo harda malam Arɗo da kansa”.

Kai ya gyaɗa sannan ya fice ba dadewa Malam Arɗo suka shigo tare da zama kana suka yi Masa ta'aziyya
ahankali Moddibo yace.

“Ashe Ramadan lokaci yayi Allah ya masa rahma”.

Cikin sanyi Lamiɗo yace.

“Ameen Moddibo ya mukaji da taraddadin rashin Jameelu har yanzu shiru ko?”.

Cikin sanyi Moddibo yayi ƙasa da kansa tare da matse yatsun hannunsa batare da yace Uffan ba sai kai
da ya gyaɗa masa.

Da-dai lokacin mai gadi ya sake shigowa tare da cewa.

“Ranka ya daɗe ga Ɗan gidan Arɗo Ja'eh yazo yi maka ta'aziyya”.

Kai Lamiɗo ya gyaɗa da fadin kace ya shigo”.

Fita mai gadin yayi tare da sanar da baƙon.


Da Sallama Bararojin Fulanin dajin yashiga falon Lamiɗo cikin shigarsu irin ta Fulani hannunsa riƙe da
sanda kusa da ƙafar Lamiɗo ya zauna kana suka gaisa sannan ya musu ta'aziyya.

Juyawa yayi ya kalli Malam, Arɗo, Moddibo, Alhj Musa Alhj Ibrahim ya gaishesu tare da yi musu
ta'aziyya.

Kallonsa Lamiɗo yayi kana yace.

“Ori ya Baban naka?”.

Cikin yanayin rashin wadatacciyar Hausa yace.

“Ai bashi da lafiya ne shiyasa bai samu yazo ba, na wakilcesa munji labarin Ramadan ya rasu Allah ya
masa rahma”.

Baki ɗaya suka amsa da Ameen.

Ahankali Lamiɗo ya juya tare da kallon Moddibo kana yace.

“Moddibo da gaske wai har yanzu babu labarin Jameelu”.

Ahankali Moddibo ya ɗago kansa dake ƙasa ya kalli Lamiɗo cikin rawan murya.

“Eh har yanzu babu labarinsa, yanzu kam ma sun daina kira, sannan kuma wayarsa ma da ake kira ta
daina shiga zuwa yanzu munsa hukuma a cikima sunyi iya bincikensu ba labari”.

Malam Arɗo ne ya gyara zamansa tare da faɗin.

“Ai wannan Zamani da Allah ya kawo mu sai dai Ubangiji ya rufa mana asiri amma an maida satan
al'ummar kamar satan ƴaƴan awaki”.

Ido Ori ya zuba masa tare da sakin Ajiyar zuciya.

Malam Arɗo yace.

“Kisan rai kuma ba adaukesa abakin komai ba, ran mutum ya dawo kamar ran kishiya, baki ɗaya duniyar
nan ta canza ta burkice ta koma abin tsoro, in ba haka ba kamar Malam Jameelu asace sa bashi babu
labarinsa”.

Alhj Musa da Alhj Ibrahim kuwa kai suka jinjina da faɗin.


“Sosai kuwa yanzu idan kana da dukiya hankalin ka ba akwance ba, haka zalika idan kana talaka ma baka
da nutsuwa, sai dai Allah ya kawo mana ɗauki amma baki ɗaya jama'ar duniyar ta canza, yanzu ma idan
muka fita daga nan zamuje wajen Alhj Bashir ɗin muyi masa jaje”.

Malam Arɗo ya gyaɗa kai tare da cewa.

“Muma yanzu daga can muka fito”.

Jinjina kai Alhji Musa yayi da faɗin.

“Allah sarki Jameelu yaro mai mutunci da karamci, ga sanin darajar manya Ubangiji ya bayyana shi”.

Gyara zama Ori yayi tare da fuskantar Lamiɗo cikin rashin ingantaccen hausarsu yace.

“Hmmm Lamiɗo wato ai wannan duniyar ta zama abin tsoro kwanan nan abinda na gani acikin dajin mu,
saman dutsen Membilla aƙasan wata bishiya har zuwa yau hankalina bai gama dawowa jikinaba har
zuwa yanzu wanda yasan ni da ya ganni ayanzu yasan ban gama dawowa cikin hayyacinaba”.

Atare Moddibo da sauran jama'ar dake falon suka juya suka kallesa kusan a tare sukace.

“Me ka gani?”.

Girgiza kai yayi da faɗin.

“Kai tashin hankalin fa ya tsananta, muda muke daji ai munfi ku ganin tashin hankali, ku ai kuna cikin gari
ba abinda kuke gani sai dai in an ɗauke muku mutum kuke ganin tashin hankali”.

Lokaci ɗaya zuciyar Moddibo ya tsinke da masifar ƙarfi yana bada sautin dib-dib-dib cikin sauri ya sanya
tafin hannunsa na dama ya dafe saitin ƙahon zuciyarsa kana ya runtse Idanunsa yayin da gaba ɗaya
ilahirin jikinsa ya hau kyarma wani zufa mai ɗumi ya keto Masa daga tsakiyar kansa cikin raunin murya
yace.

“Amma meyafaru meka gani bawan Allah!”.

Girgiza kai Buba yayi da faɗin.

“Abinfa ba daɗin gani, domin ya wuce tunanin mutum”.

Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe tare da faɗin.

“Toh Allah ya rufa mana asiri amma baki ɗaya zamani ya zama abin tsoro, to amma Ori mai kagani acikin
dajin da har ya gigita ka haka, bayan ku Fulani daji kun saba ganin abubuwa!”.

Cikin sauri Ori ya girgiza kai da faɗin.


“Kai gane ganen da muka saba ba irin wannan bane! Duk abinda muke gani na yau da kullum lamuran
iska ko halittun dajine”.

Alhj Musa dake fuskantarsane yace.

“To amma meka gani haka?

Ya kamata idan kunga abu irin wannan na tsoro Ku riƙa faɗa acikin gari wurin jami'an tsaro”.

Girgiza kai Ori yayi cikin sanyin murya yace.

“Uhm muna tsoro ai”.

Lamiɗo ne ya sauƙe Ajiyar zuciya da faɗin.

“To amma meka gani?”.

Gyara zama yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya kana yace.

“Abinda nagani abin tsoro ne, to amma dai banga amfanin ɓoye muku ba, yau tsawon kwana bakwai
kenan ina kiwon shanu na akan Dutsen Membilla”.

Duk ido suka zuba masa tare da maida nutsuwarsu kansa suna saurarensa.

Gyara zama Ori yayi kana ya cigaba da cewa.

“Ina nufar kan dutsen sabida ɗebo kanya, naji wani irin wari mai gigitarwa da fitar da hayyacin ɗan Adam
Atake tsoro ya kamani na rasa wani irin wari ne wanan.

Saboda ban taɓa jin wari makamancin wannan ba!”.

Cikin sauri Lamiɗo ya kallesa da faɗin.

“To wannan wani irin wari ne!?”.

Ajiyar zuciya ya sauke da faɗin.

“Hmmm Lamiɗo nima kaina na gigice.

Saboda ban taɓa jin makamancin wari irin wannan ba a duniya!”.

Alhj Ibrahim ya fesar da numfashi kana yace.

“To amma me kagani awajen haka?”.

Girgiza kai yayi da alamun damuwa atare dashi yace.


“Ban taɓa ganin abinda ya tayar min da hankali ya kiɗimani ba irin wannan domin ina jin warin na haura
na nufi wajen agindin wata Bishiyar kanya”.

Cikin zaƙuwa da gajiyawa za tsinkewar zuciya Modibbo yace.

“Uhmmm!!”.

Shi kuwa Ori runtse Idanunsa cike da damuwa ya cigaba da cewa.

“Ina haurawa kan dutsen. Naga gawa ɗaure a jikin bishiyar, da igiyoyi tako ina.

Wanda da alamu abin ya kwana biyu domin tuni mutumin ya rasu gawace aɗaure, bisa ga duk kan alamu
tunda ransa aka dauresa har ya rasu domin har ya kumbura yayi dam sai wani irin sheƙi fuskarsa duk
sauran jinka keyi, fuskara ɗauke da murmushi duk da ya rasu, sai kuma alamun kwaranyar hawaye a kan
kumatunsa gemunsa da sajensa sai sheƙi sukeyi tamkar wanda kullum ana shafa masa maine kai in ka
ganshi kace balarabene wannan warin ne kaɗai ke nuni da gawane, domin a lokacin bai fasheba jikinsa
fes”.

Cikin sauri da wani irin azabebben tsinkewar zuciya Moddibo ya runtse Idanunsa tare da taune lips ɗinsa
na ƙasa kana yace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakil”.

Malam Arɗo kuwa cike da tsoro ya kalli Ori kana yace.

“To amma kai Meyesa baka zo ka faɗa acikin gari ba!?”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.

“Tsoro nakeji domin Atake awajen na fara sheƙa amai da gudawa saboda warin dana shaka karshe ma
agigice na koma gida, domin bana cikin nutsuwa ta kuma tunda na koma saida nayi kwana uku bani da
lafiya ko kiwo sai ƙanina ne ya karba, kuma dole muka canza wajen kiwo saboda warin da wannan
yankin keyi”.

Cikin sauri da ɓacin rai Lamiɗo yace.

“Haba Ori ya za ayi kuyi haka kuda kuke tare dani ai idan kunga makamancin abu irin wannan, sai ku
kirani ku faɗa min idan yaso in tura ƴan sanda su duba ko menene ya za ayi kuyi shiru!?”.

Cikin tsoro da cikekken gaskiya Ori ya sauƙe ajiyan zuciya tare da Girgiza kai kana yace.

“Hmmm ire-iren waɗannan abubuwan gaba ɗaya mu Fulani ma zauna daji ake ɗaurawa alhakin sa,
wanda bamusan komai ba banda Bautar Allah da kiwon dabbobin mu, amma baki ɗaya an ɗauki baƙin
jini da tsana an ɗaura mana”.
Kallonsa kawai suke zuciyarsu na tsinkewa.

Shi kuwa a hankali ya cigaba da cewa.

“Mutanen gari na cewa Fulani sune ƴan Kidnapping, to idan mun faɗi ire-iren waɗannan abubuwan sai
azo ace mu muka aikata ayi ta kamamu, shiyasa mukeyin shiru, kuma nima Aruɗe na koma gida baki
ɗaya bana cikin nutsuwa ta shiyasa”.

Cike da damuwa Malam Arɗo yace.

“Allah mai iko kai wannan zamani Allah ya rufa mana asiri”.

Kallonsa ya mayar kan Moddibo da har zuwa lokacin jikinsa ke tsuma kana tun lokacin daya runtse
Idanunsa har yanzu bai buɗe ba cikin sanyin murya Malam Arɗo yace.

“Amma Moddibo ka shirya muje wajen mu duba gawan waye!”.

Cikin sauri Moddibo ya buɗe Idanunsa dake rintse ya kallesa kana yace.

“Nikam bazan jeba Malam Arɗo me kake nufi kana nufin J ɗina ne?”.

Girgiza kai Malam Arɗo yayi tare da cewa.

“Ba haka nake nufi ba bakaji bahaushe yace idan raƙumin ka ya ɓataba ko cikin ramin allura ka duba ba
to muje mu duba mana”.

Jinjina kai Lamiɗo yayi da faɗin.

“Tabbas kam ya kamata aje aduba yanzu kuje ku faɗawa Mahaifinsa Ni kuma zan kira hukumar ƴan
sanda sai muje dasu”.

Girgiza kai Moddibo yayi tare da fesar da numfashi mai zafi kana cikin rawan murya yace.

“Nifa bazan jeba dan nasan in Sha Allah ba J ɗina bane, bakuji yace muku gawa bane kuma tuntuni ya
mutu har ya kumbura ni kuma J ɗina bai mutuba inaji Ajikina in Sha Allah yana raye”.

Dafa kafaɗar sa Malam Arɗo yayi tare da cewa.

“Moddibo kada kiɗima yasa ka furta kalmar alamar sanin gaibu”.

Cikin sauri Moddibo ya Girgiza kai kana muryarsa na rawa yace.

“Astagafirullah³ amma dai inaji Ajikina kamar J ɗina yana raye”.

Cikin sanyin murya Malam Arɗo yace.


“Eh duk da haka dai muje”.

Girgiza kai yayi tare da cewa.

“Nifa bazan jeba”.

Cikin lallashi Lamiɗo yace.

“A'a Moddibo ka daure dai kuje Allah yasa ba shiɗin bane amma dai aje aduba ɗin”.

Kai Buba ya gyaɗa kana yace.

“Eh suje su duba kuma alokacin ma na samu an ajiye wayoyi agabansa da kuma goran ruwa fuskarsa ma
bata wani kumbura ba dan kyanshi bai ɓaceba”.

Atsorace Moddibo ya kallesa zuciyarsa na bugawa da masifar ƙarfi yace.

“Harda waya kuma shikenan bari Muje mu gani ɗin?”.

Ya faɗa tare da miƙewa suka fita kai tsaye gidan Abba suka nufa kana malam Arɗo ya masa bayani.

Kallon Abba Moddibo yayi cikin raunin murya yace.

“Abba ni dai inaji Ajikina in Sha Allah ba J ɗinmu bane, amma dai tunda sunce muje to muje ɗin”.

Cikin rarrashi Malam Arɗo yace.

“Alhj kayi haƙuri muje mu gani”.

Cikin sanyi da rauni kana da tsinkewar zuciya Abba ya gyaɗa kai dai-dai lokacin da folisawan suka iso tare
da Lamiɗo.

Fita sukayi cikin shirin tafiya Abba, Lamiɗo malam Arɗo da Moddibo suka shiga mota ɗaya Ori kuma ya
shiga motar Ƴan sanda suka tafi.

Suna isa dajin bayan sunyi Parking din Motar daga can nesa, suka fara haurawa saman dutsen.

Da sauri suka fara kallon juna sabida jin wani irin ni'imtaccen ƙamshi mai sanyin shaƙa, babu wari kamar
yanda ya faɗa musu yasa Moddibo juyawa ya kalli Ori kana cikin sanyi yace.

“Ya gaba ɗaya babu warin da kace sai ma wani irin amintaccen ƙamshi”.

Kallonsa Ori yayi da faɗin.


“Toh yaufa kusan kwana takwas kenan da labarin dana baku ai dole wari ya baje dan zuwa yanzu Nasan
gawar ya fashe bare kuma ruwan sama da ake ai dole zai za gonye sai dai kuma nima nayi mamakin
wannan ƙamshi!”.

Cikin sanyi Malam Arɗo yace.

“Allah mai iko wannan wani irin ni'imtaccen ƙamshi ne a tsakiyar daji”.

Abba kuwa kasa furta komai yayi sai zuciyarsa dake bugawa da masifar ƙarfi yana jin wani irin masifaffen
tsinkewar zuciya haka zalika Moddibo suna masu shaƙar ƙamshi.

Lamiɗo da polices din kuma sai lumshe idanu suke sabida daɗin ƙamshin da Ubangijin talikai ya wadata
wurin dashi.

Yayinda suna kara haurawa suna ƙara jin ƙamshin.

Cikin tsanananin fargaba da tsinkewar zuciya suka cigaba da haurawa wajen suna gama haurawa Ori
yayi saurin cewa.

“Yawwa ga can bishiyar”.

Da sauri Moddibo ya ɗaga Idanunsa tare da kallon jikin Bishiyar ganin gawa ɗaure ajikin Bishiya yayi har
ya zagwanye idanunsa sun rarake sai ramuka kaɗai sai kuma maiƙo dake zube aƙasa da wani irin
sassayan ƙamshin dake tashi a wurin.

Cikin tsanananin tsinkewar zuciya ya sauƙe idanunsa akasa dai-dai kan ƙafar gawar dake maƙale da
takalmin cikin sauri ya runtse Idanunsa tare da dafe ƙahon zuciyarsa dake bugawa da masifar ƙarfi.

Abba kuwa da sauri ya ƙarasa jikin Bishiyar dai-dai Inda goran faron ke ajiye Idanunsa suka sauƙa akan
wayoyin dake wajen hannunsa na rawa ya ɗago wayar tare da jujjuyawa.

Cikin tsanananin tashin hankali da ruɗu yace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!”.

Juyawa yayi tare da kallon Moddibo cikin raunin murya yace.

“Aliyu wayoyin Jameelu na neeeee”.

Cikin sauri Moddibo ya juya tare da dafe saitin ƙohon zuciyarsa cikin raunin murya mai cike da tsantsar
tashin hankali yace.

“Abba wayar J kuma”.

Kai Abba ya gyaɗa yayin da wasu irin hawaye masu masifar zafi ke koro juna subabin kuncinsa murya na
rawa yace.
“Eh”, Ahankali Moddibo ya juya ta gefen da gawar ke daure tare da tsaida idanunsa akan hannun gawar
na dama da har ya bushe idanunsa ya zubawa zoben dake hannu gawar.

Cikin tsanananin kaɗuwa da wani masifaffen tsinkewar zuciya mai cike da ɗimuwa da tashin hankali
Moddibo yace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Abba kalli zobunnan hannunsa zobunnan hannun J ɗina ne da agogon”.

Ya ida maganar tare da yanke jiki ya faɗi babu numfashi atare dashi....!

Wannan littafin dai na kuɗi ne.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

32

Baya Moddibo ya koma. Suuuuuu ya faɗi a sume, cikin sauri Lamiɗo ya tarosa, ya faɗa jikinsa cike da
tashin hankali Lamiɗo yace.

“Innalillahi ya suma fa Subhanallah!”.

Cikin sauri Malam Arɗo ya ƙara sa kusa da Lamiɗo idanunsa akan Moddibo ya shiga kiran sunan sa yana
faɗin.

“Moddibo!, Moddibo!!, Moddibo!!!”.

Ina tuni Moddibo ya sume babu alamar numfashi atare dashi.

Abba kuwa kansa ya ɗaga tare da kallon fuskar skeleton M Jameel kana ya maida Idanunsa ƙasa kan
takalmin dake sanye aƙafarsa ahankali ya leƙa bayan idanunsa suka sauƙa akan guntun rigarsa da bai
gama sauƙa daga jikin skeleton ba jinjina kansa yayi cikin wata dakakkiyar murya ya juya ya kalli
Moddibo dake sume kai ya girgiza tare da sakin murmushin da yafi kuka ciwo murmushi da yafi ihu zafi,
murmushin da yafi ciwo, Ciwo murmushin da yafi raɗaɗi zafi, ya saki kana ya juya ya kalli sauran
mutanen dake tsaye sai ya kuma kalli fuskar skeleton tare da maida kallonsa kan yatsun hannunsa.

Cikin wata dakakkiyar murya me ɗauke da tarin raɗaɗi da ƙuna yace.


“Uhmmm Jameelu na ne”.

Kallonsa ya mayar kan Moddibo da har zuwa lokacin yake. Rungume a jikin Lamiɗo taune lips ɗinsa yayi
tare da cewa.

“Kai kam Aliyu kahuta, inama ace nima zan sume ko kuma in mace ma gaba ɗaya da hakan yafi min
sauƙi”.

Cikin sauri ɗaya police ɗin ya juya tare da isa gefen Abba ya riƙe sa cike da alhini da tarin tausayawa
yace.

“Alhj Bashir kayi addu'a kaji”.

Kai Abba ya gyaɗa cikin wata dakakkiyar murya yace.

_“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n lahaula wala ƙuwwata Illah billahil aliyul Azhim Hasbunallahu wani'imal
wakil Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu
Minal Zhalimin”_ sune Adduo'in da yake iya maimaitawa afili da kuma ransa.

Ori dake tsaye ciki ruɗu da tausayawa yayi saurin ƙarasawa gaban skeleton gawar M Jameel ya ɗauko
goran ruwan kana ya dawo tare da miƙawa Lamiɗo yana mai cewa.

“Lamiɗo gashi ayayyafa masa”.

Karɓa Lamiɗo yayi kana ya buɗe tare da yayyafawa Moddibo dake kwance jikinsa amma ko kaɗan
Moddibo bai motsa ba.

Kallon Buba Lamiɗo yayi kana yace.

“Ori taimaka min mu saka shi cikin Mota”.

Kai Buba ya gyaɗa.

Ɗaya daga cikin Folisawan ne yace.

“Ranka shi daɗe bari mu saka shi”.

Ya faɗa tare da kallon ɗan gidansa da Ido ya masa alamar yazo su kama Moddibo ƙarasawa yayi sannan
suka ɗauki Moddibo suka sauƙa kasan dutsen, tare da sanya shi abayan Motar Malam Arɗo.

Folisawan kuwa ƙara sawa sukayi suka shiga ɗaukar hoton gawar skeleton M Jameel.

Bayan sun gama ɗauka tare yan dube-dubensu, da Babbansu da sauran suka saka handglove suka ƙarasa
gaban gawar da niyyar sunjanye gawar Babbansun najan Igiyar da aka ɗauɗaureshi ƙasusuwan suka
kakkarye tare da zubewa a ƙasa babu ta yanda zasu iya daukarsa Babban su ya umarci Coustable yaje ya
ɗauko musu kwali abayan mota kana suka tattara gawar suka zuba acikin kwalin kana suka kwashe
takalmansa da wayoyinsa suka saka awata leda.

Abba kuwa cikin wani irin yanayi ya nufi cikin jejin yana tafiya ba tare da shi kansa yasan inda ya nufaba.

Cikin sauri Lamiɗo ya nufesa tare da riƙe hannunsa cike da tausayawa yace.

“Alhj banan zamu bi ba can baya ne, hanyar kazo innu na maka hanyar da zamu bi”.

Kai Abba ya gyaɗa tare da bin bayan Lamiɗo baki ɗaya baya cikin nutsuwarsa ya kasa gane shin mafarki
yake ko kuma azahirance komai ke faruwa.

Bayan sun isa Lamiɗo da kansa ya buɗe masa mota yashiga sannan shima yashiga.

Folisawan kuwa kwalin da gawar M Jameel ke ciki suka ɗauka tare da sawa abayan motarsu suka tafi
gida.

Abba kuwa kallon hanya kawai yake baki ɗaya baya cikin hayyacinsa ganin yanayin da yake ciki ne yasa
Malam Arɗo ya fara yi masa Adduo'i yana tofa masa kana yana faɗa afili.

Ahankali Abba ya fara sakin Ajiyar zuciya kana yashiga maimaita Adduo'in sannu Ahankali ya fara jin
hankalinsa ya fara dawowa jikinsa.

Motar da Moddibo ke ciki Ori da police ɗaya ne aciki direct Asibiti suka nufa dashi.

Yayin da Motar dasu Abba da kuma gawar M Jameel ke ciki kai tsaye gida suka wuce, suna isa kai tsaye
falonsa suka wuce police ɗin ne ya ɗauko kwalin Gawar M Jameel ya shigo dashi kana ya ajiye agabansu.

Hajiya Turai dake sashenta tana jin tsayuwar motoci ta fito zuwa falon Abba.

Ganin Abba zaune tare dasu Lamiɗo yasa ta nufi gefen Abba cikin yanayin damuwa tace.

“Alhj lafiya ya ake ciki Gawar waye kuka samu?”.

Ahankali ya ɗago Idanunsa da suka kaɗa sukayi jawur ya kalleta kana yayi ƙasa da kansa cikin raunin
murya yace.

“Gawar Jameelu na ne!”.

Arazane Hajiya Turai ta kallesa zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi Idanunta akansa tace.

“Gawar Jameelu kuma!?”.

Kai ya gyaɗa mata Cikin tsananin tashin hankali da ruɗu ta fashe da kuka me tsuma zuciya tana furta.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ina gawar yake?”.


Da hannu ya nuna mata kwalin dake gabansa.

Da kallo tabi kwalin cikin sauri ta sake Kallonsa Idanunta cike da ruwan hawaye tace.

“Gawar Jameelu ne acikin kwali haka?”.

Kai ya gyaɗa batare daya ɗago kaiba yace.

“Shine”.

Wani sabon kuka ta fashe dashi tana Girgiza kai Kukanta ne ya fito da Hajiya Karima itama ganin abinda
ke faruwa yasa ta fashe da kuka.

Acan Asibiti kuwa ana kai Moddibo likitoci suka shiga bashi temakon Gaggawa saidai koda wasa bai
farfaɗo ba ganin haka yasa suka dauƙo wani na'ura mai kama da Iron akafara danna masa aƙirji.

Amman ina babu alamun zai motsa, sosai likitocin suka dugufa wurin ganin sun cetoshi, a karo na biyu
suka kuma danna mishi a ƙirjunshi, amman ina, Dr Lukman ne ya karɓi aikin tare da goggoga jikin na'urar
ya manna masa a kirjinsa da ƙarfi.

Cikin ikon Allah yaja wani dogon numfashin sake dannawa yayi da karfi wani irin maraitaccen numfashi
ya sake ja amma still bai farfaɗo ba sake dannawa sukayi akaro na biyar ne yaja wani dogon numfashi
tare da buɗe idanunsa kana yace.

“Jyyyyyyy”.

Malam Arɗo da bai daɗe da dawowa daga gidan Abba bane, yayi saurin riƙe hannunsa tare da cewa.

“Moddibo kayi addu'a”.

Duk da cewa baya Cikin nutsuwarsa hakan bai hanashi maimaita duk wata addu'a da tazo bakinsa ba
ahankali ya ɗago kansa tare da kallon Malam Arɗo yace.

“Malam J ɗina nefa!”.

Jinjina kai Malam Arɗo yayi cike da tausayawa yace.

“Eh shine Moddibo Allah ya karɓi Jameelu muyi masa addu'a Allah ya karɓi shahadarsa”.

Girgiza kai Moddibo yayi tare da cije lips ɗin sa duka biyu, kana ya runtse Idanunsa cikin wani irin yanayi
mai wuya yace.

“Malam Arɗo mutuwar azaba suka masafa, ɗaure sa sukayi suka ajiye masa goran ruwan agabansa ta
yanda yana ji yana gani bashi da damar sha sun barshi da azabar ƙishi”.

Kallonsa Malam Arɗo keyi cike da tausayawa yana ganin yanda zuciyarsa ke bugawa da ƙarfi.
Cikin wata raunan'niyar murya Moddibo ya cigaba da cewa.

“Malam ɗaure sa sukayi suka ajiye masa wayoyinsa agabansa ta yanda yana kallon muna kiransa bashi
da damar ɗauka bare yace mukawo masa ɗauki”.

Sai kuma ya rintse idanunsa da masifan ƙarfi zuciyarsa na cigaba da buguwa da masifaffen ƙarfi kana
yace.

“Ɗaure sa sukayi ta yanda yana ganin ga hanyar tsira sai dai bashi da damar kiran wani ya kawo masa
ɗauki ɗaure sa fa sukayi ta yanda yana ganin kiran mu amma bashi da damar ɗauka”.

Jujjuya kansa ya farayi kamar zautacce hawaye na bin gefe da gefen idanunsa har suna shiga kunnensa
cikin Muryan kuka yace.

“Ɗauresa fa sukayi ta yanda yana ganin kiran Abbansa bashi da damar ɗauka,Mutuwar azaba da raɗaɗi
suka masa da ƙishi fa suka kasheshi”.

Kasa ƙarasa maganar yayi kawai ya fashe da matsanancin kuka mai tafiya da numfashi Atake
numfashinsa ya ɗauke ya sake sumewa!.

Cikin sauri Malam Arɗo ya miƙe tare da kiran likitoci kana ya sanar dasu ya sake suma taruwa likitocin
sukayi akansa kana suka shiga bashi temakon Gaggawa da kyar da temakon Allah suka samu ya farfaɗo
ganin ya farfaɗo yasa Dr ya masa Alluran bacci Atake baccin wahala ya ɗauke sa.

Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe tare da miƙewa ya fita kana yayi dearling number Lamiɗo yana ɗauka
yace.

“Ranka shi daɗe yaron nan fa gashi agigice yake baki ɗaya da zaran ya farfaɗo sunan Marigayi Jameelu
yake kira, yana kiran sunan kuma zai sake suma!”.

Acan gidan Abba kuwa zaune yake afalonsa hannunsa riƙe da waya tunda suka dawo yake zaune awajen
ya kasa koda motsawa se kwalin Gawar Jameelu daya zubawa Ido yana jujjuya wayar hannunsa ajiyar
zuciya ya sauƙe tare da kiran number Ummi Yana Jin tayi picking ya fesar da numfashi kana yace.

“Fatima”.

Cike da mamaki Ummi tace.

“Abban Jameel”. Jin muryansa.

Cikin raunin murya ya sake cewa.

“Fatima”.
Anutse Ummi ta amsa da.

“Na'am”.

Runtse Idanunsa yayi kana yasake cewa.

“Fatima”.

Cikin dakiya Ummi da taji zuciyarta ya tsinke da Masifar ƙarfi tace.

“Na'am Abban Jameel ka faɗa min me yasamu Jameelu na sun kira ne ko kuma yaya!?”.

Cikin rauni yace.

“Hmmm”.

ya faɗa tare da katse kiran kana ya fito da Number Malam Ahmad.

Malam Ahmad na ɗagawa Abba yace.

“Malam kazo da Fatima da yaranta!?”.

Cikin tsinkewar zuciya Malam Ahmad dake Bedroom ɗinsa ya miƙe tare da cewa.

“Meya faru Alhj Bashir ka faɗa min”.

Girgiza kai Abba yayi tare da taune lips ɗinsa kana yace.

“Ga gawar Jameelu na agabana”.

Cikin tsanananin tashin hankali Malam Ahmad ya dafe bango tare da faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha”.

Katse kiran Abba yayi cikin sauri ya fito falon tsaye ya samu Ummi riƙe da waya a hannunta cikin ƙoƙarin
ɓoye tashin hankalin sa yace.

“Fatima Lafiya!?”.

Ahankali Ummi ta juya ta kallesa tare da cewa.

“Yan zun nan Abban Jameel ya kirani, to kuma ya yanke gashi kuma ina ta sake kira naji line Busy”.

Da ƙyar ya haɗiye wani abu mai masifar ɗaci kana cikin ƙoƙarin ɓoye damuwarsa yace.

“Toh kada ki damu kizo muje muji meke faruwa”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.


“Toh”.

Sannan ta nufi hanyar fita.

Kallon Bashir da Asma'u dake tsaye yayi kana yace.

“Kuma kuzo mu tafi”.

Kai suka gyaɗa kana suka bi bayansa suka fita.

Suna isa falon suka samu Hajiya Turai da Hajiya Karima da ƴaƴan Hajiya Karima na kuka cikin sauri Ummi
ta ƙara sa shiga falon tare da tsayawa agaban Abba kana tace.

“Abban Jameel meye faru?”.

Ahankali ya ɗago ido ya kalleta, sai alokacin yaji kuka ya kufce masa ganin Ummi agabansa baki ɗaya ta
gigice jikinta na rawa.

Cikin rawan murya tace.

“Abban Jameel meyafaru!?”.

Kasa cewa komai Abba yayi sai kuka da yake tamkar ƙaramin yaro.

Da sauri Ummi ta juya tare da kallon yanda su Hajiya Turai ke kuka cikin rawan murya da yanayin tashin
hankali tace.

“Ku faɗa min mana meke faruwa!?”.

Tayi tambayar baki ɗaya ilahirin jikinta na rawa.

Asma'u da Bashir dake tsaye Atare suka fashe da matsanancin kuka ganin yanda ƙannen M Jameel ke
kuka.

Ahankali Malam Ahmad ya matso kusa da Ummi tare da cewa.

“Fatima ki zauna”.

Girgiza kai tayi kana tace.

“Ni bazan zauna ba kafaɗa min abinda ke faruwa”.

Cikin sanyin murya Lamiɗo yace.

“Maman Jameel kiyi haƙuri ki zauna”.

Kallon sa tayi tare da cewa.


“In zauna?”.

Kai ya gyaɗa mata kana yace.

“Eh”.

Cike da tausayawa Malam Ahmad ya janyo hannunta tare da zaunar da ita.

Abba kuwa kallonta yayi cikin tsanananin fargaba da tashin hankali yace.

“Fatima”.

Cikin rawan murya da raunin zuciya tace.

“Na'am Alhj Bashir”.

Cikin sauri Abba ya kalleta wannan shine karo na farko arayuwar sa da yaji ta kira sunan shi kai tsaye.

Jinjina kai tayi Idanunta tsaye akansa tace.

“Eh Alhj Bashir ka faɗa min menene? kafaɗa meke faruwa”.

Rintse idanunsa yayi yana jin kansa na sarawa Araunane yace.

“Fatima Jameelun mu”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Eh nasani akan Jameelu ne to Menene ya faru?”.

Kasa cewa komai Abba yayi kawai sai ya fashe da matsanancin kuka yayin da hawaye ke bin kuncinsa
Shar-shar-shar.

Cikin raunin murya yace.

“Fatima ga Gawar Jameelun mu”.

Atake maganar ya daki dodon kunnenta kana ya ratsa ƙwaƙwalwar ta zuwa zuciyarta saurin kallon Abba
tayi tare da sakin Murmushi kana ta juya tare da kallon su Hajiya Karima dake kuka cikin wata dakakkiyar
murya mai cike da ƙuna tace.

“Toh kukan me kukeyi!?,

Juyawa tayi tare da kallon Abban M Jameel kana tace.


“Har kaima kuka kakeyi!?Haba Alhj Bashir Addu'a ya kamata ka masa amma ba kuka ba!, Su mata suyi
kuka kaina kayi Yanzu ina yake?”.

Cikin sheshsheƙan Kuka Abba ya nuna mata kwalin da ya tsarsa kana yace.

“Gashi can”.

Saurin Kallon wajen tayi Zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi still Muryanta adake da wani irin bushewa
da hurawar zuciya tace.

“Gawar ne kuma acikin kwali”.

Cikin wata raunan'niyar murya ya Girgiza kai kana yace.

“Kiyi haƙuri kiyi ta maimaita Addu'a”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da rintse Idanunta kana tace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin La'ilaha Illah anta subhanaka inni kuntu
Minal Zhalimin Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha³”.

Ahankali ta gyara zamanta tare da naɗe ƙafafunta tare da sakin murmushi kana ta fuskanci gabas yayin
da Idanunta suka kaɗa sukayi jawur jikinta na wani irin tsuma na tsananin tashin hankali cikin raunin
murya tace.

“Ya Allah kaine ka bani Jameelu, kai kasa ya zamemini Garkuwa, ya Allah kajiƙan sa da rahma, ya Allah
kasa ya huta Alfarman Annabi da Alkur'ani, Allah kayi mana SAKAYYAH akan dukkan waɗanda suka cutar
damu ya Allah kayi mana SAKAYYAH”.

Kusan a haɗe baki daya mutanen falon suka amsa da Ameen.

Wani irin kuka mai tsuma zuciya ne ya kufcewa Asma'u da Bashir musamman Asma'u numfashinta har
fisga yake baki ɗaya Falon kaurewa yayi da koke cikin rawan murya Ummi tace.

“Ina gawar yanzu Jameelu na ne haka acikin kwali?”.

Jinjina mata kai Abba yayi tare da cewa.

“Eh shine”.

Still Muryanta adake tace.

“Wani irin mutuwa yayi da har gawarsa zata ƙankace ya zauma acikin kwali”.

Asp dake tsaye ya kalli Ummi cike da tausayawa yace.


“Hajiya kiyi haƙuri ya riga daya bushe, shiyasa ana taɓa shi ya kakkarye!”.

Ahankali ta juya ta kalli Asp kana tace.

“Toh ya akayi kuka tabbatar Jameelu na ne?”.

Cike da tausayawa Asp ya ƙara sa gaban Kwalin kana ya buɗe mata ahankali Ummi ta tsirawa jerarrun
gabɓan gawar dake cikin kwalin ido ahankali ta sauƙe Idanunta akan zara-zaran yatsun, hannunsa da
suka bushe kana ta tsirawa zoben hannunsa ido.

Cikin wani irin yanayi na ƙunan zuciya da sadaukarwa tace.

“Hmmm!”.

Ahankali Asp ya sake nuna mata takalmin M Jameel dake cikin leda da kuma wayoyinsa cikin sanyin
murya yace.

“Ga takalmansa da kuma wayoyinsa duk agabansa muka samu sun ajiye masa da goran ruwa.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana tace.

“Tabbas Jameelu na ne”.

Ahankali ta matsa jikin kwalin sosai tare da sanya tafin hannunta ta rufe kana ta sunkuyar da kanta akan
kwalin cikin Muryan ta daya fara karaya tace.

“Babana bazan yi maka kuka ba, sannan baza zubar maka da hawaye ba, kana bazan yi maka Ihu da
kururuwa ba, amma zan ƙarashe baki ɗaya sauran rayuwata ina maka addu'a, zan ƙare rayuwata da
ƙunan rashinka zan ƙare rayuwata babban giɓin rashinka”.

Wani irin tausayinta ya ratsa baki ɗaya jama'ar dake falon ahankali Malam Ahmad da Lamiɗo suka sanya
hannu tare da share hawayen da suka saƙƙo musu.

Cike da rauni Ummi ta cigaba da cewa.

“Babana zan ƙare baki ɗaya sauran rayuwata ina maka addu'ar Ubangiji ya karbi shahadarka Allah ya
maka SAKAYYAH tun daga nan duniya akan wa anda suka zalince ka har zuwa ranar tashin Alkiyama.
Allah Ubangiji yajiƙan ka da rahma Allah ya gafarta maka yasa kahuta”.

Cikin sauri Hajiya Turai ta ƙarasa kusa da ita tare da Rungumeta ajikinta kana cikin Muryan kuka tace.

“Kiyi haƙuri Hajiya Fatima kiyi shiru”.


Kallonta Ummi tayi still Muryanta adake tace.

“Idan banyi haƙuri ba Hajiya Turai ya zanyi. Ubangijin daya ɗauke Jameelu shi yabani shi kuma shi ya
ɗauke sa kana ya fini sanin wanene Jameelu agareni, sannan ya fini sanin Jameelu Allah ya masa rahma”.

Ta ida maganar tare da janye Jikinta daga na Hajiya Turai tare da juyawa ta kalli Abba kana tace.

“Ina Moddibo!?”.

Tana gama fadar haka tayi baya tare da sumewa.

Cikin sauri Hajiya Karima ta mike tare da ɗauko ruwa ta yayyafa mata dogon numfashi Ummi taja tare da
buɗe Idanunta kana tace.

“Ina Moddibo yake?”.

Cike da tausayawa Abba yace.

“Moddibo yana asibiti asume tunda abin ya faru daya farfaɗo idan ya kira sunan Jameel zai sake
sumewa, yanzu ne da aka samu ya farfaɗo aka masa Alluran bacci”.

Araunane tace.

“Ku kaini inga Moddibo sannan kada aje abinne Jameelu abari sai Moddibo ya farfaɗo yaga J ɗinsa na
ƙarshe ya tabbatar cewa J dinsa tafi ya barsa bari na har abada, idan yaga haka zai dangana ya sawa
ransa haƙuri amma yanzu dan Allah ku kaini wajen Moddibo”.

Abba ne yace.

“Yanzu zaki tafi can?”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh ku kaini wajensa”.

Ahankali Malam Ahmad ya miƙe tare da riƙe hannunta suka tafi.

Asma'u da Bashir kuwa kuka suka sake fashewa dashi har muryarsu baya fita saboda tsananin tashin
hankali.

Rintse Idanu Abba yayi cike da tausayawa ya kallesu kana yace.

“Ku daina kukan nan kuyi masa addu'a babu abinda Jameelu ke buƙata awajenmu yanzu kamar addu'a.
Acan asibiti kuwa Ummi da Malam Ahmad na isa a reception suka samu Malam Arɗo tsaye ganinsu yasa
ya ƙara sa kusa dasu kana yace.

“Maman Jameelu kiyi haƙuri. Ubangiji Allah ya jikansa da rahma Allah ya gafarta masa Ubangiji ya amshi
shahadarsa”.

Cikin sanyin murya tace.

“Ameen Malam Arɗo ina Moddibo?”.

Ahankali ya gyara tsayuwar sa kana yace.

“Gashi can yana ciki”.Ya faɗa tare da shiga gaba Ummi da Malam Ahmad na biye dashi.

Suna shiga ɗakin Ummi ta zubawa Moddibo idanu dake kwance plat Fuskarsa tayi fayau duk da bacci
yake amma tashin hankali da fargaba ne kwance asaman fuskarsa.

Ahankali ta riƙe hannunsa acikin nata kana tace.

“Moddibo munyi rashi, rashin da baza mu maimaita gurbinsa ba, munyi rashi rashin da har abada ba
zamu mance shiba, munyi rashi rashin da saidai namu mutuwar ne zai mantar mana dashi”.

Moddibo kuwa duk da Alluran baccin dake jikinsa hakan bai hana shi jiyo sautin muryan Ummi ba. So
yake ya farka domin kunnuwansa na sauraronta haka zalika yana iya motsa gaɓɓansa sai dai koda ya
buɗe idanunsa baya ganin komai cikin wani irin yanayi ya damƙe hannun Ummi acikin nasa, yayinda
zuciyarsa ke cigaba da bugawa da masifar ƙarfi.

Kallon Malam Ahmad Malam Arɗo yayi kana yace.

“Toh tunda kunzo bari na wuce na faɗawa Kakarsa halin da ake ciki”.

Jinjina kai Malam Ahmad yayi tare da cewa.

“Ya kamata kam aje afaɗa mata sannan itama ataho da ita”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana ya juya ya fita kai tsaye gidan su Moddibo ya nufa yana isa yayi Parking
ɗin motarsa kana ya shiga gate din farko ya daga sautin muryarsa tare da yin sallama.

Cikin sauri Innayi ta fito ganinsa yasa ta saki Ajiyar zuciya tare da cewa.

“Alhamdulillah dama yanzu nake tunanin in kira ka dan. Moddibo tun safe daya fita bai dawo ba, duk da
cewa dama yanzu bai cika dawowa da wuri ba”.

Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe kana yace.

“Ki zo mutafi”.
Saurin Kallonsa tayi kana tace.

“Ina zamuje”.

Cikin sanyin Murya Malam Arɗo yace.

“Wajen Moddibo zamuje yana asibiti”.

Da sauri ta dafe ƙirjinta sai kuma ta juya ta nufi cikin gida hijabinta ta ɗauko ta sanya kana ta rurrufe
kofofin gidan kafin ta fita.

Bayan sun fara tafiya acikin motar Malam Arɗo ya kalli Innayi kana yace.

“An samo gawar Jameelu fa!”.

Cikin tsanananin ruɗu da tashin hankali ta dafe ƙirjinta tare da faɗin.

“Gawar Jameelu kuma?”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace.

“Eh gawar Jameelu aka samu sun kashe sa”.

Atake hawaye suka shiga zubowa Innayi cikin tashin hankali da jimami ta saki sassayan kuka tare da
addu'o'i.

A dai daren wannan ranar haka kowa ya kwana cikin ƙunci da raɗaɗi azuciya.

Asp da tawagarsa sun koma gida bayan sun gama dukkan abinda ya dace na bincikensu, haka zalika
Lamiɗo ma ya koma gida Abba kuwa kwana yayi da gawar Jameelun sa agabansa batare daya rintsa ba.

Asma'u kuwa Hajiya Turai ta jata zuwa ɗakinta Anan ta kwana duk da cewa ba tayi bacci ba.

Bashir kuwa aɗakin ƙannen M Jameel ya kwana tare dasu Aɓangaren Moddibo kuwa haka ya kwana
cikin wani irin yanayi shi ba bacci ba kuma kuma shiba Ido biyu ba ba kuma a sumeba.

Ana kiran Assalatun Farko acikin kunnen Moddibo sannu Ahankali ya fara bude idanunsa da yaji sunyi
masifar nauyi har ya sauƙesu akan Ummi dake riƙe da hannunsa Idanunta abushe alamar ko rintsawa ba
tayi ba bare kuma bacci.

Cikin wata murya mai cike da karaya da kuma rauni yace.

“Ummi”.

Kallonsa Ummi tayi tare da faɗin.


“Na'am Aliyu”.

Girgiza kai yayi yayinda zuciyarsa ke cigaba da bugawa da masifar ƙarfi yace.

“Ummi J ɗina”.

Cike da tausayawa ta rintse Idanunta kana tace.

“Aliyu kayi haƙuri”.

Cije Lips ɗinsa yayi tare da damƙe hannunta acikin nasa kana yace.

“Ummi J ɗina”.

Jinjina kai tayi tare da sauƙe ajiyar zuciya tace.

“Kayi haƙuri kaje kayi sallah duk abinda kake ji Aranka kana so ka faɗa min ka faɗawa Ubangiji”.

Cikin sauri Malam Ahmad dake tsaye ya ƙara so bakin gadon tare da riƙe hannun Moddibo cikin sanyin
murya yace.

“Kayi haƙuri kaje kayi alwala”.

Kallon Malam Ahmad Ummi tayi kana tace.

“Toh ni yanzu zan tafi gida”.

Girgiza kai Malam Ahmad yayi tare da cewa.

“A'a ki bari mu tafi gidan Alhj Bashir yanzu”.

Girgiza kai tayi kana tace.

“A'a mu tafi gidanmu dai”.

Girgiza mata kai yayi kana yace.

“A'a gidan Alhj Bashir zamu je acan fa za ayi jana'izar mu tafi can ɗin!”.

Shiru kawai Ummi tayi ahankali.

Moddibo da har yanzu hannunsa ke cikin nata yace.

“A'a Ummi dan Allah muje gidan Abba”.

Kai ta gyaɗa masa cikin sanyi tace.


“Toh shikenan”.

Batare da an sallamesu ba suka fita Moddibo da Malam Ahmad suka shiga gaba Ummi tashiga baya
Anutse Malam Ahmad yayiwa motar key kana yaja suka bar Asibitin kai tsaye gidan Abba suka nufa suna
isa Malam Ahmad ya danna hong ta cikin ƙaramin ɓulin. Mai gadi ya leƙa jin ana ta danna hong ganin
motar da tazo jiya da safe ne yasa ya koma cikin gida tare da sanarwar Abba yaga motar da jiya tazo
yauma ta dawo.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“Eh kaje ka buɗe musu Maman Jameel ne yanzu aka sallame su daga asibiti kaje ka buɗe musu”.

Kai ya gyaɗa sannan ya buɗe musu gate din suka shiga bayan Malam Ahmad yayi Parking suka fito kai
tsaye falon Abba suka shiga.

Zaune suka samesa shi kaɗai a falon hannunsa riƙe da Carbi ya tsirawa kwalin Gawar Jameel Ido.

Ahankali Ummi ta ƙarasa tare da zama agefen kwalin shima Moddibo zama yayi agefen kwalin Malam
Ahmad ma ya zauna agefen kwalin sai ya zamana sun saka kwalin Atsakiyar su.

Moddibo kuwa kallon kwalin yayi kana ya kalli Ummi cikin raunin murya yace.

“Ummi yanzu J ɗinane aciki?.

Ummi da gaske J ɗina ne ya rasu!?”.

Kai Ummi ta jinjina kana tace.

“Da gaskene Moddibo, tabbas Jameelu ne yarasu Jameelu ya tafi yabar mu bari na har abada, ba zamu
sake ganinsa ko jin sautin muryarsa ba sai dai ahoto”.

Girgiza kai Moddibo yayi tare da ɗaura kansa akan kwalin ya fashe da wani irin kuka me tsuma zuciya
cikin sheshsheƙan Kuka yace.

“Yanzu shikenan J ɗina mun rabu har abada bayan yana burin yin Aure ya zauna gida ɗaya da Ummi da
ƙannensa yanzu shikenan wannan burin ya tafi”.

Ya sake Rungume Kwalin tare da cewa.

“Yanzu shikenan J ya tafi ya barni shin dawa zan rayu duk wani farin ciki ne da walwala na J ɗina ne shin
waye zai fahimcini a duniya? J ɗina ne kaɗai yake iya fuskarta halin da nake ciki shikenan sun rabani da
aminina kuma farin cikina!”.

Wani irin tausayinsa ne ke ratsasu Abba kam kasa daure wa yayi ya sunkuyar da kansa ƙasa hawaye na
zuba.
Cikin sheshsheƙa Moddibo ya ɗago kansa tare da kallon Ummi idanunsa cike da ruwan hawaye yace.

“Shikenan Ummu sunyi mai kisan gillah, sun hanashi shan ruwa, ya mutu da kishi da begenmu, yana
ganin muna kiransa amma bashida damar ɗauka, Ummi ashe duk kiran da mukewa J yana kallon kiran
mu!”.

Sai kuma ya kife kansa akan kwalin hawayen sa na sauka akai yace.

“Ummi J yana ganin kiran mu amma bazai iya ɗagawa ba Ummi sun azabtar da J ya mutu da tsananin
begenmu da muradin son kasancewa damu Ummi sun cutar da J mutumin da koda ƙwaro baya iya
cutarwa bare bil adam shin wani irin zunubi suka aikata!”.

Jin ankira assalatu yasa Malam Ahmad sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.

“Moddibo kayi haƙuri ku tashi muyi alwala mu tafi masallaci”.

Ahankali Moddibo ya ɗago kansa akan kwalin daya jiƙe da hawayensa cikin ransa yace shikenan J ya tafi
yabarni bari na har abada shikenan ni kaɗai zan rayu.

Hajiya Turai ce ta shigo falon tare da jan Ummi suka tafi ɗakinta Anan sukayi sallah.

Dole Gawar M Jameel yanda ya kasance a kakkarye ahaka aka yayyafa masa ruwa madadin wonkan kana
aka kaisa makwancinsa na gaskiya.

Jana'izar data samu halarta ɗumbin jama'ar domin kafin gari ya waye mutuwar ta zagaye cikin
Gembulan da kewayenta har Taraba Yola da dai sauransu.

Rayuwa tayiwa duk wani makusancin M Jameel ƙunci da zafi musamman Ummi, Abba, Moddibo,
Asma'u, Bashir daga Jiya zuwa yau sunyi wani masifaffen ramewa kallo ɗaya zaka musu kasan cewa suna
cikin tsananin ƙuncin rayuwa musamman Moddibo baki daya ya fita cikin hayyacinsa duk ya gigice ya
sake zama wani shiru.

Misalin ƙarfe biyu na rana bayan andawo daga sallar jana'izar M Jameel Lamiɗo ya koma gidansa kai
tsaye falon Mommy ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama.

Anutse Mommy da Khausar dake zaune suka amsa masa Sallamar.

Cike da kulawa Mommy tace.

“Sannu da zuwa yinin yau duk baka nan sau biyu ina zuwa sashenka”.
Zama yayi akan 3sitter tare da sauƙe ajiyar zuciya kana ya jingina bayansa da jikin kushin ɗin tare da
lumshe idanunsa kana yace.

“Eh yanzu na dawo daga jana'iza”.

Cikin sauri ta kallesa tare da cewa.

“Jana'iza kuma?”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.

“Eh”.

Gyara zama tayi tare da faɗin.

“Janaizar waye!?”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da dafe kansa kana yace.

“Janaizar Jameelu”.

Cikin sauri Khausar ta dafe ƙirjinta tare da kallon Lamiɗo kana tace.

“Abbah waye”.

Kallonta Lamiɗo yayi kana yace.

“Malam Jameelu”.

Cikin tashin hankali Mommy tace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Jameelu Yayan Asma'u”.

Kai Lamiɗo ya gyaɗa kana yace.

“Eh shi ɗin dai Allah ya masa rasuwa”.

Cike da kaɗuwa tace.

“Innalillahi Ayyah Ummin Asma'u Allahu Akbar duniya yanzu yaron nan kashesa sukayi”.

Khausar kuwa tunda ta dafe hannunta aƙirji ta kasa koda ƙokƙwaran motsi ne wani irin bugawa da
masifaffen ƙarfi zuciyarta keyi.

Atake wani irin kuka mai tsuma zuciya ya kufce mata cikin sheshsheƙan kuka mai cike da tausayi da
tashin hankali tace.
“Abba Yaya Jameel ya rasu!? Abba kashe Yah Jameel sukayi? Abba me yayi musu da zasu kashesa, suka
rabasa da rayuwarsa”.

Kai ya gyaɗa mata kana yace.

“Eh Khausar sun kashesa kisa mafi ciwo".

Sau kuma ya zayyane musu yanda suka samu labarin har suka je wajen da kuma yanda suka samu gawar.

Cike da tausayawa Khausar ke jujjuya kai tana cigaba da kuka yayinda numfashinta ke sarƙewa.

Kallon Mommy da hawaye ke kwaranya daga idanunta Lamiɗo yayi kana yace.

“Tun jiya ne, ai muka samu gasar, ban dai faɗa muku bane, dan kada in hanaku bacci.

Yanzu ku shirya anjima idan anyi Sallar La'asar zan kaiku gidan kuyi musu ta'aziyya”.

Cikin muryan kuka Mommy ta gyaɗa masa kai cike da rauni tace.

“Ayyah Ummin Jameel ta ɗandani mutuwa me raɗaɗi da ƙunan zuciya”.

Ta faɗa tana tuno Ramadan domin ko Rasuwar Ramadan bata samu tayi kuka haka ba bayan Lamiɗo ya
sake rarrashin sune ya miƙe ya nufi sashen Hajiya Bunayya ya sanar mata.

Khausar kuwa Kuka takeyi tamkar zata mace.

Bayan anyi sallar La'asar Lamiɗo ya ɗebe su suka tafi gidan Abba.

Suna zuwa falon Hajiya Turai suka nufa Cikin gidan da falon cike yake da mutane ƴan ta'aziyya duk
wanda yaji rasuwar M Jameel da kuma yanda aka samu gawarsa saiya zubda hawaye tare da la'antar wa
anda suka aikata masa haka.

Asma'u dake gefen Ummi zaune Idanunta cike da hawaye tana ganin Khausar ta fashe da sabon kuka
kana ta miƙa mata hannu cikin sauri Khausar ta kamo hannunta tare da zama gefenta ta.

Rungume juna sukay tare da fashewa da wani irin kuka mai tsuma zuciya.

Mommy da Hajiya Bunayya kuwa kusa da Ummi suka zauna.

Mommy na Kallon Ummi taji wasu sabbin hawaye sun zubo mata cike da tausayawa Mommy tace.
“Ummi Sannu”.

Sunkuyar da kai Ummi tayi cike da dauriya tace.

“Toh ya zamuyi Aysha ya zamuyi da hukuncin Ubangiji.

Jameelu ya riga mu gidan gaskiya ya tafi ya barni da gurbin da bansan ya zai cikeminba”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.

“Kiyi haƙuri Ummi”.

Kasa ƙara sawa tayi sabida kuka yaci ƙarfin ta kawai saita kife kanta gefen Ummi ta shiga rera kuka.

Ajiyar zuciyar Ummi ta sauƙe cikin sanyin murya me ɗauke da ƙuna tace.

“Kiyi haƙuri Aysha haka Ubangiji ya tsara bamu isa muja da lamarinsa ba addu'ar mu suke buƙata muyi
musu addu'a Allah ya gafarta musu”.

Cikin sheshsheƙa Mommy tace.

“Ameen”.

Ahankali Mommy ta juya suka gaisa da Hajiya Turai da Hajiya Karima sannan da ƙannen Abban Jameel
Hajiya Maryam da Hajiya Fa'iza suka yi musu ta'aziyya.

Khausar dake Rungume da Asma'u cikin Muryan kuka tace.

“Asma'u yanzu da gaske Yah Jameel ya rasu shikenan ya tafi ya barmu!”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa.

“Da gaske Khausar Yah Jameel ya rasu shikenan gatanmu ya rasu rufin asirin mu ya tafi garkuwan mu ya
barmu Inuwarmu wajen fakewar mu ya gushe, bangon da muke jingina muji daɗi ya fadi ƙasa”.

Kasa ƙara sawa tayi kawai ta fashe da kuka me tsuma zuciya.

Cikin sauri Ummi ta girgiza mata kai Araunane tace.

“Kul Asma'u!,Kada ki faɗi haka kada kiyi butulci ga Ubangiji domin shi ya bamu Jameelu kuma shi ya
ɗauke mana shi kuma zai jibanci laluranmu muddin mukayi tawakkali”.

Innayi dake gefe ta matso kusa da Asma'u da Khausar ta janyosu jikinta tare da ɗaura kansu akan
cinyarta cikin Muryan rarrashi tace.

“Kuyi haƙuri kuyi masa addu'a”.


Ahankali Khausar ta ɗago tare da kallon Innayi kana tace.

“Innayi yanzu shikenan Yah Jameel ya tafi ya barmu har abada baza ku sake ganinsa ba!? Bazai sakeyi
mana nasihaba, bazai sake neman al'farma a wajenaba ashe Yah Jameel Wasiyya yayi ta barmin a
wancar ranar”.

Shafa kanta Innayi tayi kana tace.

“Khausar kada kiyi kuka muyi masa addu'a shine abinda yake buƙata awajenmu kana mu cika masa
dukkan wasiyar daya bar mana”.

Kai Khausar ta gyaɗa kana ta cigaba da kuka mai ciwo har Idanunta suka kumbura.

Sai Bayan sun idar da Sallar Maghariba kafin Lamiɗo ya ɗebe su suka tafi

A wannan daren ranar baki ɗaya haka suka kwana cikin ƙunci zuciya da alhini Moddibo kuwa baya um
bare Um-um ko awajen zaman makoki idan akace masa sannu baya magana saidai kallo sai ance Allah ya
jikansa kafin yace.

“Ameen ya Allah Nagode”. Iya abinda yake iya faɗi kenan.

Haka rayuwa tayi musu ƙunci da ɗaci haka aka ɗauki tsawon kwanaki bakwai ana zaman makoki har
awannan kwanaki kullum cikin gida da waje a cike yake da masu zuwa ta'aziyya.

Washe garin rana ta takwas da safe Moddibo na fita bai nufi ko ina ba sai gidan Ummi bakinsa ɗauke da
Sallama yashiga falon zaune ya sameta hannunta riƙe da carbi ta zubawa waje ɗaya ido.

Jin Sallamar sane yasa ta ɗago kanta tare da tsira masa Ido agefenta ya zauna.

Cikin sanyi tace.

“Babana”.

Ahankali yace.

“Na'am Ummi”.

Cike da tausayawa Ummi tace.

“Babana kalli yanda ka sake dawowa fa yaushe zaka sawa ranka dangana ne? Kadafa muyi abinda Allah
bayaso”.

Batare da yace Uffan ba yayi ƙasa da kansa yana jin wani irin zafi azuciyarsa.

Jin muryarsa yasa Asma'u dake Bedroom ta fito tare da zama agefensa kana ta gaishesa.
Ahankali Moddibo ya juya ya kalli Ummi kana yace.

“Ummi yanzu a Duniya babu abinda nake buri daya wuce ingano su waye suka sace J sannan suka yi
masa kisan gillah ina so insani. Ummi inaso inyi bincike akai ina so inga lallai a hukunta su kwatankwacin
zalinci da suka mana”.

Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe tare da cewa.

“Aikuwa Yah Moddibo Khausar tana da dan abinda ta sani.

Domin ranan da muka rabu da Yah Jameel na karshe aranan ne ya maida Khausar gida kuma tace mana.

Taga wata mota na binsu.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe kana tace.

“Amma Babana Meye amfanin bincike bayan sun kashesa!?”.

Cikin sauri yace.

“To ai Ummi nan nema yake da amfani tunda suka kashesa dama mun biye musu ne saboda munji
tsoron kada su kashesa shiyasa mukabi tsarinsu!”.

Girgiza kai Ummi tayi kana tace.

“Toh amma dai ni inaganin barin shi yafi A'ala kada kai ɗinma da ka rage mana su cutar mana da kai”.

Sam Ummi ta rigada ta saki komai na duniya shiyasa duk yadda yaso ayi mgnar a sake buɗe file din
binciken taki.

Fahimtarsa bazata yardabane yasa ya nuna mata ya hakura.

Kallon Asma'u yayi tare da miƙewa kana yace.

“Asma'u zamuyi magana”.

Kai ta gyaɗa sannan ya fice.

Yau ya kama sati biyu da rasuwar Ramadan wanda yayi daidai da kwanaki sha biyu da jana'izar M
Jameel.

Acan gidan Lamiɗo kuwa da misalin karfe sha biyu na rana Hajiya Ruƙayya da Mommy da kuma Khausar
na zaune afalo suna hira kamar daga sama suka jiyo Sallamar Hajja Nana da faɗin.

“Assalamu Alaikum”...!
*Kada kyiwa labarin bahagon fahimta. Wasu abubuwa na cikin Labarin gaba ɗaya gaskiyane ya faru da
gaske. Ina mai roƙonku da Allah kuyiwa Jameel Addu'o'i Allah ya jiƙamsa da rahama ya kuma toni asirin
waɗanda sunka saceshi suka kasheshi kisa mai muni. Ku sashi a addu'o'i ku, domin Wallahi tallahi
rasuwar Jameel gsky ne kuma ya faru, da gaske wanda nasan mafi akasarin mazauna Adamawa zasu san
labarin rasuwar Jamilu matashi mai Kekkyawan ɗabi'un sun kashewa sun bar mahaifiyarsa da ƙunshin a
zuciya, sun sa mahaifinshi a rauni mai ciwo. Yah Allah ka jiƙan Jamilu kayi masa rahama da gafara, ka
tausashi zuciyar iyayensa ka ƙara zamewa mahaifiyarsa Gatan*

🤝🏻KADA KUMA KU DAMU ZAKUSHA MAMAKIN YADDA LABARIN ZAI SAKU FARINCI DA SHAUƘI ZAKUSHA
MMKIN YADDA LAMARIN ZAI BADA CITTA, KU DAI KU BIYONI KUSHA LABARI, WACCE BATA BIYA TA
BIYA.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

33

Cikin ɗan sakin fuska Mommy ta miƙe tare da cewa.

“Wa'alaikum Salam Hajja Nana sannunku da zuwa”.

Hajja Nana na zama aɗaya daga cikin kujerun falon tacce.

“Yawwa Aysha sannunki”.

Cike da farin ciki Khausar ta miƙe tare da riƙe hannun Dije kana ta jata suka zauna akan 2sitter.

Murmushi Mommy tayi tare da juyawa ta shiga kichen.

Ta kawo mu abin taɓa,

Fuska ɗauke da murmushi Khausar dake riƙe da hannun Dije ta juya tare da kallon Hajja data zuba mata
Ido, cikin sanyi tace.

“Maraba Hajja Nana ya gida ya Baffa Liman, Baffa Jauro,Baffa Sadu, Baffa, Garga Yaya Sadik? Duk kowa
da kowa dai”.

Harara Hajja Nana ta watsa mata kana tace.


“Sai yanzu kika ganni wacce ta dameki ai gashi tun shigowarta kika jata jiki, kuke gaisawa idan kin matsu
da sanin yanda suke sai kije ki duba su da kanki”.

Uhum kawai Khausar ce tare da loggobar da kai dan har yau bata dawo dai-dai ba cikin sanyi tace.

“Kai wannan tsohuwa ke dai akwai ki da kishi, da mita ina ce dai yanzu gashi na gaishe ki amaimakon ki
amsa shine sai kin cakaleni”.

Riƙe haɓa Hajja Nana tayi tare da maka mata Harara kana tace.

“Yo ki riƙe abinki mana ko wata tsiyar gaisuwar ki zai min?”.

Ta ida maganar tare da sauƙa ta ɗauki Cup ɗin tea da Mommy ta zuba mata kana ta kurɓa”.

Taɓe baki Khausar tayi tare da cewa.

“Oho dai ai ko bazai miki amfani ba kin nema bare ma amfanin zai miki”.

Mommy da fitowarta daga kichen kenan tayiwa Khausar alamar tayi shiru kana ta zauna gefen Hajja
Nana cike da girmamawa ta gaisheta tare da tambayar mutane gida.

Miƙewa Khausar tayi tare da riƙe hannun Dije tace.

“Zo mushiga ciki”.

Saurin Kallonta Hajja Nana tayi tare da faɗin.

“Dawo ki zauna”.

Tsayawa tayi tare da kallon Hajja Nana still hannunta na riƙe da Dije tace.

“Toh me kuma zan miki?”.

Sassauta murya Hajja Nana tayi tare da faɗin.

“Ke kam ki dawo ki zauna mana”.

Sake hannun Dije tayi tare da tsare Hajja Nana da ido kana tace.

“To wai mai zan miki zamuje muyi hiranmu irin na ƴan Uwanta kema kuyi hiranku mana ko sai dole na
zauna ne?”.

Harara Hajja Nana ta maka mata tare da cewa.


“Wato ke dai daga zuwana sai kinsa mun raba hali, ko ba a isa ace yi kiyiba sai kinyi musu?”.

Kallon Khausar Mommy tayi tare da cewa.

“Ke dai ki dawo ki zauna mana koma menene ai zaki ji”.

Kai ta gyaɗa tare da janyo hannu Dije suka zauna gefen Mommy ya zamana Khausar na fuskantar Hajja
Nana.

Hajja Nana kuwa zamanta ta gyara tare da fuskantar Mommy Cike da isa, gadara, taƙama, Iko, kana da
Power da take jin tana dashi akan Khausar da kuma rigima irin ta tsofaffi tace.

“Alhamdilillah mun godewa Allah daya nuna mana lokacin da Khausar ta gama karatu lafiya”.

Cikin sauri Khausar ta kalleta tare da cewa.

“An gama karatu lafiya ko kuma anfara taka matsayin karatu? Ko tsakiyar karatu ma naje ne bare akai ga
maganar gamawa?”.

Wani kallo Hajja Nana ta watsa mata tare da cewa.

“Karatun ƙa'ida kam nasan angama shi tunda kinyi haddar Alkur'ani kin sauƙe sannan kinsan, Ahallari,
Kinsan ishmawi, Kinsan Fiqhu, Kinsan Arbauna, Kinsan Sira da sauransu yanzu wani karatu ya rage miki”.

kallonta kawai take sai data gama jerawa kafin tace.

“Karatu kam wanda ya ragene yafi yawa aisharan fage kawai nayi acikin karatu”.

Harara Hajja Nana ta watsa mata cikin yanayin zafinta tace.

“A'a sannu Al-huda-huda sarkin karatu dole kika ce sharen fagi kikayi mana, tunda kin samu anbarki kinyi
wannan ɗin”.

Sake baki Khausar tayi tare tura baki kana tace.

“Ikon Allah dana samu anbarni nayi da mekike nufi kenan, ko kuma dama kece zaki tsara min abinda
zanyi?”.

Gyara zama Hajja Nana tayi cikin ƙanƙance Ido tace.

“Ke ko kunya bakya ji dube ki fa duk kin gama girma agida shekarunki kusan Ashirin ai wannan ma
taumaka miki za'ayi dan kin gama tsufa”.
Buɗe baki Khausar tayi tare da kallon kanta kana ta kalli Hajja Nana cike da Isa Hajja Nana tace.

“Kalleni da kyau yo ƙarya na miki, ƙannen bayanki nawa aka Aurar wasu da yara bibbiyu wasu kuma
ɗaddaya ke kam wannan wani sai dai yace bazawara ce ke dan kin gama girma”.

Wani kallo Khausar ta mata tare da cewa.

“A'a Hajja Nana ya isa haka cin fuska dan wlh bazan juraba.Wanda suka fini dubu nawa ne basuyi Aure
ba, sai dai idan A Rugar kune ake irin wannan Auren, amma nikam yanzu ma nayi ƙarama da Aure.

Mommy kuwa kallon Khausar tayi tare da ɗaga mata hannu kana tace.

“Haka naki Khausar kiyi mana shiru”.

Sunkuyar da kanta ƙasa tayi batare da ta sake cewa Uffan ba kawai dai tasan in ba ita ke tare Hajja Nana
ba Mommy kam ba abinda zatace tanaji tana gani za'a tauyeta.

Hajja Nana Khausar ta nunata da ɗan yatsa tace.

“Ki kiyayeni bada ke nake magana ba fitsararriya mara kunya!”.

Gyara zama Khausar tayi tare da juya mata manyan Idanunta da kawar da kai gefe.

Murmushi Dije dake gefen Khausar tayi tare da riƙe hannun ta da ido tayi mata alamar ta daina.

Gyaran murya Hajja Nana tayi tare da cewa.

“Aysha Ni dake nake magana bada Khausar ba, ya batun maganar da mukayi tunda Allah yasa tagama
yanzu, sannan makon daya gabata Baffanta yazo daga Adamawa aranan daya zo aranan ya koma”.

Sai kuma ta kalli Khausar tare da watsa mata Harara kana ta maida kallonta kan Mommy dake
sauraronta tace.

“Toh dama ace yazo da niyyar kwana zamu ƙara so nan, ayi magana to amma ke me kikace tsakaninta da
Aliyu ɗan Uwanta!?”.

Ahankali Mommy ta sunkuyar da kanta ƙasa kana tayi shiru cikin yanayin sanyinta da Kawaici, da
mutumtaka da kuma kamala tace.

“Toh Hajja Nana wannan magana duk yanda kuka zantar ai hakane Baffanta shine me Aurar da ita, dan
haka duk abinda ya yanke akanta shine dai-dai”.

Jinjina kai Hajja Nana tayi tare da tura kallabin kanta kana ta gyara zamanta cikin jin daɗi tace.
“Shima yace min Insha Allah nan da wata ɗaya ko sati uku zai zo idan ya samu sarari zaizo su zanta da
Uban goyon yarinyar, shima abashi mutuncinsa tunda shi ya raineta tun tana da wata wata uku shi
yamata komai”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da faɗin.

“Bakomai duk abinda kuka tsara yayi Idan har Auren Khausar da ɗan Uwanta Al'khairi ne Allah ya
tabbatar mana da alkhairinsa”.

Cikin sauri Khausar ta tura bakinta tare da cewa.

“Ni dai bana sonshi kuma ke dai Mommy ayita Addu'ar alkhairi”.

Wani kallo Mommy ta watsa mata alamar rufe min baki, shiru Khausar tayi tare da sunkuyar da kanta
ƙasa Mommy kuwa kallon Hajja Nana tayi cikin sanyin murya tace.

“Ni dai Allah ya tabbatar da al'khairi idan al'khairi ne Allah ya tabbatar ya kuma zaɓa musu abinda yafi
zama al'khairi atsakanin su.

Gyara zama Hajja Nana tayi kana tace.

“Ammen,Kuma Insha Allahu ma alkhairi ne”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.

“Adduar da mukeyi kenan”.

Miƙewa Khausar tayi tare da riƙe hannun Dije da alamun ɓacin rai tace.

“Dije mu tafi”.

Harara Hajja Nana ta watsa mata tare da sake tura daurin Kallabinta gaba kana tace.

“Aikuwa wannan magana ya zama dole ki saurareta tunda batu ne na Aurenki akeyi”.

Cikin ƙankance Ido Khausar tace.

“Nifa bazanyi Aureba ehe ke baki da aiki sai ƙaƙale ƙaƙalen magana ina ruwanki da batun Aurena!?”.

Afusace ta kalleta kana tayi Ƙwaffa tare da cewa.

“Aikuwa dan Ubanki nike da ruwa dake kuma dole kiyu Aure”.

cikin tsirawa Hajja Nana ido tace.


“Amma dai na faɗa miki ki daina zagin mahaifina Aure kuwa idan Allah ya nufa zanyi amma ba wanda
kike cewa ba kam!?”.

Ajiyar zuciya Hajja Nana ta sauke kana tana kallonta bako ƙyaftawa sai kuma ta sauƙe ajiyar zuciya tare
da cewa.

“To wa kike so ki Aura?”.

Juya ido Khausar tayi tare da cewa.

“Aini nasan wanda zan Aura, kuma dan haka babu ruwanki dani sai kace ke lokacin da zaki yi Aure zaɓa
miki wanda zaki Aura akayi ba ke kika zaɓa da kanki ba!”.

Girgiza kai Mommy tayi tare da nunawa Khausar hanya da hannu alamar tabar wajen ita har ga Allah
bata so ma Hajja Nana ta tsaida Khausar a cikin mgnar ba in bana tsohuwaba taya zata tsaida Khausar
bayan tasan yadda suke da juna.

Tura baki Khausar tayi tare da jan hannun Dije dake murmushi sam bata gajiya da kallon Dramer Khausar
da Hajja Nana.

Khausar da Dije na isa ƙofar Bedroom ɗin zasu shiga Akuma dai-dai lokacin Asma'u tayi sallama cike da
ladabi tsugunna agaban Mommy ta gaisheta Cike da kulawa Mommy ta amsa tare da tambayarta ya
Umminta ta amsa da tana lafiya.

Kana ahankali ta maida kallonta kan Hajja Nana dake cin Inabi tace.

“Hajja Nana inayini fatan kunzo lafiya?”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da cewa.

“Lafiya lau Alhamdulillah Allah ya miki albarka kar dai ki riƙa ɗaukar hallayar wasu ƙawaye na tsiwa”.

Ɗan murmushi Asma'u tayi kana cikin sanyi ta gyaɗa kanta Khausar dake tsaye bakin ƙofa ta wani ɓata
fuska tare da kawar da kai gefe.

Miƙewa Asma'u tayi ta nufi wajensu Khausar suka shiga Bedroom cikin ɗan sakin fuska da sanyi Asma'u
tace.

“A Dije sannu da zuwa ya gida ya mutanen Jauro yaya!?”.

Murmushi Dije tayi cikin yanayin sanyin ta tace.

“Duk lafiya lau?”.


Kallon Dije Khausar tayi kana cikin sanyin tace.

“Ayyah Dije yayan Asma'u Malam Jameel Allah ya masa rasuwa kwanan nan ƴan Kidnapping suka
kashesa!”.

Cike da tausayawa Dije tace.

“Ayyah Ubangiji Allah yajiƙan sa da rahma sukuma Allah ya tona musu asiri”.

Atare Asma'u da Khausar suka amsa da.

“Ameen”.

Asma'u kuwa Idanunta ne suka ciko da ruwan hawaye.

Cikin sanyi Khausar ta dafa kafaɗar ta kana tace.

“Dan Allah Asma'u kiyi haƙuri kin sani babu abinda Yah Jameel ke buƙata awajenmu face addu'a Insha
Allah Yah Jameel na cikin rahamar Allah”.

Jinjina kai Asma'u tayi kana cikin sanyin murya tace.

“Insha Allah muna yi kuma zamu cigaba dayi”.

Miƙewa Asma'u tayi tare da kallon khausar cikin sanyin murya tace.

“Toni zan tafi”.

Da sauri Khausar ta ɗago kanta cike da kulawa tace.

“Sauri-sauri haka”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare da lumshe Idanunta cikin sanyin murya daya zame mata jiki tace.

“Wallahi gidan Innayi nake son zuwa dama na biyo ne akan ince muje ki rakani kuma sai na ganki da
baƙuwa, shiyasa nayi shiru bance komai ba”.

Ajiyar zuciya Khausar ta sauke tare da tsira mata ido cikin fesar da numfashi tace.

“Ayyah wallahi kuwa badan baƙuwar ba ai da naje na rakaki amma lafiya kuwa?”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tana gyaran zaman hijabinta tace.

“Eh Ummi ce ta aikeni wajen Innayi akan Inje wajen.

Yaya Moddibo yau kusan sati kenan bai sake zuwa gidanmu ba sannan kuma Innayi ma ta kirata tana
faɗa mata ko cikin gida baya fita”.

Jinjina kai Khausar tayi cike da tausayinsu tace.


“Allah sarki Malam Moddibo dole ya shiga cikin tashin hankali da alhinin rashin.

Yah Jameel insha Allahu jinin Yah Jameel da hakkinmu ba zai taɓa bari wannan mutanen su samu
salama acikin rayuwarsu ba!”.

Kai Asma'u ta gyaɗa cikin sheshsheƙan Kuka tace.

“Tabbas sun cutar da rayuwar mu, cuta mafi muni sun zalunce mu kana sun ɗauke mana duk wani farin
ciki da walwalarmu. Yah Jameel shine Komai namu Yah Jameel shine fitilar dake haska zukatanmu amma
dare ɗaya suka rabamu da wannan hasken kuma jigonmu”.

Cikin sanyi da tausayawa Dije tace.

“Asmau'u kiyi haƙuri Allah baya zalunci sannan baya bari ayi zalunci da sannu Ubangiji zai fallasa asirin
wanda suka aikata wannan ta'asar sannan sai sun wulaƙanta wulaƙanci mai muni insha Allah”.

Cikin sanyi da Khausar da su kaji mutuwar ya dawo musu sabo suka hada baki wajen cewa.

“Ameen”.

Miƙewa Asma'u tayi tare da faɗi.

“Bari na tafi dan Ummi tayi ta kiran wayarsa baya ɗauka sannan itama Ummi baki daya bata jin daɗin
jikinta sosai ta dawo tamkar majinyaciya.

Khausar sai kinga gidanmu baki ɗaya duniyar bata mana daɗi”.

Cikin sanyin da rarrashi Khausar tace.

“Ayyah Asma'u am haka rayuwa ta gada Ubangiji Allah ya jikan Yah Jameel da rahma mu kuma Ubangiji
yasa mana dangana azuciyarmu sannan mu cigaba dayi masa addu'a gatan da zamu nuna masa kenan”.

Kai Asma'u ta gyaɗa kana tace.

“in sha Allah, na tafi”.

Kai Khausar ta gyaɗa sannan ta kalli Dije tace.

“Muje mu rakata”.

Miƙewa Dije tayi sannan suka fita bayan Asma'u ta yiwa Mommy da Hajja Nana sallama har bakin hanya
suka rakata saida ta samu adaidaita ta hau sannan suka koma.

Asma'u na isa gidan direct Sashen Innayi ta nufa zaune ta hango Innayi kan barandar ta tayi tagumi da
hannunta na dama jin anɓude ƙofa yasa tayi saurin ɗaga kanta ganin Asma'u yasa ta saki Ajiyar zuciya.

Cikin sanyi Asma'u ta ƙarasa tare da zama agefenta cikin sanyin murya tace.
“Innayi”.

Numfashi Innayi ta fesar tare da tsira mata ido cikin alamun damuwa tace.

“Na'am Asma'u kin zo ya jikin Umminki!?”.

Kanta aƙasa tace.

“Innayi da sauƙi Ina Yah Moddibo fa?”.

Ajiyar zuciya me nauyi Innayi taja kafin ta sauƙe cike da damuwa tace.

“Asma'u bansan wani irin yanayi Moddibo yake ƙoƙarin shiga ba baki ɗaya ya zama wani iri ya dawo
tamkar mara lafiya ya zama abin tausayi koda fitowa bayayi”.

Sai kuma ta runtse Idanunta cike da damuwa kana ta buɗe su tare da cewa.

“Ko abinci idan bana nuna masa ɓacin raina ba baya ci banda ruwan tea Babu abinda yake sha baki ɗaya
ya sauya duk hankalina ya tashi na rasa yanda zanyi.

Gaba daya ƙasar nan tafi raina duniyar ta isheni”.

Sunkuyar da kai Asma'u tayi tana jin hawaye na cika kwarmin Idanunta.

Cikin raunin murya Innayi ta kalli Asma'u tare da cewa.

“Na rasa yanda zanyi da Moddibo ɗazun nan ma Abban Jameel ya fita dalilin zuwansa da yayi masa.

Nasiyya da kwantar masa da hankali shine ma muka samu ɗazun yasha kunu”.

Numfashi mai zafi Asma'u ta fesar tare da kallon Innayi tace.

“Ummi ma tace tana som ganinsa baki ɗaya ta damu da rashin zuwansa kuma koda ta kira wayarsa baya
shiga bare taji muryarsa, Innayi barin shiga wajensa”.

Kai Innayi ta gyaɗa kana tace.

“Shikenan ba matsala muje”.

Miƙewa Asma'u tayi tare da nufar Sashen sa Innayi na biye da ita.

Innayin ce ta tura ƙofar falon suka shiga ahankali Idanun Asma'u suka sauƙa akan Moddibo dake zaune
kan 1sitter Ƙirjinsa Rungume da Alkur'ani yayinda idanunsa ke lumshe suna tsiyayar da hawaye kana
dashash-shiyar muryarsa na rera karatun Alkur'ani.
Cikin mutuwar jiki Asma'u ta zauna daga gefen ƙafafunsa Innayi kuma ta zauna daga saman kujeran.

Ganin yanda hawaye ke fita Shar-shar-shar a idanunsa yasa Asma'u fashewa da kuka mai gunji hadda
sheshsheƙa.

Jin sheshsheƙan Kukan Asma'u yasa Moddibo da idanunsa ke lumshe saurin buɗewa ganin yanda Asma'u
ke kuka da sheshsheƙa yasa yayi saurin sanya tafin hannunsa yashiga goge hawayen dake saman
kuncinsa.

Cikin sanyi Innayi ta kallesa tare da cewa.

“Moddibo!, Moddibo!!, Moddibo!!!”.

Ahankali ya ɗago kumburarrun Idanun sa da suka jiƙe da hawaye kana Eyelashes ɗinsa sun kwanta cikin
sanyi ya kalleta.

Innayi kuwa cikin tsaresa da Ido tace.

“Moddibo za kayi fushi da hukuncin Ubangiji ne?”.

Cikin sauri ya girgiza mata kai tare da cewa.

“Astagafirullah³”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta tsira masa Ido tace.

“Toh Meyesa Moddibo baka fita, baka cin abinci sannan baka walwala, kenan fushi kake da Ubangijin
daya bamu Jameelu sannan ya ɗaukesa!?”.

Kai ya girgiza mata batare da yace Uffan ba!.

Cikin sanyi da rauni Innayi ta zuba masa Ido baki ɗaya Garin Jahar Taraba da maƙasar Nigeria yafi ta
ranta, fesar da numfashi kana tace.

“Toh Meyesa sai dai ka ɗauki Kur'ani ka rungume kana karatu kana kuka”.

Cikin wata dashash-shiyar murya me cike da rauni da tashin hankali yace.

“Innayi mai zan fita nayi acikin garin Gembulan? Innayi da waye zan fita? Innayi baki ɗaya garin nan ya
fita raina bana son garin nan na tsani garin nan garin nan ya fita min araina”.

Sai kuma ya runtse Idanunsa da ƙarfi yayin da jijiyoyin kansa suka tashi ruɗu ruɗu dasu kana zuciyarsa ta
shiga bugawa da masifar ƙarfi cikin dauriya ya buɗe idanunsa da suka yi masifar Ja yace.
“Innayi duk inda na wulga acikin garin Gembulan zanga kamar J ɗina na akusa dani, shin Innayi taya zan
fara fita da waye zanyi yawo da waye zanje masallaci da waye zanyi dariya da wa zan dawo gida da wa
zan zauna inci abinci!?”.

Asma'u kuwa kife kanta jikin kushin ɗin da yake zaune tayi tare da fashewa da wani irin kuka tabbas
sunyi rashin da baza su sake samun kwatankwacin saba sannan kuma anzalince su zalinci mai muni da
raɗaɗi.

Jin yanda Asma'u ke kuka kamar ranta zai fita yasa Moddibo juyawa ya kalleta cikin sanyi da tausayinta
yace.

“Asma'u ki daina kuka ki yiwa J addu'a domin shine abinda yake buƙata atare damu”.

Innayi kuwa kallonsa tayi har zuwa lokacin hawaye na zuba daga idanunsa ajiyar zuciya ta sauƙe kana
tace.

“Toh Moddibo kaima fa kukan kake ya za ayi Asma'u ba zatayi kuka ba”.

Kallon Innayi yayi tare da lumshe idanunsa wasu hawaye masu masifar zafi suka zubo masa.

Anutse ya goge tare da cewa.

“Innayi idan har bana samu na rungume Kur'ani ina karatu ba bana samun damar hawaye suna zubo
min, sannan aduk lokacin da hawayena ke zuba inaji kamar ana zare min wani abu mai nauyi ne acikin
ƙoƙon raina, shiyasa nake rufe kaina ni kaɗai nayi ta kuka”.

A tausashe ya kalli Innayi data tsaresa da ido ya cije Lip ɗinsa kana yace.

“Innayi idan har banyi kuka ba menene amfanin Idanuna da hawayena? idan ban zubar dasu arashin J ba
J fa Innayi J ɗina”.

Numfashi Innayi ta fesar cikin sanyi tace.

“To ai addu'a zaka yi masa Moddibo”.

Cikin dashash-shiyar muryarsa daya dishe da kuka da tashin hankali yace.

“Innayi to ai ina masa addu'a”.

Asma'u kuwa ahankali ta ɗago Idanunta dake jiƙe da ruwan hawaye ta kallesa cikin sanyi tace.

“Yah Moddibo Meyesa ka daina zuwa wajen Ummi?.


Baki ɗaya hankalinta ya tashi ta dawo kamar mara lafiya?”.

Girgiza kai yayi tare da kallonta kana cikin sanyi yace.

“Asma'u ki cewa Ummi tayi haƙuri insha Allah zan zo amma ina jin wanin irin yanayi ne taya zan kalli
al'amarin tayaya zan iya zuwa wajen Ummi ba tare da J na kusa dani ba?”.

Numfashi mai zafi ya fesar da karfi kana yace.

“Baki ɗaya rayuwa tayi min ƙunci na rasa madafa, komai ya min duhu acikin duniyar nan na rasa yanda
zanyi da kaina baki ɗaya na rasa yanda zan fuskanci al'amarin”.

Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe tare da fesar da nunfashi ta kallesa tare da faɗin.

“Ni dai Yah Moddibo mu tafi, idan har baka jeba Ummi na cikin tashin hankali da damuwar rashinka,
koda magana da Ummi ba tayi idan ba mun matsa mata ba amma sai ta zauna shiru ita kadai afalo baki
ɗaya gidan ya daina yi mana daɗi”.

Ahankali Moddibo ya taune Lip ɗinsa kana yace.

“Insha Allah zan zo ki cewa Ummi tayi haƙuri”.

Girgiza kai Asma'u tayi kana tace.

“A'a Yah Moddibo nidai gaskiya Ummi tace sai dai muje tare”.

Gyara zama Innayi tayi tare da fuskantar Moddibo cike da kulawa tace.

“Toh ka tashi kuje matuƙar kana son farin ciki da kwanciyar hankalin Ummin ka, kada ka haɗa mata ciwo
biyu Moddibo kasan rashin ka awajen Ummi babban matsala ne”.

Cikin sauri Asma'u tace.

“Wallahi kuwa Yah Moddibo baki daya ƙuncin ya mana yawa, ba kai babu Yah Jameel. Baki ɗaya
zuciyarmu acunkushe yake da damuwa amma ganinka zai ɗebe mana kewa”.

Cikin sanyi da rarrashi Innayi tace.

“Ka daure kaje ko hankalinsu zai kwanta kuma kaima za kaji sauki acikin ranka”.

Ta ida Maganar tare da miƙa masa key tsohuwar motar data fara saya mishi.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da karɓa kana ya miƙe cikin sanyi ya Murɗa handle din ƙofar

tare da fitowa wajen, cikin sauri ya lumshe idanunsa rabonsa da ganin haske irin haka ko kuma ya taka
kofar falon yau tsawon kwana biyar kenan ko da sallah agida yake baya fita jam'i kai tsaye inda Motarsa
yake ya nufa ya shiga sannan yaja suka tafi.
Innayi kuwa na ganin tafiyarsu ta kira Number Malam Arɗo bayan ya ɗaga tace.

“Dan Allah Malam Arɗo idan babu damuwa kazo ina da magana da kai”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Toh badamuwa Insha Allah zan zo”.

Modibbo kuwa suna isa memory sa ya shiga tariyo masa hoton fuskar J ɗin sa cikin sauri ya juya gefen
damansa jin kamar sautin murya J ɗinsa cikin dariya yana cewa A.J tsayuwar me kakeyi Please kazo mu
shiga inga Ummina kasan dai nayi missing dinta da yawa.

afili ya furta.

“J kai ko nima ainayi kewarta kuma dan na tsaya jiranka ne da tuni na taho”.

Murmushi yaga M Jameel ya sakar masa sannan ya janye hannunsa daga cikin nasa ya juya ya fara tafiya
yana jujjuya masa hannu alamar Byebye.

Da sauri Moddibo ya juya tare da cewa.

“J ina kuma zaka je ba kace ka matsu kaga Ummi ba?”.

Cikin sauri Asma'u dake Kallonsa ta tashare hawayen dake kwaranya a Idanunta kana tace.

“Yah Moddibo Yah Jameel fa baya nan sannan bazai taɓa zuwa inda muke ba”.

Moddibo kuwa ido ya tsirawa Asma'u kamar mai son fahimtar abinda take faɗa sai kuma yayi saurin dafe
kansa tare da maimaita Kalmar Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n shi kansa yasan zuwa zuwa yanzu dai
kamar zautacce yake.

Numfashin ya fesar sannan ya nufi falon bakinsa ɗauke da Sallama Asma'u na biye dashi.

Ahankali idanunsa suka sauƙa akan Ummi dake zaune kan 3sitter ta daura guiwar hannunta duka biyu
akan cinyarta tayi tagumi tare ta tsirawa waje ɗaya Ido baki ɗaya ta rame fuskarta yayi fayau.

Cikin sauri Moddibo ya ƙarasa shiga falon tare da zama agefenta kana ya janye tagumin da tayi ya maida
hannunta kan gwiwoyinta.

Ummi kuwa cikin sauri ta sunkuyar da kanta nan take hawaye suka fara zuba Shar-shar-shar cikin sanyin
murya ya kalleta kana yace.
“Ummi dan Allah kiyafemin. Insha Allahu bazan sake nesa dake ba, kinji Ummina ki daina zubar da
hawayenki, dan baza mu iya juran. Kallon hawayen ki na zuba ba”.

Kallonsa Ummi tayi cikin wata raunan'niyar murya tace.

“Babana idan har baka zuwa wajena ya zanyi?Kana so ka haɗa min zafi biyu alokaci ɗaya ne?

Babu Jameeluna sannan kaima baka kusa dani mekake tunanin zanji arayuwata, kana so inshiga wani
hali ne?”.

Cikin sauri ya girgiza mata kai kana muryarsa na rawa yace.

“Insha Allahu bazan sake nesa da keba, zan kasance atare daku tamkar yanda J ke kasancewa atare
daku, zan sanya ku farin ciki tamkar yanda J ɗina ke saku insha Allah zan kiyaye”.

Ya kalli Ummi da har zuwa lokacin hawaye ke zuba a Idanunta ya ɗaura tafin hannunsa akan nata cikin
rawan murya yace.

“Insha Allah zan zame muku farin ciki kuma Garkuwa kamar yanda J ɗina ya kasance agareku Ummi.
Asma'u Bashir Insha Allah bazan bari hawayenku ya zuba ba tamkar yanda J ɗina baya bari su zubo ba
nayi al'ƙawarin zan zame muku farin ciki zan maye muku gurbin J ɗina”.

Ya ƙarasa maganar tare da fashewa da kuka kasa rarrashin sa Ummi tayi kawai itama hawaye ya cigaba
da zuba daga idanunta haka Asma'u da Bashir suka riƙa kuka harda sheshsheƙa baki daya Moddibo baya
jin zai iya hana kansa kuka bare kuma ya samu kuzarin rarrashinsu hakan yasa aka rasa wanda zai
rarrashi wani acikinsu.

Malam Ahmad da dawowansa kenan ya zuba musu ido cike da tausayinsu ganin yanda suke kukan kasan
daga ainihin zuciyarsu yake fitowa.

Cikin sanyi malam Ahmad ya zauna gefen Ummi ya zamana yana fuskantar Moddibo, Asma'u da Bashir
dake ƙasa cike da tausayawa da kuma rinƙa rarrashisu da basu baki.

Ahankali Ummi ta maida bayanta da jikin kushin ɗin ta jingina hawaye na cigaba da zubo mata Moddibo
kuwa kasa yayi da kansa yana jin wani irin yanayi azuciyarsa shikenan J ya tafi ya barsa bari na har abada.

Kallonsu Malam Ahmad yayi kana ya cigaba da cewa.

“Insha Allahu da yardan Ubangiji Jameelu yana cikin rahama, salama nutsuwa da kwanciyar hankali
domin Jameelu ya kasance bawa mai tsananin Biyayya ga dokokin ubangiji sannan Jameelu yaro ne me
biyayya ga Iyayensa akullum burinsa yaga ya sanya Iyayensa da shalinsa acikin farin ciki”.
Jinjina kai sukayi Atare cike da gamsuwa da maganarsa tabbas ta ko wanni fanni Jameel bashi da
makusa.

Ajiyar zuciya Malam Ahmad ya sauƙe kana yace.

“Jameel ya kasance mutum mai tsananin tausayi da temakon al'umma Jameel baya taɓa kallon mutum
acikin halin neman temako sannan ya wuce batare daya temakesa ba, duk wanda yasan Jameel da
addu'a yake binsa na Ubangiji ya jiƙansa dama mutane masu Kirki da karamci Ubangiji bai fiye barinsu
tagayyaraba sam Jameelu bai cancanci kuka agare kuba, addu'a ya cancanci ku masa domin da izinin
Ubangiji yana can cikin rahmar Allah da yardan sa”.

Kai Bashir ya gyaɗa tare da share hawayen saman fuskarsa kana cikin sauri yace.

“Hakane ma Abba abinda kake faɗa yanzu shine abinda.

Yah Jameel ya faɗa min acikin Mafarkina jiya da daddare yace. in faɗawa Ummi ta daina yi masa kuka
domin duniyar da yake ayanzu tafi wannan duniyar da muke ciki daɗi, nutsuwa, salama, da kuma
aminci”.

Cikin sharce hawaye ya gyara zamansa tare da fuskantar Ummi kana yace.

“Sannan yace bayason wannan kukan da Ummi ke masa, shikam addu'a yake buƙata duk wannan koke
koken bayaso adaina yi masa.”

Kallonsa ya mayar kan Moddibo tare da cewa.

“Sannan kaima Yah Moddibo acikin mafarkin da nayi da Yah Jameel yace in Faɗa maka ka cigaba da
yimasa addu'a sannan kayi ƙoƙari ka cika masa wasiyyar da yayi maka ta gefen Innayi ya jadda min kuma
ka taya Abbansa kula da lamuran kasuwancinsa”.

Saurin ɗago kai Moddibo yayi tare da cewa.

“Ummi wani wasiyya kuma J ɗina ya bari akaina??”.

Girgiza kai Ummi tayi tare da fashewa da matsanancin kuka batare da tace Uffan ba.

Ajiyar zuciya Malam Ahmad ya sauƙe tare da kallon Ummi dake sheshsheƙa kana yace.

“Fatima yanzu kuka za kiyiwa Jameelu? shin kinsan Rahman da Ubangiji ya tanadar wa da duk wa'anda
aka zalunta da rabasu da rayuwarsu?

Kada fa ki manta Ubangiji ya tana dar da rahma wa duk rayukan da aka kashe batare da hakkinsa ba”.
Ahankali Ummi ta ɗago kanta kana ta sanya tafin hannunta ta share hawayen ta Numfashi malam
Ahmad ya fesar kana yace.

“ki tuna ni'imomin da Allah yayiwa muminai tanadin su.”

Lokaci ɗaya Ummi ta saki murmushi wanda tun bayan sace M Jameel ba tayi irinsa ba wani irin nutsuwa
da salama taji yashigeta lokaci ɗaya tabbas tana ji ajikinta Jameelun ta na cikin rahmar Ubangiji.

Moddibo ma murmushi yayi wanda ya fito daga ainihin zuciyarsa in sha Allah J dinsa yana cikin
kwanciyar hankali da salama da izinin Ubangiji addu'a kawai J dinsa ke buƙata atare dashi Insha Allah
kuwa zai cigaba da masa hakan yasa suka cigaba da hirar rahmar da M Jameel zai kasance da izinin
Ubangiji cikin sakin fuska suka cigaba da hira.

Acan gidan Lamiɗo kuwa ƙarfe biyar dai-dai Hajja Nana ta mike tare da kallon Dije dake zaune gefen
Khausar suna hira tace.

“Ke Dije tashi mu tafi”.

Kai Dije ta gyaɗa tare da miƙewa cike da girmamawa Mommy ta haɗa mata tsaraba sannan ta bawa
Khausar ta riƙe suka fito.

Suna fita coumpund ɗin Hajja Nana ta kalli Khausar tare da cewa.

“Insha Allah idan Baffa Jimeta yazo zamu zo tare”.

Ko uffan Khausar bata ce da ita ba haka zalika Mommy, bayan Khausar sun koma falon ta kalli Mommy
cikin sanyin murya tace.

“Mommy yanzu dan Allah biye mata zakiyi?”.

Ahankali Mommy ta zauna tare da kallon Khausar cikin sanyi tace.

“Yanzu Khausar idan ban biye mataba wa kika tsayar? sannan tsohuwar nan tunda ta rantse akan dole
sai anmiki aure tofa babu makawa, sannan babu yanda zanyi dole sai an Aurar dake ke dai kiyi fatan
Allah ya miki zaɓin alkhairi, sannan ya baki mijin da zai barki ki cigaba da karatunki ki kuma cika burin ki”.

Wani abu mai masifar ɗaci Khausar ta haɗiye cikin raunin murya tace.

“Mommy nifa Banason sa”.

Kallonta Mommy tayi kana cikin tsareta da ido tace.

“To idan bakya sonsa wakike dashi ko kuma wa kika tsayar babu wani saurayi dake zuwa wajenki Naseer
da ake maganar sa yanzu ya fita sabgarki kuma hakama yafi min.
Ni yanzu abinda na fahimta ma kamar soyayya suke da Amina”.

Khausar kuwa kallon Mommy tayi tare da tura baki kana tace.

“Eh Mommy soyayya suke to amma.

Ni me ruwana dasu ni dai bazan Auri Yah Aliyu ba Naseer kuwa bana sauraron maganarsa bare insa shi
araina”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da gyara zaman ta cikin sanyin murya tace.

“Toh Allah ya mana zaɓin alkhairi”.

ta faɗa tare da miƙewa tashiga Bedroom ɗin ta Khausar kuwa jingina bayanta da jikin kushin tayi tare da
lumshe Idanunta.

Da yammaci Misalin ƙarfe biyar da rabi Hajiya Bunayya da Hajiya Lami ce zaune agaban Boka Kar'uzu.

Cikin farin ciki Hajiya Lami ta gyara zamanta tare da kallon Boka Kar'uzu dake taune laɓɓansa na ƙasa
duk yayi muni ba kyan gani cikin sassauta murya tace.

“Na gaishe ka Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu ina mai farin cikin sanar da kai
shekaran jiya Alhj ya tafi Saudia kaga yanzu sai ka shirya ka koma gidana kaje kayi sati ba matsala”.

Wata mahaukaciyar dariya Boka Kar'uzu ya fashe dashi wanda yasa ganyen bishiyar dake wajen suka
soma zubowa yana mai ƙara wangale wawakeken bakinsa yace.

“Anjima da daddare zanzo, maza ku tashi ku tafi da ƙafar hagu yanzu zanyi manyan baƙi da kukar
bulikiya Ɗan Jaƙunana mai ƙaho Atsakiyar kai da da jela zai ƙaraso”.

Ai cikin sauri suka miƙe suka fita daga wajen kamar yanda ya faɗa.

Acan gidan Innayi kuwa zaune suke da Malam Arɗo asaman baranda Moddibo.

Cikin nitsuwa Innayi ta kalli Malam Arɗo cikin sanyin murya tace.

“Toh kaji yanda mukayi dashi, yanzu abinda nake so idan Allah ya nufa zaka je kasamu Abban Jameelu
kayi masa bayani idan yaso sai mu isar da manufarmu ga mahaifin yarinyar”.

Jinina kai Malam Arɗo yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya kana yace.

“Insha Allahu idan Allah ya yarda zan shiga wannan maganar da iyakacin ƙarfina zan shigeta da izinin
Ubangiji”.
Kai Innayi ta jinjina tare da cewa.

“Toh ba matsala Insha Allah Nagode matuka”.

Acan gidan Ummi kuwa bayan fitar Malam Ahmad Moddibo ya kalli Ummi cikin sanyin murya da
damuwa yace.

“Ummi nayi al'ƙawari da izinin Ubangiji da yardan Allah sainayi duk yanda zanyi sai an gano waɗanda
sukayi mana wannan cuta.

“Domin duniya tasan irin baƙin zunubin da suka aikata, sannan akamasu ayi musu hukunci dai-dai da
zunubinsu, domin wasu su tsira agaba kada su sake cutar da wasu kamar yanda suka cutar damu, da
zukatanmu da kuma ahalinmu”.

Numfashi Ummi ta fesar tare da sauƙe ajiyar zuciya kana tace.

“Hummmm?".

Cikin sauƙe numfashi Asma'u tace.

“Toh ammn ta ina zamu fara Yah Modibbo!?”.

Ahankali Ummi ta kalleta kana ta kalli Moddibo ta sauke ajiyar zuciya mai sanyi tace.

“Nima abinda nake tunani kenan, ta ina zaku fara wannan ba ƙaramin case bane dole yakasance mutum
nada ƙwararan hujjoji kafin ya tun kari lamarin mu kuma bamu da sahihiyar Hujja dan haka mu barwa
Allah lamarinsa”.

Jinjina kai Asma'u tayi tare da gyara zaman ta tace.

“Makama ɗaya muke da shi batun Khausar”

Cikin zurfafa nazari Moddibo yace.

“Kin tabbata Asma'u zata bamu haske kan batun?”.

Kai ta gyaɗa masa kana cikin gaskiya da gaskiya tace.

“Na tabbatar Yah Moddibo”.

Kallon Ummi dake Kallonsu yayi kana cikin ƙarfin gwiwa yace.

“Ummi”.

Cikin sanyi da tausayinsa tace.


“Na'am Babana”.

Cikin alamun samun nasara da jin daɗi yace.

“Ummi zamu fara bincike”.

Kai Ummi ta gyaɗa kana cikin wani irin yanayi tace.

“Nikam ina tsoro Babana ina tsoron kada kaima Azo acutar mana da kai ina tsoro kada wani abu ya
sameka kawai abar maganar nan”.

Cike da mamaki da kuma sanyi Moddibo yace.

“Ummi tayaya”.

Girgiza kai Ummi tayi kana tace.

“Babana Abar Maganar kawai”.

Kai ya gyaɗa mata sannan suka dauka wani hiran sosai kowannen su ya samu nutsuwa sosai sukaji
damuwar suya fara raguwa kaɗan sai bayan da Moddibo yayi sallar maghariba kafin yayiwa Ummi
Sallama ya tafi.

Bayan Sallar Isha'i Malam Arɗo ne zaune gaban Abba wanda baki ɗaya ya rame yayi wani iri dashi.

Kallonsa Malam Arɗo yayi kana yace.

“Toh Alh kaji yanda akayi kuma shine abinda ya kawo ni”.

Jinjina kai Abba yayi cikin yanayin sanyinsa yace.

“Nima nasani Jameelu ya faɗa min”.

Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe tare da faɗin.

“Masha Allah abu yazo da sauƙi kenan”.

Jinjina kai Abba yayi kana cikin sanyi yace.

“Ba matsala Insha Allah zuwa jibi zamuyi kokari muyi maganar”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa tare da cewa.

“Ayyah Jameelu Insha Allah zamu cika masa burinsa tunda har yayiwa Amininsa zaɓin mata yayi fatan ya
haɗa wannan Auren kafin ya tafi zamu cika masa burinsa da izinin Ubangiji zamuyi ƙoƙarin cika wasiyyar
daya bar mana”.
Kai Abba ya gyaɗa cikin sanyi ya gyara zamansa tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Insha Allah zan tsaya akan lamarin sannan zanyi iyakacin bakin ƙoƙarina ganin ancika masa duk kan
wasiyyar daya bari”.

Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe tare da jinjina kai yace.

“Insha Allah babu damuwa idan Allah yakai mu jibin zanzo ba matsala”.

Godiya Abba ya masa sannan Malam Arɗo ya masa Sallama ya tafi.

Bayan kwana biyu: Moddibo ya fito daga gida jikinsa sanye da Gezner fari soll yayin da kansa ke sanye da
hula tangaran baƙa yalwataccen sumar kansa irin na Fulanin Usul yana kwance aƙeyarsa fuskarsa tayi
fayau manyan Idanunsa na lumshe yayinda jikinsa ke fitar da sanyayyan ƙamshin tularen Oud Khareem
kai tsaye gidan Ummi ya nufa bakinsa ɗauke da sallama ya shiga coumpund ɗin Abaranda ya hango
Asma'u na Morping Jin ƙaran buɗe ƙofa yasa Asma'u ta juya ganin Moddibo yasa tace.

“Yah Moddibo sannu da zuwa ka iso mana”.

Ahankali ya gyara tsayuwar sa tare da cewa.

“Ummin fa naji gidan shiru?”.

Tana matse mopan dake hannunta tace.

“Bata nan”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Ke kaɗai ce agida?”.

Girgiza kai tayi kana tace.

“A'a Bashir na ciki?”.

Kai ya gyaɗa tare da gyara zaman hular dake kansa kana yace.

“Ina Ummi taje?”.

Ahankali ta jinginar da Moper kana tace.

“Ummi ta tafi asibiti saboda kwanan nan ciwon kai yana yawan damunta taje adubuta”.

Cike da kulawa da kuma sanyi yace.


“Subhanallah toh Allah ya sawwaƙe”.

Ahankali Asma'u tace.

“Ameen”.

Moddibo kuwa gyara tsayuwar sa yayi cike da nutsuwa da kuma sanyi yace.

“Asma'u zo muje ki rakani gidansu.

Khausar akwai tambayoyin da nake so nayi mata”.

Kai Asma'u ta gyaɗa cike da jin daɗin hukuncin da yake son ɗauka tace.

“Toh Shikenan Yah Moddibo bari in kira Ummi in Faɗa mata”.

Cikin sauri ya girgiza mata kai kana yayi ƙasa da muryarsa yace.

“A'a kada ki faɗawa Ummi, zata hana mu binciken idan kika faɗa mata zata hana amma yanzu kiyi sauri
muje kafin ta dawo yanzu zamu dawo”.

Jinjina kai tayi tare da faɗin.

“Toh shikenan”,Sannan tashiga ta dauki Maroon hijabinta har ƙasa kana ta kalli Bashir dake karatun wani
littafi na addini tace.

“Bari muje gidan su Khausar nida Yah Moddibo”.

Ta Ida maganar tare da fitowa.

Miƙewa Bashir yayi tare da fita kana yace.

“Laa Yah Moddibo Sannu da zuwa”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.

“Yawwa Bashir koda Ummi ta dawo kada ka faɗa mata can mukaje kace gidan Innayi muka je”.

Ahankali Bashir ya gyaɗa masa kai kana yace.

“Toh shikenan Yah Moddibo sai kun dawo”.

Suna fita suka shiga mota kana Moddibo yaja suka tafi.
Acan gidan Lamiɗo kuwa cikin sauri Khausar ta fita daga side dinsu ta nufi sashen Gimbiya Bunayya tun
kafin ta ƙarasa shiga tace.

“Ummah!, Ummah!!Ummah!!!”.

Daga ciki Hajiya Bunayya tace.

“Na'am”.

Khausar na karasa shiga tace.

“Ummah Raudat tashigo?”.

Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa kana tace.

“Eh tashigo”.

Ƙarasa shiga Khausar tayi tare da Hararan Raudat dake ɓuya tace.

“Raudat kizo muje in miki wanka amma sai wani bauɗewa kikeyi tun ɗazu kina ta gudu”.

Maƙale ka faɗa Raudat tayi tare da tura ƙaramin bakinta tace.

“Ni dai na faɗa miki bana son wankan nan akwai sanyi”.

Cikin rarrashi Khausar tace.

“To ai da ruwan ɗumi zan miki”.

Girgiza kai Raudat tayi tare da tura bakinta tace.

“Ni dai Banason gaskiya”.

Ganin tana son ɓata mata lokaci yasa Khausar ta shiga tare da janyo hannunta tace.

“Maza wuce muje in miki zan baki waya kafin fito kiyi game”.

Bubbuga kafa Raudat tayi cike da Shagwaɓa tace.

“Addah Khausi Ni dai ki ƙyaleni bana so”.

Ahankali Khausar tayi ƙasa da muryanta tace.

“Harda Game ɗin bakya so?”.

Ware Ido Raudat tayi tare da ƙyalƙyala dariya kana tace.

“Allah dagaske Addah Khausi zaki bani?”.


Murmushi Khausar tayi tare da lakace mata hanci tace.

“Eh”.

Suna shiga Bedroom ɗin Raudat ta zauna gefen gado sannan Khausar ta mika mata wayar bayan tasa
mata game ɗin _Subway surf_ ta bata murmushi Raudat tayi kana ta fara buga game ɗin.

Khausar kuwa dogon rigar jikinta ta cire tare da ɗaura towel iya ƙugunta ta shiga toilet.

Akuma dai-dai lokacin Moddibo yayi Parking afarfajiyar gida dai dai nan Lamiɗo ya fito da motarsa ganin
Moddibon yasa Lamiɗo yayi Parking din motarsa ya fito cikin sauri Moddibo ya ƙarasa kusa dashi tare da
basa hannu sukayi Musabaha cike da kulawa Lamiɗo yace.

“Moddibo bar kadai ya gida ya kuma Ƙarin haƙurin rashin Jameelu?”.

Cikin sanyin Murya Moddibo yace.

“Alhamdulillah hakuri mungode Allah”.

Cike da kulawa Lamiɗo yace.

“Allah ya gafarta masa ayi ya masa addu'a”.

Cikin sanyin yace.

“Ameen Mai Martaba Nagode.

dama munzo wajen Khausar ce”.

Cike da kulawa Lamiɗo yace.

“Toh ba matsala Asma'u ku isa”.

Ahankali Moddibo yayi ƙasa da kansa tare da cewa.

“A mai Martaba baza'a a bari daga nan ba”.

Girgiza kai Lamiɗo yayi kana yace.

“Ku shiga ba matsala bari na kira Aysha in Faɗa mata”.

Hannu ya sanya a aljihunsa tare da ciro wayarsa yayi dearling number Mommy tana ɗagawa yace.

“Aysha ga baƙi Moddibo da Asma'u zasu shigo”.

Cike da kulawa Mommy tace.

“Toh ba damuwa su shigo mana”.


Katse wayar Lamiɗo yayi tare da yi musu Sallama kana ya shiga motarsa ya fita.

Moddibo da Asma'u kuwa suka nufi sashen Mommy suna isa bakin barandar Moddibo ya tsaya Asma'u
ta ƙarasa shiga falon tare da cewa.

“Assalamu Alaikum”.

Shiru falon ba Kowa sai dai ko ina tsaf-tsaf kana ga ƙamshin dake tashi. Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe
tare da nufar Bedroom din Mommy tana cewa.

“Mommy!, Ta ƙarasa tare da shiga Bedroom din Mommy dake sanye da hijabi tace.

“Asma'u kun ƙara so Ina Moddibo?”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh amma yana waje”.

Mommy na zama gefen gado tace.

“Toh kice masa yashigo mana ya zaki barshi atsaye”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh Mommy”.

Sannan ta juya tare da fita falon ta leƙa ƙofan Falon cikin sanyin Murya tace.

“Yah Moddibo wai kashigo”.

Ahankali ya ɗago kansa tare da buɗe Idanunsa dake lumshe yace.

“Toh”.

Sannan ya shiga falon da komai ke kintse yana fitar da sanyayyan ƙamshin ahankali ya zauna akan 1sitter
dake fuskantar ƙofar Bedroom din Khausar.

Asma'u kuwa juyawa tayi tare da kallon Moddibo kana tace.

“Yah Moddibo bari in sanarwa Mommy ka ƙara so”.

Bata jira amsar saba ta nufi Bedroom ɗin Mommy.


Khausar kuwa ahankali ta fito daga toilet tare da juya kanta yalwataccen sumar kanta dake jiƙe ya
mannu da wuyanta da kuma gefen fuskarta dake da damshin ruwa fararen cinyoyinta masu haske da
santsi na ɗauke da damshin ruwa.

Ware Ido Raudat dake Game tayi tare da kife wayarta akan gadon kana ta dira tare da ficewa da gudu
saida ta isa kofar Bedroom din kafin ta tsaya.

Cike da mamaki Khausar ke kallonta kana tana tafiya ahankali tace.

“Raudat ina kuma zaki je?”.

Tura baki Raudat tayi tare da juya Idanunta tace.

“A ni dai Banason wankan nan da kwai sanyi”.

Sake baki Khausar tayi wato ita Raudat zata yiwa wayau, ɓata fuska tayi tare da cewa.

“Aikuwa baki isa ba kisa in. Baki wayata kiyi game sannan yanzu kinga na fito kice zaki gudu”.

Gwalo Raudat ta mata tare da fita da gudu.

Ware ido Khausar tayi tare da bin bayanta da gudu dariya Raudat ta ƙyalƙyale dashi tare da nufar
hanyar fita sai kuma ta karya kwana ta nufi Bedroom ɗin Mommy.

Khausar kuwa garin zata karya kwana ta nufi Bedroom din Mommy santsin ruwan dake ƙafarta da kuma
santsin tlyes ya jata tayi baya Suuuuuu ta faɗi a ƙasa kana towel ɗinta ya since ya zame yayi ƙ...!

Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama 1k ne kacal 0661110170
GTBank AISHA ALIYU GARKUWA.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

34
*LITTAFIN SAKAYYAH DAI NA KUDINE KO KIN GANSHI A WASU WURAREN DA BA WURINA BA TOH NA
SATANE KI BIYA KI KARANTA CIKIN AMINCI BABU HAƘƘIN WANI A GANKI LITTAFIN SAKAYYAH 1K NE
KACAL DUK DA YAWANSA DA DAƊINSA DUBU ƊAYA NEFA KACAL, ki biya dubunki ɗaya ki karanta
maimkyau ba sallake-sallake babu kin samu wasu PAGE ɗin baki samu wasuba ki karanta abinki one by
one tura kuɗin samun damar karantawa ta asusuna na GTBank. 0661110170 GTBank AISHA ALIYU
GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 sai in tura miki karanta lfy lafiya.
Mu guji yaƙin wani duk ƙanƙantarsa domin na watan nan dai na Allah ya isane atoh*

34

Towel din na sincewa ya zame yayi ƙasa, manyan caɓɓullenta masu haske da sheƙi suka bayyana a fili,
yayinda ita kuwa ta zame tayi ƙasan cikin jin zafi da raɗaɗi ta guiwowinta da suka bugu tayis ɗin ta
runtse Idanunta cike da raki tace.

“Washhh! Allah Mommy na”.

A can cikin daki kuma

Kallon Asma'u Mommy dake ninke kaya tayi kana tace.

“Asma'u ki kai masa abin taɓa wa yanzu zan fito”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh Mommy”.

Kana ta fita.

Moddibo kuwa baki daya abinda ya faru akan Idanunsa ya faru cikin wani irin yanayi ya ware manyan
idanunsa dake ɗauke da launin Ja akan tantsama-tantsaman caɓbulenta da suke tsaye cirko cirko dasu
masu masifar haske da sheƙi kana kansu sunyi ja sai sheƙi da ɗaukar ido suke haka zalika har ramin
cibiyar ta yana ɗan iya hangowa.

Atake yaji zuciyarsa da A ɗinsa sunyi wani irin harbawa da masifaffen ƙarfi tamkar zasu fito waje ya taka
rawa.

Cikin wani irin sauri ya matse ƙafafunsa da masifan ƙarfi kana ya shiga ƙoƙarin rintse idanunsa da don
janyesu daga kan abinda ke ƙoƙarin tafiya da nutsuwarsa da kuma numfashinsa amma baki ɗaya ya kasa
janye Idanunsa dake kan manyan caɓɓullen ta dake neman zautar dashi bare yayi nasarar kawar da
kansa.
Akuma dai-dai lokacin idanun Asma'u data fito yanzu suka sauƙa akan Khausar dake kwance ƙasa cikin
sauri ta nufi kanta tana faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n sannu Khausar”.

Khausar kuwa jin Muryar Asma'u yasa tayi saurin ɗago kanta Atake Idanunsu suka sarƙafe dana Moddibo
daya wani irin zuba mata mayatattun idanunsa da suka sake canza launi ko ƙyiftawa ba yayi sai lips dinsa
da suka fara rawa kar-kar.

Cikin wani irin yanayi na tsananin kunya da zafi Khausar tayi saurin janye Idanunta daga nasa ta mayar
ganinta dai-dai inda ya tsiwara Ido cike da masifaffen kunya ta rintse Idanunta ganin yadda ya tsare.

Ƙirjinta Ido musamman saman Nipples ɗinta da sukayi ja suna tsaye cir dasu tamkar zasu tsole masa ido.

Asma'u kuwa na ƙarasawo tayi saurin sanya hannunta tare da ɗagota kana tace.

“Subhanallah Khausar sannu”.

Cikin wani irin karfi mai haɗe da kunya Khausar ta janyo towel ɗin sama tare da miƙewa da gudu ta
koma Bedroom ɗinta yayin da zuciyarta ya cigaba da bugawa da masifaffen ƙarfi kana gaba ɗaya ilahirin
jikinta na rawa babu kalmar da take maimaitawa face Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n, jingina bayanta da
jikin wodurob tayi cikin tsanananin kunya da takaici gami da tsoro still jikinta na cigaba da rawa.

Asma'u kuwa bayan Khausar tabi ganin yanda ta jingina da jikin wodurob baƙi ɗaya ilahirin jikinta na
rawa yasa cikin sanyin murya Asma'u tace.

“Sannu Khausar”.

Kallonta kawai Khausar keyi.

Asma'u kuwa murmushi ne ya subce mata ganin yanda gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa, sai kuma ta
tuna yanda. Moddibo ya zubawa Khausar ido yana kallon Breast ɗinta tamkar wani zautacce sai kuma ta
tuna yanda jikin Khausar ke rawa yana wani irin tsuma bisalamu gani take kamar mafarkine haka ne yasa
Asma'u sakin.

Dariya tare ƙyalƙyalewa har tana dafe gefen cikinta, kana ta cigaba da ƙyalƙyala dariya tana nuna
Khausar da hannu.

Khausar kuwa Ido ta zubawa Asma'u madadin haushin dariyar da Asma'u ke mata da ji ciwon
guiwowinta keyi ta sinci kanta da zubawa Asma'u ido kana aranta tace Allah sarki Asma'u rabon da inga
dariyar ki haka tun kan a sace Yah Jameel sai yau, hakan yasa ta gyara tsayuwarta tare da sake ɗaure
towel ɗinta da kyau Asma'u kuwa dariya ta cigaba dayi harda hawaye da zaran ta tuna yanda Moddibo
ya kafe kirjin Khausar ɗin da ido da kuma yanda Khausar ta zare ido sai ta sake ƙyalƙyalewa da dariya.
Cikin sanyin murya me ɗauke da tsoro da kuma kunya tace.

“Kin gama dariyar!?”.

Kallon ta Asma'u tayi still tana riƙe da cikinta kana da murmushi afuskarta tace.

“Ikon Allah lallai Yah Moddibo Yayi farin gani”.

Harara Khausar ta watsa mata tare da tura bakinta kana tace.

“Ɗan Iska kawai harda wani tsayawa ya tsura min ido sai kace maye, wato ya samu gani na bati ko? toni
dai Yaseen ban yafe ba ato”.

Dariya Asma'u ta kuma ƙyalƙyalawa dashi ganin yanda Khausar tayi kicin-kicin da fuska kana har zuwa
lokacin jikinta bai daina rawa ba.

Ahankali Khausar ta zauna gefen gado tare da kallon Asma'u da har zuwa lokacin fuskarta ɗauke da
murmushi tace.

“Tukunna ma wai meye kawoshi gidan mu har cikin falon Mommy na!?”.

Zama Asma'u tayi agefenta tare da cewa.

“Wajenki yazo”.

Wani kallo Khausar ta mata tare da ɗage girarta na dama tace.

“Wajena kuma lallai ya kama tashar da ba Passenger. Dan wallahi babu inda zan fita ya samu damar ƙare
min kallo dan yanzu ko ariga ya gani nasan zai iya siffanta kamannin su”.

Wani sabon dariya Asma'u ta fashe dashi tare da faɗin.

“Um-um Fattanah banda dai sharri kallon second nawa ya musu da har zaki ce zai iya siffanta wa a'a kin
manta drawing zaiyi kamar ba shiba”.

Duka Khausar ta kai mata cikin Sauri Asma'u ta kauce tare da cewa.

“Ke kuwa abin kallo ya samu ai dole abawa Ido hakkinsa”.

Anutse Mommy ta fito daga Bedroom tare da kallon Moddibo da har zuwa lokacin Idanunsa ke kan inda
Khausar ta faɗi cike da kulawa tace.

“Maraba Moddibo”.

Jin muryan Mommy ya ratsa dodon kunnensa yasa yayi saurin lumshe idanunsa da sai yanzu ya samu
dawowa nitsuwarsa matse jikinsa yayu tare da jan ajiyar zuciya kana ahankali ya fesar da wani numfashi
mai Masifarr nauyi mai ɗauke da wani irin yanayin na tsananin matsuwa.
Kana cikin sanyi ya sake sunkuyar da kansa ƙasa yayin da ya sake matse muhallinsa da yaji yana neman
fallasashi cikin sanyun murya yace.

“Ina yini Mommy ya gida fatan mun same ku lafiya? Ya hakurin rashin Ramadan”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.

“Lafiya lau Alhamdulillah haƙuri ya zama dole”.

“Allah ya jinƙasa da rahama”.

“Amin ya Allah, ai Lamiɗo ya gayamin kunzo ta'aziyar ne kuka samu labarin Jameel shiyasa baku isoba”.

Cikin nitsuwa yace.

“Eh”.

Sassayan numfashi Mommy ta fesar kana tace.

“Ya karin haƙurinmu.da wajensu Ummi?”.

Kansa a ƙasa yace.

“Alhammadullih. Ummi na lafiya tace ma agaisheki".

Mommy kuwa kallon falon tayi tare da Kallonsa kana tace.

“A'a Ina su Asma'u kuwa?”.

Cikin sauri Raudat dake tsaye bayan Kushin tace.

“Mommy Adda Asma'u tana ɗaki Addah Khausi kuma tana ta dariya”.

Jin haka yasa Mommy ta ɗaga sautin Muryanta tare da cewa.

“Asma'u”.

Cikin sauri Asma'u ta fito tare da cewa.

“Na'am Mommy”.

Ahankali Mommy ta kalleta tare da cewa.

“Asma'u kinzo kin bar baƙo shi kaɗai ko ruwa baki kawo masa ba?”.

Cikin sauri ta nufi hanyar kichen tare da cewa.


“Toh Mommy bari na kawo masa”.

Ta faɗa tare da shiga kichen ta buɗe fridge kana ta ɗauki Plate tasa masa ruwa da exotic ta fito ta ajiye
masa agabansa kallonta Mommy tayi tare da cewa.

“Ina khausar kuma?”.

Satan kallon idon Moddibo Asma'u tayi sai taga hankalinsa na kan inda Khausar ta faɗi har yanzu bai cire
idoba, cikin ƙasa da murya tace.

“Mommy khausar fa tace baza ta fito ba!”.

Kallon mamaki Mommy tayi mata kana tace.

“Ha'a baza taxo ta Gaishe da Malamin su ba kuma?”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare Da yin ƙasa da kanta tace.

“Eh Mommy faɗuwa tayi kuma taji ciwo a Ƙafarta”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da faɗin.

“Toh bari Inje in ganta”

Anutse Mommy ta nufi ɗakin bakinta ɗauke da sallama ta shiga a inda Asma'u ta barta azaune anan
Mommy ta shigo ta sameta bata ko motsa ba.

Ahankali Mommy ta zuba mata ido ganin yanda ta lumshe Idanunta tare da rungume hannunta aƙirji har
zuwa lokacin towel ne ajikinta kana zuciyarta na cigaba da bugawa da masifar ƙarfi cikin sanyi murya
Mommy tace.

“Khausar baza ki fito ki Gaishe da Malamin kuba”.

Langwaɓar da kai Khausar tayi tare da Shagwaɓe murya kana tace.

“Mommy faɗuwa fa nayi kuma naji ciwo aƙafa na bazan iya fita ba”.

Girgiza kai Mommy tayi tare da ɓata fuska kana tace.

“A'a sai kin fita ya za ayi Malamin ki yazo kuma kice baza ki fita ki Gaishe sa ba kema kinsan bai dace ba!
Kuma ma ta'aziyyar Ramadan yazo mana fa”. Ta faɗi hakan dan ita a tunaninta gaisuwar Ramadan ɗin
yazo musu.

Saurin Kallonta khausar tayi tare da yin Rau-rau da ido Muryanta na rawa tace.

“Don Allah don darajar Manzon Allah (S.A.W) Mommy ki bari ba sai nafi ta ba. Ni dai gaskiya bana son
fita Mommy kawai ki barni ai mun gaisama fa”.
Cikin tsira mata ido Mommy ta jingina bayanta da jikin ƙofar kana babu walwala afuskarta tace.

“Kin tabbata?”.

Kai ta gyaɗawa Mommy ba tare da tace Uffanba saima ƙasa da tayi da kanta tana wasa da yatsun
hannunta tare da mgnar zuci.

Aiko mungaisa tunda har abuna ya gani.

Dai-dai lokacin Asma'u ta shigo kallon Mommy tayi kana ta kalli Khausar dake wasa da yatsun hannunta
tace.

“Mommy faɗuwa tayi agaban sa kuma har towel ɗinta ya since”.

Cikin sauri Mommy ta kalli Khausar tare da cewa.

“Subhanallahi to keme Khausar bakya girma ya za ayi kiyita guje-guje daga ke sai towel wannan abun
kunyar har ina ace ke dai har abada bazaki nitsuba mitsee Allah ya kawo miki nitsuwa”.

Marairaice fuska Khausar tayi tare da tura ƙaramin bakinta kana tace.

“Mommy Raudat fa nabi zan kama shegiyar yarinyar nan taja na fadi agaban wani kato ai yau saina mata
dukan tsiya”.

Girgiza kai Mommy tayi tare da gyara tsayuwar ta kana tace.

“A'a babu ruwan Raudat ai da kin bari sai abita ahankali a lallaɓa ta amma yanzu kin jawa kanki kunyar
babu gaira babu dalili saboda shirmen ki na banza da wofi sakariyar banza ke har abada bazaki dena
rawar kaiba”.

Fuska Khausar ta ƙwaɓe tare da tura madedecin bakinta gaba still Hannunta na ƙirjinta arungume gani
take da zaran ta cire hannunta Moddibo zai sake ganinsu.

Mommy kuwa kofa ta nunawa Khausar babu walwala atare da ita tace.

“Ki tashi kije ku gaisa ai baza ma zakiyi ba da zaran kun gaisa zaki dawo”.

Ware ido Khausar tayi tare da Rau-rau da ido Atake hawaye suka fara zubowa daga Idanunta Shar-shar-
shar cikin muryan kuka tace.

“Allah Mommy ni dai bazan jeba ya ganni ahaka wallahi kunyar ganinsa nakeyi, kuma shima nasan yanzu
kunyar gani na yake dan Allah ki barni”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da cewa.


“Toh shikenan”.

Sai kuma ta maida kallonta kan Asma'u dake murmushi ƙasa-ƙasa tace.

“Asma'u amma lafiya dai ko?”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare da ƙaƙalo murmushi tace.

“Eh lafiya Mommy ba komai bakomai dama munje unguwa ne shine muka biyo ta nan ɗin”.

Ta faɗa dan tasan da zaran ta sanarwa Mommy dalilin zuwansu zata faɗawa Ummi Ummi kuwa zata
hanasu bin cike akai.

Asma'u kuwa kallon Khausar dake ta faman damƙe towel tayi cikin sigar zolaya tayi ƙasa da murya yanda
Mommy dake fita daga ɗakin baza ta jiba tace.

“Toh Madam Fattanah ai sai atashi asa kaya kada ahukunta towel da baiji ba bai gani ba”.

Harara Khausar ta watsa mata tare da tura bakinta kana tace.

“Ai wallahi ya kalli Wuta bal-bal dan ba yafewa zanyi ba kawai ya cuceni ya riga mijina kallon abu mai
daraja da farashi”.

Ware ido Asma'u tayi tare da ƙyalƙyalewa da dariya kana cikin ƙasa da murya tace.

“Wallahi Khausar kinfi ƙarfina”.

Saurin juyowa Mommy dake bakin kofar tayi tana kallon Asma'u domin ita ma rabon da taga dariyar ta
tun kafin ɓatan M Jameel Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.

“Asma'u kin bar Moddibo shi kaɗai afalo kuma kinga Khausar ba fita zata yiba taho mu fita”.

Ahankali Asma'u ta tsaida dariyar ta tare da gyaɗa kanta cikin Muryan ta dake ɗauke dariya tace.

“Toh Mommy”.

Sannan ta juya ta fiye bayan ta ɗagawa Khausar hannun.

Ahankali Asma'u ta fita fallon tare da kallon Moddibo daya tsirawa waje ɗaya ido still ƙafafunsa amatsa
yayin da Lips ɗinsa suka motsawa ahankali.

Cikin sanyin murya Asma'u ta tsaya daga gefensa kana tace.

“Yah Moddibo Khausar fa tace baza ta fito ba”.


Ajiyar zuciya ya sauƙe cikin muryarsa da yasake sanyi fiye da da yace.

“Toh shikenan bari mu tafi”.

Ya ida maganar tare da miƙewa.

Dai-dai lokacin Mommy ta ƙaraso wanjesu cikin sauri yayi ƙasa da kansa kana yace.

“Toh Mommy bari mu tafi”.

Cike da kulawa Mommy tace.

“Toh mungode Moddibo Allah yasaka da alkhairi ka gaida Mutanen gida”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Zasuji”.

sannan suka fice.

Acan gidan Hajiya Lami kuwa zaune suke tare da Samira afalon ƙaramin tsaki Hajiya Lami taja tare da
kallon Samira kana tace.

“Boka Kar'uzu yace tun ranan can zai zo gashi har yanzu bai zoba yau kwana uku kenan”.

Kai Samira dake sanye cikin riga da skirt na Atamfa ɗinki ya zauna ɗass ajikinta saman Breast ɗinta sun
fito ta waje ta gyaɗa tare da zare ido cike da damuwa tace.

“Toh Mommy Meyesa Kar dai ya fasa bazai yi mana aikin bane?”.

Girgiza kai Hajiya Lami tayi kana tace.

“Kada ki damu gobe da wuri zan koma wajensa”.

Cikin sauri Samira ta gyaɗa Kai tare da faɗin.

“Aikuwa dai Mommy gwara ki koma ayi magana domin Moddibo shine rayuwata bazan taɓa rayuwar
farin ciki ba idan har baya tare dani”.

Kafin Mommy tace wani abu suka jiyo sautin wata mahaukaciyar dariya mai kama da gurnani da kuma
kukan baƙar jaka.

Cikin sauri da alamun razani suka juya tare da kallon bakin ƙofa wani gauron numfashi Hajiya Lami ta
sauƙe tare da washe baki cike da farin ciki tace.
“Maraba da zuwa Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu uban mugaye tsinanne
Uban tsinannun yanzu muke maganar ka”.

Boka Kar'uzu kuwa cike da jin daɗin kirarin da ta masa ya sake kecewa da wata mahaukaciyar dariya me
gigita lissafi kana cikin muryarsa mara daɗin Amo yace.

“Nayi tafiya ne Aljani ɗan Jaƙunana mai ƙaho da jela ya nemi ganina abirnin Sin naje nayi kwana uku
yanzun dawowa na nace barin nazo in fasa ƙuruciya”.

Cike da farin ciki Hajiya Lami tace.

“Toh sannu Boka”.

Cikin razananniyar muryarsa mai sa ɗimuwa yace.

“Ina ne masauƙi na bana son ɓata lokaci”.

Cikin sauri Hajiya Lami ta mike tare da ratsa gefensa ta wuce sannan ya biyo bayanta kai tsaye BQ su
tanufa dashi har bakin ƙofar ta ƙarasa tare da cewa.

“Ga nan masauƙin ka sannan yanzu zan turo Samira ta kawo maka abinci.

Kai ya gyaɗa kana cikin tsawa yace.

“Maza ki juya ki koma da baya har ki isa ɗakin ki”.

Da sauri ta juya ta fara tafiya shi kuma ya buɗe ƙofar ɗakin ya shiga.

Ido ya tsirawa dakin babban falo dake ɗauke da kujeru bakwai masu kyau kana ga Canies Capet a ƙasa ga
TV plasma dake manne da bango ga kuma Cottons masu kyau jinjina kai yayi tare da nufar Bedroom din
nan ma Komai akimtse ga Lafiyayyan Italian bed da sha shimfiɗa na alfarma Atake ya kece da wata
mahaukaciyar dariya tare da bubaga ƙafarsa a ƙasa acikin ransa yace yau Nine Boka Kar'uzu acikin
wannan ƙayataccen masauƙi na alfarma tare da Santaleliyar budurwa tunda yake bai taɓa samun
Santaleliyar budurwa da zaisa fasa ɗanye budurcinta kamar wannan ba, gata ɗanya sharaf ta nuna da
kyau tuna hakan yasa ya sake kecewa da wata dariya

Hajiya Lami na shigo falonta ta sauƙe ajiyar zuciya mai nauyi kana cike da farin ciki ta kalli Samira data
zabga Uban tagumi da hannu bibbiyu tace.

“Yawwa Samira ɗauki abincin dake Warmers ɗin can ki kai masa”.

Cikin yanayin rashin gamsuwa da damuwa Samira ta ɗago kanta tare da kallon Hajiya Lami tace.
“Mommy ki kallin jikinsa kuwa tamkar mahaukaci har wani bashi-bashi da warin kwata yake sai wani
shegen turare mai masifar hawa kai dake tashi ajikinsa sannan kinga kansa kuwa!?”.

Sake baki Hajiya Lami tayi tana kallonta kafin tace.

“In dai har kina son burinki ya cika to ki rufawa kanki asiri ina ruwanki da shigarsa ta mahaukata ke dai
burinki ya cika”.

Numfashi Samira ta fesar tare da cewa.

“Amma Mommy tsoro nake ji kinsan ban taɓa yi ba kuma naji wata ƙawarmu da tayi Aure tace da zafi”.

Girgiza kai Hajiya Lami tayi tare da sassauta murya tace.

“Ƙarya ta miki ba wani zafi sannan kuna yi da safe zai baki magani ba wani zafi da zakiji saima daɗi in ba
sa'a ba ko an gama na maganin ma kice ya ƙara miki”.

Ta ida maganar tana ƴar dariya irin talalatattun iyaye marasa kan gado.

Girgiza Kai Samira tayi cikin tsinkewar zuciya da fargaba tace.

“Ni dai wallahi Momcy ina tsoro gaskiya zuciyata tsinkewa take”.

Harara Hajiya Lami ta watsa mata sai kuma tayi saurin sassauta Muryanta tace.

“Kenan bakya son Moddibo sannan bakyason burinki ya cika tunda har kike wannan ɗari-ɗarin”.

Cikin sauri Samira ta kalleta kana tace.

“A'a Mommy Ina son shi mana, sannan ina son in auresa kinsan bani da burin daya wuce in Mallakesa
amatsayin mijina”.

Gyara tsayuwa Hajiya Lami tayi kana tace.

“Toh da dai yafi miki ki cire duk wani tsoro da fargaba”.

Cikin sanyin ta gyaɗa kai.

Juyawa Hajiya Lami tayi jin wayarta na ruri tana ɗagowa taga Hajiya Bunayya murmushi tayi tare da
Picking ta kai kunnenta.

Batare da Hajiya Bunayya tayi sallama ba tace.


“Hajiya Lami wai har yanzu Boka Kar'uzu bai zoba!?”.

Dariya Hajiya Lami tayi kana tace.

“Yazo amma bai daɗe ba kinga yanzu na nake ƙoƙarin tura ƴar taki ma amma ta tsaya nuƙu-nuƙu wai
tsoro takeji”.

Fuska Hajiya Bunayya ta ɓata tare da cewa.

“Maza bata wayar kaji min shashashar yarinya”.

Miƙawa Samira wayar Hajiya Lami tayi kana tace.

“Toh gata”.

Cikin sassauta murya da lallashi Hajiya Bunayya tace.

“Samira ƴar Albarka kada ki damu kije ba zaki ji zafi ba, kuma yana gamawa zai baki magani ki rinƙa
tsarki da shi zaki ji lafiya lau baki da wata matsala”.

Cikin rawan murya da tarin damuwa Samira tayi rau-rau da ido kana ta kalli Hajiya Lami dake sakar mata
murmushi ta haɗiye wani abu da kyar kana tace.

“Ummah to Budurcina fa idan nayi Aure Moddibo ya sameni ba amatsayin cikakkiyar budurwa ba fa?”.

Cikin sauri Hajiya Bunayya ta katseta da cewa.

“Kaji shashasha Sokuwa yaushe zai gane ai Boka zai baki maganin da zai haɗe Budurcinki ki dawo har
kinfi da ma”.

Samira kuwa cikin tsinkewar zuciya da tsoron abinda zai faru tace.

“Toh shikenan Ummah amma wallahi tsoro nakeji kada yamin da zafi”.

Sake sassauta murya Hajiya Bunayya tayi tace.

“Haba Samira kada ki bani kunya mana, ina miki kallon wayayyi ya Meye abin tsoro yara nawa da basu
kaiki shekarunki ba aka musu aure har suka haihu amma ke akan ƙalilan abu kike tada hankalin ki”.

Siririn tsaki Hajiya Lami taja tare da Amsar wayar ta katse kana ta fuskanci Samira Babu walwala atare da
ita tace.

“Kinga fa Samira kada ki ɓata min lokacin sai kace wacce za akai anyanka Meye abin tsoro acikin dan
wannan abin amma kin tsaya rawan jiki na babu gaira babu dalili ke adole tsoro kike ji”.
Jin abinda Hajiya Lami tace.

Yasa Samira tayi narai-narai da Ido jikinta na kyarman tsoro tace.

“Shikenan Mommy kada afasa zanje amma wallahi ni dai ina tsoro kada ya kasheni”.

Sassauta murya Hajiya Lami tayi tare da shafa kanta tace.

“Kada ki damu ai na faɗa miki babu zafin da zaki ji yanzu kije kiyi wanka”.

Fuska Samira ta yamutse tare da taɓe baki tace.

“Lallai ma Mommy wani wanka zanyi bayan shi wari yake nikam na tafi kuma wallahi idan naga bazan iya
ba guduwa zanyi”.

Ta faɗa tare da shiga kichen ta jera kayan abincin ta fita kai tsaye BQ ta nufa tana zuwa ta tura ƙofar ta
shiga.

Dai-dai lokacin Boka Kar'uzu ya fito daga Bedroom din ya tsaya atsakanin falo da Bedroom ya ƙura mata
Ido kana ya kece da wata mahaukaciyar dariya na nasara.

Cike da tsoro da tsinkewar zuciya Samira taja baya zuciyarta na bugawa da wani masifaffen ƙarfi yayinda
zuciyarta ke tashi saboda wani hamami-hamami gafi-gafi da yake.

Cikin sauri ya nufi inda take tare da karɓan Tray abincin hannunta ya ajiye akan stool dake tsakiyar falon
kana ya kamo hannunta na dama tare da Ɗaurawa akan ƙazamtaccen abunsa kana yace.

“Kinji ko wannan shine mahaɗin aikin ki kuma cikar burinki”.

Zare ido Samira tayi cike da tsoro jin yanda abu mai kama data baƙar jaka ke tsaye lokaci ɗaya jikinta ya
shiga rawa da masifar ƙarfi yana bada sautin dib-dib.

Girgiza mata kai yayi kana cikin muryarsa mara daɗin amo yace.

“Ki kwantar da hankalin ki”.

Ya faɗa tare da janyota jikinsa ya rungumeta tare da tura kabcecen hannunsa acikin rigarta ya kamo
caɓɓullen da ƙarfi, cikin sauri ya runtse Idanunsa tare da cewa.

“Wayyo!Tabbas burinki zai cika domin Dan Ƙundalo na tare damu tabbas dashi za ayi wannan aikin mai
tarin ganima”.

Samira kuwa yana matseta ajikinsa taga sun koma Bedroom.


Lokaci ɗaya jikinta ya fara rawa cike da masifar tsoro daya lulluɓe ta cikin rawan murya me ɗauke da
tashin hankali tace.

“Nifa tsoro nakeji”.

Cikin wani irin yanayi daya fara shiga ya kece da mahaukaciyar dariya daya bayyanar da korayen
haƙoransa masu kama da gantsakuka kana ya buɗe wangamemen bakinsa wanda laɓɓansa na ƙasa duk
ya gutsutstsire yayi ja ba kyan gani yace.

“Kada ki damu ba zaki ji zafi ba kicire tsoro ki samu biyan buƙatar ki”.

Ƙasa cewa komai Samira tayi amma baki daya ilahirin jikinta rawa yake Shi kuwa Fatarin jan ƙyallen dake
jikinsa ya ɗaga sama.

Samira kuwa cikin sauri ta toshe hancinta da masifar ɗoyin da yake kana ta runtse Idanunta ganin yanda
zugururunsa mai kama dana jaki ke harbin Iska yana tsirtar da wawwaran ruwa.

Dariya yayi sai dai wannan karon bamai ƙara bane kana yace.

“Buɗe Idonki ki gani wannan shine zai zama cikon burinki na mallaka miki shi ki juya shi son ranki
wannan shine zai zama makamar aikin ki”.

Girgiza kai Samira keyi cike da tsoro da tashin hankali baki ɗaya ilahirin jikinta rawa keyi duk da cewa
bata taɓa kallon surar Namiji ba amma tasan baza ataɓa samun namiji mai irinsa ba mutun kamar jaki
ko doki kama aljani.

Bai damu da yanayin tsoron da take ciki ba ya sanya hannunsa ya keta rigar dake jikinta kana ya kai
wawakeken bakinsa kan kirjinta ya kamo ya zuƙa da ƙarfi.

Cikin tsanananin jin zafi Samira ta runtse Idanunta domin ji tayi tamkar ya zuƙo wani abu daga
ƙwaƙwalwar kanta kana Atake taji wani masifaffen abu ya diro mata.

Cikin wani irin yanayi na begen tsafi daya cusa mata, tasa tafin hannunta acikin dugujejen sumar kansa
mai kama da kazar bingi-bingi saboda yanda yayi cibir-Cibir ga Bushesh-shen ganye ta tura yatsunta aciki
duk da kuwa tsoro da take amma tsafin da ya mata ya danne tsoron.

Cikin wani irin yanayi Boka Kar'uzu ya miƙe tare da yage Fatarin jikinsa yayi wurgi dashi kana ƙwayoyin
Idanunsa suka sauya launi zuwa wani iri su ba baƙi ba su ba kaba domin duk lokacin da zaiyi Sex da
Shaiɗanun aljanunsa sukeyi.

Samira dake kwance cikin tsanananin tsoro take kallon abun Jaki ta haɗiye wani abu mai masifar ɗaci.
Hawa gadon Boka Kar'uzu yayi tare da yaga Skirt din dake jikinta murmushin mugunta yayi dan sanin
cikakkiyar budurwa wacce bata taɓa kusantar wani ɗa na miji ba.

Murmushin jin daɗin yayi tare da kamo lalatarsa dake tafe da gazantaccen yanayi ya nufeta tare
lalatata da duka ƙarfinsa duk da yanayin ƙanƙantar ta.

Cikin wani irin Masifaffen zafi da raɗaɗi da azaba mai gigitarwa daya ratsata tun daga babban yatsanta
har ƙwaƙwalwar kanta ta saki wani azabebben Ihu mai tafiya da numfashi.

Cikin sauri Hajiya Lami dake zaune a falonta ta miƙe cike da farin ciki ta ƙyalƙyale dariya kana tace.

“Alhamdulillah aiki ya kammata”.

_(Wa'iyazi billah shashashar Uwa amaimakon taji baƙin ciki da takaici Ƴarta ta rasa abu mafi
muhimmanci da daraja arayuwarta amma saita ɓige da dariya burin ƴarta zai cika bisa hanyar saɓon
Allah”.

Acan ɓangaren Samira kuwa Baki ɗaya ilahirin jikinta rawa yake yayin da hawaye ke kwaranya daga
idanunta.

Boka Kar'uzu kuwa wani irin kuka da gurnani mai kama da kukan halittun daji iri daban daban yake tunda
yasa kansa ajikinta yake wani irin kumbura yana sake girma da zaran ya ritsata zataji har tsakiyar
maƙogoronta saboda abu na shaiɗanu cikin tsanananin farinciki da yake ji ya cigaba da kukan jaki yana
haɗawa dana kare yana keta ƙuruciyarta kana yana sake lalata mata ƙuruciya da gazantaciyar ha'ittarsa
da buɗata lokaci ɗaya.

Samira kuwa baki ɗaya ta fita hayyacinta cike da azaba ta suma Boka Kar'uzu kuwa bai damu da hakan
ba yasa tafin hannunsa ya ɗagota tare da manna wargajejen bakinsa akan nata kana ya sake azama
ajikinta wani dogon numfashi Samira taja cike da fitar hayyaci ta zuba Idanunta acikin nasa wanda kallo
ɗaya zaka musu kasan bashi kaɗai bane yana tare da aljanu. cikin azaba ta shiga ƙoƙarin janye bakinta
acikin nasa amma ta kasa haka ya cigaba da lalatata cike da mugunta, a haka numfashinta ya ɗauke ta
sake suma.

Acan ɓangaren Moddibo kuwa kwance yake rub da ciki akan makeken gadonsa Idanunsa abuɗe sun sake
ƙanƙancewa kana sunyi ja da zaran ya lumshe idanunsa kyawawan caɓullen Khausar yake gani ciki. Wani
irin yanayi yasa hannunsa na dama ya damƙe saman maransa tare da taune Lip ɗinsa na ƙasa.

Aransa ya tuna yaushe rabon daya kasance cikin irin wannan yanayin tun kafin a sace J ɗinsa yau
Kimanin wata biyu kenan amma yau tunda Idanunsa sukayi arba da Khausar A ɗin sa ya miƙe ya tsaya
wani irin masifaffen Sha'awa ya taso masa juyi yake akan gado yana murƙususu jin wani irin azabebben
ciwon mara baki daya bashi da damar runtse Idanunsa daya runtse zai buɗe saboda ƙirjin Khausar dake
masa gezo.

Aɓangaren Boka Kar'uzu kuwa haka ya cigaba da lalata Samira Yana cakuɗa ta domin ji yake tamkar ana
ƙara masa ƙarfi da kuzari ne Samira kuwa data suma zata sake farfaɗowa da kanta sabida azaba.

Miƙewa Boka Kar'uzu yayi tare da sakin kukan kuliya.

Cikin tsanananin azaba Samira ta farfaɗo tare da ƙwalla ƙara da muryanta daya dishe da kuka kana ta
sake sumewa.

Boka Kar'uzu kuwa haka ya cigaba da abar jakarsa sai yayi kamar zai barta sai ya sake addabarta still
hannunsa na kan ƙirjinta yana dirzawa da azaban ƙarfi.

Abu tun misalin ƙarfe Sha ɗaya na dare boka Kar'uzu ke azabtar da Samira har Misalin ƙarfe shida na safe
dai-dai lokacin ta sake suma haka ya cigaba da abu daya duk bedsheet din ya jiƙe da jini da Sparm
miƙewa yayi ya fara zubar da wani irin abu daka gani zakasan bana mutum kaɗai bana da akwai na
aljanu aciki tun yana zubawa acikin jikinta har ya jakar abunshu waje yana bin duk ilahirin jikinta dashi
zuwa lokacin har ta sake farfaɗowa sai dai bata da kataɓus ɗin motsa jiki ta ta dawo tamkar gawa sai
numfashin kawai da take kana tana kallon yanda yake shash-shafa jikinta zuwa saman ƙirjinta da taji
tamkar ana soka mata allura runtse Idanunta tayi da karfi asanda yakai hannunsa inda ya illatata yana
shafawa saboda wani azabebben zafi har tana jin yanda yake kumbure saboda azabar daya shayar mata.

Ahankali ta buɗe Idanunta ta kalli yanda hannunsa na dama ke riƙe da abun yana fesa mata
ƙazamtaccen ruwa.

Ɗaya hannunsa kuma yana shafa ko ina na jikinta har sumar kanta.

Zare ido tayi ganin ya saita abakinta sai dai bata da kataɓus ɗin motsawa kanta ya ɗago tare da buɗe
bakinta ya fara zazzaga mata abin dake zuba kamar an buɗe Famfo rufe bakinta tayi abin na bin gefen
bakinta yana zuba bata sha ganin haka yasa boka Kar'uzu toshe hancinta bakinta ya fara ɗurawa.

Atake ta fara haɗiye wa got-got-got yakai kimanin minti ashirin yana matsa mata saida yaga cikinta ya
ciko tukunna ya barta Atake tayi wani irin gyatsa.

Acan Falon Hajiya Lami kuwa tsaye take Atsakiyar falon cikin sanyi ta kalli Agogon dake manne Atsakiyar
falon dake nuni da ƙarfe 8:00am baki ɗaya ta fara shiga damuwa gashi ta daina jiyo koda sautin Kukanta
ne da sauri tabi shawarar zuciyarta tare da fita ta nufi BQ tana isa ta tura ƙofar falon shiru ba kowa sai
Farantin abinci dake kan Centre table kai tsaye Bedroom din ta nufa kana ta tura ƙofar ɗakin ta shiga
Idanunta suka sauƙa akan Boka Kar'uzu dake zaune akan gado tsirara hannunsa riƙe da jagularsa d yana
kaɗawa har lokacin bawai ya gaji da ita bane kawai dai ya haƙura ne.

Cikin sauri ta maida Idanunta kan Samira dake kwance tsirara tana maida numfashi da gudu ta nufi kanta
cikin tsanananin tashin hankali tace.

“Samira!, Samira!!, Samira!!!.

Wayyo nashiga uku! Boka Kar'uzu kaddai ta mutu!?”.

Cikin ɗaga sautin murya yace.

“Ba abinda ya sameta kada ki taɓa ta³ yanzu nan zan haɗa mata magani maza kawo min ruwan zafi”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh”, Kana ta fice da gudu tana isa kichen ɗinta ta ɗauko Flaks din ruwa zafi kana ta dawo tare da miƙa
masa still suna yanda ta barsu Buɗe Flaks din Yayi tare da tsiyayan ruwan amurfin Flaks din.

Hannunsa ya ɗaga sama Atake wani ƙullin magani ya faɗo kan hannunsa budewa yayi tare da juyewa
acikin ruwan zafin Flaks din.

Zare ido Hajiya Lami tayi cike da mamaki ganin yanda ruwan ke ta farfasa ahannunsa.

Miƙewa yayi tare da isa kan Samira ya ɓude ƙafafunta.

Cikin sauri Hajiya Lami ta kalli fuskar Samira da hawayen azaba ke zuba kana ta kalli gabanta daya canza
siffa ya wani irin kumbura.

Boka Kar'uzu kuwa ruwan maganin ya dinga ɗiba yana shafa mata a wurin raunin sannu Ahankali Samira
ta fara sauƙe Ajiyar zuciya tana jan numfashi kamar ƙiftawa da Bismillah ta Mike ta zauna tare da kallon
Hajiya Lami.

Cike da tausayawa Hajiya Lami tace.

“Sannu Samira”.

Numfashi Samira ta fesar kana tace.

“Yawwa”.

Kallon Samira Yayi tare da ƙurawa gabanta Ido kana ya lashe wangamemen laɓɓansa yace.

“Ina yake miki ciwo!?”.

Girgiza kai tayi tare da faɗin.


“Babu”.

Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauke tare da cewa.

“Bari in kawo muku abinci kuje kuyi wanka tukunna”.

Boka Kar'uzu kuwa Girgiza mata dugujejen kansa yayi kana yace.

“A'a ba yanzu za tayi wanka ba sai anjima inaso wannan abin ya bubbushe ajikinta domin shine mahaɗin
aikin dan yadda yake ƙyalli a jikinta haka Modibbo zai rinƙa ganin ƙyallinta kuma dole shi da kanshi zai
nemota”.

Cikin sanyin Murya Hajiya Lami tace.

“Toh yanzu sai yaushe Samira bakya jin yunwa ne?”.

Girgiza Kai Samira tayi kana tace.

“Mommy bana jin yunwa”.

Wata mahaukaciyar dariya ya fashe dashi wanda yasa Hajiya Lami da Samira saurin Kallonsa cikin wata
murya yace.

“Kinsan abinda na bata tasha kuwa?.

Na bata abinda babu namijin da ya isa bata tasha na bata abinda babu ita babu yunwa har na tsawon
sati in dai zan cigaba da bata wannan ba dai taci abinci dan yunwa ba saidai ta buƙaci abinci dan kuzari”.

Kai Hajiya Lami ta gyaɗa still Idanunta na Kan Samira.

Cikin tsawa yace.

“Ki fita ki bamu waje zamu ɗaura daga inda muka tsaya”.

Ya faɗa tare da kamo hannun Samira.

(Wa'iyazu Billah lalacacciyar uwa mai lalatacciyar tarbiya da ƙeƙyasashiyar zuciya).

Daga wannan rana haka Boka Kar'uzu ya cigaba da lalata rayuwar Samira Amma dake Hajiya Lami
lalacacciyar Uwa ce da ba Allah da Manzonsa a ranta bare digon imani bata damu ba acikin kwanakin
Hajiya Bunayya ta kawo musu ziyara sunanta hira, harda murnar gwara da suka canza Naseer da Jameel
dan da shi suka riƙa gashi na ya rasu.

Kana tun ranan da Samira ta shiga ɗakin bata fita ba duk wani abu da suke buƙata Hajiya Lami na kai
musu Boka Kar'uzu kuwa ko yaushe yana manne da ita yana addabarta a haka har ya cika satinsa da yace
saida yayi gyaran kwana uku sannan ya koma gidansa bayan komawarsa da kwana biyar Baban Samira
ya dawo.

*LITTAFIN SAKAYYAH DAI NA KUDINE KO KIN GANSHI A WASU WURAREN DA BA WURINA BA TOH NA
SATANE KI BIYA KI KARANTA CIKIN AMINCI BABU HAƘƘIN WANI A GANKI LITTAFIN SAKAYYAH 1K NE
KACAL DUK DA YAWANSA DA DAƊINSA DUBU ƊAYA NEFA KACAL, ki biya dubunki ɗaya ki karanta
maimkyau ba sallake-sallake babu kin samu wasu PAGE ɗin baki samu wasuba ki karanta abinki one by
one tura kuɗin samun damar karantawa ta asusuna na GTBank. 0661110170 GTBank AISHA ALIYU
GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 sai in tura miki karanta lfy lafiya.
Mu guji yaƙin wani duk ƙanƙantarsa domin na watan nan dai na Allah ya isane atoh*

*Jauro Yaya*

Hajja Nana ce zaune da ƙoron Abincin agefenta yayinda Dije da bata daɗe da zuwa ba ke zaune gefenta
cikin sauri Hajja Nana ta miƙe tsaye jin tsayuwar mota aƙofar gida kallon Dije tayi fuskarta ɗauke da
murmushi tace.

“Ya naji kamar ƙaran mota?”.

Kai Dije ta gyaɗa tare da miƙewa kana tace.

“Nima Hajja Nana haka naji kamar ƙaran Mota”.

Cike da zaƙuwa tace.

“Maza je ki duba waye ne?”.

Kai Dije ta gyaɗa tare da fita tana ganin motar tayi dariya tare da ɗaga sautin Muryanta tace.

“Laaa Hajja Nana Baffa Jimeta ne”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Masha Allah dan albarka ya ɗauki abin da muhimmanci ne”.

Anutse Baffa Jimeta ya shigo cikin gidan.

Cikin sauri Dije ta shimfiɗa masa tabirma ya zauna suka gaisa ba daɗewa baki daya ƙannenta suka shigo.

Bayan sun gama gaishe-gaishe Hajja Nana ta kalli Baffa Jimeta fuskarta ɗauke da murmushi tace.
“Kazo kenan?”.

Kai Baffa Jimeta ya gyaɗa cike da ladabi yace.

“Nazo Hajja Nana”.

Murmushi tayi tare da gyara zamanta kana tace.

“Kazo batun Khausar ko?”.

Jinjina kai yayi cikin sanyin murya yace.

“Ai dole na inzo domin cika Umarnin ki”.

Kallon ƙannenta tayi cikin alamun jin daɗi tace.

“Toh Idan Allah ya kaimu gobe da safe zamu tafi can”.

Ahankali ya gyara zamansa sannan yace.

“Toh shikenan Allah ya kaimu lafiya”.

Da daddare Misalin karfe 7:30 malam Arɗo da Abba ne zaune acikin mota Kallon Abba dake tuƙi Malam
Arɗo yayi tare da sauke ajiyar zuciya kana yace.

“Insha Allah yau zamuje mu isar da nufin Mu”.

Jinjina kai Abba yayi cikin sanyin Murya yace.

“Insha Allah yau zamu ida Wasiyyar Jameelu na sai muji abinda mahaifin yarinyar zai faɗa”. daga nan
suka nufi gidan Ummi

Washe gari da safe Misalin ƙarfe tara Hajja Nana da Baffa Jimeta tare da Malam Liman suka isa gidan
Lamiɗo kai tsaye Sashen Mommy ta nufa Dije na biye da ita.

Malam Liman da Baffa Jimeta kuma suka nufi falon Lamiɗo.

Cike sauri Mommy dake shirya dining table ta juya jin Sallamar Hajja Nana cike da girmamawa tace.

“Hajja lale marhaba kece”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.

“Wallahi kuwa”.
Murmushi Mommy tayi tare da miƙewa bayan sun gaisa ta nufi dining table ta kawo musu Flaks din tea
da soyayyan ƙwai da buredi da kuma ɗumamen tuwon shinkafa miyar taushe ta ajiye musu sannan ta
basu waje dake basuyi breakfast suka taho nan suka ci.

Bayan sun gama Mommy na murmushi tace.

“Amma kunyi saurin isowa”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tana gyara zaman Flaks din tace.

“Eh ai bani kaɗai bace da Malam Liman da kuma Baffa Jimeta muka zo akan dai Maganar Auren Khausar
dana miki ne”.

Khausar dake zuba chips afaranti tayi saurin kallon Hajja Nana babu walwala atare da ita tace.

“Wai dan Allah Hajja Nana mena tsare miki ne arayuwar duniyar nan?”.

Kallonta Hajja Nana tayi cikin sassauta murya tace.

“Ni ba abinda kika tsare min, kawai dai gata nake so na Miki domin Aure shine rufin asiri da kuma gatan
ƴa mace, sannan ga ɗan uwanki zai riƙe ki da Amana da gaskiya”.

Ta dire ayar mgnar tare da murmushi ta kallon Khausar data tsareta da ido kana ta sassauta murya ta
cigaba da cewa.

“Ga Babansa ma munzo tare, dan in muka gama magana ma, shi yau zai wuce mu kuma motar Kasuwa
zamu hau kawai”.

Kallonta kawai Khausar keyi Muryanta na rawa tace.

“Wai dan Allah Hajja Nana Meyesa kike min haka ne?.

Agaskiya ni banason abinda kike min?”.

Taɓe baki Hajja Nana tayi tare da tsira mata ido tace.

“Ko bakyaso dole sai anyi”.

Cikin sauri Khausar tace.

“Wallahi Ni dai baza ayimin dole ba”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe da alamun ɓacin rai ta kalli Khausar tace.
“Wai Khausar Meyesa haka ne bana son abinda kike min fa banaso kifa kiyayi kanki ki barni inji da abu
ɗaya”.

Dai-dai lokacin Lamiɗo ya shigo falon tare da zama aƙasa kana cike da ladabi ya Marabci Hajja Nana.

juyawa yayi ya kalli matarsa tuni ya gano ɓacin ran dake fuskarta kawai kawaici takeyi shiyasa bata
nunawa amman wani lokaci ma daɗi takeji in Khausar na titse kakartata.

Anutse ya gyara zamansa kana yayi ƙasa da kansa cike da ladabi da kuma mutuntawa yace.

“Addah Nana yanzu mukayi magana da Alhj Muhammadu da kuma Malam Liman mun gama magana
dasu”.

Murmushi Hajja Nana tayi tare da jinjina kai kana tace.

“Yawwa sun maka bayani ko?”.

Jinjina kai yayi cike da ladabi yace.

“Eh sunyi min”.

Miƙewa Khausar tayi tare da kallon Dije tace.

“Dija mu tafi”.

Numfashi Lamiɗo ya fesar kana yace.

“A'a Khausar zauna”.

Kai ta gyaɗa tare da komawa ta zauna kana ta sunkuyar da kanta ƙasa hawaye na ciko mata ido.

Ahankali Lamiɗo ya sake yin ƙasa da kansa kana yace.

“Toh Hajja Nana naji abinda yake tafe daku, akan batun Khausar da ɗan Uwanta Aliyu”.

Cikin sauri Khausar ta ɗago kanta tare da kallon Lamiɗo sai kuma tayi saurin sunkuyar da kanta hawaye
na kwaranyo mata kana zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi.

Ahankali Abba ya cigaba da cewa.

“Ni babu wata matsala daga gareni, duk da da akwai ƙanina ɗan Yafendo na dake son Khausar tun tana
ƙarama, toh amma sawun giwa ya take na raƙumi, abinda kuke ce shi za ayi domin koda inada power
akan Khausar kun fini ƙarfi”.

Sai kuma ya ɗago kansa tare da kallon Hajja Nana data tsaresa da ido Ajiyar zuciya ya sauƙe kana ya
cigaba da cewa.
“Amma Koda batun Naseer bazai kau da batun ku na kawo na Naseer ba, duk da cewa bamu ji ta bakin
yarinya ba duk da naga alamun ta dai-dai-ta da ɗan Uwanta tun da yanzu bana ganinsu da Naseer”.

Ya kare mgnar tare da kallon Khausar da tayi ƙasa da kanta fuskarta cike da hawaye numfashin ya ɗan
fesar kana yace.

“Sannan ba aji ra'ayin Khausar ba, domin yaran yanzu ba ayi musu dole sabida haka ya kamata aji ra'ayin
Khausar idan tanason.

Ɗan Uwanta tofa sawun Giwa ya take na raƙumi idan kuma Naseer take so tou sai mu nemi al'farma a
wurinku”.

Ƙankance ido Hajja Nana tayi kana ta shiga girgiza ƙafanta tare da kallon Lamiɗo tace.

“Lalle kam kamar yanda ka faɗa haka ne, sawun Giwa ya take na raƙumi, sannan batun so kuke ɓata
ƴaƴanku mu da ai sai dai a aura maka ko kana so ko baka so, kuma hakan be hana zaman lafiya ba”.

Ahankali Lamiɗo ya sunkuyar da kansa cikin girmamawa da tausashi harshe yace.

“Ai zamani ne ya sauya Hajja Nana Da da yanzu ba ɗaya bane amman yanzu bari muji ta bakinta”.

Ya kare mgnar tare da gyara zamansa ya fuskanci Khausar cikin tausasawa yace.

“Khausar”.

Murya na rawa ta amsa, yayinda tuni hawaye ke kwaranya.

Mommy kam numfashi mai nauyi ta fesar tare da kauda kanta ranta cike da tausayin yarta.

Shi kuwa Lamido cikin kulawa yace.

“Ki dena kuka Khausar kada ki damu ki gaya min cikin mutun biyu Aliyu Dan uwanki da Naseer wa kikeso,
kada kiji tsoro kinjiko Mamana gaya min”.

Jin hakane yasa Khausar ɗago kanta ahankali zuciyarta na cike da wani irin masifaffen rauni murya na
rawa ido na kwaranyar da hawaye ta kalli Lamiɗo tare da cewa.

“Abba Ni dai bana sonsa”.

Cikin sauri Hajja Nana ta kalli Khausar tare da ƙankance Ido a faɗace tace.

“Don Ubanki to Naseerun kike so dangin Mayu!?”.

Sassayan kuka Khausar ta saki tare da cewa.

“Nikam shima bana sonsa”.


Kusan a tare Mommy da Hajja Nana da Lamiɗo duk suka kalleta.

Cikin tsawa da masifar isa da iko Hajja Nana tace.

“Toh wa kike so?, sannan me kike nufi ?,wa zaki Aura?, tunda kince bakyaso Aliyu ba kyason Naseerun?”.

Shiru batace komaiba, sai kuka.

Ganin haka yasa Lamido yin gyaran murya cikin Muryar lallashi yace.

“Toh wa kikeso Manana?”.

Kukan ne ya fara tsanantan mata kana a raunace ta ƙara sunkuyar da kanta.

Afusace Hajja Nana tace.

“Toh dan ubanki wa zaki Aura? Wa kikeso?”.

Cike da sanyi murya na rawa tace.

“Ni dai akwai wanda zan aura?”

Mommy kuwa da sauri ta kalli Khausar wacce tunda aka fara magana bata ce Uffan ba cike da mamaki
tace.

“Khausar dawa ye kike soyyayya ban saniba wa kike so wa zaki Aura!?”.

Ahankali Khausar ta gyara zamanta tare da sun kuyar da kanta ƙasa kana tace.

“Ni Moddibo nake so”...!

*LITTAFIN SAKAYYAH DAI NA KUDINE KO KIN GANSHI A WASU WURAREN DA BA WURINA BA TOH NA
SATANE KI BIYA KI KARANTA CIKIN AMINCI BABU HAƘƘIN WANI A GANKI LITTAFIN SAKAYYAH 1K NE
KACAL DUK DA YAWANSA DA DAƊINSA DUBU ƊAYA NEFA KACAL, ki biya dubunki ɗaya ki karanta
maimkyau ba sallake-sallake babu kin samu wasu PAGE ɗin baki samu wasuba ki karanta abinki one by
one tura kuɗin samun damar karantawa ta asusuna na GTBank. 0661110170 GTBank AISHA ALIYU
GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 sai in tura miki karanta lfy lafiya.
Mu guji yaƙin wani duk ƙanƙantarsa domin na watan nan dai na Allah ya isane atoh*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*
SAKAYYAH

35

Zare ido Hajja Nana tayi cike da matsanancin mamaki al'ajabi haɗi da alhini.

Tayi salati tare da tafa hannu.

Muryanta na cike da mmki, takaici, haɗi da fusata ta cigaba da cewa.

“Ohh Allah ya kawo mu ƙarshen duniya, yarinya babu tsoron Allah bare aje ga babin kunya ki dubi tsabar
Idona ki kuma dubi tsabar idon Mutumin dake matsayin Mahaifinki, sannan ki dubi tsakar idon
Mahaifiyarki kice wai wane kike so!”.

Cikin raunin Khausar tayi ƙasa da kanta tana mai rumtse idonta tana jin wani irin yanayi mai cike da rauni
azuciyarta.

Wani shegen kallo Hajja Nana ta watsa mata cikin tsananin fushi da ɓacin rai tace.

“Wanene shi Moddibo? wani gantalellen yadine Moddibon? shin inane tushensa su waye ne Asalinsa
dame yafi ɗan uwanki da har kika zaɓe sa kika ƙyale ɗan Uwanki dame yake taƙama!?”.

Ta ida maganar tana me tsare Khausar da ta ɗan ɗago kanta fuska cike da rauni, ita Hajja Nana da idanun
fusata ta banka mata harara.

Ita kuwa Khausar ahankali ta sake sunkuyar da kanta ƙasa batare da tace. Uffan ba yayin da gaba ɗaya
ilahirin jikinta ke tsuma.

Cikin sanyi Lamiɗo ya sauƙe ajiyar zuciya mai nauyi tare da jinjina kansa kana ya maida kallonsa kan
Khausar da kanta ke ƙasa.

Mommy kuwa cikin yanayin mamaki da yadda maganar tazo mata abazata ta tsirawa Khausar Ido tana
maimaita abinda Khausar ta faɗa aƙasan ranta.

Girgiza kai Hajja Nana tayi tare da juyawa ta kalli Mommy tare da sakin kuka kana tace.

“Yanzu Aysha Ina magana kema kinyi min banza, baza ku bani amsaba, wato ni zaku mayar gantalalliya
ga tsohuwar banza tana magana dole ku shareni tunda kun mayar dani bansan abinda nake ba”.

Sai kuma ta maida kallonta kan Khausar cikin matsanancin ɓacin rai da kuka tsufa tace.
“Yanzu abinda kika zaɓawa kanki kenan Khausar!?.

Yanzu abinda zaki yimin kenan? Kice ba kyason ɗan Uwanki?. Wannan dangin Mayu da kika ce bakyaso
ai ban damu ba amma ki dubi tsabar Idona kice bakyason jininki ɗan uwanki yaro mai mutunci da
kamala?”.

Mommy, Lamiɗo, da Dije baki ɗaya Idanu suka zubawa Hajja Nana suna kallon yadda take kukan
tsakaninta da Allah Khausar kuwa still Kanta na ƙasa ita kadai tasan abinda take ji.

Cikin fushi da tsawa Hajja Nana ta kalli Khausar data ƙi ɗago kanta tace.

“Waye shin dame yafi Aliyu?.

Wato dai ya tabbata babu tsoron Allah acikin waɗannan tsayayyun idanun naki, banda lalacewa da
taɓarɓarewar tarbiyarki shin har kina da bakin da Iyayenki na maganar aurenki zaki sanya naki aciki da
masifar tijara?”.

Cikin sanyi Khausar ta ɗago kanta, tare da buɗe idanunta wanda tuni suka sauya launi daga farin madara
zuwa jan rushi, cikin rauni ta kalli Hajja Nana dake zazzaga bala'i kamar ba gobe.

Sai kuma ta lumshe idanunta kana ta buɗe, amma ko ƙala bata ceba.

Afusace Hajja Nana dake kuka tace.

“Maza ki daina kallona da wannan.

Fitsararrun idanunki dake tsaye kamar Nonon maza tunda kin shafawa Idanunki baƙin kwalli, adole gaki
ƴar tijara.

Ohoɗijam kai ni wallahi tallahi billahil-azem tunda nake ban taɓa kallon abinda ya gigitani ya ratsa
ƙwaƙwalwa ta irin wannan maganar taki ba!”.

Sai kuma ta sanya bakin zaninta tare da sharce hawaye da yar majina still tana kuka tace.

“Yanzu Khausar me kike nufi dani?, kina nufin Baffanki da yayi tattaki tun daga Adamawa yazo nan yazo
abanza mu taso tun daga Jauro yaya da sanyin safiya munyi a wofi kenan?.

Ki dubi tsabar Idanun mu saboda baki da kunya kice bakyason Jikana sannan ki dubi tsabar idon Baffanki
kice bakyason.

Ɗansa bayan shi zai bada Aurenki?”.

Kasa ɗago kai Khausar tayi ta kalleta sabida wani irin abu take ji azuciyarta yayin da hawaye suka shiga
bin kuncinta.
Mommy Kam ta gumi tayi baki ɗaya kanta ya kulle da lamarin ta rasa ta yanda zata fara misalta abin.

Lamiɗo kuwa ganin yanda Hajja Nana ke kuka haiƙan ƙadaran tana surutai yasa ya sassauta muryarsa
tare da cewa.

“Dan Allah Hajja Nana kiyi haƙuri ki daina wannan kukan”.

Saurin ɗaga masa hannu tayi still tana kuka tace.

“A'a barni idan banyi kuka ba me kake so inyi tunda Allah ya haɗani da gantalalliyar jika dake son
kunyatani a Idanun duniya anya yarinyar nan tana da hankali kuwa kodai akwai abinda ke damun
aƙwaƙwalwar , hegiya fitsararriya”.

Cikin rauni da alamun damuwa Khausar ta ɗago Idanunta dake jiƙe da ruwan hawaye ta kalli Hajja Nana
muryanta na rawa cikin sanyin tace.

“Dan Allah ni. Ki daina zagina Hajja Nana ki daina Sheganta ni ke kinfi kowa sanin cewa niba Shegiya bace
kuma ki daina zagin Ubana ki daina saka shi acikin wannan maganar ki barshi ya kwanta akabarinsa cikin
nutsuwa da salama tun da dai ba wani mugun abu na aikata ba bare kiyita ihu kina son tara mana
mutane”.

Cikin fushi da takaici Mommy ta Kai hannunta na dama tare da kwaɗawa bakinta mari kana ta watsa
mata Harara tare da cewa.

“Rufe min baki fitsarariya mara kunya. Wallahi Khausar kin bani mamaki sam ban taɓa zaton haka daga
gareki ba agaban idanun mu Khausar yaushe kika zama haka ni zaki kunyata?”.

Da sauri Khausar taja baya tare da fashewa da matsanancin kuka me tsuma zuciya.

Cikin sanyi Lamiɗo ya kalli Khausar dake kuka tamkar ranta zai fita kana yace.

“Khausar tashi ki tafi ɗaki”.

Da gudu ta miƙe ta nufi ɗakinta, kana Dije ta mara mata baya. Khausar na shiga ɗaki ta faɗa kan gado
tare da fashewa da matsanancin Kuka me tsuma zuciya da ban tausayi yayin da hawaye wani ke bin wani
suna kwaranya daga Idanunta.

Acan Falon kuwa ta inda Hajja Nana ke shiga ba tanan take fita ba, baki ɗaya Idanunta sun rufe sai
Masifa take zazzaga musu musamman Mommy ganin yanda take zazzaga Masifa ba Full stop bare
commer yasa Lamiɗo kasa fadar abinda ke ransa cikin sanyin murya da ladabi yace.
“Dan Allah Hajja Nana kiyi haƙuri, muyi mgnar a tsanake, kinfa san shi Aure fa rabone, sannan nufi ne na
Ubangiji sannan matar mutum kabarinsa, idan har Allah ya ƙadarta cewa Aliyu shine mijin Khausar to fa
duk duniya idan za'a haɗu babu wanda ya isa ya raba wannan auren”.

Wani irin kallo Hajja Nana ke binsa dashi tana mai tafasa dan masifa.

Cike da ladabi da kuma sanyin murya Lamiɗo ya cigaba da cewa.

“Idan kuma har Allah bai ƙadarta cewa Aliyu shine mijinta ba, tofa babu wanda ya isa yasa hakan ya
kasance, dan haka dan Allah kiyi haƙuri Insha Allah komai zai dai-dai ta”.

Girgiza kai Hajja Nana tayi tare da juyawa ta kalli Mommy da kanta ke ƙasa cikin fushi tace.

“Lallai Aysha dama irin wannan tarbiyyar kika bawa ƴarki kenan?

Yanzu mu awajen mu wace yarinya ce ta isa ta kalli tsabar idon magabatan ta tace wai ga wanda take so
wannan abin kunyar har ina?”.

Cikin sanyi da alamun damuwa Mommy ke kallonta baki daya ta rasa wani kalma za tayi amfani dashi
wajen bawa Hajja Nana haƙuri.

Hajja Nana kuwa ƙwaffa tayi cikin rawan murya ta cigaba da cewa.

“Tirrr da wannan rayuwa wai yarinya ƙarama kamar Khausar har tasan ta tsaya agaban manya tace ita ga
wanda take so, watoma kenan itace zatayiwa kanta zaɓin mijin da zata aura.

To mu azamanin mu koda ya rinya itace Sarauniyar kyau idan magabatan ta suka zaba mata miji koda
kuma shine Sarkin munin duniya haka zata zauna dashi bare me Khausar zata nunawa Aliyu?Mutumin da
koda kyaune ya fita”.

Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauke tare da gyara zaman sa kana ya tsira mata idanu yana mamakin yanda ta
ɗauki al'amarin da zafi kawai dan Khausar tace Moddibo take so shine ta kafa aƙota sai kace wacce
akace tayi cikin shege shi kam baiga abin tada jijiyoyin wuya akan maganar ba.

Numfashi ya fesar tare da sassauta muryarsa yace.

“Dan Allah Hajja Nana kiyi haƙuri Insha Allah komai zai dai-dai ta akwai yarinta atare da Khausar har
yanzu bata mallaki hankalin kanta ba, amma bawai dan baki isa da ita bane yasa tayi magana”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da ɗago kanta kana cikin sanyin murya ta kalli Hajja Nana dake
matsar kwallar da taƙi fitowa tace.
“Dan Allah Hajja kiyi haƙuri wallahi Ni kaina ban taɓa jin wannan kalmar abakin Khausar ba, sai yau da
ace tun farko naji to wallahi bazan bari ya fito fili ba zan dakatar da ita”.

Wani irin kallo Hajja Nana ta watsa mata tare da ƙankance ido tace.

“Wallahi ƙarya kike Aysha Babu ta yanda za ayi ƴarki na soyayya da wani amma baki sani ba, kawai dai so
kike kinuna min iyakata akan Khausar kuma kisani duk abinda zakiyi ke dai baki isa ki canza matsayina
ba”.

Kai Mommy ta girgiza cikin sanyi da ladabi ta cigaba da bata haƙuri haka zalika Lamiɗo hakuri kawai suke
bata.

Miƙewa Hajja Nana tayi tare da ƙankance Ido ta kalli Lamiɗo da Mommy kana ta ya mutse baki tare da
cewa.

“Ni dai Wallahi Allah wannan maganar jinta nake kamar saɓon Allah”.

Cike da damuwa Mommy tace.

“Dan Allah kiyi haƙuri ki zauna. Khausar tayi kuskure amma zamuyi wa tufkar hanci”.

Cikin sauri Hajja Nana ta kalli Mommy tare da faɗin.

“In zauna fa kika ce? Inani ina zaman nan? Ina sam nikam banga wajen zama ba. Subhanallah Allah ya
tsareni ai sai Girgiza ƙasa ya rufta dani aciki yarinya budurwa yarinya ƙarama har tanada tsaurin idon da
zata zauna tsakanin magabatan ta masu aurar da ita, ta iya buɗe baki tace bata son zaɓin su sai zabinta”.

Ta ida maganar tare da ficewa tana mita, da korwa da kororowa haɗi da kormoto.

Cikin sauri Lamiɗo da Mommy suka bi bayanta cike da girmamawa suke bata haƙuri amma firr wannan
fitinenniyar tsohuwa taƙi sauraronsu tafiya kawai take tana kumfar baki, har ta isa Farfajiyar gidan.

Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya ta fito tare da kallon Hajja Nana sai kuma ta maida kallonta kan Mommy
dake aikin rarrashin Hajja Nana tana bata haƙuri tace.

“Aysha lafiya kuwa yau nakeji hayaniya naga kamar ran Hajja Nana aɓace".

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe cikin sanyin murya tace.

“Dan Allah Hajiya ki tayamu bata haƙuri fushi tayi”.

Kallon Hajja Nana. Hajiya Bunayya tayi da murmushi afuskarta tace.

“Ayyah Hajja Nana kiyi haƙuri dan Allah”.

Ko kallonta Hajja Nana ba tayi ba bare ta tanka ta ta nufi jikin mota.


Baffa Jimeta da Baffa Liman dake zaune Falon Lamiɗo kuwa jiyo hayaniyarta yasa sukayi saurin miƙewa
tsaye, sai kuma suka nufi wajan jin Muryan Hajja Nana na tashi cikin sauri suka fito tsaye suka hangota
jikin motar tana ta sababi kallon Baffa Liman Baffa Jimeta yayi cike da mamaki yace.

“Yau kuma waya taɓo Hajja Nana haka?".

Girgiza kai Baffa Liman yayi tare da faɗin.

“Allahu a'alam amma dai baya wuce Khausar ba”.

Suna isa jikin Motar Baffa Jimeta ya matsa kusa da ita tare da sassauta murya yace.

“Hajja lafiya kuwa me yafaru?”.

Kallonsa tayi cikin fushi tace.

“Wuce mu tafi ina Liman maza ku wuce mutafi wannan gida ba gidan zuwa bane gidan fitsararru da
rashin tarbiyya”.

Dai-dai lokacin Gimbiya Dadu ta fito daga sashen ta jin hayaniyar babu walwala afuskarta ta kalli Hajja
Nana tare da cewa.

“Dakata!, Mukam ba fitsararru marasa tarbiyya bane Jikar kice dai fitsararriya mara tarbiyya”.

Afusace Hajja Nana ta kalleta tare da ɗaga mata hannu cikin fushi da ɗaga murya tace.

“Keee dakata kada kice zaki faɗa min magana”.

Cikin sauri Lamiɗo ya juya ya kalli Gimbiya Dadu cikin sanyin murya yace.

“Dan Allah Mama kada kiyi magana, ki taya mu bata haƙuri baki san meye ɓata mata rai ba”.

Taɓe baki Gimbiya Dadu tayi kana tace.

“Yo aiji nayi tana haɗa mana Jami'n zuriya gaba ɗaya ne tana aibanta mu”.

Tafe hannu Hajja Nana tayi tare da ƙankance ido kana tace.

“Toh Zuri'ar taku ta arziƙi ce? Nace zuru'ar taku har wata kayan gabas ce? Kin sani dai na sani. ko kuma
wata tsiyace da ita zuri'ar Mayu”.

Girgiza kai Baffa Jimeta yayi tare da cewa.


“Inalillahi Ash'sha haba Hajja Nana dan Allah kiyi haƙuri mana”.

Kusa da ita Baffa Liman ya matsa cike da rarrashi yace.

“Dan Allah Addah Hajja am kiyi haƙuri ki kwantar da hankalin ki kizo muje mu zauna”.

Girgiza kai tayi tare da faɗin.

“Inaaa zan zauna mutafi kawai nifa bazan zauna awannan gidan ba wallahi banga wajen zama ba
wannan abin kunya da tashin zuciyar ba dani ba”.

Ganin yanda ta tashi hankalinta yasa Baffa Jimeta ya buɗe mata bayan mota tashiga sannan ya zagaya
yashiga mazaunin Driver Baffa Liman ya zauna gefensa.

Ahankali Lamiɗo ya matsa jikin motar ta Side din da hajja Nana ke zaune cike da ladabi yace.

“Dan Allah Hajja kiyi haƙuri akan abin da ya faru”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“Ba komai Lamiɗo ai ba laifin ka bane, ai kai baka da laifi aciki laifin uwarta ne da ita kanta”.

Mommy Kam da kallo tabi motar har ya fice daga gidan.

Bayan sun fita Baffa Jimeta ya juya tare da kallon Hajja Nana da tayi kicin-kicin da fuska kana yace.

“Toh Hajja yanzu gida zamu tafi kenan?”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“Kaini gidan ƙawata Innare”.

Jinjina kai yayi kana yace.

“Toh”.

Kai tsaye gidan su Moddibo ya nufa da motar.

Acan gidansu Abba kuwa zaune yake afalonsa cikin yanayin shiru-shirun daya saba ya tallafe haɓarsa da
hannunsa na dama baki ɗaya ya rame dan bai cika Lafiya ba ahankali ya kalli center table dake gabansa
jin wayarsa na ruri ɗauka sunan Manager company sa dake Marocco ne ya bayyana Picking Yayi tare da
kaiwa Kunnensa sannan yayi sallama.
Bayan sun gaisa Manager ya fara mishi mgn da larabci kamar yadda suka saba yace.

“Yallaɓai sabbin kaya da mukayi Order daga Chaina sun iso gaba ɗaya sannan ana bukatar kai ko ni wani
ya zamana yana wajen domin aikin sabbin na'uran sarrafa Arabia Gawn da mukeson fara sabbin
samfurin.

To gashi kuma ni yanzu ba na nan, kasan ina India naje aduba min lafiyar ƙafana to dole since sai an
wakilta wani kafin asauke kayan aga yanayin da abubuwan suka iso lafiya”.

Jingina kai Abba yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya kana yace.

“Toh kuma gashi nima kuma ban cika lafiya ba kullum ina fama da matsanancin ciwon kai, dama can a
tsarina Jameel ne zai wakilceni aiyi aikin”.

Cike da tausayawa Manager yace.

“Ayyah Allah Ubangiji ya sawwaka.

Yallaɓai sai dai a cigaba da haƙuri Jameelu kuwa Allah yajiƙan sa ya gafarta masa, amma ya kamata
asamu awakilta wani tunda bana nan ga kaya sun iso gashi audugar da aka tura da Nigeria ta iso, kuma
tunda tazoma bamuyi mgnar ba sabida wannan iftila'in ɓatan Jameel”.

Jinjina kai Abba yayi tare da cewa.

“Toh shikenan, amman bazan samu zuwa ba, domin nima kaina ba lafiyar bace dani amma Insha Allah
zan turo Aliyu yazo zaiyi dukkan abinda ya dace”.

Kai Manager ya gyaɗa kana yace.

“Toh Allah ya bada iko dan kaya sun iso tun jiya suketa ƙoƙarin za afara aikin sauƙe kayayyakin da
ayyukan su masu motocin ma sun matsa min don suna so su fita cikin Company'n dan sunce basu son su
wuce kwana biyar zuwa takwas, in sun wuce haka kuma sai in za'ainta biyansu ne”.

Cikin sanyin murya Abba yace.

“Toh shikenan ba komai Insha Allah zanyi wa Moddibo magana zai zo yanzu zan kira shi in sha Allah in
this week zai shigo Marocco”.

Acan gidan su Moddibo kuwa abakin ƙofa Baffa Jimeta yayi Parking din motarsa cikin sauri Hajja Nana ta
buɗe Murfin motar ta fita tare da buɗe gate din gidan tashiga.

Da kallo Baffa Jimeta da Baffa Liman suka bita har ta shige cikin gidan.
Ita kuwa tana shiga tun daga ƙaramin gate da zai sadata da ɗaya sashen ta fara doka sallama tare da
faɗin.

“Innare! Innare!! Innare!!!Bakya Nan ne!?”.

Cikin sauri Innayi ta fito daga ɗakinta da murmushi afuskarta tace.

“A'a wannan muryar wa nake ji kamar Hajja Nana”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh Innare nice dai”.

Murmushi Innayi tayi tare da ƙarasawa kusa da ita tace.

“A lale maraba Barka da zuwa Maraba maraba mu shiga daga ciki”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa sannan suka shiga ciki cike da kulawa Innayi ta ajiye mata ruwa da abin taɓawa
Sannan ta kalli Hajja Nana dake ta cika tana batsewa tace.

“Hajjia Nana mutan maka da Madina Bismillahi”.

Girgiza kai Hajja Nana tayi kana tace.

“A'a bazan iya cin komai ba barshi kawai Nagode”.

“Meye faru kuma?”.

Girgiza kai tayi cike datakaici tace.

“Ƴaƴan zamani kai Allah ya kyauta”.

Zama Innayi ta gyara tare da cewa.

“Waya taɓoki?”.

Ƙwaffa Hajja Nana tayi kana tace.

“Hegiyar yarinyar nanne fitsararriya gantalalliyar yarinya da batasan abin da ya dace da kanta ba, ana
nuna mata gabas tana ga yamma.”

Sai kuma ta fesar da numfashin kana taci gaba.

“Uyumm yarinya har an kai matakin da yarinya ƙarama ana magana tana mgna ta fetsare Idanunta ta
kalli idanun Magabatan ta tace wai tayiwa kanta zaɓin mijin Aure”.
Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da kallon Hajja Nana kana tace.

“Wace yarinya ce haka”.

Cike da takaici Hajja Nana tace.

“Khausar mana”.

Cike da Mamaki Innayi tace.

“Ha'a Khausar kuma wace Khausar ɗin?".

Jinina kai Hajja Nana tayi tace.

“Eh Khausar jikata”.

Gyaɗa kai Innayi tayi tare da cewa.

“Eh na fahimta.”

Kallonta Hajja Nana tayi kana tace.

“Yanzu na fito daga gidan Lamiɗo ai”.

Cike da mamaki Innayi tace.

“Dama Khausar ɗin gidan Lamiɗo itace jikar ki?”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh itace jikata ɗin mana”.

Numfashi mai nauyi Innayi ta sauƙe tare da gyara zamanta kana tace.

“Toh ki kwantar da hankalin ki me yayi tsanani aciki?”.

Ƙwaffa Hajja Nana tayi tare da kallon Innayi tace.

“Mun zo da batun Aurenta da ɗan Uwanta, sannan dama anan cikin zuri'ar gidan Lamiɗo kin sansu
Zuri'ar Mayune to wai akwai wani yaro Naseeru da yake sonta”.

Gyara zama Innayi tayi tana kallonta.

ita ko Hajja Nana ta cigaba da cewa.

“To Ni duk atunanina ma idan batason Aliyu Naseeru zata ce tana so amma wai.

Yarinya nan tace wai wani take so, saboda rainin hankali wai Uwar ma batasan da batun ba”.
Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da fuskantar Hajja Nana tace.

“Toh me abin tashin hankali kinsan zamanin da dana yanzu ba ɗaya bane, abinda aka mana muka jura na
yanzu ba zasu jura ba, bama a isa ayi musu ba, bare kuma har aje matakin su ɗauka, amma yanzu kisha
ruwa ranki yayi sanyi tukun”.

Numfashi Hajja Nana ta fesar kana tace.

“Wallahi baki daya a fusace nake yarinya tayi matuƙar ɓata min rai ta fusata min zuciya ni zata wa tsawa
ƙasa a ido.

Baffanta yayi tattaki gari ya garara yazo amma tace bata son ɗan sa saboda bata da mutunci”.

Innayi kuwa ruwa ta miƙa mata tare da cewa.

“Ke dai kisha ruwa zuciyarki yayi sanyi”.

Karɓa tayi tare da kafawa abakinta ta fara sha

Acan Falon Moddibo kuwa zaune yake akan Sallaya bayan ya idar da sallar Walha hannunsa riƙe da
Alkur'ani yana karanta suratul Tauba yana Aya ta ɗari da ashirin da bakwai yaji wayarsa na Vibrating
Kallon screen ɗin wayar yayi ganin sunan Abba yasa ya cigaba da karatun kasancewar saura Ayoyin biyun
ƙarshe yasa ya cigaba yana ƙarasawa ya shafa addu'ar dai-dai lokacin wani sabon kiran ya sake shigowa.

Anutse ya ɗaga wayar tare da kaiwa Kunnensa yayi Sallama.

Cikin sanyin murya Abba ya amsa tare da cewa.

“Aliyu”.

Ahankali Moddibo yace.

“Na'am Abba ina kwana ya ƙarfin jikin naka?”.

Cikin sanyin murya Abba yace.

“Lafiya lau Alhamdulillah ya gida? Aliyu ya kwana biyu duk ban jika ba”.

Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe kana yace.

“Wlh kuwa Abba ya ƙarfin jikin naka?”.

Ahankali Abba ya sauƙe numfashi kana yace.


“Jiki da sauƙi”.

gyara zamansa yayi tare da cewa.

“Toh Abba Allah ya ƙara sauƙi amma lafiya kuwa?”.

“Eh lfy lau. Yanzuma nayi waya da.

Mgnar Company na dake Marocco, to dama akwai kayan da mukayi Order sabbbin Injuna, sabida tsoffin
sun fara samun matsala kasancewar sun kwana biyu to an kawo sabbin kuma Manager baya nan yaje
duba lafiyarsa, kuma yanzu dole ana buƙatar sai akwai sahalewar wani da kuma sa hannu na kafin afara
sauƙe kayan dole kuma akwai buƙatar tsayeyye da zai sa ido kan aikin kafa musarrafan da za'ayi”.

Tunda Abba ya fara magana Moddibo ya lumshe idanunsa yana cigaba da sauraron sa.

Abba ya cigaba da cewa.

“To yanemi da Inje, to ni kuma bazan iya ba, kullum ina fama da ciwon kai kuma kaga ga yanayin da
nake ciki har yanzu ana zuwa min gaisuwa, shiyasa nake so ka shirya ka wakilceni, kaje ka fuskanci aikin
idan yaso idan komai ya dai-dai-ta aka fara aiki in anyi rukunin forko saika dawo ba zaka daɗe ba”.

Moddibo kuwa shiru yayi tare da jingina bayansa da jikin Cushing.

Daga ɗaya ɓangaren Abba yace.

“Hello! Aliyu Hello!!, Hello!!! Aliyu kana jina kuwa?”.

Shi kuwa Moddibo cije Lip ɗinsa na ƙasa yayi Aransa yace bana son garin Gembila baki ɗaya jihar Taraba
ta fitar masa ji yake tamkar wuta ake watsa masa aduk lokacin daya tuna shi kaɗaine ke rayuwa babu J
ɗinsa, babu wani akusa dashi idan zai tafi masallaci shi kaɗai sannan idan zai dawo shi kaɗai kana idan
zaici abinci shi kaɗai baki ɗaya ilahirin garin ya masa duhu kana ya masa ƙunci sam baya son zama
acikinsa Nigeria kanta ta fice masa arai.

To amma kuma idan ya tafi Ummi ya zatayi.

Cikin sauri ya buɗe Idanunsa dake lumshe jin Abba na cewa.

“Aliyu ya dai kayi shiru baka ce komai ba?”.

Numfashi mai tsayi yaja kafin ya sauƙe ahankali cikin sanyin murya yace.

“Abba Ummi idan na tafi nayi nesa da Ummi ba zata ji daɗi ba sannan Innayina, da waye zan barta?”.

Ahankali Abba ya sauƙe Ajiyar zuciya tare da sauƙe dogon numfashi kana yace.
“Ba komai Aliyu Insha Allah za ayi ƙoƙari akula da duk kan al'amurran su sannan ba daɗewa zaka yiba”.

Cikin raunin murya Moddibo yace.

“Abba Ummi tace idan banje wajenta ba hankalinta na tashi damuwarta na tsananta. Abba bana son
ganin Ummi cikin wani yanayi, Innayi na kuma bata da kowa a duniya saini in nayi nesa da ita ya zataji”.

Ajiyar zuciya Abba ya kuma sauƙe kana yace.

“Bakomai Insha Allah za muyi magana da Malam Ahmad za'a kwantar mata da hankalin ta, sannan dama
inaso zamuyi magana dakai Innayi kuma kada ka damu zata iya dawowa gidana kafin ka dawo ko gidan
Ummin”.

Ahankali Moddibo ya gyara zaman wayar akunnensa.

Yayinda Abba kuma ya cigaba da cewa.

“Akan kuɗin da aka har haɗa aka turo wanda Fatima ta saida Sarƙoƙinta da kuma motarta kazo zamuyi
maganar ka karɓi kuɗin Asiya mata wata motar sannan sauran ta ajiye idan zata sai wasu kadarorin ma
ta ajiye”.

A hankali ya gyara zamansa tare da rintse idanunsa kana ya cigaba da cewa.

“Sannan kaima naga motar da kake Amfani da ita tsohuwar mota ce ya kamata ka siya wata sabuwar
motar ka riƙa hawa”.

Girgiza kai Moddibo yayi cikin raunin murya yace.

“Abba me zanyi da wata sabuwar mota Abba bana son Kuɗin dan Allah kadaina maganar Abba ni dai
bana son Kuɗin Abba bana son su”.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da girgiza kai kana yace.

“A'a Aliyu ya za ayi kace haka?”.

Moddibo kuwa rumtse idanunsa yayi tare da taune Lip ɗinsa na ƙasa kana yace.

“Toh Abba me zanyi da kuɗin da suka kasa ceton min J me zanyi da kuɗin da suka kasa temakon ceto
mun rayuwar J Abba bana son Kuɗin Abba dan Allah kada kayi min maganar kuɗin”.

Numfashi Abba ya fesar cikin sassauta murya yace.

“Aliyu kayi haƙuri dole muyi maganar kuɗin nan kaima kace baka son maganar kuɗin nan to ni kuma me
zanyi dasu Aliyu kayi haƙuri kaji sannan dan Allah kayi ƙoƙari ka shirya ka tafi Marocco E PASSPORT naka
zaka fitar dan Allah, mu fara neman damar fitan ko ta online zakayi komai, cikin makon nan nakeso ka
tafin in Allah yasa ka samu buse”.

Shiru Moddibo yayi lokaci da yaji maganar Bashir ya dawo masa kunne na cewa yayi mafarki da M
Jameel sannan yace ya faɗa masa cewa ya taya Abba harƙan kasuwancin sa dogon numfashi yaja mai
sanyi duk da cewa baya so ya tafi ya bar Ummi da Innayi amma ji yake ya tsani zaman cikin Taraba da
Gembila baki ɗaya Jahar Jaligo ta fita Aransa ga kuma tuno da abinda Bashir di ya faɗa ya sauƙe
numfashi cikin sanyin murya yace.

“Toh shikenan Abba bari nayi magana da Innayi da Ummi”.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“Toh shikenan idan kunyi maganar dan Allah ka kirani yanzu yanzu ina jiranka”.

Cikin sanyin murya Moddibo yace.

“Toh shikenan ba matsala”.

Sannan ya katse kiran ya miƙe.

Acan ɗakin Innayi kuwa Hajja Nana na gama shan ruwan ta ajiye Cup ɗin tana sakin ajiyar zuciya.

Ahankali Innayi tace.

“Toh kici abinci”.

Girgiza kai tayi tare da faɗin.

“A'a bazan iya cin abinci ba barni kawai”.

Kallonta Innayi tayi kana tace.

“Toh Wai me ya tsananta ne har ya tayar miki da hankali haka?”.

Ƙwaffa Hajja Nana tayi tare da riƙe haɓa cike da takaici tace.

“Wai fa Khausar cewa tayi bata son Aliyu wai wani take so”.

Gyara zama Innayi tayi kana tace.

“Wai wani waye shi wanda take son?”.

Cikin fushi Hajja Nana taja dogon tsaki tare da cewa.


“Wai wani wai shi Moddibo take so Malamin Makarantar su inji Lamiɗo”.

Cikin sauri Innayi ta kalleta tare da jan dogon numfashi kana ta lumshe Idanunta tare da buɗe su cikin
sanyi ta kalli Hajja Nana kana tace.

“Moddibo?".

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.

“Eh Moddibo?”.

Jinjina kai Innayi tayi kana tace.

“Kuma wai malamin su?".

Still Kai Hajja Nana ta gyaɗa mata.

Dai-dai lokacin Moddibo ya isa bakin barandar ɗakin Innayi yana son ya mata bayanin Abba ya kira sa
akan yaje yasa yazo wurinta, yana taka step ɗin firko ne.

Ya jiyo sautin Muryan Innayi na cewa.

“Toh Moddibo ai jika nane Hajja Nana.”

Sai kuma tayi murmushi mai cike da jin dadi kana taci gaba da cewa.

“kinga shikenan faɗuwa tazo dai-dai da zama Aliyu jikana aishine Moddibon kinga sai muyi tuwonmu
manmu”.

Cikin sauri Hajja Nana ta miƙe tare da kallon Innayi kana ta zare ido sannan ta buga hannunta aƙirji tare
da cewa.

“Ji kanki?”.

Jinjina kai Innayi tayi tare da faɗin.

“Eh jikana ne Aliyu”.

Still Hajja Nana na tsaye cikin zare ido tace.

“Shine Moddibo kenan?".

Kai Innayi ta gyaɗa mata cikin tabbatarwa.

Ita kuwa Hajja Nana cikin wani yanayi tace.

“Sannan kuma shine Malamin nasu?”.


Kai Innayi ta kuna gyaɗa mata kana cikin sanyi tace.

“Tabbas shine jikana Moddibo”.

Cike da mamaki Hajja Nana tace.

“Kenan jikanki ne Moddibo wanda Khausar ke so?”.

Still Kai Innayi ta gyaɗaa karo na barkatai tare da cewa.

“Eh".

Cikin wani irin masiyacin kallo Hajja Nana ta kalleta tare da cewa.

“Aikuwa baza ta saɓu ba bindiga aruwa, ai wannan ma ta tsuniyace mara wanzuwa ai wannan ma
zancen banza ne, wannan ƙarya ne wlh. Khausar bata isa ba mu zata lalatawa tushe da asalin zuri'a”.

Cikin sauri Innayi ta mike tare da zare ido ta kalli Hajja Nana cike da mmki tace.

“Wannan wace irin kalma kike faɗa?”.

Gyara tsayuwa Hajja Nana tayi kana tace.

“Toh Innare waye bai san cewa jikanki bashi da asali ba, wani mahaukacin ne zai ɗauki ƴa ya baku? waye
zai so haɗa zuri'a da jikan ki da bashi da asali! ɗan shege da kika samu akwararo ɗan da ba'asan tushe da
Asalinsa ba!!!”.

Cike da matsanancin mamaki Innayi ke kallonta Hajja Nana ta cigaba da cewa.

“Ɗan da ba asan tabbacinsa ba asan asalinsa ba. Yaron da ake da tabbacin cewa ba ɗan sunna bane ɗan
zina ne. Shine za ahaɗa zuri'a ta dashi ai wallahi wannan ba zata yuba”.

Ta ƙarashe mgnar cikin yanayinta na ba shina ba sabo.

Cikin fushi da ɓacin rai Innayi ta watsa mata wani irin kallo tare da cewa.

“Ke dakata Hajja Nana ki kama kanki".

Dogon tsaki Hajja Nana taja tare da cewa.

“Bazan kama ba, tabbas abinda na faɗa gaskiya ne, idan har yana da uba to waye Ubansa tun da kuka
zauna tsawon rayuwarku shekaru talatin da acikin Garin Gembila waya san Asalinsa wayasan Ubansa
wayasan tushensa na faɗa na ƙara fada da ƙarfi shi ɗan shege ne ke kuma magajiya”.

Moddibo dake baranda atsaye ne, yayi wani irin jan numfashi tare da rumtse idanunsa domin tamkar
sauƙan aradu haka maganganunta suka ratsa ƙwaƙwalwarsa zuwa dodon kunnensa.

Hajja Nana kuwa cikin fushi da ɓacin rai tace.


“Shegene jikan naki na faɗa zan kuma faɗa”.

Wani irin kallo Innayi ke binta dashi zuciyarta na wani irin tafarfasa ta kalli Hajja Nana kana tace.

“Tabbas babu wanda yasan asalin Jikana sannan babu wanda yasan ina ne tushen jikana amma ke dai
baki isa ki jefe mu da mugayen kalamai irin wannan ba”.

Taɓe baki Hajja Nana tayi tare da watsa mata Harara kana tace.

“Na nawa kuma ance da kuturu Allah ya la'ance ka, jikan ki dan kwararo ne ɗa mara tushe da galihu”.

Cikin tsanananin tashin hankali da ruɗu da wani irin tsinkewar zuciya mai tafiya da nunfashi Moddibo ya
dafe kansa da hannu bibbiyu tare da rintse idanunsa...!

Littafin SAKAYYAH dai na kuɗi Hajia ba free book bane dan haka ki saya ki karanta cikin Aminci da salama
1k ne kacal kuɗin samun damar karantawa 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min
shaidar

biyanki ta WHATSAPP 09097853276

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

36

Runtse idanunsa yayi da karfi, tare dasa hannunsa duka biyu ya matse kansa, sabida yadda ya fara jin
kansa yana juyawa tare da sarawa, yayin da kalaman Hajja Nana ke dukan tsakiyar ƙoƙon kansa yana
ratsa ƙwaƙwalwar kansa tare da jin suna ratsa kunnuwansa suna yawo tamkar yanda aradu ke yawo
asararin samaniya, baki ɗaya idanunsa sun juye sun kaɗa sunyi Jawur, kab ilahirin jikinsa rawa yake kar-
kar-kar tamkar mazari cikin wani irin sauri zuciyarsa ke bugawa da kaso Cassa'in da tara cikin ɗari, tana
mai wanzar da jini litter-litter a cikin dukkan daƙiƙu yana watsashi wa jijiyoyin jikinsa.

Hakan yasa tuni rigarsa ta fara jikewa da zufa, duda yanayin garin Gembila da ba'a musu zafi.
Sai ga tashin hankali ya sashi tsats-tsafo zufa sabida yadda zuciyarsa ke bugawa da Masifaffen ƙarfi yayin
da numfashinsa ke fusga tamkar zai bar ganganar jikinsa, cikin tsanananin tashin hankali da wani irin
masifaffen juyi da kansa keyi ya ƙara matse kansa da hannu bibbiyu, da ƙyar ya iya daga ƙafarsa ya sauka
daga barandar ya nufi side ɗinsa yana tafiya tare tangaɗi tamkar ɗan maye yayin da kuma jiri ke ɗibarsa.

Yana cikin tafiya tamkar zai faɗi ya tsinkayo muryar Innayi cikin tsananin fushi da takaici cikin zafin zuciya
tace.

“Zaki sha mamaki kuwa.

Hajja Nana zan nuna miki ƙarfin iko da isan ɗan shegen da kike faɗi. Zaki gane kinyi kuskure ambatonsa
da wannan sunan da yafi ƙarfinsa. Auren nan kuma da izinin Ubangiji tamkar anyi sa angama ma, in dai
wannan auren nen kika tashi ki kace zaki yaƙesa sannan kika ce zaki hana toki sa. Aranki anyishi an ɗaura
shi angama domin ke dai baki isa ki haramta abinda Allah ya halastaba wlh muddin ina raye toh in Sha
Allah kamar ma anyi auren nan an gama zan shayar dake mamaki”.

Wani irin kallon rainin hankali me ɗauke da zafin zuciya Hajja Nana tabi Innayi dashi.

Ita kuwa Innayi. Cikin fushi ta cigaba da cewa.

“Babu wani mahaluki na duniya daya isa ya hana wannan ɗaurin Auren sai Ubangiji daya halicci sammai
da ƙassai. idan har kinga wannan Auren bai kasance ba to daga Rabbus Sanawati ne amma ba daga ke
Hajja Nana mai kaɗa kai kamar Ƙadangariya ba”.

Wuhuhu ina wuta Hjja na ta faɗa ciki.

Cikin fushi da hatsala Hajja Nana dake ƙoƙarin fita ta tsaya tare da juyawa ta kalleta sai kuma tayi
murmushi tare da gyara tsayuwar ta kana tace.

“Wani ƙarfin iko ko kuma isa. Ɗan shege ke dashi? Ai sai dai kuje kunemi watsatstsiya ƴar gaba da Fatiha
ku Aura masa, amma dai ba jikata dake da asali da tushe ba zuri'ata tayi miki nisa sai dai hange daga
nesa?”.

Afusace Innayi da Idanunta suka kaɗa tamkar garwashi tace.

“Tabbas zaki ga isa da kuma ƙarfin Iko irin na ɗan shegen da kike faɗa agaban idanunki za'a ɗaura
Aurensa da Khausar sannan ya ɗauketa su tafi ke babu yanda kika iya, zakisha mmkin ganin tushensa
daya girmi tunaninki ya kuma zarta zatonki. domin ke ba kowa bace a kansa, Allah ya wadaran aminiyar
da bata mutunta amintaka, kin kasance mara ɗa'a da sanin ya kamata!”.

Ita kuwa Hajja Nana mugun kallo ta watsawa Innayi tare da nuna kanta da tsaya kana tace.

”Ni kika faɗawa haka?”.


Kai Innayi ta gyaɗa cikin tsawa tace.

“An faɗa miki wacece ke?Ko kina tunanin nan ma Jauro yaya ne da kike baza ikon ki da mulkinki kina
kaɗa kai uwa ƙadangaruwa, kina abinda kika ga dama? to a hir ɗinki ki sani kece kika shigo muhalli na
toh ki sani duk da cewa mu muke neman aure a ƙarƙashin ku ba za ki taka muba in barkiba domin mace
bata bada Aure dan haka ki ficemin agidana”.

Wani irin dogon tsaki taja kana tace.

“Ko da baki ce in fice miki agida ba dole zan fita, amma kisa Aranki badai.

Ɗai shegen jikanki da tsarkakakkiyar jikata su haɗa Aure ba”.

Tana faɗin hakan

ta ida ficewa daga ɗakin amma still Idanunta na cikin dakin tace.

“Dama ace ansan tushe ansan asalinku sannan ansan jikan ki tsarka kekkene wanda aka haifa ta sunna,
to ba komai amma jikanki da yake Najasa wanda aka haifa ta hanyar ƙazanta ba zaiyu abashi auren jikata
ba, zaki ga ƙarfin Ikona da isata sannan kuma da Izzata akan al'amarin auren nan”.

Innayi da zuciyarta ke wani irin tafarfasa tace.

“Toh mu zuba mu gani kada ki fasa idan har ke kin cika mai karfin iko da Izzah”.

Ƙwaffa Hajja Nana tayi tare da sauƙa daga barandar ta juya fuuuu kamar zata tashi sama ta nufi waje.

Moddibo kuwa yana shiga falonsa ya maida ƙofar ya rufe, kana ya zame tare da zama aƙasan daɓas ya
jingina bayansa da jikin ƙofan Falon lokaci ɗaya yashiga kokuwa da numfashinsa dake ƙoƙarin ɗauke wa.

Atake wani irin azabebben kuka mai gunji ya kufce masa cikin raunin murya da tsantsar tashin hankali
ya shiga furta.

_“Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha Ya wadud³ ya zul'arshil Majeed ya fa'alillima
yurid As'aluka bi izzatil lati layura wa mulki kallazi la yurad Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n_”.

Cikin wani irin tashin hankali ya cigaba da karanta duk wata addu'a da tazo bakinsa.

Kana wani azabebben kuka mai sa rawan jiki ya sake kufce masa lokaci ɗaya wani masifaffen zazzaɓi ya
rufe sa cikin kiɗima ya fara zantukan zuci. Aransa yace.

Innalillahi Wa'inna ilahi rajiu'n. Shin wannan wace irin Masifa ce? wani irin rayuwa ce take fukantoni!
sannan inane tushena.

Ko-ko dai da gaske ne kalmar wannan matar gskyace, cewa bani da asali.”
Sai kuma ya rumtse idanunsa da ɗan karen ƙarfi.

Tare da fara ƙanana mgn a saman lips dinsa dake tsuma.

“Hahhhh da ƙamshin gaskiya acikin kalaman matar nanfa, domin da inada tushe da asali da tuni Innayi ta
kaini garesu sannan ta nuna min tushena shin da gskene kenan bata hanyar aure sunnanr Manzon Allah
Sallallahu alaihi Wasallama aka samar da niba Yah salam.”

Sai kuma ya fara mgn cikin rawan murya.

“Ya Ubangiji Allah kada kasa zargina da zatona na tsawon shekaru ya tabbata ta wajen furucin wannan
matar.”

Ya ida mgnar tare da kife kansa bisa guiwowinsa.

Domin shi akaran kansa ya daɗe yana tunanin wataƙil shi ɗan shegene shiyasa Innayi bata taɓa faɗa
masa Asalinsa ba kuma bai taɓa ganin wani saba dangi na gefen uwa ko uba, ya kuwa san bazai taɓa
yiwuwa ace kab duniya bayi da wani ɗan uwa ko ƴar uwa da za'ace nase sai dai in har shi ɗin ɗan Shegen
ne, shiyasa Akullum yake tsoron tambayarta wanene shi domin kada yaji abinda zai tarwatsa masa
ƙwaƙwalwarsa da kuma lissafin sa sabida tsoron hakanne yasa baya bincike kan tushensa sabida shi
kansa ya fara zargan lamarin.

Lumshe Idanunsa yayi hakan ne ya bawa hawayen ciki damar kwaranyowa da masifar zafi suka zubo
masa, cikin ransa yace dama nasani dole irin wannan ranan zai zo ranan da wasu mutane zasu fuskance
mu gaba da gaba su tuhumi nagartata. sannan su kirani da shege idan har basu samu gamsasshiyar
amsaba. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.

Hajja Nana kuwa Afusace ta fita daga gida tare da buga Murfin gate din tana zuwa ta buɗe motar tashiga
tana wani irin huci na tsananin ɓacin rai da takaici kallon Baffa Jimeta tayi kana tace.

“Mu tafi baki ɗaya mutanen cikin wannan garin basu da hankali basu san abinda suke yiba”.

Cikin sanyin murya Baffa Jimeta yace.

“Subhanallah Hajja Nana kada kice haka kada kiyiwa baki ɗaya mutanen garin nan kuɗin goro sam hakan
be cancantu ba”.

Harara ta watsa masa kana cikin fushi tace.

“Rufe min baki kaja mota mutafi bana son maganar banza”.

Kai ya gyaɗa kana yayiwa motar key suka bar kofar gidan kai tsaye hanyar Jauro yaya suka nufa.

Anutse Malam Liman ya juya tare da kallonta kana cikin sanyin murya yace.
“Kiyi haƙuri Hajja Nana ita rayuwar nan na duniya komai sai da haƙuri ake fuskantar sa, abinda fa hakuri
bai warware saba tofa rashin haƙuri ba zai warware saba, dan Allah ki kwantar da hankalin ki koma
menene Khausar tayi yarinya ce bazaki sa shi amizani da zai tayar miki da hankali har haka ba”.

Cikin sauri Hajja Nana data tsirawa madubi ido ta juya ta kallesa kana cikin fushi tace.

“Wai Ni Khausar zata dubi tsabar Idona tace bata son Aliyu”.

Anutse Baffa Jimeta dake driving ya dan juya tare da kallonta kana cikin sanyin murya yace.

“Toh Hajja Nana menene aciki dan Khausar tace batason Aliyu ainima kaina bazan yiwa Khausar auren
dole ba, duk da cewa Aliyu ya kasance ɗana amma bazan tauyeta in Aura mata shi adole ba tunda bata
son shi”.

Afusace Hajja Nana ta buga masa tsawa tare da faɗin.

“Rufe min baki me kake nufi kenan?”.

Ahankali ya sassauta muryarsa cike da girmamawa yace.

“Hajja Nana kiyi haƙuri ki gafarceni Idan har abinda zan faɗa zai ɓata miki rai, amma abinda nake nufi a
aura mata wanda take so.”

Sheƙeƙe Hajja Nana ke Kallonsa da Idanunta dake cike da Masifa cike da iko da kuma Izza tace.

“Wannan ne kuma baku isaba ba'a haifi wanda ya isa ya ƙaddamar da wannan abin ba”.

Ajiyar zuciya Baffa Jimeta ya sauƙe tare da kallon Baffa Liman daya tsirawa titi idanu kana ya sake
sassauta muryarsa tare da cewa.

“Dan Allah Hajja Nana ki gafarceni Ayiwa yarinya abinda take so”.

“Bafa ku isa ba”.

Ta faɗa a taƙaice.

Kai Baffa Jimeta ya gyaɗa batare da yace Uffan ba ya cigaba da Driving.

Ahankali Malam Liman ya sauƙe Ajiyar tare da juyawa ya fuskanci Hajja Nana da kyau kana yace.

“Adda Hajja to dan tace batason Aliyu shine hankalin ki ya tashi haka?”.

Sake baki Hajja Nana tayi tare da cewa.


“Au don ne ma kake cewa, wato baka ɗauki abinda muhimmanci ba, wannan ɗin bai kai hankalina ya
tashi bane?Sannan ma wanda tace tana so ɗin dama ace mutum me tushe ne da asali to ai da sauƙi”.

Dogon numfashi Malam Liman yaja tare da sauƙewa kana yace.

“Toh waye ne tace tana son din ne?”.

Dogon tsaki Hajja Nana taja tare da yin ƙwaffa kana tace.

“Wai wani Malamin Makarantar sune, Moddibo ne ko Momodu ne ohon mata, wannan yaron dai da
Malam Arɗo yaje dashi Jauro yaya ashekarun baya sannan akwanakin baya muka je muka sameshi
agidan Malam Arɗon tofa wai shi take so”.

Jinjina kai Malam Liman yayi alamun ya gane.

Ita kuwa cike da takaici ta cigaba da cewa.

“Toh Jikan wannan Ƙawar tawa Innare, kuma sanin kanku ne tunda nasha baku labari cewa babu wanda
yasan asalinsu, sannan babu wanda yasan tushen su a iya binciken da nayi a iya sanin su da nayi muke
zuwa Makka tare yaron nan ɗan shegene”.

Cikin sauri Baffa Jimeta dake Driving ya juya ya kalleta jin furucin daya fito daga bakinta.

Harara ta galla masa kana ta cigaba da faɗin.

“Ɗan shegene bashi da asali ɗane da aka haifeshi ta hanyar zina ta ƙazantacciyar hanya, shin taya zamu
haɗa alaƙar aure dashi kalen ya lalata mana sunan zuri'a asamu abin faɗa aciki.

Girgiza kai Malam Liman yayi kana ahankali ya juya da fuskarsa gareta ya fuskanceta sosai yace.

Um-uhum kiyi haƙuri Addah Hajja kada ranki ya ɓaci”.

Girgiza kai tayi tana huci tace.

“Ai dole raina ya ɓaci Liman”.

Gyara Alkyabbar sa yayi kana yace.

“Dan Allah kiyi haƙuri amma kada ki sake aibanta yaron, domin koda maganar ki hakan take, sam bai da
ceba duk da cewa kin bada hujjarki akan cewa shi shegene, tofa koda ya kasance shegen ba laifinsa
bane, laifin Iyayensa ne da suka haifesa ta hanyar zina”.

Tallafe kunci Hajja Nana tayi tare da tsira masa ido babu keftawa, Malam Liman kuwa cikin sanyin murya
da son nusar da ita ya cigaba da cewa.
“Sannan babu inda Shari'a ta hana Auren wanda aka haifesa ta hanyar zina.

Shari'a bata haramta Aurensa da Khausar ba, bai haramta ba a musulunci sai dai idan har akwai wani na
ƙasu atare dashi wanda yake aikatawa shine zai zama lalura, sannan dan Allah irin wa'annan kalaman
idan zaki furta su ki rinƙa tauna su saboda suna da nauyi”.

Atsawace ta kallesa kana tace.

“Liman Karka fara yimin wannan wa'aze wa'azen'kan nan masu sauya ra'ayi mutum”.

Cike da ladabi malam Liman ya sunkuyar da kansa ƙasa kana yace.

“Dole ne in fara yimi ki wa'azi, domin kada ki faɗa cikin furucin da zai kaiki ga fushin Ubangiji”.

Salati ta rafka tare da riƙe haɓa kana tace.

“Ikon mai duka Fadar gaskiyar ne zesa in fada cikin fushin Ubangiji, ko kuma yana da Uban ne ai tun yana
jariri yana cikin tsumma da ka gani kasan cewa ƴarta ce ko ɗanta ya haifo shege ya kawo mata shiyasa ta
gudu dashi saboda abin kunya yau tsawon shekara talatin harda ɗoriya kenan bata da wata ƙawa sama
dani amma koni bansan tushen suba, bansan asalinsu ba sannan bansan daga ina suke ba”.

Girgiza kai Malam Liman yayi kana yace.

“Kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki amma. Duk da haka Addah Hajja baki da hujjar shegan tasa”.

Cikin sanyi ya cigaba da yi mata nasiyya yana nuna mata kuskuren abinda take amma firrr Hajja Nana
taƙi sauraronsa. Baffa Jimeta kuwa Uffan bai sake cewa ba har sukayi nisa da tafiya.

Ɓangaren Moddibo kuwa wani irin zazzafan zazzaɓi mai zafin gaskene ya lulluɓe sa wanda gaba ɗaya
ilahirin jikinsa ke rawa.

Innayi dake tsaye ɗaki ma baki ɗaya jikinta rawa yake sai Safa da marwa take daga ƙarshe ta zame ta
zauna kana ta fashe da kuka cur-cur-cur tamkar ƙaramar yarinya cikin Muryan kuka tace.

“Bansani ba Aliyu bansan wannan abin zai zame maka tabo ba acikin al'amuran kaba, bansan zai zame
maka na ƙasu da kuma abin nunawa acikin al'amuran kaba Aliyu”.

Cikin tsanananin tashin hankali da tarin damuwa take maganganu tana zubar da hawaye.

Acan ɓangaren Abba kuwa bayan sun gama waya da Moddibo number Malam Ahmad yayi dearling jin
yayi Picking yasa yayi gyaran murya tare da sallama kana suka gaisa bayan sun gaisa Abba ya sauƙe ajiyar
zuciya tare da gyara zamansa kana cikin sanyin murya yace.
“Dan Allah Malam idan anyi sallar La'asar ko zan samu ganinka?”.

Cikin daddataku yace.

“Toh badamuwa Insha Allah zanzo, Allah dai yasa lafiya?”.

Jinjina kai Abba yayi tare da faɗin.

“Eh babu komai Allah ya kawo ka lafiya”.

Bayan Malam Ahmad ya katse kiran ya juya ya kalli Ummi dake gefensa kan 2sitter sai kuma Asma'u da
Bashir dake kan 3sitter cikin sanyin murya yace.

“Abban Jameelu ne ya kirani”.

Cikin alamun damuwa Ummi tace.

“Lafiya kuwa!?".

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Lafiya lau”.

Girgiza kai tayi hawaye na taruwa akwarmin Idanunta tace.

“Ka dai ƙara tabbayarsa”.

Ganin bata gamsu bane yace.

“Toh bari in tambayan”.

Ya ida maganar tare da dearling number Abba.

Abba na ɗagawa Malam Ahmad yayi Sallama kana yace.

“Dama na faɗawa Fatima gashi-gashi yanda mu kayi to amma tace wai dan Allah meyake faruwa lafiya
kuwa?”.

Kai Abba ya gyaɗa cikin sanyin murya da tarin damuwa yace.

“Eh lafiya lau dama ina so ne kuɗaɗen da suka haɗa na motar ta data saida da kuma na Sarƙoƙinta tunda
ga yanda Ubangiji ya ƙaddara to shine kuɗin nake so kazo in baka su sai ka maida mata su, sannan kayi
mata bayani tare da kwantar mata da hankali”.

Kai Malam Ahmad ya gyaɗa tare da faɗin.

“Toh shikenan bari zan faɗa mata”.


Ahankali ya juya ya kalli Ummi bayan ya katse kiran kana ya mata bayanin duk yanda sukayi.

Cikin rauni ta sunkuyar da kanta hawaye na kwaranya daga Idanunta Shar-shar-shar suna zuba akuncinta
cike da tausayawa suke kallonta musamman Asma'u lokaci ɗaya itama Idanunta suka fara zubar da
ƙwalla.

Asanyaye Ummi ta ɗago kanta tare da kallon Malam Ahmad Muryanta na rawa tace.

“Kace masa bana son Kuɗin Na yafe me zanyi da kuɗin da suka kasa ceto min Jameel me zanyi dasu?.

Me zanyi da duk wani kayan ƙawa bana so bana ɓuƙatar su nayafe su duniya da lahira bana ƙaunarsu”.

Anutse Malam Ahmad ya girgiza mata kai cikin rarrashi yace.

“Kada kice haka Fatima kiyi haƙuri Jameelu addu'a zaki yi masa, kuɗin nan kada kice ba zaki karɓaba,
idan har kika ce ba zaki karɓa ba zaki sake saka Mahaifinsa cikin damuwa da tashin hankali aransa”.

Kai ta girgiza tare da miƙewa ta nufi Bedroom ɗinta still hawaye na bin kuncinta.

Asma'u kuwa kife kanta da jikin cushin tayi tare da fashewa da sassayan kuka me gunji cikin sauri Bashir
ya ɗagota tare da share mata hawaye cikin sanyin murya yace.

“Asma'u Yah Jameel baya ɓuƙatar kukan mu addu'ar mu kawai yake buƙata, dan Allah ki daina yi masa
kuka kinji, na tabbata Yah Jameel baya son wannan kukan”.

Kai ta gyaɗa masa still hawaye na bin fuskarta tace.

“Bashir ya zanyi idan na tuna Yah Jameel ya barmu bari na har abada nakan ji zafi da ƙuna acikin
zuciyata, nakan ji raɗaɗi mai zafin gaske nakanji.

Tamkar zuciyata zata fashe”.

Cikin sanyin murya Bashir yace.

“Toh ya zamuyi da hukuncin Ubangiji Asma'u haka Allah ya tsara Yah Jameel ba zaiyi tsawon rai ba, koda
ace basu sace sa sun kashe ba na tabbata ba zai wuce wannan kwanakin ba mu dai kawai addu'ar mu
yake buƙata a hankali kuma waɗanda suka aikata masa hakan zasuga SAKAYYAH mabayyaniya addu'a
kawai zakiyi ta masa kinji”.

Jinjina kai tayi kana tace.

“Inayi kuma zan cigaba da har ƙarshen rayuwata da izinin Ubangiji”.

Ummi nashiga Bedroom ta zaune gefen gado tare da fashewa da kuka Malam Ahmad na shiga cikin
daƙin ya zauna gefenta kana ya sanya hannunsa tare da janyota ya mannata da jikinsa cikin sanyin
murya yace.
“Kiyi hakuri ki daina kuka Fatima, ki yiwa Jameelu addu'a Ubangiji ya masa rahma sannan madadin kice
ba zaki karɓi kuɗin nan ba ki sake sakawa mahaifinsa damuwa to ki karɓa”.

Cikin rauni Ummi ta sake manna kanta da ka fadarsa kana ta cigaba da sheshsheƙan kuka.

Tafin hannunta Malam Ahmad ya damƙe acikin nasa kana ya cigaba da cewa.

“Idan yaso idan kika amshi kuɗin sai kiyi amfani dasu wajen yiwa Jameelu Sadaƙatul Jariya.

Kamar Gina Masallaci, Ko kuma gidan marayu, Ko Asibiti,ko makarantar addini, ko kuma yin Bohorle
rijiya da dai sauransu da nufin Allah ya kai ladan garesa kinji ko Fatima kada ki butulcewa Ubangiji”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana yace.

“Kada kice ba zaki karɓa ba Ubangiji shi yabamu Jameelu, sannan kuma shi ya ɗauke Jameelu bamu da
abinda zamu yiwa Jameelu sama da addu'a shine kaɗai soyayyar daza mu nuna masa amma idan kika bar
kuɗin ya mahaifinsa zaiyi dasu?”.

Jinjina kai Ummi tayi cike da gamsuwa kana tace.

“Shike nan insha Allah zanyi yanda kace Allah yajiƙan Jameelu Allah ya gafarta tamasa Ubangiji ya
jaddada rahma agaresa”.

Malam Ahmad na share mata hawaye ya amsa da.

“Ameen”.

Ɓangaren Hajiya Lami kuwa zaune take afalonta cikin sanyi Samira ta fito daga Bedroom ta zauna
gefenta tare da tsira mata idanu.

Kallonta Hajiya Lami dake riƙe da wayarta tayi kana tace.

“Lafiya kuwa Samira?”.

Girgiza kai Samira tayi cikin sanyin murya tace.

“Mommy cikina ke ciwo”.

Ahankali Hajiya Lami ta ajiye wayarta tare da tsira mata Ido kana tace.

“Meke damunki ne kwanan nan kina yawan complain din cikin ki yana ciwo”.

Rau-rau tayi da ido still Muryanta na rawa tace.

“Mommy nikam wannan ciwon cikin ya fara damuna,


duk fa lokacin daya Murɗa Mommy wani farin ruwa ne yake fito min ta gaba na.

Mommy har saina sa Path agabana kamar mai yin period kuma ba jini bane kawai ruwa ne yake fito min
mai ƙarni da masifar wari”.

Zare ido Hajiya Lami tayi tare da cewa.

“Ruwa kuma?,Ni Lami wani irin ruwa kenan?”.

Cikin rawan murya Samira tace.

“Ruwane kamar Sparm yake fita sannan da yawa da yauƙi yake fita Mommy ga wari da ƙarnin Masifa
yanzu bakya jin ƙarnin da na matsoki”.

Da sauri ta jujjuya mata kai alamun a'a.

Ita kuwa Samira cike da damuwa taci gaba da cewa.

“Nifa idan na sunkuyar da kaina ƙasa ƙarnin da warin nakeji”.

Girgiza kai Hajiya Lami tayi tare da haɗiye wani abu mai masifar ɗaci kana ta kalli Samira tare da cewa.

“A'a Samira nikam ban jiba. Amma tun yaushe ya fara miki haka?”.

Kallonta Samira tayi tare da faɗin.

“Yafi kwana biyar idan naji cikina ya Murɗa ya Murɗa, sai wannan abin ya zubo da fari ya fara zubowa
kaɗan-kaɗan, to amma yanzu ya fara zubowa dayawa, sannan ciwon cikin yana ƙaruwa baki daya
hankalina ya tashi Mommy!”.

Cikin sauri Hajiya Lami tace.

“To bari zan shirya Inje wajen boka Kar'uzu in Faɗa masa halin da ake ciki”.

Suna cikin magana suka ji ƙaran buɗe Bedroom ɗin Abban Samira.

Ganinsa yasa Hajiya Lami wayancewa da faɗin.

“Eh Samira Insha Allah Idan Daddy ki ya bari zanje induba Aminan Hajiya Bunayya dake fama da ciwon
ciki”.

Cikin nutsuwar Kamilin Dattijo dake cike da kamala da nutsuwa ya ƙaraso cikin falon tare da kallon Hajiya
Lami cike da dattako yace.

“Ayyah Subhanallah lallai dai naji kuna maganar ciwon ciki ashe Amina ce ba lafiya Allah ya sawwaƙa”.
Da sauri Hajia Lami tace.

“Amin dai”.

Shi kuwa yana gwara zaman hular kansa yaci gaba da cewa.

“Shiyasa na kwana biyu ban gantaba ashe ba lafiya ne?”.

Kai Hajiya Lami ta gyar'ɗa tare da cewa.

“Eh wallahi dama so nake idan ka fito zanje in dubata Idan ka amince”.

Jinjina kai yayi kana yace.

“Ayyah to ba matsala ki Gaishe su”.

Acan gidan Lamiɗo kuwa Hajiya Bunayya na shiga falonta ta kalli Amina dake zaune kan 2sitter gyara
zama Amina tayi tare da cewa.

“Mommy wai ɗazu hayaniyar me nake jine ina waya da Uncle Naseer ne yana gaya min tsarin ginin
gidansa da ake gyarawa a cikin Abuja yace min in anyi aure zamu zauna a nan na wata ɗaya zuwa biyu
kafin mu tafi India, shiyasa ban fito ba”.

Cikin jin dadi tace.

“Alhamdullah kice dai abu yanata kankama”.

Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.

“ Eh Ummah Amman Hayaniyar me akayi ɗazun”.

Taɓe baki Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.

“Ooo Kakar Khausar ce kuma yau tazo tana ta bala'i, banma san bala'in da take ba na dai ji tana cewa
Khausar bata da kunya zata kalli tsabar idonta tace batason mijin da ta zaɓa mata tana da wanda take
so, to bansan ya ake ciki ba dai. Ni dai tsoro na kaddai Nasseru take so?”.

Gyara zama Amina tayi tare da Girgiza kai kana tace.

“Ba dai Uncle Naseer ba Dan ko magana bata mishi, sai in shi ya mata, shima kuma baya mata magana
sosai da nace masa bana so.

Sai dai ko ina wani can daban wayasan mata”.

Cikin jin daɗi Hajia Bunayya tace.

“Ato da sauƙi”.
Ita ko Amina gyara zama tayi tare da cewa.

“Uncle Naseer Kam yanzu ma wayar da muke yine, ya hanani fita.

Kuma cewa yayi anfara hada kayan lefe sannan kuma idan an tashi da kayan lefe da kayan gishi da goro
da sadaki da kayan rufi duk za ahaɗa rana ɗaya za akawo”.

Murmushi Hajiya Bunayya tayi tare da Jinjina kai.

Ajiyar zuciya Amina tayi kana ta cigaba da cewa.

“Kuma yace nan da wata ɗaya za'a ɗaura Auren mu sannan ana gama bikin a Abuja zamu tare baza mu
wuce wata biyu ba in yayi yawa ne uku zamu wuce India sannan zai nema min admission In cigaba da
karatuna”.

Dariya Hajiya Bunayya tayi tare da ran gaɗa guɗa kana tace.

“Alhamdulillah burina ya cika haka nake son ji da ace mun na cewa batun wannan yaron Jameel gashi
ƴan Kidnapping sun kashesa a wofi”.

Kai Amina ta gyaɗa tare da cewa.

“Ai dai kam Umma Allah ya rufa mnaasa asiri da na nacewa batun Malam Jameel da yanzu na zama
matar Mamaci ina takaba”.

Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa tare da faɗin.

“Aikam Allah ya tsareki yaje can Allah ya jikansa da Rahma”.

Cikin sanyin murya Amina tace.

“Ameen dai tun da yana da kirki Allah ya jikansa Allah yasa ya huta amma dai na kama dahir dana kama
Uncle Naseer”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.

“Kin kama dahir kam”.

Asiya ce da bata cika shiga mgnar suba, tunda Hajia Bunayyah tace mata zata tsine mata in tana
damunta da batunsuji tsoron Allah, a hankali ta ninke hijabin da tayi salla dashi tare da miƙewa ta fito
falo tana maiyi musu addu'ar shiriya.

Ita kuwa Amina da baki ta nunata.

Shashar uwa sai dariya tayi.


Suna cikin hiran wayar Hajiya Bunayya ya hau ruri tana dubawa taga Hajiya Lami cikin sauri tayi Picking
tare da kaiwa Kunnenta Hajiya Lami najin tayi Picking batare da tayi Sallama ba ta fara kora mata
jawabin abinda Samira ta faɗa mata.

Zare ido tayi cike da damuwa tace.

“Subhanallah toh Meyesa haka?”.

Cike da damuwa Hajiya Lami tace.

“Ban saniba amma ki shirya da daddare bayan sallar Isha'i ki rakani”.

Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh nima zanje dama in Faɗa masa maganar Amina don tuni anfara hada kayan lefe, Gishiri, Goro,
kayan rufi, da sadaki duk lokaci ɗaya za'a kawo kinga hankali ya kwanta”.

Jinjina kai Hajiya Lami tayi tare da faɗin.

“A hankali ya kwanta kam bari sai nazo ɗin dai”.

Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa kana tace.

“Toh sai kinzo ba komai ki kwantar da hankalin ki”.

Aɓangaren Innayi kuwa har maghariba bata ji motsin Moddibo ba sosai hankalinta ya sake tashi.

Wunin ranan yini tayi tana kuka wanda lokaci ɗaya zazzaɓi ya kamata baki daya tunaninta ya ta allaka
akan idan ta mutu ya Moddibo zai kasance awannan gari ya zaiyi.

Wasa-wasa har aka Idar da maghariba da Isha'i har misalin goma ba Moddibo ba labarinsa cikin sanyin
jiki da tashin hankali ta miƙe ta nufi sashen sa tun kafin ta ƙarasa hawa barandar ta jiyo sheshsheƙan
kukan sa cikin sauri ta ƙarasa hawa barandar tare da Murɗa Kofar falon tashiga kan Sallaya ta hangosa
yayi Sujjada yana sheshsheƙa.

Cikin sauri ta zauna gefensa Muryanta na rawa tace.

“Subhanallah haba, Aliyu!, Haba Aliyu!!. Meyesa haka Aliyu ka ɗauki dangana mana kuka shine abinda
zakayi ta raka Jameelu dashi arayuwar ka wannan soyayya itace zaka nunawa Jameelu kenan?”.

Anutse ya ɗago daga Sujjada tare da yin tahiya kana yayi sallama yana sheshsheƙa kana ya daga
hannunsa biyu sama cikin raunin murya yace.
“Ya Allah Ubangiji kasa mafarki nake, Allah kasa in farka daga wannan hautsinennen mafarkin da
nakeyi”.

Ahankali Innayi ta matsa kusa dashi tare da Kallonsa cikin sanyin murya tace.

“Haba Aliyu Meyesa kakeyi yin haka? ka kwantar da hankalin ka babu abinda ya gagari lamarin Ubangiji”.

Domin Ita batasan cewa yaji maganar da sukayi da Hajja Nana ba.

Ahankali ya ɗago idanunsa da suke kada sukayi jawur tamkar garwashi cike da mamaki take kallon yanda
idanunsa suka sauya launi Muryanta na rawa tace.

“Aliyu lafiyar ka kuwa?”.

Kai ya Girgiza tare da cewa.

“Bakomai”.

Ya faɗa tare da lumshe Idanunsa domin ya rasa ta yaya zai fara tambayarta shin inane asalinsa shin waye
mahaifinsa su waye ne tushensa, yanaso ya tamyan amma ya najin tsoro da fargaba da taraddadin ya
tambaye, ya zama cewa kalaman da Hajja Nana ta faɗa da kuma zarginsa na tsawon shekaru ya zama
gaskiya hakan yasa yaji tsoron tambayarta kamar yadda ya saba, haka ya meda tambayar cikin ransa,
sunkuyar da kansa ƙasa yayi.

Innayi kuwa cikin sanyin murya ta cigaba da rarrashin sa domin duk azatonta mutuwar Jameel ya tuna
cikin rarrashi ta cigaba da cewa.

“Aliyu kayi haƙuri kowa da irin ƙaddarar da Ubangiji yake masa Addu'a zamu masa”.

Sunkuyar da kai Moddibo yayi hawaye ya cigaba da kwaranya daga Idanunsa.

Innayi kuwa cikin sanyin murya ta cigaba da cewa.

“Kada kayi kuka Aliyu ko wani irin matsala ka shiga arayuwar duniya kada ka butulcewa Ubangiji da irin
wannan kukan, babu abinda zai kawo maka banda tashin hankali da damuwa”.

Ta ida maganar tana zubda zafafan hawaye, kukan abubuwa biyu ne suke haɗe mata alokaci ɗaya
kalaman Hajja Nana da kuma halin da taga Moddibo aciki yayi masifar ɗaga mata hankali.

Anutse Moddibo yasanya tafin hannunsa yashiga share hawayen fuskarsa muryarsa na rawa yace.

“Toh shikenan Innayi nayi shiru dan Allah kema ki daina kuka Ubangiji Allah yarufa mana asiri”.

Cikin muryan kuka tace.

“Ameen ya Allah”.
Miƙewa tayi tare da fita ba daɗewa ta dawo hannunta riƙe da Warmers din abinci ta ajiye masa
agabansa kana tace.

“Gashi kaci abinci”.

Kai ya Girgiza kana yace.

“A'a Innayi bazan ciba aƙoshe nake”.

Jinjina kai tayi tare da miƙewa ta dawo hannunta riƙe da wani bowl dake ɗauke da Fruit ta ajiye masa
kana tace.

“Toh kaci wannan”.

Kai ya gyaɗa kana ya fara ci ahankali.

Ganin ya fara ci yasa ta sauke ajiyar zuciya tare da cewa.

“Toh sai da safe”.

Sannan ta fice domin bata da nutsuwa atare da ita.

Washe gari Da safe Ganin Moddibo bai zoba yasa Abba yashiga motarsa kai tsaye gidansu Moddibo ya
nufa yana isa yayi Parking ya fito daga bakin gate ɗin farko ya tsaya yayi sallama Innayi dake Alwalan
sallar Walha ta miƙe bayan ta ida ta nufi ƙofar tare da amsa masa Sallamar.

Bayan sun gaisa Abba ya gyara tsayuwar sa tare da cewa.

“Dama Moddibo ne nake son ganinsa kuma bai zoba”.

Cikin sanyin murya Innayi tace.

“Hmm Moddibo ai jiya wuni yayi aɗaki yana kuka babu inda ya fita”.

Cike da alhini Abba yace.

“Subhanallah ni kuwa dama al'farma nazo nema Aliyu yamin taimako”.

ya ida mgnar cikin alamun neman al'farmar.

Haka yasa Innayi ta ɗan juyo ta kalleshi da kyau kana a hankali tace.

“Alhji Bashir ai ka wuce haka, kawai Umarni zakiywa Aliyu, kamar yadda kakeyiwa Jameelu da izinin
UBANGIJI kuma zai cika maka umarninki. Aliyu ɗan ka ne, kadama kacemin komai kawai ka bashi umarni
yamaka duk abinda kakeso ni kam na amince duniya da ƙiyama”.

Cikin jin daɗi kara da kawaicinta gareshi yace.


“Nagode da mutuntaka Allah ya bar zumunci”.

Amin tace tare da juyawa

tayi gaba.

Abba na bin bayanta zuwa falon Moddibo tsaye Abba ya gansa afalon yana ƙoƙarin fita.

Cike da ladabi yace.

“Ha'a Abba kazo ne?”.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“Eh naga shiru-shiru Aliyu ba kazo ba tun jiya”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da faɗin.

“Eh dama yanzu nake shirin fita zan biya ta gidan Ummi sannan na ƙara so wajenka”.

Ahankali Abba yace.

“Allah sarki to zamu tafi tare”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.

“Toh”,Sannan suka fita.

Cikin sanyi da

disesshiyar murya yace

“Abba na rasa ta ya zan gayawa Innayi batun

tafiyar nanfa”.

Juyowa Abba ya ɗan yi

ya kalleshi na second uku kana yace.

“Munyi mgnar da Innayi tace, babu matsala duk abinda ya dace in saka kayi min ta amince”.

Cike da mamakin amincewar tan yace.

“Ta yarda”.
Ka Abba ya gyaɗa mishi yana mai ci gaba da tuƙi.

Acan gidan Lamiɗo kuwa tun bayan tafiyar Hajja Nana Mommy ta fita sabgar Khausar da zaran ta gifta
gefen da Mommy take Mommy zata kawar da kanta tare da dauke Idanunta akanta kana Uffan bata ce
mata ba ko da safe da Mommy ke haɗa breakfast Khausar na shiga da niyyar tayata ta batare da tace
mata Uffan ba ta nuna mata hanyar fita cikin rauni tace.

“Dan Allah Mommy kiyi haƙuri na tuba”.

Cikin fushi Mommy ta nuna mata hanyar fita ba tare da tace komai ba.

Da gudu Khausar ta juya tare da nufar Bedroom ɗinta tana shiga ta faɗa kan gado tare da fashewa da
matsanancin kuka.

Haiydar ne yashigo falon jin sheshsheƙan Kukan ta a Bedroom yasa ya nufi Bedroom Cike da kulawa
yace.

“Adda Khausi Meye sameki?”.

Ɗago Idanunta dake jiƙe da ruwan hawaye tayi tare da Kallonsa tace.

“Haiydar Mommy fushi take dani”.

Cike da Mamaki yace.

“Fushi kuma? to me kika mata?”.

Kai ta girgiza still tana kuka tace.

“Nima ban sani ba amma Mommy fushi take dani”.

Ajiyar zuciya Haiydar ya sauke tare da cewa.

“Toh Addah Khausi muje kibata haƙuri kinji ko?”.

Nunfashi me zafi ta fesar tare da Kallonsa kana tace.

“Haiydar Ina tsoro”.

Kai ya Girgiza tare da sassauta muryarsa yace.

“Toh idan baki bata haƙuri ba so kike tayi ta fushi dake?”.


Be jira cewar ta ba ya riƙo tsintsiyar hannunta suka fita, ganin Mommy bata falon yasa suka nufi kichen
still Nan ma bata nan kai tsaye Bedroom ɗinta suka nufa zaune suka sameta abakin gado da alamar bata
daɗe da fitowa daga wanka ba ta gama shiryawa tana ɗaure yalwataccen sumar kanta da Ribont.

Tsugunna wa Haiydar yayi agabanta tare da jan hannun Khausar itama ta tsugunna cikin sanyin murya da
neman yafiya Haiydar yace.

“Ayyah Mommy dan Allah kiyi haƙuri Addah Khausi tace kinyi fushi da ita tun jiya bakya mata magana”.

Kallonsu Mommy tayi tare da kawar da kanta gefe Khausar kuwa da hawaye ke kwaranya daga Idanunta
yayin da kanta ke ƙasa.

Miƙewa Mommy tayi kana ta cigaba da shirinta ba tare data tanka suba ta ɗauki turare ta feshe jikinta.

Cikin sanyi Haiydar ya mike tare da ƙarasawa gaban Dressing mirrow ya durƙusa kana Cike da ladabi
yace.

“Dan Allah Mommy kiyi haƙuri Idan akwai abinda tayi miki mu baki haƙuri”.

Banza Mommy tayi dasu ta cigaba da shirinta.

Cikin raunin murya da tsanananin tashin hankali Khausar ta shiga Girgiza kanta tana sakin kuka, kana
Idanunta na zubar da hawaye Shar-shar muryanta na rawa tace.

“Dan Allah Mommy kiyi haƙuri ki yafemin, kinsan fushinki masifa ce agareni”.

Uffan Mommy bata ceba ta koma bakin gado ta zauna cikin sanyi jiki Haiydar da Khausar suka bita da
rarrafe suka durƙusa a gabanta, ido ta zuba Khausar tana kallon yadda take kuka,

Ita kuwa Khausar ta kasa ɗago kanta, sai hawaye dake cigaba da zuba shar-shar.

Cikin muryar dake nuna ɓacin rai Mommy tace.

“Toh Kuma kukan me kike yi bayan kinyi abinda ranki keso.

Ai dariya ya kamata kiyi tunda har kin kai matsayin zaɓawa kanki miji, kin iya fetsare idanu gaban manya
kice ke ga wanda kikeso. kin jamin tashin hankali da zagi awajen kakarki”.

Haiydar kam ido ya zubawa Mommy don bai taɓa ganin tsananin ɓacin ranta irin na yau ba.

Mommy kuwa cikin fushi ta cigaba da cewa.

“Tsohuwar da kinsan ba kirki da kara bane da ita, ta fita tsakiyar gida tana min ihu da haushi tana tara
min mutane, Kina sane da cewa duk abinda kika yi laifinsa kaina yake dawowa, sannan duk abinda kikayi
Ni bansan dashi ba bansan yaushe kika tsara ba ban isa ki gaya min sirrinki mu biyuba sai kin bari a
tsakiyar mutane”.
Ajiyar zuciya Haiydar ya sauƙe tare da cewa.

“Dan Allah Mommy me tayi miki ne?”.

Cike da ɓacin rai Mommy ta kalli Khausar kana tace.

“Ai ita tasani ta faɗa maka me tayi”.

Ahankali Haiydar ya juya tare da kallon Khausar yace.

“Addah Khausi me kikayi?”.

Kallon Mommy Khausar tayi Muryanta na rawa tace.

“Dan Allah Mommy kiyi haƙuri?”.

Girgiza kai Mommy tayi babu walwala atare da ita tace.

“Toh me kike nufi da kalmar da kika faɗa?

Kince ba kyason Naseer na gamsu domin Ni kaina bana son Naseer tunda nasan abinda ke tafiya, sannan
na fahimci yanzu Ameena yake so”.

Kuka kawai Khausar keyi Allah ne kaɗai yasan me take ji aranta.

Mommy ta cigaba da cewa.

“To amma shi Aliyu Meye lefinsa ɗan uwanki ne sannan zai riƙe da amana da gaskiya kamar yadda ya
riƙe yar uwarki. Baffanki bazai bari ya to zarta kiba sannan kinzo min da wata magana wai Moddibo kike
so ko kunya baki jiba”.

Ahankali Khausar ta ɗago kanta kana ta rumtse idanunta dake zubar da hawaye Muryanta na rawa tace.

“Mommy dan Allah kiyi haƙuri abar batun Yah Aliyu ayi batun Aurena dashi Mommy wlh ni Moddibo
nake...!

Ikon Allah sai kallo wai fa Modibbo takeso.

*Littafin SAKAYYAH dai na kuɗi ki biya ki karanta cikin Aminci yafi ki karanta na sata kuma na Allah ya isa,
1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP
09097853276. Sai in tura miki littafin*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*
SAKAYYAH

37

*Alamomin infection sune kamar haka*. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi
kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan
ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin
har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin
har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin
fitsari, da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin yana kwaranya. Zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA sai ya
gama yi miki illah. Wanda kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan
sinadaran ni'imomin ki, da sha'awarki, duk kyan kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da
abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I
yau, duk nacin oga da yi miki wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata
bayyana kanta har sai ta gama yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai
kiji Doctor's suna kira miki, ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin sherrin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki
dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection
cutace mai masifar naci, so yar uwa dole kema ki nace masa da maganin mu, set ɗin10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin indai
ita tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma
a saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba dan kun kai
mishi amarya a rarake bayan kun san kuɗin sadaki ya ƙara sama. Saboda yanayin garin yasa ina raba
rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi a 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga account
number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min mgn ta
WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau
kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan
mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan
baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA'AURATA.

37

Cikin yanayin ɓacin rai Mommy ta ture kanta dake kan cinyar ta babu walwala atare da ita tace.

“To ai shikenan Khausar hankalinki ya kwanta, zagine da abin kunya kunja min, kukan me kuma zaki zo
kina min, in banda rashin hankali dama rashin kunya Khausar yaushe Moddibo yace yana sonki yaushe
Moddibo ya taɓa zuwa wajenki?”.

Kasa cewa komai Khausar tayi sai hawaye dake cigaba da kwaranya a Idanunta Shar-shar.

Cike da takaici Mommy ta cigaba da cewa.

“Mutumin da ko Amakaranta tsakaninki dashi sai dai faɗa kyara da hantara. Duk abinda ke faruwa ina
sane ai ana bani labari amma saboda tsabar shashanci ki rasa wanda zaki ce kina so sai mutumin da
bakwa zama inuwa ɗaya!”.

Kuka sosai Khausar ta fashe dashi cikin sheshsheƙan Kukan tace.

“Wallahi Mommy ba haka bane dan Allah ki tsaya ki saurareni”.

Kai Mommy ta Girgiza tare da tsira mata Ido tace.

“Hmmm Khausar kenan me zan saurara kuma, ai babu abinda zanji daga gareki tunda ke kika haifi kanki
ke zaki yankewa kanki hukunci sannan ke zaki zaɓawa kanki miji wai ki kalli tsabar Idanunmu saboda
tsaurin Ido kice Modibbo kike so to yaushe yace yana sonki?”.

Girgiza kai kawai tayi cikin matsanancin kuka da tashin hankali tace.

“Dan Allah Mommy kiyi haƙuri wallahi ba rashin kunya bane dolene yasa haka Mommy ki sanya mana
al'barka acikin rayuwar auren da zamu yi”.

Cike da takaici Mommy ta kalleta kana tace.

“Toh Khausar tambayar da zan miki Moddibo yace yana sonki ko kuma ke kike haukanki?”.

Girgiza kai Khausar tayi cikin rawan murya tace.

“Mommy I don't know either he love me or not”.


Miƙewa Mommy tayi tare da jan dogon tsaki ta fice daga ɗakin ta nufi Falon Lamiɗo.

Khausar kuwa kanta ta kife ajikin katifa ta fashe da sassayan kuka tana sheshsheƙa Ajiyar zuciya Haiydar
ya sauƙe tare da kallon Khausar cikin sanyin murya da rashin fahimta yace.

“Addah Khausi ban fahimci abinda Mommy take faɗa ba wai Malam Moddibo kike so ko kuma wa?”.

Kai ta gyaɗa masa Muryanta na rawa tace.

“Eh shi nake so”.

Zare ido Haiydar yayi tare da sanya salati kana yace.

“Toh shi Malam Moddibo yana sonki ne?,”.

Kai Khausar ta girgiza tare da ɗago Idanunta dake jiƙe da hawaye cikin raunin murya tace.

“Ban saniba Haiydar I really don't know”.

Cike da matsanancin mamaki da damuwa Haiydar yace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Khausar baki sani ba kuma?”.

Jinjina kai Khausar tayi cikin raunin murya tace.

“Bansani ba Haiydar Bansani ba Haiydar”.

Miƙewa Haiydar yayi cike da takaici yaja dogon tsaki tare da faɗin.

“Wallahi dama nasan hakane babu abinda zaisa in rakoki wajen Mommy”.

Ya ida maganar tare da ficewa cike da takaici da ban haushi.

Cikin rauni Khausar ta miƙe tare da nufar Bedroom ɗinta tana shiga ta faɗa bisa gado tare da sakin kuka
mai masifar ɗaci da ƙuna.

Mommy kuwa kai tsaye falon Lamiɗo ta nufa bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon zaune ta samu
Abba akan 2sitter.

Anutse Lamiɗo ya ɗago kansa tare da sakar mata da lallausan murmushi kana yace.

“Shatu Ikon Allah mai kuma ya ɓatawa Gimbiya Aysha rai”.

Fuska Mommy ta ɓata tare da narkar da murya kana tace.


“Na lura ma al'amarin Khausar dariya yake baka, baki ɗaya tun jiya Yarinyar nan ta ɓata min rai ta
hargitsa min lissafi, sam kakarta bata da kirki tsohuwa ce mai zafi ta saba da iko da gadara akan
ƙannenta ta saba da maganar ta kamar yankan wuƙace”.

Kallonta kawai Lamiɗo yake yana murmushi.

Cikin yanayin damuwa ta cigaba da cewa.

“Duk abinda ta faɗa haka ne babu wanda ya isa ya musan ta mata gashi Khausar tazo tayi mata abinda
bashi neba ta tafi tana zagina yanzu tana zuwa Rugar nan zata baza sunan Khausar hakan zanji daɗi ne?”.

Murmushi Lamiɗo yayi tare da gyara zaman sa kana ya miƙa mata hannunsa tare da cewa taho nan zo
nan Shatuna”.

Maƙe kafaɗa tayi tare da tura baki kana ta narkar da fuska.

Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa.

“Ki zauna mana”.

Kallonsa kawai take amma ba tace Uffan ba.

Ahankali ya sanya hannunsa ya janyo tsintsiyar hannunta tare da zaunar da ita agefen sa cikin sanyin
murya yace.

“To amma ai akwai abinda baki sani ba”.

Asanyaye ta kallesa tare da cewa.

“Toh menene ban sani ba?”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da tsira mata ido kana yace.

“Jiya Hajja Nana bata bani dama inyi mata Magana ba saboda yanda ta ɗauki abin da zafi take ta ihu da
kururuwa da Masifa sannan dole mu bita ayanda taso”.

Jinjina Kai Mommy tayi tare da sauƙe numfashi.

Cikin sanyin Murya ya cigaba da cewa.

“Tun da kinga tsohuwa ce sannan tana da ƙarfin iko akan Khausar babu yanda muka iya, amma Baffanta
ya fahimta domin yau kafin ya koma Ɓadamaya yabiyo nan munyi magana dashi”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana ya kalli Mommy da itama shi take kallo yace.
“Sannan yace ba zai mata dole ba kamar yanda idan Mahaifinta yana raye ba zai mata dole ba kamar
yanda zai yiwa ƴaƴan sa haka zai mata saboda yana da ƴaƴa mata da yawa kamar yanda bai musu dole
ba haka itama ba zai mata dole ba dan mahaifinta baya raye”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana tace.

“Na sani shi yana da fahimta, amma ita tsohuwar ce gaba ɗaya ba zata fahimta ba”.

Lakace mata hanci Lamiɗo yayi kana da murmushi afuskarsa yace.

“Kada ki damu ɗan zai fahimtar da ita, dan yace ya bata haƙuri sannan idan ta huce zai sake dawowa ya
bata haƙuri kuma Insha Allah zata fahimta”.

Jinjina kai Mommy tayi tare da gyara zamanta kana tace.

“Toh naji ta wannan gefen an samu fahimta amma fa Moddibo baya Son Khausar din ita da bakinta fa
tace min bata san yana sonta ko baya sonta ba, ka taɓa ganin Moddibo yazo wajen Khausar ne?”.

Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.

“Eh na taɓa gani mana kwanaki sunzo da Asma'u”.

Girgiza kai Mommy tayi tare da fesar da numfashi kana tace.

“Zuwan da kaga yayi ta'aziyyan Ramadan yazo min domin yace alokacin da suka zo yimin ta'aziyya sun
haɗu da Ori da ya muku bayani gawar Jameel toh sun fita bai shigo ya min ta'aziyya ba, shine suka zo da
Asma'u yamin amma fa baice yana son Khausar ba hasalima Khausar da Moddibo basa zama inuwa
ɗaya”.

Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe tare da gyara zamansa ya fuskanceta tare da cewa.

“Ki nutsu mana Ni nafi so ki nutsu Ayshatu idan kin nutsu sai in miki bayani”.

Marairaice fuska tayi tare da langwaɓar da kai kana tace.

“Toh ai yanzu ma Anutse nake ranka shi daɗe kai nake sauraro”.

Murmushi yayi tare da riƙe tafin hannunta acikin nasa kana ya lumshe idanunsa tare da cewa.

“Jiya ma hargowar Hajja Nana ce ya hana in miki bayani shekaran jiya baki ji cewa nayi baƙi ba?”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.


“Eh naji”.

Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauke kana ahankali yace.

“Toh Malam, Arɗo ne da Alh Bashir mai Dala Mahaifin marigayi Malam Jameel da kuma Malam Ahmad
Baban Asma'u suka zo”.

Jinjina kai Mommy tayi kana cikin sanyin murya tace.

“Ooh sune suka zo!?”..

Kai ya gyaɗa mata still hannunsa na cikin nata yace.

“Eh”.

fesar da numfashi yayi kama yace.

“Toh kinsan me yaka wo su?”.

Kai ta Girgiza kana tace.

“A'a sai ka faɗa”.

Atake yanayin fuskarsa ya sauya daga murmushi zuwa rauni cikin sanyin murya da rauni yace.

“Magana suka zo akan wasiyyar da Marigayi Jameelu ya bari”.

Saurin Kallonsa Mommy tayi cikin sanyin murya da damuwa tace.

“Wasiyya kuma!?”.

Jinjina mata kai Lamiɗo yayi tare da fesar da numfashi kana yace.

“Eh”.

Ahankali tace.

“Wasiyya kuma Jameel ya bari akan me!?”.

Zamansa ya gyara tare da janye hannunsa ɗaya daga cikin na Mommy ya dafe goshinsa cikin raunin
murya yace.

“Jameel yabar wasiyya ne akan Moddibo da Khausar”.

Lokaci ɗaya idanun Mommy suka ciko da Hawaye cikin raunin murya tace.
“Wasiyya akan Moddibo da Khausar kuma to akan me?”.

Jinjina mata kai yayi still muryarsa Araunane yace.

“Tabbas Mahaifinsa ya faɗa min cewa akwai ranan da suka je shi da Moddibo gidansa alokacin saura
kwana uku asace sa har yake faɗa masa yafa zaɓawa Moddibo matar da zai Aura Amma shi kansa
Moddibo bai sani ba domin koda Jameel ya faɗa murmushi Moddibo yayi alokacin har yake cewa Alhaji
Bashiru. Abba kaji fa wai ni J zai za ɓawa mata kamar wani yaro ko makaho”.

Lumshe ido Lamiɗo yayi cikin rauni ya cigaba da cewa.

“Alokacin Abban sa yace ya faɗa masa wace mata ce sai Jameelu yayi dariya yace sai ya dawo asirri zai
faɗa masa to bayan da ya dawo sai yace wa mahaifinsa dan Allah Abba ina neman alfarma acikin
kwanakin nan domin wata ƙila akwai abinda zai iya faruwa acikin kwanakin nan wataƙil agaban ido na
wataƙil kuma abayan Idona”.

Cikin sauri Mommy ta rintse Idanunta Hawaye masu zafi suka zubo mata ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe
kana yace.

“A lokacin sai mahaifinsa yace.

“In sha Allah a gaban idon ka nema Jameeluna ina zakaje”.

Sai yayi murumshi tare da sunkuyar da kansa murya a sanyaye yace.

“Wata ƙil kafin nan na tafi Marocco ko wata duniyar. Dan haka ga mata na zaɓawa Moddibo koda bayan
bana nan Abba ayi ƙoƙari ahaɗa auren Moddibo da Khausar sai Abban sa yace to Meyesa kace haka sai
yace wa Mahaifinsa shi dai yana fata kuma yana buri ahaɗa auren Moddibo da Khausar domin Moddibo
yana ɓuƙatar Aure fiye dashi shiyasa ya fara yi masa zaɓin mata”.

A hankali Lamiɗo ya fesar da numfashi mai zafi kana ya cigaba da cewa.

“Sannan Marigayi Jameelu ya sanar da mahaifiyarsa maganar kana ya sanar da Kakar Moddibo maganar
har ta kira Malam Arɗo ta sanar dashi maganar domin wasiyya ce alokacin yake cewa ayi ƙoƙari ayi
auren cikin gaggawa domin Moddibo yana bukatar aure shiyasa yake so ayi kokari ayi auren cikin
gaggawa koda baya nan babu wanda baisan da maganar ba sai Moddibo shiyasa shekaran jiya suka zo
akan neman alfarma ga Uzurin da suka zo dashi”.

Sai kuma ya numfasa kana yaci gaba da cewa.

“Akan wasiyyar da yabari toh na faɗa musu lallai Nine mariƙin Khausar Kuma Khausar tamkar ƴa take
awajena, saidai bani da iko da kuma ƴan cin da zan bada Auren Khausar garesu batare da izinin Yayan
mahaifinta ba da kuma sahalewar kakarta”.
Gyara zama tayi tare da kallon Mommy da tayi sanyi hawaye na zuba daga idanunta numfashi ya fesar
kana yace.

“Toh nace suje bayan kwanaki zasu jini, toh dana niyyata zamu je Jauro yaya muyi wa Hajja Nana bayani
sannan mu faɗa mata wasiyya ne duk abinda ake ciki dama nace idan muka dawo zan faɗa musu”.

Kallonsa kawai Mommy take bako kyaftawa tana sake jin tsoron Allah Mabuwayi gagara Misali aranta
cikin sanyin murya Abba ya cigaba da cewa.

“Kuma tunda kika ji Khausar ta furta haka wataƙil itama akwai abinda ta sani acikin wannan al'amarin”.

Dogon numfashi Mommy taja tare da fesarwa kana ta lumshe Idanunta hawaye masu zafi suka zubo
ahankali ta sunkuyar da kanta cikin raunin murya tace.

“Allah sarki toh Ubangiji Allah ya jikansa da rahma idan al'khairi ne Allah ya tabbatar idan kuma ba
al'khairi bane Allah ya sauya musu da mafi al'khairi”.

Jinjina kai Lamiɗo yayi tare da sauƙe numfashi kana yace.

“Yawwa Aysha yanzu kika gane addu'ar da zaki yi kenan, sannan kada kiyi fushi da Khausar fadan nan
dakike yi bashi da amfani zama zakiyi da ita ki fahimci Meye dalilinta na fadar haka”.

Kai ta gyaɗa kana cikin sanyin murya tace.

“Toh shikenan Insha Allah zan kiyaye”.

Sai da aka kira sallar azahar Lamiɗo ya fita ya tafi masallaci kana Mommy ta miƙe ta nufi sashenta tana
shiga falon ta fara jiyo sheshsheƙan Kukan Khausar abakin ƙofar Bedroom ɗinta ta tsaya tare da ɗaga
labulen ta kalli Khausar ba yabo ba fallasa tace.

“Idan kin gama kukan ki tashi kije kiyi al'wala kiyi sallah”.

Cikin sanyi ta gyaɗa mata kai kana ta miƙe tashiga toilet ta ɗaura al'wala ta fito Anutse ta gabatar da
sallah.

Mommy ma na shiga Bedroom ɗinta ta ɗaura al'wala sannan ta gabatar da sallah.

Bayan Khausar ta idar da Sallah kai tsaye ɗakin Mommy ta nufa.


Acan ɓangaren Hajiya Lami kuwa zaune take akan kujera taji ƙa garin magani da tsamiya da kuma ruwan
zafi ta kalli Samira dake zaune gefenta ta zabga ta gumi cikin sanyi tace.

“Gashi ki karɓi maganin kisha dama wannan yace sai da rana-rana zaki riƙa sha wanda kika sha jiya da
daddare kuma dare-dare zaki sha”.

Karɓan kofin Samira tayi tare da tsira masa Ido ganin yanda ta tsirawa kofin Ido yasa Hajiya Lami cewa.

“Kisha mana”.

Cikin raunin murya Samira tace.

“Mommy nifa na jiya da daddare nan ma dana sha babu abinda ya ragu saima zubar ruwan daya ƙaru”.

Ahankali Hajiya Lami tace.

“Toh Sokuwa wataƙil ruwan ai zai zube ne ya gama ƙarewa idan ya gama zuba shikenan magana ya
ƙare”.

Cikin raunin da tashin hankali Samira ta kalli mahaifiyar ta da Idanunta dake cike da ruwan hawaye kana
tace.

“Toh Mommy ruwan fa da ƙarni da wari yake zuba yanzu ma bakiji yanda nake ƙarni ba?”.

Cikin tsinkewar zuciya ta kalli Samira sai kuma ta basar domin bata son bawa ƴartata tsoro amma baki
ɗaya hankalinta ya tashi kar dai ƴarta ta samu wata matsala numfashi ta fesar tare da kallonta kana tace.

“Ni dai banji wani wari ba hancin kine dai da shegen jiye-jiye kina nan da hanci kamar na kule ke dai
kisha magani tunda yace kisha na tsawon sati biyu kafin mu koma”.

Zare ido tayi cike da tashin hankali tace.

“Mommy har sati biyu kuma?”.

Kai Hajiya Lami ta gyaɗa kana tace.

“Eh saboda zaiyi tafiya so koda munje baza mu same shiba”.

Ajiyar zuciya Samira ta sauƙe tare da cewa.

“Toh bari in sha”.

Aɓangaren Naseer kuwa zaune suke afalon Mahaifiyar sa da Addarsa Hindu da kuma Mahaifiyar su
Hajiya Kubra yayin da akwatuna ke jere agabansu cikin su sanye da Atamfofi, Leshuna, Shadda, English
wear, Turaruka, Mayuka,Takalma.
Gyara zama Naseer yayi tare da kallon Addah Hindu murmushi ya sakar mata tare da ɗage mata gira
ɗaya kana yace.

“Insha Allah Addah Hindu burina ya kusa cika”.

Murmushi tayi tare da jinjina masa hannu kana tace.

“Ƙwarai kuwa nan da ƙanƙanin lokaci ma kuwa”.

Gyara zama Hajiya Kubra tayi tare da kallon Naseer tace.

“Toh yanzu me yarage acikin kayan Auren nan ba asaba!?”.

Ajiyar zuciya Naseer ya sauƙe tare da cewa.

“Kayan Aure kam yanzu ai kusan an gama komai kawai yanzu gishiri da goro za asiya sai kuma sadaki i
think suka ɗaine suka rage”.

Kai Addah Hindu ta gyaɗa tare da faɗin.

“Eh saura kayan rufi ba ahaɗa ba”.

Kai ya jinjina kana yace.

“Toh badamuwa yaushe za akai?”.

Kallon akwatunan tayi kana ta kallesa numfashi ta fesar ta da sakin murmushi tace.

“Idan Allah ya yarda nan da sati za akai saura gyalullulka dana aika akawo min daga Kano basu iso ba
tukunna”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Toh ba matsala sai sun iso”.

Bayan Moddibo da Abba sun idar da sallar Azahar Amasallacin Kofar gidan Abba kai tsaye gidan Ummi
suka nufa bayan sun isa Moddibo yayi Parking suka fito daga motar kana suka tsaya daga coumpund ɗin
Moddibo yayi sallama daga ciki Malam Ahmad ya amsa kana ya fito ganin Abba yasa ya faɗaɗa
Murmushin fuskarsa tare da cewa.

“A'a Alh Bashir yau har da kaine agidanmu sannu da zuwa sannu da zuwa maraba lale ku iso mana”.

Kai Abba ya girgiza kana yace.

“A'a nan ma yayi”.

Ahankali malam Ahmad yace.


“A'a bakomai Abban Jameel mu shiga mana ai an zama ɗaya haba dai mushiga dan Allah”.

Murmushi Abba yayi cikin sanyin murya yace.

“Toh shikenan Nagode”.

Sannan suka nufi falon Ummi Asma'u dake zaune ta miƙe tare da yi musu Barka da zuwa kana ta koma
kichen ta dauki Plate ta kawo musu ruwa da drinks da kuma Fruit ta ajiye masu kana ta Gaishe su cike da
ladabi.

Ahankali Moddibo ya jingina bayansa da jikin kujera ya lumshe idanunsa baki ɗaya ya tsani garin
Gembulan da jahar Taraba ji yake tamkar ana yayyafa nasa garwashin wuta ajiki baiƙi ace ko yaushe
yana ɗaki baya fita ko ƙofar takashi ba.

Ummi dake Bedroom zaune kan Sallaya ta miƙe ta fito jin muryan Asma'u na gaishe da Moddibo kana
tace.

“A'a Moddibo ne”.

Ganin Abba zaune yasa ta tsaya cike da Mamaki tace.

“A'a Alhaji Bashir”.

Cikin sanyin murya Abba yace.

“Na'am Fatima”.

Kallonta Malam Ahmad yayi sanye take da hijabi har ƙasa hannunta riƙe da Carbi cike da kulawa yace.

“Ki ƙara so mana ku gaisa”.

Kai ta gyaɗa tare da ƙarasawa ta zauna daga gefe.

Anutse Moddibo ya daga kai ya kalleta kana yace.

“Ummi ina yini”.

Kallonsa Ummi tayi ba tare data amsa gaisuwar ba tace.

“Babana jiya duk baka leƙoni ba”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.

“Eh Ummi”.
Cikin sanyin murya tace.

“Kuma na kira wayarka baka ɗaga ba sai nayi tunanin ko kana bacci ne?”.

Kai ya girgiza tare da sunkuyar da kansa ƙasa yace.

“Kuma Ummi ban kulaba ban miss call ɗin ba”.

Jinjina kai tayi tare da fadin.

“Ayyah”, Kana suka gaisa.

Anutse Abba ya kalleta tare da cewa.

“Fatima ina yini”.

Ahankali ta gyara zamanta tare da faɗin.

“Lafiya”.

Cikin sanyin murya yace.

“Ya muka ƙara ji da haƙuri”.

Lumshe Idanunta tayi kana tace.

“Haƙuri ya zama dole”.

Jinjina kai yayi tare da cewa.

“Toh Allah yajiƙan Jameelu Ubangiji ya masa rahama”.

Baki ɗayan su suka amsa da Ameen ya Allah.

Gyara zamansa yayi kana yace.

“Fatima kada ki yiwa Jameelu kuka ki tayi masa addu'a shine abinda ya dace kinji ko?”.

Kai ta gyaɗa tare da sunkuyar da kanta ƙasa tace.

“Insha Allahu bazan yiwa Jameelu na kuka bai Insha Allah zan ta binsa da addu'a”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Hakan yafi”.
Anutse ya gyara zamansa tare da kallon Moddibo da kansa ke ƙasa kana ya kalli Ummi da itama still
Kanta ke ƙasa ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.

“Dama nazo da Moddibo ne inne ma masa uzini awajenki”.

Cikin sauri ta ɗago kanta tare da Kallonsa tace.

“Izinin me kuma?”.

Numfashi ya fesar tare da cewa.

“Dama Abune da yashafi kasuwanci na acan Company mu na Marocco wanda Jameelu ne yake komai na
Company nin toh kuma yanzu kin gani Allah ya dauke mana Jameelu”.

Cikin sauri Ummi ta lumshe Idanunta tare da gyara wuyan hijabinta.

Abba ya cigaba da cewa.

“To Kuma Manager company shima ba shida lafiya toh sun nemi da Inje kuma nima bana jin daɗin jikina
bazan iya zuwa ba”.

Ahankali Ummi ta ɗago kanta tare da kallon sa gani tayi baki ɗaya ya rame ya zama wani so silent dashi.

Cikin sanyin murya da tausayawa tace.

“Toh Abban Jameel Idan bamu sa haƙuri aranmu ba ya zamuyi ka kwantar da hankalin ka Ubangiji Allah
yajiƙan Jameelu shine kawai fatan mu da addu'ar mu”.

Kai ya gyara tare da sauƙe numfashi yace.

“Insha Allah zan kiyaye.

Yanzu mshawan jinin ne baki ɗaya yasani agaba duk kan magungunan da nake sha sai yazama kamar
basa min aiki”.

Jinjina kai tayi cikin sanyin murya tace.

“Allah ya sawwaƙa amma ka rage tunani koda kana shan magani idan baka rage tunani ba ba zaiyi aiki
ba”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana yace.

“Toh Fatima ya zanyi idan banyi tunani ba!?”.

Ahankali ta sunkuyar da kanta hawaye na zuba daga idanunta.


Gyara zama Abba yayi cikin sanyin murya yace.

“Toh dama shine nake so Moddibo ya wakilceni yaje shine yake cemin bawai zuwan bane baya so amma
baya so yayi nesa da Umminsa”.

Ahankali ta ɗago Idanunta dake jiƙe da ruwan hawaye ta kalli Moddibo murmushi tayi kana tace.

“Ba komai Babana kaje wannan ma ai abin farin ciki da al'fahari ne zaka cika burin da Jameeluna yake
son cikawa. Ubangiji Allah yakai ka lafiya ya dawo da kai lafiya Allah ya maka albarka”.

Cikin sanyin murya da tausayawa Moddibo ya amsa da Ameen asaman laɓɓansa.

Ahankali Ummi ta cigaba da cewa.

“Insha Allah zanyi ta binka da addu'a ba komai Babana ai muna tare ina nan ina Marocco amma idan ya
gama zai dawo ko?”.

Ta ƙarasa maganar ta sigar tambaya tana kallon Abba.

Kai Abba ya gyaɗa mata kana yace.

“Eh zai dawo Insha Allah bazai wuce sati biyu”.

Jinjina kai tayi tare da kallon Moddibo kana tace.

“Badamuwa Babana ai zamu nayin waya”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Shikenan Ummi ba matsala tunda kin amince.

Murmushi tayi still Idanunta cike da ruwan hawaye tace.

“Na amince Babana Allah Ubangiji ya kaika lafiya Allah ya dawo da kai lafiya Allah yasanya alkhairi da
albarka acikin tafiyar.

Ahankali yace.

“Ameen Ummi”.

Ajiyar zuciya Abba ya sauke tare da kallonta kana yace.

“Yanzu kuma sai batun kuɗin ku da aka har haɗa”.

Sunkuyar da kai Ummi tayi Atake hawaye suka cigaba da zubowa daga Idanunta cikin raunin murya tace.
“Toni me zanyi da kuɗin nan ne Abban Jameel?”.

Kai Abba ya Girgiza cikin rawan murya da rauni yace.

“Toh nima ɗin idan kun barsu awajena me zanyi dasu ga kuɗin Aliyu ga naki kowa ya karɓi kuɗin sa kowa
yana da bukatarsa motar ki da Sarƙoƙinki kika siyar ki sayi wata mota amfani dashi”.

Kallonsa ya mayar kan Moddibo kana yace.

“Kaima Moddibo ka karɓi kuɗin ka ka sayi mota sannan sauran kuɗin kayi abinda ya dace dasu”.

Kai Moddibo ya girdiza ciki rauni yace.

“Abba me zanyi da kuɗin?.

Ai kuɗi na gama abinda ya dace inyi dasu Babu abinda zanyi dasu tun da har basu tseratar min da J ɗina
ba wani amfani zasu yimin?”.

Cikin rauni Abba yace.

“Bakomai Moddibo ka karɓi kuɗin nan idan ka barsu awajena kun barmin tashin hankali da damuwa”.

Jinjina kai Malam Ahmad yayi tare da faɗin.

“Kuyi hakuri duk kan tsanani yana tare da sauƙi addu'a kaɗai zamuyi wa Jameelu amma kamar yanda
yace ne Moddibo ka karɓi kuɗin nan sannan kema Fatima ki karɓi kuɗin na shine abu mafi a'ala”.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.

“Yawwa shine dai ki bani account number inyi Miki transfer”.

Kai Ummi ta shiga Girgizawa hawaye na kwaranya daga Idanunta.

Ganin haka yasa Malam Ahmad ya karbi wayarta tare da fito da account number ya faɗawa Abba Atake
Abba ya mata transfer kuɗinta Naira million goma da dubu ɗari takwas kasancewar yana da account
number Moddibo Shima Atake ya Masa transfer kuɗinsa.

Anutse ya gyara zamansa tare da Kallonsu cikin sanyin murya yace.

“Nagode da halarcinku agareni musamman ma kai Moddibo Allah Ubangijin ya biya da mafificin
alkhairi”.

Atake Moddibo yaji wani irin rauni ya mamaye sa kallon Abba yayi muryarsa na rawa yace.

“Abba akan J ne kake min godiya?”.

Numfashi Abba ya fesar tare da sauƙe ajiyar zuciya yace.


“Toh Aliyu ya zanyi kayi min halarci duk kan inda Aboki na gari ya cika ka cika Ubangiji Allah yasaka da
alkhairi Nagode da halarcin ka”.

Cikin raunin murya Moddibo yace.

“Ameen Abba”.

Kallon Ummi Abba yayi kana yace.

“Toh insha Allah sammako zaiyi ya tafi kinsan akwai tazara tsakaninmu da Adamawa kuma can zai shiga
jirgin zuwa Abuja”.

“Toh Allah ya kaimu Allah yakai ka lafiya Babana Allah ya kareka”.

Cikin sanyin murya yace.

“Ameen Ummi”.

Miƙewa Abba yayi tare da cewa.

“Toh bari mu tafi”.

Godiya suka masa har sun fita Ummi ta miƙe tare da bin bayansu abakin barandar ta tsaya tare da cewa.

“Babana amma ai zaka dawo daddare muyi sallama ko?”.

Jinjina kai yayi kana yace.

“Insha Allah Ummi zan zo”.

Bayan sun fita kai tsaye gidan Malam Arɗo Abba ya ajiye Moddibo zaiyi masa sallama kana Abba ya wuce
gida.

Cikin sanyin jiki Khausar ta isa Bedroom din Mommy, a hankali ta zauna agabanta cikin Muryan kuka
tace.

“Mommy kiyi haƙuri kada kiyi fushi dani”.

Tsira mata Ido Mommy tayi ba tare da tace Uffan ba.

Cikin raunin murya Khausar ta haɗa hannunta waje ɗaya kana ta fashe da matsanancin kuka da
sheshsheƙan tace.
“Mommy dan girman Allah kiyi haƙuri ki daina fushi dani”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da fesar da nunfashi kana tace.

“Khausar to ni me zan ce miki?.

Bani da abinda zan ce miki tunda ai hukunci ne kin riga da kin gama yanke shi baki nemi shawarata ko
izinina ba”.

Girgiza kai Khausar tayi hawaye na cigaba da kwaranya daga Idanunta.

Ita kuwa Mommy kauda kayi tayi gefe kaba ta cigaba da cewa.

“Kawai kin fadi maganarki gaba gaɗi, sannan koda akeɓance baki taɓa faɗa min tsakanina ni dake ba, sai
da kika zaɓi cikin mutane sannan kika faɗa saboda ki kunya tani kin bani mamaki ban taɓa zaton haka
daga gareki ba”.

Khausar kuwa kai take Girgiza cikin muryan kuka mai gunji kana Muryanta na rawa tace.

“Mommy nima ina tsoron Modibbo bafa, dan nasan baya sona”.

Kallonta Mommy tayi cikin da mmki ta tsareta da ido tare da cewa.

“Toh kina tsoron Auren Moddibo kuma, akan wani dalili zaki ce zaki Aureshi? Kuma bayan kina sane
baya sonki”.

Sunkuyar da kai ƙasa tayi cikin gunjin kuka ta lumshe Idanunta tare da taune Lip ɗinta cikin raunin murya
tace.

“Mommy wasiyyar Yah Jameel ne Yah Jameel ne ya roƙi al'farma awajena sannan tun lokacin daya faɗa
min yace min wasiyya ya barmin yace koda ya mutu kada in manta ya nemi wannan al'farma awajena”.

Sai kuma ta kasa ci gaba da mgnar sakamakon kuka da yaci ƙarfinta hannu ta sanya ta goge hawayen
fuskarta wani na sake zubowa Muryanta na rawa ta cigaba da cewa.

“Aranan da za'a ɗauke Yah Jameel bayan mun taho amota yace min yana neman alfarma awajena in na
ɗauka Alfarman da yake nema awajena tamkar wasiyya ce".

Sai kuma ta kife kanta kan cinyar Mommy tana mai sakin wani irin raunataccen kuka murya na karkarwa
taci gaba da cewa.

“Mommy a ranar a gabana Yah Jameel yayi ta kuka kamar yaro ƙaramin ya rinƙa haɗani da Allah da
Manzonsa cikin sanyin murya da neman alfarma yace dan Allah kada ince bazan yi masa ba yana so koda
bayan Ransa in Auri Moddibo”.

Kallon ta kawai Mommy keyi bako ƙyaftawa yayinda itama hawaye ke zubo mata.
Cikin sheshsheƙan Kuka Khausar ta lumshe Idanunta tana tuna lokacin da suka kasance da M Jameel
amota yana faɗa mata magana da sauri ta sanya tafin hannunta ta rufe fuskarta kana muryanta na rawa
tace.

“Mommy alokacin Cike da damuwa na kalli Yah Jameel nace ya Jameel Meyesa kake Fadar haka Meyesa
kake magana me karyar da zuciya dan Allah kada kace wasiyya nidai ka faɗi ko wace irin alfarma kake so
zanyi maka domin kafi ƙarfin alfarma awajena”.

Taja hanci tare da kallon Mommy da yanayin ta ya sauya Muryanta na rawa kana numfashinta na fusga
tace.

“Sai yace min Khausar koda ace kin riski labarin mutuwa ta ki tuna da Alfarman da kuma Wasiyyar da na
bar miki ki Auri Moddibo idan kuma Allah yasa ina raye zanfi kowa farin cikin ganin An ɗaura Aurenki da
Moddibo”.

Ahankali Mommy ta sun kuyar da kanta ƙasa cikin wani irin yanayi na tsananin tausayawa da kuma
tsoron Allah Mabuwayi gagara Misali tol-tol haka hawayenta ke zuba jin Khausar taci gaba da cewa.

“Mommy Yah Jameel ya faɗa min cewa ya fadawa. Kakar Moddibo cewa dan Allah ayi Aurena da
Moddibo Mommy dan girman Allah ki tayani cikawa Yah Jameel Wasiyyar daya barmin bani da abinda
zanyi masa a wannan duniyar wanda zaisa Yah Jameel farin ciki amakwancinsa sama da in cika masa
burinsa naji na gani zan rayu da Moddibo duk da nasan ya tsaneni zan rayu dashi sabida darajar Yah
Jameel da wasiyarsa zan juri dukkan uƙubar da Moddibo zaimin koda kuwa zai kasheni zan zan cikawa
Yah Jameel burinsa”.

Cikin sheshsheƙan Kuka da fisgar numfashi tace.

“Mommy wannan buri da fatan Yah Jameel ne dan Allah da Manzonsa ku barni in cika masa burinsa, tun
da muke rayuwa da Moddibo Amakaranta yace ko yaushe kallon mu yake amatsayin mata da miji yace
bashi da buri sama da wannan Mommy yace min da ɗan Adam yana da zabi idan ajalinsa yazo to da zai
roƙa ajinkirta masa ajalinsa yaga kasancewa ta da Moddibo a Inuwa ɗaya a gidan aure”.

Sai kuma tayi saurin dafe ƙirjinta jin yanda numfashinta ke fusga.

Ta sauƙe wani irin numfashi tare da dafe kanta kana ta cigaba da cewa.

“Yace min Khausy zanso naga wani irin zama zakuyi keda Moddibon.

Yace min zaiso ace Allah ya bashi Aron Rai ya rayu ya ganni gida ɗaya a Inuwa ɗaya da Moddibo yaga
wani irin Rayuwar aure zamuyi koda na wuni ɗaya ne.

Allah sarki ya Jameel ashe bazai ganiba.


Dan Allah Mommy ki barni in cikawa Yah Jameel burinsa Mommy Dan Allah kiyi haƙuri ki barni in cikawa
Yah Jameel Wasiyyar sa”.

Taƙarashe mgnar tare da fashewa da matsanancin kuka mai masifar ƙuna da ɗaci sai kuma tace.

“Mommy wallahi ina tsorin son Moddibo har Raina, kawai na faɗa ne domin kada Hajja Nana tace dole
sai na Auri Yah Aliyu shiyasa na faɗa alokacin, amma bawai dan in kunya taki bane Mommy kinfi kowa
sanin halina banyi hakan da wata manufa ba face cika wasiyyar Yah Jameel”.

Numfashi mai tsawo taja cikin Muryanta da baya fita tace.

“Mommy ina matuƙar girmama Yah Jameel Mommy Ina so in cika Masa burinsa wannan shine wasiyyar
Yah Jameel na karshe kuma shine karshen maganarmu dan Allah ki tayani cika masa wasiyyar sa na
roƙeki”.

Wasu irin hawaye masu zafi ne suka fara bin kuncin Mommy cikin sanyi da raunin murya tace.

“Insha Allahu Khausar da izinin Ubangiji za acikawa Jameel burinsa...!

*LITTAFIN SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama ba haƙƙin kowa a kanki
1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP
09097853276. In dai baki biyaba kika karanta to na satane, kuma na Allah ya isane*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

38

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.
Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya Zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki
dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection
cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin
kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin
kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana
dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya
musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki
aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa
ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga
account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min
mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi
Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari
da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan
Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR
MA'AURATA.

38

Khausar kuwa cikin sanyi da rauni tunowa da M Jameel da ya dawo mata sabo ahankali ta kife kanta
abakin gado tafashe da kuka mai cike da fargaba da kuma tsoron Allah.

Kallonta Mommy tayi cike da tausayawa tace.


“Kiyi haƙuri ki daina kuka Khausar addu'a zaki yiwa Jameelu sannan Insha Allah za acika masa burinsa da
wasiyyar daya bari in Allah ya ya nufa”.

Ta ƙare mgnar tare da sauƙe numfashi.

Idanta ta tsaida kan Khausar da har zuwa lokacin kanta ke kife jikin gado cikin tausasawa tace.

“Amma kisa Aranki cewa haƙuri zakiyi da duk rayuwar da zakije ki tarar, sannan wasiyya zaki cikawa
Jameel, sannan ki sani shi zaman Aure kansa Ibada ne, koda ana son juna wata ran akanji babu daɗi,
bare ke da dama kin san matsayinki a wurin wanda kike ganin kina da ƙarfin guiwar zama dashi,

dan haka kisa Aranki cewa ba lallai ne kiji daɗin zama da Moddibo ba, amma tunda kince kinji kin gani
zakiyi abinda Jameel ya buƙata kafin barinsa duniya zan biki da addu'a Ubangij ya tabbatar da al'khairi
tunda har iyayensa duk ya gayawa kuma tuni suma sun sa baki a mgnar, kinga ni bani data cewa tunda
kun mamayeni”.

Cikin rauni Khausar ta sake fashewa da sabon kuka tabbas gaskiya Mommy ta faɗa ba Lallai tayi zaman
daɗi da Moddibo ba tunda baya sonta hasalima koda kallonta ne baya sonyi tuno da hakan yasa wasu
hawaye masu masifar zafi suka zubo mata tama sani tabbas cikin uƙuba zata rayu dashi, to amman ya
zatayi rayuwa Yah Jameel al'ƙawarin amincewa da batun auren Amininsa.

Cikin sanyin murya Mommy ta cigaba da cewa.

“Sanin bake kaɗai Jameelu ya barwa wasiyya ba yasanarwa da Kakar Moddibo sannan ya sanarwa
Umminsa da kuma Abbansa nima da farko hankalina ya tashi.

Amma yanzu barina ɗakin Abbanku yake cemin shekaran jiya da daddare Abban Jameel da Malam
Ahmad da malam Arɗo sunzo da batun, abinda yasa baiyi mgnar ba Hajja Nana bata bashi dama bane
daya mata bayani”.

Wani irin rauni, Kunya,damuwa da rasuwar Jameel ne suka dawowa Khausar alokaci ɗaya.

Cikin sanyi jiki ta miƙe ta nufi ɗakinta tana shiga ta faɗa kan gadonta kana ta cigaba da kuka cikin rauni
tasan dai iyaye keyiwa ƴaƴansu auren dole a tarihin duniya, sai gashi ita dai itace zatayiwa kanta da
kanta auren dole bisa wasiyar Yan Jameel malami na musamman mai matsayin babban Yaya wanda ita
dai da fari har ranta shi takeyiwa kallon mai iya jiɓantan lamuranta.

Washe gari da safe Misalin ƙarfe 8:00 Anutse Moddibo ya fito daga falonsa cikin wani ɗanyen Boyel Sky
blue Fuskarsa tayi fayau manyan Idanunsa dake lumshe sun sake girma sabida ramar da yayi, sajensa ya
sake yawaita yayi fadi da cika, yana kuma ɗan hargitse alamun an kwana biyu ba'a gyarashi.

Kafadarsa na dama rataye da jakar laptop ɗinsa daga zip ɗin gefen wayoyinsa ya zira, sai hannunsa dake
riƙe da jakar kayansa, a hankali yake tafiya, yayinda jikinsa ke fitar da sanyayyan ƙamshin tularen sa.
Kai tsaye sashen Innayi ya nufa ahankali Innayi dake breakfast ta ɗago Kai ta kallesa Anutse ya ƙarasa
tare da zama gefenta.

Da mamaki take Kallonsa ganin kamar alamar cikin shirin tafiya yake.

Cikin sauri tace.

“Aliyu”.

Kallonta yayi da sauri domin bata fiye kiransa da Aliyu ba sai da babban dalili.

Cikin sanyin murya yace.

“Na'am Innayi”.

Hannunta riƙe da kofin tea tace.

“Ya haka? ya na ganka kamar mai yin tafiya?”.

Kai ya gyaɗa mata tare da tanƙwashe ƙafafunsa kana ya fuskanceta cikin ƙoƙarin danne damuwarsa kana
yana mai jin farin cikin zai bar garin Gembila haka nan ya tsinci kansa da jin farin cikin yau dai zai bar
Jahar Taraba domin baki ɗaya garin ya fice masa arai cikin sanyin murya yace.

“Innayi ba kama bace tafiyar ce”.

Cike da mamaki ta ɗago kanta kana tace.

“Aliyu tafiya zaka yi amma ban sani ba sai dai in ganka kana fita da jaka haka?”.

Ahankali ya riƙo tafin hannunta acikin nasa cike da mmkia yace.

“Kiyi haƙuri Innayi tafiyar ce nima tazo min a bazata kuma ba jiya Abban Jameel ya gaya mikiba”.

Kai ta girgirza tare da cewa.

“A'a bai gaya minba zakayi tafiya ba, ya dai cemin yana neman al'farma ni kuwa nace umurni kawai zai
baka kamar yadda yake bawa Jameel ni na amince duniya da ƙiyama, ban bari yamin bayaniba sabida kar
yaga kamar zan hanaƙa yaji ba daɗi. To waima Tafiya zuwa ina zakaje?”.

Cikin kwantar da murya yace.

“Tafiya zuwa Marocco!”.

Cikin tsananin kaɗuwa ta zaro idanunta baki ɗaya lokacin ɗaya ta ƙware tare da fara tari sakamakon
ƙwarewa da tayi da dankalin dake bakinta”

Moddibo kuwa ganin yanda ta ƙware yasa yayi saurin daukan kofin ruwa ya miƙa mata tare da cewa.
“Sannu”.

Amsa tayi tasha amma still tarin bai tsaya ba lokaci ɗaya Idanunta yayi ja zufa ya shiga tsats-tsafo mata
agaba ɗaya ilahirin jikinta shi kuwa Modibbo ido ya zuba mata tare da jera mata sannu da kuma ɗan
bubbuga bayanta kaɗan-kaɗan yana mmkin wasu al'amuran a ranta domin ya sani tsawon zamansu da J
ta hanashi zuwa Marocco wanda bai san me dalilntaba, kasancewar sa ba mutum ne mai yawan
bincikeba yasa bai taɓa mata musuba ko bincike.

Ahankali ya ke mata sannu cike da tausayawa takai kimanin minti biyar kafin tarin ya lafa sannu Ahankali
ta fara maida numfashi.

Tana sauƙe ajiyar zuciya ta juya ta kallesa kana tace.

“Marocco!!!! kuma Aliyu?”.

Jinjina kai yayi cikin sanyin murya yace.

“Eh Innayi Marocco zanje amma idan har kin amince, idan bakya so, bazanje ba sai in bawa Abba
haƙuri”.

Ahankali ta gyara zama tare da fuskantar sa da kyau kana tace.

“Toh amma mai zakaje kayi a can?”.

Tayi tambayar zuciyarta na mai cigaba da bugawa da ƙarfi.

Lumshe Idanunsa yayi tare da sauƙe Ajiyar zuciya kana yace.

“Abba ne ya nemi al'farma da Inje in kula da Company'nsa sannan kuma jiya daya zo nayi tunanin kunyi
cikekkiyar maganar ne dashi kafin ku shiga wurina, shiyasa ni ban faɗa miki ba, ya nemi taimako da Inje
in taimaka masa akan batun Company sa buga Abaya, jallabiya, Carpet, Sallayu blanket's da dai
sauransu”.

Kallonsa kawai Innayi keyi yayin da take ji tamkar zuciyarta zai fito saboda yanda yake bugawa.

Cikin sanyi Moddibo ya riƙe Hannunta dake cikin nasa yace.

“Akwai sabbin injinan aiki da za'a sauƙe na Company, sannan kuma za'a fara aikin dasa Injina za'a
kakkafa toh akwai ɓuƙatar sa ido da kuma kula da abubuwan, amma Insha Allah bazan wuce wata biyu
zuwa uku ba zan zo Innayi”.

Girgiza kai tayi tare da jingina bayanta da jikin bango ta lumshe Idanunta kana ta shiga maida numfashi.
Moddibo kuwa ido ya zuba mata kana Asanyaye yace.

“Amma Innayi idan har bakyason Inje zan kira Abba in Faɗa masa yayi haƙuri”.

Uffan bata ceba kana bata buɗe Idanunta ba daga ita sai Ubangiji kaɗai suka san mai take tunawa aranta
takai kimanin minti biyar ahaka kafin ta ɗago Idanunta ta kallesa kana taja dogon numfashi ta sauƙe tare
da sakin Murmushin mai tarin ma'anoni sannan tace.

“Bazan hanaka tafiya ba Aliyu, domin ko baka tafi yanzu ba, dama lokacin tafiyar ya ƙarato. na amince
kayi masa duk kan abinda Jameelu zai masa daya kasance araye, domin hakan zai rage masa raɗaɗin
ciwon rashin Jameelu”.

Kai Modibbo ya gyaɗa yana kallon yanayin fuskartar ahankali yace.

“Toh shikenan Insha Allah zanyi hakan”.

Innayi kuwa kallonsa tayi kana cikin sanyin murya tace.

“Amma yanzu-yanzu tafiyar kenan Aliyu?”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Eh Innayi zanbi jirgi zuwa Abuja ne, in naga komai biza na ya fito zan wuce”.

Jinjina kai tayi tare da cewa.

“Shikenan Ubangiji Allah ya sanya alkhairi Allah ya tabbatar da alkhairi sai nazo”.

Saurin Kallonta yayi cike da Mamaki yace.

“Sai kinzo kuma?”.

Sunkuyar da kanta ƙasa tayi tare da Girgiza masa kai kana tace.

“Mantawa nayi sai ka dawo nake son cewa".

A hankali ya zaro ATM ɗinshi na Zenith Bank daga al'jihunsa, cikin tafin Hannun ta yasa matashi kana a
hankali yace.

“Ga ATM ɗina na Zenith Bank, kin san pin number ɗin, akwai kuɗi a ciki kusan 5 Million”.

Da sauri tace.

“Ina ka samosu?”.

Gyara zamanshi yayi kana yayi mata bayanin yadda sukayi da Abba sannan ya ɗaura da cewa.
“Akwai wasu a wurina, wannan ki riƙe kiyi dukkan abinda kike buƙata kafin in dawo, in haɗasu muyi
ƙoƙarin barin garin nan, domin ya fita raina”.

Yayi mgnar yana tuno kalaman Hajja Nana ita kuwa Innayi cike da sanyi tace.

“Uhmmm Aliyu in Sha Allah kamar ma mun barima ai kama barin kai kam”.

Cikin sanyi ya jinjina

Kai tare da miƙewa yace.

“Toh shikenan Innayi amma dai bakiyi fushi dani bako?”.

Da sauri tace.

“La la la Aliyu banyi fushi da kaiba”.

hannunta ya riƙo tare da ɗaurawa a kanshi kana yace.

“Toh kuma baki samin Albarka ba”.

Cikin sanyin Murya tace.

“Allah yasan ya Albarka Ubangiji ya tsare gabanka da bayanka Allah maidakai lafiya ya kuma tsareka da
lafiyarka, Ubangiji ya rabaka da sharrin duk kan abin ƙi walau mutum ko aljan ko wani irin abune ya
*Tsareka da Tsoffin magauta ya hanasu ganeka bare cutar da kai kafin isarka tushenka”.*

Lumshe Idanunsa yayi kana yace.

“Ameen ya Allah Innayi ni zan tafi”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh ka tsaya bari na zo".

Kai ya gyaɗa sannan ya tsaya ɗaki tashiga ba daɗewa ta fito sanye da hijabi, suka nufi wurin motarsa,

“Yau innayi zafa ki koma gidan Abba ko Ummi dan zamani ke ɗaya a nan bai minba”.

Cikin sauri tace.

“Eh toh gsky k nima ina tsoro Ni kaɗai a nan to amman, gsky gwara min gidan Ummin Jameel kaga ita
kamar ɗiya take a gareni gidan Abba kuwa ba wani sabawa nayi da matansa ba, amman can zamu zauna
ɗakin Asma'u nasam Malam Ahmad kuma baida matsala”.

Cikin gamsuwa da haka yace.

“Gsky kam hakan yafi, zan gaya Abban in kin gama haɗa kayanki Asma'u zata zo ku tafi”.
Kai ta jinjina cikin gamsuwa tace.

“Ba laifi”.

Jingina yayi da jikin motar bayan yasa jakarsa gefen mai zaman banza.

Ita kuwa Innayi a hankali ta matso kusa da marfin motar zira hannunta tayi ta ciki, zip ɗin jakarsa tabuɗe
tasa jim kaɗan kuma ta maida ta rufe kana sukayi sallama ya mota ya tafi.

Kai tsaye gidan Ummi Moddibo ya nufa cikin nutsuwa yake Driving yayin da yake sauraran ƙira'ar Ahmad
Sulaiman cikin suratul An'am yana isa gidan Ummi yayi Parking aƙofar kana ya fita ya shiga coumpund
ɗin yana tafiya ahankali yana ɗaura ƙafarsa akan farandar sautin muryar Khausar ya ratsa Dodon
Kukensa cikin sauri ya tsaya tare da rumtse idanunsa.

Sabida jin yadda tsikar jikinsa ya fara tashi tun daga tafin ƙafarsa har tsakiyar ƙwaƙwalwan kansa,
ahankali ya jingina bayan sa da jikin bango yayin da zuciyarsa ta shiga bugawa da kaso Cassa'in da tara
cikin ɗari.

Aransa yakeji kamar ya koma domin gaba ɗaya ya rasa meke sashi shiga wani yanayi da zaran yaji sautin
Muryanta zaiji tamkar ana tsikara masa allura yama rasa ta wani irin yanayi zai misalta yanda yake ji
akan yarinyar shin kunyarta yake ko kuma tsoronta yakeji, ko shakkarta shi kansa ya kasa tantancewa,
taune Lip ɗinsa na ƙasa yayi da ƙarfi tare da buɗe idanunsa da suka sauya launi kana ya tura ƙofar falon
tare da sallama yana mai tsare fuska.

Ummi dake zaune ta tsira masa ido tare da cewa.

“Babana har ka shirya kenan?

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Eh Ummi”.

Kana ya zauna agefenta ya zamana yana facing ɗin kichen.

Kallonsa Ummi tayi cike da kulawa tace.

“Amma dai ba kayi breakfast”.

Kai ya girgiza kana yace.

“Uhm-Uhm”.

Da Mamaki tace.
“Toh ya za'a ayi ka tafi da yunwa ba zaiyu ba Babana ba zaka tafi da yunwa ba”.

Langwaɓar da kai yayi tare da Marerece murya yace.

“Ummi bana jin yunwa fa”.

Fuska ta ɓata kana tace.

“Bafa zaiyu ba Babana baza ka tafi da yunwa ba”.

Khausar na fitowa daga kichen ta girgiza kai tare da kallon Asma'u tace.

“Toh ni zan tafi sai anjima”.

Da mamaki Asma'u ta kalleta kana tace.

“Bangane ba kamar ya sauri kike?

Dama ba nan kika zoba ne?”.

Khausar kuwa kai ta girgiza tare da kallonta kana tace.

“A'a ba nan nazo ba dama gidan Aunty Ruƙayya naje to da naje sai na sameta tare da baƙi shine na kira
Mommy nace zan ƙaraso nan mu gaisa.

Mommy kam cewa tayi wai da safiyar nan zanzo”.

Moddibo kuwa tunda yaji sautin Muryanta akusa dashi ya kasa ɗauke idanunsa akanta duk da cewa
kallon Kasan ido yake mata.

Cikin sanyi Khausar ta cigaba da cewa.

“Toh shine nace tayi hakuri ba daɗewa zanyi ba shine fa tace inzo amma kada in daɗe saboda mune da
aikin rana zan koma in ta yata nazo muyi wata mgna ce, kuma nafasa”.

Da sauri Asma'u tace.

“Dan Allah muyita”.

Kai ta jujjuya tare da cewa.

“Ba damuwa in kin samu dama kizo zamuyita, yanzun sauri nake”.

Ta ida maganar tare ɗago kanta.

Idanunta ne suka sauƙa cikin idanun Moddibo.


Atsorace ta zira Idonta cikin nasa tare da juya su acikin nasa wanda hakan ya zama kamar hararansa tayi
ita kuma cikin mamakin yadda ya rame ya wani zama shiru, ne yayi matuƙar bata mamaki da tausayi
domin da dane da tuni ya danna mata harara.

Cike da tsoro ta janye kwayar idanunta daga garesa, tana mai mamakin sauyinsa rayuwa, cikin wani irin
sauri ta nufi ƙofar falon yayin da jikinta ke tsuma Muryanta na rawa tace.

“Ummi ni na tafi”.

Kallon yanda ta nufi ƙofar Ummi tayi kana ta kallo Moddibo da har zuwa lokacin idanunsa ke ƙasa da
mamaki tace.

“Ya da sauri kamar kinga Dodo?”.

Kai ta girgiza batare data juya ba tace.

“A'a Ummi nikam na tafi”.

Cike da kulawa Ummi tace.

“Toh ki tsaya Kiyi breakfast mana”.

Kai ta girgiza still jikinta na tsuma tace.

“A'a Ummi Allah Mommy na za tayi faɗa idan na daɗe”.

Jinjina kai Ummi tayi kana tace.

“Toh shikenan nagode ki gaida Mommy ki gashi kin ki kitsaya kiyi breakfast”.

Da sauri tace.

“Allah Ummi sai da nayi breakfast agida kafin na fito”.

Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.

“Ki gaida Mommy naki da Raudat dasu Haiydar”.

Cikin sauri ta fice daga falon bayan tace zasuji.

Moddibo kuwa ahankali ya jinginar da kansa da jikin kujeran tare da lumshe Idanunsa kana ya cije Lip
ɗinsa na ƙasa, sai kuma yayi saurin buɗesu sabida ganin surar jikinta da yayi ziraran miraran.

Gashi da zaran yaji muryan yarinyar zai riƙa jin wani irin abu mai wuyar fassarawa kana lokacin da
ƙwayar idanunsu suka haɗu babu abinda suka hango masa face.
Ƙirjinta tamkar zasu tsole mishi idanu.

Asma'u Mommy tasa ta kawo masa ɗan waken da sukayi sai ruwan Tea ba laifi yaci danwaken da ɗan
dama kana yasha ruwan Tea.

Malam Ahmad ne yashigo tare da yi masa addu'ar Allah ya tsare miƙewa yayi ya fita kana yaja tsohuwar
motarsa zuwan gidan Abba yana isa yayi Hong mai gadi ya buɗe masa Parking Yayi aharabar gidan kana
yashiga sashen Abba bakinsa ɗauke da sallama ya shiga falon Cike da kulawa Abba da Hajiya Turai dake
zaune gefensa suka amsa masa.

Anutse ya ƙarasa tare da zama gefen Abba cike da kulawa Abba yace.

“Aliyu ka ƙara so?”.

Jinjina kai Moddibo yayi cikin sanyin murya yace.

“Eh Abba ina kwana ya ƙarfin jikin”.

“Jiki da sauƙi Aliyu”.

Bayan sun gama gaisawa Abba yayiwa Moddibo duk kan wasu bayanai kana ya bashi wasu takardu da
duk wani abu daya kamata sai da Abba ya masa bayani.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.

“Toh Abba ni zan tafi”.

Ahankali Abba ya sanya hannu a aljihu tare da ciro key mota sabo dal ƙiran PRADO ya miƙa Masa tare da
cewa.

“Ga wannan Aliyu za'a kaika Airport dashi, in Manu driver ya dawo kuma gidan ku zaije ya ajiye maka
ita”.

Cikin sauri Moddibo ya ɗago kansa tare da Kallonsa.

“Abba mota kuma?”.

Kai Abba ya gyaɗa masa alamar eh.

Cikin sanyi Moddibo ya sake kallon key motar kana yace.

“Abba to ai ina da mota”.


Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.

“Uhm-Uhm Aliyu kenan. Ɗan Allah kada kayi min gardama ka karɓa kawai ka sanya albarka aciki”.

Sunkuyar da kai Moddibo yayi batare da da yace Uffan ba.

Kallonsa Hajiya Turai tayi kana tace.

“Ka karɓa mana Aliyu ai yanzu kam an zama ɗaya”.

Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.

“Toh shikenan Abba Nagode Allah yasaka da Akhairi Ubangiji Allah ya mayar maka da dubunsa”.

Murmushi Abba yayi kana yace.

“Ameen”.

Nan take ya ɗauko takardun motar ya miƙa masa tare da cewa.

“Jiya mukayi magana da Alhj Abubakar nasa ya kawo min da yamma gatanan lafiyarta ƙalau anyi mata
dukkan abinda ya dace”.

Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.

“Nagode Abba Allah yasaka da alkhairi ni zan tafi”.

Ahankali Abba yace.

“Allah ya tsare Aliyu Allah ya bada abinda akaje nema”.

Ameen ya amsa kana ya miƙe Abba ya rakasa da kansa ya buɗe masa bayan motar ya shiga, sabuwar
motarsa sosai motar ta burgesa duda bai wani damu da bakin abuba, amman collor bakin yayi masifar
kyau dan sai sheƙin sabunta takeyi,

Manu ne ya shiga yaja motar suka fita.

Kai tsaye gidan Malam Arɗo ya wuce dashi bisa umarninsa.

Sallama yayi masa kana daga nan suka ɗauki hanyar da zata sadasu da cikin Taraba Jaligo ja gari na Baba
Abasu babban birnin Gembila kenan wanda kuma tsakanin local government ɗin nasu zuwa cikin
ƙwaryar birnin Taraban tafiyace ta musamman.

Koda suka isa cikin Taraba, basu tsayaba suka nausa hanyar Adamawa Yola.
Jauro yaya

Baffan Liman ne zaune agaban Hajja Nana cikin sanyi murya da ladabi yayi ƙasa da kansa tare da cewa.

“Hajja kiyi haƙuri bai kamata ace kina fushi akan abinda bai kai ya kawoba, wannan al'amari ba wani
al'amari mai girma bane bai kamata ace ki ɗauki zafi akansa har haka ba”.

Kallonsa kawai Hajja Nana keyi tana girgiza ƙafa tare da girgiza kai.

Ajiyar zuciya Baffa Liman ya sauke kana ya cigaba da cewa.

“Idan kin lura Khausar fa jika ce agareki ba ƴa bace, kinga kuwa duk ikon ka akan jika yana zama mai
rauni, bare wannan zamanin da muke ya bambanta dana baya dan Allah Addah Hajja kiyi wa wannan
al'amarin Kyakkyawan fahimta”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana tace.

“Na lura sannan na fahimci Liman da kai dasu Garga, Sadu, Jauro baki ɗaya bakin ku ɗaya akan al'amarin
Khausar tun da haka kuka ce ni bani da abinda zance kuje kuyi duk yanda kuka ga dama”.

Ahankali Baffa Liman ya ɗago ya kalleta kana ya sake sunkuyar da kansa.

Cikin alamun ɓacin rai ta cigaba da cewa.

“Amma fa kusa ni ba zata Auri wannan yaron ba, tunda har ta iya buɗe baki ta kalli tsabar idona tace
bata son. Aliyu jikina kuma ɗan Uwanta toni babu hannu na akanta kuyi mata yanda take so amma
banda Auren mara tushe da asali”.

Gyaran murya Baffa Garga yayi kana yace.

“Dan Allah Addah Hajja kiyi haƙuri shikansa. Muhammadu Jimeta yace zai zo amma yafi so yazo ya
sameki cikin farin ciki kada akan batun Khausar ranki ya dinga ɓaci abanza a wofi”.

Fuska ta ɓata tare da Kallonsu ɗaya bayan ɗaya kana tace.

“Idan yayi niyyar zuwa yazo idan kuma baiyi niyyar zuwa ba yayi ta zama tunda shi kansa bayanta yake
bi, tun da wai har cewa yake bazai yi mata dole ba”.

Baffa Liman ya sake sassauta muryarsa yace.

“Dan Allah Addah Hajja kiyi haƙuri ki bi lamarin asannu da izinin Ubangiji komai zai dai-dai-ta amma
bama son ganinki cikin damuwa”.
Haka suka riƙa Rarrashinta tare da kalamai masu kwantar da zuciya.

Acan ɓangaren Moddibo kuwa tafiya tsakanin Taraba da Yola tafiya ce mai zaman kanta sai dai bata
wuce awa biyu zuwa uku, tuƙi Manu keyi cike da ƙwarewa ga samun sabuwar mota.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya fesar da sassayan numfashi.

Sabida ji yake wani irin yanayi yana lullubeshi gaba ɗaya tunanin J ɗin sa ya dawo masa ji yake tamkar
idan ya juya gefen damansa zai ga J ɗin sa, ahankali ya zira hannunsa ya kara volume din ƙira'ar da yake
ji acikin Suratul Nisa'i, sai kuma ya koma baya ya jingina bayanshi da jikin Seat ɗin.

Domin idan har ba karatu yake jiba ko kuma yake yi sam baya taɓa samun nutsuwa, saidai kuma ta wani
ɓangaren haka nan yake jin wani irin farin ciki da yabar garin Gembila, ji yake tamkar yabar wani yanki
da yake da tarin ƙunci, ji yake tamkar yabar wani waje mai duhu da zafi ji yake tamkar ana zare ransa da
ruhinsa daga waje mai ƙunci da azaba, kana kamar ana nufar dashi awaje mai tarin nutsuwa da salama
yakeji.

Domin tun bayan rasuwar Amininsa garin Gembila tayi masa zafi da ƙunci kana tayi masa duhu baya
kallon haskenta gaba ɗaya ya tsani garin, to dama Meya rage masa da garin Innayinsa ce kaɗai sai kuma
Ummi dasu Asma'u.

Sai Misalin ƙarfe biyu da rabi ya shiga cikin Adamawa suna isa cikin Adamawa.

Manu yayi Parking A dai-dai Masallacin jum'ae dake cikin Atiku Abubakar shopping mall ɗinsu nan
sukayi Al'wala sukayi sallar Azahar Kasancewar hanya zai kama, ɗan tafiya yasa a gaba shiyasa yayi niyar
ƙasaru ya haɗa da sallar La'asar domin karfe uku dai-dai jirginsu zai tashi.

Baya jin zai iya cin wani abu haka yasa ya kalli Manu cikin mutuntaka yace.

“Manu sannu da yunwa”.

Cikin girmamawa Manu yace.

“Laa ba komai ai kafin mu fito ma naci abinci”.

Kai ya jinjina kana yace.

“Muje ka kaini cikin Airport ɗin, sai kayi sauri ka juya, kada kayi dare a komawa”.

Cike da gamsuwa Manu yace.

“Toh”.
Daga nan ya kaishi Airport sannan shi kuma ya fito, ya ɗan samu abin da ya taɓa kana ya kama hanyar
komawa Taraba, Gembila.

Ƙarfe uku Dai-dai jirginsu Modibbo ya tashi daga Adamawa zuwa birnin tarayyar Nigeria Abuja.

Alhamdulillah cikin kwanaki huɗu bizi'nsa ya fito da yake business bisa ne ba wuya.

Alhamdulillah ranar Al'hamis da misalin ƙarfe biyu dai-dai jirginsu ya ɗaga daga Abujam Nigeria.

Zuwa Rabat babban birnin ƙasar Marocco kenan

A hankali ya fesar da wani irin zazzafan numfashi dai-dai lokacin da tayun jirginsu ke raɓuwa da ƙasar
Nigeria, rumtse idanunsa yayi da karfi sabida wasu irin zafafan hawaye da yaji suna tsastsafo mishi ta
cikin dukkan jijiyoyin idanunsa.

Wani irin yanayin da bai taɓajiba duk tafiye-tafiyen da yakeyi yaji yana dabaibaye rayuwarsa haka kawai
yakeji kamar ya bar kasar kenan bari na har abada.

Lokaci ɗaya tunanin Jameel ya dawo masa, wanda hakan yasa yayi saurin jingina bayansa da kujerar
jirgin.

Yana mai jin wani irin sassayan kuka na taso mishi daga can cikin ƙahon zuciyarsa, hakanne yasa ya fara
karatun Alqur'ani mai girma a hankali.

Yayinda mutanen cikin jirgin kuwa kowa keta hidimar gabansa.

Shi kuwa Modibbo tunda ya zauna bai ɗago kansa ya kalli kowaba.

Sabida yanayin da yakeji.

A hankali dai tafiya ta fara nisa, tuni sun kutsa cikin sararin samaniya jirgi ya kama hanyarsa.
Koda akazo tambayarsu me yake buƙata.

Cewa yayi baya buƙatar komai.

A ƙalla sunyi tafiyar awa uku a sararin samaniya.

Zuwa yanzu kam mafi akasarin matafiyan kowa ya nitsu hada-hadar ta ragu matuƙa, wanda zuwa lokacin
kuma sauran musu 57 minutes su dira cikin birnin Rabat sabida daga Abuja zuwa can tafiyar awa uku da
minti hamsin da bakwai ne cib-cib.

A hankali ya gyara zamansa tare da kallon farin matashi da ya zo ya zauna gefensa wanda bazai wuce
sa'anan ba.

Murmushi matashin yayi tare da miƙa masa hannun yana mai mishi wani irin kallo mai cike da tambayo
al'ajabi da kaɗuwa.

Shima ɗan murmushin yayi tare da bashi hannu sukayi musabaha.

“Jabeer bin Jabeer Joɗa. Wanda ya kira kansa da Jabeer ɗan Jabeer Joɗa ɗin ya kare mgnar cike da
masifar mamaki da zurawa fuskar Modibbo idanu yana matuƙar mamakin kamanninsa.

Shi kuwa Modibbo cikin yanayin sanyi yace.

“Aliyu Youssef Muhammad Mouley”.

Cikin tsananin bayyanar mamaki ya zazzaro idanu waje tare da juyowa garesa da kyau cikin alamu rawan
jiki ya juya harshe zuwa larabci yace.

“Yah Salam toh kuma yaushe kazo”.

Cikin ɗan sanyi Modibbo shima juya harshe ih zuwa asalin amintaccen larabci yace.

“Nazo kuma? Nida ƙasata, me zanje yi a Marocco dai zaka ce”.

Kai Jabeer bin Jabeer Joɗa ya jujjuya tare da juyawa yayi mishi mgn da hausa yace.

“Kamar yaya ƙasar kuma?”.

Ga mamakin Jabeer sai yaji Moddibon na bashi amsa da harshen hausa.

“Sabida ni ɗan Nigeria ne girman Nigeria”.

Da sauri Jabeer yace.


“A'a wannan ai ko makaho ya shafa yasan kai ba ɗan Nigeria bane kuma ma sunan da ka fadi ai ya isa
shaidar inda ka nufa komawa zaka yi ba zuwaba”. Ya ƙare mgnar da iya haƙiƙanin gskyrsa da rawan jiki.

Cikin ɗan ƙosawa da surutun sa Modibbo yace.

“To sabida me?”.

Da sauri Jabeer yace.

“Sabida kafi kama da Larabawa”.

“Toh gashi kuma kaima da larabawan kake kama”.

Gyara zama Jabeer yayi tare da cewa.

“Kuma ni dai ba fullatanine”.

A hankali shima Middibo yace.

“Minfu mi pullo”.

To zuwa yanzu kam mamakin Jabeer ya tsananta.

Ya buɗi baki da niyar zaiyi wata mgnar kenan aka kirashi a baya bisa dukkan alamu Kakanshi ne da sauri
ya tashi ya nufi can bayan.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya fesar da numfashin gajiya da surutun da Jabeer ya sashin.

Tare da fara karatun Alqur'ani mai girma.

Jim kaɗan da tafiya Jabeer sai gashi ya dawo zama yayi bakinsa cike da tarin mgn to amman samun yana
karatun Alqur'ani mai girma yasa dole ya haɗiye dukkan rogowar mgnarsa da tarin tambayoyinsa.

A hankali Moddibon ya ɗago manyan idanunsa tare da kallon taswirar kasar Rarat da suka iso tsakiyarta.

Wanda tuni an sanar musu.

Haka nan yake jin wani irin salama da kwanciyar hankali kana da nutsuwa tunda suka shiga yankin ƙasar
Marocco yake jin wani irin sanyi da more happy Wanda har ya iya jure surutun Jabeer.
Numfashin mai sanyi ya fesar tare da ƙara ware manyan idanunsa yana kallon garin ta window'n jirgin.

Haka nan yakeji tamkar yabar damuwarsa baki ɗaya acikin Nigeria ya kuma saki dukkan ƙuncinsa a cikin
Taraba.

Cikin nutsuwa da kwanciyar hankali yake bin tsarin dogayen benayen gidajen garin da kallo kana
sassayan muryarsa na ratsa kunnuwansa yana jin sautin karatunsa da yakeyi jikin suratul Kahf.

Misalin ƙarfe shida saura minti uku rak.

Jirginsu yayi sauƙar angulu a cikin babban Airport dinsu.

Rabat Sale international airport.

Wanda dai-dai lokacin kuma ya dire ayar ƙarshe ta Suratul Kahf ɗin tuni kuma jirginsu ya dai-dai-ta
da'irar tsayuwarsa.

Da sauri Jabeer ya kalleshi sai kuma yayi sauri ya mayar kallonshi gefen damanshi ganin har an buɗe
ƙofar jirgin.

Juyowar da zaiyi kuwa sai ganin Middibo yayi a tsaye yana jawo jakarsa daga drower dake samansu.

Da sauri ya miƙe shima, sai kuma yaji ana kiransa a baya, da sauri ya nufi bayan.

Shi kuwa Modibbo agogon dake hannunsa ya kalla, da ɗan hanzarin sa ya nufi wajen sabida ƙaratowar
lokacin sallan magrib.

A hankali ya fesar da sassayan numfashi, dai-dai lokacin da ya taka step na forko wanda ya fito da kanshi
sararin garin Rarat, duk da dai duk Arfica ne amman ƙasar Marocco sunyi mana rata zarrama mai girma,
sunada ci gaba na musamman.

A hankali ya furta.

“Yah Salam”.

Sabida wani irin ni'imtaccen iskane mai cike da salama ke ratsashi yana shiga duk ta inda hudar gashin
jikinsa yake.

Wani rin amintaccen numfashin mai cike da yanayin sauƙe ajiyar zuciya ya shaka, like ɗan da ya daɗe
baiga mahaifiyarsa ba, kuma yayi kuka.

A hankali yaci gaba da taka steps din yana sauƙo ƙasa.


Wani saurin runtse idanunsa yayi lokacin da ya dire tafin ƙafarsa kan ƙasar Marocco cikin yankin Rarat.

Wani irin tsuma yaji naman jikinsa nayi tun daga can cikin jikinsa da zuciyarsa yakejiyo wani irin tsuma.

Wanda ya ta'allaƙa hakan da tsananin yanayin sanyin garin ne.

“Alhamdulillah!!!”.

Ya furta a saman lips inshi sabida, tunda Allah ya halicce shi bai taɓajiba irin yanayin da yakeji a yanzu, ko
Saudia yaje bayajin yanayin nan.

Yana mai shaƙar sassayan iskan garin ya fara bin ayarin sauran matafiya.

Yayinda can gefen kuma manyan motocine na al'farma wanda bisa dukkan alamun wani babba akazo
ɗauka.

Su kuwa a cikin yanayin gajiya suka ƙaraso inda masu tarɓarsu suke.

Ɗan dube-dube ya yayi.

Da sauri ya nufi wani Balarabe dake jingina da Taxi yana riƙe da ɗan allon tarba wanda aka rubuta Aliyu
Youssef Muhammad Mouley.

Yana isa yayi masa sallama.

Cike da tsananin girmamawa Balaraben yayi saurin buɗe masa marfin motar tare da cewa.

“Marhababuka”.

Kai ya jinjina masa cike da gajiya da ƙosawa.

Yasan Taxi Abba ne ya turosa.

Da sauri shima ya shiga Taxi ɗin kana yaja suka fita daga cikin Airport ɗin.

A hankali yayi miƙa tare da jingina bayansa da seat ɗin dai-dai lokacin da suka ratso ta cikin unguwar Ben
slimane.

Anƙuwace ta masu alfarma, haka yasa tsarinta na musamman ne.

haka nan yaji yanayin Weather yayi masa masifar daɗi da kyau.
Gashi yanayin damuna ne Iska mai sanyi da ratsa jiki na kaɗawa gashi duk ta inda ka wulga ido bishi
yoyin dabinone masu kyan tsari ke rausayawa sunyi kore shar dasu iska na kaɗawa suna rangaji ga kasar
garin ajiƙe yake alamun anyi ruwa.

Ƙarfe shida da minti sha biyar dai-dai mai Taxi ɗin ya juya hancin motarsa kan wani gini mai kyau da
ɗaukan indo wanda a samansa aka rubuta.

Belere Hotel Rabat.

Kai da ganin masifar kyau da tsaruwan hotel ɗin kasan zaiyi masifar tsada.

Cikin taushin murya ya kalli Balaraben dake riƙon.

Tare dayin mgn da larabcin.

“Muje wani wanda bai kaishi ba”.

Cikin sanin darajar aiki mai Taxi ɗin ya ɗan kalleshi ta madubi tare da cewa.

“Toh".

Daga nan ya juya akalar motar ya ɗauki hanyar da zata sadashi da unguwar Sidi bettache.

Tafiya kaɗan sukayi suka fito kan babban titinsu.

Da sauri Modibbo yace.

“Masha Allah”.

Dai-dai lokacin da

Idanunsa suka sauƙa akan tamfatsetsen masha'hurin hotel mai masifar kyau da tsari daga can sama
tsololuwan ginin an rubuta.

Welcome to Sofitel Youssef Mouley hotel.

Da sauri yace.

“Tsaya mu shiga nan”.

Yayi mgnar still idanunsa na kan sunan hotel ɗin da yayi kama da sunanshi hakan don sunan hotel ɗin
yaji yana son sauƙa a nan.

Murmushin mai Taxi ɗin yayi tare da cewa.


“Toh ai wannan yafi wancan tsadama”.

Da sauri ya gyaɗa mishi kai tare da cewa.

“Eh shi yayi”.

Ya ƙare mgnar da lumshe idanunsa jin sautin kiransan salla a masallacin dake cikin hotel ɗin.

Haka yasa shima mai Taxi ɗin saurin shiga.

Numfashi mai sanyi ya fesar tare da buɗe Idanunsa daya lumshe kana ahankali.

Wani irin hotel ne mai masifar kyau da tsari da girma duk da cewa a farfajiyar akwai masallaci sai dai ba
wani Babba bane, amma farfajiyar babbe ne me kyau da tsari daga gefen dama wajen Parking din
Motoci ne wanda aƙalla zai ɗauki motoci settu zuwa saba'in da biyar kana daga jikin doguwar kantamgar
kuwa bishiyoyin kwakwane zagaye da ginin daga can gefe kuma wasu irin flowers ne dake wadace da
damshin ruwa haka yasa jikinsu sai sheƙi kayi, tafiya kaɗan zaka samu side ɗin shiga Reception ɗin.

Atsakiya daga gefe da gefe kuma hanya ce kana daga baya wani ƙaton gardin ne wanda yana iya hango
bishiyoyin dake ciki kana yana jiyo sautin kukan tsuntsaye kala da ban daban.

Ahankali ɗago daga jingina da seat din da yayi.

Yana Jin zuciyarsa na harbawa kaɗan kaɗan cikin sauri mai taxi ɗin ya rufe marfin gefensa cikin
sassarfa ya zagoyo gefen da Modibbo yake tare da buɗe masa murfin motar kana fuskarsa ɗauke da
murmushi yace.

“Lalle marhaba fatan an ka isa Marocco lfy”.

Cikin sanyin murya da tarin gajiya yace.

“Yawwa”.

Kana ahankali ya ziro ƙafafunsa waje ya sauke aƙasa.

Da sauri ya rumtse idanunsa tare da kuma buɗesu a lokaci ɗaya yaji wani irin abu mai masifar sanyi ya
zira masa tun daga tafin ƙafansa har zuwa ƙwaƙwalwar kansa irin dai abinda yaji daya taka ƙafarsa a
Airport. cikin sauri ya kuma lumshe idanunsa tare da furta.

“Yah Salam”.

Kana ya fito dai-dai lokacin da mai kira sallah a masallacin hutel ɗin yazo dai-dai wurin kalmar shahada.
Cikin sanyi ya fara bin kalmar shahadar, wanda hakan ya ankarar da mai taxi dinma ya amsa, tare da bin
addu'a'o'in da yaji Moddibon yanayi.

Cikin sanyin murya Mutumin yace.

“Sannu da zuwa”. Lokacin da yaga ya ɗan juyo ya kallesa.

Kai Modibbo ya gyaɗa masa tare da buɗe bayan motar ya ɗauki Breafcase ɗinsa tare da jakarsa, da sauri
mai taxi ɗin yasa hannunsa ya amshi jakar kan nasa tare da kuma miƙa masa hannun zai amshi Breafcace
ɗinma.

Kai Modibbo ya girgiza tare da faɗin.

“Barshi, zasu yi maka yawa ai”.

Cikin jin daɗi yayi gaba tare da

cewa.

“Bismillah kashiga ciki gashi ma Maghariba ta tayi”.

Cike da salama Moddibo yace.

“Bismillah”.

Yayi mgnar tare da nuna masa gabanshi alamun yayi gaba.

Cikin sauri yashiga gaba kana Moddibo yabi bayansa.

Cikin hanyar da flowers ke ajere gefe da gefe sai ɗan mawadacin hanya dake tsakani sukabi.

Ahankali Moddibo ya taka step ɗaya biyu ana ukun ya hau kan barandar Kofar falon.

Ya sanya ƙafarsa na dama aciki tare da furta.

“Masha Allahu laƙuwwata Illah billahi”.

Sosai komai na hotel ɗin keda tsari na Muslunci da burgewa.

Cikin yanayin gajiya ya ƙarasa gaban ma'aikatan dake binsa da kallon ƙurilla.

Bayan sun gaisane ya kama ɗaki, cike da mutuntaka da martabawa suka gama komai, ɗaya daga cikinsu,
ya amshi jakarsa dake hannun mai taxi ɗin.

Kana yayi gaba tare dace masu bismillahi.


Cike da gajiya yabi bayanshi.

Lifter suka shiga cikin minti biyu suka isa hawa na biyu inda na ɗakin daya kaman yake.

Ma'aikacin hotel ɗin ne da kansa ya buɗe ɗakin ya shiga kana ya shimfiɗa beshit tare blanket, kana ya
wuce da sauran kayan kamarsu Towel da Bathrobe da makilin da Brush sabulu ya ajiyesu bathroom tare
da feffesasa Air freshner kana ya fito tare da cewa mishi.

“Sir akwai abinda kake buƙatane?”.

Kai ya jujjuya mishi alamun a'a.

Ganin haka yasa ya fice.

Shi kuwa Modibbo cike da gajiya ya ajiye woyoyinsa yana mai shaƙar ƙamshin Roomfreshner tare da
kallon tsarin komai na ɗakin, komai na cikin falon Ash & maroon colour ne mai masifar kyau kama daga
Cottins carpet dama kujerun.

Cike da gajiya a shiga bathroom al'wala yayi tare da fitowa da sassarfa.

Lifter ya shiga ya sauƙa kana kai tsaye masallacin dake cikin hotel ɗin ya shiga da sassarfa jin an tada
iƙama.

Ya samu tuni sahu forko da na biyu duk sun cika sai ana uku suka tsaya

Suna shiga suka tada kabbara dai-dai lokacin kuma aka tafi ruku'un Farko.

Bayan anyi Sallah an idar Moddibo.

Yayi Adduo'insa na yau da kullum, ya kara da na neman aminci cikin wakilcin da zaiyiwa Abba tare da
samun nasara da roƙon Allah yayi riƙo da hannayensa ya bashi ikon riƙe amana.

Yana so ya jira Isha'i amma saboda yanayin gajiya da yake ji bazai iya jira ba yana so yayi wanka duk da
cewa garin akwai sanyi,

Amma yana son yayi wanka dan yaji daɗin jin kinsa da sauƙin gajiyar hanya.

A hankali ya yunƙura da niyyan tashi, cikin sauri ya juya bayansa tare da fito da Idanunsa cike da
tsananin son tabbatar da ganinsa ya miƙa da sauri saboda gani fuskar da bashi da hauki ko kokonta a kai
cewa fuskar J...!
*Littafin dai na kuɗi 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar
biyanki ta WHATSAPP 09097853276*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

39

*Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa.* Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi
kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan
ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin
har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin
har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin
fitsari, da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya Zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki
dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection
cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin
kala biyarne nasha kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin
kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana
dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya
musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki
aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa
ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga
account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min
mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi
Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari
da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan
Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR
MA'AURATA.

39

Da sauri ya juya baki ɗayansa kana ya nufi hanyar ƙofar masallacin ta waje yana ida fita yaga anja motar
dake gefe ta wajen masallacin antafi dashi cikin sauri ya sanya hannunsa duka biyu ya dafe kansa yana
maimaita duk wata addu'a da tazo bakinsa.

Batare da yace Uffan ba ya juya kansa ya nufi cikin hotel cikin raunin murya yace.

“Meyesa idanuna ke yimin gizo yau kuma J ɗina nake gani”.

Haka yaci gaba da mgnar zuci har ya shiga ɗakinsa.

Baki ɗaya abin ya fara bashi tsoro anya kuwa bai far zaucewa ba. Ya ƙare mgnar zuci tare zamewa ya
zauna bakin gadon.

Wayoyinshi guda biyu dake gefen jakarshi ya ɗan juya ya kalla sabida jin ƙaramar tana ruri.

Hannunsa yasa ya zarosu, duk da kiran ya katse. Numfashi mai sanyi ya fesar ganin tarin miss call ɗin
Abba, Innayi, Ummi da Malam Arɗo ahankali ya fesar da numfashi tun da yabar masauƙinsa na Abuja
gaba ɗaya mancewa yayi da wayoyin suna cikin jaka bai buɗe ba sai yanzu da yaji kiran. Da sauri yayi
picking call ɗin Abba da ya sake shigowa.

Cikin sanyin yayi sallama tare da cewa.

“Barka da dare Abba”.


“Barka dai Aliyu ya gajiyar hanya tun ɗazu nake ta kiranka, shiru”.

Cikin lumshe ido yace.

“Alhamdullah Abba phones ɗin ne suna cikin jaka”.

Ajiyar zuciya Abba ya sauke cike da kulawa yace.

“Amma to ya hanya”.

Murmushi Moddibo yayi kana yace.

“Lafiya lau hanya Alhamdulillah Abba gashi har na isa nayi sallar maghariba, yanzu wanka zanyi kafin
sallar Isha'i ta gabato”.

Jinjina kai Abba yayi kana yace.

“Alhamdulillah ahuta gajiya amma kafin nan ka kira Innayi da Malam Arɗo da kuma Ummin ka dan
hankalinsu ya kwanta”.

Kai ya gyaɗa cikin alamun gajiya yace.

“Toh Abba Insha Allah zan kira”.

“Wanne hotel ka sauƙa”.

Abba ya tambaya.

Ɗan guntun numfashi ya fesar tare da cewa.

Sofitel Mouley Youssef na sauƙa Abba dan naga Hotel yanada Kekkyawan tsari kuma a binciken da nayi
naga yafi kusa da Companyn' namu”.

Cikin gamsuwa Abba ce.

“Sosai ma kuwa, anan kusa da shine ma gidana yake inda nake sauƙa in nazo. Kaima dan ba'a gyarashi
bane shiyasa”.

Miƙe tsaye yayi da wayar saƙale a kafaɗarsa yace.

“Amman yanada tsada kam”.

Shi kuwa Abba gyara zama yayi tare da cewa.


“Ka zauna anan zuwa lokacin da za'a gyara gidana dake nan bayan hotel ɗin ƙadan, sai ka koma can, zan
turo maka mai gadin gidan zai zo ya kawo maka key ɗin motar da zaka rinƙa zirya dashi, zai kuma
nunnuma maka duk abubuwan da suka dace”.

cikin gamsuwa yace.

“Toh Abba sai yazo”.

Daga nan sukayi sallama.

Yana katse kiran yayi dearling number Innayi lokacin da kiran ya shiga Innayi na kan Sallaya bayan ta idar
da sallan maghariba tana ganin kiran tace Alhamdulillah kana ta ɗaga tare da kaiwa kunnenta tace.

“Moddibo”.

Lumshe Idanunsa yayi tare da komawa yayi bakin gadon ya kishingiɗa kana yace.

“Na'am Innayi”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe cikin sanyin murya tace.

“Fatan ka isa lafiya?".

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Lafiya lau Alhamdulillah”.

Numfashi ta fesar kana tace.

“Masha Allah cikin Rabat kake ko kuma cikin gefenta kake?”.

Cikin alamun gajiya yace.

“A'a cikin Rabat nake a tsakiyar garinma kuwa”.

Kai ta gyaɗa cikin sauke numfashi tace.

“Wace Unguwar?”.

Hannu yasa tare da shafa sumar kansa kana yace.

“Tsetse amman a hotel ne”.

Kai ta jinjina tare da sauke numfashi tace.

“Ayyah Tsetse kuma kai bansan Unguwar ba”.

Ware ido yayi tare da miƙewa daga kishingiɗar da yayi da mamaki yace.

“Dama to kinsan Rabat ne bare kisan Unguwannin su?”.


Cikin sauri ta girgiza kai kana tace.

“Um-um bansani ba amma ban taɓa jin sunan bane”.

Ahankali yace.

“Ayyah yanzu ina so inyi wanka ne”.

Kai ta gyaɗa cike da kulawa tace.

“Toh shikenan ahuta gajiya”.

Daga nan ya kira Ummi da Malam Arɗo bayan sun gama gaisawa ya shiga toilet, da ido yabi turaren
wanka Maclean brush towel pich colour yana kallo komai na ciki sabone Anutse ya fara wankan lokaci
ɗaya yaji tsikar jikinsa na miƙewa sabida wanirin sanyin na ratsa baki ɗaya ilahirin jikinsa, cikin sauri yaja
dogon tsaki Aransa kana yace.

Anya wannan aljanar yarinyar zata bar rayuwata ta nitsu kuwa, yarinya sai mata da nacin tsiya.

Towel ya janyo ya ɗaura kana ya ɗaura alwala ya fito dai-dai lokacin aka kira sallar Isha'i jikin Dressing
mirrow ya nufa ya shafe jikinsa da mai kana ya fesa turare sa masu daɗin ƙamshi kana ya buɗe jakarsa ya
ciro Jallabiya Sky blue me taushi kana ya ɗaura hirami kamar ɗankwali ya riƙe farin carbin sa sosai yayi
kyau tun da aka sace M Jameel aka kashe sa bai sake yin wankan daya nutsu irin na yau ba yana fita ya
nufi Masallaci akayi sallar Isha'i ana idarwa yayi adduo'i kana sai da aka wawwatse kafin ya fito ya nufi
cikin ƙoƙarin shiga ya haɗu da mai gadin na fitowa.

Kallonsa mai gadin yayi cike da girmamawa yace.

“Aliyu Youssef Mouley?”.

Ya faɗin sunan da sigar tambaya tare da duba hoton Modibbo da Abba ya tura mishi ta whatsapp.

Kai Modibbo ya haɗa mishi tare da bashi hannu.

Cikin fara'a mutum miƙo hannunsa tare da cewa.

“Assalamu alaikum Yah Mouley”.

Rumtse ido Modibbo yaui domin tunowa da Jalaladdeen ne kaɗai ke kiransa da wannan suna. Sai kuma
ya ƙara rumtse idanun da ƙarfi, sabida tunowa da tsawon lokacin da baiji motsin Jalaladdeen ba, tun
kafin a sace. Jameel, ya tabbatar babban abune kaɗai zai iya ritsa Jalaladdeen da har zai iya hanashi
nemansu na tsawon wannan lokacin.

Cikin sauri ya buɗe idanunsa tare da gyaɗa tsayuwarsa yana jan Carbin hannunsa jin Mutumin na cewa.
“Sunana Habibullah nine mai gadin gidan Alh Bashir kuma nike kanshi in yazo duk inda zaije nike kaishi
kuma nida matata ke zaune a BQ ɗin gidan”.

Kai Modibbo ya gyaɗa masa tare da cewa.

“Eh Abba ya gaya min”.

Jinjina kai mai gadin yayi tare da cewa.

“Ganan abinci na kawo maka”.

Kallonsa Moddibo yayi da mamaki yace.

“Abinci kuma?”.

Kai mai ya gyaɗa alamar Eh.

Jinjina kai Moddibo yayi tare da kallon womers ɗin hannunsa yace.

“Toh daga ina aka samu abincin?”.

Murmushi mai gadin yayi kana yace.

“Ai akwai abokin Alh anan lokacin da Marigayi Jameel yazo har ya koma daga can ake kawo masa
abinci”.

Lumshe idanu Moddibo yayi cikin sanyi yace.

“Ayyah yayi kyau angode”.

Sannan yayi gaba, mai gadin kuma na biye dashi.

Bisa kujerar ya zauna shi kuwa Habib kai tsaye dining area ya nufa kana ya ajiye mishi ɗan kondon da
kulolin ke ciki, kana ya dawo gabanshi tare da miƙa mishi key ɗin mota tare da cewa.

“Ga wannan da ita zamana fita, in kuma baka son draving ga number'n ta sai ka Kur'ani, zanzo in kaika
duk inda kakeso”.

Ya ƙare mgnar tare da miƙa masa hannunsa alamun ya bashi wayarsa ya saka mishi number's.

Wayar ya miƙa mishi ba tare da yace komai ba.

Shi kuwa Habib number's sa ya sawa wayar Modibbo kana ya miƙa mishi.

Amsa yayi tare da ajiye wayar.

Shi kuwa Habib sallama yasa kana ya miƙe ya ficee.


Shi kuwa Modibbo a hankali ya miƙe jin yadda cikinsa ke ƙugi alamun yunwa.

Dinning table ya nufa, kujerar yaja ya zauna tare da zuba abinci kana ya fara ci bayan ya gama ne ya
dawo falon.

Lumshe yayi dearling number Abba.

Bayan Abba ya ɗaga sun sake gaisawa ya sauƙe Ajiyar zuciya tare da cewa.

“Toh Abba yanzu me ake ciki idan Allah yakai mu gobe dame dame za'a fara?”.

Kai Abba ya Girgiza cikin yanayin sanyin muryarsa yace.

“A'a Moddibo gobe kam ka huta tun da kaga yau Alhamis gobe kuma jumma'a ne ba aiki a ƙasar tasu
dan jumma'a da asabar ne ranakun hutun ƙarshen makonsu, shiyasa dama naso yau ka tafi ka kwana ka
huta gobe ma huta sai jibi lahadi in Allah ya yarda zaka fara zuwa Company”.

Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.

“Toh shikenan Abba Allah ya kaimu”.

Ameen Abba ya amsa kana sukayi sallama.

Miƙewa yayi akan kushin ɗin ya lumshe Idanunsa a hankali yayi miƙa da alamun gajiya kasancewar yayi
doguwar tafiya sannan dan kusan wuni yayi a zaune, da fari akan ƙarfe tare jirginsu zai tashi. Ashe tun
dare sun mishi text sun caza lokacin tashin sun meda sai biyu zasu tashi bai ganiba, saida yazo Airport
ɗin, shiko yanaga komawa ciki wani jidaline shiyasa ya zauna anan kawai.

To hakan ne yasa ya wuni a zaune, shiyasa gaba ɗaya gaɓoɓinsa ciwo suke masa ahankali ya gyara
kwanciyar sa still Idanunsa na lumshe cikin sauri ya miƙe kana ya tashi ya zauna numfashi mai zafi ya
fesar, tsaki yaja kana ya miƙe tare da nufar ƙofan Falon ya fita yana mgnar zuci Mayya jarabebbiya nan
ɗinma sai kin adaddabeni.

Ahankali ya tsirawa coumpund ɗin ido zuwa wajen ganin yanda fitilu suka haska wajen kamar rana
komai na hotel ɗin abin burgewane da ban sha'awa ne ahankali ya fara taka step ɗin farandar yana
sauƙa kallon dattijon mai gadin dake zaune daga can wurinsa ya nufa,

Duk da tarin motocin dake wurin Hausa wurin ya cunkushe ba, yayinda kuma kowa harkar gabansa yake.

Hannu ya mikawa tsohon tare da yi mishi sallama.


Cikin tsananin girmamawa tsohon ma ya bashi hannu tare da zuba mishi ido cikin ƙare masa kallo.

Shi kuwa Modibbo a ya buɗe bakinsa tare da ɗan ɗaga sautin muryansa yanda zaiji yace.

“Baba”.

Miƙewa Dattijon yayi tare da da ɗan rusunawa kana ya ɗan ɗaura hannunsa na dama kan kirjinsa tare da
ɗan sunkuyawa cike da tsananin girmamawar da ta fara bawa Modibbo haushi ya za'ayi dottijo kamar
wannan yake kishi haka, in Habib ya mishi haka zai iya amsa sabida ya girmeshi.

Numfashi ya fesar tare da ɗan sakin fuska jin dottijon na cewa.

“Na'am Alh ya aka yi?”.

Gyara tsayuwar sa yayi kana yace.

“Baba kana zaune kai kaɗai ne?”.

Kai Dattijon mai gadin ya gyaɗa kana yace.

“Eh Alh gacan abokan aikina yanzu sune a bakin gate, ni sai da safe zan koma can kuma, yanzu anan
nake”.

Ya ƙare mgnar yana buɗe wani mutun da yazo shiga, saida mutumin ya shiga kana ya kuma rufewa.

Girgiza kai Moddibo yayi yana kallon kalimin Dattijon numfashin ya fesar tare da cewa.

“Sunana Aliyu Youssef Muhammad Mouley, daga Nigeria amma kakata tana kirana da Moddibo zaka iya
kirana Modibbo”.

Jinjina kai Dattijon mai gadin yayi yace.

“Ayyah Alh yayi kyau”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe cikin sanyin murya yace.

“A'a ba sai kace min Alh nan ba ka kirani da sunana kawai”.

Kai ya gyaɗa yana jinjina karamcinsa Aransa yace yana nan kamar ƙaninsa Ibrahim Youssef Muhammad
Mouley. Ibrahim bashi da girman kai sai dai shi Ibrahim yafi wannan dariya afili kuma sai yace.

“Toh Moddibo”.

Murmushi Moddibo yayi kana yace.

“Yawwa ai yafi sannan kuma akwai abinci da aka kawo min so naci yamin yawa, kaje ka ɗauka mana sai
kaci sabida kada ya lalace!”.
Cikin tsananin mamaki da ganin tsananin karancin Dottijon ya haɗa kai, tare da amsar key ɗin ɗakin da
Moddibo ke miƙa masa, cike da yarda aminci yace.

“Ngd Ngd matuƙa Modibbo, Allah ya kara girma ya kare zuriyar Mouley baki ɗaya”.

Gyara tsayuwa yayi tare da girgiza kai yace.

“Amin Ya Allah”.

Gefensa mai gadin yabi kana yace.

“Bari na ɗauka to”.

Ya faɗi tare da nufar cikin, cikin nitsuwa Modibbo yabi bayanshi.

Yana shiga falon ya dauko Warmers din sannan ya fita.

Cike da girmamawa Moddibo yace.

“Toh saida safe Baba”.

Mai gadin na fita yace.

“Allah ya tashe mu lafiya ahuta gajiya”.

Sannan ya fice.

Ahankali Moddibo ya rufe ƙofar falon tare da kashe wutan falon da Ac kana ya nufi Bedroom ɗinsa
Kallon AC bedroom din yayi jin kamar yayi mishi yawa ne yasa hannun ya ɗauki rimot ɗin kana ya rage
gudunshi.

Kwanciya yayi akan gadon tare da lumshe Idanunsa cikin sauri ya buɗe Idanunsa tare da dafe ƙasan
lokaci ɗaya zuciyarsa da jikinsa sunka harba a tare, baki ɗaya ya fahimci wannan muguwar yarinya haka
zatayi ta addabar rayuwarsa kenan.

awannan rana dai haka ya kwana cikin wani irin yanayi bacci rabi da rabi yayi.

Washe gari Jumma'a haka ya wani cikin hotel din sai sallan jumma'a da ya fita ana isarwa ya dawo, daga
nan ko bakin titin hotel ɗin bai leƙaba.

masallaci ne kaɗai ke fitar dashi.

Hakan yayi kwana biyu yana hutawansa.


Yau Lahadi a bisa tsarin ƙasar Marocco yau ɗin ne forkon sati.

Ƙarfe takwas ya samu Moddibo acikin Company Abba bisa jagorancin Habib.

Yana isa suka fara aiki gadan-gadan aiki ake tako ina babu kama ƙafar yaro domin dama sa hannunsa
kawai ake kira da sahalewarsa a matsayinsa na mataimakin MD duk sabbin Injina da aka kawo aka shiga
daddasasu da duk wasu gyare-gyare daya kama suka shiga yi domin samun asabunta Company da
habaƙashi don har buga atamfofi, Laces, Mayafain laffaya da duk sauran abubuwan buƙata suke so
farawa.

Domin shine Company na farko da aka buɗe sa acikin Rabat wanda aka haɓakasa sannan ake inganta
kayyakinsu.

Bai bar cikin Company ba sai shida saura kwata kai tsaye masauƙin ya wuce yana isa yayi Hong mai gadi
ya buɗe masa gate yana Parking suka gaisa.

Kana ya wuce yayi ciki. kai tsaye Bedroom ya wuce ya watsa ruwa kana ya ɗaura alwala ya fito Masallaci
kasancewar ankira Maghariba bai fito ba saida akayi Isha'i kafin ya dawo yaci abinci da Habib ya kawo
masa. bayan ya kammala ya ɗauko system ɗin sa ya tura Abba duk yanda sukayi tsare-tsaren abubuwan
da kuma hotunan yanda abubuwan suka tafi sosai yayiwa Abba bayanin sannan Abba ya kara masa
haske akan sauran abubuwan sai misalin shaɗaya ya tashi yana jin wani irin kasala bini-bini zaiyi miƙa
tare da hamma kai tsaye toilet ya nufa ya watsa ruwa.

Anutse ya fito tare da kumtsaawa, kana ya kwanta akan gado tare da lumshe idanunsa tsikar jikinsa na
tashi sanyin AC da ƙamshin Roomfreshner da kuma ƙamshin tularensa shi yasake haddasa masa jin wani
masifaffen kasala cikin wani irin yanayi ya ƙudundune tamkar yaro lokaci ɗaya bacci yayi awon gaba
dashi.

A hankali yake juye-juye yana mai jin da ganin abin kamar a mafarki kamar kuma a zahiri.

Kanshi longwaɓar cikin narkekkiyar murya yace.

“Zakeeh kasheni fa”.

Cikin tsoro tace.

“Ana asped Yah Mu'allim”.

Kai a jujjuya mata tare da cewa.

“Kije keda Allah, kiyi ta dakon zunubi, kina sane dai in har ban yafe mikiba cikin fushin Allah zaki kwana”.

Da sauri ta ƙara kwaɓe fuska, tare da cewa.


“Dan Allah Yah Mu'allim kayi haƙuri ka yafe min, nayi maka al'ƙwari ina nan tafe zanzo gare cikin aminci
da rakiyar amintattu a ranar nayi al'ƙawarin gujewa fushin Ubangiji a ranar kada ka ɗaga min ƙafa ka
mallaki dukkan ƙudurinka”.

Wani irin mataccen murmushi yayi tare da cewa.

“Yaushe ne ranar?”.

Da sauri tace.

“Nan kusa take”.

Wani irin kallo yayi mata tare da cewa.

“Ranar yaushe ce”.

A hankali tace.

“Raanar larabace ce”.

Cikin wani irin kallo yace.

“Na'amin ce, tunda al'ƙawari kikayi”.

Cikin sauri ta miƙe ta nufi toilet cikin mawuyacin hali ya ɗago idanunsa dake cike da feeling kana
muryarsa na rawa yace.

“Pleaassss Hayatieee kada ki saɓa min al'ƙawarin dan idan kika saɓa min a wannan ranar”.

Girgiza kai Khausar tayi cikin kuka da raunin murya tace.

“Bazaka mutuba”.

Amatuƙar galabaici ya yunƙura da niyyar binta tayi saurin rufe kofar toilet.

Akuma dai-dai lokacin ya farka da wani irin azabebben kasala dafe kansa yayi da hannu bibbiyu yayin da
Idanunsa suka cika da ruwan hawaye haka ya kwana cikin mawuyacin hali Allah ya sani ya fara ganin
yarinyar aljana.

Washegari da sassafe ya tashi yayi wanka kana ya shirya cikin gezner fari ƙal da ya fito da ainihin
kyawunsa Anutse ya fito falon hannunsa riƙe da Breafcase a dining area ya tsaya tare da buɗe Warmers
din da Habib ya jere Wainar shinkafa ce da miyar taushe sai kuma soyayyan Arish da tea Wainar yaci
kana yasha tea bayan ya gama ya mike tare da ɗaukar Breafcase ɗinsa da wayoyinsa da kuma mukullin
motarsa kai tsaye Company ya nufa.
Gembila

Aɓangaren Abban sosai hankalinsa ya dan kwanta fahimtar lallai Moddibo yana aiki gadan-gadan bisa
tsari da hikima komai na tafiya dai-dai.

Numfashi ya fesar tare da ciro wayarsa yayi dearling number Malam Arɗo bayan ya dauka sun gaisa.

Abba ya sauƙe Ajiyar zuciya kana yace.

“Yau kusan kwana shida kenan da zuwan mu gidan Lamiɗo akan maganar Aliyu da Khausar amma har
yau bamuji ya sake neman muba amma tunda mu muke da buƙata yakama muji ta bakinsa”.

Ya gyara zamansa wayar akunnensa kana ya cigaba da cewa.

“Musamman ma da yanzu na tura Aliyu Marocco yana rayuwa shi kaɗai ya kamata ace anyi ƙoƙari anyi
batun auren nan saboda kaɗai ci da damuwa zaiyi masa yawa”.

Jinjina kai Malam Arɗo yayi cike da gamsuwa yace.

“Nima abinda nake tunani kenan amma Insha Allahu gobe zamuje da daddare idan Allah ya kaimu rai da
Lafiya”.

Ahankali Abba ya jingina bayansa da jikin kujeran kana yace.

“Toh Allah ya kaimu bisa rai da Lafiya”.

Ameen malam Arɗo ya amsa kana suka katse kiran.

*Jauro Yaya*

Hajja Nana ce zaune ta tanƙwashe ƙafafunta Baffa Garga dake gefenta yayi Murmushi yana kallonta
yace.

“Addah Nana ɗazu nayi magana da Hammadu”.

Kallonsa tayi tare da kawar da kai gefe tace.

“Ya masa kyau”.


Murmushin Baffa Garga ya faɗaɗa yana kallon yanda tayi kicin-kicin da fuska sassauta murya yayi kana
yace In gaishe ki”.

Taɓe baki tayi ba yabo ba fallasa tace.

“Idan ya damu da gaisuwar ai sai yazo inda nake”.

Gyara zama Baffa Garga yayi kana yace.

“Addah Nana ai yace ma zai zo In sha Allahu gobe da safe zaiyi sammako yazo”.

Sassauta fuskarta tayi kana tace.

“Toh Allah ya kawo shi lafiya”.

Ameen Baffa Garga ya amsa tare da ɗauko mata wani hiran.

Washe gari:Asuban fari Baffa Jimeta yayi sammako ya ɗauko hanyar Taraba duk da sammako da yayi sai
ƙarfe biyar da rabi ya isa Jauro yaya Aka shiga gaishe-gaishe da tambayar juna koda wasa bai kawowa
Hajja Nana maganar Khausar ba sai bayan sallar Isha'i bayan sun ci abinci sun zauna da mahaifiyarsa da
kuma Kawunnansa ana hira.

Ahankali ya gyara zamansa kana ya tanƙwashe ƙafafunsa agabanta ya karyar da wuyarsa cikin sanyin
murya yace.

“Hajja Nana alfarma nake nema awajenki”.

Kallon second ukun tayi masa kana tace.

“Ni kuma wace alfarma zanyi maka ai da har ina da abinda zaka nemi alfarma awajena Umarni na zaka
bi”.

Ahankali ya sassauta muryarsa yace.

“Ai yanzu ma Umarnin ki nake bi Hajja Nana Ni dai temako nema”.

Kallonsa tayi kana tace.

“Taimako akan me?”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da yin ƙasa da kansa yace.

“Taimako akan Marainiyar Allah”.

Baki ta buɗe tare da kallon ƙannenta sai kuma ta kallesa tace.


“Ai kowa ma Maraya ne sannan kowa ma zai iya kasancewa Maraya”.

Kai ya gyaɗa yana kallon yanda take jijjiga ƙafa yace.

“Eh nasani amma akan Khausar nake magana Hajja Nana nazo ne in sake Baki haƙuri akan laifin data
aikata sannan muyi mata uzuri matsayinta na yarinya ƙarama”.

Kai ta gyaɗa ba yabo ba fallasa tace.

“Shikenan komai ya wuce tunda Ni ban kaiba Ni kaka ce kun nuna min bani da matsayi sannan banida
ikon faɗa aji”.

Da sauri Baffa Jimeta ya kalleta amma baice komai ba ta cigaba da cewa.

“Acikin maganar rayuwar Khausar to ba matsala na cire hannuna ta Auri duk wanda taga dama take so
Ni bani da damuwa aciki na janye hannu na tunda haka kuke buƙata”.

Numfashi Baffa Jimeta ya fesar cikin kwantar da murya yace.

“Toh shikenan kiyi haƙuri ki sanya Albarka aciki”.

Taɓe baki tayi kana tace.

“Zansa al'barka ai tunda bazan sa tsinuwa ba Ni dai babu bakina aciki sannan babu batub aurenta da
wancan ɗan gaba da fatihan kam”.

Kai ya girgiza cikin sassauta murya yace.

“Mu dai kiyi haƙuri dan Allah kiyi haƙuri kiyi mana fatan alkhairi aciki”.

Ahankali ta kallesa kana tace.

“Toh Allah ya kyauta ya kiyaye gaba dama maganar data kawo ka kenan??”.

Cikin sauri ya girgiza mata kai kana yace.

“A'a bashi bane ya kawoni kewar ki nayi shine nace bari nazo in gaisheki”.

Hararansa tayi tare da kallon sauran ƙannenta tace.

“Oho dai”.

Akuma dai-dai lokacin Malam Arɗo,Malam Ahmad da Abba ne zaune afalon Lamiɗo bayan sun gaisa
sannan suka yimasa jawabi kan cewa sunji shiru shiru bai sake neman suba yasa suka dawo.

Anutse Lamiɗo ya gyara zama cike da dattako yace.


“Badamuwa Insha Allahu dama nima ina shirin zan ne meku ɗin saboda bani da ikon bada ita akaran
kaina amma munyi magana da Baffan yarinya yau ɗin nan ma yazo daga can Adamawa zai nemi
sahalewar kakar yarinya”.

Ajiyar zuciya suka sauƙe atare Kallonsu Lamiɗo yayi kana ya cigaba da cewa.

“Dake Itace taso kawo tangarɗa acikin al'amarin amma yace zaiji da lamarin duk abinda ake ciki yace min
Insha Allahu gobe muyi ƙoƙari muje gamu gashi gata ya zama na munje neman Auren ne”.

Numfashi Malam Ahmad yafesar kana yace.

“To ai wannan duk mai sauƙi ne badamuwa za'ayi hakan”.

Kai Abba ya gyaɗa kana tare da faɗin.

“Bakomai Insha Allah goben zamuje”.

Murmushi Lamiɗo yayi cike da kamala yace.

“Eh zamu bari gobe idan munyi sallar Azahar sai muje kafin nan ya tattauna da mahaifiyarsa idan anyi
sa'a abin zai zo da sauƙi dake shi yana da kyakkyawar fahimta sannan bashi da son zuciya”.

Jinjina kai Malam Arɗo yayi idanunsa akan Lamiɗo yace.

“Ba matsala Insha Allah nima ina da ƙafa agarinsu dan Malamin dana ke zuwa ɗaukan karatu awajensa ai
ƙanin Kakarta ce kuma sunzo wajena tare shima nasan yana da kawaici, kara da dattako”.

Jinjina kai sukayi tare da tsaida magana akan washe gari Bayan Sallar Azahar zasu tafi.

Washe gari baki ɗayansu suka shirya har Mommy da Khausar Lamiɗo yace su shirya atafi dasu Khausar
da Mommy suna motar Lamiɗo Malam Arɗo da Malam Ahmad suna motar Abba kai tsaye suka dauki
hanyar Jauro yaya suna isa Jauro yaua kai tsaye gidan Hajja Nana suka nufa dai-dai lokacin dasu Baffa
Jimeta suka fito daga sallar La'asar Malam Liman na ganin Malam Arɗo ya faɗaɗa fara'ar fuskarsa kana
yace.

“A'a Malam marhaban lale sannunku da zuwa”.

Baffa Jimeta kuwa cikin sauri ya nufi Lamiɗo tare da miƙa masa hannu yace.

“A'a Sannunku da zuwa har kuzo kenan?”.

Murmushi Lamiɗo yayi cikin yanayin dattako da kamalarsa yace.

“Eyyy sosai ma ai ba'a bori da sanyin jiki”.

Abba dake tsaye jikin mota yace.


“Aikam dai ba'a Bori da sanyin jiki”.

Baffa Garga da fitowarsa daga masallaci kenan yace.

“A masha Allah harda Alh Usman mai Dala ne a Lallai sannun ku da zuwa maraba maraba ku karaso?”.

Ya faɗa tare da shigewa gaba kasancewar yanzu shine ƙarami tun bayan rasuwar Baffa Umaru yana shiga
ciki yace.

“Addah Hajja abamu taburmai munyi baƙi”.

Miƙewa tayi daga zaune da take da murmushi afuskarta ta ɗauko taburmai ta miƙa masa karɓa yayi kana
ya shimfiɗa musu Abaranda.

Daga ciki tace.

“Aaa baƙi mukayi sannunku da zuwa sannunku”.

Tana ƙoƙarin fita Khausar da Mommy Kuma na kokarin shiga Atake fara'ar dake fuskarta ya gushe Harara
ta watsawa Khausar sai kuma ta maida kallonta kan Mommy tace.

“A Aysha kune atafe?”.

Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.

“Eh”.

Sannan suka shiga cikin dakin mazan kuma Baffa Garga ya shimfida musu taburmai daga waje.

Koma ciki Hajja Nana tayi tare da ɗaukan ƙwaryar nono da ƙorron soyayyan Zabbi da aka yiwa Baffa
Jimeta na zuwansa ta kalli Khausar dake gefen Mommy zaune haɗe fuska tayi babu walwala atare da ita
tace.

“Toh fitsararriya uwar fitsararru zoki kai musu abin taɓawa kin zauna kina zare ido sai kace wata ta Allah
rasa kunya ɓerar tanka”.

Uffan khausar bata ce mata ba ta miƙe ta ɗauki Ƙorran ta fita ta kai musu sannan ta dawo wani ƙorron
Hajja Nana ta miƙa wa Mommy kana tace.

“Aysha Bismillah”.

Kallon yanda tayi kicin-kicin da fuska Khausar tayi taɓe baki tayi cikin tsira mata ido tace.

“Hajja Nana Ni kar inci ne?”.


Harara ta watsa mata kana tace.

“Duk yanda kika ga dama kiyi”.

Ware ido Khausar tayi ta kalli Hajja Nana data kawar da kai gefe murmushi tayi cikin sanyin Murya tace.

“A'a Idan kada inci sai inbar miki kayanki”.

Baki Hajja Nana ta taɓe kana tace.

“Oho cikin ko nawa fitsararriya Mara kunya mai ido atsakar ka”.

Fuska Khausar ta ɓata ta buɗe baki da niyyar magana Mommy tayi saurin ɗaga mata hannu alamar kada
tace komai hakan yasa ta tsuke bakinta Mommy kuwa kindirmon ta ɗaga ta burga kana tasa sugar.

Daga waje Lamiɗo yace.

“Khausar fito mana ki burga mana Nonon”.

Kai Baffa Garga ya Girgiza kana yace.

“Ba matsala bari na burga muku”.

Murmushi Lamiɗo yayi kana yace.

“A'a bari dai ita ɗin tazo ta burga mana”.

Miƙewa Khausar tayi tare da ɗaukan goran zuwa ta fita ta burga musu Nonon kana ta zuba musu zumar
sannan ta miƙe ta koma ɗaki bayan sun gama taɓe taɓe an sake gaisawa Lamiɗo ya kalli Baffa Jimeta
cikin sassauta murya yace.

“Toh Alh Muhammadu Hausawa sunce maso ɗan tsun-tsu shike binsa da jifa, mun zo wajenku neman
yafiya, afuwa da kuma alfarma sannan da neman iri domin nima ina cikin ƴan neman Auren ne”.

Cikin sauri Baffa Jimeta yayi dariya kana ya girgiza kai tare da kallon Lamiɗo yace.

“Haba Lamiɗo ba zamuyi haka da kaiba ai kai mai bada Auren Khausar ne baka cikin masu neman aure
kana cikin masu bada Auren Khausar ne”.

Murmushi Lamiɗo yayi cike da jin daɗin karancinsu yace.

“Nagode da karamci”.
Gyara zama Baffa Jimeta yayi da murmushi afuskarsa yace.

“Ka cancanci fiye da hakan Lamiɗo”.

Jinjina kai Baffa Liman yayi cike da kamala yace.

“Ai mu saidai muyi addu'a da fatan alkhairi amma kaine mai bada Khausar”.

Cikin jin dadi yace.

“Nagode da kawaici Allah yasaka da alkhairi”.

Gyara zama Malam Arɗo yayi da murmushi afuskarsa yace.

“Toh mu mun yarda mun amince mune masu neman Aure”.

Abba dake Kallonsu ya faɗaɗa Murmushin fuskarsa kana yace.

“Mune masu neman aure da kuma neman iri agareku bisa cika wasiyyar da ɗana ya bari ina fatan zan
samu sauki da haɗin kanku wajen cikawa ɗana burinsa koda bayan ransa kamar yanda ya faɗa min”.

Ya ida maganar cikin rauni idanunsa na tara ƙwalla.

Ajiyar zuciya Baffa Jimeta ya sauke cike da tausayawa yace.

“Bakomai Alh Bashir Insha Allah babu abinda zai gagara aida mu daku duk mun zama ɗaya Lamiɗo yamin
bayanin duk abinda ke tafiya kan cewa wasiyya ce daga wajen danƙa marigayi Jameelu”.

Ahankali Abba ya sunkuyar da kansa hawaye na cigaba da taruwa akwarmin Idanunsa.

Cikin sanyi Baffa Jimeta ya cigaba da cewa.

“Insha Allah bazai gagara ba zamuyi ƙoƙari amma yanzu kuyi haƙuri da al'amarin tsohuwa in Allah ya
yarda babu abinda zai gagara”.

Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauke tare da gyara zamansa yace.

“Allah Ubangiji yasa haka mukam ma da gwaɓin mu muka zo duk da cewa akwai tsoro atare damu amma
muna da kyakkyawan yaƙini akanku hakan yasa kafin muzo muka taho da gishiri da goro na neman izini”.

Murmushi Malam Liman yayi yana kallon Lamiɗo yace.

“Lallai kuwa zamu barku da Hajja Nana ku fafata”.


Zare da ido Lamiɗo yayi tare da sanya dariya kana cikin sauri yace.

“Na tuba ayimin afuwa ai Hajja Nana saiku zakuji da ita”.

Gyara zama Malam Liman yayi cike da nutsuwa yace.

“Insha Allah itama munyi ƙoƙari mun samu ta ɗan sauko amma duk da haka akwai karin ɗan lokaci da
za'a bayar”.

Anutse Mommy ta gyara zamanta tare da kallon Hajja Nana cikin sanyin murya tace.

“Dan Allah Hajja Nana kiyi haƙuri abinda ya kawo mu nazo ne in baki haƙuri naga kin tafi ranki aɓace
abinda Khausar ta aikata ba laifi na bane ba kuma da yawuna bane”.

Ta ida maganar Muryanta na rawa tamkar zata fashe da kuka.

Hajja Nana kuwa jin yanda Muryan Mommy ke rawa yasa tayi saurin Kallonta har ranta take Jin Mommy
domin alokacin zamansu tasan bata da matsala cike da kulawa tace.

“Kar kiyi kuka Aysha aina zauna dake nasan halinki fitsaran Khausar ba daga gareki bane kuma ba daga
Allah bane halitta ce da tayiwa kanta”.

Cikin sauri Khausar ta ɗago kanta ta watsa mata Harara cikin ƙasa da murya tace.

“Inma tsiwarce ai awajenki na gada”.

Harara Mommy ta watsa mata hakan yasa ta tsuke bakinta.

Ahankali Mommy ta sauƙe Ajiyar zuciya kana ta fuskanci Hajja Nana cikin sassauta murya tace.

“Itama kanta Khausar al'amarin yazo mata adolene”.

Baki Hajja Nana ta taɓe kana tace.

“Bangane yazo mata adole ba inace soyayya take da wani can yasa ta kalli tsabar idona tace bata son
ɗan Uwanta”.

Kai Mommy ta Girgiza kana ta kwashe duk yanda Khausar ta faɗa mata sunyi da M Jameel aranan da aka
sace sa kana ta daura da faɗin.

“Sannan kuma yaron shine ƴan Kidnapping suka sace sa suka ɗauresa har ya rasu”.

Ahankali Khausar tayi ƙasa da kanta hawaye na taruwa akwarmin Idanunta.

Cikin sanyi Mommy ta cigaba da cewa.


“Sai maganar tasa ta zama kamar wasiyya kuma ya roƙi alfarma ya faɗawa kakar Amininsa Moddibo
kana Ya faɗawa mahaifiyarsa da mahaifinsa yanzu ma haka da mahaifinsa muka zo kuma yace alfarma
yake nema ko bayan ransa acika masa wannan burin nasa, jin haka yasa nima baki ɗaya jikina yayi
sanyi”.

Numfashi Hajja Nana ta fesar kana tayi ƙasa da kanta cikin sanyin murya tace.

“Allah sarki shine akace ansace sa a daure sa ya rasu ko?”.

Asanyaye Mommy ta gyaɗa mata kai tare da faɗin.

“Eh shine aka sace aka ɗaure har ya rasu”.

Jinjina kai Hajja Nana tayi tare da watsawa Khausar Harara ta kalli Mommy cikin raunin murya tace.

“Ayyah Allah sarki Allah yajiƙan sa da rahma ina ma ace yana raye dashi zan bawa Khausar ya aura
wallahi koda Khausar bata auri Aliyu ba bazan damu ba”.

Cikin raunin murya Mommy tace.

“Gashi kuma shi ɗin Ubangiji bai nufa za ayi dashi ba, babu gatan da zamuyi masa sai dai addu'a”.

Jinjina kai Hajja Nana tayi cikin sanyi tace.

“Sosai ma”.

Mommy kuwa sassauta murya tayi kana tayi ƙasa da kanta tace.

“Kuma inda hali mu samu mu cika masa wasiyyar daya bari”.

Gyara zama Hajja Nana tayi tare da kallon Khausar da kanta ke ƙasa kana ta kalli Mommy nunfashi ta
fesar cikin sanyin murya tace.

“To aini bani da tacewa acikin wannan maganar sai abinda iyayenta suka faɗa tunda annuna min bani da
iko da ita”.

Dai-dai lokacin Baffa Jimeta ya shigo Anutse ya zauna gefenta ya tanƙwashe ƙafafunsa kana ya
fuskanceta da kyau yace.

“Kina da iko da ita mana muma kam mu aike kike da iko damu amma ana neman alfarma awajenki gacan
Baban yaron ma awaje sai hawaye yake zubarwa yana neman alfarma acikawa dansa wasiyyar sa”.

Daga waje ta jiyo sheshsheƙan Kukan Abba cikin sauri ta miƙe ta nufi ƙofa ta fita kusa dashi ta zauna cike
da tausayawa tace.

“Kuka kuma kake Alh Bashir?”.


Cikin sheshsheƙa Abba yace.

“Ya za ayi ba zanyi kuka ba burin da Jameeluna da kuma fatan da yake so yana tangarɗa koda aranan da
muka rabu na ƙarshe yace min shine babban burinsa daya rage aduniya”.

Cikin zubda hawaye ya cigaba da cewa.

“Yace babban burinsa yaga Moddibo yayi Aure kafin nasa Saboda Aliyu yana buƙatar mace yana buƙatar
ayi masa Aure sai dai Allah bai nufa Jameelu na zai gani ba ina tsoro saboda bani da damar da zan cika
masa wasiyarsa”.

Gyara zama Hajja Nana tayi kana ta gyara ɗaurin dankwalinta ta sunkuyar da kanta ƙasa kana ahankali ta
ɗago Muryanta na rawa tace.

“Na amince ina dai dan nice. To acikawa yaron nan burinsa Allah yajiƙan sa da rahama na amince Ayi
aure...

Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama 1k ne kacal 0661110170
GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N 09097853276.

By

*GARKUWAR FULANI*

SAKAYYAH

40

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwatanta Zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki
dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection
cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin
kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin
kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana
dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya
musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki
aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa
ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga
account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min
mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi
Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari
da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan
Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR
MA'AURATA.

40

*Book 2*

*6*

Shiru Hajja Nana tayi kafin ahankali ta ɗago ta kallesu ɗaya bayan ɗaya tace.

“Shikenan ni babu abinda zance acikin wannan al'amari zira ido da kunne nawa duk abinda yaje ya dawo
Khausar ita tajawa kanta”.
Ƙwaffa tayi kana ta cigaba da cewa.

“Tunda kuma iyayenta kuce kun amince, to ni dai babu abinda zance bare inyi baƙin jini”.

Kallon Baffa Jimeta daya sunkuyar da kai ƙasa tayi taɓe baki tayi kana tace.

“Yo ni me zai da meni tunda uban daya haifi Aliyu bai damuba yanuna ayi mata yanda take so ai
shikenan, tunda bata illar tsintacciyar mage bata mage ba, ɗan da ba'asan Asalinsa ba ba'a san tushensa
ba duk abinda ya faru ita tajawa kanta”.

Anutse Lamiɗo ya ɗago kansa ya kalli Hajja Nana cikin sauri yace.

“Insha Allahu ma babu abinda zai faru sai Al'khairi”.

Abba kuwa karɓan maganar yayi ta hanyar cewa.

“Insha Allah Moddibo zai riƙe ta da amana da gaskiya da Izinin Ubangiji Khausar ba zata tozarta ba yanda
Khausar ta amince tayi niyyar cikawa Jameelu na wasiyyar sa”.

Ahankali Khausar dake can cikin ɗaki ta lumshe Idanunta zuciyarta na bugawa da Masifaffen ƙarfi.

Cikin sanyin murya Abba ya cigaba da cewa.

“Insha Allahu Ubangiji bazai tozarta taba Allah zai cika mata burikanta na rayuwa insha Allah zata
kasance cikin kwanciyar hankali da nutsuwa”.

Kallonsa Hajja Nana tayi kana ta jinjina kai tace.

“Haka kake gani kk? Hmm ta yaro kyau take bata ƙarko, kai yanzu Alh Bashir tunda kuke kasan asalin
yaron ne?”.

Ahankali Abba ya sunkuyar da kansa ƙasa batare da yace Uffan ba.

Ƙwaffa tayi kana tace.

“Hmm ka buɗe baki kai tsaye kace baka sani ba shine magana”.

Kallonta ta mayar kan Malam Arɗo tace.

“Malam kai da suke aiki a ƙarƙashin ka kasan Asalinsa?, kasan waye Ubansa? Kasan inane Ƙasar da suka
fito kasan inane Jaharsu? kasan menene tushensa? Waye ubansa waye Uwarsa?”.

Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe kana ya kalleta Anutse yace.

“Ai a al'amarin Aure wannan duka ba magana bane”.


Kai ta girgiza cikin tsira masa ido tace.

“Yanzu ina magana da Malam Liman zai miƙe yace min Allah yace Annabi yace amma ai Aure abin
bincike ne ko”.

Cikin sanyin murya Lamiɗo yace.

“Dan Allah Addah Nana kiyi haƙuri wannan tone-tonen basu da Amfani”.

Baki ta taɓe tare da Kallonsa kana tace.

“Eh basu da amfani Ni tunda dai aka samu antsira ba ɗan Mayun bane zata aura, aishikenan sai inzira
mata ido ni naɗan ji sauƙi ma akan abin”.

Kallon ƙannenta tayi kana tace.

“Yo ai gaskiya ne na fada da kuka wani tsareni da ido, kuma dole idan gaskiya ta taso a faɗeta da ace ta
auri ɗan mayu jikan Mayu ai gwara ɗan shegen tunda taji ta gani tana so ta bone dai tayiwa ƴaƴanta da
ahalinta”.

Kai Baffa Liman ya girgiza tare da sunkuyar da kansa ƙasa cike da takaici Hajja Nana ta cigaba da cewa.

“Tunda ta yiwa kanta tabo ita tasani amma Ni dai babu ba kina babu hannu na babu ƙafana na suje can
su ƙarata sanda ƴaƴanta zasu ce ina dangin Ubansu ta nemi abin faɗa musu”.

Ahankali Mommy da Lamiɗo suka sunkuyar da kansu ƙasa Khausar kuwa hannunta riƙe da kofin
madaran da bata shaba bata ajiye ba ɗumin na ratsa tafin hannunta ta tsirawa waje ɗaya ido ba ƙeftawa.

Ajiyar zuciya Malam Liman ya sauƙe tare da girgiza kai kana cike da ladabi da nutsuwa yace.

“Dan Allah Addah Nana ya za'ayi ana kitse gaba kina warware baya dan Allah wasu furucin ki riƙa sanin
abinda zaki riƙa faɗa saboda Manzon Allah (SAW)

_Falyaƙun Khairan Auliyastumu”_.

Baki ta taɓe kana tace.

“Naji naji Liman aini zuwa yanzu ko ƙwaƙwalwar kifi ne dani yaci ace in haddace Hadisai sama da dubu
tunda duk motsin da nayi sai kace min ga abinda Allah da Manzonsa suka faɗa”.

Sunkuyar da kai Malam Liman yayi cikin taɓe baki ta cigaba da cewa.

“Ni dai na faɗa ba bakina ba hannu na babu ƙafana kuje duk abinda kuka ga ya dace kuyi. Kai kuma”.
Ta nuna Baffa Jimeta da kansa ke ƙasa kana tace.

“Tunda kaine madadin Uba agareta kace kaji ka gani ko? Sannan kaima”. Ta nuna Lamiɗo daya ɗago
kansa cikin haɗe girar sama da na kasa tace.

“Kai kuma kaine wakili kuma Uba data tashi agabansa kai kace kaji ka gani ai shikenan na cire bakina
aciki amma dan Usmanu na baya raye bazan bari jinjinsa ya cuta ba”.

Ajiyar zuciya Baffa Jimeta ya sauke kana yace.

“Insha Allahu ma ba zata cutuba da izinin Ubangiji zai riƙe ta da Amana”.

Baki ta taɓe cike da takaici ta juya cikin ɗaki.

Takalli Khausar da har zuwa lokacin hannunta ke riƙe da kofin madaran Harara ta watsa mata kana tace.

“Ke kam kinyi asara gaki mace har Mace Bafulatana tsayayyar mace Kyakkyawa zubin zamani ƙirar masu
tsada amma ace wai ke zaki buɗe baki kice kina son Namiji”.

Cikin sauri Khausar ta ɗago kai ta kalleta.

Harara Hajja Nana ta watsa mata kana tace.

“Ki ɗauke wannan tsayayyun idanun naki akaina Ke zakice kina sonsa wanda baisan dake bama sannan
baice yana sonki ba bai damu dake ba wai kice kina sonsa shi zaki Aura”.

Fuska Khausar ta ɓata kana ta kawar da kanta gefe tare da murguɗa mata baki da Ido Mommy tayi mata
alamar kar tayi magana.

Tsuke bakinta tayi tare da kawar da kanta gefe, jin lokacin sallar La'asar yayi yasa duk mazan suka miƙe
suka tafi masallaci.

Bayan sun daeone suna isa afarfajiyar gida suka zauna Anutse Abba ya gyara zamansa tare da fuskantar
su da kyau kana yace.

“Toh Alhamdulillah yanzu dai Kamar mun samawa tufkar hanci amma kuma dai Babban abu da yake tafe
damu acikin al'amarin”.

Ya sauke ajiyar zuciya kana ya cigaba da cewa.

“Ayi ƙoƙari ayi abin cikin ƙanƙanin lokaci in Allah ya yarda ya lamunce mana komai abune mai sauƙi
agaremu inhar kuma kun shirya”.

Jinjina kai Baffa Jimeta yayi kana yace.


“Bakomai in dai wannan ne mu ba matsala awajenmu tunda abin yazo na wasiyya kuma dama a
wasiyyar sa ya roƙa ayi cikin gaggawa sannan ya faɗa ya kara cewa yaron nan yana ɓuƙatar aure”.

Jinjina kai Abba da Malam Arɗo sukayi alokaci ɗaya.

Cike da kamala Baffa Jimeta ya cigaba da cewa.

“Tunda har ya fadi haka to yakamata ayi ƙoƙari ayi abinda ya kamata ni awajena Insha Allah ba matsala
tunda dama zan kwana biyu saboda zan samu inji da tsohuwar kasan fatanmu da Adduarmu Allah yasa
mu rabu dasu lafiya”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace.

“Hakane ƙwarai fatanmu da addu'ar mu rabasu da lafiya domin shi yafi al'khairi”.

Murmushi Baffa Jimeta yayi kana yace.

“Toh shine nake so in Zauna da ita Ni nan awajena duk abinda ake buƙata wanda uba zaiyiwa ɗiyarsa
Insha Allah bazai gagara ba komai Ashirye muke Insha Allah”.

Cikin sauri Lamiɗo ya Girgiza kai kana yace.

“A'a Alh Muhammadu ai wannan hurumi nane don Allah dan Annabi kada kuyi min haka Khausar ɗiyace
awajena tun tana wata uku nake tare da ita bata da bambanci da ɗiyan cikina inaji tamkar Ni na haifeta”.

Kallonsa Baffa Jimeta yayi cike da kamala yace.

“Anya Lamiɗo za ayi haka kuwa abar maka ɗawainiya?”.

Kai Lamiɗo ya Girgiza cike da dattako yace.

“Haba dai wace irin ɗawainiya kuma?,Meye aciki ai babu wani ɗawainiya acikin al'amarin nan”.

Numfashi Abba ya fesar kana ya fuskance su da kyau yace.

“Ni duka wannan aikin ma na ɓangaren Khausar da Moddibo zanso abarmin domin burin Jameeluna ne
ni kungama yimin komai da kuka lamince zaku wanzar da wasiyyar sa bayan rayuwarsa”.

Jinjina kai sukayi kana ya cigaba da cewa.

“kungama yimin komai babu abinda zan iya yi muku tukuici dashi sai dai kubarni inyi dukkan abinda ya
dace na fannin Auren nan”.

Murmushi Malam Arɗo yayi kana yace.


“Masha Allah wannan Auren yazo da al'barka Ubangiji Allah yasanya al'khairi”.

Zama Malam Liman ya gyara tare da faɗin.

“Muma kanmu duk al'amarin Khausar hakkinmu ne mu sauƙe”.

Cikin sanyin murya Abba ya kallesu kana yace.

“Ni dai dan Allah na nemi alfarma abarmin wannan aikin nayi”.

Ajiyar zuciya Baffa Jimeta ya sauƙe kana yace.

“To ai ba laifi duk zamuyi buƙatun ƴa mace suna da yawa”.

Jinjina kai Lamiɗo yayi kana yace.

“Ni dai nafi so abarmin komai na fannin Khausar”.

Dariya Malam Arɗo yayi idanunsa akan su yace.

“Lallai dai kam wannan ai sai dai ɗakuna uku za aware mata irin wannan lissafin.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“Insha Allah wannan duk bazai gagara ba da ɗakuna da kuma duk abinda za'a buƙata zanyi”.

Numfashi Baffa Jimeta ya fesar kana yace.

“Allah ya temaka nima insha Allah nan da mako ɗaya zan koma”.

Jinjina kai Abba yayi kana ya gyara zamansa cike da farin ciki yace.

“Ai shi kansa Aliyu ma yanzu haka yana can ƙasar Marocco yana kulamin da ayyukan Company na to
Auren ma bazata muke son yi masa”.

Murmushi sukayi jin sigar da Abba yayi magana Cike da farin ciki Abba ya cigaba da cewa.

“Idan yaso bayan an ɗaura auren da kaina zan Kai masa matarsa da izinin Ubangiji sai dai yaga mata dan
yanzu ya tafi yana rayuwa shi kaɗai wasu sabbin damuwa zai sake sawa ranshi”.

Cikin sauƙe numfashi Malam Arɗo yace.

“Toh Alhamdulillah gamu da gishiri da goro na tambayar mu na forko muka zo,".


Sai kuma duk suka juyo suka kalli Malam Liman sayi gyaran murya tare fuskantarsu da kyau cikin kamala
da dottaku yace.

“Tunda ga yanayin yadda abin ya kasance, mu shammaci Adda Nana, domin bata da alƙibila yanzu tace
ta yarda zuwa anjima zata iya cewa ta fasa, don haka mu ɗaura auren nan yanzu-yanzu ana da goron da
kuka kawo in dai akwai sadaki a hannunsu tunda ga waliyan yaro ga kuma nata waliyan”.

Ya ƙare mgnar tare da yin ƙasa da murya gudun kada Hajja Nana taji mgnar.

Cikin tsanananin mamaki da farin ciki mara misaltawa Abba Jameel yasa hannunshi cikin aljihunsa jiki na
rawa ya zaro sabbin kuɗin yar dubu dubu wanda ya dauko dan yin hisani. Bandir ɗaya ya ajiye a
tsakiyarsu wanda har jikinsa na rawa dan farin ciki yace.

“Gashi ina nemawa Aliyu Youseep Muhammad Mouley auren Khausar bisa sadaki dubu ɗari”.

Da sauri Bappa Jimeta ya gyara zamanshi tare da cewa.

“Na bawa Aliyu Youseep Muhammad Mouley auren ƴata Fatima Usman Abubakar Leewal bisa sadaki
dubu ɗari.”

Cikin tsananin jin daɗin wannan al'amari da yazo musu da sauƙin aka ɗauka Auren Khausar da Modibbo
a yau Litinin a cikin rugar Jauro yaya bisa shaidu Lamiɗo, Malam Arɗo, Malam Liman, da sauran ƙananan
Hajja Nana baki ɗaya.

Bayan sun gama gudanar da ɗaurin auren kamar yadda shari'ar Muslunci ta tsara.

Cike da gamsuwa haɗin da tsananin jin daɗin ɗaurin auren Baffa Jimeta yace.

“Toh ba matsala Insha Allah duk abinda ake ciki zan gayawa Hajja Nana kuma zan taushi zuciyarta”.

Sai kuma duk suka juyo suka kalli Hajja Nana dake fitowa daga cikin rumfarta tana mai cewa.

“Uhmmm ta yara kyau take bata ƙarko, ai duk abinda kuke cewa dayi ina jinku badai kun ɗaya aurenba,
toh ai hikenan maji magani”.

Cikin Sauri suka kuma kalli juna, ayi mace kunne kamar na maciji duk ƙantar sauti sai taji.

Sai kuma suka maida kallonsu kam Malam Liman dake cewa.

“Toh kisanya albarka kawai”.

Kai ta gyaɗa cike da takaici tace.

“Hmmm Allah ya sanya al'khairi Allah yasa yadda muka ɗauki mgnar marigayi da mahimmanci shima
Modibbo a ɗauki mgnar da gsky”.

Bata jira cewarsu ba kuma ta juya cikin ɗakin,


Ida ta zubawa Khausar da tun lokacin da taji Hajja Nana nacewa badai kun ɗaura aurenba ta daskare a
zaune, yayinda Mommy mgnar ta daki zuciyarta, dan batayi zaton abin da gaggawa haka ba. Sai kuma
duk suka kalli Hajja Nana dake cewa.

“Wlh kinyi asarar ƙuruciyarki da kyanki ji yadda aka ɗaura aurenki kamar na bazawara mara gata”.

Zuwa yanzu Khausar kam bazata iya fahimtar kalaman Hajja Nana ba bare ta bata amsa. Ita kanta
Mommy abin ya sata tafiya dogon nazari.

A can waje kuma

Anutse Lamiɗo ya gyara zama kana yace.

“Toh Alhamdulillah dama kwanan ake batun auren Amina nanda kwana goma, tunda an auren Khausar
za'a haɗa bikin ayishi lokaci ɗaya, kana akai ko wacce gidan mijinta”.

Kusan a tare duk sukace.

“Allah ya kaimu lokacin”.

Amin Ya amsa tare daci gaba da cewa.

“Insha Allah zuwa gobe ko jibi Insha Allah zan dawo in muyi magana mahaifiyar yarinya”.

Nan dai suka gaba da tsastsara duk yadda abin zai kasance.

Sai Misalin ƙarfe biyar suka bar Jauro yaya ahanya sukayi sallar maghariba sai gab Isha'i suka isa gida.

Kasancewar ranan girkin Hajiya Bunayya ne yasa kai tsaye Mommy ta wuce Sashen ta tare da Khausar
wacce take tafiya tamkar kazar da ƙwai ya fashewa, domin jin kanta take tamkar wacce aka rufe da
ɗanyen fatan rago, wasu abubuwa na musamman ne ke yawo a jiki da zuciyarta ita kanta ta rasa yanayin
da take ciki, kawai dai ta tsinci kanta da rayuwa da Modibbo a cikin zuciyata tun lokacin da taji wai an
ɗaura aurensu.

Suna shiga kai tsaye ɗalibta ta wuce, duk da tsalle da Raudat keyi na ganinta ta gaza yi mata mgn.

Sai Mommy ce data ruggume Raudat ɗin.

Ita kuwa Khausar a hankali ta faɗa bisa gafonta, tare da rumtse idanunta da karfi.
Sai kuma ta buɗesu ganin fuskar Modibbo a ranar da sukayi robuwar ƙarshe jujjuya idonta tayi kamar
yadda tayi mishi a lokacin, sai kuma ta lumshesu jin wasu tafasassun hawaye dake kwaranyo mata ba
ƙaƙƙautawa.

Kamar a Film haka yanayin da suke rayuwa dashi a makaranta ya fara dawo mata, one by one, har zuwa
ranar da suka kasance a mota, haka nan taji wani murmushin da batasan manufarsaba ya kumce mata,
wanda kuma ya korowa hawayen da bata san ya kubce mata da kukaba.

Sai kuma ta saki sassayyan kuka jin Mommy ta zauna kusa da ita tana mai cewa.

“Toh kuma kukan me kikeyi Fatima”.

Ta ƙare mgnar da kiran asalin sunanta wanda bata cika kiranta da shiba.

Ita kuwa Khausar cikin ci gaba da sassayan kukan tace.

“Mommy kinaji fa wai sun ɗaura auren”.

Jawota jikinta Mommy da hawaye zubomata tayi tare da ɗaura kanta bisa cinyarta tana mai danne
kukanta tace.

“Ba komai Mamana kiyi shiru, ai ba yau za'a tafi da keba ki share hawayenki, addu'arta bazata bari ki
muzantaba a gidan aurenki”.

Ta ƙare mgnar tana share mata hawaye, daga nan taci gaba tausarta da kwantar mata da hankali dan ta
lura gaba ɗaya ta ɗimauce abin ya daki zuciyarta ya kauda nitsuwarta.

Washegari Da safe Kai tsaye Bedroom din Mommy Lamiɗo ya shiga tare da yi mata bayanin duk yanda
sukayi a Jauro yaya bayan sun dawo Sallar La'asar da batun auren da suka dauran.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe cikin sanyi ta ɗago kai tare da kallon Lamiɗo kana tace.

“Toh yanzu har an ɗaura Auren kuma ba jan lokacin asan yaron yana sonta, sannan kuma ace za ayi
bikin cikin ƙankanin lokaci haka?”.

Ta ƙare mgnar cije da rauni.

Jinjina kai Abba yayi yana kallon yanayinta yace.

“Toh me za ajira Aysha ai abune na wasiyya kuma akwai damar yi sannan Already Khausar ta gama
Secondary kawai tayi Aurenta tunda Alh Bashir yace a Marocco zasu zauna kinga shida kanshi yace zai
kaita wurin mijinta”.

Kallonsa kawai Mommy keyi sabida tama rasa abincewa.

Ahankali Abba ya cigaba da cewa.


“Saboda ya lura yaron bayan son zaman nan sannan yana so yabar masa ragamar Company ahannunsa
kinga idan sunje can sai ta cigaba da karatunta acan tunda dama yanayin makarantar su akwai cikekkiyar
larabci kinga zata iya karatu a can, ta kuma yi zaman aurenta cikin aminci”.

Sunkuyar da kai Mommy tayi tana wasa da yatsun hannunta yayinda tausayin yarta yasa hawaye cika
mata idanu A hankali tace.

“Kuma ba wanda ta sani a canfa, ya zatayi”.

Abba ya cigaba da cewa.

“Kada ki damu, ɗan naji Abban Jameel yace in Malam Ahmad ya yarda da rakiyar Ummin Jameel da
Asma'u zasuje, ga kuma Hajia Bunayyah itama zan biya mata su kaita tare”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe kana tace.

“Hmmm abin ne naga kamar anyi sa da gaggawa Khausar fa yarinya ce, wlh tsoron yaronan ne fal
zuciyarta jiya kwana tayi batayi bacciba”.

Murmushi Lamiɗo yayi tare da riƙe tafin hannunta acikin nasa yace.

“A ba wani yarinta aciki ai Insha Allah komai zai tafi dai-dai zakiyi alfari da Aurenta da Moddibo ke
lokacin da aka aurar dake ai bakima kaita shekaruba, mijinta kuma bar tunanin tana tsoronshi a a bata
sonshi ke dai ku zuba ido zakusha mamakin yadda al'amarin zai kance in dai Khausar ta ɗauke ki ai kiyi
shiru kawai yaro zayi mubaya'a”.

Ya ƙare mgnar da cikin sigar wasa da son kwantar mata da hankali.

Kai ta gyaɗa kana cikin sanyi tace.

“Allah yasa”.

Amin yace tare da miƙewa ya fita.

Acan ɓangaren Ummi kuwa bayan Sallar Azahar bayan Malam Ahmad ya dawo daga gidan Abba ya
zayyanewa Ummi duk yanda Abba ya faɗa masa.

Ajiyar zuciya mai nauyi Ummi ta sauƙe tare da fesar da numfashi cikin tsananin jin daɗin kana tace.

“Alhamdulillah yau dai burin Jameeluna ya cika sannan wasiyyar daya bari ta kasance kai baki daɗin
wannan al'amarin”.

Jinjina kai Malam Ahmad yayi cike da farin ciki yace.

“insha Allah”.
Numfashi Ummi ta fesar kana tace.

“Toh Allah ya tabbatar mana da alkhairi ya kaimu lokacin tafiyar, shiru zanyi bazan gayawa Asma'u ba
tukun sai naga yadda Khausar ɗin ta nufeta da mgnar”.

Ameen ya amsa kana ya fice.

Ahankali Asma'u ta fito daga Bedroom tare da kallon Ummi kana tace.

“Ummi wai maganar me naji kuna yi kamar batun Aure?”.

Kai Ummi ta jinjina da alamun farin ciki afuskarta tace.

“Hmmm”. Sai kuma tayi shiru, ita kuwa Asma'u cikin son tabbatar da abinda kunnuwanta suka jiyemata
cike da kaɗuwa tace.

“Dan Allah Ummi ki gaya min na tuba”.

Cikin tsanananin jin dadin ɗaya kasa biya a saman fuskarta tace.

“Eh maganar Auren Moddibo mukeyi”.

Zare ido Asma'u tayi kana tace.

“Ummi Yaya Moddibo zaiyi Aurene?”.

Jinjina kai Ummi tayi tana kallonta tace.

“Eh yanayi Aure dai”.

Murmushi Asma'u tayi cike da farin ciki tace.

“Ummi Wacece matar?”.

Ummi na murmushi tace.

“Aminiyar kice matar”.

Asma'u kuwa cike da matsanancin mamaki da al'ajabi ta zare Idanunta waje kana tace.

“Khausar!?”.

Kai Ummi ta jinjina tare da faɗin.

“Tabbas kuwa da izinin Ubangiji Itace”.

Tafa hannu tayi tare da buga still da Mamaki da kuma al'ajabi tace.
_“Lahailah ha Illallahu Muhammad Rasulullahi (S.A.W)”_ Yah Moddibo da Khausar.

Kallon yanda ta zare ido da sallami Ummi tayi kana tace.

“Haƙƙun kuwa dan tuni an ɗaurama”.

Dafe kunci Asma'u tayi da matsanancin mamaki gani da kaɗuwa ɗoki da bai sake taba tace.

“Dan Allah Ummi yaushe aka fara wannan maganar?”.

Hannunta Ummi ta riƙe tare da zaunar da ita agefenta yace.

“Ki nutsu mana Asma'u me wannan kamar wanda akace an haɗa Auren mutum da Dodo!?”.

Sake baki Asma'u tayi cikin Mamaki tace.

“Tabb Ummi ai kusan Auren Dodo da mutum za ayi dan wallahi Khausar matsayin Dodo take kallon Yah
Moddibo”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauke kana tace.

“Aikuwa da saninta”.

Zare ido Asma'u tayi tamkar zasu zubo tace.

“Ummi Khausar ɗin ta sani?”.

Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.

“Eh”.

Dafe ƙirji Asma'u tayi Idanunta akan Ummi tace.

“Shine kuma bata faɗa min ba iyeee Kam bala'i bari Inje in sameta”.

Ta Ida maganar tare da miƙewa.

Cikin sauri Ummi ta riko tsintsiyar hannunta tace.

“Zauna ai zuwa ta ƙarshe naji tana cewa tazo kuyi wata magana kuma ta samu kuna aiki sannan fitowar
ku kenan taga Moddibo yazo kinga ai jikinta na rawa ta fita”.

Jinjina kai Asma'u tayi still Hannunta na cikin na Ummi tace.

“Eh dan na kirata awaya ma nace ta faɗa min shine tace idan inaso Inje gidansu inji labari ashe dama
wannan ne maganar amma Ummi tasan maganar kuma ta yarda?”.
Cikin sanyi Ummi tace.

“Eh ta sani ta yarda kuma ta amince”.

Dafe kunci Asma'u tayi kana tace.

“To amma Ummi garin ya akayi haka?”.

Kallonta Ummi tayi tare da gyara zamanta kana ta sauƙe numfashi cikin sanyi tace.

“Wasiyyar Yayanki zata cika?”.

Cikin sauri Asma'u ta kalleta fuskarta ɗauke da mamaki tace.

“Wasiyya kuma Ummi ya bar mata?”.

Jinjina kai Ummi tayi tare da fesar da numfashi kana ta jingina bayanta da jikin kushin ɗin tace.

“Idan baki manta ba Ranan da yazo gidan nan na ƙarshe itama Khausar tazo sannan tare suka tafi”.

Cikin sauri Asma'u ta jinjina kanta kana tace.

“Ƙwarai kuwa Mommy na tuna aishine tace suna tafiya taga wata mota na binsu”.

Kai Mommy ta Jinjina kana tace.

“To awannan ranan ne ya bar mata wasiyar. Mommy ta ke sanar min yanda suka yi”.

Jinjina kai Asma'u tayi cike da tausayawa Aminiyar tasan yanda Khausar ke masifar tsoron Moddibo
tabbas ta ɗauki al'ƙawari mai girma cikin sanyin murya tace.

“Allah sarki Khausar!, Allah sarki Aminiya!!, Ubangiji Allah yabar ƙauna Allah yabar ƙauna tsakaninta da
Yah Moddibo”.

Sai kuma ta kalli Ummi da fuskarta ke ɗauke da murmushi tace.

“Ummi inshirya inje”.

Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.

“Kije mana Asma'u wa zai hana ki zuwa wajen Aminiyarki”.

Cikin sauri Asma'u ta miƙe tashiga Bedroom ta sanya hijabinta kana ta fito tayiwa Ummi Sallama.

Aɓangaren Hajiya Lami kuwa miƙewa tayi daga Bedroom ɗinta ta nufi ɗakin Samira zaune ta sameta
Idanunta sun kaɗa sunyi jawur tamkar garwashi alamar tasha kuka sosai cikin sauri ta ƙarasa kana ta
zauna gefenta cike da kulawa tace.
“Samira wai lafiya yau baki fito ba meya faru?”.

Ahankali ta ɗago kanta Idanunta da suka sauya launi ta kalleta Muryanta na rawa tace.

“Mommy ni baƙi ɗaya wari nake ji idan na tambaye ki kinajin wani sai kice min bakya ji Mommy kullum
warin nan ƙaruwa yake ya zanyi da raina”.

Cike da tausayawa Hajiya Lami ta janyota jikinta cikin sanyin murya tace.

“Haba Samira ki kwantar da hankalin ki mana idan ya dawo sai mu sake komawa wajensa”.

Cikin raunin murya tace.

“Mommy wani irin in ya dawo zaku koma wajensa ni dai ina ganin mutumin nan ya lalata min rayuwa ne
yanzu ayanda nake warin nan ko maigadin gidansu Modibbo ma zai yarda ya aurenki ne bare Modibbo
da ɗan karen tsabta”.

Sai kuma sharce hawaye masu masifar zafi kana tace.

“Yanzu Mommy wani namiji ne zai kalleni bare yace yana sona! ga ruwa mai wari da ƙarni yana ta bina
ko yaushe ina tare da ƙunzugu kamar mai jego”

Cikin sanyi Hajiya Lami tace.

“Bakomai Samira kasa ki damu Insha Allah yana dawowa zamu koma wajensa”.

Cikin muryan kuka da tashin hankali tace.

“Mommy Ni dai ina ji ajikina wannan al'amari ya zama min bala'i arayuwata na saɓi Ubangiji gashi ya
kamani tun ba aje ko ina ba Wayyo Allah! Kaico na! Ni Samira”.

Asanyaye Hajiya Lami tace.

“Haba Samira kar ki karyar min da zuciyata mana Insha Allah burinki zai ciki”.

Kai ta girgiza kana tace.

“Mommy ni kam hankalina bai kwanta ba burina inga na samu lafiya wannan ruwan ya daina zuba shine
kwanciyar hankalina”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da dafa shoulder ta tace.

“Kada ki damu Insha Allah Samira Zaki samu sauƙi”.

Jinjina kai tayi kana tace.

“Allah yasa Mommy Ina fatan hakan Allah na tuba Allah kayafemin Allah kaji ƙaina ka gafarta min”.
Acan ɓangaren Lamiɗo kuwa bayan ya fita ɗakin Mommy Kai tsaye sashen Gimbiya Dadu yashiga
bakinsa ɗauke da sallama zaune ya ganta da ƙanwarta Hajiya Kubra.

Anutse ya ƙarasa tare da zama kana da murmushi afuskarsa yace.

“A Yafendo Kubra kin zo ne?”.

Kai ta gyaɗa tace.

“Eh Lamiɗo kana gida kenan?”.

Kai jinjina kana suka gaisa bayan sun gaisa Hajiya Kubra ta gyara zamanta tare da kallon sa tace.

“Toh yau dai kam nazo da aiken Ƙaninka duk da yace min iyayenshi maza sunzo”.

“Wanne ƙarin nawa”. Yayi tambayar a bauɗo domin babu wanda ya taɓa mishi mgnar.

Shi kanshi mahaifin Naseru cewa yayi yaji suna mgnar ne bakwai sun gaya mishi bane, to kuma shima sai
abin ya kwanta mishi musamman da yasan Nasiru na biye-biyen mata shiyasa ya nemi alfarma a bashi
Amina kuma ayi auren cikin gaggawa.

Murmushi tayi tare da Kallonsa tace.

“Naseeru mana”.

Kai ya jinjina kana yace.

“Ikon Allah Naseeru kuma ko ɗazun ma muna tare kuma bai faɗa min ba shine sai ya aiko ki? ai da kin
kirani ma zanzo har gida in sameki”.

Kai ta girgiza kana ta kalli Gimbiya Dadu sai kuma ta kalli Lamiɗo tace.

“A'a ai aiken ne dole muzo da kan mu tunda iri muke nema”.

Jim yayi kana yace.

“Ikon Allah wani kalar iri kenan?”.

Ƴar dariya tayi ta gyara zamanta kana tace.

“Iyeee al'amarin ne ya sauya sheƙa”.


Gyara zama Gimbiya Dadu tayi kana tace.

“Eh aihakama shi yafi alkhairi Hausawa sunce naka sai naka daɗin zama sai bare gwara dai kome za ayi
ace na kane” .

Ido kawai Lamiɗo ya zuba musu cikin rashin fahimta ko kaɗan bai taɓa fuskantar alaƙar dake tsakanin
Amina da Naseer.

Ganin yanda yake kallon Hajiya Kubra tayi murmushi tayi kana tace.

“Akan al'amarin Naseeru ne da Amina”.

Cikin sauri ya kalleta ya girgiza kai kana yace.

“Ba dai Amina da Naseeru ba saidai Nasseru da Khausar dai ko?”.

Dariya tayi tare da gyara dankwalinta tace.

“A'a da Aminar dai”.

Ido ya zuba mata cike da son nazartansu yace.

“Da Amina dai?”.

Jinjina kai tayi ta kalli Gimbiya Dadu kana tace.

“Tabbas da Amina”.

Jingina Lamiɗo yayi da jikin kujeran kana yace.

“A'a baki fahimci maganarsa da kyau ba da Khausar ce kuma al'amarin ma dai gashi nan yanda yazo
abirkice”.

Fuska Gimbiya Dadu ta ɓata kana tace.

“Babu abinda ya birkice sai dai sune ya birkice musu acan tunda Khausar ta nuna bata sonsa ai
Alhamdulillah ga ƴar Uwarsa ta soshi”.

Cike da Mamaki Lamiɗo ya ɗago kansa ya kalleta yace.

“Da ita Aminar kenan?”.

Jinjina kai Hajiya Kubura tayi kana tace.

“Eh ai Amina da Nasseru sun daɗe da haɗa kansu soyayya suke sosai basu dai fito sun faɗa maka bane
suna so sai angama shirya abubuwa komai ya kankama”.
Jinjina kai Lamiɗo yayi still da mamaki atare dashi yace.

“Allah mai iko shi kuma Naseeru ƴarsa zai Aura?”.

Cikin sauri Gimbiya Dadu ta katsesa da cewa.

“Ya haramta ne?”.

Murmushi yayi tare da girgiza kai yace.

“A'a a'a bai haramta ba na isa in haramta abinda Allah ya halatta ba wai ya haramta bane amma da yake
tana sunan ƴarshi ce”.

Baki Gimbiya Dadu ta taɓe kana tace.

“To wannan dai ba wani abu bane aciki ka dai kayi fatan alkhairi Allah yasanya albarka acikin al'amarin”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.

“Kuma haka abin ya zama kenan?”.

Kallonsa Gimbiya Dadu tayi kana ta kalli Hajiya Kubura dake murmushi tace.

“Sosai ma tunda naji Kakar Khausar tana cewa ba zata bawa Zuri'ar Mayu ba tana ƙananun surutai
shiyasa nace ya janye da nemanta ya nemi Amina ƴar Uwarsa shiyafi mana kwanciyar hankali”.

Ahankali Lamiɗo ya sunkuyar da kansa ƙasa batare da yace Uffan ba.

Dariya Hajiya Kubrua tayi kana tace.

“Ai shiyasa nace bari nazo da kaina muyi magana”.

Anutse ya ɗago kansa ya kalleta ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.

“Toh Yafendo Kubura ai wannan al'amarin Aure magana ce ta maza bata mata ba ai da Babban Naseeru
ne zaizo muyi magana zai fiko sai insamu gamsuwa da sahalewar sa za ayi dukkan maganar?”.

Cikin sauri Gimbiya Dadu ta katsesa da cewa.

“Ai zaizo amma dai ta fara zuwane ta sanar maka saboda bakasan da Maganar ba”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.

“Toh shikenan Ubangiji Allah ya mana zaɓin alkhairi”.

Gimbiya Dadu kuwa cikin sauri ta tari numfashi ta hanyar cewa.


“Shine ma alkhairi Nasseru ya auri ƴar uwarsa ita kuma taje can ta ƙarara ta auri duk wanda taga dama
da masifaffiyar Kakarta”.

Murmushi yayi kana yace.

“To Allah ya kyauta”.

Miƙewa yayi ya fita kai tsaye sashen sa ya nufa zaune ya samu Hajiya Bunayya da waya maƙale
akunnenta tana magana da Hajiya Lami ganinsa yasa tayi saurin cire wayar kana ta katse ta juya ta
kallesa zama yayi tare da tsira mata ido tamkar shine rana ta farko da yafa ganinta acikin rayuwarsa.

Ganin kallon da yake bin ta dashi ne tace.

“Ya dai Mai martaba naga kana ta kallona lafiya kuwa?”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe kana cikin tsira mata Ido yace.

“Wai me yake faru tsakanin Naseeru da Amina ne?”.

Cike da farin ciki tace.

“Meye kuma yake faruwa Lamiɗo banda lamarin Aure da muke fatan zai tabbata tunda sun daidaita
kansu”.

Wani irin kallo ya watsa mata kana yace.

“Sun dai-dai-ta kansu Meyesa ban sani ba”.

Zare ido tayi tare da ɗage hannunta sama tace.

“Lalala nima Wallahi ban saniba sai kwanan nan bai kai sati ba Amina take cemin wai zai aiko ya gama
haɗa kayan Aure su goro da kayan gishiri da kuma sadaki”.

Ido kawai Lamiɗo ya tsira mata bako ƙyaftawa ta cigaba da cewa.

“Hatta kayan rufi ya gama haɗa komansa yana so ayi auren nan da mako biyu nanne nasan da maganar
toh tsoron yi maka magana nake ta yanda zan tunkare ka da maganar”.

Cikin wani irin yanayi Lamiɗo ya tsira mata ido tamkar mai son fahimtar wani abu.

Marerece fuska tayi kana tace.

“Ya dai ka zuba min ido Lamiɗo ka yarda dani ai danasan da maganar dana faɗa maka nima abin ya
daure min kai shiyasa ban faɗa maka ba”.

Sai kuma ta sunkuyar da kanta ƙasa kana ta cigaba da cewa.


“Domin nasan da farko Khausar Naseeru yake so to amma shi Naseeru da kansa ya sameni yace Khausar
tace bata sonsa to shi ya hakura sannan Gimbiya Dadu ma tace ya nemi Amina ƴar Uwarfashi Lamiɗo ya
fesar kana yace.

“Allah ya kyauta amma batun kice baki sani ba zancene Bunayya magana kike”.

Cikin sauri ta kallesa kana tace.

“Wallahi tallahi Lamiɗo ban saniba”.

Cikin yanayin ɓacin rai da takaici yace.

“Dakata Bunayya kada ki rantse dan na lura kamar baki san girma da darajar rantsuwa ba idan kika ce
baki sani ba magana ya ƙare”.

Cikin tsinkewar zuciya take kallonsa.Cike da ɓacin rai ya cigaba da cewa.

“Idan kika faɗa kona yarda ko kar nayarda wannan tsakanina ne dake akan abinda kinsan ƙaryane
kinsani sannan nasani kuma inada tabbaci da yaƙinin ke kika ƙulla wannan alamarin”.

Cikin yanayin tashin hankali da damuwa tace.

“Fisabilillah taya zan ƙullah”.

Ƙwaffa yayi kana yace.

“Bunayya gani kike kamar bansan komai akanki ba ko?”.

Atake zuciyarta ya tsinke zufa ya fara wanke mata fuska duk da sanyin irin na garin Gembila cikin sauri
tace.

“Toh yanzu dan Allah ni menayi?”.

Kai ya girgiza still Idanunsa na kanta yace.

“Hmmm jiki magayi tunda haka kika zaɓawa kanki, duk abinda ya kasance ku kuka da kanku acikin
al'amarin nan ya kamata ace komai zakiyi kiyi shawara dani”.

Kasa cewa komai Hajiya Bunayya tayi sai zufa dake wanketa cike da takaici ya cigaba da cewa.

“Amatsayina na mijinki kuma Uba ga Amina amma bakuyi shawara dani ba sai kuka tura Iyayena ta
yanda zasu tsareni acikin maganar tunda haka kuka zaɓa magana ta ƙare, kowa ya ɗeɓo da zafi
bakinsa!!!”.

Cikin ɓoye tsoronta tace.

“Naseeru fa shiyace ya daina son Khausar”.


Cikin sauri ya katseta ta hanyar cewa.

“Khausar ko baice ya dena sontaba Ni kaina inada nufin bazan bashi Auren Khausar ba, tunda kuma yazo
ya zagaya kukayi haka ke kika sani ƴa ƴarki ce shi kuma ɗan uwana ne babu abinda zance”.

Marerece murya tayi kana tace.

“Ni dai wallahi babu abinda na sani aciki kuma itama Amina tace in faɗa maka Babansa yace zai zo
gobe”.

Wani kallo ya watsa mata Afusace yace.

“Idan kinga dama kice masa yanzu yazo aɗaure ba haka kike so ba?”.

Asanyaye ta kallesa kana tace.

“Toh fisabilillah dan Amina za tayi Aure shine zai zama laifi ko kuma so kake itama tayi ta zama kamar
yanda Asiya take zaune?”.

Cikin tsawa ya ɗaga mata hannu kana yace.

“Ki kiyayi kanki kada ki yarda kijefi Asiya da mugun furuci, Insha Allah Asiya Ubangiji zai jiɓanci lamuranta
Asiya zatayi Aure aure mai daraja da izinin Ubangiji baza ta taɓe ba”.

Kallon yanda yayi kicin-kicin da fuska Hajiya Bunayya tayi cikin fushi ya cigaba da cewa.

“Da yardan Allah tunda tayi haƙuri da jarabawar da Ubangiji ya mata za taci nasara baya ga haka duka-
duka nawa Asiya take bare Amina dududu ba shekaran daya gabata bane ta gana Secondary ba?”.

Uffan batace ta lura aharzuƙe yake cikin rashin walwala ya miƙe yashiga Bedroom ɗinsa.

*MOROCOW*

Aɓangaren Moddibo Baki daya kansa ya ɗauki zafi aiki suke gadan-gadan Anutse ya fito daga masallacin
dake cikin Company ya nufi ainihin inda ake buga Abaya, kama daga Dubai Abaya, Morocco Abaya,
Saudia Abaya, da kuma Turkiya Sai kuma Veils,Bags,shoes da sauransu.

Babba wajene sosai ankafa manyan ijinina sabbi ana ta haɗa su ga manyan-manyan AC dake aiki kana ga
sanyin garin dake sauƙa wajen ya ɗauki sanyi baki ɗaya aiki suke gadan-gadan babu kama ƙafar yaro da
alama nan da Kwanaki biyar za'a haɗa komai gashi an dakatar da aikin komai sai sabbi dake aiki Saboda
sabunta Injina da akayi Ma'aikatan na ganinsa suka nufo sa suna Cikin harshen larabci suke masa Barka
cike da mutuntawa da kuma girmamawa shima sannu yake musu yana yaba aikin da suke.
Ɗaya daga cikin ma'aikatan wanda yake shine Babba yace.

“Alh aiki na kyau yanda ake buƙata insha Allah nan da kwana biyar za'a gama daddasa Injinan da za'a
gama aikin”.

Kallon yanayin wajen Moddibo yayi kana yace.

“Masha Allah abu yayi kyau sosai”.

Kai Engineer ya Jinjina kana yace.

“Sosai ma ai saboda ansamu zaƙaƙuran ma aikata kuma baki ɗaya cikin kwanaki Ukun nan da aka
dakatar da buga Abaya's,Veils,Jakankuna da Takalma *BASJAM”.*

Ahankali Moddibo ya lumshe Idanunsa Aransa yace Allah sarki Abba gashi ya haɗa sunan sa dana J ɗina a
Company sai dai bashi da ikon aiki a Company Engineer ya cigaba da cewa.

“Baki ɗaya har abin ya fara ƙaranta zuwa ƙasashen da ake kaiwa danma ansamu antanadi masu yawa
suna zaune amma Alhamdulillah aikin zaiyi gaggawa tunda ansamu zaƙaƙuran ma'aikata”.

Jinjina kai Moddibo yayi tare da lumshe idanunsa saboda sanyin da wajen ke dashi kana yana jin yanda
Kasan mararsa ke murɗawa ahankali ya ɗaura tafin hannunsa na dama akan maransa ya danna sai kuma
ya cije Lips ɗinsa na ƙasa cikin dauriya ya kalli Engineer tun jiya ya kwana da ciwon cikin kana har yau bai
lafaba na awa ɗaya mai kyauba da zaran yayi minti talatin zai sake murɗa masa ahankali ya cije Lips
ɗinsa kana yace.

“Abu yayi kyau Allah yatemaka insha Allah nan kusa zamu kammala akoma bakin aiki a cigaba da aiki
gadan-gadan”.

Ya ida maganar tare da juyawa ya nufi gefen dama wanda office, Office ne awajen wani Corridor ya shiga
tare da buɗe makeken Office da yafi sauran kyau da tsaruwa sosai Office din ya haɗu table ne kansa
ɗauke da system da takardu sai flowers kana daga jikin bango kujera ce mai juyawa daga gaban table ɗin
kuma kuma jeru biyu ne sai Cottons sky blue da fari daga gefen dama Ac ne daga ɗaya gefen kuma
tamkar falo ne manyan kujeru ne guda bakwai suma Sky blue sai Tv Plasmer ajikin bango da frigde sai
kuma showglass dake ɗauke da kofuna ahankali ya ɗauki remote din AC yaƙara gudu duk da kuwa sanyin
da ake stugawa yayin da zufa ya shiga tsats-tsafo masa agaba ɗaya ilahirin jikinsa kana maransa na
cigaba da murɗawa jikinsa sai zufa yake karyo masa rintse idanunsa yayi da ƙarfi jin yanda mararsa ke
murɗawa tamkar zai fita ahankali ya zauna kana ya ɗaura kansa akan Center table dake tsakiyar falon ya
lumshe idanunsa sai kuma yayi saurin buɗewa kana ya lashi busassun laɓɓansa baki ɗaya jikinsa ya fara
rawa jin yanda maransa ke dunƙulewa yana tsikarinsa cike da damuwa da rauni ya soma faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.


Kana yaja wani numfashi me nauyi ya yunkura da niyyar miƙewa ji yayi bashi da kuzarin da zai iya
tsayawa ji yayi tamkar an haɗa maransa da bayansa ana dinkewa ga wani irin harbawa da zuciyarsa keyi
da Masifar ƙarfi kwanciya yayi akan 3sitter yayi rub da ciki baki daya ilahirin jikinsa rawa yake ga zufa
dake tsats-tsafo masa tamkar babu Ac saboda yanda azabebben ciwon cikin ke gallazarsa yakai kimanin
minti talatin yana murƙususu akan kujera kafin ya fara lafawa sannu Ahankali ya fara maida numfashi
yana fesaewa.

*Gembila*

Asma'u kuwa ta daɗe tsaye aƙofar gida bata samu Adaidaita ba jin kiran sallar La'asar yasa ta juya da
niyyar koma gida tayi Sallah kuma sai tasamu adaidaita shiga tayi tana isa gidan Kai tsaye falon Mommy
ta shiga bakinta ɗauke da sallama zaune ta samu Khausar da Haiydar tana riƙe da hannunsa tana yanke
masa Farce.

Haiydar kuwa kallon Khausar yayi kana yace.

“Nifa ki kula kar ki yanke min hannu”.

Hararansa tayi sai kuma ta cigaba da yankewa kana tace.

“Tunda dai baka iya ba kona yankekama kai ka jawa kanka”.

Ta ƙarasa maganar tare da sauke Idanunta akan Asma'u data gama shiga falon da sauri ta sake masa
hannunsa tare da miƙewa da sauri ta Rungume Asma'u cike da farin ciki tace.

“Oyoyo Asmeey ta”.

Zare ido Haiydar yayi tare da yarfe hannunsa yace.

“Wayyo ta yankeni Wayyo ya tsana”.

Da sauri Mommy ta fito daga Bedroom ɗinta Idanunta akan Haiydar tace.

“Lafiya kuwa”.

Yarfe hannu Haiydar yayi kana ya Marerece fuska yace.

“Mommy ki kallafa Addah Khausi ta yanke min yatsana daga kallon Asma'u”.

Langwaɓar da kai Asma'u tayi kana tace.

“Ayyah Haiydar Sorry sannu bata sani bane”.


Hararansa Khausar tayi tace.

“Rabu dashi ƙato dashi tunda dai har yanzu bai iya yanke Farce ba sai dai in yanke masa aikuwa nata
yanke masa hannu”.

Kallonta Mommy tayi kana tace.

“Wato ma da saninki kika yanke sa?”.

Cikin sauri ta girgiza kai tare da langwaɓar da kai tace.

“Wallahi Mommy ban sani ba ganin Asma'u ne yasa na tashi da sauri ashe na yanke sa”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da kallon Haiydar tace.

“Sannu Babana mu gani”.

“Mommy Ummina tace in gaisheki”

Jinjnna kai Mommy tayi kana tace.

“Ina amsawa”.

Hannun Asma'u Khausar taja suka shiga Bedroom ɗinta suna shiga Khausar tace.

“Fisabillah baki zoba sai yanzu ko dai kwana zamuyi?”.

Zare ido Asma'u tayi kana tace.

“Mu kwana kuma wa zai taya Ummina aiki da safe?”.

Langwaɓar da kai Khausar tayi sai kuma tace.

“Don Allah Asmeey mu kwana zan kira Ummi mu roƙeta”.

Kai Asma'u ta girgiza kana tace.

“A'a keto muje mu kwana mana”.

Ware ido Khausar tayi tare da sanya dariya tace.

“Caɓɓ lallai kam”.


Murmushi kawai Asma'u tayi kana ta zauna abakin gadon.

Khausar kuwa fridge ta buɗe ta ɗauki Plate ta sanya Faro water da Ayaba ta mikawa Asma'u.

Karba Asma'u tayi tana ɓare Ayaban tace.

“Ke dai bakya rabuwa da Ayaba aɗaki kina nan kamar biri”.

Murmushi Khausar tayi kana tace.

“Wallahi kuwa Ina son Banana yana min daɗi”.

Jinjina kai Asma'u tayi tare da faɗin.

“Ai lallai dai kam”.

*Morocco*

Aɓangaren Moddibo kuwa haka yaita fama bayan minti talatin cikin yake sake Murɗansa yana kallon gari
yayi duhu maghariba ta kawo kai har wasu massallatai sun fara kiran sallah amma ya kasa miƙewa
saboda yanda ciwon cikin ke kartansa jin ciwon ya lafa yasa ya miƙe tare ya fita yaga wajen shiru alamar
duk ma aikata sun tattafi sai securities da mai bawflowes ruwa kasancewar karfe biyar da wasu Mintuna
ake tashi ma tsaye wajen motarsa yashiga yaja ya fita a gate one.

Ya miƙe titin ya fito gate ɗin La riva restaurant dake Opposite da Company yazo Dai-dai wajen Traffick
sun tsaida shi saboda sauran motoci da suke wucewa ahankali yasa hannunsa ya dafe fuskarsa ta gefe
yatsunsa na dafe da kuncinsa ya tsansa ɗaya kuma na cikin bakinsa kana ya fito da fuskarsa ta wajen
motar yana ɗan shan Iska jikin katangar Company sa yana shaƙan iskar bishiyar dabino dake zagaye da
Company wanda ta ko ina sune da gudu yaga wata mota ta gilma ta gabansa wacce ta fito daga gefen
yamma zata yi gabas kana shi kuma yana gefen kudu ne idan ya samu dama zaibi arewa ganin wulgawar
motar yaga fuskar J ɗinsa ne aciki cikin sauri ya zare Idanunsa sakamakon kallon fuskar J ɗinsa aciki
Motar cikin wani irin sauri ba tare da anbasa hanya ba ya figi motar ya karya kwana yabisa har ya kusa
bige wata mota.

Da mugun gudu yake bin motar kana ga cunkoson ababen hawa kasancewar maghariba ta kawo kai ƴan
kasuwa sun taso ga kuma ma'aikata sun tattaso daga Office kowa na burin komawa gida wasu kuma na
ƙoƙarin su samu masallacai dan kada su rasa jam'i hakan yasa cunkoso yayi yawa ga kuma duhun gari
gudu yake yana bin bayan motar ga kuma cun kuson motoci da suka taresa ya cusa ta nan yaga antaresa
baki ɗaya ilahirin jikinsa rawa yake tun lokacin daya zare idonsa har yanzu bai maidasu daidaiba saboda
idanunsa sun gane masa Allah ya nuna masa fuskar Jameel ɗin sa ne yasani Koda amagagin mutuwa
yake ya tabbatar fuskar Jameel wulgawa daya zaiyi ya gane yasani wannan fuskar Jameel ɗinsa ne baki
ɗaya ilahirin jikinsa rawa yake kana yana maimaita kalmar Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n yana cigaba da
dannawa motocin gabansa hon baki daya mutane Kallonsa suke wasu kuma na cewa wannan kam
lafiyarka ina zakaje haka kamar zaka tashi sama shidai haka ya cigaba da tafiya ya kutsa tanan ya kutsa
tacan garin hakane ya bigewa wani motarsa mutumin na cewa Kai lafiya amma ina tuƙi kawai yake da
gudu baki ɗaya hankalinsa baya jikinsa wani mai Napep ne ya tare gabansa madadin ya kalli gabansa
amma baki ɗaya idanunsa na kan motar daya yaga J ɗinsa aciki yana samu ƙaramar ɗin ya kauce masa ya
cigaba da bin bayan motar yanda yake gudu da masifaffen ƙarfi haka zalika motar da yake bi ɗin ma take
gudu hakan yasa yasake tabbatarwa kansa J dinsa ne kenan gudunsa yake ko kuma yaya ahaka suka isa
wani roud about nan yaga ya ɗauki hanyar da zata sa dashi da flyover gudu yake da ƙarfi haka shima
wancen ke gudu duk da gudun da yake amma ya kasa kamo wancan motar saboda shima gudun yake ga
kuma motoci dake tsakaninsu amma yana iya hangosa kasancewar be wuce motoci biyu zuwa uku bane
agabansa sunzo daidai kan Flyover yasamu yabi sama Shima Moddibo cikin sauri yabi sama kasancewar
ba cunkoso sosai numfashi mai karfi ya sake kana ya hau kan Flyover yabi sana kafin ya isa tsakiyar
Flyover shi kuma wannan har ya sauƙa ya ɗauki hanyar Unguwar Mellila shima Moddibo cikin sauri yabi
wannan hanyar tafiya kaɗan sukayi yaga motar ta wuce wani asibiti cikin gudu shima ya wuce tafiya
kaɗan suka ƙara yaga motar taja kwana adai-dai wani tamfatsetsen gini mai masifar kyau da girma bisa
duk kan alamu asabiti ne saboda sunan dake manne asaman ginin idanunsa ya ɗaga yaga sunan dake
manne ajikin ginin *Youssef Mouley Hospital*.

Mai motar kuwa yana danna hong aka buɗe masa gate yashiga kafin ya juya akalar motarsa ya ƙarasa
wajen kuma a maida gate din ana ƙoƙarin rufewa da wani irin sauri ya danna hancin motarsa cikin gate
din.

Cikin sauri securities dake bakin gate din suka taso suka yo Kansa.

Shi kuwa mutumin cikin motar tuni yayi Parking ya buɗe motar ya fita da sauri Norses biyu suka biyu
bayansa suna faɗin.

“Welcome Sir”.

Security din kuwa kan Moddibo suka nufa suna faɗin.

“Lafiya kuwa?”.

Shi kuwa Moddibo gadan-gadan ya nufi kan security din da sauri suka kauce masa yana shiga yayi
Parking kana ya fito da sauri security suka yo kansa suna faɗin.

“Lafiya kuwa?”.

Bai tanka suba yabi bayan mutumin yana cewa.

“J!,J!!,J!!!,”.
Shikuwa Mutumin gaba yayi Norses na biye dashi jin hayaniya yasa ya juya ya kalli bayansa gani yayi
Moddibo ya nufo kansa yana cewa.

“J”.

Security kuwa ƙoƙarin riƙesa suke suna faɗin.

“Malam lafiyar ka kuwa ina zaka je?”.

Cikin sauri Moddibo ya hankaɗesu kana cikin fushi yace.

“Ka matsa min anan ka bani hanya, J!J!!”.

Wata matace ta fito daga cikin Hospital din ta ƙaraso kusa da wannan mutum kana tace.

“Dan Allah Dr Jameel kayi sauri kaceci rayuwar ƴata tana cikin hatsari”.

Jin haka ne yasa Mutumin da takira da Dr Jameel ya juya ya nufi cikin asibitin.

Moddibo kuwa da gudu yabi bayan Dr Jameel da already ya shiga cikin reception tamkar wani zautacce
haka ya dawo baki daya bashi da wani cikakkiyar nutsuwa Akuma dai-dai lokacin yaji cikinsa ya sake
kartawa da masifaffen ƙarfi da gudu ya nufi kan Dr Jameel yana cewa.

“J!,J!!,J!!! Ina zaka je”.

Afusace Dr Jameel ya tsaya tare da juyawa yace.

“Wai lafiya Malam Security ku fita dashi mana me kuke jira ha'a ya zaizo yana mana ihu yana firgita
mana marasa lafiya”.

Baki ɗaya Norses da sauran mutanen ido suka zubawa Moddibo.

Cike da girmamawa security yace.

“Yallaɓai munyi ƙoƙarin korinsa amma yaƙi tafiya sai turemu yake”.

Juyawa Moddibo yayi jin J ɗinshi na mgn da larabci wai a koreshi, da sauri ya buga hannunsa aƙirjin Dr
Jameel Cikin juya harce zuwa larabcin yace.

“J ni kake cewa akaro?,J nine fa A.J ɗinka ni kake cewa akaro?”.

Cikin fushi Dr Jameel ya fincike hannun Moddibo ajikin rigarsa yace.

“Ka sakeni wanene kai a ina na sanka kaji yanda kake ihu kana gigita mana mutane”.

Ya ƙare mgnar yana yiwa Modibbo wani irin kallo mai cike da tarin mmki da kuma son nazartan abubuwa
da yawa musamman kamaninsa.
Shi kuwa Modibbo Cikin rauni da tsanananin tashin hankali da azabebben ciwon ciki Moddibo ya sanya
tafin hannunsa ya dafe maransa muryarsa na rawa yace.

“J Nine fa J A.J ɗinka kake cewa baka gane ba Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n J nine yau kake cewa baka
sani ba?”.

Akuma dai-dai lokacin cikinsa ya sake murɗawa da masifaffen ƙarfi cike da ɓacin rai Dr Jameel ya Kalli
security kana yace.

“Ku fitar min dashi”.

Norses ɗin kuwa cikin alamun damuwa suka ce.

“Dan Allah Dr muje ka duba matarnan”.

Juyawa Dr Jameel Yayi Moddibo kuwa ganin haka yasa Cikin wani irin rauni ya kallesa muryarsa na rawa
kana numfashinsa na fusga yace.

“Jameelu nine fa aduniya Koda baza ka gane kowaba amma Ni da Ummi da Abba bamu cancanci
kamanta damu ba kuma ko me yafaru da kai aduniya Ni dai da Ummi da Abba bamu cancanci ka ce baka
gane muba A.J dinka nefa”.

Yana gama faɗar haka ya yanke jiki yayi baya...

*Zakusha Typing errors dan banyi editing ba, wani wurin zakuga kalaman a baude ko baibai*

By

*GARKUWAR FULANI*

SAKAYYAH

41

*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n
nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai
sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan
mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in
kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a
banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account
no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na
faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki
kenan*

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito
miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar
infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita
tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a
saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda
yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin
san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo
kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki,
domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan
ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah
zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce
dai GARKUWAR MA'AURATA.
41

Da ƙarfi yayi baya ya zame luuuuu yana faɗin.

“JJJ”.yana rufe bakinsa ya sume.

Ɗaya daga cikin perciens dake zaune a reception ne yayi saurin miƙewa tare da kallon Moddibo dake
kwance babu numfashi atare dashi yace.

“Dr Jameel ya suma fa”.

Ya faɗa tare da ƙara sawa kan Moddibo cike da damuwa yace.

“Bawan Allah!,Bawan Allah!!”.

Ina ko motsa wa Moddibo baiyi ba.

Juyawa Dr Jameel Yayi tare da kallon security cikin fushi yace.

“Kun sanshi?".

Atsorace security ya kalli Moddibo dake kwance kana ya kalli Dr Jameel Murya na rawa yace.

“Wallahi Sir munyi iya bakin ƙoƙarin amma mun kasa motarka na shiga shima ya shiga da ganin yanda
yake tuƙi yasa nayi ƙoƙarin hanasa badan na kauceba bige ni zaiyi”.

Ɗaya matar dake tsaye cikin tashin hankali tace.

“Dr dan Allah katemaka min ƴata na cikin hatsari katemaki Rayuwar ta”.

Jin haka yasa ya juya tare da take step zuwa inda Office dinsa yake mutumin dake tsaye kan Moddibo
yayi saurin Kallonsa cike da damuwa yace.

“Dr Jameel suma yayi fa a duba al'amarin sa shima yana bukatar temakon gaggawa”.

Tsayawa Dr Jameel Yayi ya rasa shin me zaiyi cikin raunin matar dake biye dashi tace.

“Dr ƴata dan Allah”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe kana ya kalli sauran Norses ɗin yace.

“Ku kula dashi”.


cikin sassarfa ya nufi Office ɗin sa yana shiga ya cire Jacket ɗin sa ya maƙala ajikin kujera ya fita kai tsaye
Theater room ya nufa yana shiga ya samu angama shiryata kawai shi ake jira Atake ya fara aiki cike da
tsananin ƙwarewa da iyawa na cikakkun likitoci ya fara mata C'S.

Acan ɗakin da Moddibo ke kwance kuwa baki ɗaya Norses ɗin sunyi iya bakin ƙoƙarin su wajen ganin
numfashinsa ya dawo amma abin ya faskara da alama ya tafi suma da wani ɗan ciwone dake tare dashi.

Dr Jameel kuwa sai bayan awa ɗaya ya fito daga Theater room Agajiye ya fito domin mata biyu yayiwa Cs
ɗin, Norses na biye dashi abaya tsaye ya hango Mahaifiyar Yarinyar atsaye abakin wajen kallonta yayi
tare da sakar mata da murmushi kana yace.

“Alhamdulillah ancire yaro yana lafiya kuma Insha Allah itama tana lafiya”.

Cikin sauri matar ta sauƙe ajiyar zuciya kana da murmushi afuskarta tace.

“Alhamdulillah”.

Dai-dai lokacin Norses suka turo gadon matar na kwance akai wani Corridor suka nufa yanayin tsarin
asibitin komai na musamman ne, ɗaya daga cikin Norse da sukayi Operation ne ta fito rungume da jariri
kana ta miƙawa matar dake tsaye da murmushi afuskarta tace.

“Alhamdulillah ga Baby boy nan lafiyarsa ƙalau”.

Murmushi matar tayi kana tace.

“Alhamdulillah Allah Nagode maka”.

Dr Jameel kuwa kai tsaye Office din sa ya nufa cikin sauri Norse dake kan Moddibo ta ɗago ta kalli Dr
Jameel da alamun damuwa afuskarta tace.

“Dr har ka fito?”.

Kai ya gyaɗa mata alamar Eh.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.

“Sir Wallahi har yanzu fa mutumin bai farfaɗo ba Dr kazo ka dubasa nayi ƙoƙari Inje in Samu Dr Mubarak
ya dubasa to kuma already ya tafi”.

Numfashi ya fesar kana yaja siririn tsaki Ido ya zuba mata kana yace.

“Ina Dr Eshaa?”.

Cikin sanyin murya tace.

“Itama bata nan tun Azahar ta fita tace suna da biki”.


Dafe kai yayi kana yace.

“Kenan ba Dr acikin asibitin?”.

Cikin sauri ta girgiza kai tare da cewa.

“A'a akwai perciens ne sunyi yawa akansa shiryasa nace basai na masa magana ba bari inzo wajenka”.

Tsaki yaja kana yace.

“Toh”,Yana ƙoƙarin sauƙa ɗaya daga cikin Norses da sukayi C'S ta kallesa cikin wani narkakkiyar murya
tace.

“Sir”.

Cak ya tsaya tare da juyawa ya kalleta wani irin juya masa Idanu tayi tare da kashe masa ido kana ta hura
masa kiss.

Dogon numfashi yaja tare da ƙanƙance Idanunsa kana ya narkar da muryarsa yace.

“Ohhh My Baby kasheni kike sonyi ko?”.

Bai jira cewar taba ya juya ya nufi ƙasa yabi bayan Norses data kirasa kana ita kuma wacce ya kira da
Baby ta biyo bayansa.

Yana shiga ɗakin da Moddibo ke kwance ya tsaya ya zuba masa ido yana karewa fuskar bawan Allah da
karo na farko kenan arayuwar sa ya fara Kallonsa, sai dai tabbas komai nashi baida banbanci dana
Ibrahim, toh shin waye shi din.

Ɗaya daga cikin Norses dake ɗakin ne tace.

“Sir ataima ka mishi ya daɗe da suma fa yanzu kusan awa ɗaya da rabi kenan fa yana sume”.

Nunfashi ya fesar tare da sunkuyowa kansa cike da tsantsar ƙwarewa da iyawa da kuma bijinta na ainihin
ƙwarerren Likita wanda yasan aikinsa In and Out ahankali ya kamo tafin hannunsa ya fara murzawa kana
ya kamo tafin ƙafarsa yana murzawa yana danna jijiyoyin tafin ƙafarsa yana murzawa da sauri ya kai
kimanin minti goma yana murzawa kafin ya koma murza jijiyoyin bayan wuyansa ahankali ya sunkuya
kansa ya ɗaura bakinsa akan hancinsa ya fesa masa numfashin tare da zuƙo nashi ahankali.

Hannu ya miƙawa Norse dake gefensa cikin wani salo ta ɗaura tafin hannunta akan nasa ta riƙe tana
murzawa.

Ahankali ya juya ya kalleta kana cikin wani shu'umin murya yace.

“Ruwa zaki bani ba hannun ki ba”.


Yanayin da yayi magana kaɗai zai tabbatar maka da cewa shi ɗin shu'umin Namiji ne na ƙarshen zamani
mai cike da shu'uman da sanin barikanci.

Kai ta gyaɗa kana ta fita kai tsaye Office ɗinsa ta nufa ta ɗauko masa goran ruwa ta dawo ta miƙa masa
karɓa yayi kana yasa atafin hannunsa ya watsawa Moddibo ruwan da ƙarfi dogon numfashi Moddibo
yaja kana cikin wata raunan'niyar murya yace.

“Ummi naga J ɗin mu Ummi J ɗinmu bai mutu ba Ummi ga Jameelun ki bai mutu ba”. Yayi mgnar da
larabci kasancewar dashi ya sume a bakinsa.

Baki ɗaya ido Norses ɗin suka zuba masa musamman wacce Dr Jameel ya kira da Baby wani irin kallo
take bin ilahirin jikinsa dashi musamman Lips ɗinsa da yake tattarewa yayi pinch dashi.

Dr Jameel kuwa ahankali ya ɗago Ido ya kalleta cikin wani narkakkiyar murya yace.

“Ya dai Baby wani irin kallo ne wannan kada fa ki cinye sa yana kwance agadon asibiti”.

Sai alokacin ta lura da kallon ƙurullan da take bin Moddibo dashi numfashi ta fesar kana ta narkar da
murya tace.

“Masha Allah kaga madaran kyau babu algus ga haiba da kamala”.

Harara ya watsa mata cikin muryarsa dake ɗauke da kishi yace.

“Ya fini ne?”.

Kallonsa tayi kana ta kalli Moddibo tace.

“Hmmm in dai kyaune da ƙasaita ya fika sai dai kuma ai kaine nawa kuma jaruntarka na sani”.

Ɗaya Norse data kirasa ta watsa masa Harara kana ta taɓe baki.

Moddibo kuwa ba tare daya dawo hayyacinsa ba ya cigaba da cewa.

“Ummi ga Jameelun ki ki daina kuka Abba ga J ɗina na gane J ɗina”.

Maganar Moddibo da Dr Jameel yaji shi yasa ya janyo hankalin sa ahankali ya sunkuya da kansa daidai
kunne Moddibo yace.

“Ikon Allah”.

Moddibo kuwa Jin sautin Muryan ma sak ta J ɗinsa akunnensa yasa sannu Ahankali ya fara buɗe
idanunsa domin ba zai taɓa mantawa da muryarsa ba akan Dr Jameel da har zuwa lokacin ke durƙushe
kansa ya buɗe idanunsa cikin wani irin sauri ya yunƙura ya zauna Atsakiyar gadon kana ya janyo Dr
Jameel ya fashe da wani irin kuka yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinsa ke rawa.

Lokaci ɗaya kuma jikin Norses dake ta faman rawan kai da zumiɗin ganin kyawunsa jikinsu yayi masifar
sanyi ganin yanda Kamilin mutum kana Matashi mai jini ajiki ke kuka Dr Jameel ma Baki ɗaya jikinsa ya
mutu ganin yanda mutum dake kiranshi da J ke kuka tamkar mace.

Cikin rauni da tarin damuwa kana da kuka da yaci ƙarfinsa ya cigaba da cewa.

“Alhamdulillah Allah Nagode maka Ubangiji ya cika min burina Allah na gode maka dama J kana raye?”.

Ya ida maganar tare da janye jikinsa daga na Dr Jameelu ya tallafe kuncinsa still hawaye na bin fuskarsa
kana muryarsa na rawa yace.

“J”.

Cikin sauri ya sake Rungume Dr Jameel Araunane yace.

“Ummi! Ina kike? Yau ina Abbana? Ummi ina kuke ga J ɗina Ummi J ɗina bai rasu ba Ummi gawar wani
aka nuna mana akace J ne Ummi J ɗina bai rasu ba Ummi”.

Dr Jameel kuwa cikin sauri da tsoro ya janye jikinsa daga na Moddibo kana ya nuna sa da yatsa muryarsa
na rawa yace.

“Bawan Allah ni ban sanka ba nifa ba J ɗinka nan da kake faɗa bane”.

Miƙewa Moddibo yayi ido cikin ido ya kallesa kana yace.

“J nine kake cewa baka sani ba!?,A.J ɗin ka nefa”.

Ya ida maganar kana baki daya ilahirin jikinsa rawa yake yayinda maransa ke cigaba da damƙarsa cikin
rauni ya kalli Dr Jameel daya zuba masa ido kana yace.

“A.J ɗinka nefa Amma kake cewa baka sani ba”.

Ajiyar zuciya Dr Jameel ya sauƙe tare da fesar da numfashi cikin gaskiya da gaskiya yace.

“Wallahi ban sanka bani ban taɓa ganin ka ba”.

Cikin tsanananin tashin hankali tsoro da kiɗima Moddibo yace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n J kaji tsoron Allah ka daina rantsuwa nine kake cewa baka sani ba J
Moddibo kane fa Jameelu Nine zaka ce baka saniba!?”.

Cikin yanayin rashin fahimta Dr Jameel ya Girgiza kansa kana yace.


“Wallahi ban sanka ba ni ban taɓa ganinka ba”.

Araunane Moddibo ya tsira masa idanu kana yace.

“Baka Sanni ba J kace baka taɓa kallona ba?”.

Ya ƙarasa maganar tare dasa hannu ya shafa jikinsa jin babu waya yasa yayi saurin kallon Dr Jameel yace.

“Ina wayata?”.

Araunane ya sake kallon yace.

“J naji baka sanni ba domin Ni Aminine daya cancanci ka wurgar ko? to amma J Ummi fa Ummi ma baka
santa ba?”.

Kai Dr Jameel ya girgiza kana yace.

“Wacece Ummi kuma?”.

Zare ido Moddibo yayi Aƙiɗime yace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n J Ummi mahaifiyar kace baka sani ba!?”.

Ahankali Dr Jameel ya sunkuyar da kansa ƙasa kana ya ɗago ya kalli Moddibo yace.

“Ni kuma Mahaifiyata?,Gaskiya dai inaga wannan kana da Lalurar ƙwaƙwalwa!”.

Cikin sauri Moddibo ya zauna abakin gadon ya dafe kansa da hannu bibbiyu muryarsa na rawa yace.

“J ni kake cewa ina da matsalar ƙwaƙwalwa yayi kyau J shin wani irin laifi muka yi maka aduniya da muka
cancanci irin wannan hukuncin agareka me muka yi maka mai tsanani da zaka hukunta mu ta wannan
hanyar”.

Kallonsa kawai Norse din keyi cike da tausayawa.

Cikin rauni ya cigaba da cewa.

“J Ni kake jifa da kalmar cewa ƙwaƙwalwa ta ba ɗaya bane, to koma ƙwaƙwalwa ta takasance tana da
matsala J rashinka akusa damu ne da kalmar da aka faɗa mana cewa ka rasune ya jefamu cikin wannan
halin”.

Kallon ikon Allah kawai Dr Jameel yake kana yana kallon yanda hawaye ke bin kuncin Moddibo.

Cikin sanyi da rauni Moddibo ya cigaba da cewa.

“J sannan koda na kasance mai taɓin hankali katari da gawarka da akayi da gawarka akace ka rasu shiya
jawowa ƙwaƙwalwata matsala!”.
Ahankali Dr Jameel ya matsa kusa dashi Asanyaye yace.

“Bawan Allah ka nutsu ni bansan kaba ban san mekake nufi ba”.

Cikin fushi Moddibo yace.

“J ƙarya kake”.

Miƙewa Dr Jameel yayi tare da ɗage kafaɗa yace.

“Ok toh shikenan”.

Ya ƙarasa maganar tare da ficewa Norses suka mara masa baya.

Cikin sauri Moddibo ya mike ya fita kai tsaye wajen motarsa ya nufa ya ɗauki wayarsa ya dawo reception
din ya kunna wayarsa dake ɗauke da hotonsa dana M Jameel ya nuna masa kana yace.

“Yanzu wannan ka mantani ai gaka gani”.

Kallon fuskar wayar Norses ɗin sukayi Wacce Dr Jameel ya Kira da Baby tayi saurin buɗe baki cike da
Mamaki ta kalli Dr Jameel kana tace.

“Iyee Dr da gaske fa kaine”.

Harara ya watsa mata kana yace.

“Kuma dai baku da hankali”.

Ahankali Moddibo ya juya da fuskar wayarsa nan yaga takwas tara cikin sauri yace.

“Yah salam banyi maghariba banyi Isha'i ba”.

Sai alokacin Dr Jameel ya tuna da batun sallah kallon Moddibo yayi da duk kiɗima da ruɗu kana da gigita
dake jikin mutumin amma ga mamakinsa sai ya juya ya nufi Masallacin dake cikin Hospital Kai tsaye Tap
dake wajen Moddibo ya nufa ya ɗaura alwala har zai shiga Masallacin ya tsaya ya juya tare da kallon Dr
Jameel da still Idanunsa ke kansa.

Kai ya jinjina muryarsa na rawa yace.

“Yayi kyau J nine kake cewa baka gane ba zan shiga Masallaci in faɗawa Ubangiji duk abinda ke
damuna”.

Ya ida maganar tare da shiga Masallaci nunfashi Dr Jameel ya fesar kana shima yayi alwala ya nufi
masallaci.
Yana shiga Masallaci yayi maghariba da Isha'i yana idarwa idanunsa suka sauƙa kan Moddibo daya tsira
masa ido.

Cikin sanyin murya da rauni Moddibo yace.

“J Nine kake cewa baka gane ba”.

Kai Dr Jameel ya Girgiza cikin gaskiya da gaskiya yace.

“Wallahi bawan Allah Ni bansan kaba ban kuma gane kaba kadena cemin J Ni sunana Jameel”.

Cikin sauri Moddibo ya katsesa kana yace.

“Aina sani dama sunan ka Jameel ne”.

Dr Jameel kuwa jin wayarsa na ringing yasa ya Mike ya fita kai tsaye cikin Hospital ya nufa duba matar
daya mata Theater Yana shiga Moddibo yabi bayansa bayan ya gama duba ta yafita ya kalli Moddibo
kana yace.

“Yanzu ko inda zanyi aikin ma sai kabini har ciki?”.

Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.

“Eh dole sai na bika J”.

Cikin alamun gajiyawa Dr Jameel yace.

“Toh kabarni mana ina sarara”.

Kai Moddibo ya Girgiza cikin tsaresa da ido yace.

“Ai tsakanina da kai babu sararawa sai lokacin dana danƙa ka ahannun Ummi da Abba”.

Siririn tsaki Dr Jameel yaja kana ya juya yabar wajen kai tsaye Office ɗinsa ya nufa dai-dai lokacin Baby ta
shiga.

Tana shiga ta tsaya daga bayansa bayan ya zauna akan kujera cike da salo ta sanya tafin hannunta
tashafa sajensa zuwa kan Lips ɗinsa.

Cike da shu'uman ci ya lumshe Idanunsa cikin wata narkakkiyar murya mai tarwatsa lissafin mata yace.

“Ohhhh My Baby don't kill me. Cikon Office muke fa, mu tafi gida Please I need you”.

Shagwaɓe Murya tayi tare dayi masa fari da ido tace.

“But Dr Ina da Nightduty”.


Wani kallo ya bita dashi yana shinshina wuyarta kana yace.

“Toh yanzu yakike so inyi”.

Ido ta kashe masa tare da ɗage gira tace.

“Duk yanda kace haka za ayi?”.

Cike da tsanananin Mamaki Moddibo ke kallonsu Aruɗe yace.

“J wacece wannan kuma kasan abinda kake yi kuwa?”.

Cikin tsawa ya kalli Baby kana yace.

“Ke ki sake shi baki da hankali ne?”.

Juyawa Dr Jameel Yayi tare da kallon Moddibo Up anda down Cike da takaici yace.

“Ya dai bawan Allah Meyesa kake shige min rayuwa da ƙudundunai ne?,Ko kuma dan kaga bansa
security sun jefa ka waje bane?Ina ruwanka da ita?”.

Araunane Moddibo ya kallesa kana yace.

“J baka da hankali ne J mekake yi haka? Shin wace rayuwa ka jefa kanka aciki J?”.

*Gembila*

Acan Gembila kuwa adai-dai wannan lokacin Mommy ce zaune abakin gadon Khausar yayinda Khausar
da Asma'u ke tsakiyar gadon cikin dariya Mommy ta gyara zaman wayar dake kunnenta kana tace.

“Yau dai Ummi kiyi haƙuri nice na hana Asma'u dawowa kuma Khausar ce ta hana dan Allah kiyi haƙuri ki
barta ta kwana, kinsan abokin kuka shi ake faɗawa mutuwa”.

Murmushi Khausar tayi tana kallon Mommy.

Still Mommy na Dariya tace.

“Shiyasa nace bari in kiraki in Faɗa miki kuma ɗazu nayi ta kiran wayarki yana shiga ba'a ɗauka sai
yanzun”.

Acan ɓangaren Ummi kuwa murmushi tayi cikin yanayin sakin fuska da jin daɗi tace.

“Laa bakomai ai lokacin da kika kira ina tare da Babansu ne kuma nabar wayar aɗakina muna tatauna
batun Khausar ne sai yanzu dana shiga ɗaki naga miss call ɗinki na kira”.
Murmushi Mommy tayi cikin jin daɗi tace.

“Toh Nagode Insha Allah zamu kwana gobe zata dawo”.

Khausar dake gefe tayi ƙasa da murya kana tace.

“Mommy kice mata dan Allah goben ma sai da daddare zata dawo zamu sake yini”.

Dariya Ummi dake jiyo sautin muryar Khausar tayi kana tace.

“Ai kwana ya isa basai anyini ba”.

Karɓan wayar Khausar tayi tare da langwaɓar da kai tace.

“Dan Allah Ummi idan mun kwana mu yini”.

Murmushi Ummi tayi tare da gyara rikon wayar tace.

“Ku kwana dai sannan kuzo da wuri Ina son tattaunawa dake”.

Kai Khausar ta gyaɗa kana tace.

“Toh Ummi”.

Sannan ta katse wayar.

Miƙewa Mommy tayi kasancewar girkinta bisa duk kan Alamu cikin shirin tafiya side ɗin Lamiɗo take
kallon Khausar tayi kana tace.

“Toh kizo ki rufe muku ƙofa”.

Kai suka gyaɗa atare suka miƙe da Asma'u suka bi bayanta kana suka rufe kofar.

Zama Asma'u tayi akan 2sitter kallonta Khausar tayi ta shafa cikinta kana tace.

“Asma'u mai za muci ne?”.

Kai Asma'u ta girgiza kana tace.

“Wani abinci zanci Khausar bayan kinsan Maganar daya kawoni nake so muyi amma tun yamma kin ƙi ki
zauna muyi”.

Langwaɓar da kai Khausar tayi cikin sanyin murya tace.

“Shiyasa nake so mukwana kinga yanzu ma Mommy Bata nan zamu sake muyi maganar mu”.

Jinjina kai Asma'u tayi tare da cewa.


“Toh shikenan”.

Ahankali Khausar ta shafa cikin tace.

“Gaskiya yunwa nake ji kema kuma naga ɗazu bakici abincin sosai ba”.

Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe kana tace.

“Toh shikenan muje kichen ɗin muga mai zamuyi”.

Suna shiga kichen Asma'u ta buɗe freezer Khausar kuwa na tsaye gefenta ganin ɗanyen kifi yasa Asma'u
juyawa ta kalli Khausar kana tace.

“Toh muyi Marghi special mana”.

Kai Khausar ta gyaɗa cike da gamsuwa tace.

“Toh shikenan muyi”.

Suna aikin suna taɓa hira cikin awa ɗaya suka gama kana suka soya chips aplate Asma'u ta zuba musu
sannan Khausar ta zuba musu Tea cup biyu afalo suka zauna suna ci suna kurɓan tea suna cikin ci suka ji
Knowking ahankali Khausar ta kalli ƙofar tace.

“Waye”.

Haiydar dake tsaye yace.

“Nine”.

Kurɓan tea Khausar tayi tace.

“Toh lafiya har mun rufe kofa zaka zo kana mana Knowking?”.

Murmushi yayi kana yace.

“Naji ƙamshi yana ta buɗewa ne ta ko ina shiyasa nasan wani abu kuka girka Ni dai Ku sammin kawai
yunwa nake ji dan nayi dogon hira”.

Hararan ƙofar Khausar tayi tare da cewa.

“Shegen kwaɗayi mutum yana nan da hanci kamar Mage duk abinda akayi baka ciki ma sai an baka”.

Dariya Asma'u tayi tare da miƙewa tashiga kichen ta ɗauki Plate ta zuba masa sauran kana ta buɗe ƙofar
ta miƙa masa har ta juya yayi saurin cewa.

“Toh ni baza abani shayin bane”.

Harara Khausar ta watsa masa kana tace.


“Ohh Haiydar kinga Ni Ko Asma'u da ba kin fara bashiba”.

Murmushi Asma'u tayi tare da juyawa ta koma kichen Haiydar kuwa gwalo yayiwa Khausar kana yace.

“Oho dai abani”.

Miƙa masa Asma'u tayi bayan ta zuba.

Bayan sun kammala Asma'u tace.

“Khausar mu dan watsa ruwa mana”.

“Eh to ki fara shiga".

Cewar Khausar dake gyara zamanta.

Miƙewa Asma'u tayi tare da tattare Plate ɗin ta kai kichen kana ta dawo ta watsa ruwa bayan ta fito
Khausar ma tashiga ta watsa tana fitowa ta bude Siff ta ɗauka musu sleeping dress riga da wando masu
duhu ta miƙawa Asma'u ja sannan ita ta sanya fari.

Kai tsaye falon suka fito Khausar ta kunna Tv ta rage Volume Anutse Asma'u ta juya ta kalli Khausar kana
cikin sanyin Murya tace.

“Khausar”.

Ahankali Khausar ta juya tare da tattara duk kan nutsuwarta zuwa gareta tace.

“Na'am”.

Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe kana tace.

“Khausar wai Maganar da naji gaskiya ne abu ya kankama wai har an ɗaura aurenku?”.

Numfashi Khausar ta fesar kana ta sunkuyar da kanta ƙasa cikin rauni ta riƙo hannun Asma'u ta mannasu
da kumatunta ga mamakin Asma'u sai taga hawaye na zuba Shar-shar-shar akuncinta.

Cikin sanyi da rauni Asma'u tace.

“Haba Khausar daga na miki magana sai ki fara kuka ai mu abun farin cikine”.
Ƙasa cewa komai Khausar tayi sai hawaye da take ahankali ta fara sheshsheƙa dake fita daga ainihin
zuciyarta.

Araunane Asma'u tace.

“Haba Khausar kina kuka Ni kuma ya kikeso inyi kawai daga nazo muyi magana ta tsakanin mu sai ki fara
kuka ai wannan abin farin cikine ba abin kuka ba”.

Kai Khausar ta girgiza cikin rawan murya tare da ƙoƙarin hana kanta kuka tace.

“Asma'u na amince ne saboda wasiyyar da Yah Jameel ya barmin kenan, amma ke kinsani kinsan waye
Moddibo kinsan yanda tsakanina dashi yake kuma ni wlh banyi zaton da sauri-sauri haka zasu liƙa mishi
niba”.

Hawaye na bin kuncinta ta cigaba da cewa.

“Bansan wace irin rayuwa zanyi atare dashi ba bansan wani iri zama zanyi ba bansan wani irin ƙakubalen
zan fuskanta ba amma ina cikin taraddadi da tashin hankali Asmau”.

Atake idanun Asma'u suka cika da hawaye cike da tausayin Khausar.

Araunane Khausar ta cigaba da cewa.

“Ranar ma abinda ya kaini gidanku kenan naje ne muyi maganar amma sai in rasa ta yanda zan fara
maganar ta ina zan kama mgnar ma”.

Cikin matsanancin kuka da tashin hankali tace.

“Asma'u shin menene makomata Yah Jameel ya barni da nauyi mai tarin yawa inaso in wanzar masa da
wasiyyar sa gashi ya kasantu to amman ni menene makomata”.

Cikin rauni da tarin damuwa Asmau tace.

“Khausar ki daina kuka in dai kin gamsu Saboda farin cikin Yah Jameel amakwancinsa kikayi to ki daina
kuka na tabbatar da Yah Jameel yana raye ba zaiso kukan kiba”.

Kasa da kai Khausar tayi hawaye na cigaba da zuba daga idanunta cikin zubda hawaye Asma'u ta cigaba
da cewa.

“In dai har kinyi haka saboda farin ciki da kuma Wasiyyar Yah Jameel ya bar miki toh kada kiyi Kuka Yah
Moddibo ai Namiji, ke kuma macece, kuma zuciya tana son mai kyau tata mata ke kuma mace cefa
cikekkiya mai ababen muradin dukkan namiji”.

Ta sauƙe Ajiyar zuciya still Hawaye na bin fuskarta ta cigaba da cewa.

“Ina da tabbaci Khausar ko Yah Moddibo muddin yaji wasiyya ce Yah Jameel ya bar miki sannan saboda
wasiyyar sa kika ce kinji kin gani zaki auresa nasan bazai zalunceki ba muddin bai kyautata miki ba to
bazai zalunceki ba”.
Kai Khausar ta girgiza ta tare da ƙara danne sheshsheƙan Kukan ta haka ma Asma'u cikin sauri Khausar ta
fara share mata hawayen fuskarta murya na rawa Asma'u tace.

“Khausar ban san da wani irin baki zan miki godiya ba, Ubangiji Allah ya biya ki da mafi kyawun
sakamako saboda wasiyyar ɗan uwana kika amince da mgnar duk da ba yayanki bane”.

Cikin sauri Khausar ta sa hannu ta rufe mata baki muryan ta na rawa tace.

“Asma'u meyesa zaki ce haka Yah Jameel kike cewa ba Yayana bane?”.

Kai Asma'u ta girgiza kana cikin raunin murya tace.

“Ba haka nake nufi ba Khausar”.

Araunane Khausar tace.

“Toh meyesa haka Yah Jameel Yayana ne kuma Malami nane sannan Al'farma ya nema ya haɗani da
Allah da Manzon ranan rabuwa ta na ƙarshe da Yah Jameel”.

Sai kuma tayi saurin rufe fuskarta da tafin hannunta kana cikin rauni ta cigaba da cewa.

“Yah Jameel Yana Kuka fa Asma'u yake cemin Khausar nasa zaiyi wuya inyi tsawon rayuwa alokacin daya
faɗa min hankalina ya tashi na gigice bansan lokacin da hawaye ya fara zubo minba”.

Asma'u kuwa lumshe idonta tayi tana mai jin ƙaunar Khausar aranta.

Cikin sheshsheƙa Khausar ta cigaba da cewa.

“Ganin ina kuka sai ya fara yimin dariya yana cewa dan yace min zai mutu shine xan fara kuka ai bawai
dan ya faɗa yana nufin mutuwa zaiyi ba, sannan yace min akwai Alfarma da temakon da yake nema
awajena”.

Ta lumshe Idanunta hawaye masu zafi suka zubo kana ta cigaba da cewa.

“Yasa na mishi al'ƙawari koda bayan ransa zan cika masa wasiyyar Asma'u kuma nayi nasa al'ƙawarin
idan har ban auri Moddibo ba kenan ban cikawa Yah Jameel Wasiyyar sa banyi masa taimakonba shiyasa
nace Moddibo zan aura amma ke kin sani tsoron Moddibo nake hasalima babu wacce Moddibo ya tsana
arayuwar sa sama dani kinsan shi baya sona ni kuma ina tsoronsa”.

Cikin sanyi da son ƙarfafa mata gwiwa Asma'u tace.


“Insha Allah ba zaki taɓe ba Ummi ma tayi farin ciki da wannan auren kowa kin sashi afarin ciki Insha
Allah Ubangiji zai dawwamar miki da farin ciki agidan Auren ki”.

Ajiyar zuciya mai nauyi Khausar ta sauƙe kana yace.

“Ni dai zanyi wannan al'amarin saboda Yah Jameel ne kuma na yarda zan jure duk kan ƙunci, Haranta,
Cin fuska, Tozarci, Cin zali da duk wani salon wulaƙanci da Moddibo zai min saboda cika burin Yah
Jameel”.

Asma'u kuwa kai ta girgiza kana tace.

“Insha Allah ma ba zai miki ba da yardan Allah ba zaki ƙuntata ba rayuwa ba zata miki ƙunciba tunda
Mommy ta sanya Albarka aciki komai zai tafi dai-dai”.

Ta ida maganar tare dasa hannu tana share mata hawaye murmushi tayi ko kaɗan bata son ganin
hawayen Khausar cikin son ƙawar mata da damuwarta tace.

“Keda kike amarya wayasan amarya da kuka kuma amaryar ma ango mai tsada matar Yah Moddibo?”.

Harara Khausar ta watsa mata da jiƙaƙƙun Idanunta da Eyelashes ɗinta suka sake zara-zara dasu sai
kuma ta tura baki tace.

“Ba wata amarya amarya ko kuma wahalalliya dai!?”.

Dariya Asma'u tayi kana tace.

“Ba wata wahalalliya amarya dai”.

Cikin sanyi Khausar tace.

“Hmmm Asma'u Ni dai hankalina atashe yake ina tsoron Moddibo bansan wani irin zama zamuyi ba”.

A dai-dai lokacin kuwa Samira Sani ce, da Amina ke waya tana gaya mata batun auren MODIBBO DA
Khausar, Ya Salam wannan labarin ya girgiza Samira, haka yasa bta cilla wayar bisa gado ma tare da ta
katse kiranba.

Da gudu ta nufi ɗakin Hajia Lami, tana shiga ta ganta zaune bakin gado da waya a kunne tane cewa.

“Haba dai Hajia Bunayyah wanne irin aure kuma, innalillahi ya za'a mana haka muna nan muna shiri mun
rasa nitsuwa dan jawo hankalin wannan yaro kuma azo ace wannan shegiyar yarinyar ya aura, ya zasu
fito mana a bazata”.

Sai kuma ta katse wayar tare da ruggume Samira da ta faɗa jikinta tana kuka wui-wui tare da cewa.

“Mommy shike nan ni kam nayi batam ɓaka tamtam, ni ba budurcinaba, ni ba Modibbo ba, ni ba lafiyata
ba ni da zunubin zina da boka, ga ruwa mai wari da ke bibiyata”.
Ta ƙare mgnar da fashewa da matsanancin kukan da yasa Hajia Lami ruggume mata cike da takaici ta
fara lallashinta.

Acan Falon Lamiɗo kuwa kallon Mommy dake zaune gefensa yayi ahankali ya sauke ajiyar zuciya kana
yace.

“Ɗazun Alh Bukar suka zo maganar Amina da Naseeru to kuma har angama magana anbawa Naseer
Amina since Ashirye suke nan da kwana goma suke so dan Ashirye suke”.

Murmushi Mommy tayi kana tace.

“A'a Masha Allah Abu yayi kyau Allah yasanya al'khairi”.

Anutse Lamiɗo ya gyara zamansa kana yace.

“Toh kuma tunda sakaranar yazo abakin gaba kawai za ahaɗa da ɗaurin bikin Khausar”.

Saurin Kallonsa Mommy tayi Asanyaye tace.

“Mai martaba da sauri haka?”.

Kallon yanda tayi da fuska yayi kana yace.

“Toh ke Meye damuwarki aciki?”.

Cike da damuwa tace.

“Toh Babu abinda muka shirya wa bikin nan fa”.

Numfashi ya fesar kana yace.

“Toh na saki ne ko kuma nace kishirya ne?,Ko cokali bansa ki siyawa Khausar ba kibar min ƴata Ni zan
mata komai”.

Ya ƙarasa maganar cike da kara, mutuntaka, da kuma dattako.

Cike da kunya da jin daɗin karansa Mommy tayi murmushi kana tace.

“Nagode Allah yasanya musu al'khairi duk abinda kace haka za ayi”.

Murmushi yayi kana yace.

“Haka nake son ji ke dai ki sanya Albarka acikin wannan al'amarin”.

Jinjina kai tayi cikin sanyin murya tace.

“Allah yasanya alkhairi”.


*Morocco*

Cikin fushi Dr Jameel ya watsa wa Moddibo Harara kana yace.

“Haka kawai zaka zo kana takura min rayuwa dan bansa ankore kaba?”.

Cikin wani irin yanayi Moddibo yace.

“Korana?,Kasa akoreni J ni kake cewa zaka kora?J Bismillah in baka koreni ba baka amsa sunan ka Jameel
ba”.

Afusace Dr Jameel yaja hannun farkarsa yace.

“Mu tafi Baby”.

Cikin sauri Moddibo yabi bayansa kafin ya fita tuni Dr Jameel yashiga mota, Cikin sauri yashiga motarsa
zaiyi reverse yaga wasu motoci biyu sun taresa dole sai anja daya daga ciki kafin ya samu ya fita Dr
Jameel kuwa tuni yaja motarsa ya tafi.

Da sauri Moddibo ya fito daga motarsa yace.

“Waye wannan yazo ya tare min mota ta ina zan fita”.

Dai-dai lokacin mamallakin Motar yazo cikin sanyin murya yace.

“Ayyah Bawan Allah kayi haƙuri na ajiye mota abayan naka banyi tsammanin zan daɗe ba abu kawai zan
karba”.

Uffan dai Moddibo bai ce da mutumin ba yashiga motarsa yaja ya tafi sannan Moddibo ya shiga nasa
yaja ya fita sai dai ba motar Dr Jameel ba labarinsa gefe da gefen Asibitin ya zagaya amma koda wasa
baiga alamunsa ba.

Komawa yayi da niyyar shiga asibitin security suka hanasa duk yanda yaso shiga sunƙi barinsa cikin
takaici ya juya akalar motarsa kai tsaye Mouley Youssef Hotel Rabat ya nufa cike da tunani iri-iri, yana isa
yayi Parking kana ya fito yashiga cikin harabar Hotel ɗin ya shiga reception kai tsaye ya wuce masauƙinsa
yana ya sa key ya buɗe ya shiga bakinsa ɗauke da sallama

Zama yayi akan 1sitter ya dafe kansa da hannu bibbiyu cikin sauri ya janye hannu ya ɗauki wayarsa ya
kira Number Abba amma har ya katse ba adauƙa ba.

Lokacin da kiran yashiga wayar Abba tuni yayi bacci miss call uku Moddibo yayi ganin bai ɗauka ba yasa
ya haƙura ya jinginar da kansa da jikin kushin yasani koda ace J zaiyi ko wani irin basaja ne aduniya ba
zaiyu ace anyi masa Aure Iyayensa basu sani ba kuma ga duk kan alamu ma wancan karuwa ce domin
tafi kama da karuwai wannan ne ya fara ɗarsa mishi shakku anya wannan J ɗin shi ne kuwa a fili yace.

“Ina inada tabbacin J na ba mazinaci bane, kuma bazai aikata zinaba, shin toh in ba J na bane waye
wannan”.

Kanshi ya daddafe da duka hannunsa yana mai rumtse idanunsa da ƙarfi da kuma ƙarfin yace.

“No J bazai kasance haka, ina ba J ɗina bane kuma J na ko allura bai iya yiba ba abinda ma ya haɗashi da
likitanci”.

Yayi mgnar da cikekkiyar yaƙini da yarda da hakan sabida yanzu ya fara samun nitsuwa, ya gamsu kawai
tsananin kamannine mutumin yake dashi da Jameel ɗinsa wanda hatta sautin muryarsu iri ɗaya ne da J
dinsa.

“Yah Salam. Allah mai iko to waye wannan ɗin".

Yayiwa kansa tambayar da yake masifar son sanin amsarta”.

*Gembila*

Ɓangaren Asma'u da Khausar ma haka suka raba dare wajen hira har misalin ƙarfe uku suna zaune suna
hiransu ta Aminai daga baya suka koma hiran makaranta wani abin idan sun tuna suyi dariya wani suyi
murmushi musamman rigimar kwausar da Modibbo, rayuwa kenan shikenan rayuwar makaranta ta
wuce kamar ba ayiba cikin murmushi Khausar ta gyara zamanta tare da kallon Asma'u kana ta ɗan tsuke
fuska sai kuma tayi kasa da kai cikin juya murya zuwa irin ta Modibbo tace.

“Ke uwar rawar kai”. Sai kuma taja tsaki tare da cewa.

“Ko sunanafa baya kira wai ke”

Dariya sosai Asma'u keyi tare da riƙe ciki, ita kuma Khausar baki ta ɗan taɓa kana a hankali tace.

“Da jajayen lips inshi a wurin kamar balarabe da dunduniyarsa laushi kamar ta jariyai, gashin ƙeya kamar
jikin Mage.”

Cikin nunata da yatsa Asma'u tace.

“Yah Salam ashe har haka akeson Ƴaƴana ban saniba”.

Harara ta watsawa Asma'u tare da cewa.

“Kamar yaya so”.


Tafa hannu Asma'u tayi tana faɗin.

“Toh fisabilillahi in ba soba mai ya kai hankalin da idanunki kan lips inshi harda ƙeyarshi duk yawan sa
hulanshi, shin tukun nama ya akayi kika san dunduniyarsa da taushi, na shiga uku ashe Allah ya tsare
bawan Allah da kin fyaɗeshi”.

Cikin kauda kai dan sai yanzuma taji kunyar kalamaanta a hankali tace.

“Ba wani nan kin dai san kawai ni ina son mai kyau, haka Allah yayini”.

Ta ƙare mgnar tana lumshe idanunta, a hankali ta buɗesu ganin yadda lips enshi ke motsawa in yana
mata masifa.

Haka dai sukayi ta hira mafi akasari kan Modibbo ne yanayi tana kusheshi kushen da yake naɗe da
cikekken yabon halittarsa da ɗabi'unsa.

Washegari da safe Misalin shaɗaya bayan sun gama yiwa Mommy Komai suka shirya suka tafi gidan
Ummi suna isa suka samu komai fes-fes ta gyara har ta gama girki.

Ummi kuwa murmushi tayi ganin su yasa tace.

“Yawwa ƴan al'barka tun ɗazu nake son zamu tafi gidan Abban Jameel nida Innayi, kuma gidan shiru
Bashir ya tafi sabgogin gabansa”.

Khausar na zama tace.

“Ai haka suke Ummi haka ma Haiydar shegen yawo ne da yaran nan”.

Kai Asma'u ta jinjina tace.

“Haka suke kuma idan mutum ya fita na minti biyar su riƙa cewa shine yake yawo.

Murmushi Ummi tayi kana tace.

“Yau ɗauki wannan Asma'u ki ƙaiwa Innayi yanzu na leƙa na samu tana walaha”.

Zare ido Khausar za tayi cikin sauri tace.

“Innayin tana nanne?”.

Da sauri Asma'u tace.

“Ai tunda Yah Modibbo ya tafi Marocco ta dawo nan”.

Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe ta koma ta zauna tare da faɗin.


“Au”.

Ahankali Asma'u ta jawo kular dake gaban Ummi tana buɗewa tace.

“Yau kuma mai akayiwa Innayi?”.

Kallon kulan Ummi tayi kana tace.

“Tuwo nayi mata nasan tanason tuwo”.

Kai Asma'u ta gyaɗa kana tace.

“Ayyah aikam dai”.

Ta ƙare mgnar tare da nufar ɗakinta da kular don nan innayi take.

Anutse Ummi ta maida kallonta kan Khausar cike da kulawa tace.

“Khausar”.

Cikin sanyi ta ɗago kanta tace.

“Na'am Ummi”.

Ido Ummi ta tsira mata kana tace.

“Ahaka za ayi zaman auren?”.

Khausar kuwa da sauri tayi ƙasa da kanta batare da tace Uffan ba yayin da hawaye ke cika mata kwarmin
ido.

Ahankali Ummi ta sake kiran sunan da faɗin.

“Khausar”.

Shiru Khausar tayi sake kiran sunanta ta kuma yi.

Still Bata dagoba numfashin Ummi ta fesar tare da cewa.

“Khausar ɗago mana ki kalleni”.

Ahankali ta ɗago Idanunta dake cike da ruwan hawaye cikin sauri Ummi ta girgiza mata kai kana tace.

“Kar kiyi kuka Khausar insha Allah inaji Ajikina akwai al'khairi a alaƙarki da Moddibo Ubangiji Allah ya
miki albarka”.

Cikin rauni da zubda hawaye ta amsa da Ameen asaman laɓɓanta.


Cikin rarrashi da son kwantar mata da hankali Ummi ta cigaba da cewa.

“Sai kuma batun tsoro ki daina mutumin da kike ƙoƙarin kasancewa ƙarƙashin inuwar Aurensa ai bai
canci irin wannan tsoronba, shi ba Dodo bane Aliyu da kike ganifa yana da mutunci, Kara, tausayawa, da
kuma karamci tsoron da kike nunawa akansa ya tsananta”.

Cikin sanyi ta girgiza kanta muryan ta na rawa tace.

“Ummi baki sanshi bane ba fa”.

Itama Ummi cikin sanyi tace.

“Nasan shi mana Khausar”.

Araunane Khausar ta girgiza kai cikin son Hana kanta kuka tace.

“Ummi baki san saba yana da mugunta fa”.

Kai Ummi ta girgiza kana tace.

“Ba zai miki mugunta ba Khausar in Allah yaso ya yarda Babana bazai miki mugunta ba saboda kin masa
duk kan halarcin duniya”.

Lumshe Idanunta tayi cikin raunin murya tace.

“Ummi baya sona ya tsaneni koda kallon fuskatane baya so tunda muke tare Amakaranta da zaran mun
haɗu zai nemi laifin da zai lika min kawai dan ya dake ni”.

Ta share hawayen da suka zubo mata cikin sanyi ta cigaba da cewa.

“Ummi ina tsoron rayuwa dashi sannan kuma Ummi ina so in cikawa Yah Jameel burinsa Ina so ciki
wannan al'ƙawarin dana ɗauka”.

Ahankali Ummi ta matsa kusa da ita ta janyota jikinta ta Rungume cikin ƙarfafa mata gwiwa tace.

“Kar kiyi kuka Khausar! Kada jiki tsoro! Kada ki damu ki daina tsoron Babana babu abinda zai Miki”.

Ta ƙare mgnar dasa hannunta, amshi wayar Khausar tare da cewa.

“Yanzu bani wayarki in sa miki number's, ko kinada ita?”.

Cikin sauri ta jujjuya kanta.

Ita kuwa Ummi cikin kulawa yace.

“Toh bani wayar, in sa miki, yanzu dai kin san ke matar aurece, igiyoyin aurensa na kanki, banda yawan
yawo, dukda dama nasan baku da yawan yawo".
Ta ƙare mgnar da fara sa mata number Modibbo dan wayarta ba pin, tana gama sa number's ɗin ta miƙa
mata waya.

Amsa tayi tare da kife wayar bisa cinyarta. Ita kuwa Ummi da sauri ta kalleta jin tana cewa...

Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama 1k ne kacal 0661110170
GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N na
09097853276. Kana in tura miki shi kisha karatunki cikin aminci.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

42

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

42

Araunane tace.

“Ummi dukana fa yake sawa ayitayi kawai dan mugunta”.

Cikin sassauta murya Ummi tace.

“Khausar Rayuwar makaranta da ban, sannan rayuwar da zakuyi yanzu shima daban bazai da keki ba”.

Kai ta girgiza still Hawaye na bin kuncinta tace.

“Wallahi Ummi mugunune kobai dakeni ba, zai ta cin zalina, nasani koma mene zaimi. Allah zai saka min
zan jure domin cikawa Yah Jameel Wasiyyar sa”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauke cike da ɗan murmushi tace.

“Kada ki manta Shifa ba jahili bane yana da ilimi kuma shi Modibbo mutum ne da yasan darajar ɗan
Adam. dan haka ki kwantar da hankalin ki, kinji ki daina jin tsoron dubi yanda baki ɗaya kika rame nasan
harda maganar nan yasa kika rame to ki cire abin ki sa a ranki abokin ne yanzu bawai malaminki ba”.

Numfashi Asma'u dake fitowa ta fesar tace.

“Ummi haka jiya ma tayi ta kuka da daddare nima tayi ta sani kuka”.

Still tana jikin Ummi tace.


“Kada kiyi kuka ki saki ranki rayuwar inci zakije kiyi.

ki fara shirye-shiryen ki da zuciya ɗaya Insha Allah zakiyi al'fahari da wannan auren”.

Cikin tura baki tace.

“Ummi ni kuma wani shirye-shirye zan fara”.

Ɗan murmushi Ummi tayi kana tace.

“To ai dole kiyi shiri Khausar dudu yanzu saura kwana gomane dama abinda zai kaimu gidan Abban
Jameel kenan”.

Zare ido Khausar tayi tare da dafe ƙirjinta tace.

“Kwana goma kuma Ummi da sauri haka dama dagaske ne?”.

Cikin murmushi Ummi tace.

“Dama da wasa kika ɗauka ne Khausar?”.

Kai ta girgiza tace.

“Bada wasa na faɗa ba Ummi amma kuma ai da anbari sai na gama karatuna”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauke tare da riƙe tafin hannunta tace.

“Karatu zakiyi agidan mijinki Khausar kada kiji tsoro kinji ko munyi magana ma da Mommy ki kafin ki iso,
akwai wasu kayan turarukan wuta dasu Humra da kullaca, da dai wasu abubuwa da na saya miki a wurin
AYSHA ALIYU GARKUWA, in sha Allah nanda kwana biyu zata gama haɗa miki kayan zasu taho daga
Adamawa, tam ce ta gama komai dahuwar kazane bata gama da kuma zuciyar farin rago su sabida da
rubutu ake haɗasu”.

Shiru Khausar tayi batare da tace Uffan ba, sabida Allah ya sani batayi zaton da gaggawa haka za'ayi
abinba.

cikin dabara Ummi ta riƙa kwantar mata da hankali tana mata nasiyya sai da taga ta nutsu kafin ta Miƙe
da nufin shiga ɗakin innayi ta kirata su tafi.

Sai kuma ta gyara mayafinta juyowa jin Khausar na cewa.

“Ina yini”.

Murmushi tayi ganin innayi take gaisarwa, ita ma Innayin murmushi tayi ganin yadda Khausar ɗin ta
sunkuyar da kanta.

Cikin kula da kauna tace.


“Lafiya lau kishiya ya gida".

Guntun murmushi dake iya sama lebe Khausar tayi tare da miƙe ta kama hannun Asma'u suka nufi
kitchen.

Ummi kuwa ƴar dariya tayi tare da cewa.

“Yauwa Innayi tunda kin fito tafi ko”.

Gyara mayafi Innayi tayi tare da cewa.

“Eh muje”. Nan suka fice suka tafi gidan Abban Jameel a sabuwar motar da ya sayawa Ummi.

Asma'u da Khausar kuwa suka ci-gaba da hiransu.

Suna na isa gidan Abban ta samu Malam Arɗo bayan sun gaisa Malam Arɗo yace.

“Toh jiya da daddare Lamiɗo ya kirani yace biki za'a haɗa dana ƴar wajensa kuma sunce Jumma'a na
sama nema suke so aɗaura auren kunga yau saura kwana takwas nema, toh yace za ahaɗa dana
Khausar”.

Jinjina kai innayi keyi cike da gamsuwa Malam Arɗo ya cigaba da cewa. “Sannan mun gama tattaunawa
da Abban Jameel akan ayi kawai agama tunda dama Jameelu yayi ta jaddadawa cewa ayi ƙoƙari ayi shi
cikin ƙanƙanin lokaci”.

Gyara zama Ummi tayi kana tace.

“Sosai ma ayi kokari ayi haka shiya dace”.

Gyara zama Malam Arɗo yayi kana yace .

“Sannan Alh Bashir yace kada ayi masa batun Auren”.

Kai Ummi ta gyaɗa cikin gamsuwa, shi kuwa Abban Jameel gyaran murya yayi tare da cewa.

“Innayi kada a faɗa masa fa, dan so nake muyi mishi ba zata”.

Cikin gamsuwa Innayi ta jinjina kai tare da cewa.

“Ai kuwa bazata kam suna da yawa kuma ɗin kanku akwai bazatar da zan muku.

Tunda in an ɗaura auren kai mishi ita za'ayi ko?".

Da sauri Abba yace.


“Ni zan kai mishi ita”.

Murmushi Innayi tayi tare da cewa.

“A'a kada ka damu a gayawa dangin amarya su shirya yan rakiyar amarya da basu gaza goma”.

Da sauri Ummi ta juyo ta kalleta tare da cewa.

“A'a Innayi bafa ƙasar nan bane, har Marocco nefa, ya za'ayi ace har mutun goma ai ɗawainiyar zatayi
yawa, wurin sauƙesu ma ai jidali ne”.

Cikin sauri Malam Arɗo yace sosai ma kuwa.

Abba kuwa ido kawai ya zuba musu.

Ita kuwa innayi gyara zama tayi cike da yaƙini da kuma tabbaci tace.

“Kada ki damu Ummin Jameel, ai tuwon girma miyansa nama, kuma in dai masauƙine koda Gambulan
baki ɗaya zamuje bazata rasa masauƙiba. Kana kema zakije Asma'u, Abban Jameel Malam Arɗo, dama
Lamiɗon kansa zaije”.

Murmushi mai cike da nazari Abban Jameel yayi tare da tuno abubuwan da Jameel ya gaya mishi akan
tarihin Modibbo da yace Innayi ta bashi.

Cikin gamsuwa yace.

Kada ki damu Fatima a gayawa mahaifiyar Khausar a samu mutun goma daga gefen dangin kausar na
uwa da uba da ni kuwa zan gayawa Lamiɗo”.

Kai kawai Ummi ta iya gyaɗa musu, domin abin ya bata mmki tunda Modibbo fa ya gaya mata kuɗin
tickets insa na business class 1,303,000 suku tum toh fisa bilillahi wannan kudi ai yawa garesu ace
kusan mutun goma.

Jin Malam Arɗo yace.

“Ai akwai economic tickets, kudinsa bazai kai hakaba ni dashi nake amfani duk inda nake zuwa”.

Jin hakane yasa ta gane ashe mgnar zuci da tayi ya fito fili.

Innayi kuwa kai ta jinjina tare da cewa.

“In sha Allah dai ba abinda zai gagara”.

Abba kuwa cikin nitsuwa yace.

“Kayan lefenta kuwa nasa matar aminina Dr Ahmad zata haɗa komai, wata ƙil ya iso kafin muje".

Da sauri innayi tace.


“A'a a barsu sai munje can mu haɗa ai tunda zamuje da zuriyarta duk zasu gani”.

Da sauri Ummu tace.

“Ayi haka kuwa innayi a tafi da amarya ba lefe, ai za'ayi ta surutai”.

Cikin jinjina kai innayi tace.

“Barsu suyi lokacin sune”.

Nan suka ci-gaba da tattaunawa yadda komai zai wakana.

Tun daga wannan rana suka fara shirye-shiryen biki babu kama ƙafan Yaro.

Aranan da daddare aka kawo kayan Auren Amina kaya sunyi kyau sosai su Hajiya Lami ne suka tarbi
kayan Auren Bayan anwatse Amina ta kalli Samira dake gefenta tayi tagumi wacce baki ɗaya ta rame ta
sauya ta dawo shiru-shiru.

Kallon Samira tayi kana tace.

“Samira wallahi da gaske kin fara wari dan ina jin warin”.

Cikin zubda hawaye Samira ta kalleta Muryanta na rawa tace.

“Allah Amina kina ji ko?”.

Kai Amina ta gyaɗa cikin gaskiya da tace.

“Wallahi Ina ji Amina sai kinji kamar warin Baragurbin ƙwai”.

Cikin raunin murya tace.

“Na sani dole za aji warin kawai Mommy na Idan na faɗa mata sai tace bata ji amma nasan dole za aji
warin”.

Yamutse fuska Amina tayi kana tace.

“Gaskiya dai kam kina warin Baragurbin ƙwai wallahi ki dage ki koma wajen Boka ya baki magani”.

Kai Samira ta Girgiza.

Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya ta shigo Harara ta watsawa Amina tace.

“Ke dai Wallahi Amina baki da hankali amaimakon ki kwantar mata da hankali sai ki ƙara tayar mata”.

Baki ta tura tare da kallon Hajiya Bunayya tace.


“Mommy wannan ba maganar tada hankali bane gaskiya ne kawai ku koma wajen Boka Kar'uzu yayi
ƙoƙarin nemo mata magani”.

lokacin kuma Hajiya Lami ta fito daga toilet dake Bedroom din tace.

“Boka Kar'uzu har yau bai dawo ba daga tafiyar da yayi nima jira nake ya dawo Inje ko shekara jiya naje
ban same shiba.

Cikin rauni Samira ta kallesu muryanta na rawa tace.

“Ni dai da an haƙura da neman Magani awajen Boka Kar'uzu kawai anema min maganin Islamic medicine
ko Allah zaisa adace”.

Atare Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka ce me kike faɗa haka ki dai bari asake gwadawa agani.

Shiru tayi ba tare da tace musu uffan ba.

*Morocco*

Motar Moddibo ce tsaye abakin Mouley Yussef Hospital Rabat kusan kullum sai yazo amma da zaran
security dake bakin gate din ya ga shine zai ki buɗe masa yau kwana biyu kenan yana sintirin zuwa cikin
sanyi jiki ya juya ya koma gida yana so ya faɗawa Abba to amma ta ina zai fara faɗa masa zaice Jameel
ɗinsa ko kuma yaya zuwa wannan lokacin hankalinsa ya gama tashi ya rasa shin wani irin tunani zaiyi
cikin wannan tunanin ya koma gida.

Washe gari: alhamis haka ya tashi cikin matsanancin kasala saboda yanda aka kwana ana zuga ruwan
sama gari yayi sanyi cikin damuwa da ciwon kasala da jin bugun zuciya ya kwana adaddafe ya tashi ya
shirya kai tsaye Company ya nufa ya dudduba aikin da akayi zuwa yanzu gaba ɗaya angama daddasa
Injinan da za ayi aiki dasu alissafinsu Insha Allah ranan Monday za afara bubbuga Nauikan, Abaya, Laffa,
Jallabiya, Sallayu, blankets, Jakankuna, takalma za a cigaba da sarrafa kaya.

Kai tsaye motarsa ya shiga har ya nufi gida sai kuma ya sinci kansa da juya alamar motarsa kai tsaye
Mouley Youssef Hospital Rabat ya nufa yana isa bakin gate ɗin dai-dai lokacin da security ya buɗe wa
wata mota gate wannan damar Moddibo ya samu yayi saurin cinna hancin motarsa ciki.

Yana isa yayi Parking security na ganinsa yace.

“You again”.
Iya abinda ya iya faɗa kenan domin haiba da ƙwarjinsa yasa ba zai iya korinsa ba cike da nutsuwa
Moddibo ya nufa cikin reception duk ido mutanen da Norses ɗin suka zuba masa suna kallon baiwar
kyau nutsuwa da kamala da kuma ƙwarjini da yake dashi.

Kai tsaye Office ɗin Dr Jameel ya nufa yana isa yayi Knowking ahankali idanunsa suka sauƙa akan Dr
Jameel dake tsaye Atsakiyar office Rungume da wata Norse Yana kissing din sassan jikinta cikin sauri ya
runtse Idanunsa tare da faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin,J wai wani irin sauyi ne yazo maka
arayuwar ka”.

Yayi mgnar cikin cushewar tunani duk da ɗabi'in wanda ake kira da Dr Jameel suna bashi cikekken
yaƙinin cewa ba J dinsa bane wannan tsananin kamanceceniya ne. Toh amman kamanin da hatta
muryarsu mgnar tafiyarsu komai iri ɗaya ne da na J ɗinsa yasa ya kasa amincewa kansa cewa ba J ɗinsa
bane wannan.

Cikin fushi Dr Jameel ya ɗago kansa ya kalli Moddibo kana yace.

“Wai kai wani irin mutum ne tunda nace maka ba J ɗin da kake nema bane ka barni mana Meyesa zakayi
ta bibiyar rayuwata?”.

Cikin sanyi Moddibo ya kallesa kana yace.

“Kaji tsoron Allah J! Shin wace irin rayuwa kasa kanka aciki J!? J mata ka fara bi ka maida kanka kamar
kare wanda baisan abinda yake ba J yada ilimin ka zaka maida kanka haka cikin fushin Ubangiji kake so
ka faɗa”.

Cike da ɓacin rai Dr Jameel ya juya ya kallesa kana yace.

“Anyi ɗin idan kana da iko ka hana nace maka Ni ba J ɗin ka ba kabarni inji daɗin rayuwata mana, jikinka
ko jikina rayuwarka ko rayuwata matane dole in bisu inji daɗin rayuwata yoh akwai abinda ya kaisu daɗi
ne”.

Cikin takaici Moddibo yace.

“J baka ji tsoron Allah ba da bakinka kake jaddada min aikin ka cewa zina kakeyi?”.

Harara Dr Jameel ya watsa masa cike da gadara yace.

“Anyi ɗin”.

Dafe kai Moddibo yayi tare da faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.


Cike da takaici Dr Jameel ya fisgo Norse din Wacce da alama ba musulma bace yana janyota ya manna
bakinshi da nata.

Cikinta sauri Moddibo ya runtse Idanunsa da ƙarfi ya kifa kansa da jikin bango yana karanta duk wata
addu'a da tazo bakinsa cikin sauri ya juya ya fita cikin motarsa ya zauna kasa tabuka komai yayi sai
hawaye dake kwaranyo masa cikin ransa yace.

“Na gamsu wannan ba J na bane haƙiƙa ba Jameel ɗin Ummi bane.

Amman wallahi nayi al'ƙawarin in Sha Allah, zan gyara masa rayuwarsa da yardar Allah zai zama tamkar J
dina na baya in sha Allah zaici albarkacin kamaninsa da J ɗina”.

Dr Jameel kuwa bayan sun gama aikata masha'arsu da wannan Arniyar ya shiga toilet yayi wanka yana
fitowa yaji wayarsa na ringing Yana ɗaga wayar yayi Picking tare da kaiwa Kunnensa cike da girmamawa
yace.

“Hello Unclee da kanka kuma?”.

Shiru yayi na wasu sekonni sai kuma yace.

“Toh shikenan ba matsala yanzun nan kuwa ganin zuwa.

Yana katse kiran ya gyara rigarsa tare da gyara zaman Necktie wuyansa.

Juyawa yayi ya kalli Norse din cikin bada umarni yace.

“Idan kin gama ki gyara min office ki rufe”.

Cike da yauƙi tace.

“Ok sir”.

Yana fita yashiga motarsa yaja.

Cikin sauri Moddibo dake zubda hawaye yabi bayansa duk inda ya juya akalar motarsa nan Moddibo
yake bi shi kansa Moddibo baisan inda zaije ba kuma baisan me zaice masa ba, kuma baisan abinda
zaiyiba.

Amman haka nan yaji wani irin amintaccen nitsuwa da salama a ranshi.
Haka nan yake jin farin ciki, tafiya mai nisa sukayi kafin suka wuce Sheikh Zayed hospital tafiya kamar na
kimanin minti goma suka yi suka isa Fadar masarautar ƙasar Marocco baki ɗaya.

Ta cikin jahar Rabat suna isa Dr Jameel Yayi Hong ganin motarsa yasa aka buɗe masa gate ɗin.

farko yana shiga Moddibo ya mara masa baya tare da rumtse idanunsa da ƙarfi sabida harbawar da
zuciyarsa tayi kamar zata haɗin ƙasa. Da sauri ya kuma buɗe idanunsa tare da sauƙesu can sama kan
tambarin masarautar.

Lokacin ɗaya yaji jikinsa ya fara tsuma, kana duk tsikar jikinsa ta miƙe tsaye.

Da sauri ya kutsa kai cikin tare da bin Dr Jameel bamba to bamba yana shiga yaji zuciyarsa ta buga da
Masifaffen ƙarfi wani irin tsuma yaji jikinsa nayi amaimakon yabi motar Dr Jameel da kallo sai ya kuma
bin Cikin masarautar Da kallo daga kan dogon ginin zuwa shimfiɗeɗɗen kwalta da kuma yanda tsarin
yake baki ɗaya ginin zagaye yake da bishiyoyin dabino ta ko ina masu tsawo, da sukayiwa illahirin
ganinsa ƙawanya.

Ahaka suka isa wani babban gate Dr Jameel yayi hong aka buɗe masa yana shiga Moddibo ya mara masa
baya.

Shi kuwa Dr Jameel sabida wayar da yakeyi yasa hankalin sa baya kai kan Modibbo ba.

Sassayyan numfashi Modibbo ya saukeganin yadda hadiman ke zirya da hidima.

Yayinda su kuwa

Fadawa da hadiman basuma ga fuskarsa amman a zatonsu tare yaje da Dr Jameel shiyasa basu hana shi
shigaba.

Suna shiga gate na biyu suka isa dai-dsi kan wani RounAbout mai masifar kyau tsakiyar farfajiyar fadan.
Yayinda hanyoyi guda huɗu suke zagaye dashi, kana gefe-da gefen ko wacce hanya bishi yoyin yan
gajjerun dabino ne, masu ɗauke da yaya ringis a kai.

Kana tsakanin, wanda yake miƙe da ta inda su Modibbo suka fuskanta kuwa wani babban baranda ne
wanda yake da staps goma sha biyu, a staps ɗin forko Hadimai ne, guda biyu gefen hagu da damansa, sai
kuma a steps na shida suma hadi mai biyu sai ana sha biyu su kuma hadimai bibbiyu ne hagu da dama,
wata babbar ƙoface mai kyan gani da daukar hankali da kuma taswirar manomi a cikin kekkyawar gona.

Daga nan cikin RounAbout ɗin kuwa a yalwace yake da shuke-shuke na dukkan samfurin kayyakin da
ƙasar suke nomawa kasancewarsu manomane, daga tsakiya kuma

Mutun butumin wani ingarman Doki da linzaminsan cikin ado na ƙawa kasan dokin kuma zagaye yake da
Grass Capet sai kuma mutum-mutumun mutane biyu da fatanya a hannunsu sai na ɗawisu a gaban
dokin.
Sai kuma ƙanan tituna da suka rabu kusan kashi takwas da alamu duka cikin Masarautar yake daga
saman RounAbout ɗin anrubuta Barka da zuwa Masarautar Mouley da Larabci.

Daga gefe Dr Jameel Yayi parking yana Parking ya fito shima Moddibo ahankali ya ziro ƙafarsa ya taka
ƙasa, da sauri ya rumtse idanunsa tare da dafa ƙahon zuciyarsa sabida jin yadda tsikar jikinsa ya tashi
yammm tamkar wanda aka watsawa ruwan ƙankara atsakiyar hunturun sanyi.

Cikin sauri Dr Jameel ya juya ya kallesa cike da mamaki yace.

“Yah Salam biyoni nan kayi bawan Allah Meyesa zaka bini har nan? Kasan inane nan kuwa? kasan meya
kawo ni nan? kasan me nazo yi? Nace kama san ina ne nan kuwa? Nanfa ba cikin asibiti bane”.

Moddibo kuwa kasa cewa komai yayi saboda yanda tsikar jikinsa ke tashi baki ɗaya ya rasa yanda zaiyi
sai kawai ya ƙanƙame jikinsa yana karkawar tamkar mazari.

Cikin sauri Dr Jameel

ya juya banyansu jin wata murya cikin karaji na cewa.

“Jama'a ku lura *Rinƙas* ya kunce ina Sarkin dawakai yake? *Rinƙas* ya kunce jama'a ku kauceeeeh”.

Cikin tsanani sauri fadawa da sauran jama'a dake zirya a tsakikar suka fara mannewa a jikin bishi yoyin
dabinon domin sanin irin gagarumar illar da Rinƙas keyi a duk sanda ya kubce kuma babu mai iya sarrafa
shi cikinsu sai sarki Dawaki ko Mai martaba Youseep Mouleey da kansa.

Moddibo kuwa jin yadda ake gudu da kuma ganin yadda kowa ke neman mafaka ne yasashi cewa
*Rinƙas*

Yayi mgnar a fili a cikin ransa kuma ya kuma sake cewa.

“Rinƙas a na”.

Yayi mgnar tare da saurin juyawa sabida jin wani irin takun aukuwar ingarman doki lafiyeyye ya nufo
kanshi gadan-gadan yana wani irin gigitaccen suƙuwansa da harba iska tare da barbaza gezan kwataccen
dogon gashin dake kan wuyansa.

Gab-gagab Gab-gagagab Gba-gab, ya nufosa haiƙan ƙadaran.

Dr Jameel kuwa wani irin gigitaccen kara ya sake tare da artawa a guje, ya nufi kam ƙofar fadar.

Yayinda gaba ɗaya hadimai da bayi kuwa duk suka ɗaɗdaura hannayensu a kai tare da rumtse idanunsu
baki ɗaya sabida gaba ɗaya sun gama sadaukarwa sai dai a dauke nuƙurƙushesshen gawar Modibbo.
Shi kuwa Modibbo juyawa yayi ya kalli gabas da yamma Kudu da Arewa na cikin masarautar gaba ɗaya
jama'ar da ke ziryar duk sun manne da jikin bishiyoyin kai kace kadangarune.

Wanda ke gefen damansa ya kalla yadda ya zare ido tamkar zai fiddasu waje.

Bayanshi ya juya ya da sauri jin kukan wani mutun.

Da sauri ya juyo kan zaburarran dokin da yaji an kira da Rinƙas ɗin da yayiwa farin sani a mafarkansa.

Sai kuma ya kuma kallon dottijon da kallo ɗaya zakayi mishi kasan cikekken mahaukacine tubran.

Rinƙas kuwa wani irin gigitaccen haniniya da sukuwa mai bada sautin takunsa mai jawo hankalin
mutane, yayinda daga can baya kuma mai gadin sashin dawakanne ke ihu da kururuwa tare da yin mgn
cikin tashin hankali yake cewa Modibbo.

“Ka gudu! Nace ka gudu zai kasheka fa".

Sai kuma ya ƙara ɗaga murya tare da cewa.

“Sarkim Dawaki taimakon gaggawa”.

Dai-dai lokacin kuma Rinƙas yayi wani iri-iri haniniya tare da harbin iska kana ya baza gashin kan
wuyanshi tare da zura ƙafafunsa na gaba suka tafi suuuwwwh kan Modibbo.

Shi kuwa Modibbo cikin tariyo yanayin da yake rayuwa da dokin a mafarkansa na tsawon rayuwarsa.

Ya ture hular kansa tare da girgiza kansa yayi yadda dokin yayi, kana ya saita ƙwayar idanunsa, cikin
tsakiyar idanun dokin.

Tare da ɗaga tafin hannunsa na dama ya saita kan goshin dokin.

Wanda hakan ne kuma yasa dokin sakin wani hargitstsen haniniyar da saida ta ratsa kunnuwan tsarki da
tawagarsa dake cikin fadar suna zaman yiwa Sarki Jabeer Nuruddeen Gwadabe sallama dan yau yake
shirin komawa Nigeria.

Juyowa mai martaba sarki Youssef Muhammad Mouley yayi tare da kallon gefen da Sarkin Dawaki yake
tare lunshe idanunsa wanda hakan kaɗai ya wadatar ya gane nufin Sarkin.
A can waje kuwa gaba ɗaya jama'ar idanu suka zubawa Modibbo da Rinƙas suna kallon sarautar Allah,
shi kuwa Modibbo.

Lumshe idanunsa yayi tare da buɗasu cikin na dokin.

Wani irin ɗaga sawu sama dokin yayi alamun sarawa da kuma cikekkiyar sanayya yayi Modibbo, kana
yayi ƙasa dasu a hankali ya manna goshinsa da tafin hannun Modibbo.

Shi kuwa Modibbo shafa sumar gaban goshin yayi tare da fesar da sassayyan numfashi.

Mutumin dake gefen sane yayi wani irin sake baki tare da furta Yah Salam.

Dan sai lokacin ya samu damar ƙarewa fuskantar Modibbo kallo.

Dokin kuwa cikin nuna alamun shaƙuwa da sanayya mai tarin yawa, ya rinƙa karkaɗa jelarsa tare da baza
gashin wuyansa da sakin haniniya kana ya fara zaga Modibbo tamkar maiyin ɗawafi.

Shi kuwa Modibbo wani irin mataccen murmushi yake tare da jujjuyawa yana kallon duk inda dokin yayi.

Saida ya zagayashi sau uku, sai kuma ya dawo gabanshi.

A hankali ya sunkuyo haka yasa Modibbo sumbatar wuyan dokin.

Dai-dai lokacin kuma sarki Dawaki ya buɗe ƙofar fadan ya fito da sassarfa ya fara taka steps din.

Shi kuwa Modibbo ɗan buge goshin dokin yayi sai ga dokin yayi ƙasa a hankali ya kwanta tare da
karkarɗa jelarsa alamun so yake Modibbo ya hau kanshi.

Ya ilahi ya mujibatda'awato. Yah Salam, shine kaɗai abinda gaba ɗaya al'ummar dake kewaye da
bishiyoyin suka fara faɗa tare da sauƙowa suka nufo Modibbo.
Shi kuwa Modibbo gashin saman wuyan dokin ya kamo tare da ja,

Haka yasa dokin miƙewa tsaye cike da biyayya.

Shiko Modibbon a hankali ya lumshe idanunsa, sai kuma yayi gaba dokin na biye dashi tamkar raƙumi da
akala.

Duk da babu linzami a wuyan dokin.

Shi kuwa Modibbo ido a lumshe ya juya gefen hagunsa ya fara tafiya yana mai kallon taswirar hanyar
inda zaije ya ɗaure dokin na dawo masa filla-filla kamar yadda yake gani a mafarkansa.

Wannan al'amari yayi masifar sa mamaki da kaɗuwa a zuƙatan al'ummar waje.

Dr Jameel kuwa ido ya zubawa Modibbo.

Yayinda sauran Hadiman kuwa gaba ɗaya hannun suka rinƙa ɗaurawa a ƙirzansu suna ɗan ronƙofowa
kaɗan sunayiwa Modibbo wani irin gaisuwar ban girma.

Sarki Dawaki kuwa cike da al'ajabi da ta'ajjudin ganin yadda wani ke sarrafa Rinƙas ban ya sani duk
duniya shida Abualeey ne kaɗai ke iya sarrafa dokin wato sarki Youseef, ko Ibrahim Mouley baya
matsowa kusa dashi, kana ya sani kusan mutum uku ya kashe a cikin masarautar.

Hakane yasa ya fara sassarfa, amman ina ya kasa iso Modibbo da dokin domin shima da sassarfan yake
tafiya ganin dokin na sonyin sukuwa.

Kana gaba ɗaya mutanen kuma yuuuh sukayi suka bi bayan Sarki Dawaki domin al'ajabin wannan
al'amarin.

Tafiya mai nisa sukayi kana Modibbo yayi kwanan gefen yamma nan ma tafiya mai tsawo sukayi kana
suka ɓullo kan wani ƙaton farfajiya wanda a ƙalla dawakai sun kai ɗari uku zuwa huɗu ke wurin.

Duk inda ka wulga idonka iya ganinka dawakaine a wurin. Shi kuwa Modibbo wata yalwatacciyar hanya
yabi tare da ratsa tsakiyar dawakan ya wuce.
“Iko sai Allah”. Mutumin nan dake ya shelanta tsinkewar Rinƙas da gudu ya nufosu tare da maɗaukakiyar
mamaki a fuskantar.

Shiko Modibbon ratsawa ya rinƙayi har ya isa inda nanne tirken dokin. Ɗaureshi yayi kana ya juyo.

Juyowarsa kuwa itace tasa numfashin Sarkin Dawaki kusan ɗaukewa a fili yace.

“Yah salam”. Sabida ganin kamannin fuskantar Modibbo tayi masifar girzashi, kawai sai ya ɗaura
hannunshi na dama kan ƙirjinsa ya ɗan rusunar da kai, yayinda gaba ɗaya sauran ma haka sukayi.

Shi kuwa Modibbo ratsasu yake a hankali tare da bin hanyar da bata nan ya zo ba, tafiya kaɗan yayi ya
ɓullo kan fadar.

Wanda tuni wasu hadiman sun kuma maye gurɓin waɗancan da suka tafi wurin dokin.

Jiyo alamun takun mutanene yasa ya ɗan juyo, ainkuwa zugar tawagar da ya barine suke biye dashi cike
da girmama.

Bai fahimci komaiba a cikin abinda suke mishi, kawai dai yana bin hanyoyin da ya saba gani a mafarkansa
ne, hakan yasa ya fara taka steps ɗin.

Da sauri wanda yake bakin ƙofar ya tura ƙofar tare da sa hannun sa ɗaya a ƙirji ya ɗan rusunar da kai, ɗai
hannun kuma yayi masa alamun bismlillah ga hanya ka shiga.

A hankali yake takun cike da kamala da haiba, ya kutsa kanshi cikin tamfatsestsen falo na al'farmar da
ƙasaita. Wanda komai na cikinsa ja ne, sai ratsin baƙi, bisa alamu kalan tutar ƙasarsu ce.

Babban falone wanda a ƙalla zai iya ɗaukan mutun sama da ɗari.

Yana shiga Sarkin Dawaki na biye dashi a baya.

Da sauri ya kalli gefen damanshi jin muryar yaron nan da suka haɗu a jirgi na cewa.

“Alhamadullah Abeey kaga ga wanda nacema mun haɗu dashi a jirgi, mai kama da Ibrahim”.

Faɗin hakane yasa duk suka kalleshi sai kuma suka kalli inda yake nuna musu.

Da sauri wani Kekkyawan Mutun mai cikar haiba, kamala, haɗi da ƙasaita ya miƙe tsaye cikin shiga ta
al'farmar dake nuni da shine Sarkin masarautar ƙasar Marocco.
Miƙewarsa tsayence tasa dukkan sauran mutanen kama daga Waziri, Galafima, Wambai, Ɗan Maliki,
Sarkin gida, Sarkin fada, dama gyara kimtsi Sarkin zagi kab suma suka miƙe tsaye cike da zubawa
Modibbo idanu tamkar zasu ɗagashi sama da idon.

Dr Jameel kuwa, muƙut ya haɗiye wani yawu mai haɗe da mmki dan jarabar neman mata shi bai barshi
yayi wani tunani kan kamannin Modibbo da Ibarahim ba koma yace da kawunshi ba.

Sai kuma yace.

“Har nan”.

Moddibo kuwa Jabeer bin Jabeer daya dawo gabanshi yana miƙa mishi hannu ya zubawa ido tara da
bashi hannun.

Shiko Jabeer jawoshi yayi har zuwa gaban Sarkin tare da cewa.

“Ganshifa ko makaho ne ya shafa fuskarsa ya shafa taka ko ta Ibrahim yasan wannan mallakinmu ne shi,
Abeey ba dama na gaya makaba”.

Ya ƙare mgnar da kallon Sheikh Jabeer .

Shi kuwa Sheikh Jabeer wani Gwauron numfashi ya fesar tare da yiwa Ɗan aminin nashi nuni daya
zauna.

Cike da kaɗuwa Sarkin Mouleey ya zauna kana yayiwa dukkan fada alamun su zauna.

Haka kuwa duk suka zauna.

Dr Jameel ne ya ɗanyi gyaran murya tare da rusunar da kai cikin ladab yace.

“Ayi min izini in tashi zan shiga wurin Didi in duba Rahman".

kai Sarkin fada ya gyaɗa masa tare da nuna masa hanya alamun yaje.

Cikin sauri Dr Jameel ɗin ya miƙe da tare da kamo hannun wani ɗan yaron da bazai gaza shekara gomaba
yace “Muje”. Ya ida maganar tare da jan hannunsa suka juya zasu fita.

Da sauri Modibbo ya miƙe tare da bin bayan Dr Jameel.

Cike da mmki ya tsaya ganin fadawan da suka zagayeshi da sauri kana sunkayi mishi zobe tare da baza
manyan rigunansu.

Suka tareshi baya iya ganin Dr Jameel.

Cikin sanyin murya yace.

“Yah haka Ku buɗe min hanya mana zan tafi”.


Da sauri ya juyo jin Muryar Sarkin Zagi na cewa.

“Gyara kimtsi bisa umarnin mai martaba kuyi mishi jagora sashi na musamman”.

Kafin ya fahimci mai kalaman Sarkin zagin ke nufi, sai ji yayi anja hannunsa ba tare da an cire ƙawanyar
da ankayi masaba, yaji sun fara tafiya dashi.

“Ikon Allah wai na zaune ya daɗi".

Shine abinda yake faɗi a ransa yana mai ƙoƙarin ɗago kanshi sama, wai ko zai samu yaga gabanshi
amman ina.

A hankali ya fesar da numfashi sabida tariyo masa da mafarkansa da kwakwalwarsa tayi masa.

Taku yaci gaba dayi da bin sawun Sarkin gida dake jansa wanda ta cikin ƙaton falon sukabi ta wata
babbar ƙofa, tafiya mai tsawo sukayi kana yaji sun fara hawa steps jim kaɗan kuma yaji sun ɓulo ta wata
kusurwar, ɗan gajeren tsaki yaja.

sabida jin tafiyarfa taƙi ƙarewa, kuma mutumin nan yayi mishi riƙon babban ɓarawo, ga ƙattin fadawa da
suka zagayeshi.

“Toh wai me haka”.

Ya faɗa dai-dai lokacin da yaji, an ajiyeshi bisa wata ƙasaitacciyar kujera.

Sai kuma yaga duk sun janye ƙawanyar da sukayi mishi kana suka juya suka fita.

Da ido ya rakasu har suka je bakin ƙofa ga mmkinsa sai yaga mutumin nan da ya riƙo hannunsa yaja ƙofar
da ƙarfi ya ruf....

Muje zuwa, wasa ya jiƙa, karatu dan aka biya kuɗin laranra Littafin yafi ɗadi ba haƙƙin kowa a kanki 1k ne
fa kacal ki biya kada ki kiranta na sata 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min
shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 ki biya in tura miki littafin ki karanta abinki
cikin Salam kana in saki a Group ɗin littafin kusha comments,

Tallah !! Tallah !!
Shahararriyar Marubuciyar nan Ikilima Adam (kyauta daga Allah) wacce ta nishadantar daku a littafin ta
mai suna *Kanwata* , yau ta sake dawo muku Domin tallata muku Littafin mai Suna ( Rai Daya Jan Zaki)
littafine mai kunshe da Butulci , cin amana ,zagon Kasa , soyayya irin ta gani kasheni , aminci da saura n
su basai n'a cika Ku da surutu ba Hausawa sukace Gani yakori ji.

Farashin wannan littafin Naira Dari biyar ne 500 kacal postin biyu a arana banda ranar Juma'a .

Domin Karin bayani Ku tuntubeni a lambata kamar haka (09069080725 ko Kuma + 22953726162 ) wacce
Bata shirya Siya ba kada mu batawa juna lokaci.

Domin aikawa da kudi kai tsaye . 3115484026 ikilima Adam first bank

Turo shaidar biya akan wannan 09069080725 sai najiku.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

43

*TSAYA! TSAYA!!! NACE ki TSAYAKO Sister's* duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu
inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai
tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda
dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot,
sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari
bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing, gawanda basa San anfani da Mai zaku iya
using mg's batare da kunbukaci wani Mai band 😯 wanan new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba
kugane ma idanku, domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi gida

You can check pic👇for the soap reviews🥰

Soap price:4k

maiso ga number's ɗin da zakuyi mgn bani AYSHA ALIYU GARKUWA, zakuyiwa mgn ba, gaban 👇🏻👇🏻👇🏻Ga
ta inda zakuyi magana Whatsapp

08062991549
07046881166

07067210195

Call 08064532391

Instagram:glow_with_mgs

Facebook: mg's skincare

Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki sannan akwai na amare
special Wanda inkinyi using baki Kuma bukatar kiyi Wani gyaranjiki domin keda kanki zaki shaida cewa
fatar taki ta wanku tarwai😍08062991549

Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free

Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏

43

Cike da matsanancin mamaki Moddibo ya tsirawa ƙofar da suka rufe ido, toh shin me hakan yake nufi,
gwauron numfashi ya fesar yayin da abubuwa da yawa suka riƙa dawowa cikin ƙwaƙwalwarsa, cikin
kasala ya jingina bayansa da jikin kujeran kana ya buɗe manyan idanunsa da suka sauya launi.

Ahankali ya shiga ƙarewa tsarin falon kallo, falone mai masifar girma da kyau tun daga farkon falon yake
ɗauke da wasu lumtsa-lumtsan kujeru 4couner tun daga farkon Falon har ƙarshesa kujerune zagaye
dashi ya kasance kalan Golden ne da ratsin milk kana da ɗigon Coffe ga wasu trust pillow kalan Golden
da suka sake ƙawata kyawun kushin ɗin yayin da ƙasan falon ke mamaye da wani lallausan Darduma
kalar Golden da ratsin milk kana da ɗigon Coffe daga can saman P.o.p kuwa wasu irin Gloves ne da akayi
musu dising na ƙawa da alfarma, yayin da Labulayen suma suka kasance kalan Golden ɗin, daga tsakiyar
Falon kuwa wasu stool ne masu azabar kyau guda biyu ɗaya daga farkon falon ɗaya kuma daga ƙarshe
kuma jikinsu duk akwai ƴan ƙananan stoll guda huɗu, wanda za'a iya jansu, iya tsaruwa falon ya tsaru
kana sai can gefen daga gefe kuma dinning area ne mai ɗauke da dining table shima komai goldie ne, sai
daga gefen dama can wata ƙoface dake da ƙawanyar labule, hakama gefen hagu falo ne na al'farmar kai
da ka gani kasan babu ƙaranta a cikin lamarin tsarin komai a fili zai nuna maka anci uban kuɗi a
Masaarautar daga can tsakiya wani shunfiɗeɗɗen steps ne mai faɗi wanda ake shimfi tattausan Carpet
na al'farmar busa alamun akwai wuri na musamman a saman.
Cikin fesar da numfashi ya riƙa juya idanunsa lungu da saƙo na cikin falon, kafin ahankali idanunsa suka
sauƙa akan wasu jerin hotuna masu yawa.

Ware idanunsa yayi ganin wani kyakykyawan Matashi mai masifar kama da shi tamkar an tsaga kara
babu abinda ya raba sa dashi yana cikin shiga ta al'farmar dake nuni da rainon masarautar ce.

A hankali kuma ya dire idanunsa bisa hoton dake gefen.

Wannan mutumin daya gani a fada ne amatsayin Sarki sai kuma wata kyakykyawa mata mai matsakaicin
shekaru.

Zazzafan Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da maida idanunsa dake lumshe kan wasu kyawawan mata su uku
biyu daga ciki zasu girmeshi ɗaya daga cikin kuma da alamun itace ƴar auta sai kuma hoton wani
Kekkyawan jariri da aka ɗaura saitin cinyar Sarki, sai dai bisa alamu haɗa hoton akayi.

Suna zagaye da iyayen nasu, sai kuma ya maida idanunsa kan hoton dake gaba...

Cikin sauri ya miƙe tsaye murya ɗauke da tsananin mamaki da kaɗuwa gami da al'ajabi ya motsa Pinch
lips ɗinsa tare da faɗin.

“Innayi”.

Ganin hoton Innayinsa ɓaro-ɓaro tare dana wannan ahalin duk da kuwa cewa alokacin tana da ƙarancin
shekaru bai hanashi ganeta ba, ko dan yasan hoton a wurinta ne, dan tabbas tana da hoton wanda kuma
hannunta ke riƙe da jariri fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi wanda kuma ta sha faɗi mishi shine a
hannunta a ranar da anka haifeshi akayi musu hoton.

Yatsunsa biyu na yasa ya murza idanunsa ganin ko mafarki yake.

Cikin bugawar zuciya yace.

“Wannan fa innayi ce ba gizo idanuna kemin ba”.

Cikin tsananin al'ajabi ya furta.

“Ya salam Abun Al'ajabi”.

Kafin ahankali ya ɗaga ƙafafunsa da yaji sunyi masa mugun nauyi ya nufi jikin hoton, yayin da
ƙwaƙwalwarsa ke tariyo masa cewa tabbas Innayi nada wannan hoton awajenta.

Da sauri ya dafe kansa tuno kalmarta agaresa da take cewa Kaje sai nazo.

Hannunsa duka biyu ya Sanya tare da dafe kansa lokaci ɗaya abubuwa da yawa suka shiga dawo masa
ƙwaƙwalwarsa kama daga abubuwan da yake yawan mafarkinsu, atsawon rayuwarsa wanda tunda ya
shigo masarautar nan yake ganinsu ra'anul ayn.
da kuma irin kalaman da Innayi ke masa wasu lokuta kana da tsananin kamanninsa da yaron dake jikin
hoton da kuma Sarki wanda Babu bancin dake tsakaninsu wanda zai iya nuna cewa ba mutum ba ɗaya
bane, sai dai shekarun da Sarkin yake dashi wanda shi kuma nashi basu kai haka ba kana hatta ƴan
matan dake zagaye da hoton suna tsakanin kama dashi.

Zazzafan Ajiyar zuciya ya sauƙe akaro na barkatai kana ya tsirawa farcen hannun mutanen dake jikin
hoton idanu wanda baiyi fari tasss ba yayi kalan ruwan ƙasa-ƙasa wanda haka shima nashi yake.

Kansa ne ya shiga juyawa cikin tsananin tarin mmki a zuciya yashiga jada baya yana tafiya da baya da
baya har ya isa jikin kujeran da aka ajiyesa da farko kana ya runtse idanunsa kansa ya dafe da hannunsa
na dama ya fara tunani.

“Shin me yake faruwa dani? Me hakan yake nufi? Ina ne nan? Toh menene haɗina dasu? Meyesa suka
kawoni nan suka rufe ni? Meye nufinsu? Shin ko dai mafarkaina gsky ne?.”

Tambayoyin da yake yiwa kansa kenan.

Cikin sauri ya janye hannunsa dake kansa ya shiga laluma aljihunsa da niyyar ciro wayarsa dan ya kira
Innayi. sai yaji wayam iska ya furzar mai zafi tuno cewa ya barsu acikin amota...

Acan cikin gida kuwa wani hamshaƙin falone me masifar kyau da tsari wanda yaji komai na more rayuwa
daga can tsakiyar falon kuwa wata kyakykyawar Matace wacce take cikin hoton da Moddibo ya gani
Hakimce akan wata kujera ta alfarma.

Yayinda ƴaƴanta ke zagaye da ita a hoton, sunlma suna gefenta sai dai Ba Ibrahim kana babu Rahma,
bisa alamu hira suke cike da shaƙuwa.

Cikin nutsuwa Dr Jameel suka kutsa kai cikin falon da sauri yaron da Dr Jameel ke riƙe da hannunsa ya
janye kana ya nufi gaban matar tare da riƙo hannunta da cewa.

“Didi kin san wani abu kuwa".

Cikin kula da so irin na kakannin a kan jikokinsu ta girgiza mishi kai tare da cewa.

“Toh Sarkin fada, me ka gano kuma, dan na lura in kunzo dai kana son zaman fada”.

Da sauri ya zauna gefenta tare da cewa.

“Didi wlh yanzu na ga wani mai kama da Uncle Ibrahim sai kingani kamarsa ɗaya da Uncle Ibrahim.

Sai dai shi yafi Uncle Ibrahim tsawo da kyau amma Didi babu abinda ya raba su da ace Uncle Ibrahim zai
ɓata toh wlh wannan za'a ɗauka ya maye gurbinsa”.

Cikin sauri da bugawar zuciya. Didi ta kalli Dr Jameel kana tace.


“Jameel waye shi?Akan wayake Hakim ke magana?”.

Ajiyar zuciya Dr Jameel ya sauƙe tare da zama akan Lallausan Darduman dake malale ƙasan tiles ɗin kana
yace.

“Kai Didi gsky nima abin nan yaban mamaki.

Didi yau tsawon kwana huɗu kenan yake bibiyata bansan shiba amma tun ranan farko dana fara ganinsa
yana min kama da wani sai dai na rasa da waye yake min kama ina ta tunani na rasa ganowa sabida gaba
ɗaya lamarin shi ɗauremin kai yadda yake ta nuna ya sanni”.

Sai kuma ya ɗan fesar da numfashi tare da gyara zamansa kana ya cigaba da cewa.

“Na rasa dawa yake min kama baki ɗaya abin ya kwanta min akaina, sai yau da muka zo nan naga na kalli
Fuskar Abualeey, sai na ga suna tsananin kama, sai kuma na tuni Ibraahim ashe dasu yake min kama kai
kamanninsu da Ibraahim ya ƙazanta Didi shin wanene shi”.

Cikin wani irin yanayi na tsananin al'ajabi da tsuman zuciya. Didi ke sauraransa yayin da ƴaƴanta Lalla
Khadijah, da kuma Lalla Hafsat mahaifiyar Hakim wacce take aure a Mexico wanda zuwan kakansu
Sheiyk Jabeer Nuruddeen Gwadabe Joɗa, ne yasa su zuwa dan ganawa da kakansu.

Ido suka tsira Dr Jameel cikin son fahimtar wani abu.

kana hadiman Didi kuwa dake can gefe sunkuyar da kansu sukayi

Dr Jameel kuwa ahankali ya cigaba da faɗin.

“Sannan kuma ashe ban sani ba yana bibiyata, har muka shigo gidan nan”.

Nan ya kwashe komai tun daga haɗuwarsa da Moddibo har zuwa yau ya sanar mata...

Kana ya ɗaura da cewa.

“Sannan kuma Didi ɗazun da Abualeey ya kirani kan inzo in duba jikin Rahma ciwon cikinta ya tashi. Ashe
ban sani ba yana biye dani sannan kuma shigowar da zamuyi *Rinƙas* ya ƙwace ya shigo cikin
Masarauta Didi.

zakisha mamaki idan kika ga yanda yake sarrafa Dokin nan”.

Lokaci ɗaya Lalla Khadijah da Kalla Hafsat suka kalli juna, kana suka juyo cike da mmki suka kalli Didi.

Da bugun zuciyar ta ya sake nunkuwa fiye da kaso tamanin cikin ɗari.

Cikin fesar da numfashi ya cigaba da cewa.


“Kuma kinfi kowa sanin mutum biyu ne ke kaɗai ke iya, sarrafa Rinƙas, ko Ibraahim baya iya zuwa ko
kusa dashi.

Amman shifa kai tsaye ya fuskanci dokin. Didi wlh al'amarin mutumin yayi masifar ɗaure min kai fiye da
yanda kike zato”.

Didi kuwa tun daga lokacin da Hakim ya faɗa mata yaga mai kama da Ibraahim zuciyarta ke bugawa har
zuwa yanzu da Dr Jameel ya dasa ayar mgnar, cikin sauri ta juya ta kalli Lalla Khadija da Hafsat, sai kuma
Rahma data fito yanzu ta kwanta gefenta Lalla Hafsat tana damƙe cikinta.

cikin sauri Hafsat da idanunta ke waje ta kalle Didi kana tace.

“Didi”.

Murya cike da sanyi da bugawar zuciya Didi tace.

“Na'am”.

Sai kuma suka shiga kallon juna alamar maganar ta ratsasu.

Dr Jameel kuwa batare daya lura da yanayin da suke ciki ba ya cigaba da cewa.

“Allah Didi kamannin nasu har ya ƙazanta kamanninsa da Ibraahim is too hight har Abualeey da kansa
abin ya jijjigasa kin kuwa ga Fada? yana shiga fa sai da kowa ya tashi tsaye”.

Didi kam kallonsa kawai take bako ƙyaftawa shi kuwa Dr Jameel cigaba da cewa.

“Kinga Jabeer bin Jabeer shima sosai yayi mamaki saboda naji yana cewa wai sun haɗu dashi ajirgi, dan
sai cewa Abeey yake, Abeey ka ganshi ko babu abinda ya raba shi da Ibraahim kamannin yayi yawa,
nacema zan faɗawa Didi kace kar in faɗa mata hankalinta zai tashi, gashi yanzu yazo har inda take Abeey
wlh jininmu ne. Haka yake ta faɗa yana can yana ruɗe”.

Cikin sauri da yanayin zabura Didi ta miƙe tare da kallon Jakadiyarta da kanta ke ƙasa kana tace.

“Jakadiya maza je ki duba idan Mai Martaba na nan. Kice Ina son ganinsa cikin gaggawa. In kuwa yanada
uzuri a fada, ina fatan ayi min iso”.

Cike da girmamawa Jakadiya ta gyaɗa mata kai kana ta furta.

“Toh”.

Sai kuma ta juya cikin sauri ta juya ta fita Ahankali ta riƙa ratsa tamfatsa-tamfatsan falon har ta isa bakin
ƙofar fadan wayam ba kowa alamar duk an watse.

Cikin Sassarfa ta juya ta koma falon domin sanar mata...


Acan ɓangaren Moddibo kuwa jin ana ƙwala kiran sallar Maghriba yasanshi motsa laɓɓansa yashiga bin
kiran Sallar kana yayi addu'ar da Manzon Allah (S.A.W)ya koyar sai kuma ya furta.

“Ya Salam, shin Mutanen nan me suke nufi dani, suna nufin ba zanyi Sallah acikin jam'i ba?”.

Ahankali ya juya idanunsa akan wannan Corridor dake gefen damansa cikin nutsuwa yabi hanyar yayi
tafiya mai ɗan tsayi ya hango wasu ƙofofi guda biyu gefen hagu da dama ahankali ya murɗa ƙofar dake
gefen dama.

“Ya Salam”.

Ya furta asaman laɓɓansa ganin wani tsarerren falo ahankali ya taka ya shiga ciki.

Sai kuma ya ɗan jujjuya kai, ƙofar dake kusa dashi ya nufa.

Wanda bedroom ne a hankali ya murɗa ya shiga.

Ƙofar bathroom ya sake murɗa yashiga, alwala kana ya fitowa.

Jujjuya ya kai yayi cikin sa'a yaga darduma a shimfiɗe a wata ƴar kusurwa awajen alamar ana sallah
awajen anutse yayi sallar Maghriba awajen kana ya cigaba da addu'oi har aka kira Isha'i, bayan ya idar ya
fito falon farko da aka fara ajiyesa.

Yana isa Idanunsa suka sauƙa akan dining da aka jera abinci kala-kala sai kuma ya juya kanshi hanyar
shigowa nan yaga wasu hadimai guda uku maza suna tsaye.

Ganinsa yasa sukayi saurin sunkuyar da kansu ƙasa kana suka ɗaura hannunsu aƙirji alamar Barka da
fitowa.

Cike da girmamawa ɗaya daga cikin su yace.

“Ranka ya daɗe ga abinci”.

Numfashi ya fesar kana ya tsira musu ido na second biyu tare da cewa.

“Shin meyesa aka tsareni anan?”.

Cike da ladabi da kuma Mutuntawa suke sake sunkuyar da kansu ɗaya daga cikinsu yace.

“Kayi haƙuri Ranka ya daɗe Umarni ne daga mai martaba yace kada mu bari a buɗe maka ƙofa dukkan
abinda kake buƙata akwai shi anan basai ka fita ba”.

Cike da mmki ya kallesa kana ya lumshe idanunsa tare da fesar da iska mai zafi yace.

“Akan me za'a rufeni a hanani fita bayan ina da abubuwanyi”.

Cike da ladabi Hadimin ya sake sunkuyar da kansa wanda da alama shine babban su kana yace.
“Kayi haƙuri In Sha Allah Mai martaba yana nan zai zo wajenka”.

Batare daya sake furta komai ba ya koma ya zauna akan kujeran.

Allah ya sani shi yama rasa shin wani irin tunani zaiyi abu ɗaya dai yana jin wata nitsuwa ta musamman a
jikinshi da zuciyarsa.

Anutse Hadimin ya sake biyo sa tare da cewa.

“Bismillah ka matso ga abinci”.

Kai ya girgiza duk da kuwa yunwa da yake ji amma yanayin da yake ciki bazai iya bari yaci abinci ba.

Ganin haka yasa ɗaya daga cikin hadiman ya nufi jikin Frigde kana ya kawo masa Fruits tare da ajiyewa
akan stool agabansa.

Sanyayyar iska ya fesar daga bakinsa kasancewar sa mai son ƴaƴan itatuwa yasa ya miƙa hannu ya ɗauki
apple ya ɗan fara ci ahankali...

Yayin da hadiman suka koma baya suka ci-gaba da tsayuwar anutse ya ɗago manyan idanunsa dake
lumshe ya kallesu kana yace.

“Ku zauna mana”.

Murmushi sukayi tare da faɗin.

“A'a yallaɓai babu matsala kada ka damu wannan ai aikin mune”.

Da mamaki yake kallonsu kana yashiga tunanin wannan al'amarin ya yake.

Yana zaune yaga wani Hadimin ya turo ƙofa ya shigo yayin da wasu hadimai uku mata ke biye dashi
hannunsu riƙe da manya-manyan Trolley suna shiga suka gaishesa cike da girmamawa kana suka nufi
bedroom ɗin suka buɗe Weldrop suka shirya masa kayan kana suka fito Hadimai matan suka tafi suka
bar namijin.

Shi kuwa namijin cike da ladabi ya durƙusa gabansa tare da faɗin.

“Mai martaba yace ayi maka sannu da zuwa, sannan yace afaɗa maka ka kwantar da hankalin ka ka shiga
kayi wanka ga kaya an kawo maka ka huta zuwa anjima zai zo kugana”.

Tunda ya fara magana Moddibo ke kallonsa jin ya dasa aya yasa shi faɗin.

“Ina buƙatar wayoyina suna cikin mota akawo min ko kuma suzo muyi duk maganar da zamuyi zan tafi
ina da abubuwan yi”.

Cike da girmamawa Hadimin ya furta.

“Kayi haƙuri In Sha Allah zan isar masa da saƙonka”.


Kana ya miƙe ya fita...

Acan cikin gida Side ɗin mai Martaba kuwa Didi ce ke tafiya cikin sasarfa yayin da hadimai biyu ke biye
da ita hannu ta sanya ta buɗe ƙofar falon yayin dasu kuma suka tsaya daga gefe.

Cikin Sassarfa ta ƙarasa shiga cikin falon Idanunta suka sauƙa akan Mahaifinta Sheikh Jabeer, Mijinta
Sarki Youssef Muhammad Mouley, Waziri, Jakadiyar Sarki, Galadima cikin sauri da girmamawa Jakadiyar
Sarki ta miƙa mata hannu alamar tazo ta zauna

Kai ta gyaɗa kana ta zauna tare da kallon Mahaifinta wato Sheiykh Jabeer cikin sanyi da yanayin damuwa
ta furta.

“Abiey meke faruwa? Me nakeji? Kufahimtar dani na kasa fahimtar abinda Dr Jameel da Hakim ke faɗa
min shin gaskiya ne”.

Cikin sauri Jabeer bin Jabeer ya matsa kusa da ita tare da riƙe hannunta cikin ƙauna da shaƙuwa ta Yah
da ƙani yace.

“Didi ina ji ajikina ɗankine kuma tsatsonkine, ina ji ajikina wannan mutumin dana gani ɗankine wallahi
domin babu abinda ya raba shi da Ibraahim kamanninsa da Ibraahim da kuma Mahaifinsa har ya
ƙazanta.

Didi dai-dai da faratunsa irin na ƴaƴan kine”...

Aƙage ta matse hannunsa dake cikin nata kana idanunta cike da ruwan hawaye tace.

“Toh waye shi? A ina yake? kununa min shi?, dan Allah kuyi gaggawan kaini garesa domin idanuwa sun
ƙagu suyi tozali dashi haka zalika kunnuwana su ƙagu suji sautin Muryansa”.

Gyaran murya da Sheiykh Jabeer yayi yasa ta dawo cikin nutsuwarta cike da kamala da tarin nutsuwa ya
furta.

“Fatima ki nutsu mana, ai komai yazo da sauƙi Bi'iznillahi ta'ala ɗan da muka rasa tsawon shekaru, in Sha
Allahu yazo garemu nima kaina na gamsu wannan ɗankine tsatsonkine”.

Numfashi mai martaba ya fesar tare da muskutawa kana ya furta.

“Nima inaji ajika babu haufi babu shakka ko tsoro wannan ɗana ne jini nane Abeey yaron nan Aliyu nane
babu haufi jikina da jinina da zuciyata sun shaida min”.

Sai kuma ya maida kallonsa kan Sheykh Jabeer kana yace.

“Tabbas wannan al'amari ya girmama sai dai kuma yanzu saboda idon Fada da kuma yadda al'amarin
yaja hankalin mutane yana buƙatar sirri”.
Kai Jabeer bin Jabeer ya jinjina tare da sake tuno kamannin Moddibo da kuma Ibraahim Sarki Youseep
Muhammad Mouleey kuwa numfashi ya fesar kana ya cigaba da faɗin.

“Ga kuma yanda ya shigo ya iya sarrafa *Rinƙas* yaja hankalin mutane gaba ɗaya sannan kuma muna
buƙatar tabbatarwa da shi kan al'adun masarautar da sanar dashi dukkan abinda ya dace, dan haka sai
zuwa tsakiyar dare yanda hankalin mutane duk ya kau zamu shiga wajensa dan bincike da tabbatar wa”.

Kai suka jinjina cike da gamsuwa da kalamansa sai kuma ya maida idanunsa kan Sheykh Jabeer tare da
faɗin.

“Abeey Wallahi wannan yaron ɗanane babu ma wani batun tabbarwa inaji ajikina ɗanane tsatsonane
ɗanane da muka rasa tsawon lokaci”.

Cikin fesar da numfashi Sheikh Jabeer yace.

“Ka kwantar hankalinka Youseep na sani amma akwai buƙatar bincike akwai buƙatar mu san wani abu”.

Kai ya jinjina kana yace.

“Toh shikenan”. Kasancewar Sheykh Jabeer abokin Mahaifinsa Muhammad Mouley ne yasa baya iya yi
masa musu.

Galadima da tunda aka fara magana bai ce komai ba, sai yanzu ya fesar da numfashi kana yace.

“Tabbas nima inaji ajikina wannan tsatson mune saboda inba haka ba bai isa ya sarrafa *Rinƙas* ba
sannan kamannin nan yayi yawa kana ku kalli yanda yake bin taswiran gidan nan tamkar yasan wuraren,
wannan yasa nakeda tabbacin da wuya ace akwai wani abinda bai saniba na al'adunmu sai dai abin
tambayar shin taya hakan yakasance”.

Kai suka jinjina cike da gamsuwa kana suka cigaba da tattauna maganar daga haka suka tashi daga taron.

Yayin da Didi kam daren wannan ranan haka ta suku-ku baki ɗaya zuciyarta da nutsuwarta ya tafi izuwa
ga ɗouki da kuma mararin son ganin yaron da akece yana tsananin kama da Ibrahim ɗin ta koda kuwa
abincine ta kasa ci.

Acan ɓangaren Moddibo kuwa yana zaune a inda yake batare daya motsa ba bare kuma yaci abinci
baki ɗaya abin duniya ya ishesa abubuwa goma da ashirin sun haɗe masa, tarin tambayoyin a kansa
sama da dozin wanda innayi kaɗai yakeson ji da ganin yayi mata su, ahaka ya cigaba da zama kafin daga
bisani wata zuciyar ta yanke shawarar ya tashi koda zai iya samun wata ƙofa ta baya da zai fice.

Ahankali ya miƙe tare da kallon gefen daman sa inda ya shiga yayi alwala kana ya kalli falon daga gefe ya
hango wata ƙofa ahankali ya fita idanunsa suka sauƙa akan wani falo na daban shima still yana ɗauke da
ƙofa hagu da dama murɗa ƙofar yayi ya fita anan yaga wani ƙofa hagu da dama sai kuma wani step daga
tsakiyarsu daga can sama shima kofa ce hagu da dama...
Hadimansa kuwa ganin ya fita yasa suka shiga taka masa baya tunda basu da ikon hanasa cikin tsuke
fuska ya kallesu, su kuwa cike da girmamawa ɗayansu yace.

“Ranka ya daɗe ko akwai abinda kake buƙata?”.

Girgiza kai kana yace.

“Um-um babu abinda nake buƙata”.

Kai suka gyaɗa tare da faɗin.

“Toh”.

Tunda basu da ikon hanashi tafiya.

Cike da a nitsuwa yake tafiya har ya haura step ɗin yanda ƙasan yake haka zalika saman yake komai na
ginin iri ɗaya ne sai dai tsarin Furnitures ɗin ne suka banbanta.

Kasancewar suna saman daga gefen dama komai White & Sky blue kalar Sararin samaniya sai kuma daga
can gefen Hagu komai na cikinsa ya kasance Jane da ratsin fari haka nan yakeji kamar anayi ma shi
jagorane.

Cikin fesar da numfashi ya koma kan step ɗin ya tsaya a Balcony yana mai cigaba da kallon tsananin kyau
da tsaruwan wajen tun da yake a iya tsawon rayuwarsa bai taɓa kallon falo mai masifar girma da kyau
irin wannan ba.

Ahankali ya ɗaga idanunsa sama anan ya hango ainihin tsakiyar Fadan.

Babbar Fadace mai masifar kyau da girma akwai wurare daban-daban yayin da Part-part sunfi aƙirga iya
inda idanunsa ke iya hangowa Part-part ne ashimfiɗe sai kuma hadimai da yake hangowa suna zirga-
zirga wanda bazai iya ƙiyasta yawansu ba, ga wani irin wuta mai haske da ƙyalli daya haske ko ina na
cikin fadar tamkar rana kana ga bishiyoyin dabino da mijin gwanda wanda duk ta inda ka cilla ido suke
rausayawa sai zurga-zurga Hadimai keyi.

Ahankali ya juya bayansa daga gefe nan idanunsa suka hango wani garden Mai azabebben kyau daga
can bayan Garden ɗin kuwa wani Swimming pool ne dake ɗauke da ruwa Sky blue ga wasu fararen
kujeru kaman resting Chair dake gewaye da wajen kana daga ƙasa su kuwa Grass Carpet ne da yayi dark
blue Mai azabar kyau yayin da wasu irin tsuntsaye masu kyan gani da daɗin sautin murya ke shawagi
awajen wanda da alama saboda ƙayatarwa aka ajiye su...

Ya ɗauki tsawon lokaci yana kallon wajen haka nan ya tsinci kansa da son ganin wajen domin kallon
wajen yatuno masa da Gembilan sak yanayin tsarin gidansu haka wajen yake sai dai tsarin wannan ba
suda yalwan Furanni haka kawai aransa yaji da ace za'a bashi dama zai ƙawata Ilahirin Fadar da Furanni
saboda arayuwar duniya babu abinda ke sashi farin ciki kamar yai ta kallon Furanni har misalin 11:30
yana tsaye awajen kafin ahankali ya motsa ƙafafunsa jin sun gaji da tsayuwa kana ya gangaro ya dawo
cikin ainihin falon da aka kawo sa...

Yana shiga falon ya zauna akan kujera tare da lumshe manyan idanunsa dake lumshe yana mai sakin
ajiyar zuciya akai-akai.

Zaman sa babu daɗe wa kamar misalin 12:00 yaji ƙaran ƙofa an buɗe.

Jin ƙaran buɗe ƙofa yasa ya buɗe Idanunsa dake lumshe kana yabi wajen da kallo...

Da mamaki yake kallon Jabeer bin Jabeer da suka haɗu ajirgi kasancewar shine agaba.

Jabeer bin Jabeer kuwa cikin ƙaguwa ya maida idanunsa kan Didi da Lalla Khadijah da Hafsat ke gefenta,
tare da cewa.

“Didi shigo kiganifa, Didi dan Allah ki ganshi da kyau fa”.

Sheikh Jabeer, Sarki Youseep Muhammad Mouleey, Waziri Galadima, Sarkin Dawakai, Jakadiya,
Mahaifiyar Sarki Niyna Lalla Khadijah da Lalla Hafsat sai kuma Rahama dake can biya tana biyosu da
sassarfa tare da faɗin.

“Didi ku jirani mana”.

Su kuwa cikin nutsuwa suka shiga cikin falon.

Suna shiga Moddibo ya zuba musu ido cike da mamaki yake bin Didi da Abualeey da wani irin
amintaccen kallo yana mai jin wani irin yanayi na ratsa mishi zuciya a kansu haka nan ya gaza janye
idanushi a kansu sai bugun da zuciyarsa keyi.

Lalla Khadijah da Hafsat kuwa ruggumeshi sukayi tare da sakin wani sassayyan kuka, wannan na gefen
dama wannan na gefen hagu,

Rahama kuma na isa, sai kawai ta kifen kanta bisa guiwowinsa tare da faɗin.

“Yah Aleey laisa leeh misluka abadan, ana uhubbuki hubban azeeman”.

wani irin amintaccen nitsuwa ne yaji yana ratsashi, wanda yasa baisan lokacin da yasa tafukan hannunsa
yana sharewa Lalla Khadijah da Hafsat hawayeba.

Su kuwa Khadijah da Hafsat sai kuma suka ɗan janye jikinsu tare da ruggume juna cike da tsananin farin
cikin.

Ita kuwa Rahama cikin yanayin shogwaɓar ƴan auta take ɗan kuka tare da cewa.

“Yah Ibraahim ina kake kazo kaga Yah Aleey na ya fika kyau daga yauma niba ruwana da kai”.
Dan fesar da numfashi Modibbo yayi tare da sa hannushi yana ɗan shafa bayan Rahama alamun tayi
shiru.

Sarki Youseep Mouleey kuwa cikin kamala ya zauna bisa kujera kana Sheikh Jabeer ma ya zauna gefensa
yayin da Galadima, Waziri, Sarkin Dawakai, suka zauna a ƙasa.

Amintattun Hadiman dake biye dasu kuwa daga can baya dasu suka zauna.

Jakadiya kuwa idanunta akan Moddibo ta saki yalwataccen murmushi mai cike da zallan farin ciki kana
tace.

“Masha Allah nesa ta matso kusa abin nema ya samu”.

Moddibo kuwa idanu ya zuba musu baya ko ƙyaftawa ganin Jabeer bin Jabeer ya zauna aƙasa gasu
Galadima sai shima ya zamo daga kan kushin ɗin ya zauna akan Carpet tare dasa hannunsa yana
sharewa rahama hawaye.

Yayin da yake kallon Sheikh Jabeer cike da mamaki kasancewar ya masa farin sani domin yasha zuwa
wajensa a Adamawa sai dai baya samun haɗuwa dashi cikin tsananin mamaki ya motsa laɓɓansa tare da
faɗin.

“Sheikh Jabeer”.

Sheikh Jabeer na kallonsa tare da mamakin kiran sunan sa ya furta.

“Na'am. Ka Sanni ne?”.

Ware idanu Moddibo yayi kana ya jinjina masa kai cikin sanyi Murya da yanayin nutsuwarsa yace.

“Farin sani ma kuwa shekaran Kur'anin dana rubuta na farko kusan uku awajenka wanda na rubuta daga
baya kuma yayi cika shekara ɗaya awajenka amma har yanzu ban samu an dubasuba.

Batare da Sheikh Jabeer ya janye idanunsa daga kansa ba yace.

“Menene sunan ka”.

Moddibo kuwa ahankali yace.

“Sunana Moddibo daga Taraba nake tura maka wanda aminina Jameel Bashir Mai Dala yake kai maka”.

Baki ɗaya falon ya sake yin shiru baka jin muryan kowa sai na Moddibo da Sheikh Jabeer yayin da Didi da
Sarki Youseep Mouleey kuwa jikinsu ke wani irin tsuma aduk lokacin da Muryan Moddibo ya ratsa
kunnensu.

Kai Sheikh Jabeer ya jinjina kana yace.


“Toh menene cikekken sunanka ai Moddibo ba sunan yanka bane?”.

Lumshe idanu Moddibo yayi tare da buɗe su kana ya shafa sajensa a hankali yace.

“Sunana Aliyu Youseep Muhammad Mouleey”.

Cikin matsanancin mamaki daya sake mamaye zuciyoyinsu da tabbatar musu lallai babu haufi jininsu ne,
akaro na barkatai suka juya suka shiga kallon junansu da ƙyar Sheikh Jabeer ya furta.

“Kace me sunan ka?”.

Ahankali Moddibo ya kuma motsa laɓɓansa tare da faɗin.

“Sunana Aliyu Youseep Muhammad Mouleey”.

Cike da matsanancin mamaki daya daki zuciyoyinsu suka haɗa baki wajen faɗin.

“Ikon Allah sunan ka kenan?”.

Kai ya gyaɗa yana ɗan ciza lips ɗin sa na ƙasa ya furta.

“Eh sunana kenan?”.

Ahankali Sheikh Jabeer ya furta.

“Ikon Allah toh waye mahaifinka”.

Araunane ya jingina bayansa da jikin Kujeran kana ya girgiza kai tare da lumshe idanunsa yace.

“Babana ya rasu!”.

Da sauri Lalla Khadijah tace.

“Wlh mahaifinka na raye gashi nan a gabansa kusa da kai”.

Cikin Sauri Didi ta katse Khadijah ta hanyar daga mata hannun, kana ta juyo ta kalli Modibbo zuciyarta na
cigaba da bugawa da karfi tamkar zai fasa ƙirjinta ya fito ta tace.

“Toh wacece Mahaifiyarka!?”.

Idanunsa cike da rauni ya buɗe ya kalleta kana yace.

“Mahaifiyata ma ta rasu”.

Cikin sauri Rahama tace.

“Ga Didi nan a gabanka a raye waya ce maka baka da mama”.


haka nan yakejin baya son kukan Rahma har ransa, ya kuma lura ta ƙoshi da sakalci cikin sanyi yake
jujjuya mata kai alamun kada tayi kuka.

Sarki Youseep Mouleey kuwa cikin sauri yayi gyaran murya tare da faɗin.

“Toh waya faɗa maka Iyayen ka sun rasu?”.

Moddibo kuwa cikin sanyi da fesar da numfashi ya kallesa kana ya gyara zamansa tare da faɗin.

“Kakata ce ta faɗa min”.

Aƙage Sarki Youseep Mouleey ya kuma cewa.

“Shin wacece kakar ta ka?”.

Ahankali ya ɗaga yatsarsa tare da nuna musu hoton dake manne jikin bango kana yace.

“Gata can Kakata na rasa ya akayi nazo na samu hotonta acikin wannan Fadar taku”.

Cikin jin dadi Jabeer bin Jabeer yace.

“Aha bana faɗa mukuba, ai wlh dama na sani wannan daga gani babu tambaya Aliyu ne”.

Da sauri Didi dake kuka ta matso kusa dashi tare rungumesa.

Shi kuwa Moddibo shiru yayi, sai idanunsa daya lumshe yayin da lokaci ɗaya wani irin yalwataccen farin
ciki ya lulluɓesa alokacin data rungumesa tsintar kansa yayi da ɗaura tafukansa abayanta ya rungumeta
lokaci ɗaya kuwa yaji ruwan hawaye na cika masa idanunsa wanda bai san dalilin zuwan suba kawai dai
yasan yanajin wannan matar da yaranta har cikin ƙahon zuciyarsa hakanan yakeji ya aminta da ita fiye da
aminci da yayiwa ko wacce uwa a duniya.

Haka zalika rungumar da tayi masa ji yayi kamar Innayi ce ta ruggumeshi amman sai yakejin aminci da
son fiye yadda yake ji tare da innayi wannan ruggumar jinsa yayi ruggumace ta mahaifiyar data ɗauki
cikinsa tsawon wata tara da kwana tara ce ta kuma yi naƙudarsa so a matsayin uwa zuciyarsa da jininsa
suka amshi rungumesa da tayi kamar yadda jikinsa zuciyarsa suka amshi Khadijah da Hafsat da Rahman a
matsayin tsotsonshi muharamansa, sabida jini baya ɓuya.

Ji yake tamkar rungumar da yake nemane tsawon shekara da shekaru ne wanda bai samu ba.

Didi kuwa kuka ta saki hadda shesh-sheƙa batare data raba jikinsu ba tace.

“Abeey wallahi wannan ɗana ne. Abba wallahi ɗana ne ku gani taya za'a yi kuce sai kunyi wani bincike?
ɗana ne Aliyuna ne fa Abba ɗana ne fa”.
Kalmar da take maimaitawa kenan tana cigaba da kuka.

Da sauri Sheikh Jabeer ya riƙo hannunta kana yace.

“Fatima kada kiyi kuka na gamsu na kuma yadda ɗan kine kuma tsatsonki ne nima ina ji ajikina tabbas
tsatsonki ne kuma jikana”.

Ya ida maganar yana share mata hawayen daya ƙi tsayawa a idanunta.

Sarki Youseef Mouleey kuwa cikin sauri ya buɗe wa Moddibo hannunsa kana cikin raunin murya da
tsantsar bege yake faɗin.

“Zo ɗana”.

Moddibo kuwa tsintar kansa yayi da gaza yi musu gardama, kana zuciyarsa ta gamsu da kalaman da
suke faɗa.

Yayin da yake jin su ɗin wani sashe ne na jikinsa.

Da wani irin bege da shauƙi ya faɗa jikin Sarki Youseep Mouleey ya rungumesa yayin da shima sarki
Youseep Mouleey ya ƙanƙamesa ji yake kamar idan ya sake sa tamkar zai sake nesa dashi ne ciki rauni
yake faɗin.

“Shakka babu wannan Aliyu nane”.

Kallonsa ya mayar kan Sheikh Jabeer kana yace.

“Abeey wallahi wannan ɗana ne.

Allah sarki rayuwa. Allah ya ɗauki ran Mahaifina yau da yaga jikinsa da zarrar da bai taɓa tunani da zato
ba”.

Baki ɗaya kallonsu mutanen falon keyi cike da tarin tausayinsu.

Sarki Youseep Mouleey kuwa cikin rauni da farin ciki ya sake rungume Moddibo tare da kallon
mahaifiyarsa Niyna yana faɗin.

“Niyna yau da Abbana na raye da yaga Jikinsa da Zarrar da zata girgiza Maƙiya, Da yaga jikinsa da zarrar
da zata sa zuciyoyin maƙiya cikin tashin hankali da firgita tabbas Aliyu ɗana ne Niyna kalleshi fa”.

Kai Niyna take jinjinawa cike da gamsuwa tana mai shafa kan Modibbo.
Moddibo kuwa mamaki da al'ajabi ne ya cika masa zuciya ahankali ya janye jikinsa daga na Mahaifin
nasa kana ya koma ya zauna yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya.

Ahankali ya maida idanunsa kan hoton Innayi kana ya dawo da kallonsa garesu cikin nutsuwa ya furta.

“Wacece wannan awajen ku? Kakata ce wacce da ita nake rayuwa, Kuma ita kaɗai nake da ita a
duniyata”.

Cikin sauri Didi ta girgiza masa kai tare da faɗin.

“Kana da kowa aduniya. Kana da ƙanne, kana da Yayu, Kana da Mahaifi, Kana da Kakanni kakan ka ɗaya
ne ya rasu Mahaifin Babanka, Kana da zuri'a zuri'arka mai tarin yawa gaba ɗaya wannan masarautar
family'nka ne.

Aleey a ina kuke rayuwa?”.

Tun da ta fara magana ya tsira mata idanu yana sauraren ta har sai da tadasa aya kafin yace.

“A Nigeria muke rayuwa acikin Jahar Taraba Gembila” .

Da mamaki ta kallesa tare da faɗin.

“Allah sarki Innayi tana raye?”.

Da sauri ya kalleta jin Sunan Innayin sa abakinta sai kuma ya jinjina kai kana yace.

“Eh Innayi tana raye”.

Still idanunta na zubda hawaye ta furta.

“Allah sarki Innayi tayi min halarci mai yawa ashe wasiƙar data ajiye min da gaske ne ta kular min da
ɗana kula mafi kyawu da inganci”.

Zazzafan Ajiyar zuciya ya sauke kana yace.

“Kin santa ne?”.

Kai ta jinjina masa tare da cewa.

“Na santa Hadima tace da aka haɗani da ita.

Jakadiyata da aka haɗani da ita tun daga lokacin da aka kawo ni ƙasar Marocco, ashe data tashi ƙasata ta
koma da ɗana kusa da Jahata dan ta kular min da ɗana”.

Sai kuma ta lumshe idanunta akan Moddibo kana ta cigaba da faɗin.


“Sannan sai da tayi sanadin yanda ɗana zai kasance mutumi na gari har Alkur'ani mai girma ka rubuta ka
kaiwa Mahaifina ya duba maka”.

Sai kuma ta mai da kallonta kan Sheikh Jabeer kana tace.

“Abeey Ya akayi baka taɓa kallonsa ba?”.

Sanyayyar numfashi Sheik Jabeer ya fesar cike da kamala yace.

“Fatima wannan abubuwane da tattaunawarsu sai ahankali kiyi haƙuri yanzu dai mu fara godewa Allah”.

Kai ta jinjina tana mai yin tasbihi azuciyarta...

Jakadiya kuwa cike da tsantsar farin ciki tace.

“Ai wannan ma babu bukatar wani bin cike ko wani abu tsatso ne na gidan nan, jinine na gidan nan,
haihuwa ne na gidan nan,Tarbiyya ce ta gidan nan,Masha Allah”.

Ta sauƙe Ajiyar zuciya tare da cigaba da cewa. _“Fatabarakallahu Akhsanul Khaliƙin_, Halittace ta gidan
nan daga gani ma babu tambaya tsatsone namu, ina Ibraahim yazo yaga ɗan uwansa da yake cewa yana
haɗuwa dashi acikin mafarkai”.

Haka nan suka ci-gaba da tattaunawa cike da al'ajabi da mamaki wanda mgna ce ta gsky da gsky wacce
gskyarce tayi aikin da dole Modibbo yaji zuciyarsa ta gamsu da kalamansu koda suka fara yi mishi
tambaya kan yadda ya sarrafa Rinƙas ya shaida musu yasan Rinƙas a mafarkine ga mamkinsu dukkan
wasu al'adu ko wani abu na sittin masarautar duk ya sani.

Cike da kulawa Sheikh Jabeer ya kalli Moddibo kana yace.

“Moddibo ka shiga ka kwanta in Allah ya kaimu da safe zamu ƙarasa magana”.

Kai ya jinjina kana yace.

“Wayoyina suna cikin mota ina so akawo min su ina buƙatar mgn da innayi inada tarin tambayoyin da
nakeso inyi mata”.

Kallonsa Sarki Youseep Mouleey kana ya girgiza masa kai tare da faɗin.

“Kada ka damu duk abinda kake buƙata ga hadimanka za'a yi maka sannan duk tambayoyinka ka tarasu
lokacin amsasu nan tafe”.

Kai ya gyaɗa yana mai cigaba da jin nutsuwa su kuwa sallama suka masa kana suka fice.
Nigeria Gembulan

Dai-dai lokacin kuma Naseer ne, zaune tsakiya falonshi wasu hawaye masu zafin gaskene wani ke korar
wani, tunda yaje gidan Lamiɗo, hira wurin Amina da Lamiɗo da kanshi ya sanar masa an daura auren
Khausar da Modibbo ya kasa ƙara sawa cikin gidanma ya juyo ya dawo, kuka yayi tayi tamkar mace har
yanzu ɗaya gaza bari kife kansa yayi bisa guiwowinsa a fili yake faɗin.

“Khausar ya za'ayi jinin haka, duk wani burina da sha'awata a kanki ne, na soki tun baki san kanki ba,
rana tsaka ba zato ba tsammani inji wai an aura miki Modibbo, shike nan na rasaki kenan, domin na sani
yafi ƙarfin iyawata, bani da abinda zan iyayi a kanshi, yayi min zarrar rayuwa ya kwace min ke”.

Sai kuma ya ɗan tsagaita kukan tare da kallon wayarsa da kiran Amina ya shigo, cikin tarin takaici ya
kashe wayar a fili yace.

“Khausar ne kaɗai a raina Amina zan dai aureki ne dan biyan buƙatar rayuwata, da kuma rage jarabar
rashin malakar Khausar ne”.

Haka yaci gaba da surutai kamar zautacce, Allah ya sani baiyi zaton hakaba.

Rabat Marocco

Washe gari tun shida da rabi na safe ƴan uwanshi mata suka shigo a jere, Lalla Hafsat ce riƙe da wani
tray mai ɗauke da wasu ƴan ƙaran kwanuka masu kayan gani, Ragama kuwa wayace makale a kafaɗarta.
inda yake suka nufa, jawo stoll Hafsat tayi tare da ajiye trayn kana ta fara haɗa mishi tea.

Lalla Khadijah kuwa hannun ta miƙe mishintare da yimishi sallama alamun musabaha takeso suyi.

a hankali ya ɗago hannunsa na dama ya miƙa ta, dai-dai lokacin kuma Rahama ta manna mishi wayar
dake hannunta a kunne, tare da cewa.

“Yah Aleey ga Yah Ibraahim daga jiya zuwa yau ya kirani yafi sau goma, wai in ban haɗuka ba yaji
muryarka in ya dawo bazai min mgn ba”.

Ɗan murmushin gefen baki yayi tare da sa hannushi na hagu ya amshi wayar.

It kuwa Rahama cikin jin dadi ta kalli askin kan Modibbo tare da cewa.

“Lah Yah Aleey ko askinkafa irin na ahlin masarautar Mouley ne”. sai kuma ta ƙara sunkuyowa kanshi
tare da cewa.

“Lah Adda Khadi zoki gani, wlh shima yanada naɗeɗɗen gashin irin na Abualeey”.

Numfashi me ɗan tsawo ya fesar ganin Hafsat na miƙa mishi cup ɗin tea da kuma turo masa stoll din
gabanshi tare da cewa.

“Bisimillah Didi tace ka ɗan taɓa wannan kafin ta ƙarasamaka breakfast inka”.
Longwaɓar da kai yayi tare da ɗan yamutsa fuska kana a hankali yace.

“Toh me ɗaya zanyi mgn a waya ko cin abinci ko gaisuwar ku, ko kuma kallon kaina zan bari Rahama tayi
tayi”.

Ya ƙare mgnar da amsa sallamar da yaji anyi mishi da muryar da ta kasance irin tasa sak.

Sai kuma ya ɗanyi murmushi jin Ibraahim na cewa.

“Yah Aleey ka koresu in ba hakaba bazasu Barka ka huta ba fa more especially Rahama Bata da aiki sai
suru”.

Cikin sanyi yace.

“Kana ina yanzu Ibraahim kai ban gankaba”.

Cikin jin daɗi Ibraahim yace.

“Ina Istanbul, nima jiya na tafi da safe kai kuma ka isa da yamma”.

Kai ya gyaɗa tare da kallon Hafsat dake miƙa mishi tea ɗin amsa yayi da hannunsa na dama. Ya lura
kusan halinta iri ɗaya ne da nashi bata da yawan surutu da fara'a sosai sai dai kuma tana da kula.

Lalla Khadijah kuwa miƙewa tayi tare da cewa.

“Bari inje in taya Didi aiki”.

Kai ya gyaɗa mata kana ta fita.

Daga nan yaci gaba da mgn da Ibraahim, tare da kallon Hafsat dake ƙara mishi siymil wani abinci su ne
na larabawan can da fulawa akeyishin sai dai ya wadatu da nama.

Cup din ya miƙawa Rahama tare da kallon Hafsat kana yace.

“Alhamdullah na ƙoshi, kai ta jinjina kana ta tattara wurin tare da cewa.

“Toh kaje ka ɗan kwanta ka huta, ke kuma Rahana zomi tafi".

Kai jinjina mata, daga nan suka fita suka tafi.

Sai misalin ƙarfe 9:30 Didi ce da Sarki Youseep Mouleey suka shiga falon suna shiga suka ji falon shiru
alamar baya nan yayin da suka fara jiyo wani sautin murya mai daɗi da sanya nutsuwa na karatun
Alkur'ani na ratsa kunnensu.
Cikin nutsuwa Sarki Youseep Mouleey ya fara bin direction ɗin da yake jiyo sautin karatun Yayin da Didi
ke biye dashi.

Akan darduma suka hango sa da alama Salatul duha ya idar kana idanunsa na lumshe yana karatun
akansa.

Daga gefensa suka zauna lokaci ɗaya hawaye ya shiga bin kuncinta cike da farin ciki ta ɗaga hannunta
sama kana tace.

“Alhamdulillah Innayi kinyi min duk kan gatan duniya kin bawa ɗana Ilimi mafi girman ilimi mafi tsada da
daraja wanda zai amfanesa duniya da lahira sannan zai amfanemu”.

Sai ta kuma kalli Moddibo still hawaye na kwaranya daga idanunta ta cigaba da faɗin.

“Wannan ɗana ne yake karatun Alkur'ani tamkar acikin harami wanda koda acikin harami sai an jinjina
masa”.

Moddibo kuwa jin sautin Muryanta da kuma motsin Mahaifinsa yasa ya buɗe Idanunsa jin tana cigaba da
cewa.

“Innayi Allah ya biya ki da mafificin Al'khairi Ubangiji Allah ya sadamu inyi miki *SAKAYYAH* da mafi
kyawun abinda ki kayi min sannan inyi miki godiyar da ban san da wani irin baki zan miki ba”.

Ahankali Moddibo ya shafa addu'a kasancewar yazo ƙarshen surar da yake karantawa.

Anutse ya juya ya kallesu haka nan zuciyarsa ta aminta da cewa Tabbas suɗin wasu ababene na jikinsa da
Zaran ya kalli Mahaifinsa zai ga tsananin kamanninsa dashi babu abinda ya raba su shi kansa kamanninsa
da mutumin yana bashi mamaki babu abinda ya rabasu sai dai shi Modibbo yawan shekarun sa bai kai
nasa ba zuwa yanzu ya gama gamsuwa iyayensa ne su.

Cike da ladabi ya gaishe su kana suka amsa cikin sakin fuska da tarin ƙaunarsa.

Didi kuwa ahankali ta janyo basket data shigo dashi ta ajiye agabansa, tare da fitar da kulolin, kana ta
ɗauki plate ta zuba masa abincin da ta dafa mishi da kanta, kana ta kalleshi cike da so da ƙauna tace.

“Wannan abinci da kaina na shiga kitchen na dafa maka dan kaci da kyau”.

Cikin gamsuwa da kalamanta ya jinjina kai ya tabbatar nutsuwa da kamalarta da kuma kimarta tafi ƙarfin
tayi masa ƙarya maganganun da take faɗa daga zuciyarta ne kuma gaskiya ne babu shakka ko haufi aciki
shi kanshi ya gamsu mahaifiyarsa ce ita Abualeey kuwa mahaifinsa ne masarautar Mouley kuwa tabbas
mahaifarsace...

Fuska ɗauke da yalwataccen murmushi Sarki Youseep Mouleey ya janyo Cup tare da faɗin.
“Ni kuma da kaina zan haɗa maka tea in baka duk kan kulawar daka rasa atare damu na tsawon shekaru,
in Sha Allah sai mun haɗa ta mun baka a iya tsawon sauran Rayuwar da Allah ya ƙadddara mana anan
gaba”.

Cikin wani irin tattali da kulawa suka ci-gaba da faɗa masa maganganu masu sanyi da ratsa ƙwaƙwalwa
wanda ko wani ɗa yake fatan saurara daga iyayensa.

Moddibo kuwa tamkar amafarki haka yake jin abubuwan sai dai wani lokaci wani abu ya taɓa ganinsa
amafarki sa.

Haka suka cigaba da kulawa dashi suna hira da kara fahimtar yasan komai ma masarautarsu, yinin
wannan rana suna tare dashi koda motsi yayi zasu tambayesa me yake so ko kuma me yake buƙata sai
gab Azahar suka yi masa sallama suka fita suna tafiya aka kira sallar Azahar...

Anan yayi Sallar Azahar ɗin sa yinin wannan ranan ma ba'a buɗe sa.

Haka yayi kwanaki biyu anan batare daya fita koda ƙofan falon ba sai dai akawo masa abinci sai dai kuma
su shigo suyi hira dashi...

Yau ta kasance Asabar inda ya zama kwanakinsa uku kenan a Masarautar Mouleey bayan fitar
Mahaifiyarsa, Mahaifinsa da kuma Sheikh Jabeer yana zaune a falon kamar daga sama ya fara jiyo shesh-
sheƙan kuka.

Cikin sauri ya juya ya kalli Hadiman dake tare dashi sai kuma ya kauda kansa ganin basu bane cikin
yanayin mamaki da al'ajabi ya juya gabas da yamma kudu da Arewa yaga dai duk basu bane keyi kukan.
Bisa alamu kuma kamar su basujiba, ahankali ya miƙe ya nufi Corridor har ya isa falon nan ma ba kowa
sai dai yana jin shesh-sheƙan kukan daga cikin bedroom cikin sassarfa ya nufi bedroom ɗin yana shiga ya
hangi Jalaluddeen ne zaune agefen gadon yana kuka tamkar ransa zai fita.

Cike da matsanancin mamaki gami da al'ajabi yace.

“Jalaluddeen k...”.....

LITTAFIN SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki
turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 in tura miki kisha karatunki.

GAREKU masu son Maganin infection duk maiso ta biya yau in Sha Allah jibi saƙonku zai taho.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*
SQKAYYAH

44

Tallah !! Tallah !!

Shahararriyar Marubuciyar nan Ikilima Adam (kyauta daga Allah) wacce ta nishadantar daku a littafin ta
mai suna *Kanwata* , yau ta sake dawo muku Domin tallata muku Littafin mai Suna ( Rai Daya Jan Zaki)
littafine mai kunshe da Butulci , cin amana ,zagon Kasa , soyayya irin ta gani kasheni , aminci da saura n
su basai n'a cika Ku da surutu ba Hausawa sukace Gani yakori ji.

Farashin wannan littafin Naira Dari biyar ne 500 kacal postin biyu a arana banda ranar Juma'a .

Domin Karin bayani Ku tuntubeni a lambata kamar haka (09069080725 ko Kuma + 22953726162 ) wacce
Bata shirya Siya ba kada mu batawa juna lokaci.

Domin aikawa da kudi kai tsaye . 3115484026 ikilima Adam first bank

Turo shaidar biya akan wannan 09069080725 sai najiku.

44

Jalaludeen kuwa cikin rauni ya ɗago idanunsa wanda suka zama tamkar garwashin wuta, saboda yanda
sukayi ja-jawur yayin da baki ɗaya ilahirin jikinsa ke rawa kar-kar tamkar wanda aka jona masa Shorking
kuka yake mai shiga jiki tare da ratsa zuciyar duk wani mai imani daya saurara.

Da sauri Moddibo ya ƙara sa kusa dashi gefenshi ya zauna cike da matsanancin rauni da kuma famewar
mikin dake zuciyarsa na rashin J ɗinsa ya shiga rera wani irin raunataccen kuka tamkar ransa zai fita,
kukan wanda bai samu yayi shi ba a lokacin rasuwar, baka jin sautin komai acikin ɗakin, face Shesh-
sheƙan kukan su dake cigaba da wanzuwa aƙalla sun ɗauki kimanin minti goma sha biyar suna kuka
batare da wani yayi yunƙurin rarrashin ɗan uwansa ba.

Cikin dauriya da ƙoƙarin son hana kansa kuka kana da shesh-sheƙa Jalaludeen ya ɗago tafin hannunsa
mai masifar sanyi tamkar wanda aka ciro acikin dusan ƙanƙara ya manna aƙirjin Moddibo daya ke jiyo
bugun zuciyarsa, cikin rauni yace.
“Kayi haƙuri Mouley haƙiƙa munyi rashi mai girma.

Munyi rashi mafi ciwo azuciyarmu. Kayi haƙuri Aliyu kaya femin tsawon lokaci baka ganni ba ina cikin
haramine! shiyasa baka ganniba”.

Lumshe idanu Moddibo yayi wasu hawaye masu masifar zafi suka zubo akuncinsa yayin da sanyin tafin
hannu Jalaludden ke ratsa zuciyarsa Jalaludden kuwa cikin raunatacciyar murya ya cigaba da faɗin.

“Saboda na shiga inayin I'itiƙafi tsawon lokacin nan shiyasa kuma koda na fito munyi tafiya nida Kakana
munje ƙasar Sin shiyasa baka ganni ba bansan Jameelu yashiga wannan hali ba bansan Jameelu ya
rasuba Mouley”.

Sai kuma ya fesar da numfashi mai zafi tare da cigaba da faɗin.

“Sai jiya Juma'a ne naje Taraba domin kai muku ziyara, kasancewar na daɗe ba muyi magana ba yasa na
shirya muku Surprised sai dai kawai ku ganni, toh ina isa gidan innayi na nufa, naje gidan Innayi na samu
babu kowa sai na wuce gidan Ummi”.

Kallonsa kawai Moddibo keyi hawaye na cigaba da silala daga idanunsa.

Cikin rauni Jalaludden yace.

“Acan na samu Innayi suna hiran. Jameel ya rasu kuma na tsinkayi cewa kana ƙasar Morocco, nazo ƙasar
Morocco na bibiyi al'amarin ka har na gane cewa kana cikin Fadar Rabat!”.

Kuka ne yaci karfinsa cikin kuka kamar ƙaramin yaro ya cigaba da cewa.

“Mouley munyi rashi.

Jameel ya tafi ya barmu Allah yajiƙan Jameel Allah yayi mishi rahma!”.

Cikin sanyin murya Moddibo yace.

“Amin Ya Allah. Amman nayi mamaki rashin jinka Jalaladdeen ina ka shiga, tsawon lokaci ba ɗuriyarka.
Na shiga matsanancin damuwa Jameel ɗina ya ɓace tsawon lokaci, bamu sameshi ba.

Naso ace kana kusa damu kayi mana amfani fiye da amfanin da kayi mana abaya ka faɗa mana inda
J.yake”.

Kai Jalaludden ya girgiza still hawaye na kwaranya daga idanunsa ya riƙe hannun Moddibo kana yace.

“Bana kusa Aliyu, sannan kuma koda ina kusa muma kanmu jinnu. Ubangiji bai sanar damu gaibu ba
Aliyu,
da ace Allah ya sanar damu ilimin gaibu ko a inda nake zan iya sani da zan faɗa maka, amma Allah bai
sanar damu gaibu ba.

Sanin gaibu sai Allah kaɗai bansan haka zai faru da Jameel ba.”

Numfashi Moddibo ya fesar kana ya dafe goshinsa da hannunsa na dama tare da faɗin.

“Tabbas munyi rashi mafi girma ban taɓa sanin ya ɗaci da zafin mutuwa yake azahiri ba har sai da na
rasa J ɗina, mutuwar J mutuwa ce da bazan taɓa mancewa ba. Sannan bazan daina jin zafi da raɗaɗinsa
ba har sai ranar dana koma ga Ubangiji na!”.

Kai Jalaludden ya gyaɗa kana yace.

“Sosai ma kuwa Aliyu, amman haƙuri zamuyi, domin babu abinda Jameel yafi buƙata agaremu yanzu
face addu'a addu'ar mu”.

Kai Moddibo ya jinjina tare da cewa.

“Zan cigaba da yiwa J ɗina addu'ar samun rahamar ubangiji har zuwa numfashina na ƙarshe”.

Haka suka kwana suka yini suna hira.

Washe gari da safe koda Sarki Youseef Mouley da Didi suka shiga wajen Moddibo suna tare da
Jalaludden sai dai su basu da ikon ganinsa kasancewar bai bayyana musu kansa ba,

ko Moddibo ba ma asiffar mutum yazo masa wanda sukayi karatu dashi.

Bayan fitansu ya kalli Moddibo yace.

“Kana kama da Mahaifinka”.

Da mamaki Moddibo ke kallonsa kafin ahankali yace.

“Mahaifina ko?”.

Kai Jalaludden ya gyaɗa Fuskarsa ɗauke da murmushi yace.

“Eh Mahaifinka mana, shin ban taɓa faɗa maka cewa kai ba ɗan Nigeria bane, har kaita dariya kana
tambayata to kai ɗan ina bane?”.

Kai Moddibo ya jinjina tuni lokacin suna Jami'atul Madina bayan sun fito daga darasi suna shan shayi
Jalaludden ke sanar masa.

Still da murmushi afuskarsa ya cigaba da faɗin.

“Har kace min kai ɗan ina ne nace kai ɗan Morocco ne, kace ba haka bane.
Amma ni nasan hakane saboda nayi bincike ne akan Innayinka na kuma fahimci haka”.

Zazzafan ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe cikin tsira masa idanu yace.

“Kenan kana nufin nan ƙasatace?”.

Murmushi Jalaludden yayi ta gyaɗa masa kai kana yace.

“Sosai ma kuwa ƙasar kane, tsatsonkane, Mahaifarkane. Wa'annan kuma Mahaifanka ne”.

Cikin girmamawa lamuran Ubangji mabuwayi gagara misali Moddibo yace.

“Ya Salam shin taya akayi wanna al'amarin yakasance ya akayi abin ya faru a haka, abin ne yazo min
tamkar amafarkaina na yau da kullum”.

Gyara zama Jalaludden yayi tare da faɗin.

“Kada kayi mamaki,Ka cire al'ajabi da mamaki acikin lamarin Ubangji ya wuce mamaki. Kai dai kawai kayi
godiya ga Allah”.

Ahankali Moddibo ya motsa laɓɓansayace.

“Alhamdulillah Allah kulli halin”.

Kai Jalaludden ya jinjina haka suka cigaba da hira kafin daga bisani Jalaludden ya kalli Moddibo da
murmushi afuskarsa yace.

“Sannan kuma akwai al'amarin da naje na samu ranan juma'a ya kasance amma bazan faɗa maka ba sai
ka ganin da idonka”.

Ware idanu Moddibo yayi kana ya langwaɓar da kai tare da cewa.

“Jalaluddeen nawa dan Allah ka faɗa min mana”.

Ƴar dariya Jalaludden yayi wanda ya bayyanar da fararen haƙoransa yace.

“Ok naje na samu Ummi ta shiga damuwa sosai akan tsawon kwana uku kenan tana kiran wayar ka
amma bai shiga har Abban Jameel yazo da kanshi dan Maganar dana samu suna tattaunawa da Innayi
kenan”.

Lumshe idanu Moddibo yayi yasan dole hakan zai kasance rashin jinsa awaya zai ɗaga musu hankali
musamman Innayi da Ummi shima Abba sai dai kawai yayi dauriyar maza.

Da murmushi Jalaludden ya cigaba da cewa.


“Ya faɗawa Innayi shima ya kira wayarka baya shiga tsawon kwana uku kenan, amma kuma Innayi sai
dariya take tana ce musu kada su damu kawai afara shirin kawo maka”...

Sai kuma yayi shiru tare da yin mgnar zuci. Alhamdulillah gwara da ban faɗa masa ba saboda naji suna
faɗin cewa Moddibo bai san anyi masa Aure ba..

Ɗan ware idanu Moddibo yace.

“Ana shirin kawo min me?”.

Buɗe hannu Jalaludden yayi kana yace.

“Kai dai ana shiri kawai abinda naji sun faɗa kenan”.

Langwaɓar da kai Moddibo yayi cikin Muryansa mai cike da sanyi yace.

“Kai dai Jalaludden baza ka faɗa min ba kawai”.

Kai Jalaludden ya girgiza kana yace.

“Um-um iya abinda naji kenan, kasan na faɗa maka bansan gaibu ba Allah ne kaɗai mafi sanin gaibu”.

Kai Moddibo ya jinjina cikin gamsuwa da maganarsa yace.

“Toh shikenan”.

Washe gari Litinin ya kama kwanan Moddibo biyar kenan acikin Masarautar Mouley.

Misalin ƙarfe tara na safe Moddibo ne zaune acikin tangamemen Falon kamar yanda ya saba ko yaushe
yaji an buɗe ƙofar falon anutse ya ɗaga kyawawan idanunsa tare da kallon ƙofar.

Idanunsa suka sauƙa akan.

Didi da Sarki Youseef Mouley sai wani kyakykyawan Matashi mai masifar kama dashi kallo ɗaya ya masa
ya fahimci shine Ibraahim ƙaninsa ne da Didi ke yawan bashi labarinsa duba da kamannin dake tsakanin
su. Sai kuma Lalla Khadijah da Lalla Hafsat, sai ƴar auta Rahama.

Ibraahim kuwa yalwataccen murmushi ya sakar masa domin shi yakasance mutum ne mai fara'a da son
Mutane kana da abin dariya

Suna haɗa ido da Moddibo ya ƙara fara'ar fuskarsa kana ya tafi cikin sassarfa ya rungumeshi yana mai jin
farin ciki da nutsuwa agaba ɗaya ilahirin jikinsa cike da shauƙi ya ɗago kansa kana yace.
“Yaya zance maka? Ko kuma Usaini? ko kuma Hassan ɗina?”.

Moddibo kuwa lokaci ɗaya ya tsinci kansa da ƙaunar yaron aransa rungumesa yayi kana cikin ɗan sakin
fuska yace.

“Koma me ka kirani dashi zan amsa”.

Sai kuma suka sake rungume juna yayin da ƙaunar junansu ke ratsa ko wani lungu da saƙon dake
jikinsu...

Cikin tsanananin so da ƙauna Lalla Khadijah tace.

“Kai Ibraahim ka sakeshi haka mana”.

Kalla Hafsat dake ruggume da ɗiyarta ce tayi dariya tare da zama tana kiciniyar bawa baby nono, tace.

“Ai dai kam ya maƙaleshi kamar ya fimu sonshi”.

Didi da Abualeey kam kallonsu kawai suke cike da jin daɗi mata misaltawa.

Rahama kuwa cikin tura baki ta harari Ibrahim cikin yanayin tsamar saƙo-da saƙo tace.

“Ai shi haka yake ga yadda ya maƙaleshi kamar shine auta”.

Cikin jin daɗi Abualeey yace.

“Toh mu zauna dai kafin ai ta yiwa Ibraahim ƙorafi”.

Shiko Ibraahim signal yayiwa Rahama tare da cewa.

“Ai shi nawane ni kaɗai ba dama cewa kike nine bani da ɗan uwaba toh Allah ya dawo min da ƴaƴana
dama yafi Yayunki kyau”.

Lalla Khadijah ce ta ɗan zuggure ƙayarsa.

Ɗan tsalle yayi tare da

ɗago kansa ya kallin Moddibo kana yace.

“Kaga abinda suke minko ko Yah Aleey”.

Murmushi Modibbo yayi tare da ɗan janye jikinshi gefe yana mai kallonsu ɗaya bayan ɗaya yakejin sonsu
da ƙaunarsu na ratsa mishi zuciya.

Shi kuwa Ibraahim baki ya ɗan tura tare da cewa.

“Kayi haƙuri ɗan uwana”.


“A kan me?”. Modibbo ya jefa mishi tambayar.

da sauri yace.

“Sabida rashin dawowata da wuri, sabida ranar da kazo ranar na tafi Turkiyya dan daga nan muke kai
musu dabino, toh nike wakiltan lamarin, koda Lalla Hafsat ta gaya min ji nayi kamar inyi fiffige in dawo
gashi naga dan ban dawo da wuriba kamar kafi sonsu a kaina”.

Dariya sukayi baki daya.

Sai kuma duk suka tsagaita tare da zubawa Modibbo ido ganin yadda yake dariya tare da shafa kan
Ibraahim dan ganinshi yake kamar Bashir.

Didi kuwa da su Kalla Hafsat murmushi dukeyi ganin yadda ya jawo Ibraahim ya ruggumeshi yana mai
cewa.

“Waya ce maka nafi sonsu, suda zasu koma gidajensu su barmu tare”.

Cikin dariya yayi musu gwala.

Rahama kuwa ɗan rawa tayi tare da faɗin.

“Ni dai muna tare”.

Shi kuwa Ibraahim

juyowa ya kalli Didi da Abualeey tare da cewa.

“Dan Allah Didi ku aurar da ita ta bar mana gida mu sake".

Baki ta tura tare da cewa.

“Ba ruwanka da ni”.

Didin kuwa fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi ta kallin ƴaƴan nata dake zaune reras agabanta
kana tace.

“Alhamadullah Allah na gode maka da ka cika min farin cikin ahlina”.

Kai Abualeey ya jinjina tare da faɗin.

“Masha Allah”.

Ibraahim kuwa

janye hannunsa dake cikin na Modibbo yayi kana ya juya tare da kallon Alƙibla yayi Sujudur Shukur.
Kana ya ɗago tare da komawa gefen Moddibo ya zauna still fuskarsa ɗauke da ƙayateccen murmushi ya
kalli Sarki Youseef Mouley tare da faɗin.

“Abualeey Addu'ar mu ta karɓu Ubangiji ya dawo mana da Yah Aliyu alokacin da bamuyi zato ba sannan
ba muyi tsammani ba sai nake ji kamar gaba ɗaya burikana na duniya aka gama cika min dan ganin ɗan
Uwana kuma gudan jina”.

Kai Sarki Youseef Mouley ya gyaɗa kana yace.

“Tabbas kuwa domin babu abinda ya gagari Ubangji Allah da kansa yace mu roƙeshu zai amsa mana.
Domin shi addu'a ba'a gaggawa dashi”.

Moddibo kuwa cike da tsananin so da ƙaunarsu dake ratsa ko wani magudanan jinin jikinsa yace.

“Tabbas kuɗin kun kasance min. Garkuwa ne atare dani ina jin ajikina babu abinda zanyi face godiya ga
Allah daya haɗani daku kafin na koma garesa”.

Haka suka cigaba da hira tsawon lokaci ganin suna shirin tafiya yasa Moddibo ya sunkuyar da kansa ƙasa
kana yace.

“Ayyah Abba dan Allah Ina bukatar wayoyina akawo min su”.

Murmushi Sarki Youseef Mouley yayi kana yace.

“Kada ka damu za'a kawo maka wayoyinka dan suna hannu na”.

Cikin sauri da mamaki Moddibo ya kallesa tare da faɗin.

“Abba toh a taimaka min dasu Ummi, Innayi, da Abba zasu nemini, musamman ma Innayina zata shiga
damuwar rashin jina?”.

Kai Sarki Youseef Mouley ya girgiza kana yace.

“Kada ka damu In sha Allah babu komai rashin ɗaukar wayar yana da muhimmanci, da amfanin da zaiyi
Kankane yace kada a ɗauki wayar shiyasa ma ban kawo maka ba”.

A ladabce Moddibo yace

“Abba zasu shiga damuwa saboda zasuji tsoro kada abinda ya faru da Jameel nima ya faru dani”.

Cike da kulawa Sarki Youseef Mouley yace.

“Wanene Jameelun naka?”.

Idanunsa ya lumshe tare da buɗewa kana yace.

“Ai wannan Dr Jameel ɗin dana biyo, da fari ina bibiyarshi a zatona J nane sabida tsananin kamar da
sukayi”.
Nan ya shiga basu labarin Jameel da duk abinda ya faru dashi.

Ya ɗaura da faɗin.

“Shiyasa lokacin da naga wannan Dr Jameel baki ɗaya na ɗauka cewa Jameelu na ne saboda kamanninsu
yayi yawa, hatta maganarsu, tafiyarsu, muryar su babu abinda ya raba su sai dai ɗabi'unsu ya samu
bambanci dana Jameelu na”.

Cikin raunin murya da tunowa da Jameelunsa ya basu cikekken tarihin abotarsu.

Sosai suma suka tausayawa masa tare da yiwa Jameelun fatan samun rahamar Ubangji kana ya cigaba da
faɗa musu cewa aikine ya kawo sa kamfanin Baban Jameelu.

Cikin fesar da numfashi Ibraahim yace.

“Allah sarki Yah Jameel Allah ya gafarta masa”.

Cikin sanyi Moddibo yace

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.

Lalla Khadijah ce ta gyara zama tare da fuskatarsa kana a mutunci tace.

“Da fari dai kaga iya mu yamune cikin mahaifiyarmu da wasu daga cikin amintattun fadane, suka san da
isowarka wacce dole labarin ya bazu cikin Faɗa, to Alhamdulillah zan haɗa taro na musamman damon
gabatarda kai a tsakiyar family'nka wato zuriyar sarki Aliyu Mouley, wanda zuriyace ta tun kakannin
Abbanmu da kuma kakanninmu, mu da kuma iyayenmu da ƴan bappanayenmu dama goggoninmu, in
Sha Allah zayi tarone na musamman dan dan haka ka shirya fuskatarta idanu mabanmanta.
Alhamdulillah na gamsu da nitsuwarka zuwa yau kuma na fahimci kasan komai na tsarin al'adunmu da
nake mamakin yadda akayi ka sansu”.

Da sauri Kalla Hafsat tace.

“Ke kuwa Lalla Khadijah ya za'ayi ya rayu da jakadiya kiyi tunanin akwai wata al'adar da bazai saniba”.

Murmushi Modibbo yayi domin shi dai innayi bata taɓa alaƙantashi da labarin fadaba, sai dai yasan
komai na fadar ne a cikin mafarkansa.

Abualeey ne ya gyara zama tare da cewa.

“Zuwa yanzu mun gama shiryawa komai na taron”.

Haka dai sukaci gaba da tattauna lamurran.

Washe gari ranan Asabar misalin ƙarfe uku na yamma Jirginsu Innayi yayi landing a _Rabat Sale
international airport_.
Suna sauƙa a airport motocine na alfarma guda biyar suka zo ɗaukar su bisa jagoranci Dr Ahmad abokin
Abban Jameel.

Mota ta farko Dr Ahmad ke driving yayin da Abban Jameel ke gefensa daga can baya kuma Innayi ce tare
da Hajja Nana da kuma Khausar.

Motar dake bima sa kuwa Ummi ce da Hajiya Bunayya sai kuma ƙanwar Momyn Khausar Aunty Hajara,
sai Haiydar da yake gaba gefen direba.

Yayin da mota ta uku kuwa Asiya, Asma'u ce tare da Dija. Sai Aunty Ruƙayya ƙawar Mommy

Motar dake bayansa kuwa Baffa Jimeta ne da matarsa Hajiya Umma, kana da Babbar Ƴar sa mai suna
Aunty Hawwa .

Yayin da motocin ke tafiya ajere cikin nutsuwa bisa Jagoranci Dr Ahmad

Bayan sun shiga cikin gari sun nufi unguwar Ben slimane, cikin sauƙe numfashi Innayi ta fesar da
numfashi tare da buɗe Idanunta ta kalli cikin garin da tsarukan da kuma gine-gine suka sauya alamar
garin ya sake samun cigaba fiye da da.

Cikin sanyayyar murya me cike da kewa da kuma bege ta kalli Dr Ahmad dake driving kana tace.

“Mubi ta unguwar El'gara sai mu ɓullo ta cikin Ben Ahmad dan Masarautar Rabat zamu nufa”

Cikin wani amintacciyar murmushi Abban Jameel ya juya ya kalleta kana yace.

“Kai tsaye kuma?”.

Kai ta jinjina kana tace.

“Eh can zamu nufa shine abinda yafi da cewa”

Still Idanunsa na kanta yace.

“Amma da ya kamata mu fara isa masauƙi mu huta tukunna!”.

Numfashi ta fesar tare da faɗin.

“A'a ai acan ya dace muyi hutun”.

Kai ya jinjina tare da faɗin.

“Toh shikenan”.

Shi kuwa Dr Ahmad juya akalar motar yayi, kana suma saura suma mara mishi baya.

Nan suka ci-gaba da tafiya cikin nutsuwa still motocinsu na jere.


Suna isa ƙofan Gate na farkon Masarautar Rabat ganin motoci ajere yasa cikin Sauri Hadiman dake
bakin gate ɗin mutum biyar suka miƙe biyu suka tsa gefen damar motan biyu gefen hagun motar kana
ɗaya ya tsaya agaba.

Cikin nutsuwa da yanayin jikin girma Innayi ta sanya hannu ta buɗe murfin motar kana ta fito yayin
hannunta ke riƙe da wani abu kamar murfi kolbar Vaselin sai dai bisa ga alamu ginannene kana anyi sa
da hatimin Masarautar.

Wanda ke kusa da ita ta miƙawa.

Karɓa yayi ya duba kana yayi saurin kallon fuskarta sai kuma ya juya ya miƙawa na gefensa shima ya
karɓa ya duba.

Da wani irin sauri suka ɗaura hannunsu asaman ƙirjinsu kana suka sunkuyar da kansu alamar
girmamawa.

Kai ta jinjina musu.

Kana cikin sassarfa suka juya tare da buɗe musu Gate ɗaya daga cikinsu ya tsaya abakin Gate yayin da
sauran huɗun suka marawa moticin baya cikin sassarfa suna isa Gate na biyu ɗaya daga cikin masu binsu
yayi saurin buɗe musu Gate ɗin suka shiga kai tsaye har harabar fadar suka isa, suna isa sukayi Parking
atare.

Acan motarsu Hajiya Bunayya kuwa Haiydar wani irin zazzafan ajiyar zuciya ta sauƙe mai nuni da zallan
mamaki kana ta kalli gabas da yamma kudu da Arewa wani irin daular duniya da suka shiga wanda ya
kamata akirasa da Aljannar duniya cike da al'ajabi ta maida idanunta kan Ummi kana tace.

“Toh nan kuma ina muka zo haka”.

Lallausan murmushi Ummi ta sakar mata kana tace.

“Nan gidansu Moddibo muka zo gidan Mahaifinsa”.

Dariyar sheƙiyanci Hajiya Bunayya ta saki tace.

“Kai lallai wannan ta tsuniya yawa ne dashi nan ɗin ne gidansu Moddibo?”.

Kai Ummi ta jinjina tare da faɗin.

“Toh ki zuba ido ki gani”.

Baki ta taɓe tare da yiwa Ummi wani kallo kana tace.

“Caɓ amma Ummin Jameel banyi zaton haka daga gareki ba da girmanki”.
Ta ida maganar tare da ƙyalƙyalewa da dariya ita baki ɗaya ma maganar dariya yake bata yo ai ko
amafarki Moddibo bai isa ya kasance jinin wannan ahali ba mutumin da ake kyautata zaton ɗan shegene.

Ummi kuwa da mamaki ta kalli yanda take dariya kana tace.

“Kina mamaki ne?”.

Hajiya Bunayya kuwa cikin taɓe baki tace.

“Sosai ma kuwa ai ba mamaki ba harda Al'ajabi na haɗa Moddibo fa”.

Sai ta kuma fashewa da dariyar sheƙiyanci data tuna wai Ummi tace nan gidansu Moddibo ne.

Kai kawai Ummi ta girgiza batare da tace Uffan ba tana mai bin baki ɗaya ilahirin gidan da kallo.

Acan Motarsu Asma'u kuwa cikin zumuɗi da ganin tsantsan kyawu da tsaruwan gidan Dija tace.

“Ehyeh”.

Asiya ma kallon coumpund ɗin tayi cike da shauƙi tace.

“Wowwww Masha Allah kaga wani daular duniya”.

Asma'u kuwa dogon numfashi taja tare da fesar wa tare da faɗin.

“Toh Masha Allah wannan al'amari da ban mamaki yake”.

Motocin kuwa re ras suka tsaya.

Fadawan dake tsaye bakin Fadar kuwa cikin sauri suka nufo motocin wanda aƙalla sun kai biyar isowarsu
yayi dai-dai da fitowar Innayi daga motar.

Sarkin ƙofane idanunsa suka sauƙa akanta cikin sauri ya mutsi-stika Idanunsa kana ya sake kallonta sama
da ƙasa cikin al'ajabi da mamaki tu'ajubi yace.

“Innare Jakadiyar Gimbiya Ruƙayya?”.

Murmushi Innayi tayi kana ta gyaɗa masa kai tare da faɗin.

“Eh”.

Duk da yawan shekaru kuwa sun gane juna

Cikin wani irin sauri ya juya tare da nufar cikin Fada yana shiga ya durƙusa agaban Sarki duk da cewa
yana tare da mutane na hannun damansa suna tattauna akan al'amarin Moddibo da yanda zasu
bayyanar dashi a Masarauta ga yan uwansa.
Ganin yanda ya gurfana ne yasa Sarkin zagi cewa.

“Hattara dai Sarkin Ƙofa, mene tafe da kai?”.

Cikin rawan murya tare da tsantsan farin ciki yace.

“Al'amarine mai girmane yake tafe dani”.

Duk idanu mutanen Fadan suka zuba masa ganin yanda fuskarsa ke ɗauke da tarin zumuɗin isar da
labarin.

Sarkin Fada kuwa cike da kulawa yace.

“Shin wannan wani al'amari ne?”.

Aƙage Sarkin ƙofa ya sake risinar da kansa kana yace.

“Ina so abani izini ne nayiwa Innare Tsohuwar Jakadiyar Gimbiya Ruƙayya iso wacce ta ɓace tare da
Alieeyu tsawon shekara talatin”.

Wani irin murmushi Sarki Youseef Mouley ya saki mai cike da zallan farin ciki da jin daɗi acikin ransa
yace.

Alhamdulillah ta amsa kiranmu kenan lallai wannan ya nuna ta riƙe mana ɗanmu da amana da aminci
bata kuma wofintar da al'amuran sa ba tana bibiye dashi, yanzu tsawon kwanaki biyar bataji labarinsane
ta bibiyi al'amarin sa gashi ta nufo nan ne kuma da yaƙinin cewa tabbas daya shigo ƙasar nan zai dawo
Mahaifarsa.

Afili kuma murmushi ya sakarwa Sarkin Ƙofa kana cike da nutsuwa da kamala kana da ƙasaita irin na
sarauta ya masa alama da hannu ta shigo...

Cikin sauri Sarkin Ƙofa ya miƙe kana ya fita kallin Innayi dake tsaye jikin mota yayi tare da faɗin.

“Bismillah”.

Innayi kuwa juyawa tayi tare da kallon su Abban Jameel kana tace.

“Ku ɗan yi haƙuri ina zuwa”.

Su kuwa baki ɗaya cike da ɗumbin mamaki suke kallonta.

Cikin sauƙe numfashi Hajja Nana ta gyaɗa kai tare da cewa.

“Toh mu dai munfi karfin saiduwa, koda an kawo mu nan da za'a sayar damu ne bazamu saiduba”.
Sai kuma ta juya ta kalli Khausar dake zaune gefenta wacce idanunta suka kumbura sukayi ja jawur
gashin idanu suka jiƙe yayin da suka ƙara tsayi kallo ɗaya zaka mata ka tabbatar tasha kuka tamkar mai
isarta cikin taɓe baki tace.

“Toh kuma kukan me kikayi tunda, ai burinki ya cika, ba dai auren wanda ba'asa asalinsa ba, ai gashi dai
kinga kuma wata duniyar da aka kawo mu, ko mai za'a ce mana ko mai za'a mana kuma oho domin
wannan al'amari dai yafi kama da almara”.

KhausarMouleey ya jinjina tare da faɗin.

“Ai nan Fada ce mai mutunci da karrama baƙo”.

Sake sunkuyar da kanta tayi kana tace.

“Ranka ya daɗe baƙin suna da yawa”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Koda ace baƙi ɗaya Yan yanki da kuke kika ɗebo ba zasu rasa muhalli acikin wannan Masarautar tamu
ba”.

Lallausan murmushi ta saki tare da jinjina kai kana tace.

“Toh abani jagora wanda zai kai mu masauƙin baƙin namu.

Kai ya jinjina kana yace.

“Toh shikenan babu damuwa”.

Kallon Jakadiyar sa yayi tare da faɗin.

“Jakadiya Bismillah akai su sashen Yamma a saman za'a sauƙi”.

Bi'ana saman inda Modibbo yake kenan

Sake sunkuyar da kai Innayi tayi tare da faɗin.

“Ranka ya daɗe Akwai maza tare kuma damu mata”.

“Baki da matsala”.

Ya faɗa tare da kallon Sarkin Ƙofa kana yace.

“Kai kuma ka kai Mazan Ƙofan Gabas”.

Kai ya gyaɗa cike da girmamawa yace.

“Toh”.
Kana suka fice yayin da Jakadiya ta yiwa Innayi, Hajja Nana, Ummi, Hajiya Bunayya, Asma'u, Asiya, Dija,
Khausar, Aunty Hawwa da Hajja Umma Baki daya bayan Jakadiya suka bi tayi musu Jagora.

Yayin da Abban Jameel, Baffa Jimeta, Lamiɗo, Haiydar suka bi bayan Sarkin ƙofa wani babban Hanya
suka bi kana suka hau Upstairs

Suna haura wa saiga wasu Ƙofofi biyu ɗaya aɓarin dama ɗaya aɓarin hagu Jakadiya takai su Innayi ƙofar
dama yayin da Su Abban Jameel aka kaisu ƙofan hagu ta can gefen yamma wanda bata cikin falon da
Modibbo yakeba suka ɓula ba sai dai in zadu sauƙo in sunbi ta ƙofar tsaki ta cikin falon zasu bulla...

Jakadiya kuwa tana fita daga masauƙin su Innayi kai tsaye ɗakin Didi ta nufa tana shiga falon ta zube
agaban Didi tare da faɗin.

“Albishir”.

Fuska ɗauke da murmushi Didi tace.

“Goro”.

Sake risinar da kai Jakadiya tayi kana tace.

“Fari ko Ja?”.

Still Didi na murmushi tace.

“Faro soll Dan ƙwalele”.

Washe baki Jakadiya tayi tare da cewa.

“Toh Innare na cikin Fadar Masarautar Mouley ta iso tare da al'umma baki, daga cikinsu akwai masu
tarin kamala da Alkunya kana tazo mana da kyakykyawan furanni masu haska gida”.

Didi kuwa cikin matsanancin farin ciki da jin daɗi ta miƙe kana tace.

“Masha Allah Alhamdulillah ta ina take, muje ki kaini gareta”.

Kai Jakadiya ta girgiza cike da ladabi tace.

“Amma da kiyi haƙuri ki koma ki zauna yanzu dai, farko a fara Marabtansu da abubuwan motsa baki
saboda sun ɗebo hanya sannan asanar da hadimai afara yi musu girki na musamman domin maraba”.

Cike da gamsuwa Didi ta jinjina kai kana ta kalli Hadimanta dake durƙushe ƙasa tace.

“Maza kuje ɓangaren Hadiman dake Kichen kuce maza ashirya abinci na alfarma yanzu”.

Cike da ladabi suka amsa kana suka fita.


Didi kuwa cikin wani irin farin ciki da annashuwa kana da jinjina girma da mutuntaka irin na Innayi ta
kalli Jakadiya tare da faɗin.

“Maza ashirya musu drinks, Fruits, Snack's,da ɗan gashshen nama sannan akwai nono mai sanyi da
kwakwa ahaɗa musu”.

Ta ƙare mgnar tare da kallon Lalla Khadijah sai kuma tace.

“Khadija keda Hafsat ku jagoranci aikin”.

Kai suka jinjina kana atake suka haɗa suka kai sashen su Innayi da kuma sashen su Abban Jameel...

Acan ɓangaren su Hajiya Bunayya kuwa tunda tashiga tangamemen Falon da yaji komai na more rayuwa
take kallon komai cikin ƙunan zuciya mamaki da kuma tarin takaici....

Innayi kuwa suna zama ta kamo hannun Khausar da har zuwa lokacin take shesh-sheƙan kuka kana ta
riƙo Asma'u yayin da Ummi ke biye dasu suka nufi ɗaya daga cikin ɗakin da yake 3bedrooms ne.

Ƙofar da shine na tsakiya suka shiga.

Suna shiga ta saki sassayyan numfashi tare da sakin hannun Khausar sai kuma ta zaunar da ita gefen
gadon kana ta juya ta fita.

Fitanta yayi daidai da shigowar Hadimai mata suka shigo da Fruits suka ajiye cike da girmamawa suka
gaishesu kana suka ce...

Gimbiya tace ayi muku sannu da zuwa sannan ga abubuwan motsa baki kuci kafin ta iso.

Godiya sukayi kana sukuma suka fice ba daɗewa suka sake dawo wasu hannunsu riƙe da drinks,wasu
Snack's wasu dambun dabbi da soyayyu.

Yayin da Lalla Khadijah da Lalla Hafsat ke riƙe da wasu Bowls manya da yaji Kindirmo da kwakwa da
ayaba suka ajiye.

Cikin tsura musu ido Innayi ta kalli Lalla Khadijah kana ta juyo ta kalli Lalla Hafsat.

Sai kuma ta saki murmushi gani sun ruggumeta cikin bege da kewarsu Innayi tace.

“Allah mai iko da buwaya Khadijah kune kuka girma haka”.

Sai kuma ta kalli Lalla Hafsat dake faɗin.

“Innayi ashe dai rai kanga rai, baki wani canza ba”.

Cikin mamaki dai Hajja Nana Hajia Bunayyah da dukkan su suka zuba masu ido.

Gaisawa sukayi bayan sun zauna.


Cikin kula Lalla Khadijah tace.

“Hafsat muje ko, mu barsu susha ruwa".

Kai Hafsat ta gyaɗa kana suka juya suka tafi hadimansu na taka musu.

Kana acan ɓangaren su Lamiɗo suma haka aka kai musu.

Cikin sauƙe numfashi Baffa Jimeta ya kalli Abban Jameel bayan fitar Hadiman kana yace.

“Toh Alh Bashir wannan al'amari dai da ban mamaki da kuma ɗaure kai yake toh shi wannan yaro na
rasa tantance inda al'amarinsa ya nufa”.

Murmushi Abban Jameel kana ya yace.

“Nan shine gidansu Modibbo kamar yadda kakarsa ta labarta min shi ɗan wannan ahlin ne, gidansu ne
kuma tsatso kuma jigo sannan kuma tushen sa mahaifarsa kenan”.

Kai Baffa Jimeta ya gyaɗa cike da gamsuwa yace.

“Ikon Allah wannan al'ajabi da yawa yake,ita kuma daga wannan ƙasa ta tashi ta koma Nigeria har
Lungunmun can taje ta zauna dashi.

wannan wani irin al'amari ne yasa ta ficewa daga nan ta koma can”.

Zazzafan ajiyar zuciya Abban Jameel ya sauƙe kana ya gyara zamansa tare da cewa.

“Al'amarine mai girma mai kuma ban mamaki”.

Numfashi Lamiɗo ya fesar wanda tunda aka fara magana bai ce komai ba ya muskuta kana yace.

“Ai wato sha'ani Masarauta sai ahankali idan bakayi Sa'a ba sai a saubata maka rayuwa! A banza”.

Abban Jameel na taunar Inabi yace.

“Hakanne ma yaso kasancewa shiyasa ta gudu da Moddibo domin tseratar da rayuwarsa”.

Baffa Jimeta na kurɓan drinks Mai sanyi yace.

“Allah mai iko”.

Daga nan kuma sai suka rufe maganar tare da cin kayan maƙulashen da aka kawo musu bayan sun
gamane Dr Ahmad da sauran masu jan motocin suka sakkamesu suka tafi.
Ɗaya daga cikin Hadiman dake sashin ne ya shigo cike da ladabi ya kallesu kana yace.

“Ga banɗaki sannan ga ɗakuna akwai duk wani abin buƙata da zaku buƙace”.

Murmushi Lamiɗo yayi kana yace.

“Mumgode”

Daga haka ya juya ya fice.

Bayan awa ɗaya, sun ci sun sha Hajiya Bunayya ta kalli Hajja Nana dake goge baki da Tissue tace.

“Wannan al'amari dai da ɗure kai yake”.

Cikin taɓe baki Hajja Nana tace.

“Toh Ni dai fatana dai Allah yasa basayar damu akazo yi ba ehee”.

Dariya mai sauti Innayi ta sanya ganin yanda Hajja ke magana tsakaninta da Allah cike da kamala tace.

“Babu Sai dawa sai karramawa wanda gadon mune, kuma ma in banda abinki a saidaku a nemi me, ki dai
dubafa duk wata ɓukata da ɗan Adam yake dashi muna dashi a masarautarmu”.

Ummi kam murmushi kawai take, dan talura Hajja Nana da innayi har yanzu ba'a shiryaba.

Suna cikin haka sukaji sallama, tare da ganin jagorancin Hadiman Didi

Cike da zaƙuwa ta tashigo tare da Jakadiyar ta da kuma Kakar Moddibo Niyna sai kuma su Rahama
bakinsu ɗauke da sallama.

Innayi na ganin Didi tayi saurin miƙewa tare da durƙusawa agabanta kana ta sunkuyar da kanta ƙasa
batare da tace Uffan ba.

Didi kuwa cikin yalwataccen farin ciki ta tsugunna tare da sanya hannunta akafaɗar Innayi kana ta
ɗagota ta tsayar da ita suna fuskar juna, sai kuma kawai ta ruggumeta tare da faɗin.

“Kin gama min komai Innayi kiyi min duk kan abinda ɗan Adam zai yiwa abokin zamansa na halacci, daga
yau na ƴan taki kin tashi daga Baiwa kin zama ƴa ƴan tacciya kuma Uwa amintacciya kuma kamila kuma
cikekkiyar jakadar sarki mai jirangado”.

Dariya mai sauti Innayi ta sanya wanda ke nuni da zallan farin ciki kana tace

“Alhamdulillah Nagode wa Allah ina tahowa zuciyata na tsinkewa ina tunanin shin ya rayuwa ta kasance
shin ana raye ko kuma anbar duniya zuciyata ta cika da fargaba”.
Baki ɗaya mutanen falon kallonsu suke cike da tsantsar mamaki musamman Hajiya Bunayya da wani irin
zufan hasada ke fita agoshinta.

Innayi kuwa cike da annashuwa ta cigaba da faɗin.

“Amma Alhamdulillah nayi katari da Youseef akan karagar mulki kana kema nayi katarin dake acikin
shigar Gimbiyya amma banga Ubangida naba Sarki Muhammad Aliyu Mouley”.

Kai Jakadiya ta girgiza kana tace.

“Allah yayiwa Sarki Muhammad rasuwa yanzu ɗanki ne Youseef akan Mulki”.

Cikin sanyi Innayi tace.

“Allah sarki, Sarki Muhammad Mouleey. Ubangji Allah yajiƙan sa da Rahma”.

Amin suka amsa a tare,

Ita kuwa innayi juyawa tayi tare da kallonsu Hajja Nana da suka zubo musu idanu sai kuma ta maida
idanunta kan Didi tace.

“Yanzu dai idan na fahimta Moddibona Aliyuna shine Yariman Masarautar nan? kuma Sarki Mai Jiran
gado?”.

Yalwataccen murmushi Didi ta Saki kana tace.

“Tabbas kuwa shine ɗa Namiji babba A masarautar nan kuma ɗa Mai jiran gado Ahamdulillah kuma ya
dawo alokacin da Masarauta ke jiranshi”.

Kai Jakadiya ta jinjina kana tace.

“Sosai kam”.

Didi kuwa cike da nutsuwa ta nufi kujeran dake tsakiyarsu kana ta zauna murmushi ta sakar musu da
lallausan murmushi tare da faɗin.

“Jaɓɓama Moɗon”.

Ga Mamakinsu sai sukaji tayi musu magana cikin Harshen Fullanci.

Cikin yanayin mamaki Hajja Nana tace.

“Allah bauɗo be Fulfulde voli, kamar da fulatanci kike yi mgn fa ko?”.

Murmushi ta saki kana tace.

“Sosai ma kuwa Asalina Bafulatanar Adamawa ce ni ɗuyace ga Sarkin Joɗah Sheiykh Jabeer”.

Kai Hajja Nana ta jinjina kana tace.


“Ai kuwa lallai gashi Yaren da kike mana dashi ya tabbatar mana da hakan”.

Wani irin zufa mai kamar tafasasshen ruwan zafine ke tsats-tsafowa Hajiya Bunayya abaki ɗaya ilahirin
jikinta acikin ranta take mgn kamar zautacciya.

“Toh shin Me hakan yake nufi, kenan haka nufin Khausar tayi katari ta tsinci dami a akala? Ko shegiyar
yarinyar da wayo kamar dala, ko dai dama ita tasan Modibbo ɗan manya ne, kaji shegiyar yarinya da iya
bada kafa, yoh da na sani ai wlh shi Amina zata aura.

Ashe Samira da abinda ta hanga.”

Gaba ɗaya tayi kasake ta tafi dogon tunanin.

Ƙanwar Mommy Aunty Hajara. cike da farin ciki tace.

“Khausar Lelelwal asheko da gaske Lelelwal ɗince ke”.

Murmushi Aunty Ruƙayya tayi kana tace.

“Tabbas kuwa abu yayi yadda ran masoya ke so. Dama wani hanin ga Allah Baiwa ce”.

Hira suka cigaba dayi cike da farin ciki da mutunta juna saɓanin Hajiya Bunayya dake cikin tashin hankali
da ƙunan zuciya.

Acan ɓangaren su Abban Jameel kuwa Sarki Youseef Mouley da Sheik Jabeer ne suka nufi masauƙin su.

Sheikh Lamiɗo na kallon Sheikh Jabeer ya faɗaɗa murmushin fuskarsa cike da kamala yace.

“Allah nhokke sabugo Sarkin Joɗa kana shagaban ƙungiyar TABITAL POOLAKU, da mi yetti Allah da kansa
ne a nan?”.

Kai Sheykh Jabeer ya jinjina kana cike da girmamawa yace.

“Ikon Allah Allah yayi mun haɗu kenan?”.

Murmushi Lamido yayi tare da zamewa gefensa dan shi kansa yasan idan ana batun sarauta toh in su
Sheiykh Jabeer na kusa shi dole a ƙasa zai zauna.

Shi kuwa Sheykh Jabeer cikin kamala da kulawa yace.

“Ikon Allah sai kuma muka haɗu anan, amma yanzu dai ku huta in Allah ya kaimu gobe sai muji meke
tafe daku?”.

Cikin gamsu Lamido da Abban Jameel sukace to.

Su kuwa daga nan suka fice...


Acan ɓangaren su Didi ma Sallama suka yiwa su Innayi tare da faɗin su huta gobe zasu ci gaba da
tattaunawa Godiya sukayi musu kana suka fice.

Washe gari da safe misalin ƙarfe 9:00am Innayi, Hajja Nana, Jakadiya Sheikh Jabeer, Sarki Youseef
Mouley, Galadima, Waziri, Didi Abban Jameel, Ummi, Baffa Jimeta Lamiɗo jakadiyarta zaune suke wuri
na musamman kuma keɓantaccen palon Abualeey wato sarki Youseef Mouley kenan. yayin da baki daya
idanunsu ke kan Innayi.

Innayi kuwa cikin sauƙe numfashi ta cigaba da basu labarin tun randa ta tafi da Modibbo ta wuce Nigeria
dashi kana ta nufi Taraba yankin Gembulan sabida sanin yanki fulanine domin Didi na bata labarin, kuma
ta iya fulatanci tun a lokacin domin Modibbo shine ɗa na shida a wurin iyayensa daga Khadijah da Hafsat
sai da akayi ya'ya uku maza duk basa gama arba'in ake nemansu a rasa sai bayan kwanaki sai a tsinci
gawarsu. A wannan lokacin kuma Khadijah da Hafsat sunyi girma da bazasu mance kamannin innayi ba
shiyasa sunka ganeta.

Fesar da numfashi innayi tayi kana taci gaba da labarta musu, yanda ta rayu da Moddibo yanda ya taso
da yanda yayi karatu, da irin ƙalubalen daya fuskanta, da amintakarsa da Jameel har zuwa mutuwar M
Jameel da kuma dalilin zuwansa Morocco da kuma irin ƙalubale da baƙaƙen magana da kuma hantara da
suka samu awajen mutane kana ta ɗora kuma da wasiyyar da M Jameel ya bar musu akan Modibbo,
haɗin da basu labarin Khausar da dole in dai za'a bada labarin Modibbo da Jameel toh dole cikaton na
uku Khausar ce.

Didi Kam lumshe idanunta tayi wani abin idan taji tayi murmushi wani ta zubda hawaye saboda tausayin
halin da ɗan ta yakasance cikin na rashin aminisa da kuma rashin su a kusa dashi da ya zame masa
sanadin da ake shegantashi.

Cikin sanyin murya tace.

“Allah sarki ɗana Jameel Allah baiyi zamu ganka ba bare muyi maka godiyar kekkyawar amintakarka da
gudan jinin, sai dai Alhamdulillah Innayi tunda Jameel bai mutu da rashin sanin iyayen amininsa, in Sha
Allah mukuwa zamu kasance mashinyi mishi addu'a a tsawon rayuwarmu. Ummin Jameel Ngd MATUƘA
Abban Jameel babu abinda zance daku sai addu'a. tabbas Aliyu na kuma yaga jarrabawar rayuwa wanda
nasan ya samu darussan rayuwa masu tarin yawa acikinsu Innayi na gode kinyi min halarcin da bazan
taɓa mantawa ba kin tseratar da rayuwar ɗana alokacin da ake neman hallakasa kamar yadda akayi ta
hallaka yan uwansa da suka gabata”.

Murmushi Innayi tayi kana tace.

“Wannan yiwa kai ne sannan babu godiya tsakanin mu domin kin cancanci fiye da haka sabida matsayin
uwa kika riƙeni ba Hadimarkiba, shiyasa nima nayi miki abinda zan iya yiwa ƴaƴana na cikina”.

Kai Didi ta jinjina tare da juyowa ta kalli Ummin Jameel dake sharce hawaye cikin sanyi tace.
“Ummin Jameel kada kiyi kuka ga Aliyu na in Sha Allah ya ishemu nidake baki ɗaya”.

Cikin gamsuwa Ummu tace.

“In sha Allah kuwa”.

Innayi kuma gyara zamanta tayi tare da cewa.

“Toh Alhamdulillah bayan ta howarsa nan.

Muka gama mgnar komai akan Khausar da bai sani ba. toh Alhamdulillah dama acikin labarin dana baku
na faɗa muku wasiyyar da amininsa Jameel ya bari toh Alhamdulillah a makkoni biyu da suka gabata an
Aura masa Khausar”.

Cikin wani irin Didi ta kalli innayi tare da cewa.

“Aliyun akayiwa aure!”.

Da sauri innayi ta gyaɗa mata kai kana tayi ƙasa da kanta.

Sai kuma innayi tayi saurin ɗago kanta jin Didina faɗin.

“A....!

Ba editing kam

*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n
nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai
sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan
mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in
kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a
banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account
no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na
faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki
kenan*

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.
Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito
miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar
infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita
tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a
saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda
yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin
san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo
kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki,
domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan
ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah
zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce
dai GARKUWAR MA'AURATA.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

45
*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n
nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai
sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan
mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in
kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a
banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account
no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na
faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki
kenan*

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito
miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar
infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita
tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a
saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda
yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin
san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo
kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki,
domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan
ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah
zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce
dai GARKUWAR MA'AURATA.

45

Da sauri Hajia Bunayyah ta zubawa Didi, idanu sabida a zatonta, lamarin zai zo da gardama ne, ta yadda
zasu koma Nigeria da Khausar, ga mamakinta sai taga Didi ta gaza ƙarasa kalmar bakinta, sai juyawa tayi
ta fuskanci alƙibla, tare da yin sujudul Shukur cike da yalwataccen farin ciki da yasa hawaye fara
zubomata.

Wani irin malolon bakinci ne, ya takari ƙahon zuciyarta, sai kuma tayi ƙasa da kanta, jin Didi na cewa.

“Alhamdulillah wannan mgnar itace mafi daɗi a cikin dukkan bayanan da kikayi mana Innayi kin gama
min komai a rayuwata".

Lamiɗo kuwa sassayyan numfashi ya fesar hakama Bappa Jimeta da kuma Abban Jameel. Hajja Nana
kuwa ajiyan zuciya mai nauyi ta sauƙe tare da gyara zamanta cikin jin daɗin nagartar ahlin Modibbo,
yanzu matsalarta ɗayace, ta yaya Modibbo zai karɓi Khausar wacce irin tarba zaiyi mata a matsayinta na
matar da aminshi ne yayi mishi zaɓinta, bawai dan ita ɗin zaɓin rashi bane, gouron numfashi ta kuma
fesarwa tare dayi mgnar zuci.

“Dole in sa ido kafin komawarmu inga irin tarɓa da kuma yanadin da yaron nan zai amshi Khausar a
matsayin mata, muddin naga abinda bai minba, ko alamu. Tozarci ko cin fuska, Allah shine shaida wlh
bazan bar jikata a wulaƙanta min ita a ƙasar da bata da kowa nata ba.”

Sai kuma ta juyo kanta ta kali Niyna kakar Modibbo kenan mahaifiyar Abualeey, cikin kamala kawaici
mutuntaka gami da aminci tace.

“Ku shirya idan Allah ya kaimu gobe da yamma akwai taro na musamman, wanda dama an shiryashi tun
kwana uku baya, don zamu gabatar da Aleey a gaban family'nsa, tuni Fada take amsar bakunar ƴaƴanta
da jikokinta na nesa dana kusa, domin wannan shine buri da fatan dukkan ahlinmu. Toh Alhamdulillah
gabatarwa ta ƙara armashi tunda da matar Aleey ta aure ta sunnan ma'aki S.A.W. za'ayi taro".

Sai kuma ta kalli Jakadiya tare da cewa.


“Jakadiya a sanarwa sarki shiri a shirya gangamin gabatarwar da na aure. Kana ki gayawa Gimbiyya Lailai
ta tanadi kayan amarya dana ango, a kuma fidda ƙoren al'ada”.

Cikin biyayya da girmamawa Jakadiya ke amsawa da.

“An gabama Gimbiya Shatu”.

Sai kuma ta kalli Sarki Youseep Mouleey tare da cewa.

“A sanarwar faɗa gobe babu zama, kana taron na family ne, idan Allah ya kaimu jibi kuwa za'a gabatar
da Aleey a Fada, da kuma bayyanenne matsayinss”.

Yah Salam Didi kam sai wasu hawayen farin cikin ne ke zuba mata wani ba korar wani.

Galadima kuwa da Waziri kawai murmushi sukeyi kai kace anyi musu bushara da al'jannane.

Sheykh Jabeer kuwa a gyaran murya yayi tare da kallon matar amininsa Marigayi Sarki Muhammad
Mouley, da ɗan murmushi a fuska yace.

“Da dai kada a yawanta bidi'a a lamarin, kuma da an sirranta shi ko”.

Cikin sauri Galadima yace.

“Yah Sheykh ai Aleey ya sirrantu tsawon shekaru talatin ai yanzu kam lokacin bayyanar sa ce tayi, dole ya
fito ko domin girgiza zuƙatan sauran ɗan burbushi magauta duk da dama suna zaton haka tunda kowa
yasan labarin wasiƙar da Innayi ta bari kafin tafiyar kuma a san shi ba a tsinci gawarsa ba kamar yadda
ake tsinta na yayunshi da suka gabata, masu fariyar dole sarauta ta bar hannun ahlin Aliyu Mouley, su
san cewafa ga wani Aleey mazan”.

Murmushi mai ɗan sauti Sheykh Jabeer yayi dan shi kansa al'amarin yana tsumashi yana tuna mishi irin
magautan da suka fuskanta a masarautar Joɗo, shida har tsuntsuwa aka meda mahaifiyarsa. *A Littafin
GARKUWA sai gashi kuma ƴar shima ta faɗa irin gidan*

Innayi kuwa cikin yaƙini tace.

“Da izinin Allah su da Aliyu na sai dai kallo basu da zarrar iya cutar dashi”.

Cikin gamsuwa Sarki Youseep Mouleey ya gyara zamansa tare da fuskatarsu kana yace.

“Aje a fara shiri”. Daga nan aka watse taro cike da jin daɗi.

Didi ce zaune a bakin gadon ta na alfarma yayinda

Lalla Khadijah da Hafsat dake zaune a gabanta cikin tsananin happy tace.
“Didi kin ko tuna cewa gobene birthday ɗin Aliyu”.

Kai ta jinjina tare da kallon Rahama da ta miƙe zaune tana mai danna wayarta tace.

“Didi kice inyi gayyata ta mu samman”.

Ta ƙare mgnar tana shiga group ensu na Mouley family.

Didi kuwa cikin jin daɗi tace.

“Ai kuwa Rahama ki gayyata ta musamman domin bikine na musamman.

Sai kuma ta kalli Hafsat tare da cewa.

“Ki kira ƙawarki Islam kuje Ryad square shopping mall. Ku ɗebo dukkan abinda ya dace, kama daga na
amarya da shi Aleey.

Daga nan in kun taso ku biya Marocco Mall ki ku zaɓo dukkan abin buƙata na al'adun amaren
masarautar Mouley, Hafsat so nake komai ya zama na musamman ne”.

Cikin sanin manufar mahaifiyar tasu ta ce yanzuma kuwa Didi.

Khadija kuwa da sauri tace.

Amman sai munje munga amaryar kafin mu tafi”.

Gyaɗa musu kai Didi tayi tare da cewa.

Nima yanzu zan tafi sashin Niyna dan ance min su Goggonku Salma da Zakariyya sun iso”.

Daga nan ta miƙe ta fita.

Rahama kuma tana gama fesa labarin hidimar da za'ayi a masarautar tasu gobe misalin ƙarfe huɗu na
yamma.

Ta kuma shiga group ɗin na ƙawayenta.

Nan ta fesa musu.

A masauƙinsu Khausar kuwa bayan su Ummin da Innayi sun dawo cikin farin ciki Ummu ta zauna kusa da
Khausar dake riƙe da kwanon ƙasaitacciyar mace da Ummin ta dama mata tun kafin su tafi.

Ƙwaffa tayi tare da cewa.

“Wai Khausar har yanzu baki shanye damun nan ba?”.


Fuska ta ɗan kwanɓe tare da cewa.

“Allah ko Ummi abun babu daɗin”.

Da sauri Asma'u tace.

“Ni dai Wlh yayi min daɗi gaba ɗaya gumbunan da da garukan ɗaɗine dasu, wani garɗi kamar na dabino
da aya da kwakwa harda ɗanɗannon zumafa a ciki, Ummi gashi da zaƙin su ƙungiyar alewa da kuma
mazarƙwaila”.

Da sauri Ummu tace.

“Toh sha zumami kice mana wanda aka ɗan sha ɗin ma kece kika shanye. da kike koro jawabi haka”.

Yar dariya tayi tare da rufe idonta kana tace.

“Sai daifa gsky kuma duk da kayan dadin akwai itatuwa da jijiyoyi dan naji ƙamshi jijiyar ilanwaddihi ma
da ma kwaranyi wanda kike yawan aikena in amso miki wurin Innayi”.

Harara Ummi ta cilla wa Asma'u tare da cewa.

“Dama ai mgni kam bazai yi ɗaɗiba, maza Khausar kafa kai ki shaye”.

Cikin rumtse idanun ta kafa kanta ta fara sha.

Saida tasha kusan rabi kana ta janye kwanon tare da kwaɓe fuska tace.

“Wlh Ummi ni dama can kayan zaƙi bai cika dakuna ba, nafi son abun yaji-yaji kiga mana kazar nan da
kika dafa min duk da babu daɗi amman dana zumbuɗa yaji na cinyeshi fes. Kuma Kinga Wanda Aunty
Hajara ma ta kawo min na cinyeshi. Shi kam ma yafi rashin daɗi dan da ƙyar naci tanata zagina wai dubu
ashirin da takwas ta biya AYSHA ALIYU GARKUWA ta dafa minshi wai zuciyar farin ragone”.

Haɗe fuska Ummi tayi tare da cewa.

“Kuma wannan ɗinma sai kin shanyeba”.

Jin haka yasa ta kafa kai ta shanye, tare da ajiye kwanon kana tace. “Alhamdulillah na gama”.

Cikin sauƙe numfashi Ummi tace.

“Yanzu muka dawo daga sashin kiran da akayi mana, munje bisa jagorancin innayi”.

Da sauri Asma'u tace.

“Ummi kunga Yah Modibbo?”.

Kai ta jujjuya mata tare da cewa.


“Bamu ganshiba, baima san munzoba, innayi ma sunce ta bari sai gobe zata ganshi”.

Taɓe baki Khausar tayi tare da cewa.

“Uhmm me ake ta ɓoyeshi sai kace kuɗine shi ko zinari”.

Zura mata ido Asma'u tayi tare cewa.

“Yoh ba doleba, sun san akwai mai ƙar mishi kallo har gashin ƙeyarsa ta iso”.

Harara ta cillawa Asma'u tare da cewa.

“Waya ma damu da dashi”.

Murmushi Ummi tayi tare da faɗin.

“Yanzu dai tashi kiyi Wonka, tunda dilken ya kai awa biyu a jikinki”.

Da sauri tace to, tare da miƙewa ta nufi bathroom din.

Asma'u kuwa falo ta nufa jin innayi na kiranta.

Zaune ta sameta dasu Hajia Bunayyah da kuma su Aunty Hauwa duk dai waɗanda suka zo tasu.

Gyara zama tayi tare da kallon su ɗaya bayan ɗaya kana tace.

“Idan Allah ya kaimu gobe za'a fara hidimar bikin Khausar da Modibbo kamar yadda al'adar masarautar
Mouley takeyi.

Dan haka ku shirya karfe huɗu na yamma ne za'a fara.

Zuwa Maggarib an gama na gobe sai kuma zuwa jibi.

Cikin tsinkewa da lamarin cigaban da Khausar ta samu Hajia Bunayyah tace.

“Uhmm Allah ya kaimu”.

Sai kuma ta yunƙura zata tashi.

A hankali ta koma zaune jin muryar Hajja Nana na cewa.

“Bisa alamu dai Khausar taci ribar ƙin auren ɗan mayu, abu ya haɗu, sunna ta haɗu da farilka, sakekke ya
haɗu da sakekkiya, wato bazawari ya samu bazawara ɗan maye da ƴar Mayu, jikar tsarki da jikan sarki”.

Cikin takaici Hajia Bunayyah tace.


“Kamar yaya kuma Sunan ta hadu da farilla?”.

Kai Hajja Nana ta jinjina cikin isa kasaitar data motsomata yau tace.

“Eh ɗan babban Sarkin Mouley na kasar Marocco ya auri jikar babban Sarkin Gombawa na ƙasar Nigeria
jihar Gombe, kin san su dama su Khausar kirarinsu Gombawa ɗiban fari ba'a kwana dasu ba a tashi dasu,
Gombe doma hamadar sarki lahirar sulaimanu”.

Da sauri Innayi ta kalleta cikin rashin fahimta ita kuwa Hajja Nana cikin ƙasaita tace.

“Yoh da ji kikeyi ku kadaine keda masarauta, to idan baki saniba, Sarki Buba Yero shine tsohon mijina
kuma kakansu Khausar, barina Gombe da mahaifin Khausar da bappanta Muhammad, ne yasa
masarautar ta koma hannun kaninsu ɗan abokiyar zamata, kuma shi har yanzu jira yake Yayanshi bappan
Khausar yaje ya karɓi ragamar mulki dan su masarautarsu sunada imani da ƙaunar juna babu wani
tsaface-tsaface, nice na hana sabida ni kwanciyar hankali ƙannena yafi min”.

A hankali Ummi dake jiyo Hajja Nana ta fesar da numfashi tare da cewa.

“Haba sai haka mana ƙasaita da isar Hajja Nana tayi yawa, ita kanta Khausar ƙasaitarta da kwarjinin ba
irin na normal mutane bani, kwarjinin ta yawa gareshi.

Sai kuma ta kalli Khausar da fitowar ta kenan daga Bathroom.

“Masha Allah”. Shine abinda Ummi ta faɗa sabida ganin wani irin sheƙi da ƙellin da fatar Khausar keyi kai
kace tarwaɗace, tsabar farin da tayi kace balarabiyace.

Gashin kanta dake tubke ta zubawa ido.

Sai kuma ta kalli Khausar ɗin dake tsane jikinta tare da miƙa mata.

Man shafawa, da dauko handdryer kana ta dawo ta bayanta.

Tare da fara busar mata da gashin dan ya ɗan jike. yaje mata tayi tare shafa mata mai.

Ita kuwa Khausar mai take shafawa a jikinta kusan a tare suka gama.

Ajiye handdryer ɗin Ummi tayi tare da juyowa gefen gadon inda akwatuna set ke jere, ɗaya pink ɗaya
blue, wanda Ummi ce ta bada aka haɗawa Khausar ɗin Kayan lefe, kana kuma shine aka kai gidansu
dangi da abokan arziƙi suka gani.

Wanda suma Hajia Bunayyah dai bata samu abin kushewa ba.
Na forkon ta buɗe wanda tun a gida Asma'u ta haɗa dukkan abin buƙata da kuma kayan da Khausar ɗin
zata saka har gama bikin.

Wata Dubai Abaya Ummi ta zaro mata, Black color sai kuma zare golding color da aka yiwa rigar aiki zuɓi
na musamman mai masifar kyau da ratsin fari kaɗan rigar irin mai ɗan faɗin nanne musamman daga
sama. sai kuma ta zaro mata wani tattausan mondo Wanda bazai wuce iya guiwarta ba, sai bra su duka
fararare, turare ta zaro kusan kala uku ta feshesu dashi. Kana ta ɗauko Kulaccar sirri wacce ta saya wurin
AYSHA ALIYU GARKUWA, miƙa mata tayi tare da cewa.

Gashi ki shafa wannan.

Amsa Khausar ɗin tayi tare da cewa.

“Ayyah Ummi a tubke min gashin nan”.

To Ummin tace tare da fara tubke mata shin.

Tana gama ta nufi falo tare da cewa.

In kin gama kizo, kai kawai Khausar ɗin ta gyaɗa mata.

A can Falo kuwa Hajia Bunayyah ce ta miƙe jiki a salube ta shige ɗakin da nanne masauƙinsa inta da
Aunty Hajara da kuma Aunty Ruƙayya.

Da sauri ta maida ƙofar ɗakin ta rufe tare da dannawa Hajia Lami kira a wayarta.

Bugu ɗaya ana biyu Hajia Lami ta ɗauka tare da cewa.

“Mutanen Marocco yaya akayi?”.

Cikin fesar da numfashi mai zafi Hajia Bunayyah tayi kwafa tare da cewa.

“Wllhi Allah Hajia Lami munyi babbar asara daba Samira wannan yaron ya auraba. Na rantse miki da
Allah munyi asarar samun daular duniya.

Wannan shegiyar yarinya mai idanu kamar na mujiya ko yaushe suna lunshe kamar mai jin bacci anya
ma kuwa ba idanun dunane da ita ba.

Kinga tayi nisa ta barmu da Naseer ɗin da ubansa ko Sarkin tasha bai taɓa samuba, ke kuwa ta bar miki
ƴa da wari da yoyon ƙazanta”.

Nannauyan numfashi Hajia Lami ta fesar tare da cewa.

“Toh yanzu me abinyi?".

Cikin tsananin hasada Hajia Bunayyah ta buga hannunta da jikin gini tare da cewa.
“Wallahi Allah ni dai na rantse da Allah, sai na kashe auren nan, koda zan tafi tsirarane sai na watsa
aurenan, muddin ina raye wlh Khausar bazata ji daɗin rayuwarta a gidan nan ba, idan zaki zo mu haɗa
hannun da ƙarfe mu tumɓuke auren nan, mu shiga da Samira gidan to ki fara shiri, domin ina dawowa
zamu bazama".

Cikin ƙeƙashewae zuciya Hajia Lami tace.

“Ai ke dai Allah ya dawo dake lafiya, Ƙawata na sama mana labarin wani ƙasurgumin boka a ƙasar Niger
cikin dajin Damagaran ance min aikinshi kamar yankan wuƙane, babu haufi shi bazama ka biyaba sai
buƙatar ka ta biya”.

Cikin yaƙini tace.

“Ke dai ki shirya ina dawowa zamu tafi”.

Daga nan suka katse kiran kana ta fito.

A falon kuwa da sauri su Ummi suka ƙali ƙofar falon jin sallamar Jakadiya da kuma su Lalla Khadijah da
Hafsat.

Cikin sakin fuska Ummi da Innayi suka amsa tare da nuna musu wurin zama.

Zama sukayi cikin sakin fuska da cikekken fulatancinsu da suka iya ta sanadin Didi suka kalli su gaisa cikin
mutumtaka.

Jakadiyace ta kalli Lalla Hafsat tare da juyowa ta kalli innayi kana tace.

“Dama yayun Aliyu ne suka zo ganin ƙanwar tasu tare da marabtanta.

Cikin jin dadi Ummi tace.

“Ayyah to babu laifi barin in kirawota”.

Sai kuma ta mike ta nufi dakin da Khausar take.

“Masha Allah diyata kinga yadda kikayi kyau kuwa". Murmushi tayi tare da rufe fuskarta da tafukan
hannunta.

Ita kuwa Ummi kamo hannunta tayi ta ajiyeta tare da cewa.

Zo mu je ki gaisa da yayun Modibbo.

Da sauri ta sunkuyar da kai ganin yadda Ummi ke gyara mata tarhan da tayi da gyalen abayar sosai tayi
masifar kyau ta fito cas da ita a matashiyar budurwar yar kimanin shekaru 19 zuwa 20. Duk da rigar nada
faɗi bai hana kyan surar jikinta bayyana ba.
A hankali suka fito falon.

Khausar kam kanta a ƙasa take wani irin amintaccen taku mai cike da nitsuwa.

Da sauri Lalla Khadijah ta miƙe tsaye lokacin da suka iso tsakiyar falon.

Hannunta ta buɗewa Khausar tare da faɗin.

“Wow Masha Allah, Didi dai ta samu ƙarin diya wannan ai in an ganta da Rahama kai kace tagwayene".
Murmushi mai yelwa Lalla Hafsat ma tayi tare da miƙawa Khausar hannun a hankali Khausar ta ɗan janye
jikinta dan jikin Lalla Khadijah ta ɗan saketa.

Ruggumeta Hafsat tayi tare da cewa.

“Masha Allah, Khausar muna farin ciki da shigarki Mouley family. Allah ya baki hikima da basirar zama
tsakiyar wannan Fada”.

Kusan a tare suka amsa da Amin ita kuwa Khausar yatsun hannunta take ɗan murza tare da ɗan
rusunawa kana ta gaidasu.

Amsawa sukayi suna mai ƙare mata kallo. Cikin ɗan sakin fuska Hafsat tace.

“Ai wannan komai nata kamar na Rahama zaiyi mata dai-dai”.

Cikin girmamawa Jakadiyarsu tace.

“Sosai ma kuwa”. Ita kuwa Hafsat hannun Khausar ta kamo tare da cewa.

“Takalmi sise nawa kike sawa”.

Cikin sanyin murya tace.

“37”. Da sauri Khadijah tace.

“uhm jinjina sise ɗin Rahama kenan”.

Sai kuma ita Khadijah ta kamo hannun Khausar tare da ajiyeta gefen Innayi kana tace.

“Zauna abinki. Didi da Niyna sunyi miki Barka da zuwa, masarautar Mouley. Yanzu mu zamu fita ne.”

A hankali tace.

“Allah ya kiyaye hanya."


Amin sukace a tare sai kuma suka ɗan kalli Asma'u tare dayi mata murmushi suke.

“Ke me sunanki?”.

“Asma'u”.

Murmushi Khadijah tayi kana tace.

“Yauwa toh in ba matsala innayi zamu tafi da ita, ai kin san sise ɗin Khausar da kalanta ko?”.

Cikin fara'a Asma'u tace.

“Sosai ma kuwa, Nama fita sanin abinda yake mata kyau”.

Dariya sukayi ganin hararar da Khausar ta cilla mata..

Ummi kuwa murmushi kawai tayi.

Daga nan suka fita da Asma'u.

Sune basu dawoba sai gab da Maggarib.

Acan Side din da Modibbo yake kuwa.

Zaune yake shi da Ibrahim da Dr Jameel.

Cikin tsuke fuska ya kalli Dr Jameel dake zoro wayarsa daga aljihu.

“Baby”. Ya faɗa a saman lips enshi.

Sai kuma ya tsaida idonsa kan Modibbo da ya wani irin tsaresa da idanu.

A hankali yace.

“Yah dai Malam kallon nan fa?”.

Fuska Modibbo ya kuma tsukewa tare da cewa.

“Kaji tsoron Allah, Dr J kasani. Abinda kakeyi kana tafiya cikin fushin Ubangiji ne, kuma masifar
zunubinka zaiyi ta bibiyarka tun anan gidan duniya, kasan cewa abinda kayiwa ƴaƴan wasu za'ayiwa
ƴaƴan ka, shin me ribarka a cikin in har ka jazawa ahlinka. Ka tuna shifa zina tsananin muninsa yasa Allah
baice kada kuyi zinaba, cewa yayi kadama ku kusaceshi fa. Shifa mazinaci baya zina har sai an zare mishi
imaninshi. Kasan kuwa abinda Allah ya tanadarwa mazinata abinsha a cikin jahannama?”.
Cikin tsananin sanyin jiki Dr Jameel ya rumtse idanunsu tare da cewa.

“Nifa shiyasa badon Abualeey da kansa yace min dole in kasance kusa da kaina wlh bazanzoba sabida na
lura kai mutumne mai tsaraɓe-tsaraɓen halal da haram”.

Cikin takaici Modibbo yace.

“Koda baka zo inda nakeba kasa a ranka in dai ina cikin ƙasarnan, sai na kasance tare da kai, na kuma yi
al’ƙawari zan ƴaƙi shsiɗanin dake tare da kai, in Sha Allah sai ka dawo managarci tamkar J na”.

Murmushi Dr Jameel yayi tare da kallon hadimai guda huku da suka shigo da manyan jakukkuna guda
biyar masu ɗauke da tambarin Anfaplace mall Marocco.

Da sauri Ibraahim ya miƙe tare da cewa.

“Ku shigo dasu cikin bedroom kada ku barsu a nan”.

Jin hakane yasa suka bishi a baya.

Kusan a tare suka shirya kayan cikin wodurob.

Daga bisani suka fito falon, a tsaye ya samu Dr Jameel.

“Mujeko Ibraahim”. Cewar Dr Jameel.

Kai Ibraahim ya gyaɗa tare da bin bayanshi sai kuma ya juyo ya kalli.

Moddibo dake cewa.

“Wai dan Allah Ibraahim sai yaushe za'a buɗeni in samu zuwa jam'in salla, wlh abinfa yana damuna.

Sassan numfashi Ibraahim ya fesar kana a hankali ya juyo ya dawo gaban Modibbo tare da cewa.

“Kayi haƙuri Yah Aleey in Sha Allah gobe dai a jam'i zakayi sallan magarib. Akwai babban dalilin ne da
yasa ba'a barka ka fitoba.

Ƙwaffa Modibbo yayi tare da lumshe idonsa Allah ya sani suna ƙona mishi rai da batun hanashi jam'i da
wotoyinsa.

Shi kuwa Ibraahim juyawa yayi yabi bayan Dr Jameel suka tafi.

Washe gari tun safe Dr Jameel da Jabeer bin Jabeer da kuma Ibrahim suka shigo wurin Modibbo.
Tare da wani Kekkyawan matashi wanda bazai wuce sa'an Modibbo ba.

Cikin sakin fuska matashin ya bawa Modibbo hannu tare da cewa.

“Sunana Zakariyya Khallin”.

Cikin ɗan sakin fuska Modibbo yace.

“Masha Allah”.

Ibrahim ne ya amshi mgnr da cewa.

“Yah Aleey Wannan ɗan Goggo Salma ne ƙanwar Abualeey. Shi a India yake shima likitane, taron
gabatar da kaine ya kawoshi.”

Murmushi Modibbo yayi tare sake bashi hannun, shi kuwa Zakariyya ruggume Modibbo yayi tare da
faɗin.

“Duk da zumuɗin Mami na rigata ganin ɗan yayanta”.

Shi kuwa Modibbo Ibraahim ya kalla jin yana cewa.

“Dr Jameel ma ɗan Goggonmu ne Aunty Sahrah itake bin Goggo Salam, kuma babanshi Aminin Abualeey
ne ɗan ƙasar Turkey, duk dangin babanshi suna can”.

Dr Jameel kuwa numfashi ya ɗan fesar kana yace.

“Ni ya labarin Yusuf ne, kwana biyu bamuci wayaba”.

Da sauri Zakariyya yace.

“Ya tafi Mexico kasanshi ya nacewa Zeeyada yar Lalla Hafsat”.

Sai kuma ya kalli Modibbo tare da cewa.

“Yusuf ɗan Unclee Haroon Mouley ne, ƙanin Unlee Youseep Mouleey”.

Cikin fahimta Modibbo yace.

“Na fahimta, toh amman kuma tunda nazo banga Unclee Haroon ɗinba”.

Cikin sanyi Dr Jameel yace.

“Dashi da Mamina, da Abbana duk rana daya sukayi haɗari, su sun rasu shi kuwa har yau baida lfy
tsawon shekaru ashirin da biyar kenan”.

Cikin sanyin jiki da tsananin tausayi Modibbo yace.


“Allah sarki Jameel Allah ya jiƙansu da rahama yasa sun huta shi kuma Unclee Haroon Allah ya ya bashi
lfy”.

Da Amin suka amsa baki ɗayan su.

Shi kuwa Modibbo cikin sanyi ya kalli Dr Jameel tare da cewa.

“Dan J kabar abinda kakeyi ka zamewa Aunty Sahra da Abba al'waladussaliha ko dan basa raya ka zame
musu sanadin samun lada”.

Cikin sanyi jiki Dr Jameel yayi ƙasa da kansa yana mai taunan lips inshi na ƙasa.

Shi kuwa Modibbo a raunace yace.

“Mu kuwa zamuci gaba dayi maka Addu'o'i Allah ya shiryeka”.

Amin suka amsa a tare.

Sai kuma Ibrahim yace.

“Yauwa mu shiga daga ciki masu gyara zasu shigo gyara nan ɗin".

Toh sukace kana suka shiga Corridor nan tare suka shiga ƙofar nan ta dama inda Modibbo yake, a falon
suka zauna.

Zamansu ba jimawa Rahman ta shigo da hadimai da sunka kawo musu breakfast.

Acan Side ɗin dasu Khausar suke kuwa, suma tuni an kawo musu breakfast, dama dukkan abin buƙata.

A nan wannan falon kuwa, zuwa bayan an isar da sallam la'asar duk an gama ƙawatashi da shiryashi irin
shirin nan na al'farmar da kamala.

Kujerun gaba ɗaya an mannasu da ginin duk da girman falon wai dan a samu ya ƙara girma.

Wata kujera mai zaman mutum biyu aka ajiye daka san tsakiyar falon. Sai kuma wasu datsa-datsan
Turkiy Carpet masu masifar kyau da taushi. Da aka shimfiɗa a gaban kujerar, wacce duk ta inda ka shigo
zaka kalli waɗanda ke ka kujerar. Sai kuma wasu tukwanen kasa masu zanen ɗawisu da aka jere gefe da
gefen kujerar yayinda daga sama tukwanen kuwa, gashin gezan ɗawisunne a cikin mai cikekken launi
daban-daban, sai kuma wani tim-tim da aka ajiye a guda biyu a gaban kujerar wanda da bisa alamun
anan waɗanda zasu zauna kan kujerar zasu daura sawunsu.

Sai kuma hadimai guda uku ɗaya na bayan kujerar ɗaya na gefen dama ɗaya na gefen hagu.

Kana duk inda ka wulga idanunka a falan kaskon turaren wutane mai fasar da sassayan kanshi.
Sai kuma sanyin ac dake ratsa ko ina, an sassake labulayen, tare da kuna wutan falon baki ɗaya a ƙalla
falon zai iya ɗaukan mutun settun zuwa tamanin.

A nan sashin dasu Khausar suke kuwa.

Wasu matane guda biyu, aka kawo dan shirya kausar, Kasancewarsu ƙwararrun masu shirya amare,
wanda suke zaune acikin masarautar musamman domin gyara da kuma ƙyale amare.

Wata Haɗaddiyar rigar Caftan and Takchitas suka sanyawa Khausar din, wacce ta kasance farace ƙal, mai
ɗauke da ratsin adon gold da kuma sky blue wato kalan sararin samaniya.

Rigace me tsananin kyau da takasance traditional wedding dress wanda ƴan masarautar Mouley
morocco ke sawa lokacin biki, sosai rigar ta zauna ajikin kausar, tayi mata ɗas tare da k’ara bayyana
tsantsar kyaunta, musamman da suka ɗaura mata tsadadden sarƙan gold da kuma ƴan kunne haɗi da
awarwaro da kuma zobunan gold, wanda suka ƙara cika adon nata, babban mayafin daya kasance fari
ƙal, wanda aka kewaye bakinsa da tsararren ado me kalan sky blue, suka sanya mata akanta, wanda ya
sauko har yakai ga ya rufe kyakkyawar fuskarta.

Masha Allah da wannan tsananin kyaun da kausar tayi, wanda kallo ɗaya zakayi mata kasan ta cika mace
har mace, saboda tsananin kyaun da traditional wedding dress din yayi mata, a kyawawan ƙafafunta
kuwa wani haɗadɗen takalmi irin nasu na sarauta me kalan sararin samaniya suka sanya mata, daya sake
k’awata shigan nata. Duk da kafafun nata ba lalle dan innayi ta hana a saka mata.

Su kansu sun yaba da kyaun yarinyar domin tunda suke shirya amare basu taɓa shirya amaryar da tayi
kyau sosai kamar wannan ba, kai kace asalinta balarabiyar Morocco’n ce, musamman yanda jikinta ke
fitar da sihirtaccen k’amshi kulaccar sirri da me matuk’ar ratsa zuciya haɗi da daɗin shaƙa.

“Masha Allah, tsarki ya tabbata ga Ubangiji me tsara kyawawan halittun da yayi wannan halittar da ta
kasance tamkar farin fure acikin tarin jajayen furanni, Allahumma Barik.”

Cewar Lalla Khadija da shigowarta kenan, cikin shigar ƙasaita.

“Masha Allah.”

Ta kuma faɗa tana me miƙawa su Asma’u, Dija da kuma Asiya kayan dake hannunta, wanda suna ɗaya
daga cikin kayan da aka kawowa kausar jiya, dogayen riguna ne guda uku masu matukar kyau.
“Ga wannan kuma ku sanya, domin naga kaman kune ƙawayen amarya.”

Amsa sukayi suna godiya..

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta abinki cikin Salamah 1k nefa kacal 0661110170
GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N 09097853276,
in tura miki littafin ki karanta abinki cikin salama kana in saki a Group ɗin*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

46

Assalamu alaikum mutanan arziki masoya kamshi ma abota kamshi Amaren kamshi masu jargon kamshi
Yammata wadanda sukasan darajar kamshi ni Aysha Aliyu Garkuwa na kawo muku tallan wasu
Amintattun turarukana masu matukar kamshi da Kama jiki

Masu saukin farashi sannan ga biyan bukata

Yarhjya_incense_and_more

Ta shirya tsaf domin ta gwangwajeku da Turaruka na alfarma

Farar khumrah

Bakar khumrah

Turaren Wanka

Oil 6ml 1

Oil 12ml 1

Turaren fesawa 24 hours guda 1

Duka Akan 10k kacal


Sannan kayanta suna tafiyane da guarantee duk wacce tasiya taji babu kamshin nan na alfarma ko
kuma basuda lasting to tayi alkawarin mayar muku da kudinku

Wannan garabasar zata kare on 5th September insha Allah

Ku hanzarta ku mallaki naku domin kayan yarhjya babu Danasani a cikinsa saidai kuyi alfahri da siyan
kayanta

Account number 1419787445 Amina Umar usman access bank

Kitura evidence of payment to

08092664954

Kuyi saving number TA domin ci gaba da ganin Turaruka Kala Kala

46

Yayin da gaba dakin sune bin Khausar kallon, sabida yadda annurinta ya cika fuskarta, tare da haska
ɗakin, lokaci daya ta zama tamkar tauraruwar da tafi ko wacce haske acikin duniya.

Acan cikin sauran ɗakunan kuwa, tuni su Ummi da kuma su Aunty Hajara, Aunty rukayya, Hajiya
Bunayya, sun sha kwalliya cikin shigar Alfarma, had’i da kece raini, sun kuwa yi matukar kyau, domin
hatta su Innayi da Hajja Nana ba abarsu a baya ba, musamman Hajja Nana duk tsufanta, bai hanata yin
kyau cikin doguwar rigar data sanya ba kasancewarta ƴar duma-duman tsohuwa kai hakama bata
shekarun da take da suba, dukansu sunyi kyau sai ɗaukar idanu suke, kowanne daga cikinsu kuwa kaga
ni kasan yana cikin farin ciki, musamman Innayi da ayau farincikin dake kan fuskarta ya kasa ɓuya.

Hakama ɓanƙaren su Abban Jameel da Lamiɗo da Malam Arɗo Bappa Jimeta da Haiydar harma da Dr
Jameel sosai sukayi shiga ta al'farmar.

Su tuni sun iso wurin taron bisa jagorancin Sheykh Jabeer.

Hakama su Innayi suma tuni sun sauƙo bisa jagorancin innayi, sun zauna a gefen inda su Abban Jameel
suke, don dama an ware musu wurin zamansu na musamman.
Aɓangaren Moddibo kuwa tsaye yake acikin cikin ɗakin da ya lura nanne ɗakin Ibraahim, yayinda yake
cikin wata irin Amintacceyar shiga ta al'farmar da kamala.

Dandatstsiyar jalabiya ace a jikinshi Sky blue mai masifar kyau da shaƙi sai ɗauke ido take tamkar
madubi, sai kuma wata tattausar Al'kebba fara ƙal mai ratsin Sky blue da golding kala na zaren da aka
yayyarfawa alkebbar wani irin Mashahurin aiki mai cike da tambarin masarautar Mouley ɗin. Sai kuma
farin hirami mai gidan dara-dara Sky Blue, wow Masha Allah. Wani irin sheƙi da ƙyalli yakeyi kai kace
taurarone sajenshi kuwa sai walwali yakeyi fuskarshi ta fito ras.

Cikin ɗan fesar da numfashi yace.

“Anya zan iya wannan tsaraɓe-tsaraɓen kuwa”.

Yayi mgnar cikin ƙosawa da yadda ake wani shiryashi kamar yaro.

Murmushi Ibraahim yayi, had’i da cewa.

“A’a zaka iya, mana, kayi haƙuri kasan al’adarmu ce anan, duk ranar da za’ayi wani abu na musamman,
shirya mutum ake, musamman irinka masu girman daraja.”

Kai Modibbo ya girgiza cikin yanayin k’osawa yace

“Afwan ni a barni haka”.

“A’a Yah Aleey dan Allah, kasan nan masarauta ne, kuma kana da matsayi na musamman, kadai bari
ashirya kan.”

Kokarin magana yake, sai kuma ya fasa saboda Sheykh Jabir daya shigo, cikin shiga ta alfarmar da
takasance shigarsa akoda, wanda a wurinshi Modibbo ya gaji don irin wannan shigar, ganin Modibbo’n
azaune yasa shi, bud’e baki da mamaki yace.

“Har yanzu Aleeyu basu gama shiryaka ba, lokaci yana k’urewa, tashi maza a ƙarisa shirya ka da hanzari.”

Ya k’are maganar yana me jawo hannunsa, suka nufi gaban dressing mirror wanda yake cike tab da
ababen gyaran jiki, komai na wurin tsabtsab yake, komai neat da alama Ibraahim din gwanin tsabta ne.

Suna isa wurin ɗaya daga cikin hadiman ya ja mishi kujera, ya zauna, bisa umarnin Sheykh Jabeer
way’annan hadiman suka ci gaba da shirya, shirin da ya bayyana cikakken kwarjininsa me burgewa.
“Masha Allah.”

Ibraahim ya fad’a lokacin da kwararrun hadiman nan suka nad’a masa kyakkyawan farin hirami me ratsin
adon sky blue akansa, da yayi matuk’ar k’ara bayyana kwarjininsa, still suka gyara mushi zaman
tattausan farar, alkyabbar da taji ado, me d’auke ido da jan hankali, wacce tana da faɗi kuma a buɗe
take, tabbas zan iya cewa Modibbo bai tab’ayin kyau irin na yau ba, domin shi kansa ya shaida hakan,
saboda tsananin kyaun da yayi, Sheykh Jabeer da Kuma Ibraahim murmushi kawai suke idan sun kalleshi.

Kyakkwawan takalmin sarauta light blue aka sanya masa aƙafarsa, wanda shiya ƙara cika adon nasa,
domin harda adon bit din gold ajikinsa, ahannunsa kuwa wani tsadadden agogon gold suka d’aura masa,
wanda cikinsa ke d’auke da tambarin masarautar tasu ta Mouley.

Murmushi Ibraahim ya sakeyi, wanda hakan yasa Modibbon ƙanƙan da idanunsa, cikin sanyi da taushin
muryar da taza me masa d’abi’a yace.

“Wai Ibrahim duk wanna murmushin na menene?”

Murmushi Ibraahim din yayi, yana me gyara masa zaman takalman ƙafarsa yace.

“Duk wannan murmushin da shigar taka ta musammance, yau din rana ce ta farinciki Yah Aleey, yau da
za’a gabatar dakai awajen dangin mahaifinka, yau kowa zai san da zamanka, ni gani nake kamar masu
shiryakan ma basa sauri.”

Ya ƙare maganar yana sake kallon tattausar alkyabbar dake jikin Ya Aleey’n nasa, wacce Sheykh Jabeer
ke k’ara gyara masa zamanta.

Aransa yake yaba baiwar kyau kwarjini had’i da haiba da Allah Yayiwa Aleey’n.

Abayyane kuwa cewa yayi.

“Masha Allah,

Sheikh Jabeer kuwa cikin kulawa yace.


“Fatabarakallahu fiy ahasanil khali kiyn.

Allah Ubangiji ya albarkaci rayuwarka, ya kareka daga sharrin mugun mutum da aljan, ya kuma tsareka
daga sharrin idanun al’ummar da zasu kalleka, ka shiga da addu’a, Ubangiji na tare dakai akoda yaushe.”

Amin Ya Allah, Jabeer bin Jabeer dake shigowa ya amsa.

Shi kuwa Modibbo Cikin dai ɗaurewar kai da har yanzu ya ke ciki ya gyaɗa mishi kai.

Yayinda Ibraahim kuwa, tsananin kyaun da Yah Aleey’n yayi duk ya gigitashi, hakan yasa shi zaro wayarsa
kirar iphone 14pro max ya shiga daukarsa hoto, yana me sake yaba kyawun da yayi, koda ya kammala yi
musu hoton falo ya fito, nan ya iske Dr. Jameel da kuma Zakareeya suna zaune cikin shiga ta al'farmar da
alama suma sun gama shiryawa, ganinsa yasa suka miƙe tsaye, sai kuma suka juyo jin motsin su
Modibbo kusan a tare sukace.

“Wow masha Allah, lallai jini baya ɓuya”.

Suka ƙare mgnar suna matsowa kusa da Modibbo.

Shi kuwa Ibraahim da sauro ya nufi inda za’a gudanar da taron, yana zuwa cikin babban falon taron
masarautar tasu kuwa ya tararda wajen acike maƙil, ƴan uwa duka sun hallara kowa da kowa nasu na
nan, iyaye, kakanni dama jikoki harda ƴaƴan jikoki, babban falon ya cika maƙil, yayinda acan gefe kuwa
wurin da aka warene waje na musamman na zaman amarya da ango zasu zauna a tsakiya.

Sai kuma gefen su Didi dake zaune tare dasu Lalla Hafsa da Lalla Khadija sai sauran matan Abualeey da
yaransa.

Ibraahim na shigowa Rahma ta miƙa da sauri tazo nufoshi tana fad’in.

“Yah Ibraahim, har yanzu baku gama ba, duk an fitofa ku ake jira, dangi duk sun zak’u dason ganin Yah
Aleey.”

“Yanzu zamu shigo, nazo duba yanayin wajen ne.”

Ibraahim ya amsa yana me shakan daddad’an kamshin turaren wutan dake hannunta, wanda hayakinsa
ke tashi acikin kasko.

Cikin sassarfa kuma ya juya, domin yiwa Modibbo da kuma Kakansu Sheykh Jabeer jagora.

A falon ya samesu cikin jin daɗin yace.


“Bismillah mufa ake jira”. Ya faɗa tare da tsayawa gaban Modibbo, yayinda Sheykh Jabeer kuwa yake
gefen damanshi, Zakariyya kuma da Dr Jameel a gefen hagunshi

Kana suka fito cikin Corridor da zai sadasu da falon.

Dr Jameel a hankali ya ɗan ja baya ya koma cikin falon da suka fito ɗin sabida ganin kiran Babynshi.

Amsa kiran yayi tare da maida ƙofar ya rufe.

Su Zakariyya kuwa basuma kula ɗaya komaba.

Sabida Hadiman da suke zagaye dasu.

Tafiya suke a hankali cikin ƙasaita da Kuma nutsuwa, haɗi da tsananin jinin sarautar dake gudana acikin
jinin kowannensu, musamman Modibbo, wanda yake jin kansa acikin wani irin yanayi na daban.

Tsantsar girma yake ji, haɗi da zumma da ƙasaitar da bai tab’a jin kwatan kwacinsa ba, haka suka nufo
babban falon dake cike da dangi da y’an uwa.

Acan side din da Khausar take kuwa, jakadiya ce da kanta tare da Lalla Salma wato mahaifiyar Zakariyya,
suka rik’o Khausar din wacce ta zama tamkar wata flower saboda tsabar kyau, kamshi kawai take
bazawa me tsuma zuciya.

Lalla Salma da takejin Kaunar Khausar har cikin zuciyarta ne ta ɗan sunkuyo da kanta daidai saitin
kunnen Khausar din tace.

“Ki yawaita ambaton sunan Allah a bakin ki har muje mu dawo, Ubangiji Allah Ya kareki daga sharrin
masu sharri, Allah ya tsareki ya kuma kauda idon mak’iya daga gareki, Allah Yasa ki shiga cikin zuri’ar mu
da k’afar dama, alfarmar annabi da al’qur’ani, kiyita adduan Allah ya tsareki da fuskantar k’alubalen da
surkuwarki ta fuskanta lokacin da ta shigo ahalinmu, Allah ya miki al'barka ya dauwa mar dake cikin
farinciki.”

Da “Aameen” ta amsa cikin ranta, yayinda a fili kuwa jinjina kanta kawai tayi, tanajin matar ta kwanta
mata arai, saidai tambayar azuciyarta take wai shin menene ke naɗe cikin tarihin Modibbo waye shi,
meyasa innayi ta koma dashi can? Me hakan yake nufi haka tai ta jerawa kanta tambayoyi?

Tambayar da bazata samu amsarta ayanzu ba.

Ahaka suka ci gaba da tafiya Jakadiya da kuma Lalla Salma na rike da ita, sai kuma Hadimai dake biye
dasu abaya, hadi dasu Asmau Asiya da kuma Dije.
Sassanyan busar sarewa me tsananin dadin jine ya cika kuwannuwan way’anda ke zaune a falon,
kasancewar isowar su Modibbo, wanda hakan yasa duk idanun mutanen dake wajen ya koma kansu.

“Masha Allah, fatabarakallahu fiy ahasanil kali kiyn.”

Shine abunda ke fitowa daga bakin tarin mutanen dake wajen, saboda yanda Modibbo yayi matukar
kyau had’i da k’awatuwa, tsananin kwarjini da haiba sun bayyana akan kyakkywar fuskarsa, da tayi kama
dana mahaifinsa sak, sarautar zalla yau ita ta bayyana kanta ajikinsa.

Yayinda wasu daga cikin mutanen wajen kuwa, suke raba idanunsu wajen kallonsa shida Ibraahim,
saboda tsananin kamar da sukeyi da juna.

Ayau fuskokin da yawa daga cikin masarautar ya cika da farincikin da har ya kasa ɓuya.

Cikin tsananin jin dadi suke wasu dayawa ke fitowa suna rungumar Modibbo, wanda tsananin
kwarjininsa ya haifar musu da soyayyarsa me tsanani.

Cikin sauri Innayi ta nufi inda suke tare da fara ware wannan sandar nan da take ajiye dashi da ƴan
silalla, ware sandar ta farayi daga cikin furen da aka naɗeta.

Tana isa wurin ta tsaya gaba Modibbo tare da miƙa mishi sandar, shi kuwa Modibbo cikin tsananin
mamaki da kaɗuwa ya ware idanunshi a kan fuskarta murya cike da mmki yace.

“Yah Salam wa nake gani a gabana ni Aliyu”.

Murmushi mai cike da farin ciki innayi tare da kamo hannunshi ta danƙa mishi sandar kana tace.

“Innayinka ce a gabanka ba kama bace, nice nan Modibbo nazo maka da tsaraba mafi daraja a gareka
tare da rakiyar masoyanka”.

Ta ƙare mgnar tare dayi mishi nuni da inda su Abban Jameel Malam Arɗo Bappa Jimeta Lamiɗo Haiydar,
suke zaune.

Cikin sauri ya dawo da ganinsa kan Innayi tare da cewa.

“Yah ilahi Abba harda Lamiɗo da kuma Malam Arɗo”.

Sai kuma ya kalli inda ta nuna mishi tana faɗin.

“Harda Umminka ma ba”.


Wani irin amintaccen numfashi ya fesar lokacin da kwayar idanunsa suka sauƙa kan fuskar Ummi,
yalwataccen murmushi ya sakar mata, sai kuma ya kalli Innayi da tuni ta juya ta nufi wurinsu Ummin sai
kuma ya kalli Hajia Bunayyah, tabbas ya ganeta a fili yace.

“Toh ita kuma me haɗina da ita?”.

Sai kuma ya maida kallon sa kan Haiydar dake mishi murmushi a hankali yace.

“Harda Haiydar”. Shi kuwa Haiydar cikin jin daɗi ya kalli Lamiɗo tare da cewa.

“Kai Masha Allah Abba kalli yadda Modibbo yayi kyau, kai shigar sarauta akwai kyau”.

Murmushi kawai Lamiɗo yayi dan ya fahimci cewa shima Haiydar jinin sarautar ne ya motso.

Shi kuwa Modibbo bisa jagorancin Sheykh Jabeer da kuma Ibraahim Zakariyya da Jabeer bin Jabeer ne
yasa yake biye dasu zuciyarsa fal tarin tambayoyi kana da mamakin ganin su Innayi musamman kuma
Lamiɗo barma ace ta Bappa Jimeta da baisan shiba.

Ahaka har suka isa wajen da zasu zauna, Sheykh Jabeer na riƙe da hannunsa.

Saidai kasancewar a tasu al’adar ango baya bazai zauna har harsai amarya ta ƙaraso hakan yasa koda
suka iso wajen zaman tsayawa sukayi, yayinda tuni Fadawa suka zagayesu tare da ware tabka-tabkan
rigunansu sukayi musu ƙawanya.

Suna tsayuwa kuwa suka soma jiyo, wani daddaɗan busa sarewa, me ɗauke da sassanyan kirarin da
akayita da harshen larabci da marabta baƙi.

Wanda hakan yasa gaba ɗaya idanun ya koma saman steps din dasu Khausar ke takowa, domin tuni
anfara shelan zuwan amarya.

Jin hakane yasa fadawan nan kuma janye rigunansu, tare da zagayawa suka koma bayan kujerar da aka
ƙawata dan zaman ango da amarya, yayinda wasu kuma duk suka rusuna ƙasa.

Shi kuwa Modibbo kasancewar yana fuskarta ta inda suke tahowanne yasashi saurin ware idanunshi a
saman lips enshi yace.

“Asma'u?”. Yayi mgnar da ko Ibraahim dake gab dashi baijiba, cikin son fahimtar me ke faruwa ya kuma
kalli Asiya sai kuma ya maida idonsa kan Asma'u dake sakin murmushin, shi kuwa idon shi ya maida ƙasa
tare da fara kallo su daga ƙasa.

Ahankali suke taka kan stairs din da yasha red carpet me masifar kyau da ƙawa yayinda kan ko wanne
step akwai Hadimai gefe da gefe suna riƙe da kaskon turaren wuta.
Asmau ce ke gefen damanta yayinda Asiya kuwa ke gefen hagunta, sai Dije dake gefen Asma'u.

Sai kuma wata ƴar matashiyar Haɗina dake bayanta wacce ita ke riƙe da mayafin da aka sanya mata
akanta, wanda saboda tsabar tsawonsa har jan ƙasa yake yi.

Sunyi matukar kyau da burgewa, hakan yasa duk aka maida kallo kansu.

Tafiyarta me tsananin jan hankali da ma’ana, haɗi da tsananin ƙawatuwar da shigar nata shiya sanya
Modibbo dake tsaye zuba mata ido, duk da cewar baya iya ganin fuskarta, amma tsananin annurin da
take fitarwa ya cika masa ido, yayinda takun da takeyi me kama da tafiyar ɗawisu ya tsaya masa arai,
domin yanajin tamkar ya taɓa sanin me wannan tafiyar, tabbas ya taɓa ganin irin tafiyar.

Jin ana shelar amarya ta iso tare da fara zuba kirari.

Amarya Fatima Zahra mata a gidan Aliyu Youseep Mouleey.

Da sauri ya rumtse idanunsa da ƙarfi dan so yake ya nazarci kalaman.

“Amaryar kuma? Toh amaryar waye? meyasa naji ana kiranta da matarta, wace matarta kuwa? me suke
nufi? Yaushe aka aura min ita? Toh ma wacece ita? Shin wai su waɗannan me suke nufi dani? da zasuyi
ta juya min rayuwa suna sarrafa min abinda basu nemi izininaba". waɗannan tambayoyin su suka cika
zuciyarsa da ta samu kanta cikin tsananin ruɗani.

Shin me ake nufi dashi ne? me sukeson maidashi? wani irin aurene wanda akayishi babu saninsa? Bare
sahalewarsa, toma uban waye yace musu shi ya shiryawa aure a wannan taƙin.

Ya kuma yiwa kansa tambayar yana me tsareta da idanunsa, duk da cewar baya iya ganin fuskarta
saboda mayafin da aka sanya mata.

Ji yayi kansa na wani irin juyawa zuciyarsa kuma na bugawa da ƙarfi, so yake ya buɗi bakinsa ya cewa
Sheykh Jabeer shifa kada a liƙa mishi wata jarabar amman ina ya gaza sabida ruɗanin da yake ciki.

Sun Khausar kuwa ahankali suka ƙaraso cikin parlorn, wasu daga cikin Hadiman dake ta hidima ne suka
nunawa Asma'u Asiya da Dija, wajan zaman da aka tanada musamman domin su, haka yasa cikin nitsuwa
su Asma'u suka nufi wurin zamansu, yayinda Hadiman kuma duk suka zube a ƙasa.

Yayinda su Lalla Salma kuwa suka nufo da ita wajen dasu Modibbon ke tsaye.

Da sassarfa Rahama ta taso ta biyo bayansu.

Lalla Salma ce ke rike da Khausar yayinda kowani taku ɗaya da sukeyi na kusanto inda Modibbo yake.
Hakan ke kara duk’unzuma tunanin Modibbo, wanda yakejin abubuwan suna zuwa masa awasu yanayi
na daban.

Dab dashi Lalla Salma ta kawo Khausar din, tare da sakin hannunta, da sauri Rahma ta ƙaraso hannunta
rik’e da wani babban glass bowl wanda cikinsa ke d’auke da kyakkyawan furanni masu fitar da sassanyan
k’amshi.

Cikin tsananin farinciki ta soma watsa musu furen, Lalla Salma kuwa matsowa kusa dashi tayi, tare da
ɗan ranƙwafowa ahankali tace.

“Abisa al’ada Aleey kai zaka buɗe fuskar amaryar taka ka juyata ta fuskanci family inka su ganta da kyau,
kayi Bismillah ka bud’e fuskarta, idan ka juyata an ganta sai ka riƙe hannunta ku zauna bisa kujerar nan
ka tabbatar kun zauna da bisimilla.”

Cikin sauri ya kalleta hadi da kallon Ibraahim dake gefensa na dama, sunkuyar dakai Ibrahim yayi kana
cikin yin kasa da murya yace.

“Dan Allah Yah Aleey kayi abunda Lalla Salma tace, kada kayi abunda za muji kunya, kar kayi abunda
zaisa mutane su fara tunanin babu abunda ka sani adangane al'adun masarautar da ake tunani za’a
damƙa maka ragamarta a hannunka, kayi hakuri dan Allah Yah Aleey!!”

Ya k’are maganar cikin magiyan, da yasa Modibbon juyawa ya kalli Didi da ta tsura masa ido.

Sai kuma ya ɗan juya idonshi ya kalli Innayi wacce itama kallon nasa take, tare dayi masa alama akan yin
biyayya.

Idanunsa ya dan lumshe tare da shakan numfashin dake kokarin kwace masa sabida tsanantan bugun da
zuciyarsa keyi.

Cikin bada umarni Sheykh Jabeer ya ɗan matse hannunsa dake cikin nasa, kana ya ɗan rongofo tare da
faɗin.

“Kayi abinda ya dace, umarnin kakarkace macen da tasha wuyan rainonka tsawon shekaru, kana kuma
fata ne da burin mahaifiyarka data raini cikinka tsawon wata tara da kwana tara, sannan burin
mahaifinka kanan”.

A hankali ya buɗe lumsassun idanunsa lokaci da yaji zuciysrsa na bashi umarni.


“Buɗe kaga wacece?”. ji yake wani abu na fusgarsa, batare da sani ko shiryawa hakan ba, sai ji yayi
hannayensa na motsi, duk da karkarwar da suke.

Ganin haka yasa Rahma dake bayan Khausar ɗan turo Khausar din tare da cewa.

“Yes my Aunty jeki kusa da mijinki ya buɗe mana fuskarki mu ganki”.

Sai kuma ta ɗan ƙara ɗan tureta kaɗan da kafaɗarta, wanda haka yasa Khausar da zuciyarsa ke buga
lugude tara-tara ta ɗan yi motsi kaɗan da yaɗan ƙara kusancinsu da Modibbo.

A hankali ya ɗan ɗago hannunsa, yatsunsa biyu yasa gefe da gefen mayafin nata ya kamo tare da d’an
d’ageshi sama, yanajin zuciyarsa nayi masa wani irin duka uku uku.

Yana janye mayafin kuwa kyakkyawar fuskarta na bayyana.

Cikin wani irin baƙin al'amari ya zazzaro idanunsa cike da kad’uwa had’i da mamakin ganin fuskar
Khausar, wani irin masifeffen kasalane ya rufe mishi jiki da zuciya, a take kuma yaji wani irin abu mai
masifar sanyi ya tsoki ƙahon zuciyarsa, kana a take ya kuma jin wani irin abu daya harba daga tsakiyar
maɗigan kansa, ya game dukkan sasanjikinsa, har zuwa kan babbar yatsarsa, wani abu me kama da
mamaki, hadi da mutuwar jiki ne suka lullubeshi lokaci d’aya.

Bak’on yanayi me kama da zazzafar bege da bai tab’a jiba ya lullube dukkan jikinsa, dake wani irin tsuma.

Hadi da sanya masa wani yanayi na kaucewar tunanin.

Wanda ya sashi bud’e hannayeshi tare da ware tattausar al'kyabbar dake jikinsa.

Wanda ganin hakan yasa Rahma ɗan ƙara tura Khausar, kasancewar takalmin da ta sanya me tsinine
hakan yasa ta tafiya garesa batare da ta shiryawa hakan ba.

Shi kuwa Modibbo wani irin mataccen numfashi yaja tare da fesar da sassayan numfashi mai dogon
sauti.

Kana ya yayi mata Kekkyawan masauƙi a ƙirjinsa tare bata cikekkiyar kariya

da yalwatacciyar alƙyabarsa ta hanyar bata wani irin kyakkyawan runguma, me ɗauke da ma’anoni masu
tarin yawa, da yafi kama da tsananin shauki hadi da zallar kewa da bege.
Rungumeta yayi tsam a cikin jikinshi ya mannata da ƙirjinsa da ƙarfi har yakai ga suna iya jiyo ɗumin jikin
junansu wanda kuma tuni yayi mata garkuwa da yalwatacciyar Al'kebbar jikinsa mai cike da ni'imtaccen
ƙamshi.

Lib Khausar tayi a jikinshi tare da shaƙan numfashi daya wadatu da ƙamshin turaren jikinsa wasu irin
tagwayen numfarfashi take fesarwa tare da lafewa a jikinshi da kyau tamkar mai tsoron kada a janye
mata shi haka nan takejin tamkar a barta ta rayu a kunshi a haka har gaban abadan haka yasa ta liƙe lip a
jiki nai.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya lumshe idanunsa tare da laso gefen lip inshi sama,

Yanayi ne na musamman a garesu, daya sanya su lumshe jujjuya kwayar idanunsu a tare, musamman ita
Khausar da taji ya lulluɓeta da alkyabbarsa.

Wata duniya ce ta daban me shiɗarwa suka lula.

Cikin wani irin aminci da salama Modibbo ya ɗan sunkuyo kanta kaɗan tare da kawo bakinsa dai-dai
saitin kunnenta.

Cikin sarƙafeffiyar muryarsa me kama da raɗa,cikin tsananin sanyi, ta yanda ita kadai zata iya jiyoshi
atausashe yace.

“I miss you my trouble maker. I really miss you my trouble student.”

Wow gaba ɗaya falon ya kacame da tafi da sowa.

Sai kuma sarewar da ta karaɗe falon.

Ummi kuwa wani irin amintaccen numfashi ta fesar.

Yayinda Didi kuwa tayin ƙasa da kanta tana sakin murmushin.

Su Lamiɗo da Malam Arɗo kuwa duk ƙasa sukayi da kansu cikin konciyar hankali.

Haiydar kuwa wayarshi ya zaro tare da fara musu video, hakama Rahama.

Yayinda tuni kuma masu ɗaukar hoto suka fara kebta musu.
Zakariyya ne ya ɗan zunguri kafaɗar Modibbo da tashi kafaɗar tare da cewa.

“Kai Jinin Mouley a tsakiyar mutanefa kuke, ka ritsa yar mutane kamar zaka maidata cikin ƙirjinka”.

A can sama ya jiyo muryar Zakariyya wanda ya sashi buɗe idanunsa a hankali.

Hango Lalla Khadijah da wasu mata a ƙalla su bakwai ne ya ɗan sashi sassauta rungumar da yayi mata.

Tare da ɗan jan baya kaɗan.

Fuskashi ya ɗan tsuke tare da kara ronƙofo da kanshi a hankali yasa bakinshi dai-dai iunnenta murya can
ƙasa yace.

“Toh yau dai burinki ya cika ai, na ruggume ki, hankalinki ya kwanta tunda kinji ɗumin jikina ko? Kin
samu abinda kikeso ko”.

Mui-mui tayi da bakinta

Kara matseta ya ɗanyi tare da cewa.

“Rashin kunya zakiyi minko”.

Baki ta ɗan tura tare da cewa.

“Ni ka sakeni”.

Ɗan haranta yayi tare da cewa.

“Kece ai kike riƙe dani mayya uwar son jiki, tashi min a jiki Mage”.

Da sauri ta ɗan janye jikinta kaɗan.

Dai-dai lokacin kuma Khadijah suka iso.

Kusan a tare suka fara yi musu wani irin....!

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta abinki cikin Salamah 1k ne kacal 0661110170
GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N 09097853276
in tura miki abinki ki karanta cikin salam ba tare da kin karanta na Allah ya isaba*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH
47

*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n
nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai
sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan
mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in
kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a
banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account
no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na
faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki
kenan*

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito
miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar
infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita
tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a
saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda
yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin
san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo
kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki,
domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan
ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah
zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce
dai GARKUWAR MA'AURATA.

47

Lalla Khadija da Lala Hafsat tare da wasu mata cousing Sister sa ne suka fara yi masu liƙi, cike da
nutsuwa da kuma tarin farin ciki dake bayyane asaman fuskokinsu.

Sarkin Zagi dake can gefe riƙe da Microphone ya matso dashi kusa da bakinsa kana yace.

“Maraba da Lalla Hafsat, Lalla Khadija, Autah Rahma tare da sauran Yayyun ango da ƙannensa”.

Su kuwa cike da farin ciki suka ci-gaba dayi masa liƙi bayan sun gama Lalla Khadija ta ɗan matso kusa
dashi tace.

“Kayi sauri ka buɗe fuskar Amayarka ta juya ta fuskanci dukan family”.

Ta ida maganar tare da juyawa suka bar wajen.

Shi kuwa Moddibo hankali ya ɗan ƙara matsota, cikin yanayin da shi kansa ya gaza ta tacewa, ya ɗago
lallausan tafin hannunsa tare da ware ƴan yatsunsa ya kama kafaɗar ta kana ya juyar da ita ta fuskanci
Al'ummar cikin falon baki ɗaya.

Lokaci ɗaya cikin falon ya kaure da tafi Raf-raf-raf yayin da duk wanda yayi arba da fuskar Khausar suke
kallonta cikin tsananin farin ciki da ganin baiwar kyau da Ubangji ya zuba mata suke faɗin.

“Wowwww Masha Allah”. Shine abinda mafiya yawansu suke faɗi.

Lokacin guda kuma wasu zugan matasa wanda sun kai goma sha biyar suka nufo kansa cike da izzah,
nutsuwa, ƙasaita suke musu liƙi yayin da sautin busar sarewa da ƙaran algaitu ke tashi da sassayan kiɗan
jita...
Moddibo kuwa ahankali ya ɗan juya kwayar idanunsu, ya kalli Khausar, sai kuma ya fesar da wani irin
sassayyan numfashi, tare da matse hannun ta dake cikin nasa, cikin wata irin sassautacciyar muryansa
yace.

“Toh Mazari Sarkin rawa.

ba kinji Busar sarewa da kiɗaba, kiyi rawa na.

Kiga abinda zanyi miki”.

Cikin narke fuska tace.

“Toh ni nace zanyi rawane”.

Ɗan juyo fuskarsa yayi ya ɗan kalleta tare da hura mata iskar bisa idanunta ganin yadda take jujjuyasu,
numfashi mai nauyi ya fesar tare da cewa.

“Uhmm kimayi mana ki gani in ban karya ƙugun naki ba!”.

Kallonsa tayi da shanyayyun idanunta wanda yasa bai san lokacin da ya ƙara rumtse tafin hannunsa da
nataba.

Ita kuwa cikin yin mui-mui da da bakinta kana ta tsukesu Pinch lips ɗin ta tana ɗan motsawa ahankali
alamar magana take ƙasa-ƙasa sai dai baya jin abinda take faɗa.

Sunkuyawa kanta kaɗan yayi tare da cewa.

“Ni kike turawa baki ko?”.

Ɗan kallonshi zuciya cike da ganin girmansa kimarsa gami da darajar da kuma wani matsayi na
musamman da takeji a jikinta wanda yake sakar mata kasala da son ƙamshin jiki nai,

Hararanta ya ɗanyi kana a hankali yace.

“Ci gaba da tura min baki, zanyi mgnin lips en nan, idan na tsinkesu zanga dame zaki kuma yimin rashin
kunya kije ƙiyama kuma Allah ya ƙonasu tunda mijinki kikeyiwa tsiwa”.

Wani irin lumshe idanunta tayi sabida yadda taji kalmarsa ta karshe ta ratsa mata jiki da zuciya har yasa
tsikar jikinta tashi.

Yanayin yanda suke magana ƙus-ƙus ne da yadda suke kallon juna yasa Ummi dake can wajen zamanta,
ta saki amintaccen murmushi cike da jin daɗi, mgnar Jameel ɗinta ya tabbata, domin duk wanda ya
kallesu zaiyi zaton hirar soyayya suke.

Yayin da zugan matansa suka cigaba dayi masa liƙi wasu baza su wuce sa'annun saba wasu kuma baza
su gaza shi ashekaru ba Zakariyya da Ibraahim dake tsaye suma suka shiga cikinsu suna musu Liƙi...

Sarkin Zagi dake riƙe da Microphone ya gyara masa zana tare da kaiwa bakinsa kana yace.
“Duk wa'anan Cousing Brother's ɗin Ango ne, Ƴaƴan Baffanunsa,da kuma ƴaƴan Goggonninsa”.

Bayan sun gama Liƙin suka juya suka fita kana suka koma wajen zamansu.

Ibraahim kuwa kallon Moddibo yayi kana ya mishi alama da hannu su zauna.

Anutse Moddibo ya gyaɗa masa kai kana cikin nutsuwarsa ya koma ya zauna itama Khausar ta zauna
gefensa kasancewar 2sitter ne.

Hakan yasa suka samu kusanci tsananin su bayansu flowes ne masu kyau da ƙamshi sai kuma Hadimai da
suma ke tsaye bayansu.

Wani irin yalwataccen murmushi mai cike da Aminci Innayi ke saki tana mai cigaba da kallonsu.

Acan ɓangaren Lamiɗo kuwa mamakine ya kamashi aransa yace.

“Toh dama yaran nan suna soyayya da junansu ne? Koko yaya”.

Sosai yake mamakin yanda suke gudanar da komai tamkar akwai da ɗaɗɗiyar soyayya da shaƙuwa atare
dasu.

Haiydar kam hotuna da Video yake ɗaukar su, kai tsaye yake turawa cikin groups ɗinsu na family.

Cikin nutsuwa da ƙasaita kana da yalwataccen farin ciki Abualeey da Didi suka tasu,Yayin da Waziri,
Galadima, Sarkin Fada, da sauran manya suka mara musu baya, daga can bayansu kuwa Hadimai ne ke
biye dasu.

Suna isa dai-dai mazauni Moddibo da Khausar suka fara yi musu Liƙi cike da girma, sai kuma aka ƙara
ssutin Busa sarewa da kuma sautun jitan daya karaɗe baki ɗaya ilahirin wajen...

Didi dake cikin wata shiga na alfarma cikin jin daɗi ta ɗan sunkuya tare da sanya hannunta na dama ta
ɗan ɗago Fuskar Khausar ta kalleta.

Ido ta lunshs sabida jin lokaci ɗaya yarinyar ta kwanta mata arai, tana jin masifar ƙaunar yarinyar sake
sunkuyawa tayi ta rungumeta, sai kuma ta ɗago tare da tallabe fuskan Khausar kana ta sanya laɓɓanta
akan goshinta tayi mata kiss.

Fuskarta ɗauke da amintaccen murmushi tace.

“Allah ya miki albarka, Ubangji Allah yasa kin shigo da ƙafar dama, Allah ya baku zaman lafiya mai
amfani, mai albarka”.
Lumshe ido Khausar tayi yayin da take jin nutsuwa da ƙaunar matar na ratsa sassan jikinta...

Abualeey kuwa hannunsa na dama dake ɗauke da Zoben azurfa ya ɗaura akan Moddibo tare da faɗin.

“Allah ya maka albarka Ubangji Allah ya albarkanci rayuwarka. Allah ya baka zaman lafiya da matarka!”.

Haka nan Moddibo yake jin wani irin farin ciki ji yake yau kamar ranan Sallah ne, sabida wani irin nishaɗi
da yakeji tamkar wanda aka yiwa bushara da Aljanna asaman lips ɗin sa yake amswa da.

“Ameen Ameen”.

Haka nan yake jin farin cikin addu'ar da Mahaifiyar sa da Mahaifinsa keyi masa...

Liƙi suka cigaba dayi musu suna zuba musu kuɗi kamar ba'asan darajar su ba...

Sarkin zaki kuwa hannunsa riƙe da Microphone yace.

“Hattara dai manyan bisa kanku wan'nan sune manyan ƙasar Morocco baki ɗayanta. Jiga-jigan manyan
cikin birnin Rarat baki ɗaya manyane bisa kanku ku amsa da Ameen dan addu'a ce ta manyan Ameen.

Baki ɗaya mutanen falon suka amsa da.

“Ameen”.

Saboda sun san cewa addu'a da fatan Al'khairi iyayensa ke masa bayan sun gama suka juya suka tafi...

Aunty Ruƙayya da farin ciki ya gama cikata ganin yanda Moddibo da Khausar sukayi bala'in da cewa ga
kuma yanda Moddibo ke raɗawa Khausar magana akunne wanda duk mai kallonsu a matsayin zantukan
masoyane sukeyi yasa ta kalli Hajiya Bunayya wacce itace akusa da ita kana tace.

“Dan Allah Hajiya kalli Khausar da Moddibo tamkar dan junansu aka halicce su, haƙiƙa sun dace da juna
Allah yayi Khausar zaɓi da mafi Al'khairi Ubangiji ya kawar da idanun maƙiya akansu”.

Yaƙe Hajiya Bunayya tayi Amaimakon tace Ameen sai ta sunkuyar da kanta tayi tare da cewa.

“Aikam”.

Wani irin zafi da ƙuna zuciyarta keyi ba zato taji hawayen hassada da ƙyashi na zuba daga idanunta ina
ma ace Aminanta ce ke cikin wannan Daular duniya..

Daga can cikin falon kuwa Wasu zugan Maza da Mata manya ne suka nufi wajensu Moddibo da Khausar.
Sarkin Zaƙi na ganinsu ya ɗaga sautin muryarsa tare da cewa.

“Hattara dai Ango da Amarya ga Baffanayenku nan da Goggoninku”.

Ahankali Moddibo ya ɗaga kai yana kallonsu cikin wani irin yanayi mara misaltuwa wai yau shine acikin
ahalinsa ana gabatar mishi dasu sahu-sahu.

Su kuwa cike da tarin ƙaunarsa suka riƙa yi musu liƙi da kuɗaɗe masu tarin yawa.

Aunty Hawwa ce ta kalli Aunty Hajara wacce suke daga ɗaya gefen Hajiya Bunayya kana Aunty Hauwa
tace.

“Masha Allah Kinga yanda ake zubar da kuɗi tamkar ba'a cikin tsadar rayuwa”.

Dariya Aunty Hajara ta sanya tare da cewa.

“Aikam acikin wannan ahalin. Basuma san wani abu mai suna talauci ba komai nasu cikin wadata suke”.

Da ƙyar Hajiya Bunayya dake sauraransu ta haɗiye wani abu mai masifar ɗaci daya tokare mata maƙoshi
Allah ne kaɗai yasan tashin hankali da ɗimuwar hassada da take ciki...

Haka aka riƙa gabatarwa Moddibo da ƴan uwansa

Abokan arziƙi, ƴaƴan Baffaninsa. Da ƴaƴan Goggoninsa sahu-sahu.

Kana bayan an gama aka shiga gabatar masa da Hadimansa wanda zasu riƙa yi masa Hidima.

Bayan an gama wannan.

Jakadiya dake tsaye gefenshi riƙe da wasu Ƙore guda uku ahannunta babban na cike da madaran Shanu
fari ƙal.

A hankali ta ajiye su agaban timtim da ƙafan Khausar ke kai sai kuma ta ɗauki ƙamarin Ƙwaryan ta ajiye
acikin wanda yake ɗauke da ɗanyen madaran Shanu.

Kana ta ɗauki ɗayan mai matsakaici, tare da matsowa gefen Moddibo ta risina tare da cewa.

“Bismillah zaka wanke ƙafan Amarya da madara da fatan Ubangji Allah ya kareta daga sharrin da yake
cikin fadar nan kana Allah ya haɗa ta da Alkhairan dake ciki”.

Juyawa Moddibo yayi tare da kallon Ibraahim da ya dafa kafaɗarsa.


Asma'u kuwa Lumshe idanu tayi tana kallon ƙawarta cike da annashuwa kana tana mamakin tarin
al'adunsu masu matuƙar kyau da tsari babu wani abu na bidi'a aciki komai bisa tsari suke gudanar wa...

Ibraahim kuwa dake dage da kafaɗarsa cike da so da girmamawa yace.

“Bismillah Yah Aleey Don Allah kayi mana”.

Lumshe idanu Moddibo yayi tare da ɗaga juya kanshi ya kalli Innayi wacce keji tamkar ta taso tazo ta
ɗagashu tasa yayi dukkan abinda ya dace.

Ganin alamun zaƙuwa tare da itane yasashi miƙewa a hankali kana ya dawo gaban Khausar ya zauna
akan kujeran da aka ajiye kusa da tum-tim ɗin kujerar da Khausar ke kai kana ya zaune.

Sai kuma ya ɗan kalli Ibarahim dake cewa.

“Ɗa ƙafar dama zaka fara”.

Ɗan hararan Ibraahim yayi kana ya ɗan ronƙofo kaɗan ya sunkuya, a hankali ya sanya hannunsa na dama
ya kamo ƙafan Khausar na dama tare da zare mata takalmin, tare da tsirawa fatar kafar lumsassun
idanunsa,

Zakariyya ne ya ɗan yi gyaran Muryar da ya sashi,

Ɗan Lumshe ido kana ya buɗesu a hankali, yatsunta sunyi masifar kyau, kana faratun ƙafan ayanke suke
fes-fes gwanin ban sha'awa.

Aransa yace ikon Allah wannan ita kuma haka tabar ƙafar nata.

Kansa ya ɗago tare da kallon kyakykyawan fuskarta dake fitar da annuri kana ya tsuke fuska ya ɗan
harareta tare da cewa.

“Ko Amaryar shamuwa ana sa mata lalle. Amma ke naga alamun Amaren buzuzuma sun fiki ƙyalli”.

Jin abinda yace yasa ta tura baki da ɗan juya ido.

Ƙafanta ya jawo kana yasa cikin ƙwaryan dake gabansa wanda babu nono aciki ɗan matse ƙafar yayi har
saida ta ɗanyi ƙara, shi kuwa wani murmushin da shi kaɗaine yasan ma'anarsa yayi.

Jakadiya kuwa nono ta ɗebo aƙaramin ƙwaryan ta miƙa masa.

Ita kuwa Khausar jin yadda yaja ƙafanta yasa ta risino wanda dai-dai lokacin take tura baki..

Karaf sai akan idanunsa ware manyan idanunsa yayi kana ya motsa laɓɓansa tare da faɗin.

“idanfa kina hararana, ƙwaƙule idanunki zanyi, kafin kije Lahira Ubangji ys ƙona miki su”.
Saurin kallonsa Khausar tayi jin abinda yace girarsa ɗaya ya ɗaga mata tare da cigaba da faɗin.

“Yess ai na lura bakisan daraja da girman miji bako?”...

Uffan batace masa sai ma lumshe idanunta da tayi tana jin yanda ɗumkn tafin hannunsa ke ratsata...

Hannunsa na dama yasa ya tallafi ƙafartata kana ya karɓi ƙwaryar Nonon da hannunsa na hagu
ahankali yake zuba Nonon akan ƙafarta...

Yayin da aransa yake tuna tabbas ya taɓa sanin wannan al'adar amafarkinsa da yake yawanyi...

Cike da nutsu da kuma ƙwarewa yake wanke ƙafafunta daga dai-dai idon sau zuwa kan zara-zaran yatsun
ta ya wanke fess.

Ita kuwa sai mutsu-mutsi take da yatsun ƙafarta ɗan ji take kamar jakul-ku-kuli yake mata,'.

Yana gama wanke wa sai ga Didi da kanta wani farin ƙyalle mai masifar haske da ƙamshi ta miƙa masa.

Juyawa yayi yaga Mahaifiyarsa tsaye da kanta take bashi.

Didi kuwa kai ta jinjina masa alamar ya karɓa.

Ba musu ya karɓa tare da gogewa Khausar ƙafanta kana ya mayar cikin takalmin ta, sai kuma ya zaro
ƙafara na hagu ya wanke kamar yanda yayiwa na damar.

Wani farin ƙyalle kamar na farko mai azabar ƙamshi Didi ta sake miƙa masa ya goge mata ƙafar kana ya
ajiye.

Kallonsa Didi tayi tare da faɗin.

“Toh ka matso da kyau sai ka tallafi ƙwaryar Nonon cinyaka kasa hannunta duka biyu ka wanke”.

Da ɗan sauri ya ɗaga kansa ya kalleta.

Lumshe idanu tayi alamar kayi ɗan Albarka.

Kai ya jinjina hakan yau yake jinsa wani irin farin ciki mara misaltuwa tamkar wanda aka yiwa bushara da
gidan aljanna.

Kujeran yaja ya matsa kusa da Khausar sosai yayin da Gwiwoyinta ke gugan Gwiwoyinsa.

Bakajin saurin komai sai busan sarewa da tashin jits, Yayin dasu Ibraahim kuwa suka koma ta bayansa
suka tsaya, gudun kada su tsaya agaba su tare wa ƴan baya,

Hotuna yimusu ake yi babu tsayawa tako wacce kusurwa hoto ake musu, yayin da Yayunsa ke zuba
musu Liƙi.
Ahankali ya kamo lallausan tafukan hannunta ya riƙe acikin nasa kana ya tsunduma su acikin ƙwaryar
Nonon da Jakadiya ta ɗaura masa akan cinyarsa wanda aka zuba wasu Jajayen Flowes masu kyau da
tsari.

Cikin nutsuwa ya fara wanke hannun, tare da ɗan jan ƴan yatsunta, a hankali, ya ɗan ƙara ware
idanunsa lokaci da ya ja ƴar ƙaramar yatsarta ta hannun hagu, gani yadda ta tara faratunta sunyi zaƙo-
zaƙo irin dai yanda ƴan matan zamani keyi, sai dai sunyi masifar kyau musamman ma na ƙaramin
yatsanta na hagu duk yafi sauran faratun tsawo, matse hannun yayi acikin nasa.

Runtse idanunta tayi cike da raki da shagwaɓa ta furta.

“Wash! Allah”.

Ta faɗa tare da sunkuyo da kanta haɓarta na taɓa goshinsa ahankali ya ɗago kanshi, wanda hakan ya
bawa hancinsa damar gogan hancinta.

Cikin tsuke fuska ya sanya ƙwayar idanunsa cikin nata tare da faɗin.

“Meye amfanin wannan farcen da kika bari ajikin ki?”.

Cikin sanyi tace.

“Dan yin susa in ƙaiƙayi ya dameni”.

Sosai ya daure wurin danne yanayin da muryata ta sashi a ciki, a hankali ya ɗan matse yatsar kana a
hankali yace.

“Shin bakisan cewa shi farce shine rumfar shaiɗan ajikin ɗan Adam ba?”.

Shiru tayi ba tare da ta cire idonta daga kan sajenshi da takeyiwa kallon kurillaba.

Shi kuwa numfashi ya fesar tare da cewa.

“Ya za'a yi ki tarawa sheɗan Mafaka ajikin ki?No wonder shiyasa kika cika rawan kai ashe muhalli kikayi
ibilis a jikinki”.

Bakinta ta tura tana kallon yanda yake matse mata hannu.

Shi kuwa Moddibo cikin sanyin murya ya cigaba da cewa.

“Shiyada duk rashin ji da neman mgn duk kece a gaba ashe-ashe muhalli kika tarawa sheɗan agangar
jikinki. Toh kiji da kyau, ko kiyanke faratun nan ko kuwa idan na tashi da kaina zan haɗa da ƴan yatsunki
in yanke kana na wurgawa karnuka su cinye”.
Cikin yanayin tsoronsa da sanyin murya tace.

“Dan Allah ka sake min hannuna zafi fa yake min”.

Sake matsawo kusa da ita yayi tare da faɗin.

“Bazan sake ba”. Da sauri tace.

“Afwan”.

Cikin kasala yace.

“Sai kinyi al'ƙawarin zaki yanke farcen”.

Da sauri ta gyaɗa masa kai cikin narke fuska tace.

“Nayi al'ƙawari zan yanke amma zan bar ɗaya”.

Fuska ya ɗaure tare da faɗin.

“Ban yarda ba duka zaki yanke”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Na yarda zan yanke toh ka sake min hannu”.

Wani irin murmushi mutanen dake wajen sukayi yayinda wasu ke binsu da kallon sha'awa.

Asma'u kuwa hannu ta miƙawa Dije dake gefenta suka tafa cikin yanayin farin ciki Dije tace.

“Asmeey kinga wata Madarar soyayya kamar a Indi'a muke, lallai na yarda cewa Ustazan nan sunfi kowa
iya soyayya”.

Kai Asma'u ta jinjina tana mai binsu da kallon sha'awa yayin da aranta take musu addu'ar samun dawwa-
Mam-miyar farin ciki tace.

“Ai kam ko tattabaru bazasu gwadawa su Khausy zama da junaba, kinaga wani irin mayataccen kallon da
Yah Modibbo keyi mata, ko me yake gaya mata?”.

Da sauri Aseeya tace.

“Sai Allah gashi dai tun ɗazu suketa wani ƙus-ƙus ji Khausar yadda take lumshe ido”.

Dariya sukayi dukansu


Zakariyya kuwa cikin sarawa salon Modibbo ya ɗan sunkuyo daf da kunne Moddibo kana yace.

“Dan Allah ka riƙa tunawa, cikin mutane da kuke.

Na lura gaba ɗaya ka zauce ƙa kauce hanya baki ɗaya, ka wani gigice daga ganin yarinya kana ƙoƙarin
taɓarewa acikin tsakiyar taron al'umma duk kuma wani narkewa”.

Khausar kam kanta na ƙasa Zakariyya kuwa cike da sheƙiyanci ya cigaba da cewa.

“A cikin Family fa kake ba cikin falonku kuke ba”.

Shi kuwa Modibbo Numfashi ya sauƙe mai nauyi A ransa yace.

ohhh ni Aliyu na lura Zakariyya magana ne abakinsa shida. Dr Jameel sai dai Allah ya shirye su.

Hannunsa na dama yasa ya damƙe nata da ƙarfi, sai ya zama na kamar sunayin musabaha ne.

Sai kuma yayi shiru tare da rintse idanunsa da sanya haƙoransa ya cije gefen lips ɗinsa na ƙasa kana ya
sunkuyar da kansa ƙasa, wani irin abu yake ji tun daga tsakiyan maɗigan ƙwaƙwalwar kansa, har zuwa
tsakiyar tafin ƙafarsa, lokaci ɗaya yaji gangar jikinsa ya fara tsuma baki ɗaya jikinsa ya fara tsuma amma
ta ciki yanda babu wanda zai fahimta sai shi...

Ibraahim ne ya tsugunna kansa tare da faɗin.

“Bismillah Yah Aleey, Continue”.

Jin muryan Ibraahim yasa ya fesar da sanyayyan numfashi sai alokacin ya fara dawowa hayyacinsa.

Ahankali ya buɗe Idanunsa da suka kaɗa sukayi Jawur ya kalli Khausar yana mai jan wani dogon
numfashi da ɗan ƙarfi ya sauƙe numfashin kana ya ɗago idanu ya kalleta.

Da sauri ta fito da idanunta waje ganin yanda ƙwayar idanunsa suka sauya launi baki ɗaya.

Khausar kuwa ahankali tace.

“Ayyah kasake min hannu na zafi”.

Numfashi ya fesar tare da sakin hannu kana ya kamo yatsunta.

Didi dake tsaye ta dauki wani ƙyalle me kyau kamar farko ta miƙa masa karɓa yayi kana ya goge mata
tafin hannun zuwan ƴan saffa-saffa yatsunta.

Rahma kuwa kaskon turaren wuta dake fitar da wani Masifeffen ƙamshi ta miƙa masa.
Ƙamshin da ya fara gigita masa tunaninsa lokaci ɗaya ya fara jin wani irin yanayi yana game masa gangar
jikinsa da ruhinsa baki ɗaya.

Kaskon turaren wutan ya ɗaura akansa kasancewar gindin Kaskon nada faɗi sai ya kamo hannayenta ya
kife akai.

Ahankali hayaƙin turaren wutan ke ratsa yatsunta yana buga fuskanta.

Mai busa Algaita ne ya cigaba da busawa dare da haɗawa da kirari.

Sarkin Zaƙi kuwa hura Microphone yayi tare da cewa.

“Idan akwai ƙanin Amarya ko ƙanwar amarya ta fito, ta amshi kaskon bisa al'adarmu”.

Cikin sauri Haiydar dake ta faman Video ya miƙe ya fita kana ya zare Kaskon turaren wutan kasancewar
haka Al'adarsu take.

Shi kuwa Haiydar sunkuyowa kan Khausar yaui tare da faɗin.

“Kai Addah Khausi kunyi kyau.

Kinga yanda kika zama kamar wata acikin taurari baki ɗaya ke kike haska wajen nan”.

Kallonsa tayi cikin yanayi gajiya, sai kuma ta ɗan hararesa kana tace.

“Dole mana kace haka tunda ni kaɗai ce ƴar Uwarka”.

Murmushi yayi kana cikin gaskiya da gaskiya yace.

“Wallahi ba haka bane Addah Khausy kinyi masifar kyau fa”.

Ya ida maganar tare da miƙawa Jakadiya Kaskon.

Jakadiya kuwa da ido ta yiwa Moddibo alamar ya tashi ya koma kan kujera.

Kai ya gyaɗa tare da komawa mazauninsa.

Haka ma Didi da yayunsa suka koma wajen zamansu...

Sarkin Zaƙi kuwa cike da rakaɗi yace.

“Alhamdulillah da wannan al'adar tamu mu kazo ƙarshen wannan taro na yau, sai kuma gobe idan Allah
ya kaimu bisa dai da lafiya, za'a fitar da Aleeyu Youseep Muhammad Mouley atsakiyar fada, domin
gabatar dashi atsakiyan Fada a matsayinsa na sarki mai jiran gado”.
Daga nan aka tashi kasancewar ƙofofine da dama cikin falon, yasa lokaci ɗaya duk aka fita cikin
nutsuwa batare da wani cunkuso ba duk da kuwa yawan mutanen.

Acan ɓangaren Innayi kuwa cikin sauri ta nufi wajensu Moddibo tare da riƙe hannun Khausar ta juya.

Moddibo kuwa baki ɗaya Cousing Brother's ɗin sa ne suka riƙa bashi hannu suna rungumesa cike da
ƙaunarsa tare da gabatar mishi da sunayensu da dangatakar su.

Shima cikin yalwataccen farin ciki yake rungunarsu.

Kafaɗarsa Zakariyya ya dafa tare da faɗin.

Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta abinki cikin Salamah 1k ne kacal 0661110170
GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N 09097853276,
in tura miki ki karanta abinki salamun Salam.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

48

Assalamu alaikum mutanan arziki masoya kamshi ma abota kamshi Amaren kamshi masu jargon kamshi
Yammata wadanda sukasan darajar kamshi ni Aysha Aliyu Garkuwa na kawo muku tallan wasu
Amintattun turarukana masu matukar kamshi da Kama jiki

Masu saukin farashi sannan ga biyan bukata

Yarhjya_incense_and_more

Ta shirya tsaf domin ta gwangwajeku da Turaruka na alfarma

Farar khumrah

Bakar khumrah

Turaren Wanka

Oil 6ml 1
Oil 12ml 1

Turaren fesawa 100ml 24 hours guda 1

Duka Akan 8k kacal

Sannan kayanta suna tafiyane da guarantee duk wacce tasiya taji babu kamshin nan na alfarma ko
kuma basuda lasting to tayi alkawarin mayar muku da kudinku

Wannan garabasar zata kare on 5th September insha Allah

Ku hanzarta ku mallaki naku domin kayan yarhjya babu Danasani a cikinsa saidai kuyi alfahri da siyan
kayanta

Account number 1419787445 Amina Umar usman access bank

Kitura evidence of payment to

08092664954

Kuyi saving number TA domin ci gaba da ganin Turaruka Kala Kala

Normal price

Bakar khumrah 1500

Farar khumrah 2k

Turaren Wanka 1500

Oils 6ml 800

Oils 12ml 1500

Turaren fesawa 100ml 3500

Turaren fesawa 50ml 2k

Kayanmu available ne a koda Yaushe

Akwai turarukan wuta na jiki na Kaya Dana daki duka sai Wanda kika zaba

48

“Kazo mu koma ciki Maghriba tayi muje muyi alwala mu tafi masallaci”.
Cikin gamsuwa ya gyaɗa kai,

Ibraahim kuwa hannun Moddibo ya riƙe tare da faɗin.

“Yah Aleey daga yanzu zaka riƙa zuwa jam'i yanda kake buri da fata da marari”.

Sanyayyan numfashi Moddibo ya fesar kana yace.

“Alhamdulillah, dan babu abinda nafi bege kamar zuwa sallah jam'i da kuma Innayi na”.

Ya ida maganar tare da bin bayan Ibraahim suka fara tafiya.

Tuni ƴan Uwa sun fiffita falon ya rage babu mutane sai ɗaɗ-ɗaya.

Innayi dake riƙe da hannu Khausar ta nufi wajensu Ummi tare da faɗin.

“Kuzo mu koma masauƙinmu sai kuma gobe idan Allah ya kaimu, za'a cigaba da hidima”.

Sheikh Jabeer kuwa da kansa ya nufi inda su Abban Jameel ke zaune yace.

“Kuzo mu tafi Maghriba ta ƙara to”.

Kai suka gyaɗa kana suka miƙe suka bi ta ɗaya ƙofar suka tafi.

Moddibo da su Ibraahim kuwa a hankali suke tafiya cikin nitsuwa auka shiga Corridor da zai sada su da
falon Side da suke.

Su Khausar kuwa sun fara haurawa kan steps din.

Asma'u ta juya da sauri ta kalli Ummi tare da faɗin.

“Ayyah Ummi bari inje na gaida Yah Moddibo in faɗa masa saƙon Bashir”.

Ƴar dariya Ummi tayi kana tace.

“Bismillah keda ɗan Uwanki”.

Kai ta gyaɗa cikin sauri ta juya ta nufi wajensu Moddibo tana faɗin.

“Yah Moddibo! Yah Modibbo”.

Moddibo kuwa Already sun riga sun shiga falon da Dr Jameel ke ciki.
Shi kuwa Dr Jameel jiyo motsinsu ne yasa ya sassauta murya cikin wani irin yanayi da yake ciki bisa ga
duk kan alamu hirar batsa suke awayar cikin lumshe idanu yace.

“Please Baby kiyi haƙuri muna cikin wani Uzuri ne fa na Fada”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Ok bye bye Amma please kazo Ina jiranka, kasan cewa kwana biyu bamu haɗu ba ina kewarka”.

Ta ida maganar tare da katse kiran.

Dr Jameel na miƙewa su Moddibo na shiga....

Cikin yanayin takaicin halayyarsa Zakariyya ya maka masa harara tare da cewa.

“Wallahi kai dai kam Jameel kayi asara, komai aka shirya da kai da zaran mace tashiga ciki saita ware ka
cikin mu, musamman wannan shegiyar Baby na rasa yanda zanyi in raba ka da ita”.

Moddibo dake jinsu ne ya girgiza kai kana yace.

“Alhamdulillahi kaima kenan abin na damunka Zakariyya?”.

Kai Zakariyya ya gyaɗa yana mai cigaba da hararan Dr Jameel dake murmushi yace.

“Sosai ma kaga an tsara fitan nan dashi amma dayake shi Mamajone mayen mata, ni wlh ban na lura da
lokacin daya zame ya dawo ciki ba, sai da muka shiga na gane baya tare damu”.

Sai kuma Moddibo yayi saurin juyawa jin muryan Asma'u na cewa.

“Yah Moddibo”.

Da murmushi afuskarsa yace.

“A'a Asma'u”.

Asma'u kuwa idanunta ta zare tare da ɗaura hannunta ɗaya akai kana ta buga ɗaya hannunta a ƙirjinta
tare da faɗin.

“Yah Jameel”.

Tayi maganar idanunta na kan Dr Jameel dashi ma ita yake kallo.

Cikin sauri Moddibo ya juya ya kalli Asma'u sai kuma ya juya ya kalli Dr Jameel.
Cikin yanayin kaɗuwa, mamaki, Al'ajabi ta fara takowa har ta isa gaban Dr Jameel ta tsaya cikin sarkewar
murya ta furta.

“Yah Jameel”.

Kallonta Moddibo yayi tare da girgiza kai yace.

“A'a Asma'u”.

Cikin ficewar hayyaci ta ɗaura hannunta akai tare da faɗin.

“Ummiiii kizo ga Yah Jameel”.

Sai kuma tayi baya luuu idanunta sukayi sama.

Cikin wani irin sauri Dr Jameel da tun time data kira sunansa ya zuba mata idanu yana kallon ƙiranta da
kuma yanda Ubangji ya ƙawata surarta, lokaci ɗaya yaji wani irin yanayi da bai taɓa jin makamancin sa
ba akan ko wacce irin mace da yake mu'amala da ita karon farko yaji wani irin tsarkakekken soyayyar ta
ya mamaye masa zuciya.

Azabure ya nufe ta ganin saura kaɗan takai ƙasa ya tallafota jikinsa ta faɗa kan ƙirjinsa asume.

Faɗawa jikinsa da tayi yasa ya koma baya ya faɗa kan kushin ya zauna, hannunsa yasa ya tallafo fuskarta
sai kuma ya ɗaga kansa ya kalli Moddibo kana yace.

“Suma fa tayi”.

Cikin Sauri Moddibo ya riƙe tsintsiyar hannunta cikin yanayin damuwa yake faɗin.

“Asma'u”.

Ina tuni ta samu kallon Ibraahim yayi kana yace.

“Ibraahim ka miƙo min ruwa”.

Dr Jameel kuwa kallon Moddibo yayi cikin wata kasalalliyar murya gami da shauƙi yace.

“Ya dai kake shiga hurumin daba naka ba, ya ina matsayin Dr sannan ta suma ajikina kake cewa amiƙo
maka ruwa”.

Wani kallo Moddibo ya mata tare da watsa masa harara kana ya buga masa tsawa da faɗin.

“Kai Mahaukacin ina ne ya yarinya zata suma sannan ka tsaya kana maganar sai huruminka wani irin
hurumi kake dashi a kanta, idan zakayi abinda zata farfaɗo kayi ka wani maƙale yarinya atsakanin cinya
haukane akan ka”.

Kallon Moddibo yayi tare da juya idanunsa kana yace.


“Kamar ya kake cewa haukane akaina Ni naga matar Aure”.

Cikin tsawa da hararansa Moddibo yace.

“Koma yayane yanzu kayi abunda yarinya zata farfaɗo”.

Ahankali Zakariyya ya tsugunna kansa tare da bubbuga kumatunta yana kiran sunan da yaji Moddibo na
kiranta da.

“Asma'u³”.

Hannunsa Dr Jameel ya janye kana ya ture gefe tare da cewa.

“Dakata Zakariyya nasan kai Likita ne amma wannan ba hurumin ka bane Saboda wannan hiruminane”.

Alalace Zakariyya ya banka masa harara tare da faɗin.

“Mayen banza mayen wofi, wato daga ganin Yarinya itama ka ɗaura ƙolafacinka da kwadayin ka akanta”.

Araunane ya ɗago kansa ya kallesu baki ɗaya cikin yanayin gaskiya da gaskiya yace.

“Wallahi ban kalleta da idanun da nake kallon sauran ƴan matan da nake mu'amala dasu ba, na kalleta
ne da wasu irin idanu masu matuƙar daraja domin ita mai darace da mutunci”.

Tsaki Moddibo yayi cikin hasala da abinda Dr Jameel keyi ya karɓi goran ruwan da Ibraahim ke miƙa
masa ya watsa mata afuska amma bata farfaɗo ba.

Langwaɓar da kai Dr Jameel yayi tare da faɗin.

“Dan Allah kar ka jiƙamu Ni nasan yanda zanyi in farfaɗo da abuna”.

Moddibo kuwa cikin mamaki ya zubawa Dr Jameel idanu yana kallon ikon Allah da karfin hali.

Cikin lumshe idanu Dr Jameel da har zuwa lokacin yake rungume da Asma'u ya sunkuyo da kanta.

Da wani irin azabebben sauri Moddibo ya riƙe ka sa fuskarsa babu walwala yace.

“Wallahi kada ka kuskura, Idan ka yarda ka kuskura Ni nasan abinda zanyi maka hauka ne akan ka? Ko
kuma kayi tunanin itama irin ƴan matan da kake rayuwa dasu ne da zakayi ƙoƙarin kai bakinka kan
nata?”
Hannunsa biyu ya haɗa kana yace.

“Dan Allah kayi haƙuri Moddibo na rantse da Ubangijin daya busa min numfashi bana kallon wannan
Baiwar Allah Asma'u amatsayin matar da zanyi lalata da ita”.

Sai kuma ya furzar da iska mai zafi daga bakinsa kana ya cigaba da cewa.

“Idanuna suna kallonta ne amatsayin matar Aurena, kuma uwar ƴaƴana wallahi bawai kissing ɗin ta
zanyi ba ya kuke maidani kamar Bunsurune zanyi ƙoƙarin dawo mata da numfashinta nefa”.

Still babu walwala atare da Moddibo ya gyaɗa kai kana yace.

“Ok”.

Dr Jameel kuwa cikin lumshe idanu ya sunkuyar da kansa kanta kana ya ɗaura bakinsa kan hancinta yana
hura mata numfashi.

Asma'u kuwa ahankali taja wani dogon numfashi tare da faɗin.

“Ummi wallahi Yah Jameel ɗin mu bai rasuba ga Yah Jameel ɗin mu na ganshi da rabshi”.

Sai kuma ta buɗe Idanunta ganinta kwance acinyar Dr Jameel cikin sauri ta yunƙura ta zauna tare da
faɗa wa kansa ta rungumesa yayin da take kuka mai tsuma zuciya kana tace.

“Yanzu dama Yah Jameel baka mutu ba, aka kawo mana gawar wani akace ka mutu?”.

Kasa ƙara sa Maganar tayi saboda yanda kuka yaci ƙarfinta kana kallo zaka san daga ainihin zuciyarta
maganar ke fitowa.

Lokaci ɗaya tausayin ta ya mamaye baki ɗaya ilahirin zuciyar Dr Jameel hannu ya ɗago da niyyar
rungumeta.

Da sauri Moddibo ya buge hannunsa.

Shi kuwa Dr Jameel zafin bugun da Moddibo ya masane yasa shi saurin mayar da hannunsa yana yarfawa
sai kuma ya kalli fuskar Asma'u dake cigaba da kuka yace.

“Asma'u Wayyo Allana Yayanki zai kashe Ni kafin komai ya kankama”.

Moddibo kuwa ahankali ya kira sunanta cikin girma da kamalada da zame mata matsayin babban wanta
kana jagoro kuma uba yace.

“Asma'u”.

Ahankali ta juya ta kalli Moddibo sai kuma ta maida kallonta kan Dr Jameel ta sake rungumesa.
Ganin haka yasa Moddibo saurin fin cikota daga jikin Dr Jameel ya tsaidata sai kuma yace.

“Zo ki zauna anan”.

Ya faɗa tare da zaunar da ita akan Kujeran cikin yanayin nutsuwarsa da tuno yadda J ɗinsa ke killacesu
da basu kariya akan kamilallun mazama bare irin Dr Jameel a hankali yace.

“Asma'u ki buɗe ido ki kalleni da kyau”.

Idanunta ta buɗe da tuni hawaye suka kwaranya ta kalli Moddibo.

Cikin fesar da numfashi ya gyara zamansa tare da cewa.

“Wanene Ni awajenki?”.

Cikin raunin murya tace.

“Yah Moddibo Yah Jameel”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Menene matsayina awajenki?”.

Still idanunta na zubar da hawaye tace.

“Tamkar uba kuma tamkar Yaya Jameel”.

Zazzafan Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da faɗin.

“Toh kiyi haƙuri da abinda zan faɗa miki, Dr Jameel ba J ɗina bane mai kama dashi ne kawai, nima
nashiga irin yanayin da kika shiga lokacin dana fara ganinsa”.

Kai Asma'u ke girgiza wa tare da cewa.

“Wallahi Yah Moddibo ban yarda ba Yah Jameel ne”.

Cikin rauni ya kira sunanta da faɗin.

“Asma'u”.

Ahankali ta ɗaga ido ta kallesa cikin sanyi Murya yace.

“Na taɓa yi miki ƙarya ne?”.

Cikin wata raunatacciyar murya ta girgiza masa kai tare da cewa.

“Yah Moddibo baka taɓa yimin ƙarya ba, amma wallahi bazan yarda da abinda kake faɗa ba”.

Ta ida maganar tare da miƙewa ta nufi Corridor data shigo tana gudu tana cewa.
“Ummi Ummi”.

Ahankali Moddibo ya koma ya zauna tare da ɗaura hannunsa duka biyu ya dafe kansa.

Ya tabbar kafin Asma'u ta yarda cewa wannan ba ɗan uwanta bane za'a ɗauki lokaci.

Sai kuma ya ɗaga kansa tare da kallon Dr Jameel dake ƙoƙarin binta yana kiran Asma'u asanyaye yace.

“Ka dawo ka zauna saboda bazata saurareka ba.

Wallahi Ni kaina zuciyata bata gama yarda min cewa ba J ɗina bane kai.

Kawai jikina da zuciyata tana gamsuwa da cewa Kai ba J ɗina bane”.

Sai kuma ya lumshe idanunsa da yake jin ruwan hawaye na tsats-tsafowa kana ya cigaba da cewa.

“Saboda yanayin lalacacciyar ɗabi'ar da kake yi na tabbatar kuma babu abinda zaisa Ummi, Asma'u,da
Bashir su yarda cewa ba kai bane J sai In har sun fuskanci mummunan ɗabi'unka da halayyar ka da
yanayin ka na neman mata shine kaɗai zaisa su yadda”.

Sai kuma ya sanya bayan hannunsa tare da goge hawayen da suka saƙƙo asaman kuncinsa kana ya
cigaba da faɗin.

“Saboda J ɗina Amintaccene mai Aminci mai kamala ne mai mutunci ne, kuma tsarkakekkene bai
kasance yanayin makamancin ɗabi'unka ba”.

Tunda Moddibo ya fara magana jikin Dr Jameel yayi bala'in sanyi, ganin maganar da Moddibo keyi daga
ainihin zuciyarsa ke fitowa kana yana jin magan-ganunsa nada muhimmanci da kuma ƙarfi kana yana
ganin yana da yaƙini da gamsuwa.

Cikin mutuwar jiki ya koma ya zauna karo na farko arayuwarsa daya fara jin tsananin ƙyamar kansa da
kansa akan ɗabi'unsa na neman mata.

Lokaci ɗaya ya riski kansa da wani mummunan tsinkewar zuciya saboda har ƙasan ransa Allah ya
jarabcesa da son wannan yarinya daya gani wacce ake kira da Asma'u.

Wacce ita kuma take masa kallon ɗan uwanta wanda zuwa yanzu ya fahimci komai nasa yana mata kama
da ɗan Uwanta ne daya rasu.

Hakanan ne yasa zuciyarsa ya cika da tsoro da taraddadi anya Moddibo zai lamunce abashi Auren
Asma'u ayanda yake nuna tsananin ƙyamarsa akan halayyarsa na zina...
Kansa ya riƙe da hannunsa duka biyu kana ya furta.

_“Astagfirullah wa'atubu ilaik”_.

Moddibo kuwa cikin sanyi jiki ya juya ya kalli Zakariyya dake cewa.

“Moddibo muyi alwala muyi sallah ana kiran Sallah”.

Kai suka gyaɗa kana suka miƙe sukayi al'wala kana nufi masallaci alayi ɗaya sukayi jam'i koda suka idar
da Maghriba basu dawo gida ba saida akayi Isha'i kana suka dawo.

Suna dawowa suka samu an shirya musu komai na a binci dining....

Acan falon da aka sauƙe su Khausar kuwa cikin gigita Asma'u ta shiga falon tare da faɗawa kan Ummi
dake zaune cikin ficewar hayyaci take faɗin.

“Wallahi Ummi naga Yah Jameel”.

Da sauri Ummi ta zaro ido kana tace.

“Me kike faɗa Asma'u”.

Cikin zubda hawaye da rauni Asma'u ta gyaɗa kai tare da cewa.

“Wallahi Ummi naga Yah Jameel tare da Yah Moddibo”.

Yanayin da take magana cikin alamun kiɗima da gigita yasa Ummi saurin janyota ta riƙe ta.

Innayi ma matsowa kanta tayi kana ta riƙe hannunta tare da cewa.

“Asma'u wanda ya rasu yana dawowa ne?”.

Kallon Innayi tayi da jiƙaƙkun idanunta kana tace.

“Innayi wallahi Yah Jameelu na gani naga Yah Jameel Wallahi na ganshi”.

Cikin fesar da numfashi Ummi tace.

“Asma'u ki nutsu mana, In dai Jameelu ne da gaske ai zai iso mu”.

Ummi kam kallonta kawai take aranta tasani cewa tabbas Jameelunta ya rasu ya barta tasan cewa babu
wani Jameelu sai dai in gezo yake wa Asma'u ta.

Aunty Ruƙayya dake zaune can gefe ta miƙe ta matso gefen Asma'u ta zauna tare da riƙe hannunta tace.
“Asma'u ya za'a yi wanda ya mutu ya dawo? Shi wanda ya mutu baya dawowa ai shi mutuwa ɗayace
idan mutum yayi ta yayi ta har abada”.

Cikin matsanancin kuka Asma'u ke girgiza kai kana tace.

“Wallahi Allah Aunty Ruƙayya na gansa”.

Ƙiran Sallar Maghriba da akayi ne yasa Ummi kallon Asma'u cikin tsawa ta haɗe fuska kana tace.

“Maza tashi Kije kiyi a''wala kizo kiyi Sallah”.

Da sauri tace.

“Wallahi! Wallahi!! Ummi Yah Jameel na gani, ki yarda dani”.

Cikin haɗe fuska Ummi tace.

“Zakije kiyi salla ko zaki tsaya hauka”.

Jiki asanyaye ta miƙe taje tayi al'wala kana tazo ta shimfiɗa Sallah kana tayi Sallah koda suka idar da
sallar Maghriba Azkhar sukayi har aka kira Isha'i kana sukayi ...

Bayan sun idar da Isha'i Asma'u ta koma gaban Ummi ta zauna cikin muryan kuka tace.

“Wallahi Ummi Yah Jameel na gani Ummi ki yarda dani ku nemi Yah Moddibo wallahi Yah Jameel na gani
fa Ummi”.

Ganin yanda ta rikice yasa Ummi sauke zazzafan ajiyar zuciya tare da kallon Innayi da tazo gabansu kana
tace.

“Innayi ane momin Moddibo al'amarin Asma'u yayi yawa fa, gaba ɗaya agigice take kinga Sallar nan har
aka idar da Maghriba kuka take har aka zauna Azkhar still kuka take har muka jira Isha'i kuka Asma'u
keyi”.

Kai Innayi ta jinjina tare da faɗin.

“Toh shikenan”.

Ta faɗa tare da miƙewa ta nufi side ɗin Didi.

Tana shiga Side ɗin Didi suka sake gaisawa kana ta yiwa Didi bayanin abinda ke faruwa.

Cikin sauƙe numfashi Didi tace.

“Tabbas ai shima kanshi Aleeyu sanadin shigowar sa Masarautar nan haɗuwar sa da Dr Jameel ne”.

Cikin yanayin mamaki Innayi ta tallafe kuncinta tare da faɗin.


“Toh waye Dr Jameel ɗin?”.

Ahankali Didi ta shiga bata Labarin da Dr Jameel ya bata.

Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe kana tace.

“Toh dan Allah ayi min iso zuwa Side ɗin dasu Moddibo suke dan bansan inda suke ba”.

Ƴar dariya Didi tayi tare da cewa.

“Ai suna kusa daku suna ƙasa, kuna sama bari nayiwa Jakadiya magana ta rakaki”.

Nan Didi ta umarci Jakadiya kana ta yiwa Innayi jagora zuwa sashen dasu Moddibo suke...

Innayi na shiga ta samu Zakariyya Dr Jameel Ibraahim suna Kan dining yayin da ta haɗu da Moddibo
gab bakin ƙofa da alamun zai tafi wajensu ne, dan ya duba halin da Asma'u ta tafi.

Yana ganin Innayi sai yayi saurin komawa baya.

Innayi kuwa tana ganinsa tayi murmushi.

Shi kam hannunta ya riƙe suka ƙarasa cikin falon kana suka zauna kan kujera suna zama kan kujera yace.

“Innayi nayi kewarki”

Cikin jin daɗin ganinsa ta gyara zama tare da faɗin.

“Nima nayi kewarka, amman dama ai nasan cikin danginka za taho nasan ka dawo cikin ƴan uwanka
muhallinka”.

Kai ya jinjina kana yace.

“Innayi wani irin tarin abubuwa kikayi ta ɓoye min a iya tsawon rayuwata?”.

Numfashi ta fesar da cewa.

“Sai ahankali yanzu dai farko waye Asma'u ta gani ta koma tana ihu tana ce mana Jameel ne”.

Kai ya jinjina tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Gashi can Innayi juya ki kallesa baiyi miki kama da Jameel ba?”.

Da ƙarfi Innayi ta tashi kana ta buga hannunta akan ƙirjinta cikin tsananin ruɗu tace.

“Kamar yaya kama?,Aliyu kace min Jameel dai Ashe gaskiyan Asma'u Jameelu ta gani”.

Ta ida Maganar tare da juyawa ta nufi dining area cikin sassarfa.


Tana zuwa ta kamo hannun Dr Jameel tare da riƙewa tace.

“Jameelu”

Kallonta yayi tare da yin murmushi shima kansa yanda suke zuzuta tsananin kamansa da Jameelu ya fara
bashi tsoro da mamaki.

Innayi kuwa batare data jira komai ba ta kama hannunsa tana ja.

Shi kuwa Dr Jameel tsintar kansa da bin bayanta yayi.

Shima Moddibo cikin sauri yabi bayansu yana cewa.

“Innayi ba Jameelu bane wallahi tsananin kama ne”.

Ina tuni Innayi ta fice batare data sauraresa ba ta fara haurawa step ɗin tana cewa.

“Ummin Jameel”.

Zakariyya da Ibraahim ma na biye dasu suna shiga Falon da Ummu ke zaune Innayi na cigaba da cewa.

“Ummin Jameel Wallahi gaskiyar Asma'u ne Jameelun kine”.

Akuma dai-dai lokacin Ummi ta juya da sauri idanunta suka sauƙa akan Fuskar dake tsananin kama da
Jameelunta komai na Jameelunta a fili.

cikin wata raunatacciyar murya tace.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”.

Sai kuma ta koma ta faɗa kan kujera idanunta na zubda hawaye shar-shar-shar.

Itama Asma'u cikin sauri ta riƙe hannun Ummi tare da faɗin.

“Ummi ba kin gani ba na faɗa miki Yah Jameel ne”.

Sai kuma ta saki hannun Ummi ta koma ta riƙe hannun Dr Jameel na dama Innayi kuma na riƙe da
hannunsa na hagu suka zo gaban Ummi suka durƙusa sai shima ya tsinci kansa da durƙusawa agabanta,
haka nan yaji kima da martaban matar sun cika masa idanu.

Da sauri Moddibo ya ƙarasa shiga wa falon tare da zama gefen Ummi wacce ke kan 3sitter kana cikin
raunin murya yace.

“Ummi”.

Cikin zubda hawaye ta juya ta kallesa cikin rauni ya cigaba da cewa.


“Ummi ki kalli duk komai na Jameel ne muryansa, Tafiyarsa, Gangar jikinsa, Har fa asakin da Jameel keyi
shi yake yi amma wallahi Ummi ba Jameelunki bane kamannin ne yayi yawa Wallahi!³ Ummi ba
Jameelunki bane”.

Juyawa Ummi tayi ta kallesa cikin jinjina masa take cigaba da gyaɗa kanta jikinta yana bata ba Jameelu
bane domin jikinta ba amsheshi a matsayin Jameel ba wannan bawai ɗan ta bane agabanta amma
zuciyarta taƙi yarda.

Kai ta girgiza still hawaye na bin fuskarta ta juya ta kalli Dr Jameel da yake durƙushe agabanta.

Ganin yanda take zubar da hawaye yasa shima yake zubar da hawaye.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Toh meyesa ka kuma?”.

Ahankali ya ɗago kai ya kalleta cikin tarin tausayinta da kuma rauni yace.

“Saboda kukan da naga kunayi shiyasani kuka, nasan ko waye Jameel awajenku mutum ne mai daraja,
mai kima wanda shine jigo acikin rayuwarku”.

Kallonsa kawai Ummi keyi hawaye na cigaba da zuba daga idanunta sabida yadda muryasa ma sai ta
Jameel ɗinta.

Shi kuwa Dr Jameel kuwa cikin rauni da zubda hawaye ya cigaba da faɗin.

“Na fahimci kuna jin ƙuna na rashinsa amma Ummi nayi miki al'ƙawari in dai kin amince kun bani dama
in sha Allah zan maye muku gurbinsa”....

*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n
nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai
sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan
mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in
kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a
banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account
no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na
faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki
kenan*

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito
miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar
infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita
tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a
saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda
yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin
san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo
kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki,
domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan
ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah
zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce
dai GARKUWAR MA'AURATA.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH
49

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

49
Ummi kuwa cikin sanyi jiki da raunin zuciya take kallonsa sam, jikinta bai faɗa mata cewa wannan ɗan ta
bane, amma zuciyarta yaƙi amincewa da hakan.

Juyawa tayi ta kalli Asma'u da hawaye ke cigaba da zuba daga idanunta, kai ta girgiza kana ta maida
idanunta kan Moddibo dake cewa.

“Wallahi Ummi wannan ba Jameel ɗinki bane. Nima kaina na gamsu da komai nashi na *J* ne amma
ɗabi'unsa ba irin na *J* bane sam sun bambanta tako wacce siga ta hali da ɗabi'a”.

A hankali Dr Jameel dake durƙushe gaban Ummi ya kalli Modibbo tare da rausayar da ƙwayar idanunta
acikin nasa alamar kada ka zubar min da mutuncina agaban idonta.

Numfashi Moddibo ya fesar fahimtar kallon Dr Jameel ɗin yamasa shi yasa yayi shiru...

Innayi, Asiya, Aunty Ruƙayya, Aunty Hajara da duk suke tsaye daga gefe suna kallon ikon Allah da Al'ajabi
na tsanananin kamannin Dr Jameel da marigayi M Jameel.

Zama Ummi ta gyara tare da jan dogon numfashi kana ta sauƙe cikin sanyi tace.

“Shikenan na gamsu Moddibo, na yarda da kai saboda sanin kai nane, baka taɓa yimin ƙarya ba, kuma
koda wasa kake min baka min ƙarya aciki, dan haka na yarda na gamsu wannan ba Jameeluna bane”.

Ta ƙare mgnar tare da lumshe idanunta hawaye masu zafin gaske suka zubo kana ta cigaba da faɗin.

“Amma wannan kamanni da yawa yake.

Kuma Alhamdulillah na godewa Allah daya da wannan Rahma da yayi min na nuna min mai kamannin
Fuskar Jameeluna har muryarsa irin na Jameeluna da komai nashi fa”.

Dr Jameel kuwa cikin yanayin buɗe war ido, da kuma gskyar zuciyarsa ya kalli Ummi duk da kuwa yana
cikin rauni da tausayinsu, a hankali ya fesar da numfashi tare da maida idanunsa kan Asma'u kana Yace.

“Ummi”.

Da sauri Ummi ta ware idanunta dake cike taf da hawaye jin ya kirata da Ummi.

Sake langwaɓar da kansa yayi idanunsa na kan Ummi ya cigaba da faɗin.

“Ummi da zan samu a bani Asma'u in Aura wlh ina so.

Kinga shikenan sai na zame miki ɗanki Jameel In maye maki gurbin shi”.
Ware idanu Ummi tayi tarexa kallonsa cikin mmkin mgnar shi da tazo mata a bazata, sai kuma taji
murmushi ya suɓuce mata batare da tace komai ba ta miƙe ta shiga bedroom..

Asmau kuwa, wani irin fitinennen sanyi kalamashi suka sakar mata, so take ta yunƙu ta mike a guje ta
bar wurin amman ta gaza hanan, sabida yadda gaba ɗaya guiwowinta suka sake.

Aunty Hajara, Aunty Ruƙayya, Asiya atare suka saki murmushi kana suka miƙe cike da gamsuwan cewa
ba Jameel bane kawai dai kamanni ne, domin da Jameel ne bazai ce zai Auri Asma'u ba wannan kalmar
kaɗai ta gamsar dasu cewa ba Jameel bane, domin idan M. Jameel ne babu ta yanda za'a yi yace zai Auri
ƴar uwarsa ƙanwarsa da suka kasance uwa ɗaya kana suka sha nono ɗaya, da wannan

gamsassun hujjoji suka bi bayan Ummi zuwa bedroom.

Innayi kam murmushi tayi cike da gamsuwa cewa lalle wannan ba M Jameel bane kamanni ne kawai,
fuskarta ɗauke da amintaccen murmushi ta kalli Dr Jameel tare da faɗin.

“Toh an baka”.

Saurin kallonta Moddibo yayi babu walwala atare dashi yace.

“Kece me bada Asma'u koni ne mai bada ita?”.

Still Innayi na murmushi tace.

“Kaine Mai bada ita amma kaima ai ina da iko akan ka”.

Kai ya jinjina tare da faɗin.

“Eh kina da iko akaina Innayi, amma ai shi Aure ɗan bincike ne sai na bincikesa nasan ingancin sa
tukunna kafin na bashi Asma'u”.

Asma'u kuwa tun lokacin da yace yana sonta data daskare zaune, sai yanzu taji tayi azamar miƙewa
sabida jin kuzarinta ya dawo,

Da gudu ta miƙe tabar wajen yayin da Khausar ta miƙe tabi bayanta.

Cikin lumshe idanu Moddibo yabi Khausar da kallo har ta ɓacewa kallonsa idonsa na kanta wani
sassayyan numfashi ya fesar tare da lumshe ƙwayar idanunsa.

Zakariyya kuwa tunda suka shigo idonshi na kan Aseeya gaba ɗaya ya gaza ɗauke idanshi a kanta.

Ibraahim kuwa shiru yayi yana kallonsu kawai.


Ganin duk sun watse yasa Innayi maida kallonta kan Moddibo kana tace.

“Bismillah kuje kuci abinci naga kamar abinci kuke ci na tada daku”.

Kai suka gyaɗa tare dayi mata sallama kana suka tafi.

Suna shiga Falon Dr Jameel ya kamo hannun Moddibo tare da langwaɓar da kai kana cikin sanyin murya
da neman alfarma yace.

“Na roƙeka da girman Allah Moddibo kada ka faɗi wani abu da zai zubar min da kima da daraja a idon
Ummi”.

Kallonsa kawai Moddibo, Ibraahim, Zakariyya sukeyi Shi kuwa cikin sanyi da neman alfarma ya cigaba da
cewa.

“Na lura tana kallona da kima da daraja kuma Wallahi har cikin raina ina ƙaunar Asma'u kuma Aurenta
zanyi”.

Cikin sauri Moddibo ya tari numfashinsa ta hanyar cewa.

“Gaskiya ayanayin kan nan dana lura da kai. Wallahi bazan baka Asma'u ba, Asma'u nine nan mai bada
ita,Tana da mahaifi, Lallai Mahaifinta shine zai bada ita.

Amma bisa yaƙinina zai bada ita. Ni kuma bani da yaƙini akan ka”.

Sai kuma ya ɗan furzar da iska mai zafi yana tuno yanayin munanan halayyar Dr Jameel kai ya girgiza
kana yace.

“Baka da tsarkakan da zan baka tsarka-kakkiyar yarinya saboda Asma'u tsarka-kakkiyar ce.

Kallonsa kawai Dr Jameel keyi cikin rauni da nadama ɗabi'unsa da yakega zasu kasance mihsi barazana
daga mallakar ƴarinyar da yakeji in bai setaba zai zauce.

Moddibo kuwa cikin yaƙini da gaskiya ya cigaba da faɗin.

“Saboda Faɗin Allah ma ɗaukakin sarki ne, cewa. Mazinaci baya Aure sai Mazinaciya ƴar uwarsa Asma'u
kuwa tsarka-kakkiya ce ba Mazinaciya bace kai kuma kafi kowa sanin kanka”.

Ahankali Zakariyya da tausayin Dr Jameel ya gama cikawa zuciya ya kamo hannun Moddibo suka zauna
kana cikin nutsuwa yace.
“Kayi haƙuri Moddibo ai abu da yawa yana zama sanadin shiryuwar mutum kada kayi mamaki Auren
Asma'u ya kasance hanyar shiryuwan Dr Jameel”.

Kai Ibraahim dake gefe ya jinjina tare da cewa.

“Hakane Yah Aleey tunda har yace yana sonta da dai ashige masa gaba ba ba mamaki wannan abin da
yake rashin mata ne”.

Dr Jameel kuwa cikin gaskiya da gaskiya ya kalli Moddibo kana yace.

“Wallahi! Wallahi!! Wallahi!!! In dai za'a bani Asma'u Ni dai nayi al'ƙawari zan rabu da duk wata ƴa
mace”.

Ganin gaskiya acikin ƙwayar idanunsa yasa Moddibo fesar da numfashi tare da cewa.

“Shikenan ka fara rabuwa dasu tukunna idan na gamsu ka rabu dasu.

Ni kuma zan baka ita In dai har na gamsu”.

Cike da farin ciki Dr Jameel ya gyaɗa kai kana yace.

“Ni kuma nayi maka al'ƙawari daga yau daga yanzu na rabu dasu”.

Ya ida maganar tare da zaro wayarsa kana ya shiga contact tare da blooking ɗin Number duk ƴan matan
sa kana ya nunawa Moddibo.

Murmushi Moddibo yayi kana yace.

“Toh Allah yasa kayi iya deleting ɗin su acikin Mind ɗin ka da zuciyarka kamar yanda kayi awayarka”.

Asanyaye Dr Jameel ya furta.

“In sha Allahu babu kowa a raina”.

Juyowa Modibbo yayi ya kalli Ibarahim dake miƙa mishi woyoyinsa,

Murmushi Ibraahim yayi tare cewa.

“Tun da safe Abualeey ya bani su yace amman in bari sai dare in baki”.

Murmushi Modibbo yayi tare da cewa.

“Ummm yayi kyau”.

Cikin wasa Ibraahim yace.


“Nasa maka caji ne dan naga sun mutu sabida kiraye-karen da akayi ta maka”.

Miƙewa yayi tare da cewa.

“Yoh ba dole su mutuba moko guda”.

“Eh amman ai yanzu duk a cike suke”.

Cewar Ibraahim.

Kai Modibbo ya gyaɗa mishi yana mai kunna woyoyin nasa.

Acan ɓangaren su Khausar kuwa tunda suka shiga bedroom take sakin murmushi idanunta akan Asma'u
da duk tayi zuru-zuru da ita kana tace.

“Asma'u Wallahi wannan ba Yan Jameel bane”.

Kallon mamaki Asma'u tayi mata Still hawaye na bin fuskarta tace.

“Kamar ya zakice ba Yah Jameel bane”.

Hannunta Khausar ta riƙe tare da cewa.

“Asma'u jikina ya faɗa min ba Yah Jameel bane.

Ki sani da Yah Jameel ne ko cutan hauka yayi ba zai kalleki yace yana sonki amatsayin matar Aure ba”.

Sai kuma ta sake damƙe hannun Asma'u acikin nata cikin son tabbar mata da gaskiya ta cigaba da cewa.

“Ki tuna fa Nono ɗaya kuka sha mahaifiya ɗaya ce ta haife ku fa wallahi Asma'u ba Yah Jameel bane,
kawai ni inajin farin ciki araina ne. Alhamdulillah bazan rayu Ni kaɗai aƙasar nan ba zan rayu tare dake,
zai ɗakko min ke ya dawo min dake ƙasar nan mu rayu tare”.

Zazzafan Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe idanunta akan Khausar tace.

“Wallahi nifa Khausar har yanzu ban gamsu cewa ba Yah Jameel bane”

Kai Khausar ta girgiza tare da cewa.

“Wallahi Asma'u ba Yah Jameel bane ya za'a yi Yah Jameel yace yana sonki zai Aure ki, Asma'u kiyi tunani
mana hakan bazai taɓa faruwa bafa”.

Haka dai sukaci gaba da tattaunawa.


A daren wannan ranan haka suka cika da alhini da al'ajabi...

Acan Side ɗin Didi kuwa zaune suke da ƙannenta da kuma Yayyanta da suka zo.

Baki ɗaya hirar tasu akan Khausar ce suna yabon kyawu da kuma haibar da Khausar tayi kowa na faɗin
albarkanci bakinsa.

A wannan ranan haka duka ahalin suka kwana cikin yalwataccen farin ciki.

Washe gari aka shirya taro na alfarma wanda baki ɗaya manyan Fada da kuma manyan Masarautar
Morocco ne taro ne wanda yafi na jiya sai dai wannan taro ne na maza zalla saboda an gabatar da
Moddibo amatsayin Sarki mai jiran gado kana ana gabatar dashi a baki ɗaya idon Fada sosai Moddibo
yayi jawabi daya ratsa zukatan mutane kasancewar shi aka bawa Microphone ya rufe taron da addu'a.

Al'amarin da ya gigita jama'ar masarautar jin yanda ya dinga zazzago addu'oi yana rerawa cikin zazzaƙan
muryansa.

Wani irin farin cikine ya mamaye zuciyar Abualeey ya tabbatar da cewa ɗan sa ya samu kyakkyawan
tarbiyya da jigon da zai iya mulkar masarautar Mouley.

Cikin jin daɗi yake kallonsa,

Shi kuwa Modibbo addu'oin daya ta jerawa na yayi dai-dai da lokacin da aka kira Sallar Azahar.

Limamin masallacin Fadan dake zaune gefe wanda tsohone tukuf ya tsufa sosai bisa alamu kuma sa
yanayin jinya na tsufa.

Cikin jin dadin ya sauke A tare da karɓan Microphone ɗin kana yayi jawabin cewa,

Shi ya fahimci wannan Yariman yana da cikekken ilimin addini dan haka daga yau ya sauƙa daga kan
karagata na limanci shine zai cigaba da limanci masallacin masarautar su kasancewar tsufar da ya
cimasan da kuma sanyin da muryasa keyi wacce wasu lokutan bata isarwa mabiyan jam'inshi.

koda Modibbo yaji haka yayi ƙoƙarin maida tayin da limamin yayi mishi amman ina yaƙi sabida da
gskyarsa sufa tacin mishi.

Sai kallon Modibbo yake cikin so da

Amintaccen murmushi mai cike da yarda da yaƙini kamilin dattijon yake bin Modibbo da Addu'o'i kana
ya ɗaura da cewa.
Hakan za'a yi kuwa domin Modibbo ya cancanta sai dai ko in baka kusa ko kayi tafiya ko wani abu dai to
sai in jamu.

Daga haka taron ya tashi da yaƙin cewa an bar mishi Limanci...

Aranar Modibbo ne yaja limancin sallar Azahar, wanda baki ɗaya sautin zazzaƙan muryarsa ya cika
masarautar.

Wanda baki ɗaya al'umma cikin Masarauta ke yaba zaƙin muryansa.

Bayan an idar da sallar Azahar Direct sashen Didi Ibraahim ya nufa cike da farin ciki ya zauna gefen Didi
tare da riƙe hannunta kana yace.

“Didi kinsan waya ja mana jam'i?”.

Kai ta girgiza tare da faɗin.

“A'a sai ka faɗa?”.

Cike da matsanancin farin ciki yace.

“Wallahi Yah Aleey ne Kai Didi wlh Innayi ta gama mana dukkan gata na duniya”.

Fuska ɗauke da yalwataccen farin ciki Didi tace.

“Kai Alhamdulillah”.

A ɓanƙaren su Modibbo kuwa, Sheiyk Jabeer ne tare Modibbo sai Jabeer bin Jabeer cikin kulawa
Modibbo yace.

“Sheiykh yau yau kuma zaku koma?”.

Gyaran murya Sheikh Jabeer yayi tare da cewa.

“In Allah kuwa yanzuma zamu tafi airport dama kafin mu tafi masallaci nayi sallama da kowa na Fada
harma da Didinku munyi sallama.

Tafiyar ce ta gaggawa ta sameni zan koma ne saboda gobe da yamma muna da zama da ƙungiyar *MI
YETTI ALLAH* Akam matsalolin Garkuwa da mutane ƙasarmu ke fuskanta.

Toh yadda ake maida akalar zargin kan cewa Fulani ne keda alhaƙin hakanne yasa ƙungiyar *TABITAL
POOLAKU* shiga mgnar da keɓance ƴaƴanta Fulani da wonkesu daga zargin da ake musu domin suma
fulanin basu tsiraba, anayi musu wannan zalumcin su a ƙara da kashesu ma”.
Cikin sauƙe nannauyan numfashi Modibbo yace.

“Gsky wannan ƙudurine mai kyau, domin abune daya addabi ƙasarmu, kaga wala Allah cikin haka a gano
masu aikata hakan”.

Cikin kulawa Sheiykh yace.

“In sha Allah kuwa, domin fulanin zamu wakilta mu naɗasu aikin bamu rahoton duk abinda ke gudana
cikin dajukan za mu rabasu ko wanne state na Nigeria”.

Sai kuma suka kalli Jabeer bin Jabeer dake cewa.

“Musamman Zamfara Sokoto Katsina abun yafi tsamari a can”.

Moddibo ne ya ɗan fesar da numfashin mai zafi kana yace.

“Ni kuwa ina so a ruɓanya masu binciken Taraba yankin Gembulan domin anayi musu illa sosai, a
sanadin su na rasa J na”.

Sheykh ne ya ɗan kali agogo dake hannunsa tare da cewa.

“Eh nima da batun Jameel da kayi mana bayani na kuduri aniyar in sha Allah, sai na gano waɗanda suka
yi masa wannan kisan gillan, in ban mantaba kace min akwai wacce taga mota bibiyarsu kuma har ta
ɗauki number'n ko?”. Da sauri Modibbo yace.

“Eh Khausar ce”.

Cikin samun cikekken yaƙini kan binciken Sheykh yace.

“Toh ba matsala idan kun nitsu, ka nemi min cikekken bayanin a wurinta, sai ka tura min komai, in Allah
ya yarda jininshi bazai tafi a banzaba”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“In sha Allah kuwa”.

Daga nan sukayi sallama, Abualeey da kanshi yayiwa surkin nashi da ƙanin matarsa rakiya zuwa Airport,
bai dawoba saida jirginsu ya tashi.

Acan ɓangaren su Khausar kuwa zaune take kan sallayar tun bayan data idar da sallar Azahar bata motsa
ba.

Innayi dake gefe ta saki murmushi tare da faɗin.

“Kai Alhamdulillah naji daɗin nagartar Moddibo ina farin ciki da hakan”.

Kai Ummi dake gefenta ta jinjina kana tace.


“Ai dai kam Alhamdulillah”.

Daga haka suka cigaba da hira wanda mafi yawa akan Moddibo ne...

Acan ɓangaren Hajiya Bunayya kuwa zaune take a bedroom ita kaɗai yayin da Asiya ke toilet tana
wanka.

Hajiya Bunayya kuwa wayane maƙale a kunnenta tana magana da Amina dogon tsaki taja tare da faɗin.

“Ke dai Amina bari wallahi dana san haka daular nan take da mu mukayi sihiri kika Auri Moddibo”.

Amina dake zaune acikin wani ƙaton falo na al'farma a Abuja tayi murmushi tare da faɗin.

“Umma kada ki damu nan ma wallahi muna cikin daula kinga gidan da aka kama nin kuwa, dan dai baki
zo kinga gidan da aka kawo ni bane gidane mai masifar kyau na nunawa sa'afa”.

Sai kuma ta juya idanunta tare da kallon mashshurin falon nata kana ta cigaba da cewa.

“Kinga manyan falona guda biyu da 3bedroom atsakiyar birnin Abuja fa muke inda muke ma ai
alhamdulillah kuma kin manta muma zamu tafi Indi'a ne kwanan nan da Uncle Naseer”.

Dogon tsaki Hajiya Bunayya taja kana tace.

“Ke bakiga daular dake cikin nan bane shiyasa kike faɗin hakan”.

Murmushi Amina tayi tare da faɗin.

“Umma kema fa bakisan daular da nake ciki bane ki kwantar da hankalin ki in kin dawo kinzo zaki sha
mmaki”.

Cikin gaskata wa Amina ta cigaba da kwantar wa da mahaifiyarta hankali kana ta ɗaura da faɗin.

“Umma kada fa ki manta muma Indi'a zamu tare kuma Indi'a ma ai tafi Morocco sanuwa da suna”.

Kai Hajiya Bunayya ta girgiza kana tace.

“Hmmm Amina kenan ta yaro kyau take bata ƙarko, abine da baki gani ba, duk labarin da zan baki
bazaki gane bane irin cigaba, da nasara, wadatar da Khausar ta riska awannan masarauta ya wuce
zatonki”.

Sai kuma ta ha ɗiye wani yawu mai masifar ɗaci kana ta cigaba da cewa.

“Bazaki taɓa fahimtar abinda nake faɗa ba har sai idonki ya gane miki.

Yoh Naseer da ko Sarkin Tasha Uban sa bai taɓa mulka ba, ina za'a haɗashi da Modibbo, kina sane da
cewa Khausar kuwa mijinta shine Yarima mai jiran gadon mulkin Ƙasar Morocco gaba ɗayanta fa, sannan
kuma shine babban ɗa Namiji awajen Mahaifinsa”.
Amina dake zaune ta dafe ƙirji cike da ƙyashi da hasadar jin matsayi da kuma nasaran da Khausar ta
samu.

Hajiya Bunayya kam cikin ƙunan zuciya da tarin hassada ta cigaba da faɗin.

“Wannan tsinanniyar tsohuwar Innayi ta cucemu data ɓoye mana wannan al'amari nasarar Modibbo da
mun san da wannan nasaba da yake dashi haka ai wallahi ko zan tafi tsirara ne wlh sai kin Auri
Moddibo”.

Zazzafan Ajiyar zuciya Amina ta sauƙe kana tace.

“Umma ke kam kada ki damu”.

Kai Hajiya Bunayya ta girgiza ji take kamar ta ɗaura hannu aka tayi ta zunduma ihu cikin damuwa tace.

“Ya bazan damu ba Amina dole in damu gaba ɗaya hankalina ya tashi baƙin ba, yanda ban samu ba suma
su rasa Wallahi, duk yanda zanyi Amina nayi miki al'ƙawarin sai na raba Auren Khausar da Moddibo ko
ana Hamaza ha mata.

In dai dawo Nigeria ne kawai yafi wuya”.

Cikin sauƙe numfashi Amina tace.

“Gaskiya dai nima yanda kike zuzuta wannan cigaban nata, da dai ta wuceni gwara a kaso Auren nata ta
dawo gida ta zauna”.

Yamutse fuska tayi tare da gyara zamanta kana ta cigaba da cewa.

“Ƴar banza agola kawai tazo tafi ƴaƴan masu gida nasara”.

Ƙwaffa Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Ke dai bari”.

Dai dai lokacin da Asiya ta fito daga wanka kallonta tayi tare da girgiza kai cikin yanayin sanyinta tace.

“Hmmmm Allah ya kyauta”.

Alalace ta kalleta tare da faɗin.

“Toh shegiya mai baƙin hali meye?

Ƴar masu matacciyar zuciya da bakisan abinda yake miki ciwo ba sai wani yaƙe baki kike kina murmushi
adole kinga nasarar wani”.
Tana zama gaban dreesing mirror tace.

“Umma idan har bakayi baƙin ciki da nasarar wani ba kaima Allah zai kawo maka naka narasan”.

Ahantare Hajiya Bunayya ta harareta tare da cewa.

“Dalla can rufe min baki,Ki ɓace min daga ɗaki”.

Kai ta gyaɗa tare da ficewa daga dakin kasancewar tasa kayanta kai tsaye ɗakin su Khausar ta nufa...

Acan ɓangaren Moddibo kuwa bayan sun Sheykh Jabeer sun tafi. suka cigaba da gaisawa da Manyan
baƙi.

Har aka kira La'asar bayan an idar da sallar La'asar baki ɗaya baƙi suka tafi anci ansha wasu irin abinci na
alfarma aka dafa wanda ma'aikatan manyan restaurant aka ɗebo sukayi girkin gargajiya dana zamani
domin afita kunya.

kuma Alhamdulillah kwalliya ta biya kuɗin sabulu.

Moddibo kuwa gaba ɗaya wunin yau ɗin duk abinda yake Khausar ce ke faɗo masa arai da Zaran ya
lumshe Idanunsa zai tuna sanda ya rungumeta yana budewa kuwa lokacin da yake wanke mata hannu
acikin Madarane ke masa gizo duk wani abu da yake dauriya kawai yake.

Yayin da wani ɓangare na zuciyarsa ya tafi ga halin da Asma'u ke ciki kasancewar har suma tayi a daren
jiya kana ko bayan barinsa sashen da sukenma bata cikin nutsuwarta, tun safe yaso zuwa dubata amma
bai samu ba saboda hidindimu da suka yi masa yawa...

Acan Falon su Khausar kuwa suka zaune Jakadiya ta shigo bayan sun gaisa ta kalli Innayi tare da cewa.

“Innayi Didi na buƙatar ku baki ɗaya asashenta amma banda Khausar sannan abarta da mutum ɗaya
kada ta zauna ita kaɗai”.

Kai Innayi ta jinjina tare da cewa.

“Toh ba damuwa sai abarta da Hajja Nana”.

Ta ida maganar tare da miƙewa ta nufi ƙofa yayin da Hajiya Bunayya,Aunty Ruƙayya, Aunty Hawwa,
Aunty Hajara Asiya, Dije suka mara mata baya.

Kai tsaye suka nufi sashen Didi bakinsu ɗauke da sallama suka shiga tangamemen Falon suna shiga
idanunsu ya sauƙa akan Wasu Mashahuran Akwatuna set biyar ko wannen kalansa da ban.
Lalla Khadijah ne ta ɗaga kai tare da kallon Innayi kana tace.

“Ku shigo ku zauna mana”.

Murmushi Innayi tayi kana suka shiga suka zazzauna akan lumtsa-lumtsan kujerun na al'farma.

Ɗaya daga cikinsu ne Yayar Didi wacce ta kasance ƴar farinsu ce Mai suna Afreen wacce kira da Ashshe
matsawa tayi suka gaisa kana cikin sakin fuska tace.

“Toh Alhamdulillah ga lefe nan mun gama haɗawa na.

Amaryanmu so mun kira kune kuzo ku gani in Sha Allah za'a bawa Hadimai su kaishi Side ɗin da zasu
zauna ne”.

Cike da tarin farin ciki Innayi ke kallon Set ɗin akwatunan kana tace.

“Masha Allah Alhamdulillah”.

Ummi kuwa cikin yanayin farin ciki tace.

“Kai masha Allah wannan duka lefene!?”.

Lokaci ɗaya Hajiya Bunayya ta nemi ƴar nutsuwarta ta rasa atake yanayin fuskarta ya rikiɗe afili zuwa
hassada da ƙyashi ta kasa ɓoye baƙin cikinta.

Cikin fusata taja wani dogon tsaki tare da sauƙe numfashi wanda yaja hankali da yawa daga cikin
mutanen falon suka kalleta.

Asiya dake gefenta tayi saurin dafa kafaɗarta ganin yanda ake kallonsu yasa tace.

“Umma lafiya?”.

Kai ta gyaɗa tare da yamutse fuska kana tace.

“Ƙirjina ne yake ciwo sai to kareni yake”.

A yatsine Lalla Hafsat ta kalleta tare da cewa.

“Ok ba matsala bari na kira Dr Jameel yazo ya duba ki da jiki sai ya baki magani”.

Ta ƙare mgnar a yaysine dan har ga Allah matar bata konta mata a raiba....

Littafin SAKAYYAH dai na kuɗi ki biya ki karanta cikin Aminci.


By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

50

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwatanta Zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki
dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection
cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin
kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin
kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana
dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya
musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki
aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa
ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga
account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min
mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi
Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari
da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan
Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR
MA'AURATA.

50

Cikin sauri ta girgiza kai tare da faɗin.

“A'a Nagode inada magani in mun koma zansha”.

Baki Lalla Hafsat ta taɓe kana ta fara buɗe musu Set ɗin akwatin farko na ƙasan idanunsu suka sauƙa
akan wasu EGYPT Abaya masu masifar kyau da tsada baki daya cikin akwatin cike take da Abayas kala
daban-daban kama daga Turkey Abaya, Itally Abaya, Dubai Abaya Wanda aƙalla zasu kai arba'in sai kuma
ɗaya akwatin dake ɗauke da wasu Samfarin laffaya masu masifar kyau da tsada wanda zasu kai hamsin,
sai mai binshi kuma Jakankuna da takalma masu shegen kyau da tsada sunfi set shabiyar ɗayan kuma
mayafaine da mai binshi Sleeping drees masu shegen kyau da ɗaukan hankali yayinda da mai bi masa
ɗan ƙaramin ke ɗauke da sarƙoƙin Gwal da ɗan kunnayensa da, kuma murjani irin na Masarautar, haka
aka riƙa buɗe musu Set ɗin farko har ƙarshe ana shiga na biyun suka sake gyara zama domin ganin abin
na yine, nan sukaci gaba da kallo...

Dai-dai lokacin kuma Moddibo suka dawo shida Ibraahim da Zakariyya suna shiga Falonsu kai tsaye
bedroom Moddibo ya nufa kallonsa Ibraahim yayi tare da faɗin.

“Ya dai Yah Aleey?”.

Cikin fesar da numfashi Moddibo ya kallesa kana yace.

“So nake in ɗan watsa ruwa ne baki ɗaya yau atakure nake”.

Kai ya gyaɗa da faɗin.

“Toh ba matsala”.
Cike da kasala Moddibo ya nufi toilet ya watsa ruwa ya fito bayan ya fito ya shafa mai tare da feshe
jikinsa da turaruka masu daɗin ƙamshi kana ya sanya Jeans Blue da Farin Riga mai guntun hannu
yalwataccen sumar kansa zuwa kwantaccen sajensa yasha gyara yayin da jikinsa ke fitar da wani
sihirtaccen ƙamshi.

Ibraahim da idanunsa ke ƙofar bedroom yace

“Wowww Yah Aleey dama haka ƙananan kaya ke masifar yi maka kyau tun da na kazo ban gaba da
ƙananun kaya ba sai yau ni nai zatonma ko baka sawa ne”.

Murmushi Moddibo yayi tare da shafa sumarsa kana yace.

“Ina ɗan sawa time to time, so nake in ɗan sake dan naji yanayin garin yau kamar akwai ɗumi”.

Ya ida maganar tare da nufar kofar fita a falon yana mai ƙara matse jikinsa da Jeans ɗin da yasa don ya
ɓoye yanayin da yaje ciki.

Zakariyya dake zaune yayi saurin cewa.

“Ya dai ina zaka je”.

Lumshe idanu Moddibo yayi tare da buɗe su akansa kana yace.

“Zan ɗan fita ne dama ina so zan duba Asma'u”.

Ajiyar zuciya Zakariyya ya sauƙe tare da cewa.

“Ok dama ina so mu ɗanyi magana ne dan gaskiya gobe nake tunanin zan wuce amma yanzu akwai
dalilin da zai tsadani”.

Anutse Moddibo ya gyara tsayuwar tare da faɗin.

“Wace magana ce?”.

Zakariyya na kallonsa yace.

“Naga kamar kuma sauri kake”.

Kai Moddibo ya girgiza tare da cewa.

“A'a In ba mai daɗewa bane ina jinka”.

Zama Zakariyya ya gyara kana ya kalli Moddibo tare da cewa.

“Toh kazo ka zauna mana”.


Baya Moddibo ya dawo kana ya zauna gefensa.

Numfashi Zakariyya ya fesar kana yace.

“Gaskiya nima fa naga matar Aure acikin ƙwayen Amaryanka”.

Da mamaki Moddibo ya kallesa kana yace.

“Wacce fa?”.

Hannu Zakariyya ya buɗe tare da faɗin.

“Naji dai jiya kamar ana kiranta me ma? Na dai manta sunan amma wata ƴar doguwa haka dai fara mai
sanyi”.

Ahankali Moddibo yace.

“Ko dai Asiya?”.

Yatsu Zakariyya ya ƙyasta da murmushi afuskarsa yace.

“Yes of course ita, Ita nake nufi naga ta kwanta min dan tana da nutsuwa ni gaskiya yanzu bani da wani
tunani in ba nata ba”.

Murmushi Moddibo yayi wanda ya sake bayyanar da kyawun fuskarsa kana yace.

“Toh Lallai dai kam toh ba laifi in Sha Allah zanyi nazari akai.

Amma yanzu bari inje idan na dawo zanyi nazari akai sai muyi maganar”.

Numfashi Zakariyya ya fesar tare da faɗin.

“Toh shikenan ba matsala amman dai ka sani ni ba irin Dr Jameel bane da zakace sai kayi nazari”.

Dariya kawai Modibbo yayi

Kana ya mike ya tafi...

Acan Falon su Khausar kuwa Hajja Nana ce kaɗai zaune adining area yayin da Khausar ta fito daga
bedroom rabonta da abinci tun Breakfast har zuwa yanzu babu komai acikin sai tarin damun gumbuna
da kuma garuka dasu tsumin masu ratsa jiki da cire yunwa da Ummi ka bata.

Sanye take cikin wani tattausan material Blue Black me ɗan ratsin Pinch daga saman rigar atsuke atake
yayin daga ƙasan kuwa abuɗe yake daga ƙirjin rigan net ne haka ma hannun net ne tayi ɗaurin ɗankwali
as-down yalwataccen sumar kanta ya kwanta luf-luf bisa goshinta ,duk da cewa ba tayi makeup ba
Amma tayi masifar kyau farar powder ce kawai a fuskarta sai kwalli da ta zizara aƙwayar idanunta mai
haske kaman Madaran sai kuma laɓɓanta yake shiƙin Man baki sai tafi to tamkar wata tauraruwa.

Kallon Hajja Nana dake zaune da.

Fruits agabanta tayi cikin sanyi jiki ta nufi ɗaya daga cikin kujerun Falon zata zauna cikin tsira mata idanu
Hajja Nana tace.

“Zo nan?”.

Ɗan tura baki tayi cikin yanayin sanyin da tunda aka ɗaura aurenta ya ziyarceta tace.

“Menene?”.

Hararanta Hajja Nana tayi tare da cewa.

“Bace miki nayi kizo ba, toh kizo mana tunda na kiraki, ai in kinzo koma menene zakiji, ke da Allah yayiki
ba'a miki abin arziƙi, sai yiwa mutum gardama?”.

Batare da tace Uffan ba ta nufi dining ɗin kana taja kujera ta zauna gefenta.

Cike da kulawa Hajja Nana tace.

“Meyesa bakya son cin abinci?”.

Langwaɓar da kai tayi tana wasa da yatsun hannunta, baki ɗaya tayi sanyi ahankali ta ɗago Idanunta
dake ƙyallin hawaye ta kalleta.

Haɓa Hajja Nana ta riƙe kana tace.

“Ikon Allah kuka kuma zakiyi keda kika ce shi kike so? an kawo ki gidansa ai sai dai kiyita dariya da farin
ciki bawai kuka ba”.

Kai ta girgiza Muryanta cike da rauni ta kalli Hajja Nana tare da faɗin.

“Baza ki gane bane Hajja Nana Ina kewar Momyna sannan ina kewar Raudat, kuma yanzu gashi Haiydar
ma wai ance idan antashi tafiya dashi za'a yi akace”.

Kai Hajja Nana ta jinjina kana tace.

“Eh tafiya za'a yi dashi mana, dukansu ma tafiya zasuyi nice dai zan zauna”.

Jin abinda tace yasa farin ciki ya mamaye zuciyar Khausar ahankali tace.

“Da gaske zamu zauna Hajja Nana?”.


Kai Hajja Nana ta gyaɗa cikin yanayinta na ƙasaita da zafi tace.

“Toh badole in zauna ba tunda kece kika ce kina son shi, bashi bane yace yana sonki, ai dole in zauna In
jira inga wani irin tarba zai miki, inga kamun ludayinsa,dan wlh Allah kenan In naga ya Miki abinda bai
min ba duk da ke kikace kinji kin gani kina so wallahi ɗaukarki zanyi mu tafi tare”.

Wani irin sanyayyar ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tana kallonta cike da jin daɗi dan harga Allah ta fara
tsoron a tafi a barta ba kowa nata tare da mutumin da in baici zalinta ba baya jin daɗi ta kuma san baya
sonta.

Hajja Nana kuwa cike da izzah da ƙasaita ta cigaba da cewa.

“Na faɗawa Baffanki ma tun jiya ya fara cewa inyi haƙuri kuma Wallahi babu abinda zai tafiyar dani,
zama daram anan sai naga yanayin kamun ludayinsa mutumin da an bani labarin tun a makarantar ma
ba shiri kuke ba kinga ko nida tafiya sai naga abinda ya turewa buzu naɗi”.

Kai Khausar ta girgiza tare da sunkuyarwa ƙasa ita kanta ta san.

Moddibo baya ko ƙaunae ganinta kuma tafi kowa sanin tsanar daya mata baya son alaƙa da ita koda
kallonta ne baya son yi”.

Hannu Hajja Nana ta sanya ta ɗago haɓarta kana ta tura mata Bowl ɗin dake ɗauke da Fruits ɗin gabanta
da Mukara dake ɗauke da Juice kana tace.

“Gashi kici wannan koda baki ci Abinci ba shi zai ɗan taimaka miki, kinga gaba ɗaya ki rame”

Akuma dai-dai lokacin suka ɗaga kansu suka kalli ƙofan Falon jin Antura ƙofar an shigo...

Da sauri Khausar ta sunkuyar da kanta ƙasa ganin Moddibo Hajja Nana kuwa sallamarsa ta amsa tare
da zuba masa ido.

Cikin ranta tace.

“Uhmmm ai ba banza Khausar tace taji ta gani wannan kyau haka ai masha Allah, Ɗan ko maƙiyinsa
yasan shi mai kyau ne”.

Shi kuwa Modibbo a tsakiyar Falon ya tsaya kana ya kalli Hajja Nana dake cikin shiga ta alfarma duk da
tsufanta bai hanata kyawunta fita ba cikin ɗan sakin fuska kaɗan yace.

“Ku kaɗai ne”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa masa tare da cewa.


“Eh”.

Cikin sauƙe numfashi yace.

“Ina Innayi?”

Tana tauna Inabi ta amsa da.

“Sun sauƙa ƙasa wajen Didi”.

Ajiyar zuciya mai nauyi ya sauke tare da faɗin.

“Uhmmy”.

Sai kuma ya nufi dining area ɗin.

Sassayyan numfashi Khausar ta shaƙa jin yadda ƙamshin jikinsa ya karaɗe wurin.

Shi kuwa cikin wani irin narkekken yanayi yasa hannunshi ya ɗan ja kujeran dake Facing ɗin Khausar.

A hankali ya zauna yayin da ƙamshin Kwallacar sirri da Khausar tayi amfani dashi ya cika masa hanci da
ƙara sake mishi wata fitinenniyar kasala.

Kallon Hajja Nana dake shan Fruit yayi kana yace.

“Ya kike?”.

Cikin tsareshi da tace.

“Lau nake”. Da gefen idonshi ya kalleta jin yadda ta amsa kamar a faɗace, bakinshi ya ɗan taɓe tare da
ɗan ƙara kwantar da kanshi jikin kujerar,

Tare da zaro wayarsa ya shiga latsawa a zahiri wayarsa yake kallon, amman a baɗinin kuwa ƙafafun
Khausar dake ƙasan Table ɗin yake kallon yadda ta ɗan ɗaura ɗaya bayan ɗaya, wanda hakan ya bawa
sharaɓanta dama bayyana a fili.

Khausar kuwa batare da ta ɗago ta kallesa ba ta cigaba da juya Tuffan dake hannunta batare da taci ba.

Ɗan leƙa ƙasan dining table din ya kumayi a hankali ya lunshe ido ganin tana ɗan kaɗa ƙafafunta yasashi
ɗan tura nasa ƙafar dama ƙasa kusa da nata, a hankali ya zare takalminsa.

Sai kuma ya ɗan juya idonshi ya kalleta, still dai wasa take sa Apple ɗin

A hankali ya ɗago ƙafarsa, tare ɗan mannashi kan sharabart kana a hankali ya jawoshi yayi ƙasa dashi
har zuwa kan rumfar sawun nata ya shafa da sassayan tafin ƙafarshi mai taushi.
Da sauri ta ɗago ta kalleshi tare da sakin ajiyan zuciya dan sanyin tafin sawunshin daya ratsa mata jiki da
zuciya.

Hajja Nana kuwa, baki ta ɗan sake tana kallon yadda Modibbo ya tsare Khausar ɗin da ido, sai kuma ta
juya ta kalli Khausar ɗin da ta ɗan lunshe idanunta ganin shima ɗin ita yake kallo.

Jin yadda ya wani irin murza tafin kafarshi kan natane yasa ta sake buɗe idanunta tare da kallonshi tana
maijin wasu baƙin abubuwan na fitowa daga cikin idanunsa suna ratsa nata idanun,

Dan shima ɗin ita ya zuwa idanunshi tamkar zai mannesu cikin nata.

Ahankali ya motsa lips ɗin sa wanda ko Hajja Nana dake gefensu bataji, abinda ya faɗa daga shi sai ita
yace.

“Baki iya gaisuwa ba ko?”.

Yayi mgnar cikin kasalalelliyar muryar data sa Khausar ƙara kallonsa domin bata taɓa saninsa da wannan
kuryarba.

Ahankali ta sake yin ƙasa da kanta tana mai ɗan jin yadda yake mata wani irin abu da yatsunsa, cikin
sanyi ta kawar da kanta gefe sai kuma ta motsa laɓɓanta tare da cewa.

“Ina yini”.

Yana shaƙan ƙamshin Kwallacar ta dake hargitsa mushimi kwanya yace.

“Lahfeyyahhh”.

Ƙasa tayi da kanta tana cigaba da wasa da Tuffan dake hannunta ita bata gutsira ba ita bata ajiye ba sai
kuma yaji gaba ɗaya jikinta na amsa sabbin yanayi sabida sautin murya yadda ya amsa mata gaisuwar da
yasata jin tsikar jikinta ya bada salon yum.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya sake sanya babban yatsansa da mai bi masa akan sangalalina zuwa kan
rumfar ƙafartan yana saƙƙo dashi a hankali tare da jujjuya kan yatsar.

Ahankali Khausar ta ɗago manya idanunta dake sheƙi ta kallesa.

Girarsa na dama ya ɗaga mata tare da jan dogon numfashi kana ya jingina bayansa da jikin Kujeran sai
kuma ya marairaice idanunsa da suka fara rikiɗewa lokaci ɗaya wani irin yanayi ya fara ratsa sassan
jikinsa musamman daya shaƙi ƙamshin Daddaɗan Kwallaca da kuma Humran da Momy ta siya mata
wajen

_Aysha Aliyu Garkuwa_ .


Hajja Nana dake gefensu kuwa baki ta saki da ido cike da mamaki take binsu da kallo ganin wani irin
shu'umi kana mayataccen kallon da sukewa juna kai kace tattabarune.

Da zaran ta kalli Khausar sai kuma ta juya ta kalli Namijin duniyan da shi yama mance da ita a wurin.

Zamansa ya gyara tare da sake tura ƙafarsa ya taɓa ƙafanta da kyau.

Ahankali ta kuma ɗaga manyan idanunta ta kallesa.

Ganin tana kallonsa yasa ya mata Signal tare da kashe mata ido ɗaya.

Ya Salam shine abinda ta iya faɗi cikin ranta.

Sabida abin yazo mata da saƙonni masu zafi, shi Modibbo ne kuwa, ya akayi haka harda signal abun yan
ikkah ya iya.

Shi kuwa Modibbo cikin wani irin amintaccen yanayi ya kuma ɗaga mata girarsa ɗaya, sai kuma ya miƙe
daga jinginar da yayi daga jikin Kujeran ya zauna dai-dai. Cikin yanayin gaza sarrafa tunaninsa da jikinsa
ya ɗan fesar da numfashi tare da laso lips enshi kana a

hankali ya ɗago hannunsa tare da kafa guiwar hannun nasa, bisa table ɗin.

Hannunta dake kan Mug din dake gabanta ya riƙo cikin nasa hannun.

A tare suka ja nannauyan numfashi, kana a tare suka fesar da numfashin.

Ita kuwa Khausar ɗaya hannun nata da har zuwa lokacin take riƙe da Apple taci gaba da jujjuyawa tana
maijin tamkar saman gajumare yake turata.

Yayinda shi kuma gwiwar hannunsa ke tokare da table ɗin.

Cikin yanayin mamaki ta buɗe Idanunta da baki tana kallonsa.

Gira ɗaya ya sake ɗaga mata yana lumshe idanunsa, a hankali ya matse hannunta acikin nasa bawai
yanda zataji zafi irin dai ƴar matsarnan da tafi kama da tausaya yayiwa hannun yatsunta ya ɗan matse
tare da zubawa faratunta ido .

Cikin wata irin kasala mai cike da shauƙi da dawowar yanayin da ya rayu kafin a sace J ɗinsa ya dawo
mishi sabo, motsa laɓɓansa yayi a hankali tare da sanya ƙwayar idanunsa anata kana yace.

“Yahh mukayeeh dahh kehhh?”.


A kasalance ta lumshe idanunta acikin nasa kana ta buɗesu, baki ɗaya yanayin da yake mata magana ya
tsumata wani irin yanayi take ji yana huda ko wani magudanan jinin jikinta yayin da sautin muryansa ke
ratsa har ƙoƙon zuciyarta cikin wata shagwaɓaɓbiyar murya ta kalli idanunsa kana ahankali ta furta.

“Akan me ɗin?”.

Da sauri ya matse jikinsa, kana ya lumshe idanunsa sautin Muryanta nayi masa amsa kuwwa acikin
dodon kunnensa yace.

“Ba cewa nayi ki yanke farcen nan ba?”.

Langwaɓar da kai tayi tana lumshe idanunta ta motsa laɓɓanta tare da cewa.

“Zan yanke ai”.

Numfashi ya fesar kana yace.

“Sai yaushe kenan?”.

Shiru tayi ta gaza cewa komai, sai zubawa sajensa ido da tayi sabida salonshi ya fara a yanayin da bata
zataba.

Shi kuwa cikin sanyi ya ɗan ƙara matsowa tare yin mgnar can ƙasan maƙoshi yace.

“Ba tun jiya nace ki yanke ba baki yankeba, still yau ɗin tunda gari ya waye baki yanke ba har yanzu”.

Ta wani langwaɓar da kai tana mai narkar da ƙwayar idanunta cikin nasa tare da faɗin.

“To ai zan yanke”.

Baki sake Hajja Nana ke kallonsu ta kalli Khausar ta kalli Moddibo dake riƙe da hannun Khausar yana
shafa saman tafin hannuntan da babbar yatsarshi ga wani irin fitinennen kalo da yake binta dashi kai
kace zai cinyeta ɗanye ita kuwa Khausar duk ta saki da alamun da zata samu dama narkewa zatayi a
jikinshi.

Moddibo kuwa har ga Allah har cikin ransa ya manta da cewa akwai wani mutum awajen.

Cikin lumshe idanu ya cigaba da shafa ƙafanta Khausar kuwa wani irin yanayi take ji aduk lokacin da
sanyayyar yatsunsa suka sauka akan sharaɓanta.

Hajja Nana kam ta gaza ɗauke idanunta akansa kallon ikon Allah kawai take.

Ita kam Khausar jin yanda yatsun ƙafansa ke yawa anata yasa cikin kasala tace.
“To ai zan yanke”.

Kai ya girgiza still Muryansa ƙasa-ƙasa yace.

“Um-um baza ki yanke ɗin ba”.

Da sauri ta ɗan ware idanunta acikin nasa dake cike da zallan fitina da mayata tace.

“Allah zan yanke”.

Sassayan numfashi ya fesar tare da faɗin.

“Ko dai kinfi so ni ɗin na yanke mikinne?”.

Da ɗan sauri ta girgiza masa kai tunawa da tayi jiya cewa yayi idan zai yanke zai haɗa da kan ƴan ya
tsunta.

Hajja Nana kam sai raba ido take ta kallesa ta kuma kalli Khausar kallon ikon Allah da abin al'ajabi take
aranta tace.

“Iyye kaji ƴaƴan zamani kaji ja'irin yaro agaban nawa lahaula fisha'atillahi”.

Moddibo kam har ga Allah ya manta da ita awajen.

Yayin da Khausar ma halin da Moddibo ya jafeta na wani irin kasala da mutuwar jiki yasa ta mance da ita
Allah yasani da zata samu kwanciya takesonyi sabida jikinta daya gama sakewa tuno nitsuwa da salaman
da taji lokacin daya ruggume ta yasa takejin da jikinshi da tayi bacci.

Cikin nutsuwarsa da kuma yanayin da yake ciki ya ɗan fusgo hannunta dake cikin nasa wanda yasa dole
Khausar matsowa ya zamana ɗaya hannunta ya sauƙa akan table ɗin ga mamakinta sai taji ya kai
ƙaramin yatsarta cikin bakinsa.

Yana kai ya tsanta cikin bakinsa Hajja Nana ta rumtse idanunta da ƙarfi tare miƙewa da sauri tabar wajen
jikinta na rawa, ganin rashin kunyar da suke ba abinda take maimaitawa abakinta sai Innalillahi wa'inna
ilaihi raji'un gani take kamar saɓon Allah suke, wannan wace irin fitina da tsaurin ido ne da yaran zamani
sukeyi, yaro salla-salla ashe ashe ko al'wala bai iyaba ita kuma hegiya kamar ba ita ke kuka yanzu, sai
wani lumshe ido take kamar ɓera na lasar gari wato ita hegiya ga miji ko, Allah mai iko. har ta fice daga
wajen tana jajanta al'amarin aranta tana mgnar zuci.

Moddibo kuwa yana sa yatsarta abaki ahankali ya manna yatsar tsakiyar harshensa.

A tare suka lumshe ido domin kusan a tare baƙon lamarin ya ziyarcesu.
Kusa 1 minute sukayi a haka kana suka buɗe idon a tare.

Manyan idanunsa da suka sirance ya liƙa mata, kana ya fara ɗan datsa dai-dai kan farcen da haƙoransa
na gaba, ahankali yake cigaba da datsawa yana mai lumshe idanunsa har ya gama cire farcen.

ahankali ya zare yatsan daga bakinsa, kana ya ɗan kawar da kansa gefe tare da tufar da farcen.

Idanunsa da suka sake rikiɗewa ya mayar kanta kana ya ɗaga mata girarsa.

Khausar kuwa kallon ƙwayar idanunsa take tana hango wani fitinan nan al'amari acikinsu wanda ya sake
haddasa mata kasala da wani irin baƙon al'amari Narkewa take tamkar kitsen ji take tamkar bazata iya
sarrafa kanta azaune ba.

A hankali ya kuma maida yatsan baki ganin kamar farcen bai gama yankuwa ba cikin kasala ya datse shi
kana ya tofar wani irin tsuma naman jikinsa keyi daga can ciki.

Sai kuma ya sake kamo mai binsa shima ya sanya abakinsa ya datse.

Idanunta dake lumshe ta buɗe jin hannunsa dake riƙe da nata yana kar-karwa ta ɗan kallesa.

Shima kallonta yayi kafin ahankali yayi wani irin miƙa kana ya maida ƙaramin yatsanta bakinsa wanda ya
yanke cikin wani irin salo da tsananin shauƙi ya shiga tsotsan ya tsan tamkar wanda ya kama Fida.

Atake taji tsikan jikinta ya miƙe yam-yam wani irin abu taji yana ratsata tun daga tsakiyan kanta har tafin
ƙafanta.

Da sauri ta lumshe idanunta.

Cikin wani irin yanayi da bai taɓa riskansa ba ya buɗe Idanunsa ya kalli yanda ta runtse nata da kuma
yanda jikinta ke tsuma da kuma yanayin fitinennen lasala daya bayyana tare da ita.

Ahankali ya zare tsayan tare da fitarwa daga bakinsa jin ya fitar da yatsan yasa ta buɗe Idanunta ta
kallesa jin yanda baki ɗaya ilahirin jikinsa ke rawa ga kuma ƙwayar idanunsa da suka cika taf da hawaye.

Ahankali ya lumshe Idanunsa sai ga hawaye sharrr sun z....

*Masu son Maganin infection da maganin mata, ku marmatso wannan account no in ne naku ta ciki zaku
turo kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP
NUMBER'N na 09097853276. akwai sabbin kaya masu zafi suna nan bisa hanya, ki turo kuɗinki a saki
cikin lissafi. Kayanen mata masu zafi sadidan daga Chadi akwaisu Garukan daka, gumbunan,
Tsumummuka, cida Ciccibi Abodi cida kaza ci da jan nama kwanon ƙasaitacciyar mace biyar sirri, furar
mata, gumbar madara Gumbar kolli mai ƙyallin al'khairi gumbar uku al'khairi, gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, gumbar riɗi, garin maɗi garin melɗamhi garin ilanwaddihi garin mallaka, tsumin riɗi tsumin
tsirtai tsumin kinfi budurwa, tsumin riɗi, tsumin ta baje Sabaya, matsin maliƙi mai masifar matse mace
matsin daɗi har maɗiga, mai ɗan kare kyau. Kullacar sirri al'ajabu shu'umar Humra, da duk sauran kan
ƙamshi. Haɗin amarya budurwa ko bazawara haɗin mai jego ko uwar gida, akwaisu Available set ɗinmu
hawa hawane akwai manya akwai ƙananan, ƙanan daga 40k ne 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙarami
haɗina na karshe sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar shi 7k ne shine ƙarshen haɗina kenan... Manyan
set ɗin kuma daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k ke zaki faɗi haɗin nawa kikeso anyi miki kana kimin bayanin
yadda kikeso da matsalarki ni kuwa nasan abinda zan haɗa miki, ina araha kam amman ina hana bashi*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

51

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwatanta Zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.
INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki
dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection
cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin
kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin
kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana
dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya
musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki
aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa
ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga
account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min
mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi
Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari
da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan
Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR
MA'AURATA.

*Littafin Sakayya dai na kuɗi ne 1k ne kacal 0661110170 gtbank Aisha Aliyu Garkuwa, ki biya sai ki Turi
min evidence of permit 09097853276 sai in tura miki littafin ki karanta abinki cikin aminci ba haƙin wani
bisa kanki baki karanta na sata kuma na Allah ya isa ne*

51

Yana lumshe idanunsa sharrr wasu hawaye Masu masifar sanyi suka zubo bisa fuskarsa.

Khausar kuwa ahankali ta cigaba da kallonsa cikin mamaki ganin hawaye kwance asaman fuskarsa
yayinda itama gaba ɗaya hukunta tsuma yake yi saboda jin ya manna bayan hannunta bisa sakenta da
yake masifar mata kyau, haka nan ta tsinci kanta da shafa bayan hannun nata kan saken sai wani
amintaccen numfashi ta farar jin wani irin sulɓu da tashin da sajen keda shi.

Ya Salam shine abinda Modibbo ya iya faɗi can ƙasan maƙoshinsa. Ahankali ya sanya hannunsa akan
table ɗin kana ya kifa kansa saboda wani irin fitinenne yanayi da yake firo kishi, still hannunsa na riƙe da
nata wani irin yanayi yakeji da bazai taɓa iya jumrewa ba shi kansa ya rasa shin Khausar wacce irince da
muddin yayi tozali da ita nitsuwara ke gushewa duk yadda zaiyi sai ya gaza sarrafa kanshi da tunaninshi.
Sun daɗe ahaka batare da wani yayi magana ba ko kuma ya janye hannunsa daga cikin na ɗan uwansa.

Ji yake bazai taɓa jurewa ba, muddin zaici gaba da ganinta ko ta wulga gabansa yasan bazai iya kama
kanshi tabbas zaiyi abinda yakeji baison nuna ƙulafacinsa.

Khausar ce ta fara jin alamar ana haurowa kuma bisa duk kan alamu Asma'u ce dan taji muryarta kamar
waya takeyi da Bashir.

Mutsu-mutsun ta fara tare da ƙoƙarin ƙwace hannunta kansa ya ɗago ya kalleta da rikitattun idanunsa.

nan taga idanunsa sun sake kaɗawa sunyi masifar Jaa kana ga alamun sun sake cika taf da hawaye sai
dai hawayen basu zubo ba sai sheƙi suke suna bada kalan hazo-hazo yayin da jikinsa ke cigaba da tsuma.

Ƙoƙarin janye hannunta ta cigaba dayi, a kasalance ya ɗago kansa ya kalleta, sai kuma ya tsuke fuska tare
da ɗan hararanta yace.

“Sakeni mana”.

Cikin ɗan karen kasalan daya zuba mata tace.

“Ai banice ke riƙa da kaiba, kane kake riƙe dani fa”.

A fakaice yace

“A zahiri ba”.

Sai kuma ya zare hannunshi sabida shima yaji alamun ana haurowa kan steps ɗin.

Ahankali yaja dogon numfashi mai ƙarfi kana ya miƙe tsaye tare da juya bayansa ya buɗe Labulen jikin
dining ɗin ya tsirawa harabar Side din nasu ido wanda yake ɗauke da wani Kekkyawan gate golding sai
farafajiyar da zata iya ɗaukan motoci bakwai sai kuma can ƙasa da ya hongu alamun BQ ne daga bakin
gate kuma babban ɗakine da bayi a ciki da alamun Hadiman yankinsa ne.

Asma'u ce ta shigo ganinsa tsaye yasa tace.

“La Yah Moddibo kashigo?”.

Batare daya juya ya kalleta ba ya gyaɗa kai tare da cewa.

“Eh na shigone inga ya yanayin jikin ki dan jiya suma kikayi”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.

“Jikina da sauƙi Yah Moddibo.


Amma ni dai har yanzu gani nake Yah Jameel nane, duk da kowa ya yarda cewa ba Yah Jameel bane. Ni
na kasa yarda”.

Kai ya girgiza still batare daya juya ba yace.

“Ba *J* bane Asma'u ba kiji na faɗa miki ba Jameel bane ina har rantse miki nayi”.

Kai ta gyaɗa kana ta fesar da numfashi bawai dan ta yarda ba sai dan batason yi masa musu yasa tayi
ƙasa da kanta tare da faɗin.

“Toh shikenan Yah Moddibo”.

Still Idanunsa na farfajiyar gidan yace.

“Ina Innayi?”.

Ahankali tace.

“Suna can tukunna nima an turo nine inzo in faɗawa Khausar ta shirya masu zuwa yi mata lalle zasu zo
su fara yi mata shiyasa nazo”

Ta ƙarashe maganar tana kallon Khausar dake ta faman lumshe idanu

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Ok”.

Daga nan ya juya yabi ta bayan Asma'u batare da ya yarda sun haɗa ido ba ya fita.

Asma'u kuwa idanunta akan Khausar tace.

“Khausar wai ki shirya masu zuwa yi miki lalle zasu zo inji Lalla Khadijah”.

Ta ida maganar tana kallon Khausar sai kuma ta juya Idanunta tsakiyar Falon ganin tuni Moddibo ya fita
yasa.

Ta gyaɗa kai tana lumshe idanunta tace.

“Toh shikenan sai sunzo”.

Murmushi Asma'u tayi kana tace.

“Iyeee lalle Yah Moddibo har an fara biyo hanya kenan?”.

Hararanta Khausar tayi tare da cewa.

“Ban gane ya fara biyo hanya ba”.


Dariya Asma'u ta sanya kana tace.

“A gani nayi ya fara zirya shiyasa.

Acan Falo naji Lalla Khadijah na cewa ayi agyaraki ayi miki lalle da turaraki, da sauransu dan gobe za'a kai
ki Side ɗinki inda zaku zauna aima gwara ayi akai ki tunda ya fara zirya”.

Hararanta Khausar tayi tare da faɗin.

“Wani irin ya fara zirya kefa Asma'u baki da mutunci.

Yanzu ina kina ji ce miki yayi yazo ya duba ki ne da jiki ni tunda yazo ko magana ya min ne ma?”.

Dariya Asma'u ta sanya ganin duk maganar da take jikinta ba kuzari sai wani irin fitinennen miƙa da
takeyi da sauƙe ajiyan zuciya, cikin dariyar tace.

“Toh waya sani abu a duhu wannan ba tsakanin ku ba, ni ƙanwar miji ƙawar amarya me nawa aciki”.

Fitowa Hajja Nana tayi daga bedroom kasancwar tana jin duk abinda Asma'u ke faɗa tana hararan
Khausar tace.

“Faɗa mata dai Asma'u Munafuka ai Ni yau naga abinda yafi ƙarfin idanuna ashe-ashe yanzu ko ba muga
ruwan sama ba kada muyi mamakin abinda bai kawo saba fitsaran da ake zubawa ne”.

Dariya Asma'u ta sheƙe dashi ganin Hajja Nana tsakaninta da Allah take maganar sassauta dariyata tayi
tare da cewa.

“Hajja Nana me sukayi?”.

Zare idanu Hajja Nana tayi tare da kallon dining ɗin kamar dai har zuwa lokaci ganin su take kana tace.

“Menene ma basuyi ba Asma'u, yaro idanu asoye wannan ɗa yaban mamaki”.

Sosai Asma'u ke dariya kana tace.

“Yo Hajja Nana bake kike cewa ba zaki koma ba sai kin tabbatar yana sonta ko baya sonta ba”.

Haɓa Hajja Nana ta riƙe da alama har yanzu mamakin bai bar ranta ba tace.

“Eh lallai kam naga alama zai nuna min ƙashin tijara kenan”.

Kallon Khausar data zubawa dining ido Asma'u tayi kana ta maida idanunta kan Hajja Nana tare da cewa.

“Kai Hajja Nana kar kiyiwa Yah Moddibon mu sharri mutum ne mai kunya”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa kana tace.

“Ai kam dai ni naga kunya, ganin idona.

Ni nasan yana da kunya naga kuwa Kunya ganin Idona har gudu yake a idanunsa”.

Ta ida maganar tare da jan tsaki ta juya kana tace.

“Shegun Yara”.

Shiru Khausar tayi tare da bin Hajja Nana data shige bedroom da ido.

Asma'u kuwa har takai bakin kofa ta juya ta kalli Khausar tare da faɗin.

“Yawwa Ummi tace In faɗa miki ki ɗauki wannan sauran damun da aka miki ki ɗauka ki shanye”.

Langwaɓar da kai Khausar tayi cikin sanyi murya tace.

“Wallahi nikam na gaji da ɗure-ɗuren nan shiyasa bana iya kocin abinci aɗura ma wannan aɗura ma
wancan”.

Murmushi Asma'u tayi tare da faɗin.

“Idan baza kisha ba Ni kibani in sha dan Ni gyarane tun daga yanzu sai In fara yiwa wanda zan Aura ba
ruwana”.

Zama Khausar ta gyara kana tace.

“Kinji jiki wallahi, kema idan naki yazo ana ƙaƙaba miki bazaki shaba”.

Ware idanu Asma'u tayi tare da faɗin.

“Wallahi sha zanyi Ni kuma irinki ne? Kin san dama ni inaso abun zaƙi-zaki ke kuma kin fison abu mai ɗan
yaji-yaji, sai ki zauna kiyi ta noƙe-noƙe baza ki shaba”.

Tana gama maganar ta juya ta tafi.

Bayan tafiyar Asma'u da minti talatin masu yiwa Khausar Lalle suka zo.

Cike da ƙwarewa da sanin aikinsu suka fara Cancaɗa mata jan lalle cikin tafin hannu da baya kana suka yi
mata manyan flowes abinka da faran fata atake tayi wani masifar kyau.
Kana sukayi mata atafin ƙafa zuwa sama wani irin kyau na ban mamaki yayi tun kafin a wanke ita kanta
Khausar kallon lallen take tamkar wata sarauniya.

Ɗaya daga cikinsu ta dawo bayanta cikin harshen Larabci tace.

“Kiyi haƙuri zamuyi abayanki”.

Ɗan ware idanu Khausar tayi kasancewar tana jin larabci tace.

“Harda baya kuma?”.

Kai mai Lallen ta gyaɗa mata tare da faɗin.

“Eh harda baya ma”.

Ta faɗa tare da zuge zip ɗin rigar ta fara zana mata wani irin zanen ɗawisu mai masifar kyau da ƙawa
kana ta dawo ta gaba asaman ƙirjinta ta zana mata wani siririn star kamar Tatu nan kyawunta ya sake
fitowa ta zamo tamkar sarauniyar kyau...

Sai gab Maghriba su Innayi suka dawo dai-dai lokacin da masu lallen ke shirin fita kallon Innayi tayi tare
da cewa.

“Idan lallen ya bushe baku zaku wanke mata ba ku bari zamu zo mu haɗa mata ruwan wankewan”.

Kai Innayi ta gyaɗa kana suka shige.

Bayan sallar Maghriba suna dawo suka wanke mata lallen...

Acan Abuja Birnin tarayya kuwa Amina ce zaune a tangamemen Falon ta yayin da Uncle Naseer ke
gefenta ba suyi sallar Maghriba ba kuma basu shiryawa tashi yiba.

Ahankali ya shafo fuskarta tare da cewa.

“Nayi missing naki”.

Hannunsa dake shafa fuskar tasa ta riƙe tare da faɗin.

“Nima nayi missing ɗin ka Uncle Naseer yau fa tun safe daka fita baka dawo ba”.

Yana binta da wani shu'umin kallo yace”.

“Na ɗan yi tafiya ne Shiyasa”.

Ashagwaɓe ta marairaice fuska tare da faɗin.

“Uncle Naseer ina kaje?”.


Fuskanta ya tallafo kana ya motsa laɓɓansa kusa da kunnenta yace.

“Wajen abokaina naje”.

Kafin tace wani abu ya janyota jikin tare da kissing ɗin wuyanta yana shinshina sassan jikinta kafin
ahankali ya zuge mata zip ɗin rigar ta tare da kama Breast ɗin ta yana sarrafata cikin ƙwarewa tashiga
mayar masa da martani ƙasa ya zamo daita kana cikin zafi-zafi suke romance juna har suka biyawa
junansu buƙata anan falon yana gama ya tashi ya shiga dakin da tunda suka zo bai barta ta shiga ba ko
fita zaiyi saiya rufe wanda kuma lokuta da dama tana jin huci daga cikin ɗakin amman koda ta gaya kishi
bai kulataba, da wannan tunanin itama ta miƙewa ta nufi ɗakinta...

*Morocco*

Bayan an idar da sallar Maghriba matan da sukayi mata lallene suka shigo suka haɗa mata ruwan da
zatayi wanka ruwane me masifar kyau da ƙamshi koda tayi wankan ta fito wani irin sheƙi da ƙamshi take
bazawa lallen ya kwanta akan farin fatar ta da yayi smooth ta dawo kamar wata tarwaɗa fatan ta sai
haske da ƙyallin Amarci yake.

Already tayi alwala kafin ta fito zama tayi awani kujera suka fara turara mata jikinta da turare bayan sun
gama suka fara turara mata gashinta da wasu masu daɗin ƙamshi nan da nan gashin ya dauki sheƙi da
haske..

Kai tsaye ta nufi bedroom ta gabatar da sallar Maghriba kana tana zaune har aka kira Isha'i ta idar
Misalin ƙarfe goma Ummi ta kalli Khausar hannunta riƙe da Damun data dama kana tace.

“Gashi ki karɓa kisha”.

Ahankali Khausar ta ɗaga idanunta ta kalleta cikin yanayin kasala da baƙon lamarin dake ratsa jikinta ta
fesar da numfashi tare da cewa.

“Ummi wallahi cikina ya ƙoshi bazan iya shaba”.

Ummi na kallonta tace.

“Bana son haka Khausar kar kiyi min musu tun bayan la'asar nace Asma'u ta faɗa miki kisha.

Ni nayi tsammanin kinsha ashe baki sha ba”.

Karɓa tayi cikin kasala da sanyi ta motsa laɓɓanta tare da cewa.

“Wallahi Ummi baki daya shi yake cika min cikina shiyasa ko abinci bana iya ci aɗuramin wannan
aɗuramin wancan abarni haka mana In huta”.

Harara Aunty Hajara ta watsa mata cikin ɗaure fuska tace.

“Zaki karɓa kisha ko kuma saina ɓata miki rai”.


Cike da tsoronta ta karɓa tasha kamar zatayi kuka...

Hajja Nana dake kallonsu tace.

“Hmmm Allah ya kawo saukin wato wai yanzu duniya ta kai duniyar da har ɗuwawu yana da kwallinsa
wai in zaku Aurar da ƴaƴa kuyi ta musu shungullah da hidima”.

Murmushi Innayi tayi tare da faɗin.

“Toh ai tun zamanin mu da ɗin ma ana gyara kam sai dai inke bakiyi gyara ba amma tun da kam ana
gyara”.

Wani kallo Hajja Nana ta watsa mata tana gyara zama tace.

“Kyanuna min gyara kema Baiwa kikace kinsan gyara bare mu matan Sarakuna”.

Dariya Innayi tare da shewa ta tafa hannu kana tace.

“Da ne nake baiwa yanzu kin manta agaban idonki aka ƴantani ai yanzu dai-dai nake dake”.

Zare idanu Hajja Nana tayi tare da cewa.

“Za dai kiyi dai-dai dani amma bazaki taɓa dai-dai dani ba ai wutsiyar raƙumi tayi nesa da ƙasa”.

Kallon Hajja Nana Khausar tayi kana tace.

“Kiyiwa Allah da Annabi Hajja Nana kada araba hali dake a ƙasar da ba naki ba nan fa ba muhallin ki bane
ba kuma cikin ƙannenki kikeba”.

Cikin sanin halin Hajja Nana Innayi ta kalli Khausar cike daso tace.

“Yi shiru abunki barni da ita, ai in da sabo tuni na saba”.

Baki sake Hajja Nana ke kallon Khausar kafin ta harareta da faɗin.

“Iyyeee kaji shegiyar Yarinya.

Toh naji ke kam muhallinki ne ai nan ɗin gidan Ubanki ne ko da zakice ba muhalli na bane”.

Lumshe idanu Khausar tayi tare da tura bakinta kana tace.

“To ko ba gidan Ubana bane ai gidan mijinane kam”.

Tafa hannu Hajja Nana tayi tare da Salati ta sanar da Ubangji kana tace.
“Eh ba shakka ba ƙarya wato ɗazun da yazo zugaki yayi ya Fom-famkaki ya zizzira miki”.

Cikin lumshe ido Khausar tace.

“Me kuma zai zira min?,Ya ziramin kamar wata rijiya”.

Ummi da Aunty Rukayya da Hajja Umma kam dariya sukeyi dramer Khausar da Hajja Nana baya ƙarewa.

Hajiya Bunayya kuwa Ayatsine ta kalli Khausar tare da jan tsaki kana ta kawar da kai gefe...

Asma'u kuwa ka faɗan Khausar ta dafa tare da faɗin.

“Allah yaja da Zamanin Matar Sarki”.

Murmushi Khausar tayi tare da Fari da idanu kana tace.

“Aaa faɗawa tsohuwa dai taji”.

Cikin mamaki da sarewa da halin Khausar Hajja Nana tace.

“A lallai kin samu baki Munafuka, ai ɗazu kam kuka kika tayi sai da na rarrasheki.

Amma yanzu saboda kinga kuna tare shiyasa kike min haka toh zasu tafi kuma har nima tafiya zanyi na
fasa zama, tunda kwaye min baya zakiyi”.

Dariya Asma'u ta sanya tare da faɗin.

“A'a Hajja Nana baza ayi haka ba dan Allah kiyi haƙuri ki zauna”.

Mutsike idanu Hajja Nana tayi tana hararan Khausar tace.

“Wallahi bazan zauna ba tafiya zanyi waɗannan fitsararrun ai in mutum ya zauna babu abinda ba zasuyi
agaban idanunsa ba”.

Jin abinda tace yasa Khausar langwaɓar da kai cikin sanyin Murya tace.

“Don Allah dan Darajar Annabi Hajja Nana na mu zauna mana kada ku tafi ku barni ni kadai”.

Sai kuma ta maida idanunta kan Ummi tare da cewa.

“Ayyah Ummi dan Allah za'a bar Asma'u anan ina?”.

Sai ta kuma juyawa ta kalli Hajiya Bunayya kana tace.

“Umma dan Allah ki barmin Addah Asiya”.


Cike da tsanarta Hajiya Bunayya tace.

“Eh dole abar miki su dole sai tunda su ba aure zasuje suyi ba”.

Araunane ta girgiza kai tare da faɗin.

“Ayyah ba haka bane dan Allah Ummi ku bar min su”.

Kai Ummi ta girgiza kana tace.

“A'a Khausar kada muyi haka dake.

Kada ma mufara haka dake”.

Rau-rau tayi da idanunta yayin da ruwan hawaye suka cika alamar gan take da fara kuma.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da faɗin.

“Um-um ki kwantar da hankalin ki kada kiyi kuka ai Asma'u kuna tare”.

Murmushi tayi Ummi kuwa miƙewa tayi ta nufi bedroom ɗin ta...

Agefen Moddibo kuwa tun da ya koma sashen sa ya samu Ibraahim da Zakariyya suna zaune batare
daya kalli inda suke ba ya wuce bedroom ɗinsa ya kwanta akife kana ya runtse idanunsa baki ɗaya
ilahirin jikinsa rawa yake wani irin Masifeffen feeling yake ji na fitar hankali.

Ji yake tamkar ya ɗaura hannunsa aka yaita zunduma ihu ko zaiji sassaucin abinda yakeji.

Wani irin tsuma jikinsa keyi da dama da zai iya yin sex da katifar koda zaiji sassaucin abinda yake ji juyi
kawai yake akan katifar cikin tsananin feeling dake addabar sa yayin da *A* ɗin sa ya miƙe tunda yake
bai taɓa jin azabebben feeling irin na yau ba baki daya na yau ya bambanta da duk na sauran lokutan da
yake ji.

Dr Jameel ne ya shi lokacin alwalan sallar Maghriba ganin yanda yake murƙususu yace.

“Ya dai tun ɗazu nazo Ibraahim suka cemin kashiga ciki kana kwance lafiya dai?”.

Shiru Moddibo yayi dan ya tabbatar idan yace zai buɗe baki yayi magana kuka ne zai kufce nasa koda
kuka bai kufce masa ba to Muryansa bazai fita.

Sake matsawa jikin gadon Dr Jameel yayi kana yace.

“Lafiya kuwa? Na tafi na Barka ɗazu lafiya kalau kuma yanzu tunda nazo kana kwance”.

Ya ƙara sa Maganar tare da taɓa wuyan zafi rau ya ratsa hannunsa.


Cike da kulawa yace.

“Subhanallah baka da lafiya ne?”.

Araunane Moddibo ya kallesa kana ya girgiza kai tare da cewa.

“Nima ban sani ba”.

Ya ƙare maganar cikin ruwar murya.

Da mamaki Dr Jameel yace.

“Kamar ya baka sani ba baza ka rasa sanin meke damunka ba mana?”.

Shiru Moddibo yayi yana murƙususu.

Ganin yanayin da yake ciki sai ƙaruwa yake yasa Dr Jameel cewa.

“Ko dai zamu tafi asibitine, kaga yanayin ka baki ɗaya jikin ka rawa yake ga zufa da kake fitarwa duk da
sanyin da ake”.

Still shiru Moddibo ya masa.

Dr Jameel kuwa hannu yasa tare da yaye blanket ɗin daya rufu ware idanu yayi ganin yanda *A* ɗin sa
ya miƙe kamar zai fasa wandon Jeans ɗin ya fito.

Dariya Dr Jameel ya fashe dashi harda riƙe ciki kana yace.

“Ashe dai bani kaɗai bane mayen matan, kaiɗin ma gashinan ka gaza haƙura, yanzu ka dubi yanayin da
kake ciki to kai me matsalar ka tunda ga mata an kawo maka zuwa anjima dai kuna tare”.

Hararansa Moddibo yayi kana yace.

“Kai fa ɗan Iska ne”.

Still Dr Jameel na dariya yace.

“Ƴan Iska dai zakace.

ai kai kam ma wa ɗan'nan shaiɗanun idanunka masu cike da shu'umaci sai ka casani, toh ni nama isa inyi
ko rabin abinda idonka ke nunawa ne ko amafarki ban isa in aikata abinda zaka aikata ba dan wlh in ka
ritsar ƴar mutane zata gane kurenta”.

Lumshe idanu Moddibo yayi tare da hararansa kana yace.

“Kamar yaya mene aikata? yanzu Jameel kai duk abinda kake aikatawa kace ko rabin abinda zanyi baza
ku aikata ba ko amafarki amman wlh ka cuceni?”.
Kai Dr Jameel ya jinjina tare da cewa.

“Sosai ma kuwa”.

Cikin yanayin gajiya da maganar da kuma feeling dake addabar sa ya miƙe dare da yin miƙa atake *A*
ɗin sa ya kuma miƙewa duk da wandon Jeans ne ajikinsa saida ya nuna.

Dariya Dr Jameel ya sheƙe dashi kana yace.

“Toh da ace baka da mata ne sai ince zan baka magani ko kuma In maka allurai dan wlh in ace zaka rayu
na wata ɗaya a haka Allah ne kaɗai yasa adadin matan da zaka danne.

to amma Alhamdulillah ba wannan duk cikin biyun tunda ga matarka nan shikenan nan magana ya
ƙare”.

Hararansa Moddibo yayi yana ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa.

Murmushi Dr Jameel yayi kana ya ɗage masa giransa tare da cewa.

“Kamayi Sa'a ɗazun na biya sashen Didi naji tana cewa gobe In Sha Allah za'a kai maka matarka sashenta
dama already an gama gyarawa”.

Hararansa Moddibo yayi kana ya wuce ya shiga toilet bayan ya fito suka tafi Sallah koda aka idar da
Maghriba basu dawo ba sai da akayi Isha'i.

Haka ya kwana baiyi bacci ba sai juyi yake saboda tsananin feeling da fitinar dake addabar sa baki daya
ya rasa samun nutsuwa da kwanciyar hankali da Zaran ya lumshe idanunsa zai tuna moment ɗin da suka
kasance a dining sai ya riƙa jin tafin hannunsa kamar yana yawo acikin nata wani irin azabebben tsuma
jikinsa keyi baki daya *A* ɗin sa ya takura sa a duk sanda ya tuna yadda take shafa hannunta bisa
sajenshi sai yaji kamar zai zauce...

Acan ɓangaren Khausar kuwa kwance suke a bedroom su uku Khausar, Asma'u sai Dije.

Juye-juye Khausar keyi tare da jan tsaki bini-bini zataja tsaki.

Ahankali Asma'u ta janyo wayarta tare da duba time taga 1:00am juyawa tayi ta kalli Khausar tare da
faɗin.

“Khausar ya dai?,Lafiya kuwa naga tun ɗaxu sai tsaki kike ba kiyi bacci ba?”.

Kai Khausar ta girgiza cikin sanyi murya tace.

“A'a bakomai”.

Ido Asma'u ta tsira mata tare da cewa.


“Ya zakice ba komai gashi tun ɗazu sai juye-juye kike”.

Lumshe idanu Khausar tayi kana tace.

“Da gaske bakomai kawai dai bacci be bai zo idona ba shiyasa”.

Kallonta Asma'u ta kuma yi kana tace.

“Amma kuma dai lafiyar ki ƙalau kam?”.

Kai ta jinjina tare da sauƙe numfashi tace.

“Lafiya ta ƙalau mana Asma'u”.

Ahankali Asma'u ta furta.

“Toh me ya ha naki bacci?”.

Cikin wata irin kasala da yanayin dake tsikaranta tun daga ƙwaƙwalwar kanta har zuwa tafin ƙafanta ta
fesar da numfashi tare da faɗin.

“Hmmmm”.

Sai kuma ta jawo Pillow ta kwanta tare da lumshe idanunta atake fuskar Moddibo ya bayyana acikin
ƙwayar idanunta lokacin da yake zubar da hawaye.

Kana ahankali ta shiga tuna moment da suka kasance jiya awajen taro daya rungumeta.

Ahankali taja dogon numfashi jin har zuwa lokaci ji take kamar ƙamshin na jikinta.

Runtse idanunta tayi da ƙarfi kana ta rungume Pillow da ƙarfi kamar yanda ya matseta alokacin.

Sake juyawa Asma'u tayi ta kalleta sai kuma tayi murmushi tare da cewa.

“Ko dai zan rakaki ɗakin Yah Moddibo ne?”.

Jin abinda Asma'u tace ne yasa ta buɗe Idanunta tare da kallonta tace.

“Kamar ya kuma ko zaki rakani ɗakin Yah Moddibo? Kefa kika ce Asma'u kin iya maganan banza? nifa na
faɗa miki bana son irin maganar nan, ke kuma yanzu so kike kinuna min gaba ɗaya yanzu kin zama ƴar
iskane ma”.

Gira Asma'u ta ɗaga mata tare da cewa.

“Rufa min asiri kar ki tara mana jama'a nagane kin kasa bacci sai juyi kike kina rungume-rungumen Pillow
nasan meyene matsalarki”.

Hararanta Khausar tayi da idanunta dake lumshe kana tace.


“Toh Ni bani da wata matsala”.

Dariya Asma'u ta sanya tare da faɗin...

*Masu son Maganin infection da maganin mata, ku marmatso wannan account no in ne naku ta ciki zaku
turo kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP
NUMBER'N na 09097853276. akwai sabbin kaya masu zafi suna nan bisa hanya, ki turo kuɗinki a saki
cikin lissafi. Kayanen mata masu zafi sadidan daga Chadi akwaisu Garukan daka, gumbunan,
Tsumummuka, cida Ciccibi Abodi cida kaza ci da jan nama kwanon ƙasaitacciyar mace biyar sirri, furar
mata, gumbar madara Gumbar kolli mai ƙyallin al'khairi gumbar uku al'khairi, gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, gumbar riɗi, garin maɗi garin melɗamhi garin ilanwaddihi garin mallaka, tsumin riɗi tsumin
tsirtai tsumin kinfi budurwa, tsumin riɗi, tsumin ta baje Sabaya, matsin maliƙi mai masifar matse mace
matsin daɗi har maɗiga, mai ɗan kare kyau. Kullacar sirri al'ajabu shu'umar Humra, da duk sauran kan
ƙamshi. Haɗin amarya budurwa ko bazawara haɗin mai jego ko uwar gida, akwaisu Available set ɗinmu
hawa hawane akwai manya akwai ƙananan, ƙanan daga 40k ne 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙarami
haɗina na karshe sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar shi 7k ne shine ƙarshen haɗina kenan... Manyan
set ɗin kuma daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k ke zaki faɗi haɗin nawa kikeso anyi miki kana kimin bayanin
yadda kikeso da matsalarki ni kuwa nasan abinda zan haɗa miki, ina araha kam amman ina hana bashi*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

52

“Ki faɗi gaskiya dai ko dai ko dai Magungunan _Aunty Aysha Aliyu Garkuwa_ sun fara aiki ajikin kine dan
naji yanda su Aunty Ruƙayya da Aunty Hajara ke tabbatar da kyau da inganci maganin”.

Khausar na gyara kwanciya tace.

“A kin manta ba aiki ba uban aiki suka fara”.

Dariya Asma'u ta sanya tare da faɗin.

“Toh bani na kar zomon ba”....


Cikin sauri ta juya baya tare da rumtse idanunta, tana maganar zuci. haba da gskyar Asma'u inaga harda
wannan tsume-tsumen ke ƙara gigitani gashi shima wannan Yah Modibbo duk ya hautsuna min natsuwa
da rikitattun idanunsa masu kashe jiki,

da haka bacci ya kwasheta.

Washe gari tun da safe akazo akafara shirya Khausar ahaɗa mata wannan ruwan ƙamshin da Zaran ta
gama ta fita za'a sake haɗa mata wani aƙalla sai da aka kusan haɗa mata kala bakwai zuwa dare.

kana aka koma na turaren hayaƙi da zai tsumata suma sun kai kala goma yinin wannan ranan haɗa ta
akayi wani irin Masifeffen ƙamshi take da Zaran ta tashi awaje ƙamshinta zai bule.

Yayinda tuni kuma an kai mata Set ɗin akwatinanta duk anje anjere a Side ɗin ta...

Bayan an idar da sallar Isha'i Jakadiya, Lalla Hafsat, Rahma ne suka shigo falon su Khausar yayin da
hannunsu ke riƙe da wata jaka abakin gado Lalla Hafsat ta ajiye kana ta juya ta kalli Khausar tace.

“Ya dai ƙanwata?”.

Khausar na murmushi ta sunkuyar da kanta tare da faɗin.

“Lafiya lau Aunty Hafsat ya gida?”.

Cikin sakin fuska tace.

“Alhamdulillah ya gajiyar biki da hidima mun kasa barinki ki huta ko?”.

Murmushi tayi batare da tace komai ba.

Tana zama tace.

“Kiyi haƙuri muɗin ne muna da yawan al'adu dan ma abin ne yazo ahaka an rage saura”.

Murmushi Khausar tayi akaro na biyu ta kuma sunkuyar da kanta.

Kallon Khausar dake wasa da yatsun hannunta tayi tare da cewa.

“Yanzu ki tashi Kije kiyi wanka in Sha Allah daga yau zaki samu ki kwanta kiyi bacci za'a kai ki Side ɗin ki”.

Ummi dake gefe tayi murmushi kana tace.

“Ai dai kam muna shan hidima”.


Dariya Lalla Hafsat ta sanya tare da faɗin.

“Ai dai kam biki ne na musamman Shiyasa baki ɗaya abubuwan komai na musamman ne”.

Kallon Khausar dake zaune Ummi tayi kana tace.

“Toh tashi Kije kiyi wankan mana”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da miƙewa tashiga toilet ɗin daya ƙawatu komai fes-fes gwanin ban sha'awa
kallon Bathtub ɗin da aka cikisa da ruwam haɗe-haɗen turaruka wanda tsaban turare da wasu
abubuwan sirri daya sha sai da ya koma Sky blue ga wasu jan Flowes masu masifar kyau da suka ƙawata
saman cike da farin ciki ta shiga tayi wanka bayan ta gama ta fito ɗauke da ƙaton Towel days sauƙa har
gwiwanta tana fitowa Lalla Hafsat da kanta ta ɗauki Hand-drayea ta busar mata da gashin kanta kana ta
ɗauki mayukan gashi masu kyau da turaren kai ta shafa mata su kana ta tufke mata su.

Bayan ta gama ta bata man shafawa tana shafawa a Fuskarta Lalla Hafsat kuwa da kanta ta tsugunna
tana shafa mata aƙafanta ahankali ta ɗago kai ta kalleta kana tace.

“Masha Allah wallahi skin ɗin ki yayi kyau Sosai”.

Sunkuyar da kai Khausar tayi ba tare da tace komaiba.

Miƙewa Lalla Hafsat tayi bayan ta gama shafa mata man ta miƙa mata wani tattausan Boxes irin na mata
mai masifar taushi wanda bai wuce cinyarta ba kana ta miƙa mata Brasseir tare da cewa.

“Ki shiga Corridor ki sanya”.

Kai ta gyaɗa tare da karɓa tashiga Corridor ta Sanya.

Bayan ta saka Lalla Hafsat ta zaro wasu riga da wando Farare sol acikin jakar masu masifar taushi da
santsi taushinsu ya wuce gaban kwatance tamkar jikin Mage haka suke.

Karɓa Khausar tayi ta saka.

Wani irin masifar amsarta kayan yayin da manyan Hips ɗinta suka baje aciki tamkar dan ita akayi su.

Kunya ce ta kama Khausar ganin yanda wanda ya kamata Hips ɗin ta suka baje aciki.

Wani Lifaya mai masifar kyau da taushi Jaa mai ratsin baƙi-baƙi kana shara-shara ne Lalla Hafsat ta
warware tare da naɗawa Khausar sosai Khausar tayi wani kyau na ban mamaki ga yalwataccen sumanta
da yasha gyara kana Lalla Hafsat ta jera mata wasu fulawowi masu kyau da tsari kana ta sa mata wani
siririn sarkan Gwal da ɗan kunnensa sirara marasa nauyi zaunar da ita tayi abakin gado kana ta miƙa
mata Kaskon turaren wuta.
Atake Khausar ta shiga baza ƙamshi kai kace A Company turare aka sanyata wasu turaruka kusan kala
biyar masu sanyin ƙamshi Lalla Hafsat ta kuma fesa mata.

Tana gamawa Rahma na shigowa idanunta akan Khausar tace.

“Wowww Masha Allah Lalla Hafsat kin yiwa ƙaninki shiri irin wannan tanadi duk Yah Aleey ake yiwa?”.

Murmushi Lalla Hafsat tayi kana tace.

“Ba dole ba ɗan ƙaninmu munefa mafi soyuwa a garemu ai dele mu nema masa farin cikinsa mutu masa
duk abinda zai sashi farin cikin duniya”.

Da sauri Khausar ta rumtse idanunta sani tsinkewar da zuciyarta tayi tare bugawa ya bada sautin bu-bu-
gum wani irin tsoro ne ya ka mata.

Matsawa kusa da ita Rahma tayi ta manna kumatunta dana Khausar tayi musu selfie.

Murmushi Khausar tayi wanda ya sake ƙawata kyawun fuskarta.

Cikin sakin fuska da ƙaunarta Rahma tace.

“Matar yaya dan Allah akular mana da ɗan Uwan mu asashi farin ciki akwantar mishi da hankali asama
mishi nutsuwa da jin daɗi”.

Ware idanu Lalla Hafsat tayi kana ta riƙe haɓa tare da cewa.

“Lalle Rahma yaushe kika fanɗare kika zama haka?".

Murmushi tayi tare da langwaɓar da kai kana tace.

“Ai gaskiya ne Lalla Hafsat ina faɗa mata ne ta kula da Yah Aleey saboda gwara ta sani shi ɗan gata ne
ɗan lelenmu ne muna sonshi fiye da yanda muke son kanmu”.

Khausar Kam wani irin tsinkewar zuciya da tsoro na ya mamaye zuciyarta.

Asma'u da bata wani daɗe da shiga ba ta kalli idanun Khausar cikin sauri ta ƙunshe dariyar ta.

Jakadiya ce ta kalli Lalla Hafsat kana tace.

“Hafsat kije ki duba kigani idan sun gama shiri sai muje mu kaita”.

Kai Lalla Hafsat ta gyaɗa tare da faɗin.


“Toh shikenan”

Kana ta fice ta sauƙa ƙasa kai tsaye Sashen dasu Moddibo suke ta shiga.

Zaune ta samu Ibraahim, Zakariyya, Dr Jameel suna zaune a falon.

Ibraahim na ganinta yace.

“My Aunty”.

Kafaɗarsa ta dafa tare da shafa sajen fuskarsa tace.

“Ɗan Uwana kaima gaba ɗaya abirkice kake agama dai kaima ka samu hutu kowa ma ya huta”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Ai bana ma jin gajiyar My Aunty saboda farin ciki na da kuma kwanciyar hankali na Inga komai na ɗan
uwana ya kan kama”.

Murmushi tayi tare da kallon Dr Jameel da yake faɗin.

“My Aunty kwana biyu”.

Murmushi tayi kana tace.

“Lafiya lau”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Ya jikin Rahma?”.

Tana gyara tsayuwar ta tace.

“Ai tunda kazo ka bata magani alhamdulillah jiki yayi sauƙi sai iyayi take zubawa”.

Numfashi ya fesar kana yace.

“Toh Alhamdulillah”.

Juyawa tayi tare da mayar da kallonta kan Zakariyya dake cewa.

“Ke Ni baza ki gaishe Ni bane?”.

Ware idanunta tayi tana kallonsa fuskarta ɗauke da murmushi tace.

“Wai kai kam ka manta nice babba akan ka wai?”.

Zamansa ya gyara yana murmushin yace.


“Ni duk shekarun da kike bani kura ya cinye sa”.

“Uyum yayi kyau”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“My Aunty nima fa naga Matar Aure acikin wa'annan ƴan Uwan Amarya”.

Dariya tayi kana tace.

“A'a Alhamdulillah barkanmu gauraye zasu ragu”.

Dr Jameel dake latsa wayarsa yayi dariya tare da cewa.

“Zako su ragu kam In Sha Allah ku shirya biki kam ma ina ga biyu zakuyi lokaci ɗaya”.

Cikin yanayin ƙaunarsu da sabo Lalla Hafsat tace.

“A lallai kam Masha Allah Abu yayi kyau”.

Kallonta ta mayar kan Ibraahim kana tare da faɗin.

“Ina Aleeyu?”.

Yana kallon ƙofar bedroom din yace

“Tun da muka dawo sallama Isha'i yana daki ko abinci ma bai ci ba”.

Da damuwa tace.

“Subhanallah lafiyarsa amma”.

Ajiyar zuciya Dr Jameel ya sauƙe tare da cewa.

“Wai baya jin daɗi ne”.

Cikin sauri ta nufi bedroom ɗin abakin ƙofa ta tsaya tayi sallama.

Jin Sallamar ta yasa Moddibo ya miƙe ya zauna agefen gadon kana ya amsa mata Sallamar.

Jin ya amsa yasa ta shiga kana ta tsaya agefensa tana kallonsa.

Ahankali ya ɗago kansa ya kalleta.


Tana gyara tsayuwar ta tace.

“Ya dai Aleeyu lafiya kam?”.

Kai ya gyara tare da faɗin.

“Um lafiya bakomai”.

“Kuma Dr Jameel yace min haka jin daɗi”.

Ta faɗa tana nazartan yanayin sa.

Numfashi ya fesar kana yace.

“A'a Lafiya ta ƙalau kawai gajiya ne na gaji ina so in dan huta ne”.

“Ayyah sannu In Sha Allah zaka huta yanzu tashi kashiga kayi wanka zan bawa Ibraahim kayan da zaka sa
zai kawo maka”.

Saurin kallonta yayi kana yace.

“Toh kuma yanzu ma wani abu za'a yi ne da sai an kawo min kayan da zansa na daban?”.

Kai ta girgiza tare da cewa.

“A'a ba wani abu kawai zaka koma Side ɗin ka inda zaka zauna ne saboda asama zaku zauna ɗaya gefen
da suke tunda Side biyu ne dan can aka shirya muku”.

Numfashi yaja tare da gyada mata kai ya rasa me yake tunawa aranshi ya kuma gaza gane yanayinma da
yake ciki.

Har ta juya ta fita ta isa bakin ƙofar ta tsaya tare da kallonsa ganin yana zaune tace.

“Dan Allah kayi haƙuri kayi sauri ka tashi ka shiga wanka”.

Kai ya gyaɗa tare da miƙewa ya shiga toilet ɗin yayi wanka.

Lalla Hafsat na fita ta kalli Ibraahim da suke hira kana tace.

“Yawwa Ibraahim zo muje ka karɓo masa kayan da zaisa.

Kallonta yayi tare da cewa.


“Ai Lalla Khadijah ma ta kawo kayan gasunan harda tsaraba waɗannan womers ɗin nace nakune ai a'a
kada mu taɓa na amarya da angone in mun tashi tafiya muje da dasu abincinsu ne”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe da faɗin.

“Yawwa Alhamdulillah dama inata tunanin kar an manta da girkin”.

Kana ta fice.

Ibraahim kuwa sai da ya dai daici Moddibo ya fito kafin ya miƙe ya kai masa kayan tare da faɗin.

“Yah Aleey ga kayan”

Karɓan kayan Moddibo yayi da mamaki ganin Jamfofine farare ƙal da gare irin na matasan zamani yayin
da yake ƙamshi ahankali yace.

“Wannan kayan fa daga ina?”.

Dariya Ibraahim yayi tare da cewa.

“Innayi ce wai tazo dasu tace duk ranan da zaka tare su zaka sa”.

Wani lallausan murmushi ya saki aransa yace.

“Ayyah Innayi kamar kinsan su nake bukatar sawa”

Anutse ya sanya kayan wani irin masifar kyau yayi na ban mamaki kamar asace sa agudu yayin da ya
ɗauki hula Sky blue da rastin fari yasa haka zalika takalmin ma Sky blue da rastin fari kyawun da yayi sam
bazai misaltuba...

Turaruka Dr Jameel ya ɗauka sun kai kala uku ya riƙa fesa masa.

Ahankali Moddibo ya kallesa tare da cewa.

“Wai kai kam mura kake son sakani?”.

Dr Jameel na cigaba da fesa masa yace.

“A'a gyaraka dai kawai zanyi dan kaji daɗin yanayin”.

Numfashi Moddibo ya fesar tare da faɗin.

“To ai turaren nan yayi yawa”.


Ware idanu Dr Jameel yayi yana cigaba da fesa masa yace.

“Waya faɗa maka ƙamshi yana yiwa Ango yawa aishi ƙamshinsa baya yawa”.

Falo suka fito Ibraahim ya ɗauki wayarsa yayi kira jin an ɗaga yasa yace.

“Ya kun gama kai musu kayan ne?”.

Daga ɗaya bangaren akace.

“Eh angama kai musu duk an shirya wa Moddibo nashi a Siff ɗinsa”.

Daga nan ya dauki wamers nan kana suka fito.

Ahankali suka fita suka fara haura step ɗin daya haura sama step ɗin ya rabu kashi biyu ɗaya ya kwanta
ta gefen dama ɗaya ta gefen hagu.

Gefen dama suka bi sunyi tafiya mai tsawo akan step ɗin daya kwanta kafin suka isa wani Corridor suna
shiga Corrido ƙofan farko Ibraahim ya buɗe ƙofan falon tare da cewa.

“Yah Aleeyu Bismillah ka ga Side din Auntyna ɗin”.

Masha Allah falone Mai masifar kyau da tsari kujerune set biyu ne Pinch and white ga wani madaidaicin
center table atsakiyar falon samansa anyi masa ado da wani glass Mai ƙayatarwa komai na cikin falon
Pinch and white ne wasu irin Cottons ne masu masifar taushi da sheƙi ajikin window haka zalika Karfet
dake malale ƙasan ɗakin shima Pinch ne da ratsin fari yayin da ɗakin ke fitar da wani sihirtaccen ƙamshi.

Sosai suka taba kyau da tsaruwan sashen.

Ibraahim na murmushi ya kalli Moddibo tare da cewa.

“Yah Aleey kai kuma ga naka agaba”.

Ya faɗa tare da nuna masa wani ƙofa dake cikin falon corridor wanda sai In dai zai shiga ko fita to dole
sai ya bi ta bakin ƙofar falon Khausar dun yayin da window bedroom ɗin ta ke gab da window falonshi.

Kana falonshi na ɗauke da 2 bedroom daga can Corridor kuma sauran window ne sai kuma wani 1
bedroom daga baya wanda wanda yake fuskantar ƙofar corridor bisa alamu ɗakin hadimai ne.

Suna shiga sahensa ya lumshe idanu komai na falonsa irin ɗaya ne dana falon Khausar Colour ne kawai
ya banbantasu danshi komai nasa fari ƙalll ne babu sirkin komai sai wani Masifeffen ƙamshi dake ratsa
hancinsu acan bedroom ɗinsa kuwa wani round bed ne da aka ƙawatashi da wani bedsheet fari sol mai
masifar taushi kana wani ma dai-dacin farin ƙyalle mai fasalin zuciya farine kal 🤍 sai dai gefen shi zagaye
yake da jan zare.
sai Siff daga can gefe bedroom ɗin ba wani tarkace amma yayi kyau na ban mamaki.

Acan ɓangaren su Khausar kuwa Lalla Hafsat Lalla Khadijah, Ashshe ce suka shiga bedroom din.

Yayin da Ummi, Hajiya Bunayya, Asiya, Innayi ke zaune Khausar na tsakiyan.

Ashshe ce ta riƙe Khausar tare da rufe mata fuskarta da Lifayan jikinta kana suka fita daga falon.

Cikin sauri Hajja Nana ta kalli Ashshe tare da cewa.

“Nima ɗin ai zanje”.

Dariya tayi tare da cewa.

“Kizo muje mana ai nan kusa ne”.

Anutse suka fita suka fara tafiya dake tsakanin da ɗan tazara sunyi tafiya kafin suka isa falon nata.

Suna shiga Falon suka fara yaba kyau da tsaruwan kowa na faɗin albarkanci bakinsa amma banda Hajiya
Bunayya dake ji kamar zuciyarta zai fasa ƙirjinta ya fita saboda baƙin ciki.

Kai tsaye bedroom ɗin dake gefen dama suka shiga ta tare da ajiyeta akan gadon.

Lalla Khadijah ce ta kira Ibraahim awaya akan suzo.

Cikin nutsuwa Ibraahim, Zakariyya, Dr Jameel suka rako Moddibo kai tsaye bedroom suka wuce bayan
sun gaisa.

Lalla, Hafsat Lalla Khadijah Aunty Ashshe suka bi bayansa zuwa bedroom din.

Ramaha suka samu tsaye kusa da Khausar dake zaune bakin gadon.

A hankali ta ɗaga wani dake take riƙe da shi abu kamar towel kamar ƙyalle Fari ne ƙall mai masifar
taushi sai ƙamshi yake zubawa yana naɗe cikin leda any wrapping ɗin sa kamar Heart warwareshi tayi
tare da shinfiɗashi tsakiyar gadon.

A hankali Ashshe tayi tayi masu nuni da hannu alamar su ƙarara shigowa ɗakin.

Ibraahim ne ya miƙawa Asma'u warmers dake hannunsa tare da cewa.


“Ayyah ɗan ajiyeshi a can”.

Ya ƙare mgnar yana nuna mata kan bedside durowa.

Amsa tayi tare da juyawa ta ajiye, yayinda gaba ɗaya idanunta ke kan Dr Jameel shima ɗin ita yake kallo
cike da sakin fuska yace.

“Ƙanwata ya gida”.

Lumshe ido tayi sabida hatta muryasa sak na M Jameel ne.

Ummi kuwa Moddibo dake gaisheta ta kalla tare da amsawa kana tace.

“Toh babana Allah ya sanya al'khairi Allah yayi yau dai kam mun gama cika wasiyar J ɗinka, gashi kuma
Allah yasa ka sake yin katari da mai kamanninsa kaga kenan Allah ya cike maka gurbin J dinka”.

Cikin wani irin sanyi mai cike da rauni Modibbo ke kallon Ummi amman ina ya gaza cewa komai.

Ita kuwa Khausar haka nan taji hawaye masu ɗumi na kwaranyo mata sai kuma ta fara sakin sassayyan
Shesh-sheƙan kuka mai ɗan sauti,

Baki Hajja Nana ta taɓa tare da cewa.

“Ni dai wannan kukan muna furcin ya isheni kecefa da kanki kikayiwa kanki zaɓi kika fito ido da ido kika
cemin Modibbo kike so in ba Modibbo ke ba wanda zaki aura, toh ai gashi an bakishi an aura miki an
kawo mishi ke sannan ki tsaida koke-koke gulma ai tunda kin samu wanda kikace kinaso mgn ta ƙare
tunda da bakinki kikacewa iyayenki Ni Modibbo nake to hike nan kuma gaki gashi”.

Tunda Hajja Nana ta fara mgnar Modibbo ke kallonta, sai dai jin kalmar da tai ta nanatawa cewa wai ke
kikace Modibbo kikeso.

Sai ya rumtse idanunsa da masifan karfi wani irin abu yaji zeeerr ya tsirga masa da can maɗigar kanshi
har zuwa kan babbar yatsarshi.

Wani irin amintaccen numfashi mai cike da yanayi na musamman ya fesar lokacin da yaji tana kuma
cewa.

“Tunda kin samu Modibbon da kike so kuma ai sai ki bar idanunki su huta”.

Yah Salam shine abinda ya iya furta cikin ransa sai kuma kalmar Ba kince Modibbo kike soba da yake ta
maimaitawa tamkar mai son haddace kalaman wani irin fitinenne tsalle zuciyarsa keyi da daurawa
domin kalmar tazo mishi a bazata wani irin aminci nitsuwa salama gamida yaƙini yake ji yana rufeshi.
Ita kuwa Khausar wani irin kunya haɗi da takaicin ne yasata sakin sassayyan kukan sabida yadda Hajja
Nana ta tsinkata gaban Modibbo, domin duk yayunshi sai murmushin jin dadi suke. Ummi kuwa kai
kawai ta jinjina dan lamarin Hajja Nana sai shiru.

cikin sanyi Innayi ta kalli Ummi tare da cewa.

“Ai Abban Jameel yace min in Sha Allah zai mishi dukan bayanin”.

Ita dai Hajja Nana ƙwaffa tayi tare da juyawa tana dube-dube ba tare da tace ko ƙalaba.

Zakariyya kuwa cikin sanyi yace.

“Lalla Khadi mufa zamu tafi”.

Cikin sauri ta kalli Modibbo tare da cewa.

“Bismillah a buɗe fuskar amarya, taga ɗakinta”.

Haka nan shima kanshi yakejin yana son yaga fuskarta, a cikin wannan yanayi da har yanzu yake
mamakin ya akayi aka aura mishi ita.

Ashshe ce ta kamo hannunsa tare da matsowa kusa da Khausar da shi ɗin kana mishi alamun buɗe.

Wani irin sassayyan numfashi ya fesar tare da sunkuyowa yaje buɗe fuskar ta.

Wani irin lumshe idanunsa yayi atake yaji bashi da buri da yawuce ganin kyakykyawan fuskanta saboda
hango ƙafafunta daya sha jan lalle da yayi ganin yanda sukayi masifar kyau lalle ya amshi ƙafarta.

Ahankali ya ƙara sunkuyowa kanta tare da shaƙan daddaɗan ƙamshin da take sai kuma yasa ya tsunsa
biyu ya ɗan ƙara daga Lifayan atake kyakykyawan fuskarta ya bayyana ras a gabanshi

Juyawa yayi tare da kallon Lalla Hafsat kana yai musu alamar gashi ya buɗe.

Ibraahim dake tsaye ya miƙa masa Bounch na kuɗi alamar ya mata liƙi.

Cikin nutsuwa ya karɓa kana ɗaura mata shi kan cinyata tare da ɗan kauda fuska murya can ƙasa yace.

“Ibraahim ne yace a baki”.

Ya ida maganar yanayi mata wani irin fitinennen kalo daya sa kasala rufeta.
Yayin da Asma'u keta faman yi musu video tana murmushi.

Shi kuwa a hankali ya ɗan tashi tsaye.

Lalla Hafsat ta janyo ta tare da miƙar da ita tsaye.

Tana tsayuwa akan ƙafafunta Lalla Hafsat ta bashi wasu Bounch ɗin kuɗi alamar yayi mata liƙi.

A hankali yasa hannunshi ya amsa tare da fara yaryaɗa matasu tamkar ruwan sama.

Ibrahim Asma'u kuwa sai hotuna sukeyi musu.

Rahama kuwa wani turare mai sassayan kanshi ne ta fara fesa musu mai fidda zaren furanni masu color
daban daban.

Ashshe ce tayi musu alamun su fita tare da cewa.

“Allah ya baku zaman lafiya da zuriya ɗaiyiba”.

Haka yasa gaba ɗaya suka haɗa baki wurin cewa.

“Amin Amin”. Kana duk suka fito a tare.

Ita kam Khausar bata san me suke cewaba, bare tasan sun fita.

.shi kuwa Modibbo sautin Shesh-sheƙan kukanta ne ke ratsa kunneshi so bai barshi yaji mgnar suba bare
fitansu, sai sautin rufe ƙofar ne da yaji ya ɗan sashi juyowa ya kalli ƙofar, tuni an rufe ƙofar bisa alamu
duk sun tafi.

Su kuwa hakanne duk sun fita, Lalla Khadijah ce karshen fita falon bayan ta kashe wutan falon kana taja
ƙofar ta fita ta bi bayansu.

A corridor ta samu Kalla Hafsat na jiranta suna fita sukaja ƙofar corridor suka rufe wacce bata sai ta ciki
sai in da key a hannun mutum ko ƙasa pin ɗin ƙofar .
A can cikin ɗakin kuwa, wani irin maraitaccen kuka Khausar keyi mai sassayan sautin da ya fara kashe jiki
da ruhi da dukkan gangan jikin Modibbo.

Yayinda kalaman Hajja Nana keyi minshi yawo akunne zuwa tsakiyar kai tamkar busan sarewa.

Wani irin fitinennen rauni hadi da kasalance sukayi mishi rudugun da yasa bai san lokacin da ya ware
hannunshi tare da buɗe garen jikinsa dake baza sassayan ƙamshi, a hankali ya jawota jikinsa tare dayi
mata wani irin sahihin rugguma dayi mata ƙawanya da garensa kana ya bata Kekkyawan masauƙi da
ƙirjinsa haɗin dayi nata cikekken GARKUWA da hannayeshi ya matseta tsam a cikin jikinshi....

*Littafin Sakayya dai na kuɗi ne yar uwa ki biya in tura miki littafin ki karanta cikin aminci da salama ba
haƙƙin kowa aka ki, 1k ne fa kacal 0661110170 Gtbank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min evidence inki
ta Whatsapp no na 09097853276, in tura miki littafin Kisha karatun ki.*

*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n
nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai
sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan
mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in
kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a
banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account
no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na
faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki
kenan*

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.
KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito
miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar
infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita
tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a
saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda
yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin
san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo
kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki,
domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan
ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah
zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce
dai GARKUWAR MA'AURATA.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

53

*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n
nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai
sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan
mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in
kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a
banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account
no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na
faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki
kenan*

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito
miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar
infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita
tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a
saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda
yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin
san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo
kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567 ko kuma ta wannan 09097853276
sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho,
ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum
24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari
sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA'AURATA.

53

A hankali ya ɗan sunkuyo kanta, tare da cusa kanshi tsankanin wuyanta da kafaɗarta, wani amintaccen
numfashi mai haɗe da zazzafan shauƙi ya shaƙa, sai kuma ya ƙara ruggume ta da karfi, saboda jin
numfashinsa na gab da yankewa ya bar gangan jikinsa, wani irin tsuma naman jikinsa keyi tamkar wanda
aka jonawa wutar nepa, lokaci ɗaya lips inshi suka fara tattarewa tare da fara rawa.

Ita kuwa Khausar, jin yadda yake fuzgar numfashi, tare da ƙwaƙumeta ne, ya ƙara ta azzara ido cike da
tsoronshi cikin zuciya da jikinta, hannunta tasa bisa ƙirjinshi tana ƙoƙarin tureshi, tare da sakin Shesh-
sheƙan kuka, mai nuni da tsananin tsoronta a fili.

Can cikin duniyar da ƙamshin turaren ta, ya jefa shi ya fara jiyo, Shesh-sheƙan kukanta, murya cike da
tsoro rauni kana muryar na rawa tace.

“Wayyo Allah Mommy na, sun tafi sun barni ni kaɗai, ba'a barmin kowaba”. Sai kuma ta fashe da kuka
jiki na rawa taci gaba da tureshi cikin muryar kukan taci gaba da cewa.

“Dan Allah ka sakeni, numfashi na zai dauke”.

Sai kuma ta fashe da raunataccen kuka mai nuni da tsananin tsoronta da kuɗawa da kuma raunin dake
tabbatar da cewa daga can ƙasan zuciyarta kukan ke fitowa.

Wani irin mataccen numfashi yaja da masifan ƙarfi, kana ya samu ya fesar da numfashi a hankali yayinda
jikinsa ya saki wani irin rawa tamkar mazari wanda hakan yasa baisan sanda ya saketa ba.

ita kuwa Khausar jin ya saketa ne, yasa ta naje jikinta, ta koma bakin gadon ta hau ta zauna, tare da
takure kanta wuri ɗaya, kana ta kife kanta bisa guiwowinta tana mai sakin maraitaccen kuka, mai cike da
raunin da dole ya haifar da tausayinta ga duk zuciyar wanda kunnensa yaji sautin kukan, cikin sassayan
sauti mai cike da rauni take kukan gami da yin mgnar da har zuciyarta take faɗin.

“Yah Jameel na, cika maka wasiyarka, cikin rashin sanin cewa wata duniyar da bani da kowa za'a kawoni
a wurgar dani, kamar ba'a sona, an nesantani da Mommy na da Raudat.”
Shi kuwa Modibbo zuwa yanzu, sawunshi sun fara gaza ɗaukan nauyin gangar jikinsa da hakan yasa.

Dole yaja kafafunshi da ƙyar ya jingina da jikin wodurob, yayinda ya kife kansa, da jikin durowar, tare da
sa haƙoransa na dama, ya taune gefen lip inshi na ƙasa.

Kusan tsawon 21 minutes suka ɗauka a haka, amman madadin yanayin da yake ciki ya ragu sai ma
ƙaruwa da yakeyi, wanda hakan ne ya tilasta mishi juyowa, ya kalli Khausar ɗin da zuwa yanzu ta koma
yin kukan ƙasa-ƙasa bisa alamu bacci ne ya fara surarta a haka.

Wani irin kallo mai tafiya da dukkan nitsuwarsa Yake Binta dashi, tun daga kan yatsun ƙafanta da suka
sha zanen lalle har zuwa kanta da mayafin laffayan ya zame ya ɗan sauka ƙasa.

Wani irin sheƙi da ƙamshi gashinta ke zubawa, wanda ya haddasa mishi jin wani irin miƙewar tsikar
jikinai baƙi ɗaya.

Sai kuma ya ƙara ware idanunshi da suka koma kalar hazo, bisa fuskarta jin taja dogon ajiyan zuciya da
ya tabbatar mishi da tayi bacci.

Ajiyan zuciya mai nauyi ya fesar tare da yin wani irin fitinennen miƙar da yasa M ɗinshi miƙe iya tsawon
da Allah ya halitta masa.

Wani irin tsaki mai sanyi yaja, cike da takaicin yadda wannan abu nashi yake addabar rayuwarsa da
rashin haƙuri.

A hankali yasa hannunsa ya ɗauki wayarta da Asma'u ta ajiye mata a bakin gadon.

Cikin wahaltaccen ya juya ya nufi ƙofar fita.

A bakin ƙofar yasa hannun ya kashe wutan ɗakin kana ya fara takawa a hankali domin karkarwa da
jikinsa keyi,

“Yah Salam”. Shine abinda ya iya furta a saman lips inshi sabida jin gaba ɗaya gangan jikinsa yana
sakewa, dai-dai lokacin da ya iso tsakiya falon, wanda yake mamaye da duhu, bisa alamu, tun fitansu
Lalla Khadijah ne suka kashe wutan falon.

Wayarta da ya ke cikin a'jihunsa ya zaro lokacin da yaji ya tafi ƙasa ya gaza tsayuwa, sabida wani irin
fitinennen damƙa da mararsa tayi haɗi da harbawa.
Da kyar ya isa ɗan haska fuskar wayar, sai kuma ya kife wayar bisa kujerar da ke gefenshi kana shi kuwa
ya miƙe plat a tsakiyar falon bisa tattausan Marocco Carpet Wanda a jikinsa ke tube MRS Aleeyu
Youseep Mouleey din.

Wani irin tsuma da karkarwa jikinsa keyi tamkar mai cutar zazzaɓin da ke sa sanyi.

A can Side dinsu Asma'u kuwa.

Ita da Dija da Ummi dake waya da Mommy ne, bisa gada.

Cikin sanyi Ummin ta ɗan fesar da numfashi tare da juyowa ta kalli inda Asma'u da Dija ke kwance kana a
hankali tace.

“Uhmmm ke dai bari Mommyn Khausar wlh Ni kaina, tunda muka dawo kai Khausy side ɗinta na gaza
bacci, gaba ɗaya ita nake tuna, abinda baka san wahalarsa, bare da yanayin ƙarancin shekaru in dai an
haɗa da na Modibbo ai Khausar yarinca tunda dudu fa yanzu suka cika shekaru sha tara.”

Cikin fesar da numfashi Mommy dake zaune bakin gadon tace.

“Wallahi kuwa Ummin Jameel, gaba ɗaya na kasa rumtsawa, bare ɗazu dana kirata, kuka tai ramin tana
magoya wai dan Allah in roƙeki a bar mata Asma'u, itafa bata san kowaba a garin.

Wai da nace mata ai kowa da haka yake sabawa, sai cewa tayi. Mommy kamar bakya sona, kin san haka
za'ace za'abarni ni kaɗai shine baki bani Raudat”.

Cikin sanyi Ummi tace.

“Ba komai in sha Allah, wlh Aliyu bazai tozarta zaɓin Jamilu naba, koda kuwa ace baya sonta, barema
wlh Mommyn Khausar iyayen Modibbo masu mutumci ne, barema kuma ai zamu bar Innayi anan".

Cikin rauni da tausayi irin na iyayen a dararen da suka san an kaɗai ta yarsu da mijin aurenta, Mommy
tace.

“Kayya Ummin Jameel wani sabawa ne, Khausar tayi da Innayi”.

Cikin bada ƙarfin guiwa Ummi tace.

“In sha Allah ba komai sai al'khairi”.

A hankali Mommy tace.

“Ɗazu muna waya da Haiydar ke cemin, wai ranar Jumma'a zaku dawo ko?".

Cikin sauƙe numfashi Ummi tace.


“Eh haka dai Abban Jameel ke cemin, amman shi Abban Jameel zai ɗan zauna sabida yanzu dole shi zai
tsaya yayi aikin da ya turo Aliyun yayi. Kuma yacemin sune suka shirya komai na tafiyar namu, sun
hanashi kashe ko asi”.

Cikin sanyi Mommy tace.

“Wato dai ya tabbata zaku dawo ku barmin Khausar na, can ita ɗaya, Khausar da shegen tsoro ace an
barta a ƙasar da bata da kowa nata, da mijin da sonta yake ba, ko ya rayuwa zata juya mata, wlh Ummin
Jameel wannan abufa yana damuna, dama ace Modibbo shine yace yana sonta da bazan shiga damuwa
sosaiba”.

Cikin sanyi Ummi tace.

“Wallahi kada ki damu Khausar fa, ta samu karɓu sosai a masarautar Mouley”.

“Uhmm Toh Allah ya dawo daku lafiya”.

Mommy tace kana daga nan sukayi sallama.

Sai kuma ta miƙe ta shiga Bathroom tayi al'wala kana ta fito ta fara Nafila tare da roƙawa Khausar ɗinta
samun aminci da konciyar hankali.

Ummi ma nafilan ta fara

Yayinda can cikin masarautar Mouley kuwa a side ɗin Didi.

Cikin sanyi Lalla Khadijah ta kalli Aunty Afreen wacce take ƴar Didice.

Cikin sanyi tace.

“Aunty Allah dai yasa ɗankun nan, ya bar ƴar mutane ta sarara, ta samu ta huta, domin na lura shi ɗin sai
a hankali”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Ina ruwanki mutum da matarsa in banda sa ido”.

Dariya tayi tare da leƙa idon Lalla Hafsat da ke cewa.


“Gsky dai kam, Allah yasa ya barta, kinfa san in bai barta ba, muma ba hutawa za muyiba da wannan
tsaraɓe-tsaraɓen al'dun wannan masarautar Mouley munnan, ni har ga Allah abin kunya yake bani da
takaici”.

Cikin sauƙe numfashi Afree tace.

“Idan dai har ya kasance kamar kakanshi mahaifinmu to, babu shakka zai gyara muku masarautarku duk
randa ya hau karagar mulki zai rabaku da duk wasu bauɗaɗɗun al'adu ya fuskantar daku addini, kamar
yadda Sheykh Jabeer yayi gyara masarautar Joɗa”.

Cikin sauke numfashi Lalla Hafsat tace.

“Allah yasa haka”. Da Amin suka amsa, kana ita sukaci gaba hirarsu.

A can Side ɗin Khausar kuwa, cikin wahalallan baccin da takeyi a takure wanda ya jaza mata nauyin
ƙirjine, ta ɗan mirgina sabida takuranda taji, cikin akasi tayi ƙasa rib kasan cewar a bakin gadon take.

Cikin wani irin raɗaɗin da ya game guiwowinta da suka sauƙa gib kan tayis ɗin ne, ta buɗe idanunta da
sauri sai kuma ta sake rufesu da ƙarfi, tare da faɗin.

“Innalillahi wa innalillahi raji'un”.

Sabida ganin duhun daya mamaye ganinta, cikin gigita haɗi da kiɗima, ta miƙe tsaye tare da fara laluɓe-
laluɓe tana kuma faɗin.

“Na shiga uku, innalillahi ba kowa ne a nan, wayyo Allah Ummi”.

Ta ƙarasa kiran Ummin da ƙarfi.

Sai kuma tayi saurin juyawa jin yadda ta buge kanta da jikin gini.

Kuka mai cike da tsoro ta saki tare da ci gaba da lalubawa, jin hannunta jikin labulena yasa tayi saurin
yaye labulen, wanda na window ne, buɗe labulen da ta ɗanyi ne yasa ta ɗan samu hasken dake cikin
correct ya ɗan haska ɗakin, da sauri ta juya ciki tana laluba ta inda wutan yake, amman ina bata ganoba
sai dai tayi kamari da ƙofar fita, haka yasa ta fita da sauri, yayinda laffayar jikinta ke ja da ƙasa sabida ya
warware.

Shi kuwa Modibbo tun farkawarta yaji muryarta, da motsinta, sai dai bashi da dama ko iko da ingin
motsawa.

Sai karkarwar da jikinsa keyi daya ƙara tsananta. Hannunsa duka biyu ne, dafe da mararsa yayinda lips
inshi suke rawa tamkar wanda aka cilla cikin dusar ƙanƙara, sabida rawar da ya tsananta har haƙoransa
na dukan juna suna bada sautin gat-gat-gatt.
Ita kuwa Khausar da sassarfa ta fito falon, tana mai dannawa Ummi kira.

Dai-dai lokacin da ta iso tsakiyar falon kusa dashi laffayar ta zame tayi ƙasa ya harɗe sawunta da sauri ta
daga ƙafarta da nufin ta zare samu ta cikin akasi kuma tayi tuntube da Modibbo dake kwance tsakiyar
falon.

Luu ta tafi ta faɗa kanshi, ba zato ba tsammani ta jita bisa ruwan cikin mutum.

Ihu ta kurma da ƙarfi, wanda har saida Ummi dake Nafila ta jita, cikin sauri ta rumtse idanunta dan a
zatonta, Modibbo ne ya rutsa Khausar ɗin a fili tace.

“Kai yaran zamani ka barta ta huta mana ko na mako ɗaya ne, ka bita a hankali”.

Ta kare mgnar cikin yin ƙasa da murya da kuma ci gaba da tasbihinta.

Shi kuwa Modibbo cikin tsakin gigitan yanayin da yake ciki ya jawota jikinshi tare da ruggume ta da
masifan karfi.

Yah Salam wani irin karkarwa Khausar ta farayi kamar wacce za'a zarewa rai da ƙarfi ta daddage da nufin
kurma wani ihun, sai kuma ta zazzaro idanunta waje, jin yasa tafin Hannunshi na dama ya rufe bakin
nata.

Jin yadda take karkarwa da fesar da numfashi kamar mai shirin shiɗewane yasashi ɗan buɗe mata bakin.

Cikin sassayan murya ya buɗe baki murya na karkarwa yace.

“Meyasa baki da nitsuwa ne? Ki nitsumana!”.

Cike da razani tasa hannunta ta ɗan riƙe hannunsa tare da cewa.

“Waye ne kai ɗin?”.

Cikin fuzgo maganar a hankali yace.

“Nine”.

“Kai waye ɗin?”.

Cikin Lumshe ido yace.


“Mijinki ne Aliyu”.

Wani irin dogon numfashi taja mai gwaraye da tsoro da kuma sassauci murya a sarƙafe tace.

“Moddibbooooo”. Cikin wani irin sabon ruɗanin da muryarta da ɗumin jikinta ya jefa shi ne yace mata.

“Uhhhhhhhmmmmmm”.

Cikin sauri ta janye jikinta daga gareshi ya koma gefe kana murya a sarƙafe tace.

“Dan Allah ka tashi ka maidani wurinsu Ummin”.

Hannunshi yasa ya lalubo wayarta da ya kife bisa kujera, cikin sanyi ya danna hasken fuskar wayar,
wanda haka yasa Khausar sakin sassayyan numfashi.

Shi kuwa cikin karkarwar da jikinsa keyi ya yunƙara da kyar ya miƙe zaune, tare da kunna tocin wayar
kana ya ajiye, tare da zuba mata fitunannun idanunsa da suka sirance.

Da sauri tace.

“Dan Allah kayi haƙuri ka tashi ka kaini”.

Cikin sanyin murya dake can ƙasan maƙosjinsa yace.

“Ce miki akayi ni ɗan rakiyarki ne, ko ɗan aikenki”.

Da sauri ta turo baki tare da cewa.

“Toh Wlh ni dai bazan kwana a nan ba, cikin duhu”.

Da hannunshi na hagu yayi mata alamun ga hanya ai ki tafi mana.

Hannunshi na dama kuma Al'kebbar jikinsa ya gyara tare da rufe cinyoyinsa.

Ita kuwa cikin sanyi tace.

“Ai tsoro nakeji fita ni ɗaya”.

Kanshi ya sunkuyar ba tare da yace mata kimaiba sabida ganinta cikin shigar tayi masifar zaburar dashi.

Ita kuwa Khausar can gefe ta koma ta tsaya tana tura baki tare da mgna ƙasa-ƙasa.
“Wallahi babu inda su Ummi zasu tafi su barni a nan ƙafarsu ƙafata”.

Sai kuma tayi shiru jin, an kwaɗa kiran sallan forko a matsallacin Masarautar, sassayan numfashi ta fesar
tare da cewa.

“Alhamdulillah”.

Shi kuwa Modibbo cikin ɓoye yanayin da yake ciki ya yunƙura ya miƙe tsaye tare da ɗaukar wayar tata,
kana ya nufi hanyar fita da sauri tace.

“Ka bani wayata”.

Ba tare da ya juyo ya kalleta ba yace.

“Kina da ƙarfi ai kizo ki ƙwata”. Ya ida maganar tare da ficewa.

Yana shiga bedroom ɗinshi kai tsaye bathroom ya wuce, ruwan mai ɗan zafi ya sakarwa kansa daga
bisani yayi al'wala kana ya fito tare da kmtsawa cikin wata tattausar jallabiya baƙa mai ɗan karen taushi,
turare ya fesa, kana ya fara nafila.

Ita kuwa Khausar yana fita, ta kunna watan falon da sauri, kana ta shiga Bathroom dake falon tayi
al'wala, laffayan ta naɗa a jikinta sannan ta fara nafila bisa Carpet din, jin an kira assalatune yasa tayi
rak'atsinil fajir, kana rai ta tasbihi.

Shi kuwa Modibbo jin anyi assalatune yasa ya miƙe tare da ƙara fesa turaren ya fice zuwa masalaccin.

Jin an yada iƙamane kuma yasa Khausar miƙe itama takabbarta.

Bisa jagorancin Modibbo akayi salkan.

Koda aka idar da salla Modibbo bai tashiba hakama Ibraahim da Abualeey da kuma da yawa cikin
manyan fada wasu karatun qura'an sukeyi wasu tasbihi.

Saida lokacin fitowar rana yayi kana suka riƙa yin nafila raka'a bibbiyu kamar yadda Manzon Allah ya
kwaɗaitar damu, hadisi ne sahihi cewa duk wanda yayi sallan asuba, yaci gaba da zama'a wurin har rana
ta fito kana yayi nafila raka'a biyu toh yaba da ladan aikin hajji.
Bayan sun fito daga cikin masallancin bisa umarni da jagorancin Abualeey da Ibraahim da Sarkin fada da
su Galadima Waziri, Wambai, Ɗan Maliki Dan Muram, da dai sauran, aka rinka yagayawa dashi ana nuna
mishi lungu da saƙi na masarautar kofa-kofa Part-part haka aka rinƙa kaishi ana nuna mishi ƴan uwa da
abokan arziƙu.

Daga ƙarshe suka shiga part ɗin da yafi kusa da na Didi wanda nan ne Part ɗin ƙanin Abualeey wanda
baida lafiya tsawon shekaru anyi neman mgnin duniya an gaji an zubawa sarautar Allah ido.

Daga bisani suka shiga part ɗin Niyna anan suka yada zango suka sha tea ƙarfe tara da kwata dai-dai suka
fito, daga nan kuma part ɗin Didi suka shiga.

Shi da Abualeey da Ibraahim, yayinda duk sauran kowa ya nufi gidansa.

Suna shiga suka samu sau Lalla Khadijah a falo.

Kusan a tare suka haɗa baki wurin gaida mahaifin nasu, zama shi ya gyara bisa kujerara kana ya kalli
taron ƴaƴan nashi.

Murmushi yayi jin Lalla Khadijah na cewa Modibbo.

“Ango mai jiran gadaje biyu na sarautar Mouley dana amarya.

Kanshi ya ɗan kauda gefe ba tare da yace komai ba sai ɗan gudun murmushin gefen baki da yayi, sai
kuma ya kama hannun Hakim tare da cewa.

“Meya hanaka zuwa masallaci”.

Ibraahim ne ya ɗan mari ƙeyar Hakim ɗin tare da cewa.

“Baccin banza mana, in ya samu Game sai ya kai karfe biyun dare yana abu ɗaya”.

Cikin tsuke fuska yace.

“Daga yau kada in sake zuwa Masallaci ban gankaba”.

Cikin jin daɗi duk suke kallonsa,

Shi kuwa Hakim cikin jin shakka da ganin kwarjin Modibbo yace.

“In sha Allah bazan ƙaraba Unclee Aleyyh, kuma dama in a gidane wlh kullum da Abbana muke zuwa
Masallaci ka tambayi Mom kaji”.

Da sauri Lalla Khadijah tace.

“A'a ba ruwana ni bazanyi shaidar zurba”.


Shi kuwa Modibbo a hankali ya kalli Rahama da Didi da suka fito yanzu Hannu Didi ta miƙa mishi alamun
suyi muhabaha, murmushi yayi cike da jin kaunar ta a ranshi ya miƙa mata hannun.

Cikin so ƙauna kulawa ta kalleshi, sai kuma ta kalli gefen hagu da damanshi, cikin yanayin zazzafan
shaƙuwa dake shiga tsakaninsu yayi mata kallun alamun.

“Me kike nema".

Ɗan matse hannunsa tayi tare da cewa.

“Naga banga ƴata ɗaya bane a nan ɗin. Ina ka baro min ita?”. Ciki ware manyan idanunsa yace.

“Didi bansanta ba”.

Kusan a tare duk sukace.

“Matar takace baka saniba”.

Sai kuma ya kalli Abualeey da yace.

“Ayi mishi uzuri yau dai kam, dan daga Masallaci muka wuce zagaya fada, wata ƙil shiyasa bai taho da
itaba”.

Cikin ɗan tsare fuska Didi tace.

“Toh maza tashi kaje ka taho min da ɗiyata, yanzu-yanzu”.

Cikin karya wuya yace.

“Didi Rahman t..."

Da sauri ya katseta da cewa.

“Tashi maza kuje, Ibraahim nuna mishi hanyar tsakiyan nan”.

Toh Ibraahim yace kana ya miƙe yayi gaba.

Daga nan cikin falon Didi suka bi cikin wani dogon corridor mai faɗi.

Tafiya mai ɗan tsawo sukayi, yaga sun ɓullo, ta kan steps nan da zai sadasu da saman kuma basubi, cikin
babban falon nan ba.

Cikin sanyi Ibraahim yace.

“Ga hanyar dake tsakanin ka da Didi, ni inda ka zauna ɗinnan nanne Side ɗina, sai kuma ta gefen nan
akwai hanyar da zaku fita ba sai kabi cikin falon nanba, tana ƙofar part ɗinka yake, ko da mota zaka fita
ranan gate ɗin ka yake”.
Cikin gamsuwa Modibbo ya gyaɗa mishi kai.

Shi kuwa Ibraahim fara sauƙa yayi ta hanyar da zata sauƙa dashi ta cikin falon yana mai cewa Modibbo.

“Nima bari inje in ɗanyi wanka kafin ku fito”.

Kai kawai Modibbo ya gyaɗa mishi kana ya wuce cikin corridor insu kana ya maida ƙofar ya rufe.

Khausar kuwa tunda tayi sallan asuba ta kwanta a nan a falon tai baccinta, sai ƙarfe tara dai-dai ta farka
tana tashi kuwa ta shiga wonka.

Dai dai lokacin yake haurowan kuma khausar ɗin ke tsaye gaban dressin mirror cikin wata chiga ta
al'farmar da alamun yanzu ta fito wanka ta kuma fesa kolliya.

Ɗinkin doguwar rigar Getzener ce maroon color mai masifar maiƙo da sheƙi, an yiwa rigar aiki da zaren
Golden color mai ɗan karen sheƙi, sai rashin fari, da kuma yellow da blue kaɗan-kaɗan wanda daga ƙasa
zuwa tsakiya ne aka watsa tsaren da salon jelar ɗawisu, daga sama kuwa wasu irin duwatsun karaine
masu masifar ɗaukan ido aka watsa a jiki wanda suka kuma an jerasu kamar tsarin gashin ƙirjin ɗawisu.

Cib-cib da jikinta rigar tayi wacce har ta ɗan matseta daga saman ƙirjinta da ƙasan mazaunanta da suka
fito hani'an.

murza ɗaurin ɗan kwalin turban tayi ya zauna ras yayinda daga tsakiyar ɗan kwalin ta baya ta fito da
jelam gashinta, wanda bata kitseshi ba.

Ƴan kunnen da sarƙa na gold masu ƙaramin nauyi tasa, sai kuma zobe.

Fuskar ta ta kalla a madubin, sai kuma ta tura baki, ganin har yanzu idanunta na ɗan kumbure kaɗan,
yayinda ƙasansu dai-dai inda akesa kolli yayi ja, kamar dai kollin jambaki, hannunta tasa ta ɗauki ɗaya
daga cikin hodar da aka jera mata a gaba dressin mirror, sai kuma ta maida ta ajiye tare da tura baki
kana tace.

“Ba kollinyan da zanyi ma, harshenta, ta ɗan sa ta lashi pich lips inta, sai kuma dai ta ɗauki man bakin ta
ɗan goga a yatsarta ma nuniya kana ta ɗan murza yatsar kan lips inta, wani irin sheƙi suka fara kamar ta
samusu jambaki.

Turare kawai ta fara fesawa.

Shi kuwa Modibbo a hankali yake takawa har ya iso, dai-dai bakin ƙofar falonta, ƙofar na buɗe amman
kuma ba kowa, sai tv data kunna ana karatun qura'an.

Wucewa yayi ya shiga falonsa, kai tsaye Bathroom ɗinsa ya shiga, ya shiga wanka.
A Side dinsu Ummi Innayi kuwa Ummin Jameel ce ke waya da Mommyn Khausar cikin ɗan yin ƙasa da
murya tace.

“Wallahi nima tun ɗazu nake kiran wayarta yana shiga amman bata ɗagawa, na rasa ma ta ina zan fara
na kirata yafi sau shida”.

Wani irin numfashi tausayi Mommy taja kana cikin sanyi tace.

“Ni nayi mata kira yafi goma, yanzuma saida na kira bata ɗayaba, Ummin Jameel kiyi ƙoƙarin zuwa inda
take”.

Da sauri tace.

“Ok ba matsala in Sha Allah yanzu zanyuwa innayi mgnar”.

Daga nan suka katse kiran kana ta juyo ta kalli Innayi tare da cewa.

“Innayi ko zamuje wurin Khausar? Tun ɗazu muje kiranta bata ɗagawa”.

Murmushi Innayi tare da cewa.

“Ai in da buƙatar zuwanmu sashinta Jakadiya zata sanar mana.

Yanzu babu mai zuwa inda take, kuma itama ƙofar Didi kawai zataje, shima dan wannan zuwan shine
madubin da za'a gane cewa, ya ta kasance tare da mijinta, kuma in akwaida abinda ya faru za'a nemu.
Kiranta kuwa bari zuwa anjima ku sake gwadawa”.

Innayin ta kare mgnar a dungule, wacca kuma tuni Ummi da Aunty Rukayya sun gane ma take nufi.

Haka yasa Ummi sauƙe numfashi kana ta kira Mommy ta ɗan kwantar mata da hankali toh kawai
Mommy tace amman taci gaba da kiran.

Nigeria

Abuja, cikin Maitama. Amina da Unclee Naseer tsaye a bakin falonsu, bisa alamu fita zaiyi, cikin
salo na musamman, ya ɗan jawota jikinshi tare da ruggume ta cike da yaudara yace.

“My Dear Kada ki damu bazan daɗeba zan dawo, bazan wuce awa biyu ba”.

Cikin yauƙi tace.

“Ni da mu tafi tare”.

Kai jujjuya tare da ɗan janye jikinshi kana yace.


“Baby mitin fa zamuyi, kuma duk mu ya mune maza. Ki dai yi haƙuri kinji, bari in tafi kada in makara”.

Cikin kwarkwasa tace.

“Toh sai ka dawo”.

Ɗan shafa fuskarta yayi kana ya fice.

Ita kuwa ƙofar ta maida ta rufe.

Tare da komawa cikin falon, bisa 2 str ta kwanta tare da ci gaba da chating.

A hankali ta ɗan juya kanta, jin kamar alamun an buɗe ƙofar ɗakin nan da bata taɓa shigaba, kai ta
maida ta jingina taci gaba da latsa wayar, sabida ganin ƙofar nan a rufe.

Sai kuma ta ɗan dakata da latsa wayar sabida jin kamar hucub numfashin mutun, haka nan kuma wani
irin kasala da tsoro ya diro nata, a hankali ta juya idonta zuwa kan A.C wanda a zatonsa hushin fesar da
sanyinsa ne.

Da sauri ta tashi zaune jin hucin ya karuwa da kuma ƙara matsota. Wani irin gigitaccen kara da tsalle ta
haɗa tayi a tare, sabida ganin wani irin zabgegen maciji baƙƙirin da yake mirgina a tsakiyar falon yana
mai baza wani irin fitinennen huci da zaro harshe, abinka da babu alla a cikin rai, gaba ɗaya ta mance da
addu'a sai karkarwar da ihun da takeyi, tare da dira ta bayan kujerar cikin kiɗima, ta fara lalubar
wayarta, tana ɗaukan wayar ta dannawa, Unclee Naseer ɗin kira, amman bai dagaba, da gudu ta nufi
bedroom ɗinta, tana shiga taci gaba da danna mishi kira babu ƙaƙƙautawa amman ko sau ɗaya bai
ɗagaba.

Sai kuma ta fara kiran number Hajia Bunayyah itama waya mata ringgin amman ba'a ɗagawa.

Wani irin gigitaccen ihu ta fara kurmawa lokacin da taji hucin na ƙara matsowa bedroom ɗin nata, ga
gida ita kaɗai babu ko mai gadi.

Can kuma sai taji hucin ya bari, ajiyan zuciya ta fara sauƙe tare da yarfe zufar dake ɗiga mata tako ina,
dai-dai lokacin kuma taji Unclee Naseer na kiranta tare da bubbuga mata kofar.

Cikin rawan jiki tazo ta buɗe ƙofar ganinshi yasa ta faɗa jikinshi tare da sakin kuka.

“Ah Baby lfy kuwa meya faru?”.

Cikin tsoro tace.

“Uncle Naseer ƙaton maciji fa na gani, a tsakiyar falonmu, inata kiranka baka ɗauka”.
Wani irin makirin murmushi Naseer yayi tare da cewa.

“Oh my god Baby dama dan wannan macijin ne kika rufe, kilata ihun nan, ihunki nefa ya dawo dani dan
dana sauƙa ƙasan na tsaya ina ɗan waya da Kesi shiyasa ban fita da wuriba”.

Cikin tarin mmki tace.

“Dama kasan da macijin ne a cikin gidan?”.

Hannunta ya kawo suka fito falon, bisa kujera suka zauna yace.

“Na san dashi mana, ai shiyasa nace karki shiga ɗakinnan dan a ciki yake, kuma babu abinda zai miki
kawai dai nasan, idan kika ganshi zaki firgitane, shiyasa nace kada ki shiga, amman babu abinda zai miki
shi gadin gidan yakeyi, babu wani abin cutarwar da zai shigo muddin yananan, dan haka ki kwantar da
hankali ki”.

Cikin ɗan sauran taradadi tace.

“Da gaske ba abinda zaimin?”.

Cike da yaudara yace.

“Shin bakiga bamu da mai gadi a gidanba?”.

Da sauri ta gyaɗa mishi kai.

“Toh ai dan nasan ibada wannan macijinne shiyasa ban wani nemi wani mai gadiba.

Kada kiji tsoro gaba ko ya fito, kada ki gudu babu abinda zai miki ko kan cinyarki ya hau, in Kinga ya fito
dai yunwa ne yakeji, ni har gado ɗaya muna kwana dashi”. Cikin bashi dukkan yarda tace.

“Da gaske ba abinda zai min?”.

Cikin son samata yarda yace.

“Wallahi ba abinda zai miki ke dai ko jikinki yace zai hau ki barshi kada ki gudu”.

Daga nan yaci gaba da rubta tunaninta saida yaga ta ɗan nitsu kana ya sake fita.

Taraba Gembulan.

Hajia Lami ce zaune bakin gadon da Samira take kwance cikin toshe hanci tace.

“Ki tashi ki shirya muje asibiti, dan wannan wari ya fara yawa, ni kaina tsoron matsowa kusa dake nake”.
Cikin zubda hawayeba Samira tace.

“Uhmmm Momy kenan, amman kuma lokacin da nake cewa bazanje boka yayi lalata da nuba, kece
kikayi ta ingizani kina turani harda nuna zakiyi fushi dani in banjeba, sai gashi yanzu kuma harda ke a
cikin masu guduna sabida warin da nakeyi"...

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYA

54

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 08069423567 ko
kuma ta wannan 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare
Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida.


😘

Sai kuma ta fashe da kula mai cike da rauni, murya na rawa tace.

“Momy da kin kasancemun uwa ta gari da haka bai faru da niba, mun sake Allah mun kama boka baga
masifar da ta biyo bayan kauce gaskiyaba, gashi yanzu munaji muna gani Modibbo ya auri Khausar, a
lokacin da ahlinsa suka bayyana da irin matsayin da ko wacce mace zasayi fatan samu, duk da ni dai
Allah ya sani ba kuɗi babu ba, naso Modibbo ne har raina sabida iliminshi da kyanshi”.

Cikin zuƙar warin da Samiran keyi Hajia Lami tace.

“Yanzu dai zaki tashi mu tafi asibitin ko sai kin gama zagina”.

Cikin sharce hawaye tace.

“Kiyi haƙuri Momy bazan zagekiba, wannan zunubin dana aikata ma ya isheni ba sai na ƙara wani ba na
zagin mahaifiya, ki yafe min mutafi”.

Ta ƙare mgnar da miƙewa suka fita.

Marocco

A hankali ya fito daga falon nashi yana mai zuba wani irin fitinennen ƙamshi, tare da sheƙi da ƙellin
fuska.

Ware manyan idanunsa yayi lokacin da yaji ƙaran wayar Khausar da ya ajiye bisa, dinnin table a hankali
ya nufi kan Dinning area ɗin.

Ido ya zubawa fuskar wayar ganin.

*My happiness* a fuskar wayar ya sashi rumtse idanunsa da ƙarfi sabida jin.

Wani irin abu mai masifar ɗaci da maƙaƙi ya tokari maƙoshinsa.


Rumtse idanunsa ya kumayi kana ya buɗesu da sauri, hakanne da kuma ganin a saman lips inshi yace.

“My happiness”.

Waye?”.

Sai kuma ya sa hannunsa ya ɗauki wayar tare da juyawa da sauri ya nufi falonta.

Can ya hangota a bakin ƙofar corridor ɗin tanata kiciniyar buɗewa amman ta gaza gane ta yaya ne ake
buɗe ƙofar.

Da sauri ta juyo jin alamun takun mutun, cikin sauri tayi kasa da kanta ganin wani irin kallon da yake
liƙamata shi kuwa kanta ya nufa gadan-gadan ganin hakane yasa ta fara ja da baya da baya jin ta jingina
da ƙofarne yasa ta buɗe idanunta.

Da sauri ta kuma rumtse idanunta ganin yadda ya matsota gab da gab, cikin wata irin muryar da shi
kansa bai tantace ta meneba yace.

“Wayeshi”. Ya ƙare mgnar tare da nuna mata fuskar wayar,

sassayan numfashi ta fesar tare da miƙa hannunta alamun zata amshi wayar, cikin tsawa yace.

“Ce miki nayi ubanwaye ne shi, baki bani amsaba kike miƙo hannu zaki amsa”.

Cikin tura baki da sauƙe numfashi tace.

“Toh ni ka bani wayata mana, me ruwanka da masu kirana”.

Wani irin gigitaccen abune yaji ya soƙi ƙahon zuciyarsa, cikin juyewar yanayi ya danna mata wani irin
gigitaccen tsawa tare da ceea.

“Wane ɗan iskanne shi da zai kira m...”

sai kuma yayi shiru ganin wani kiran ya kuma shigowa.

Ita kuwa Khausar wani irin numfashi tsoro taja tare da takure jikinta wuri ɗaya sabida ganin kamar
marinta zaiyi.

Amsa kiran yayi tare da liƙa wayar a kunnensa ba tare da yace komai ba.

Wani irin ɓoyeyen ajiyan zuciya mai nauyi ya fesar jin murya Mommy Khausar ce, cikin nitsuwa kamala
kawaici hadi da girmamawa yace.

“Wa alaikassalam”.
Cikin sanyi Mommyn ta fesar da numfashi dan ta gane muryarshi.

“Mommy ina kwana?”. Ya kuma cewa jin tayi shiru.

Ita kuwa Mommy cikin girmama kai tace.

“Lfy lau Moddibo ya gida”.

Wani irin amintaccen numfashi ya kuma fesarwa tare da sa hannunshi ya kamo hannun Khausar ɗin kan
ya juya da ita suka nufi falonta yana mai cewa.

“Alhamdullah Mommy yasu Raudat”.

Ya kare mgnar tare da sake hannunta kana ya zauna bisa kuje.

“Suna lfy, gatama tun ɗazu take ta kuka wai in Kira mata Adda Khausy”.

Juyowa yayi ya kalli Khausar ɗin da ta matso kusa dashi tana mai miƙa mishi hannun alamun ya bata
wayar, fuska ya tsuke tare da dannan mata harara.

Kana yace Mommy kuwa.

“Toh a bawa Raudat ɗin”.

Cikin kawaici Mommyn ta miƙawa Raudat ɗin waya tana amsa tace.

“Hello Adda Khausy nayi missing inki”.

“A'ah Raudat ya akayi yau bakije school ba?".

Jin hakane yasa Khausar kara matsowa gareshi cikin zumuɗi da son jin muryar Raudat ɗin dan tun
shekaran jiya basuyi mgn ba, da sauri ta miƙo hannunta har tana taɓa sajenshi.

Juyowa yayi yana maiyi mata wani irin kallon mai haɗa da saƙonni masu yawa, katse kiran yayi baƙi ɗaya
ya xora wayar a aljihun rigar shaddar dake jikinsa wacce iri ɗaya ne da nata.

Cikin tsuke fuska ya tsira mata ido tare da juyowa ya fuskanceta da kyau idonshi ya zira cikin nata tare da
cewa.

“Na dai lura ke, in baki taɓani ba, bakya jin daɗin rayuwarki, na gama fahimtarki ban san me kikeso inyi
mikiba da kike shigemin rayuwa da jiki, gaba ɗaya in kin gannin jikinki rawa yake, ji kike kamar kin
cinyeni ɗanye dan rashin ta ido, yanzu ji yadda kike wani son kamani ban san uwar me kikeso inyi miki
ba”.

Ya ƙare mgnar cikin ƙarfin hali.

Ita kam Khausar cikin mmki da tsoron lamarin shi ta buɗe baki tare da cewa.
“Ni dai Allah ya sani ba abinda ya dameni da kai, kawai wayata zaka bani, toh ma ni me ruwana da kai”.

Ta ƙare mgnar tana tura baki.

Da hannunshi yasa ya kamo hannunta tare da matsewa har saida tayi ƙara kana yace.

“A hakan dai kikace kina sona! Ga yadda kike kallona kamar ki haɗiyeni ni ban masan me sajena ya tsare
mikiba".

Da sauri ta kwaɓe fuska tare da yin ƙasa da kanta tace.

“Toh ni ai wayata nake kalla".

Ta ƙare maganar tana tura baki.

Shi kuma cikin tsareta da ido yace.

“Jiya da dare ba biyoni kikayi ba”.

Sai kuma ya miƙe tsaye tare da motsowa kusa da ita cikin wata irin sassautacciyar muryansa can ƙasan
maƙoshi yace..

“Ni kikeyiwa haka ko? Zanyi maganinki zan miki abin da kike son inyi mikin, tunda na lura a hannu kike”.
Ita batama fahimci mgnar ba sai dai jujjuya ido da tayi cikin shaƙar ƙamshin jikinsa tace.

“Ni dai ka bani wayata”. Tsuke fuska yayi tare da matse jikinsa baga ɗaya kana cikin danne yanayin da
yake ciki yace.

“Bazan badawa”.

Sai kuma yayi mata kallon sama da ƙasa kai ya jinjina ganin mayafin jikinta ya ɗan rufe mata ƙirji, juyawa
yayi kana ya ɗan zagaya bayanta tare da cewa.

“Mu tafi Didi na kiranki". Zuwa yanzu tasan waye Didi tasan nasabarta da kuma kimarta, haka yasa cikin
nitsuwa tayi gaba batare da tacemai ko ƙalaba, bayanta yabi, tare da sauƙe ganinsa kan ƙugunta dake
juyawa kai kace kamar da gayya takeyi.

Kiciniyar buɗewa kofar ta fara, shi kuwa ido kawai ya zuba mata, kusan one minute tana kiciniyar, gani,
ta gazane ta juyo ta kalleshi tare ɗan tura baki tace.

“Na kasa buɗewa”. Kallon gefen ido yayi mata kana yace.

“Uhmmm dama ke me kika iya banda rawan kai”.

Wasu pin number dake jikin ɗan ƙofar ya danna wanda shima Ibraahim ne ya nuna masa.

Da hannun yayi mata alamun su tafi.


A hankali suka fito kana yaja ƙofar ya rufe, jujjuya kai tayi don so take ta gane ta inane inda su Ummi
suke amman ta gaza ganewa kasancewar idonta a rufe suka fito, kuma ma ƙofofin wurin sunyi yawa.

A hankali ta fara taka steps din suna sauƙa ga mamakinta sai taga basu ɓullo cikin falon nanba, sai
ganinta da tayi cikin corridor nan mai faɗi, kusan a jere suke tafiya yayinda suke baza wani irin fitinennen
ƙamshi kamar furannin.

Da sauri tayi ƙasa da kanta lokacin da taga sun ɓullo cikin wani ƙasaitaccen falo, wanda tayi arba da
Rahama dake tsaye, da sauri Rahama ta nufeta tare da buɗe mata hannun.

A hankali ta ware hannunta suka ruggume juna.

Didi kuwa murmushi ta saki tare da miƙewa, ruggume su tayi duka biyu tana mai cewa.

“A onmi jam nɓingel am". Kin tashi lafiya ɗiyata”.

Cikin mmkin yadda akayi Didi da yaranta kab da yawa da cikin mutanen makusantansu suka iya fllanci
ras ta ɗan kalli fuskar Didi tare da cewa.

“Jam Alhamdulillah Didi noi Chomri".

Lfy lau Alhamdulillah Didi ya gajiya.

Murmushi Didi tayi tare da kallon Modibbo da ya zuba musu ido ko keftawa bayayi.

Sai kuma ta juyo cikin falon jin su Lalla Khadijah suna dariya tare da cewa.

“Didi kalli Ibarahim yadda ya wani zumbura baki, wai sun kwace mishi fada”.

Cikin dariya tace.

“Yoh ai bashi kadaiba kalli Yayan nashi ma yadda ya tsaremu da ido".

Da sauri Modibbo ya kauda kanshi jin abinda Abualeey ke mishi dariya.

Saita nitsuwarsa yayi cikin yanayinsa mishkilanci ya raɓa gefensu ya wuce, biyoshi sukayi a baya.

Ita kuwa Khausar a hankali ta rusuna gaban Abualeey cikin sanyi da girmama tace.

“Barka da safiya Abba”.

Cikin kula yace.

“Barka dai Khausar ya bakunta".


Cikin yin ƙasa da kai tace.

“Alhamdullillah".

Sai kuma ta miƙe sabida kamo hannunta da Aunty Khadija tayi tare da cewa.

“Bismillah zo muje muyi breakfast”.

Kai ta gyaɗa mata kana tabi bayanta.

Yayinda suma duk saura suka bi bayansu suka nufi wani tamfatsestsen Dinning table wanda a ƙalla yake
da kujeru goma sha biyu.

Sai kuma duk suka tsaya, har saida Didi da Abualeey suka iso suka zauna sannan duk suka zauna.

Didi da Abualeey suna kan karshen table ɗin a jere, sai kuma Khausar dake gefen Didi forkon layin kenan
sai kuma ɗaya gefen forkon layin Modibbo ne zaune wanda ya zama yana fuskarta Khausar.

Sai Ibrahim dake gefshi yana fuskarta Rahama dake gefen Khausar, sai kuma Lalla Hafsat dake fuskantar
Hakim sai kuma Lalla Khadijah, dake fuskantar Ashshe.

Ya zama kujeru uku ne babu kowa a kansu.

A hankali Lalla Khadijah ta miƙa tsaye tare da fara savin dinsu ɗaya bayan ɗaya duk da kowa da irin kalan
abinda ta zuba mishi.

Abualeey masace mai haɗa da miyar daddageggen nama, sai kuma Modibbo da Ibarahim da ta zuba
musu soyayyan dankali, da dege-dege da yaji naman kaza da kuma fararen tsokokin kifi sai kuma
wadatacciyar albasar da take sa ɗan sauran gwaninta, sosai yajin yayi meɗeu a cikin domin Ibarahim na
son yaji sosai sai kuma soyayyan kwai da yaji vegetables wani iri daddaɗan ƙamshi mai tada tsohuwar
yunwa dege-dege ke gazawa, shi ta zubawa Khausar ma da Rahama, sai kuma ta sawa Ashshe da Lalla
Hafsat masa da miyan ita kuma irin nasu Khausar Hakim ma Masa da miyarsun ta saka mishi.

Da sauri duk suka juyo jin muryar Dr Jameel da Zakariyya da kusan a tare suka shiga.

Bisa kujeru dake gefen Lalla Khadijah suka zauna bayan sun gama hausawa.

Suna ta zuba musu abincin.


Bismillahi suka kana duk suka fara ci.

Yayinda Khausar kuwa ke riƙe da fork din tana ɗan jujjuyawa tana ganin yadda miyar taji nama da kifi.

Da sauri Didi ta kalleta tare da cewa.

“Bismillah ɗiyata kici abinci”.

Murmushi ta ɗanyi tare da cewa.

“Toh”. Sai kuma ta ƙare mgnar tare da kallon Modibbo dayi loman forko, da sauri ya lumsh idanunsa,
yana maijin ɗan-ɗanon abincin mai gamsarwa na ratsa mishi harce, sai dai kuma wani irin gigitaccen
yajin da yaji yana gama gaba ɗaya jijiyoyin bakinshi manya da kananan. Allah ya sani shi dai yana masifar
tsoron yaji.

Rahama ce ta kalleshi cikin murmushi tace.

“Yah Aleey yayi daɗiko nice nayi mana girkin da kaina”.

Cikin danne azabebben yajin dake gab da gigitashi yace.

“Yes kinci a baki tukuici”.

Sai kuma ya ɗan kalli Ibarahim dake cewa.

“Wow masha Allah ai ɗaɗi kam sosai ma, wannan girki ko yau aka aurar da ke ai bamu da haufi”.

Kai Khausar ta ɗan sunkuyar tare da soka dankali ɗaya ta haɗa da kifin kadan tasa a baki.

Wani irin zar taji yawun bakinta ya tsinke Allah ya sani tana da masifar cin yaji, shiyasa taji abinci yayi
mata yadda takeso, sai dai duk da haka yajin ya fitini harshenta.

A hankali ta kalli Lalla Hafsat da kuma Lalla Khadijah dake cin abinci cike da kwanciyar hankali alamun
suma manyan askarawa ne a cin yaji.

Sai kuma ta kalli Dr Jameel ta ɗan kalli Abualeey tare da jan plate gabansa ya fara cin masa da miyar
Abualeey da aka sa mishi.

A hankali ta dawo da kallonta kan Modibbo da ya kai hannunsa kanshi yana ɗan shafawa tare da yin ƙasa
da hannunsa har zuwa ƙeyarsa.

A hankali ta kuma kai loma na biyu wanda zuwa lokacin Ibrahim dasu Kalla Khadijah har sun kusa cin
kaso ɗaya bisa ukun na abinci da ke kan plate dinsu.
Shi kuwa Modibbo cikin sanyi ya kai loma ta huɗu wanda tuni idanunsa sun cika da hawaye sabida
azabar yaji daya fitini bakinsa.

A hankali ta tsaida idanunta kanshi tana mai tuno wasu kalaman Yah Jameel a ranar da sukayi rabuwar
ƙarshe a cikin Shopping mall da suka shiga, a lokacin da yaga ta ɗauki robar dakekken yaji yace mata.

“Na lura kina son Yaji matuƙa, MJ ɗina kuma yana masifar tsoron yaji, kuma muddin yaga mutun yana
son a yaba masa kan girkinsa to baya taɓa kushewa, kuma duk rintsi sai yaci dan shi mutum ne da baya
son gwatsale mutum.

Shiyasa ko yaya bazai faɗaba, gwara ki sani dan kada kije kiyi ta zabga mishi yaji ki kashe min aminina.

Domin ko yaya bazai faɗa mikiba sai dai idan yaji ya gigita shi, zakiga, zaita shafa kanshi musamman
ƙeyarsa kuma idanunshi zasu cika da hawaye, baza kuma su zuboba haka kuma zakiga duk sanyi zai fara
zufa toh da zan kinga haka ki sani yajine ya gigitashi”.

Tuno hakanne yasa dawo da hankalinta kanshi ai kuwa zufan yakeyi duk da masifeffen sanyi da AC ke
busa musu.

A hankali ta sauƙe numfashi tare da sa hannunta ta dauki goran ruwan dake gefenta wanda yake zuba
nason sanyi, a cup ta zuba mishi ruwan tare da miƙa mishi.

Da sauri ya zura mata idanunshi dake cike tab da hawaye, ba musu yasa hannunshi ya amshi cup din tare
da kaiwa baki, lokaci ɗaya ya zuƙe ruwan tare da ajiye cup din.

Didi kuwa da Abualeey duk ido suka zuba mishi Ashshe kuwa da sauri tace.

“A'a Aleey ko dai kaima irin su Hafsat ne da yaji ke gigitaku”.

Juyowa yayi ta kalleta da idanunsa da tamkar hawayen zasu zubo, sai shafa ƙeyarsa zuwa sajensa yake
tamkar ba gobe.

Juyowa sukayi baki ɗayansu suna kallon Khausar data ƙara mishi ruwan sanyi tare da cewa.

“Issah”. Sai kuma tajanye plate ɗin daga gabanshi tare da turawa Ibraahim da har ya cinye nasa cikin ɗan
sanyi tace.

“Yayanka kam in yaci wannan zai iya sume mana a nan”.

Cikin dariya Ibrahim yace.

“Kai haba dai”.

Lalla Khadijah cewa tayi.

“Yah Salam Aliyeeh ashe baka cin yaji kuma bazama faɗa minba”.
Ina bazai iya mgn ba yanzu sai sauƙe numfashi yake da shan yaji a hankali tare da bin Khausar da kallo
mai cike da mamaki ya sani duk duniya J ɗinshi ne kaɗai yake iya gane dukkan motsinshi koda ko baiyi
mgn ba, toh ya akayi ta gane duk halin da yake ciki”.

Didi kuwa cikin murmushi da tsareshi da ido ta zuba mishi abincin da akeyi dan Abualeey ta miƙa mishi
tare da cewa.

“Sak komai nashi na Abbanku ne, wato har yadda idanunsa sukayi haka nan idanun Abbanku keyi
matuƙar dai yanacin yaji, kuma wai bazasu faɗaba, yanzu in badon Allah ya baka mace Mai lura da
kulaba ya zakayi kenan”.

Shi dai sai shafa saje yake dan har yanzu baya jin zai iya mgn.

Abualeey kuwa cikin kulawa yace.

“Daga yau kada ku sake bashi abincin da Rahama ta dafa, dan na lura ita harshenta ya mutu baya jin yaji
ita da Ibrahim da Khadijah”.

Dr Jameel kuwa dariya yai tare da cewa.

Ai ni ko gigin bacci nake bazanci abincin da Ibrahim yaci ba yaro kamar maye”.

Sai kuma duk suka juyo kan Modibbo jin Khausar na ce Mushin.

“Isah yar diyam fahin". Kai ya ɗan jujjuya mata zuwa yanzu duk hawayen sun ɓace sai dai zirin idonshi da
yayi ja.

Sannu suka rinƙa jera mishi Rahama kuwa kamar zatayi kuka tace.

“Allah ko Abualeey ban san baya cin yajiba ni yamin irin Yah Ibraahim ne shima, kuma in Sha Allah daga
yau cikin abincinka zai rinka ci".

Sai yanzu ya ɗan fesar da numfashin kana yayi ɗan murmushi gefen baki tare da cewa.

“Kada ki damu Rahama abincinka yayi”. Cikin murmushi jin daɗin ya yaba mata ta kuma ce mishi sannu.

Zakariyya ne yace.

“Ni dai banji wani yajinba”.

“Yoh dama kai zakaji ne tunda kaima irin Ibrahim ne”.

Cewar Kalla Hafsat.


Daga nan suka ci gaba da cin Abinci shi kuwa a hankali yake cin abinci yana kallon Khausar ta ƙasan ido
da mamkin lamarinta.

Bayan sun gama cin abincin ne duk suka dawo tsakiyar falon da sauri Dr Jameel yabi bayan Abualeey
dake shirin fita.

“Cikin girmama yace Abualeey, ka kirani”.

Cikin kulawa da son Dr Jameel daya kasance ɗane ga marigayi Aminin Abualeey wanda bashi da kamarsa
a duniya a hankali yace.

“Eh dama cemaka zanyi kuɗauki bakin nan ku fita dasu da kai da Ibrahim da Zakariyya ku kaisu su ɗan ga
gari, dan yau saura kwana biyu zasu koma Ibrahim da Haroon zasu fita da mazan kai kuma sa Zakariyya
ku fita da matan”.

Cikin girmama yace.

“Toh”. Sai kuma yaci gaba da binshi ganin hakane yasa Abualeey juyowa ya ɗan kalleshi tare da cewa.

“Da mgn ne”.

Cikin yin ƙasa da kai yace.

“Eh Abualeey”. Daga nan kuma ya kwashe labarin Asma'u ya bashi ya ɗauka da cewa.

“Wlh kuma Abualeey ina sonta har raina”.

Cikin tsanananin jin dadi Abualeey yace.

“In sha Allah kuwa ka sameta, kada ka damu kaje abunka sanyi mgn da manyansu”.

Daga nan ya juya ya koma ciki.

Shi kuwa Abualeey daga nan kai tsaye wurinsu Abban Jameel ya nufa, bayan yayi musu dukkan bayanin
sosai abin yayi musu daɗi domin dama tun jiya Zakariyya kam yayi mishi mgnar Aseeya a cewarsa ya lura
Modibbo ɗan tsarine.

Lamiɗo kam daga wurin ma yace in dai Aseeya ta yarda ya bawa Zakariyya ita.

Domin ranshi ya cika da farin ciki ya kuma gamsu da kamalarsu yasan ko ba komai Allah yayiwa Asiya
zaɓin mafi Al'khairi a gareta.
A can falon kuwa cikin jin daɗi Dr Jameel ya faɗawa Zakariyya da Ibraahim yadda sukayi da Abba.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya kalli Didi tare da cewa bari inje wurin Abban Jameel.

“Ka gaidashi”.

Tace mishi tana mai miƙawa Khausar hannu alamun tazo.

Shi kuwa Modibbo hannunshi ya miƙawa Dr Jameel tare da cewa.

“Zo muje wurin Abba yaga mai kama da Jamilunshi”.

Dr Jameel na miƙewa yace.

“Ai Innayi ta kaini wurinsu jiya, yayi ta kuka saida nima ya sani kuka”.

Ya ƙare mgnar yana bin bayan Modibbo.

Yayinda Zakariyya kuma ya kamo hannun Ibrahim tare da ce mishi.

“Zo ka rakani wurinsu Innayi”.

Toh yace kana ya miƙe suka tafi can.

Shi kuwa Modibbo bisa jagaroncin Dr Jameel , sukaje Side dinsu Abba.

A falo suka samu Lamiɗo da kuma Bappa Jimeta da Malam Arɗo.

Sai Haiydar dake can kan danning table.

Ganin Modibbo da Dr Jameel ne yasa ya sauko da sauri tare da isowa tsakiyar falon.

Shi kuwa Modibbo cikin nitsuwa suka gaisa dasu Lamiɗo.

Bayan ya gaidasu ne kuma ya ɗan kalli Malam Arɗo dake cewa.

“Yanxu dai ya tabbata kun guji makaranta kenan?”.

Yayi mgnar yana kallon Dr Jameel da tamkar M Jameel ne ke zaune gabansa,

Murmushi Dr Jameel yakeyi tare da binsu da ido ganin yadda suke kallonsa cike da rauni.
Shi kuwa Modibbo

Kai ya ɗan juya tare da miƙawa Haiydar hannun, sai kuma ya juyo kan Malam Arɗo tare da cewa.

“In sha Allah nan kusa ai zamu dawo”.

Murmushi Abba Jameel dake fitowa daga cikin ɗaki yayi tare da cewa.

“Uhmmm Aliyu kace dai za kuje, amman ai komawa kam banga alamaba”.

Ya ƙare mgnar da zama kusa dasu tare da shafa kan Dr Jameel dake cewa Abban.

“Barka da safiya Abba na”.

Cikin zuba mishi ido da ta'ajjudin kamannin daya zarta zaton mai zato yace.

“Barka dai Jamilu na”.

Sai kuma ya ɗanyi shiru tare da sunkuyar da kai dan muryarshi data fara rawa.

Moddibo kuwa a hankali ya ɗan taune lips inshi ta gefen tare da gyara zamanshi ganin Abban Jameel ɗin
ma ya zauna tare da cewa.

“Yanzu Mai martaba da Waziri da Galadima suka fita nan”.

Cikin sanyi Modibbo ya gyaɗa mishi kai.

“Sunzo mun tattauna kan lamarin Jameel da Asmau da kuma Asiya da Zakariyya Alhamdulillah kuma
mun tsaida matsaya.”

Cikin sanyi Modibbo ke jinjina mishi kai

Sai kuma ya kalli Haiydar dake cewa.

“Yah Modibbo ina Adda Khausy”.

A hankali yace.

“Tana wurin Didi”.

“Tun ɗazu nake ta kiranta bata ɗaukaba, Mommy ma tace min tai ta kiranta bata ɗauka ba”.

Cikin kauda kai yace.


“Eh wayar ce tana hannuna”.

Kai Haiydar ya jinjina tare da cewa.

“Ina son zuwa wurinta”.

“Toh sai na tashi tafiya”. Ya Bashi amsa.

Daga nan kuma Haiydar ɗin ya nufi wata ƙofa yana cewa.

“Bari inje in canza kaya dan ance zamu fita”.

Da ido kawai suka rakashi.

“A wanne hotel ne ka sauka da kazo”. Abban Jameel ya jefawa Modibbo tambayar.

Cikin girmama yace.

“Sofiyel Mouley Youseep hotel na sauka”.

Cikin sauri Dr Jameel yace.

“Hotel ɗin Abualeey ne ai”.

Kai Abba ya jinjina tare da cewa.

“Batun kayanka da kuma takardun aikinmu na Companyn'ne dama yasa nake son muje mu ɗaukosu”.

Cikin sauri Dr Jameel yace.

“Room no ɗin kawai zai gaya mana Abba, idan mun fita zamuje mu ɗauko, komai barema da Ibrahim
zamu fita da wanda komai na Hotel ɗin a hannunsa yake”.

Cikin jin daɗin abin yazo da sauƙin Abba yace.

“Toh Alhamdulillah”. Sai kuma ya ɗan gyara zamanshi tare da fuskantarsu da kyau a

hankali yayi gyaran murya tare da yiwa Dr Jameel wani irin kallo mai cike da sonshi, ganin ko zamanshi
yadda Jamilunsa ke zama a gabanshi haka ya zauna.

Cikin danne raunin sa ya kira Modibbo.


Shi kuwa Modibbo cikin nitsuwa ya amsa tare da takwashe sawunshi yayi ƙasa da kai.

Abba kuwa cike da sanyi ya fara bashi labarin wasiyar J ɗinsa, da kuma yadda sukayi ta fafutukar samun
auren ya kasance daga forkon har ƙarshe sai dai abinda ke gefen Khausar da bai saniba.

Gaba ɗaya jikin Modibbo tsuma yakeyi duk da kafiyarsa na son hana kukanshi subcewa ya gaza.

Gaba ɗaya mutuwar J ɗinsa ta dawo mishi sabuwa dal, ashe J ɗinsa ne ya haɗa aurensa da Khausar
kenan da gaskene lokacin da yake cewa yayi mishi zaɓin matar aure, ashe Khausar ya zaɓa mishi.

Wani irin maraitaccen kuka ne ya subce mishi sabida tunowa da wasu abubuwa masu tarin yawa wanda
yake da yakinin gsky ne a zuciyar J ɗinsa kenan Sadaukarwa ce J ɗinsa yayi masa, Sadaukarwar da yayi ta
ƙoƙarin yiwa J ɗinsa tsawon shekaru na nuna baison abinda yakeso a nashi ran sabida fahimtar J ɗinsa
naso yasa yayi ta cusawa ransa nesanta da muradinsa da J ɗinsa ya mallaka.

Malam Arɗo ne ya ɗanyi gyaran Muryar tare da cewa.

“Kayi haƙuri Modibbo tun jiya muke son yi maka bayani amman tunowa cewa zamu fama maka ciwon
rashin Jameel ne yasa muka gaza hakan".

Sai kuma ya ɗan yi shiru ganin yadda Modibbo ke wani irin Shesh-sheƙan mai fitowa daga ƙasan
zuciyarsa har numfashinsa na cizgewa.

Cikin sanyi lamiɗo ya dafa kafadarshu tare da cewa.

“Kayi haƙuri Modibbo addu'a zakayiwa Jameel”.

Abban Jameel kam Ina ya gaza cewa komai shima sai kukan yake.

Malam Arɗo ne yaci gaba da cewa.

“Kaga ga Bappan Khausar wan mahaifinta, wanda suke uwa ɗaya uba ɗaya kuma ƴaƴa ne ga Sarki Buba
Yeron Gombawa.

Ya baka auren ɗiyar ƙaninshi da yaƙinin zaka riƙe mishi amar ta da kula da ita.

Kuma shi kanshi Abban Jameel da yaƙinin bazaka tozarta zaɓin da aminika ɗanshi Jameel yayi maka
bane, yasa muka shige gaba akan batun auren”.

Zuwa yanzu Modibbo kam kuka yake kamar ƙaramin yaro ya kasa cewa komai.

Sai kuma ya kalli Bappa Jimeta dake cewa.

“Ni dai al'farmar ɗaya na nema a wurinka, ka riƙe min Khausar bisa amana.
Ka duba maraicinta da kuma niyarta, kada ka bari tayi kukan maraici amanace a gareka, koda baka sonta
bata cancanci muzanciba daga gareka”.....

*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n
nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai
sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan
mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in
kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a
banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account
no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na
faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki
kenan*

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito
miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar
infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita
tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a
saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda
yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin
san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo
kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567 sai ki turo min shaidar biyanki,
domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan
ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah
zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce
dai GARKUWAR MA'AURATA.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

55

*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son
k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman
lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun
matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa
ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki
tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones
dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da
tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da
ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda
ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya
wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka
kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.
Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki
da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 08069423567 kimin mgn ta whatsApp
in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta,
muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina
nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a
ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.

0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta
wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije
gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.

GARKUWAR MA'AURATA

Cikin wani irin su yan rai Modibbo ya kife kanshi bisa cinyar Abban Jameel dake kusa dashi cikin rawan
murya da jiki.

Ya bude baki da nufin yin mgnar, sai kuma yayi saurin rumtse idanunsa sabida wani irin raunataccen
kuka daya taso mishi daga ƙasan zuciyarsa, cikin Shesh-sheƙan kuka ya ɗago fuskarsa da tayi jazir ya kalli
Bappa Jimeta da Lamiɗo da idanunsa dake kwaranyar da zafafan hawaye, sai kuma ya juyo ya kalli Abba
da Mlm Arɗo tare dasa hannunsa duka biyu ya kamo hannun Abban cikin wata irin murya mai nuna
zahirin abinda ke zuciyarsa yace.

“Abba akan abinda J ɗina ya somin ya kuma zaɓamin kuke kokonta, zan aminta dashi. Shin Abba baka
gaya musu waye ne J a wurina ba, Abba ka tambayi Ummi kaji tunda muke tsawon rayuwarmu
ra'ayinmu bai taɓa ban bantaba muddin naso abu to J zai soshi nima duk abinda J yakeso sai na soshi,
wannan ita jarabawar ƙarfin amintakarmu bamu taɓa samun saɓanin ra'ayi ba kan komai”.

Sai kuma ya rumtse idanunsa da ƙarfi domin tuno abubuwa da yawa na cikin ransa da suka zame
dalilinsa na kyara da hantarar Khausar, cikin fuzgar numfashi yace.

“Abba kace musu zan rayu da ita cikin yaƙini, da kuma kiyaye farin cikinta da haƙƙinta, amman kalmar
amana da sukace min tayi min nauyi tamin ƙarfi, ta zarta iyawata.”

Cikin zubda hawaye Abban Jameel ke shafa kansa tare da ɗan bubbuga bayanshi kaɗan.
Sai kuma ya kalli Dr Jameel tare da cewa.

“Jameel ɗaukeshi ku tafi, ka rarrasheshi, ka zame mishi madadin Jamiluna, wanda nake da ya ƙinin da
yanzu yana raye bazai taɓa barin hawayen amininshi ya zuboba”.

Cikin gamsuwa Dr Jameel ke gyaɗa kai.

Bappa Jimeta kuwa cikin sanyin jiki da kuma tausayin Modibbo yace.

“Kayi haƙuri Aliyu na fahimci yadda kakeji a zuciyarka, amman dolece tasa nake baka amanar Khausar”.

Cikin rawan jiki ya yunƙura tsaye sabida jin Dr Jameel na ɗagoshi.

So yake yayi mgn amman ina ya gaza,

Cikin Tausayawa Malam Arɗo da Lamiɗo suka haɗa baki wurin cewa.

“Jameel kuje”.

wanda hakane yasa dole yabi bayan Dr Jameel dake jan hannunsa.

Kai tsaye Side ɗin Didi ya nufa da shi.

A falo suka samu Didi dasu Lalla Khadijah, bisa alamu Khausar da Lalla Hafsat kuma na cikin bedroom ne.

Da sauri Didi ta ɗago kanta tare da zuba mishi ido.

Shi kuwa Modibbo cikin wani irin sanyin jiki gami da rauni da raɗaɗin ciwon mutuwar J ɗinsa, da kuma
raunin ɗa idan ya kasance gaban mahaifiyarsa, ya isa gareta, tare da direwa bisa guiwowinsa cikin
yanayin da bazai iya jumrewa ba, ya kife kanshi bisa cinyoyinta tare da saki wani irin maraitaccen
kukunda yasa.

Zuciyar Didi wani irin gigitaccen bugawa, yayinda Lalla Khadijah kuwa da sauri ta dawo gareshi.

Tana mai zama gefenshi.

Cikin yanayin tsoro Didi ta buɗe baki a hankali tacewa Dr Jameel.

“Jameel meya sameshi?”.

Da sauri Dr Jameel ya zauna gefen Didi ganin alamu ta shiga ɗimuwa yace.
“A'a fa Didi babu abinda ya sameshi, maganar wasiyar da Amininshi Jameel mai kama da ni, ya bar
mishine ya sashi cikin wannan yanayin".

Wani nannauyan ajiyan zuciya Didi ta sauƙe sai kuma ta daura hannunta bisa kanshi tana ɗan shafawa
tare da sa ɗaya hannun kuma tana ɗan bubbuga bayanshi, cike da tsananin tausayinshi da kuma raunin
da yasa itama ta fara zubda hawaye.

Lalla Khadijah kuwa a hankali ta sauƙe numfashi kana ta koma gefe ta zauna.

Lalla Hafsat da Khausar da yanzu suka fito ne, cikin sauri Lalla Hafsat ta matso kusa dashi cikin sanyi
tace.

“Kayi haƙuri Aliy... Sai kuma tayi shiru ganin Didi ta ɗaga mata hannun kana tayi mata alamun da ta
barshi yayi kuka, domin yin kukan zaisa yaji sanyi.

Ita kuwa Khausar cikin wani irin yanayi mai cike da rauni ta zauna tare da rumtse idanunta.

Rahman dake zaune gefen Khausar dake kusa da Lalla Hafsat kuwa sai yanzu ta dire numfashin dake
bayyana tsoron data shiga.

Ita kuwa Khausar a hankali ta buɗe idanunta, wani irin kallo take bin Modibbo dashi wanda yake tafe da
tsananin tausayi rauni jinƙai domin itace kaɗai tasan irin aminci da shaƙuwar dake tsakanin Yah Jameel
din da kuma Modibbo.

Ganin yadda yake wani irin kukanda ke gab da ficewa da numfashin sane yasata jin wasu irin tagwayen
hawaye masu masifar zafina kwaranyo mata tamkar an ɓalle bakin pampo.

Da sauri Lalla Khadijah ta dawo kusa ita tare da sa hannun ta fara sharce mata hawayen da ta sharcesu
wasu zasu meye gurminsu.

Didi kuwa kallon Khausar ɗin take cike da so da ƙauna sai kuma ta lumshe idanunta tare, da jingina kanta
jikin kujerar.

Zuwa yanzu Khausar kam itama kukan ya subce mata, sosai ya taho mata da Shesh-sheƙan mai danne
numfashin, wanda hakane yasa Didi yin guntun murmushi tare da yiwa Lalla Hafsat alamun ta ɗauki
Khausar su shiga ɗakinta.
Haka yasa Lalla Hafsat tallabe Khausar tare da janta suka, shiga ɗakin Didi mai cike da ƙawa na al'farmar,
bakin gado ta ajiyeta, tare da buɗe fridge ta dauko goran ruwa mai sanyi ta ɓalle marfin kana tasa
matashi a baki wanda dole yasa tasha.

Shan ruwan ne yasa ƙarfin kukan nata raguwa sai dai Shesh-sheƙan dake fitowa daga ƙahon zuciyarta,
cikin sanyin jiki Lalla Hafsat ta jawota ta jinginata da jikinta kana a hankali ta fara mgna.

“Kiyi hakuri Khausar ki daure ki koyawa zuciyarki dauriya, tunda kinga mijinki mutum ne da wasu
mahimman abubuwan ke sashi kasancewa mai rauni, to dole ke ki kasance jaruwa ki iya kwantar mishi
da hankali da tausarsa, a duk sanda kika ga ya kasance cikin irin wannan yanayi, ba kuka zakiyiba, lallai
ne da wuya mu mata buga mazanmu cikin damuwa mu iya hana kanmu kuka, toh amman tunda kinga a
duk sanda akayi mgnar Jameel ko tunanin Jameel ya dawo zuciyar mijinki yana ɗimaucewa da raunata,
Please na roƙeki ki daure kike hana kanki kuka, nasan ciwon da kikeji a zuciyarki domin babu abinda ke
raunata mace kamar kukan mutum hudu miji, uba, ɗan uwa yaya ko Kani da kuma ɗanka, musamman in
sun girma domin muddin kaga namiji na kuka tofa abin babbane, amman duk da haka ki koyi kontar
mishi da hankali, dan na lura in ba haka ya samuba zai iya kamuwa da cutar damuwa”.

Ta ƙare mgnar da cikekken yaƙinin ganin tsananin tausayin mai jagorantar so da Khausar keyiwa ɗan
uwan nata.

Ita kuwa Khausar cikin raunatacciyar murya tace.

“Aunty Hafsat tausayinshi nakeji, komaifa na rayuwar Duniya da Yah Jameel yakeyi, ko abinci baya iya ci
sai da Yah Jameel, tunda nake tare dasu a rayuwata sau biyu na taba ganinsu ba a tareba, ranar da nayi
rabuwa ta karshe da Yah Jameel, da kuma wata rana da naje wurin Ummi shi ya maidani nan ma yaje
neman Yah Jameel din ne.

Aunty Hafsat shifa baida wani aboki a duniya sama da Yah Jameel komai tare sukeyi”.

Sai kuma ta fashe da kuka.

Hakane yasa Lalla Hafsat ƙara ruggumeta.

A can falon kuwa kusan tsawon 21 minutes Modibbo yayi yana kuka mai ciwo a rai.

Kana a hankali ya ɗago kansa ya kalli Didi dake zubda hawaye, cikin rauni yace.

“Didi J ya tafi ya barni a lokutan da zanfi buƙatarsa, Didi J fa, shine mutumin da duk abinda yasan inaso in
dai yana da damar mallaka minshi koda rasa abin zai iya zame mishi ajali yakan sadaukar min dashi.

Didi J fa shine yayi min zaɓin matar aure, ya kuma tabbar da yayi dukkan abinda zai ta yadda gashi har
bayan ransa saida abin ya tabbata, Didi J fa shine mutum ɗaya a duniya yake gane dukkan gaskiyar dake
zuciyata da motsin jiki a koda na ɓoye abin, Didi J shike riganin sanin abinda nakeso ni kaina.
Didi akan zaɓin da J yayi minfa iyayenta ke bani Amana, Didi ta yaya zan iya cin zarafi da gaza ankilta
zaɓin J na? Didi zato suke inada muguwar zuciyar da zan iya wofintar da zaɓin J ne. Didi ki gaya musu me
sukeso inyi a duniya da zai nuna musu halaccin da zanyiwa zaɓin da J na yayi min Didi J fa ya gane
wacece ita a ƙasan zuciyata duk da kafiya da nacin da nayi wurin ɓoyewa saida ya gane shi yasa ya zaɓa
min ita”.

Zuwa yanzu kusan duk hawaye suke zubdawa.

Didi kuwa a hankali tace.

“Ba kai kadaiba Aliyu dani da ahlinka duk zamu tayaka ankiltawa da kyautawa zaɓin J dinka kuma zamu
kasance masuyi mishi Addu'o'i a cikin dukkan sallolinmu."

Sai kuma tasa hannunta duka biyu ta tallabe habarshi da yayi zafi jau.

tare da share mishi hawayen da wasu ke korar wasu kana taci gaba da cewa.

“Kayi haƙuri Babana amanarsu bazata gareka riƙewaba tunda sirrin zuciyar kace da J ɗinka ya gane”.

Kanshi ya kuma jifewa yana mai ci gaba da kukan.

Jin an kira sallan azabtar ne yasa tai ta kara bashi karfin guiwar tare dasa Dr Jameel ya kama hannunshi
suka tafi.

Kana su kuma duk sukayi al'wala.

Zakariyya ma dake tare da Asiya a falon ƙasa jin kiran sallame yasa ya ɗan kalleta cikin salon so yace.

“Baby bari muje muyi salla, kafin mu dawo kun gama shiri sai mu fita ko”.

Cikin kunya da kuma so haɗin da jin daɗi Asiya ta kali santalelen Balarabe da Allah yayi mata zaɓi dashi
duk da hantarar data sha na rashi miji a wurin uwarta taki yarda aje wurin boka gashi Allah ya mata zaɓi,
cikin nitsuwa tace.

“Toh ayi mana addu'a”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Me kikeso in roƙa mana?”.

Murmushi tayi tare dasa tafin hannuntan ta rufe fuskarta kana tace.

“Twince muke so”.


Wani irin murmushi mai cike da jin daɗi Zakariyya yayi domin wannan kalmar kaɗai ta isheshi gamsuwa
Asiya ta yarda dashi, sai kuma ya bita da ido ganin ta juya ta tafi da sassarfa.

Ibraahim ya kira kana suka tafi masallaci.

A can side ɗin Didi kuwa cikin sanyi Khausar ta juyo ta kalli Lalla Hafsat dake gefenta bayan sun isar da
sallan murya a tausashe tace.

“Aunty Hafsat kijifa a cikin sallama kuka yakeyi har aka idar da sallan baibar kukaba”.

Cikin sanyi Aunty Hafsat tace.

“Wlh naji Khausar ni kaina bansan sanda naita zubdawaye ba”.

Ita kuwa Khausar kife kanta tayi a gefen kujerar da take zauna a gabanta tana mai sassayan kuka.

Ita kuwa Hafsat ɗakin da Didi ta shiga ta nufa.

Bayan an isar da sallan kuwa Modibbo gyara zamanshi yayi cikin masallacin tare da fara karatun qura'an.

Ganin hakane yasa su Dr Jameel da Zakariyya kuwa fitowa suka nufi cikin gida.

Bayan daworsu ba ɗaɗe su Ummi suka fito.

Ummi da Hajia Bunayyah na bayan motar Dr Jameel, Asmau kuwa a gaba ta zauna gefenshi.

Hajja Umma da Aunty Rukayya kuma a motar Ibrahim, sai kuma Aunty Hajara dake gaba gefenshi.

Dan Hajja Nana da innayi sunce su bazasu jeba.

Asiya kuwa motar Zakariyya ta shiga, gaba kusa dashi sai kuma Haiydar da Hakim dake baya.

Sai su Abban kuwa da Abualeey yasa amintattun hadimansa suka fita dasu cikin motoci na al'farmar.

Su maza wuraren tarihin kasar aka kakkaisu da abinda ya shafi masarautar.


Su Dr Jameel kuwa kai tsaye The exotic bouknadel garden Rabat suka wuce.

Abujan Nigeria

Tun bayan da Unclee Naseer ɗin ya sake fita, Amina ta komai cikin bedroom bata sake fitowa falonba, sai
bayan sallam azahar wanda ita ba sallan tayiba.

A hankali ta fito saɗab-saɗab tana ɗan lelleƙawa tare da jujjuya ido.

Shiru ba komai falon, wanda hakanne yasa ta kunna TV tashar MBC Max kana ta zauna bisa kujera tare
da maida hankalinta kan Film ɗin da akeyi.

Dai-dai lokacin kuma Unclee Naseer ke zaune cikin tsakiyar taron abokansa ƴan mafiya, da suka
zagayeshi da jan ƙyalle suna surutai haɗin da surkulei suna watsa mishi wani irin ruwa, bisa alamun dai
gashi nan zaune a tsakiyarsu amman ruhinsa bai wurinsu.

Babban cikinsune wanda ya fisu mummunar shiga yake mgna kamar cikin raɗa da bada izini yake faɗin.

“Kayi maza ka juya, ka bayyana gareta, kana sane yau kwananku takwas da aure wanda tun daren
forkonku akeso ka fara zuƙo mana jininta amman ka tsaya nawa, yanzu dai kwana biyu ya rage maka ka
fara kawo mana jininta in kuwa ka bari ka cika kwana goma baka kawoba toh aikinka ya ɓaci”. Sai kuma
duk suka fara surutai da watsa mishi ruwan

Dai-dai lokacin kuma Amina tayi wani irin saurin naɗe ƙafafunta ta daurasu bisa kujera, sabida ba zato
kawai taga macijin nan gabanta.

Ga mamakinta sai taga ya kwanta lip yana kaɗa mata jelarsa.

Da sauri ta kira wayar Unclee Naseer ɗin.

Bugu ɗaya kuwa ana biyu aka ɗauka cikin tsoro tace.

“Uncle Naseer gashifa ya sake dawowa”.

Cikin Wata iriyar murya yace.

“Bafa abinda zai miki, ki sauƙe ƙafarki ki gani”.


Cikin ɓatan basirar batasan ya akayi yasan ƙafarta na sama ba, ta sauƙe ƙafar nata.

A hankali ta sunkuyo jin wani sanyi a ƙafar tata, ga mamakinta sai taga wannan ƙaton macijin ne ke lasar
kafar tata, wani irin fitinennen abu taji yana bin tafin ƙafar tata har zuwa tsakiyar kanta.

Da sauri ta sauƙe numfashi jin muryar Unclee Naseer ɗin nacewa.

“Kin gani ko babu abinda zai miki.

Ko kanki ya nuna zai hau karki hanashi”.

Cikin jin bazata taba iya bujirewa umarninsa ba tace.

“To".

Sai kuma ta zame tayi ƙasa jin yana ce mata ki sauƙo ƙasa ki zauna.

Ido ta zato cikin tsoron da yasa jikinta rawa ganin ƙaton macijin nan ya mirgina ya hau bisa cinyarta, ga
mamakinta sai gashi yana cusa kanshi cikin rigarta.

“Ki barshi ya shiga rigarki babu abinda zai miki, zai ɗan gaida kayan daɗi nane ƙadan”.

Taji muryar Unclee Naseer na faɗi mata, zuwa yanzu bazata iya mgnar ba sabida tsabar tsoro sai kai
kawai ta gyaɗa kamar yana gabanta.

Aiko haka macijin nan ya fara lasar cikinta har zuwa kan nononta.

Saida yayi kusan minti biyar yana lasarta kana ya zaronkanshi ya fitar sannan ya mirgina ya koma cikin
wannan ɗakin dai daya fito.

Ajiyan zuciya mai nauyi ta sauƙe jin dariyar Unclee Naseer ta waya yana ce mata.

“Ba gashiba babu abinda ya mikinko?”.

Cikin wata irin murya tsoro tace.

“Eh ta koma ciki mahhh”.

Dariya ya kumayi tare da cewa.

“Gani nan dawowa yanzu, amman fa kada ki faɗawa kowa”.

Da sauri tace.

“Toh”.
Rabat Marocco

Sosai fa su Ummi suka ga gari, sai ƙarfe biyar da rabi, suka nufi hanyar gida, wanda tuni su Abban Jameel
kam sun koma gida.

A hankali Dr Jameel ya kalli Asma'u dake gefenshi tare da ɗanyin ƙasa da murya yace.

“Sweetheart”.

Cikin sauri ta juyo ta kalli su Ummi dake baya, sai kuma ta juyo ta kalleshi ganin su Ummi hotunan da
suka yi a cikin Kasbah Oudaia Andalusia garden Rabat suke kallo a wayar Asma'u.

Shi kuwa Dr Jameel cikin sanyi ya ɗan karkarto gefenta tare dayin mgn a hankali yace.

“Sweetheart bari mu ɗan shiga Mahaj Ryad Shopping mall in ɗan sama miki chocolate ko?".

Cikin jin dadi da son zaƙinta tace.

“Toh Yah Jameel”.

Kai ya ɗan jujjuya mata tare da cewa.

“Habibi Jameel zakice”.

Cikin kunya ta rufe fuskarta da tafukan hannunta.

Daga nan kuwa suka shiga aiko ya jijjido mata kayan kwalama kam kala-kala.

Daga nan suka biya hotel ɗin suka ɗauko komai na Modibbo.

Sai gab da magriba suka koma gida.

Suna shiga Ummi ta kalli da bisa alamu yanzu ta fito ban ɗaki dan yin al'wala tace.

“Khausar bata zoba”.

Cikin jinjina kai Innayi tace.

“Bana gaya mikiba, al'adun masarautar ba”.

Cikin sanyi Ummi tace.


“Toh yanzu muda jibi zamu tafi kuma kenan haka zamu tafi bazamu gantaba?”.

Da sauri Innayi tace.

“Eh toh bari dai kafin mu tafin zanyiwa Didi mgn in kuma akai abunan dole za'a Abu nan".

Take mgnar da kurman baƙi.

Hajja Nana ce ta taɓe baki tare da cewa.

“Koma menene dai ki jawa jikanki kunne karya karmi jika dan ƙaramace”.

Hajia Bunayyah ce ta taɓe baki kana ta juya ta nufi ɗakinsu.

A sashin Didi kuwa, koda Lalla Hafsat tazo ta gaya mata Khausar nata kuka, da sauri taje, ga mamakinta,
sai suka samu tuni tayi bacci hakanne yasa Didi gyara mata zaman zuwa kwanciya.

Suko suka fito falon, Didi kuwa da kanta ta shiga kitchen ta haɗawa Modibbo da Abualeey lunch sai dai
ga mamakinsu ba shigoba har akayi sallan la'asar da aka idar ne Didi ke tambaya Abualeey shine yake ce
mata yanzuma yana can masallaci.

Cikin sanyi tace.

“Tun safe ba, bai kuma cin komai ba gashi yanzu har biyar ta kusa”.

Cikin kulawa Abualeey yace.

“Naso inyi mishi mgn sai kuma na fahimci karatunan da yakeyi ne kaɗai ke ɗan sama mishi nitsuwa,
shiyasa ban matsa mishi ba, amman yanzu sarki fada ke cemin ya wuce sashinsu”.

Cikin sauri Didi tace.

“Yauwa to bari inje insa matarshi ta kai mishi abincin.

Moddibo kuwa a hankali yake tafiya cikin wani irin rauni mai haɗe da zafin jiki, ya tura ƙofar falonshi ya
shiga.

Sai kuma ya kunshe idanunsa domin hawayen da suka cika mishi ido ya hanashi ganin gabanshi.

Wasu sabbin hawayene suka biyo bayan waɗanda suka zubo ɗin, wanda har yanzu ya gaza hana kanshi
kuka.

A hankali ya wuce bedroom kai tsaye ya faɗa Bathroom.


Duk da sanyin da aka fara tsulawa alamun yau garin zaiyi sanyi, hakan bai hanashi sakarwar kanshi
ruwan sanyi ba.

Didi kuwa ta kalli Lalla Hafsat tare da cewa.

“Ina ɗiyartawa, na shiga ɗakin na samu bata nan”.

“Eh ta farka daga baccin kuma, sai naji tana cewa Rahama tana son zuwa wurin su Ummin”.

Da sauri Didi tace.

“Yanzu ina take”.

“Ta shiga ɗakin Rahama wai zata kirata tazo ta rakata wurinsu”.

Da sauri Didi ta kuma cewa.

“Toh kada taje kira min ita”.

To tace kana ta shiga ɗakin Rahama ta kirata.

A tare suka fito, cikin sakin fuska Didi ta kamo hannun Khausar ɗin tare da jawota kusa da ita kana a
tausashe tace.

“Ɗiyata, kizo ki kaiwa mijinki abinci, kinga tun safe babu abinda yace, sai kuka daya wuni yi.

Ki kai mishi abincin kisashi ya ɗanci kafin ya tafi sallan magarib, kada ki bari ya tafi da yunwa kiji ko?”.

Cikin sanyi ta gyaɗa kai.

Ita kuwa Didi wani ɗan Kekkyawan basket mai masifar kyau da sheƙi wanda ke ɗauke da womers guda
biyu sai plate spoon and fork sai kuma wani ɗan Kekkyawan roba mai kama da saƙeƙƙe dake cike da
fruits sai kuma goran ruwa mai sanyi a gefe. Komai dai na buƙata na ciki.

Cikin kula tace.

Kiyi sauri kije kinga biyar har ta gota.

Cikin sanyi tace to kana tasa hannunta ta amshi kondon, sai kuma ta ɗan kalli Didi murmushi Didi yayi
tare da nuna mata hanya da hannun.
A hankali tace.

“Didi mu tafi da Rahama”.

Cikin kulawa Didi tace.

“A'a bari dai Hafsat ta rakaki”.

Kai ta gyaɗa alamun to.

Ita kuwa Hafsat murmushi tayi kana tayi gaba tare da cewa.

“Muje to”.

A hankali tabi bayanta, ita kuwa Didi da murmushi ta rakasu.

A hankali Hafsat ta tura ƙofar corridor tare da cewa shiga to.

Ɗan murmushi tayi tare da cewa.

“Toh kiyi gaba”.

To tace kana tayi gaba, ita kuma tana biye da ita a baya.

Dai-dai lokacin Modibbo kuwa ya fito daga cikin bedroom ɗinsa yana mai zuba wani irin ni'imtaccen
ƙamshi mai daɗin shaƙa tattausar jallabiya ce a jikinsa red color sai kuma al'kyabbar da ya ɗaura a
samanta fara ƙal mai shara-shara.

A hankali ya zauna bisa 2 str dake fuskantar ƙofar shigowa falon, wayarshi dake kan santa table dake
gabanshi ya ɗauka.

A hankali ya cire pin din wayar.

Hotonshi dana J ɗinsa dake fuskanta wayar tashi ya zubawa ido, wasu sabbin hawayene yaji suna zubo
mishi wani na korar wani.

Karo na forko kenan tun bayan rasuwar Jameel da yaji, bari ya shiga WHATSAPP ɗin kan number'n J
ɗinsa yaga irin hirarrakin da sukeyi in kamar ace basa tare.

WHATSAPP ɗin ya shiga bayan ya buɗe date inshi na whatsapp ɗin ido ya zubawa kan number'n J ɗinsa
da shine a sama.
Cikin sauri ya shiga cikin cart ɗin nasu ganin akwai saƙon da bai buɗe ba, cikin tarin mamaki da rauni
yake kallon time and date da J ɗinsa ya tura mishi saƙon.

A hankali ya motsa lips inshi tare da cewa.

“Innalillahi kenan a ranar aka ɗauke min J nane ya turo min saƙon”.

Sai kuma yayi sauri yayi playing voice note din da ya gani na tsawo 2 minute and 36 second.

Wani irin tsuma ne da kuma kuka mai sautine suka kubce mishi a tare jin kalmar forko da M Jameel ya
fara yi mishi a wannan ranar.

Wani irin rauni da tawayar zuciya ne sukayi mishi gamayyar data haifar mishi da matsanancin kuka mai
haɗe da raunin da zai iyasa wanda ya jishi yin kuka.

Dai-dai lokacin kuma Khausar ta tura ƙofar falonshi, bisa umarnin Hafsat dake can bayanta.

“Yah Salam”. Shine abinda ya fito kan lips ɗinta ba tare da sanintaba lokacin da taji sautin muryarsa da
kuma ganin yadda yasa hannunshi duka biyu ya tallaɓe haɓarsa yanayin wani irin raunataccen kuka mai
tsuma zuciya.

Cikin wani irin matsanancin rauni ta ƙarasa ciki a hankali.

Ta ajiye basket ɗin bisa table ɗin dake gefensa.

Cikin raunin murya tace.

“Har yanzu kuka kakeyiwa Yah Jameel”.

Kamar daga sama yaji sautin muryarta, wanda ya sashi ɗago kanshi tare da kallon fuskarta da fuskarshi
da tayi jazir sabida tsananin kuka.

Da ƙarfi ya rumtse idanunsa tare dasa hannunsa duka biyu ya kamo hannayeta ya jawota gabanshi.

Kanshi ya manna kan cikinta tare dasa hannunsa duka biyu ya zagaye ƙugunta, tare da sakin kukan da ya
zarta na forkon.

Cikin tausayi, rauni, gamida jinƙai. Khausar tasa hannunta duka biyu ruggume shi.
Tare da fashewa da kuka.

Dai-dai lokacin kuma Lalla Hafsat ta ɗan turo ƙofar da niyar shigowa.

Da sauri ta koma baya tare da jan ƙofar ta rufe sabida ganin yadda ƙanin nata ya ruggume matar tashi
gam-gam.

Su kuwa cikin falon, cikin wani irin sanyin jiki Khausar ta ɗan sunkuyo kanshi hawayenta na ɗiga bisa kan
fuskarshi daya tallabe da hannunta duka biyu.

Idonshi dake kwaranyar da hawaye ya buɗe a hankali.

Sai kuma ya jawota jikinshi gaba ɗaya ta faɗa kanshi.

Ruggumeta yayi tsam a jikinshi tare da cusa kanshi bisa ƙirjinta ya kife kanshi tsakanin Caɓ.....

*Masu son Maganin infection da maganin mata, ku marmatso wannan account no in ne naku ta ciki zaku
turo kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP
NUMBER'N na 08069423567. akwai sabbin kaya masu zafi suna nan bisa hanya, ki turo kuɗinki a saki
cikin lissafi. Kayanen mata masu zafi sadidan daga Chadi akwaisu Garukan daka, gumbunan,
Tsumummuka, cida Ciccibi Abodi cida kaza ci da jan nama kwanon ƙasaitacciyar mace biyar sirri, furar
mata, gumbar madara Gumbar kolli mai ƙyallin al'khairi gumbar uku al'khairi, gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, gumbar riɗi, garin maɗi garin melɗamhi garin ilanwaddihi garin mallaka, tsumin riɗi tsumin
tsirtai tsumin kinfi budurwa, tsumin riɗi, tsumin ta baje Sabaya, matsin maliƙi mai masifar matse mace
matsin daɗi har maɗiga, mai ɗan kare kyau. Kullacar sirri al'ajabu shu'umar Humra, da duk sauran kan
ƙamshi. Haɗin amarya budurwa ko bazawara haɗin mai jego ko uwar gida, akwaisu Available set ɗinmu
hawa hawane akwai manya akwai ƙananan, ƙanan daga 40k ne 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙarami
haɗina na karshe sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar shi 7k ne shine ƙarshen haɗina kenan... Manyan
set ɗin kuma daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k ke zaki faɗi haɗin nawa kikeso anyi miki kana kimin bayanin
yadda kikeso da matsalarki ni kuwa nasan abinda zan haɗa miki, ina araha kam amman ina hana bashi*

Labarinfa yanzu ya gama jiƙa.


Yayi zaƙi shane kawai naku masu karatu. Idan har kin san baki biyaba to wlh ki biya ki karanta cikin
aminci.

1k ne da kacal sis 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA wlh ki biya ki karanta wannan littafin yafi
miki salama dan samun shi one by one.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

56

Tallah !! Tallah !!

Shahararriyar Marubuciyar nan Ikilima Adam (kyauta daga Allah) wacce ta nishadantar daku a littafin ta
mai suna *Kanwata* *kaikajawa kanka , *Rai daya janzaki*.

yau na sake dawowa domin Domin tallata muku Littafaina mai Suna *(RUDANI )* Da kuma *Makauniyar
Shari'a* littafine mai kunshe da Butulci , cin amana ,zagon Kasa , soyayya irin ta gani kasheni , aminci da
saura n su basai n'a cika Ku da surutu ba Hausawa sukace Gani yakori ji.

Karku Manta *Makauniyar Shari'a* sabon littafi ne mai bibiyar Ma'anar sunan sa.

Ya zarce duk littafai na , na baya.

RUDANI littafine mai cike da Rudani da ban Al'ajabi , duk wacce kika fi buƙata zaki biya kudin sa Naira
ɗari biyar kacal.

Farashin kowannen su Naira Dari biyar ne 500 kacal


Domin Karin bayani Ku tuntubeni a lambata kamar haka (09069080725 ko Kuma + 22953726162 ) wacce
Bata shirya Siya ba kada mu batawa juna lokaci.

Domin aikawa da kudi kai tsaye . 3115484026 ikilima Adam first bank

Turo shaidar biya akan wannan 09069080725 sai najiku.

*LITTAFIN Sakayya dai na kuɗi ne yar uwa ki biya ki karanta cikin aminci da salama ba haƙƙin kowa a
kanki 1k ne kacal kudin littafin 0661110170 Gtbank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki
ta wannan number 09097853276 in tura Miki littafin Sakayya ki karanta abinki one by one*

Cikin gigitaccen yanayi, yake ƙara cusa kanshi tsankanin caɓɓullenta, tare da rumtse idanunsu da
masifan karfi, tare da saki wani raunataccen kuka mai cike da rauni, mai ratsa zuciya da jiki duk wanda
yaji. Yayinda gaba ɗaya jikinshi ya saki wani irin karkarwa dake nuni da tsananin ƙuncin da zuciyarsa keci.

Wasu irin tagwayen numfarfashi Khausar ta rinƙa sakewa a jere a jere, tamkar zasu fito da zuciyarta
waje, wani irin tsuma naman jikinta keyi, tamkar wacce ke cikin dusar ƙanƙara.

Wasu irin hawaye masu ɗumi ke kwaranyo mata babu ƙaƙkautawa.

Cikin sanyi ta gyara zamanta tare da ɗan kishinɗar da ta bawa Modibbo damar sakewa a jikinta baƙi ɗaya
yayi lib.

Sai kuma yasa hannunshi ɗaya ya zagaye ƙugunta, yayinda ɗaya hannun kuma ya saƙalo wuyanta, wanda
hakanne ya tilasta mata sa hannunta ɗaya bisa wuyanshi, ɗaya hannun kuma ta ɗaura bisa ƙanshi tana
ɗan shafawa a hankali tare dayin ƙasa da hannun a hankali ta rumtse idanunta tana mai jin yadda sautin
kukanshi ke ratsa jiki da zuciyarta kana yakeyi mata amsakuwa cikin kunnuwanta wani irin tausayinshi
takeji yana huda dukkan wani sashi na jikinta yana ratsa zuciyarta.

Shi kuwa Modibbo cikin wani irin fitinennen ƙasala yake sakin sautin sassayan kukan.

Tare da ƙara lafewa a jikinta.

Ji yakeyi duk duniya babu wanda yasan yadda yakeji a ransa da ruhinsa, gani yakeyi dukkan mutanen
duniya Basu san ya matsayin abota da shaƙuwarsa da amintakarsa da J ɗinsaba.

Gani yake itace kaɗai abokiyar kukanshi, domin ya sani itama J ya ɗauke ta ta musamman a rayuwarsa,
wanda hakan yasa itama take nuna Kekkyawan aminci tsakaninta da J ɗinsa.
Haka nan ya tsinci kanshi da jin sauƙin da sassauci suyar da zuciyarsa keyi tunda ya lafe a jikinta.

Wani irin rauni, kasala, sanyi, mutuwar jiki, haɗida juyewar lamarine ya fara ratsashi.

A duk lokacin da yaji ɗumun numfashin ta bisa goshinsa, a hankali ya kara lafewa a jikinta.

Tare da ɗan juyo kanshi ya zamana ya kontar da kanshi tsakiyar ƙirjin nata.

A hankali ya buɗe idanunsa da sunkayi jazir.

Ita kuwa Khausar a hankali take ɗan bubbuga ƙafarɗashi da hannun hagunta, yayinda dama kuma take
shafa, kanshi a hankali har zuwa ƙeyarshi, wani irin maraitaccen numfashin mai haɗe da ajiyar zuciya ya
sauƙe da karfi lokacin da yaji ta dire kan yatsunta uku a tsakiyar kormin ƙeyarshi tanayi mishi wani irin
abu da yafi kama da susa mai haɗe da tausa.

Yam-yam haka yaji tsikar jikinsa na miƙewa.

A hankali ya kuma buɗe idanunsa.

jin ruwan hawayenta dake ɗiga kan goshinsa.

Ita kuwa Khausar cikin tsanananin tausayinshi da jin rauni mai yawa.

Domin tasan a duniya ko Ummi bazata kai Modibbo ƙuncin zaciya akan rashin M Jameel domin, ita tana
da Asma'u da Bashir zata kallesu ta danji sanyi.

Moddibo kuwa tasan bayi da kowa a duniya, domin ta sani tunda take dasu bata taɓa ganin Modibbo da
wani abokiba fashe M Jameel ba, ta sani kuma bashi da madadin shi, itama ga yadda takeji a rai da
zuciyarta inaga shi kuma da M Jameel ya kasance mishi abokin tagwaicinsa, amininsa, ɗan uwansa,
abokin shawararsa, abokin hirarsa.

Sai kuma ta ɗan sunkuyo kanshi jin ya ɗan zaro hannunshi dake maƙale da ƙungunta, ya kifeshi kan
Caɓɓullen ta na hannun dama, wanda nan yake fuskanta.

Cikin kuka da sanyi murya can ƙasan maƙoshi tace.

“A cikin alƙawuran da nayiwa Yah Jameel, harda hana hawayenka kwaranya, cemin yayi dukkan abinda
naga ya saka hawaye, abune mai tsananin ciwo da ƙuna a zuciya.

Ya roƙeni da girman zatin Allah kan cewa in zame maka madadinshi.

Yace dani dan Allah kada in bari hawayen A.J dinsa su zuba.”
Wani irin sabon kuka ne ya subcewa Modibbo domin yana iya jiyo maganar tata can ƙasa sabida yadda
kuka ke son danne mgnar.

Cikin sanyi ya ɗan ɗago kanshi da jajayen idanunsa dake kwaranyar da hawaye yace.

“Nima cemin yayi kada in bari ki zubda hawaye. Cemin yayi ke marainiya ce, injikan maraicinki. Kuma in
maida so da shaƙuwarmu gareki, cewa yayi yana da yaƙinin zaki meye min gurbinshi a wurina.

Sai kuma ya ɗan kara jawo wuyanta tare da juyawa rigingine, goshinsu ya haɗe wuri ɗaya, cikin Shesh-
sheƙan kuka yace.

“Shin da gaske zaki iya zame min madadin J ɗina”.

Ina zuwa yanzu gaba ɗaya ta gaza mgnar sai kai take gyaɗa mishi da sauri-sauri tare da sa hannunta bisa
sajenshi ta fara shafawa a hankali.

Shi kuwa Modibbo wasu irin tagwayen numfarfashi masu haɗe da ajiyan zuciya ya fara sauƙewa, tamkar
mai shiɗewa.

Sai kuma ya juya a kife bisa kanta, tare da jan dogon numfashi ya shaƙi ƙamshin Kulaccar sirri dake
jikinta.

Wani irin fitinennen kasalane yayi mishi rubdugun da yakeji, ko kwayar idanunsu bazai iya buɗewaba.

A hankali ya kife tafukan hannunsa na dama a kan Caɓɓullen dama na hagu a kan na hagu.

Cikin wani irin yanayin da shi kanshi bazai tantanceba, yaji ya fara haɗe yatsunsa a hankali yana mai
runtsesu da matsa caɓbullan.

Yah Salam wani irin fitinennen abune yaji yayi mishi tsirrrrr tun daga tsakiyar kanshi har zuwa kan
babbar yatsarsa ta ƙafar dama.

Ita kuwa Khausar wani irin gigitaccen abune taji tsarga tsakiyar kwanyarta, wanda yasa ta saki wani irin
mataccen sautin da yasa Modibbon jin M ɗinsa yin wani irin masifeffen motsi da tunda yake a tsawon
rayuwarsa bai taɓajin yayi irin wannan zalamar ba.

Kusa a take jikinsu ya ɗauki karkarwar data sashi komawa lib a jikinta.

Domin ji yake kamar abun zai ɗagashi sama ne.

Rumtse idanunsu sukayi a tare, sai kuma suka saki numfashin a tare, wani irin fitinennen bacci ne wanda
yawan kukane ya jaza musu ya diro musu lokaci guda.
A can Side din Didi kuwa, Lalla Hafsat kam ta kasa daina murmushi, ganin hakane Lalla Khadijah ke
tambayar ta.

“Lfya kuwa kike naga duk jikinki a sanyaye kuma kinata murmushi ke kaɗai”.

Juyawa tayi ta kalli Ibarahim dake shigowa sai kuma ta ɗanyi kasa da murya tare da cewa.

“Ƙaninki ne Aliyu yake bani tausayi kuma shi yake sani murmushi".

Da sauri tace.

“Toh akan me?”.

A hankali ta ɗan fesar da numfashin tare da cewa.

“Yau fa wuni yayi kuka, da rana yazo wurin Didinshi yayi ta kukansa, har yasa matarsa kuka, toh yanzu
kuma muna isa fa, ya ƙwaƙume baiwar Allah yana can kuma ya tasata gaba yana kukan mai cike da ban
tausayi nasan itama haka zatayi ta kukan”.

A hankali tace.

“Toh me ya saki murmushi kuma”.

Cikin Yar dariya tace.

“Yoh yadda ya jawota ya ruggume ta ne kai kace ƙwace mishi ita za'ayi”.

Murmushi Lalla Khadijah tare da cewa.

“Yoh ai in ya ɗan matsetan zai ɗanji sassauci”.

Sai kuma suka kalli Ibrahim dake cewa.

“A shafa min mana! Dariyar me kukeyi? bani”.

Da sauri Lalla Hafsat tace.

“A'a hirar tamuce mata, bata maza ba".

Ta ƙare mgnar tana kallon Hakim dake biye da Ibrahim, hannunshi ya miƙa mata alamun su gaisa.

Miƙa mishi nata tayi tare da cewa.

“Sai yanzu”.

Kai ya gyaɗa mata kana ya zauna tsakaninsu nan sukaci gaba da hirarsu ta ƴan uwa, jin an kira sallan
magarib ne yasa duk suka watse.
A Side din su Ummi Jameel.

Bayan sun idar sallan isha'ih ne Ummi ta kalli Asma'u da Dija tare da cewa.

“Ku dai tabbatar kun fara kimtsa kayyakinku. Kunga jibin da sassafe jirginmu zai tashi”.

Dija ce ta ɗan gyara zama tare da cewa.

“Ni kam ma, komai na a shirye yake”.

Kai Ummi ta gyada tare da kallon Asma'u da ta ɗan miƙe ƙafa tare da cewa.

“Wallahi ni na gaji, Ummi sai gobe in shirya”.

Ƙwaffa Ummi tai tare da cewa.

“Yoh kadama ki, haɗa ni dai kin san ba haɗa miki zanyi ba”.

Murmushi ta ɗan yi tare da juyawa ta kalli Hajja Nana da innayi dake zaune gefe, bisa alamu dai yau ƴan
mutuncinne domin ba faɗa sai hira suke ƙus-ƙus suna dariya, bisa alamu tsohuwar ƙawancen ya dawo da
zafinsa.

“Hajja Nana ke kam ai kina nan ko?”.

Hararanta tayi tare da cewa.

“Eh ina nan zama daram inma biyanki Yayan naki yayi ki kora masa ni”.

Gyara zamanta tayi tare da cewa.

“Yoh ai shi ba sai ya biya wani ya kora masa keba, ko mgn ma bazaiyi da body language ɗinsa zai miki
fata-fata, dan kin dai san yayana ba kanwar lasa bane”.

Da sauri Hajja Nana tace.

“Eh wlh tabbas kuwa na sani kam, farin sanima kuwa, amman duk iyayinsa dai ya fitomin da jikata in
ganta muyi sallama kafin mu tafi”.

Ta ƙare mgnar tana kallon Innayi da murmushi a fuskarta, itama innayi murmushin tayi tare da cewa.

“Eh bari muga dai me safiyar gobe zata haifar”.

Sai kuma suka ɗan yi dariya suka miƙe, suka nufi falo.
Ummi kuwa ɗakinsu Aunty Rukayya ta nufa.

Anan wurinsu Modibbo kuwa.

Wani irin sassayyan numfashi mai cike da salama aminci gami da nitsuwa Modibbo ke sauƙewa cikin
ni'imtaccen baccin da yakeyi wanda bai taɓa yin irinsa ba a tsawon rayuwarsa.

Ita kuwa Khausar baccin takeyi amman har lau yatsunta na shafa sajenshi da take masifar so, a hankali
hankali take shafawa, tana maijin tsantsin sajen da sulɓin yana maita daɗin shafawa.

Sai kuma ta ɗan tura kan yatsun nata, cikin ɗan kwarmin ƙeyarsa tanayin abin ne duk a cikin baccin.

Shi kuwa Modibbo can cikin baccin yake juyowa wasu irin abubuwa masu wuyar jumrewa, suna fita daga
kan ƴan yatsunta, suna ratsa ƙeyarsa da sajensa yana shiga cikin jiki da zuciyarsa, a hankali farajin wani
irin fitinennen yanayi na game ruhinsa, wani irin fitinennen numfashin mai cike da zallar fileeng ya fesar
a lokacin da ya gama farkawa daga dogon baccin da sukayi.

A hankali ya mirgina kanshi tsakiyar ƙirjinta, sai kuma ya ɗan ɗago kanshi ya kalli fuskarta, baccin takeyi
bil haƙki da gsky, yayinda ta longwaɓar da kai bisa kafaɗarta, kana ta ɗan tura baki cikin yanayin
shogwaɓar da tasashi jin wani irin harbar jijiyoyin jikinshi, idonshi ya sauƙe kan busheshun hawayenta
dake kwance bisa fuskarta.

Da sauri ya rumtse idanunsa jin yadda A ɗin shi yayi wani irin zalamemmem mika tare da tsuma.

da sauri ya ɗan yunƙura ya zauna, tare dasa hannunsa duka biyu ya dafe kanshi.

Lokacin ɗaya ya farajin jikinshi na tsuma ta ciki.

Mutsu-mutsun tashin sane ya tada Khausar ɗin, a hankali ta buɗe idanunta da suka ƙara zama kalar
bacci, sai kuma ta lumshesu ganin idanun Modibbo cikin nata.

Hannunta na dama wanda ta tallabe kanshi dashi, ta ɗan rumtse sai kuma ɗan buɗeshi a hankali tare da
miƙar dashi, sabida tsamin da yayi mata, har takeji kamar ba'a jikinta yakeba.

Cikin fesar da sassayan numfashi, ya ɗan sa hannunshi ya kamo hannun nata, sai kuma ya ɗan matse
yana mai tsareta da rikitattun idanunsa da suka fara ci da wutar sha'awa, murya can ƙasa bisa lips enshi
yace.

“So sorry ciwo hannu yakeyi?”.

Cikin kwaɓe fuska ta tura baki tare da gyaɗa mishi kai, dan sosai hannun ya daskare mata.

A hankali taja wani dogon numfashi tare da yarfa ɗaya hannunta tana mai furta.
“Ashhhhh zafehhh”.

Taja a hankali jin yadda yaja hannun nata.

Ya Salam gaba ɗaya jikinsa ya ɗauki karkarwa a fili sabida yadda sautin da ta saki ya hargiza mishi
nitsuwa.

Wani irin mayataccen kallon yake bin lips inta dashi.

Sai kuma ya ɗan fara mammatse hannun tare da naɗeshi kana ya miƙar dashi.

Ido ta zubawa hannunsa ganen yadda gaba ɗaya yake rawa.

Kusan a tare suka kallo woyoyisu dake bisa stoll ɗin dake gefensu dan ɗan karar da wayarta tayi alamun
shigowar saƙo.

Da sauri ya zaro idanunsa da suka fara ƙanƙancewa.

Ganin time ɗin 10:00 dai na dare.

“Yah salam”. Ya fadi a hankali tare da miƙewa tsaye.

Sai kuma ya ɗan juyo ya kalleta tare da cewa.

“Ya akayi mukayi bacci mai tsawo haka, ƙarfe goma fa”.

Cikin miƙe hannun ta ɗan kalli shi sai kuma ta maida dubanta kan waya.

Shi kuwa Modibbo cikin mamaki yace.

“Baccin awa huɗufa mukayi”.

Sai kuma ya ɗan kalleta tare da cewa.

“Innalillahi bamuyi sallan magarib da Ishah bafa,”.

Ya ƙare mgnar yana yin wani irin fitinennen miƙar da yasa gabban jikinshi bada sautin gat-gat-gatt, tare
da ƙara rura wutar fitinar dake dirominshi babu ƙaƙƙautawa.

Wani irin fitinennen harbawa tare da miƙawa A ɗinshi tayi wanda har saida ya daga gaban jallabiyar
jikinsa.

Ita kuwa Khausar jin abinda ya faɗane, ya tuni mata basuyi salla ba yasa ta ɗago kanta da niyar miƙewa,
sai kuma tayi saurin rumtse idanunta da masifar ƙarfi.

Lokacin da tayi arba da cikekkiyar kafiyarsa dake tsaye tamkar zata hudu Jallabiyar, kar-kar haka jikinta
ya dauki rawa.
Shi kuwa Modibbo wani irin numfashi ya fesar tare da sunkuyowa ya kalleta, sai kuma yayi maza ya kalli
jikinshi ganin yadda ta rumtse idanunta ga jikinta da ke tsuma.

Ganin yadda yake miƙene, yasashi saurin matse cinyoyinsa da son ɓoye yanayin da yake ciki.

Kana murya a daburce yace.

“Tashi muyi salla, Kinga yanzuma lokaci ya ƙure mana”.

Jin hakane yasa tayi saurin miƙewa tare da nufar ƙofar falon, tun ma kafin ya rufe bakinsa, cikkn sassarfa
take tafiya da alamun rawar jiki da tsoro.

Da ido yabi ƙugunta da ke juyawa tamkar zautacce haka ya fara jujjuya kanshi.

Tare da juyawa ya nufi bedroom ɗinsa.

Ita kuwa Khausar tana shiga ɗakinta, cikin rawan jiki ta zare kayan jikinta, tare da shigewa Bathroom.

Ruwan ɗumi ta haɗa tare da shige ciki, tana mai ɗan jan tsaki dan yau tun safe da tayi wanka bata
kumaba, shiyasa gaba ɗaya taji, jikin a ɗaure.

Numfashin mai sanyi ta shaƙa tare da lumshe idanunta dan daddaɗan ƙamshi turarukan wanka da suka
ratsa mata jiki da zuciya.

Sai kuma ta ɗan buɗesu, sabida surar jikin Modibbo daya wulgawa ganinta, a hankali tace.

“Yah ilahi me hakan kenan”.

Sai kuma tayi saurin maida idonta ta lumshe tuno yadda ya ruggumeta, ranar da akayi bikin
gabatardashi, a hankali ta fesar da numfashin lokacin da ta fara tuno yadda ya yanke mata farce, da
kuma yadda ya rinƙa yi mata da ƙafarshi.

Baki ta ɗan tura a hankali tace.

“Ɗan neman mgn, haka kawai ranar ya hanani bacci, da yanayi da banma san na menene ba, gashi
yauma duk ya dabaibaye min jiki da idanu mutum kamar mai mayen ƙarfe a jikinsa”.

Sai kuma ta ɗanyi shiru tuno yadda tsulɓin sajensa yake da ɗadin taɓawa.

Kusa tsawo 7 minutes tayi tana jin ɗumin ruwa da ƙamshin na ratsata, kana daga bisani tayi wonka, tare
dayin burosh tare da al'wala.
Tana fitowa ta ɗan tsane jikinta da towel din dake jikinta, kana ta matso gaban dressing mirror, kuccalar
sirri kaɗai ta lakata tare da mulke jikinta baƙi ɗaya dashi, domin Allah ya sani ƙamshisa nayi mata daɗin
na fitar hankali.

Da sauri-sauri ta zaro wata doguwar riga After dress fari ƙal mai ɗan ratsin yellow.

Ta zura a jikinta tare da jan, zip ɗinshi, rolling kanta tayi da ɗan kwalinshi, tare da ƙara fesa jikinta da
wani turare mai ni'imtaccen ƙamshi kana ta shimfiɗa Sallah.

Magrib ta farayi, tare da yin azkar, tana idarwa, ta kumayi Isha, a hankali ta ɗan miƙe tare dayi shafa'i da
wutri.

Cikin sanyi ta zaro wata rigar bacci yellow mai ratsin fari fari da akayishi da zanen heart. Rigar mai
sulɓice, wace tsawonta iya guiwace.

Pant ta saka red color, sai kuma ta zira rigar bacci.

Wacce daga samanta duk net ne, kana wuyanta mai fadine, daga gaban rigan kuma igiyoyine a sarƙafe
haka yasa ƙirjinta ke a fili.

Sai ƙasa kuma dai-dai ƙugun shima net ne mai manyan buluka dan har cibiyarta zaka iya gani, dudu
tsawonta da kaɗan ya rufe cinyoyinta.

Ɗan kwallin After dress ɗin ta ware ta ɗaure kanta dashi.

Sai kuma ta dawo bakin gado ta zauna, tana mai shafa cikinta a fili tace.

“Wayyo Mommy na yunwa”.

Sai kuma ta ɗan hau bisa gadon da kyau jin yadda cikinta ya bada ƙugin yunwar.

sosai takejin yunwar to amman me zataci.

tsaki ta ɗan ja a fili tace.

“Dama nan na kawo abincin ɗazun nan.”

A hankali ta jawo blanket din dake bisa gadon tana fadin.

“Bana ma son cin abu mai nauyi yanzu nan, yanzu in mutum yayi garaje in zama katuwa kamar Aunty
Lami”.
Sai kuma tayi shiru jin kamar ana bubbuga ƙofa.

A hankali ta ɗan sauƙo bisa gadon tare da jawo After dress dinan ta zira a jikinta, kana taja igiyar dake
tsakiyar ta daure, ba tare da taja zip din ba.

Cikin sauri ta fito falon jiyo muryar Rahama na faɗin.

“Hello my Aunty kinyi bacci ne?”.

Da sauri ta ƙaraso bakin ƙofar tare da buɗe wa.

Murmushi tayi ganin Rahama tsaye riƙe da basket a hannunta ido ta lunshs tare da miƙamata basket din
cikin alamun ta fara bacci aka tasota tace.

“Gashi Didi tace, tun ɗazu take jiranku, baku sauƙo kunyi Dinner ba, har na fara bacci fa ta tadoni dole
wai in kawo muku”.

Amsar basket din tayu tare da sauƙe numfashi jin daɗi Allah ya sani yunwa na ƙwaƙularta.

“Toh ki shigo mana kika tsaya a baki ƙofa”.

Cikin ɗan lumshe ido Rahama tace.

“No ai zan koma”.

Da sauri tace.

“Aa dan Allah ki shigo, dama ina tsoro kwana ni ɗaya”.

Murmushi Rahama tayi tare da biyo bayanta.

Bisa 3 sitter ta kwanta tare da cewa.

“Yoh ina mijinki”.

Ta ƙare mgnar tana kallon wayarta da kira ya shigo.

Ita kuwa Khausar yi tayi kamar bata jitaba, basket ɗin ta aje bisa senter table.

Ita kuwa Rahama amsa kiran tayi tana ɗan kashe murya tace.

“Hello sweetheart bakayi bacci ba?”.

Sai kuma ta kalli Khausar tare da cewa.

“Toh ki ɗauka ki kai mishi mana, Didi tace dan Allah kada yayi bacci baiciba.
Ke kuma tace kisha yoghurt fruits ɗinan, wai ta lura kamar bakya son cin abinci”.

Murmushi Khausar tayi yayinda a ranta kuma cewa tayi.

“Tab Didi ai baki sanni bane, toh ni ko ciwo ma ai bai hanani cin abinci”.

Ita kuwa Rahama da sauri tace.

“Dan Allah dauki ki kai mai kada yayi bacci, in kinzo fita ki kashe min wutan nan”.

Kai Khausar ta ɗan juya tare da nufar bedroom da sauri kuma ta juyo jin Rahma na cewa.

“Nifa waya nakeson yi ke kuma kina dauke min hankali ki kai mishi mana”.

Cikin taɓe baki tace.

“Yah Salam kai Rahama wannan naci haka”.

Ta ƙare mgnar tare da juyawa ta ɗauki basket ɗin ta nufi falonshi.

Tana fita Rahama ta maida ƙofar ta rufe tare da kashe wutan kana ta dawo kan 3 sitter ta kwanta tana
maici gaba da yin wayarta.

Ita kuwa Khausar a hankali ta shiga falon.

Sai kuma ta ɗan tsaya ganin baya ciki.

Da alamu tunda ya shiga bai fitoba.

Ido ta ɗan jujjuya jiyo sassayan sautin muryarsa yana karanta suratul Mulki.

A hankali ta ajiye basket din kusa dana ɗazun, sai muka ta lumshe idanun tare da buɗe su.

A hankali ta nufi ƙofar bedroom ɗinsa sabida tunowa ba abinda yaci tun safe, wanda Didi tasa ta kawo
mishi ɗazunma gashi ba abinda yaci, .

Cikin sanyi ta tura ƙofar a hankali tare da kutsa kanta ciki.

“Hhhhhh Wow Yah Salam”.

Ta hade mgnar duk wuri ɗaya lokacin da idanunta sukayi arba da ƙasaitaccen ɗakin nasa da fidda wani
irin amintaccen ƙamshi da sanyi mai masifar ratsa jiki da zuciya, wanda ya haifar mata da wata iriyar
fitinenniyar kasalar datasa ta gaza karasowa ciki.
Ido ta zuba mishi hongoshi zaune bisa sallaya ya fuskanci ƙofar ɗakin bisa alama nanne alƙibla, wata
tattausar jallabiya ce royal blue mai masifar sheƙice a jikinsa, idonta ta liƙa sumar kansa, da zata iya
cewa yaune kacal karo na forko da ta ganshi babu hula, wani irin sheƙi sajensa da gemunsa zuwa gashin
kan nasa suke zubawa da ƙelli.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya ɗan ɗago idanunsa ya kalli ƙofar jin motsi alamun an buɗe ƙofar.

A hankali ya lumshe idanunsa jin numfashin sa yayi ƙasa.

Sai kuma yayi mata alamu ta shigo mana da

hannunsa.

A hankali ta kutso kanta cikin dakin.

Gefenshi ta ɗan matso tare da ɗan yin ƙasa da kanta.

Dai-dai lokacin kuma yazo ƙarshen suratul Mulk ɗin tare da shafawa, sai kuma ya ɗan juyo idanunsa da
har yanzu suke a fitine ya kalleta a saman lips enshi yace.

“Yah akayi?”.

Cikin jin sanyin tayis ɗin na ratsa tafin sawunta da ba takalmi tace.

“Didi ce, ta bawa Rahama abinci ta kawo wai dan Allah kaci kafin kayi bacci”.

A hankali yasa hannunsa ya shafa cikinsa tare da cewa.

“Toh kawo min shi nan”.

Toh tace kana ta juya

Idanunsa ya liƙa bisa mazaunanta da ke juyawa kasancewar ta daure ƙigunta da igiyar rigar ya ƙara
bayyana su.

Shyyyhhhhh ya fesar da sautin tare da tanƙwashe sawunshi.

Ita kuwa a hankali ta fita.

Jim kaɗan ta dawo da basket din duka biyu.

Cikin tsareta da ido yace.

“duka wannan ya zamuyi dashi”.


Tana ajiyewa tace.

“Ɗayan na dazune da na kawo maka ka ƙi cine”.

Cikin tsareta da ido yace.

“Toh ba ke bace kika sani bacci”.

Da sauri ta kalleshi sai kuma tace.

“Ni ɗin”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.

“Toh zauna ki samin min”.

Zaman tayi bisa Carpet ɗin dake shinfide gaban gadon.

Sai kuma yace.

“Buɗesu mu gani”.

Toh tace tare da fara buɗe wanda ta kawo ɗazun.

Jolof ɗin Couscous ne mai masifar kyau wanda yaji Vegetables da kifi sai kuma Yan bolls da ya Sha ƙwai
sai tururi suke bisa alamu kulilon masu riƙe zafine sosai sai kuma wani Bowl dake dauke da inabi da
Apple.

A hankali yace.

“Rufesu, buɗe wannan mugani”.

A hankali ta jawo basket din da Rahama ta kawo yanzu.

Kular ta buɗe, wani irin haɗiyar yawu tayi ganin wata iriyar danƙwaleliyar kaza da tasha gashi na
musamman sai tururi take zuba, ga Sultan chips dake zageye da ita, wanda yaji Vegetables sai wani irin
fitinennen ƙamshi yake zubawa, sai kuma robar dakekken yaji dake gefe bisa Mug din dake cike da
yughort fruits wanda yake ta zuba nason sanyi.

Plate ta ɗauka, tare da fara kokarin yagar kazar.

“Dagoshi duka kawai”.

Kai ta ɗago ta kalleshi da alamun duka kuma?

Kai ya gyaɗa mata, sanan nesa ta ɗago kazar dake bajewa don tayi lugub ta ajiye tsakiyar plate ɗin kana
ta zagayeshi da Sultan chips ɗin kamar yadda take cikin kular fork and knife ta sako mishi gabanshi.
Tare da ɗan tura mishi plate ɗin gabanshi.

Juyowa yayi da kyau ya fuskanceta kana ya tanƙwashe sawunshi, tare da ɗan tura plate din tsakiyarsu.

“Matso muci”. Ya faɗi yana sa fork da knife yana ɗam saluɓe tsokokin, sai kuma ya kalleta jin tana cewa.

“Na ƙoshi”. Fuskarsa ya ɗan tsuke tare da cewa “Toh me kikaci?”. A hankali tace.

“Bana jin yunwane”. Cikin nazartan yanayinta yace.

“Ƙarya kikeyi, kuma kina sane cewa ita ƙarya haramunce, kuma kin dai san duk ƙanƙantar ƙaryar da
zakimin zan gane ko”.

Shiru tayi tana ɗan wasa da yatsun hannunta ai kam tabbas ƙaryarce ta kuma tuna tabbas yana saurin
gano ƙaryarta.

Shi kuwa fork yasa mata a gabanta tare da cewa.

“Kin dai ga Didi ma fork biyu tasa, dan haka matso muci”.

Kai ta kuma jujjuyawa tare da cewa.

“Nifa bazan ciba”.

Da sauri yace.

“Ko ki matso ki ci, ko kuma ki tashi yanzun nan ki shiga Bathroom kiyita kaɗe ɗanwalinki daga nan har
asuba”.

Cikin tsoro ta zaro ido tare da kallonsa.

Girarsa ɗaya ya ɗaga mata tare da cewa.

“Yes ba kince a ƙoshe kikeba, ai wanda ya ƙunshi shi aikine ya dace yayi”.

Cikin sanyi ta amshi fork ɗin daya miƙa mata.

Shi kuwa bismillah yayi ya fara ci, sosai abinci yayi mishi ɗaɗi gashi ba yaji ko kaɗan, kallonta yayi a
lokacin ganin yadda take jujjuya fork din yayi a lokacin da ya kai lomata na uku.

“Wai meyasa ne kike da taurin kai, kinci kin tsaya kina jujjuya manyan idanu”.

A hankali ta kai fork ɗin cikin plate ɗin ta ɗan yagi farar tsokar kazar tare da ɗan haɗawa da chips guda
ɗaya.
Kana ta ɗago hannunta sai kuma ta tsaya tana jujjuyawa.

Gaba ɗaya lamarin a baƙon da ba'a zato yazo mata, wai itace zaune da Yah Modibbo yana cewa suci
abinci tare.

“Ok kaɗe ɗan kwalin kike so ko?”.

Da sauri ta jujjuya kanta ganin yadda ya tsareta da idonsa, yasa ta kai loman bakinta.

Sosai yayi mata daɗi ya kuma tada tsohowur yunwar da take ƙwaƙularta.

A hankali take sarrafashi a baki kana daga bisani ta haɗiye, cikin jin daɗi ta kalli robar yajin daya miƙo
mata.

“Amshi kisa yajin kici”.

Cikin ɗan sunkuyar da kai ta amsa kana ta buɗe robar tare da baɗa yajin a gabanta.

Cikin tsinkewar yawun ta fara ciki.

Shima cin yakeyi wanda tuni yaci kusan rabin kazar da Chips din.

Goran ruwan dake gefenshi ya dauka ya ɗan sha kana yaci gaba daci.

Saida yaci rabin kana, ya janye hannunshi.

Sai kuma ya kalleta ganin tun ɗazu data ajiye fork din Bata kuma ɗaukaba gane kallon da yake matane
yasa tace.

“Na ƙoshi fa”.

Kai ya jinnina dan yaga ta ɗanci mai ɗan dama, sai kuma ya ja Mug ɗin nan mai cike da yughort fruits, a
ƴan madai-dairan bowl dake cikin basket ɗin ya zuba tare dasa tea spoon a cikin, miƙamata ɗaya yayi
kana ya fara shan nasa.

Jujjuya tea spoon din tayi, sai kuma ta ɗan ɗiba ta kai bakinta.

Wow tace a ranra jin yadda ya wadatu da Banana da kuma Apple tare da inabi sai ɗan gogeghiyar
kwakwa, ga gardin Yughort da madarar gongoni.

Kallonshi tayi ganin ya gama shanye nashi ya aje bowl din sai kuma ta kalli natan ga mamakinta itama ta
shanye,
Mug din ya miƙata, tare da cewa.

“Sha da kyau ƙarbi wannan ɗinma”.

Ai kam ba musu ta ƙarɓa tana ɗan tura baki Allah ya sani bazata iya barin shiba.

Juyewa tayi kana ta fara sha.

Sassayan gyatsa tayi tare da gyara zamanta.

Shi kuwa Modibbo dake cije da lips in na ƙasa yana maiyi mata wani irin kallan mayata yana mai jin
zuciyarsa na raɗa mishi gudurin tabbatar da aurenshi, Allah ya sani bazai iya jumrewa abinda yakeji ba,
yanajin muradin tabbatar da ita a matsayin matar da J ɗinsa yayi mishi zaɓi haka nan yakeji bazai iya
jumre wannan yanayin na yau ɗinba.

Ita kuwa tattare plete din tayi da Bowl din ta zuba a basket ɗin kana ta yunƙura tare da miƙewa dasu a
hannunta ta nufi ƙofar fita.

A hankali yace.

“Ki kawo min phones ɗina”.

Toh tace kana ta fice, jim kaɗan kuma ta shigo, tare da miƙa mishi woyinsa da hannunta na dama
yayinda ta maida hannun hagunta kuma baya.

Amsa yayi tare da cewa.

“Bani wanda kika ɓoyen”.

Cikin kwaɓe fuska tace.

“Waya tace fa”.

Ido ya zuba mata cikin subcewar mgnar ya tsinci kansa da faɗin.

“Dake da wayar ai duk nawa ne”.

Baki ta ɗan tura tare da ƙara maƙe hannun a bayanta.

Miƙewa tsaye yayi tare da cewa. “Baneeyhh”.

Da sauri ta miƙa mishi tare da ɗan jan baya ganin yadda ya matsota.
Amsar wayar tata yayi tare da ajesu kan bed side drower, kana yace.

“Shiga nan kiyi al'wala kizo”.

Ya ƙare mgnar yana nuna mata Bathroom inshi.

Cikin sauri tace.

“Nayi sallah fa”.

Fuska ya kauda gefe tare da cewa.

“Na sani ai kije kiyi al'wala nace ko”.

Kai ta ɗan langwaɓar cikin rashin fahimtar manufarsa tace.

“Ina da al'wala”. Kai ya gyaɗa kana yace.

“Ok to shiga ki kuskure bakinki”.

Toh tace kana ta shiga Bathroom ɗin.

Shi kuwa ƙofar bedroom ɗin yaje ya rufe tare da zare key ɗin yasa a aljihunsa.

Tana fita shima ya shiga ya sabunta al'wala.

Yana fitowa ya ƙara fesa turaren wanda al'adarsa ce in dai zaiyi salla sai ya fesa turare.

Kan salla ya tsaya tare da cewa.

“Bismillah”.

Kai ta ɗan jujjuya tare da cewa.

“Banda hijabi”.

Da yatsarsa ya nuna mata gyalen after dress din jikinta tare da cewa.

“Ki rufu dashi”.

“Toh ai ni nayi salla ma fa”.

Cikin kauda kai yace.

“Eh na sani ai zamu ƙara ne dan samu lada mai yawa, ko bakya son ƙarin ladan?”.

Kai ta ɗan jinjina kana tace.


“Ina so mana”.

Da hannun ya nuna mata alamun to muyi salla.

Toh kawai tace kana ta dawo bayanshi kaɗan.

Tsayuwarsa ya gyara kana ya tada iƙama.

Nafila sukayi raka'a biyu.

Bayan sun sallamene ya ɗanyi tasbi, yayinda ita kuma take karanta Addu'o'i kwanciya bacci a lissafinta
daga ta koma ɗakinta sai kwanci.

A hankali ya juyo gareta wanda hakan yasa suka kasance gab da juna, kusan a tare zuƙatansu ke bugawa,
da sauri ta ɗan ja da baya.

Shi kuwa Modibbo cikin nitsuwa ya ɗan kauda kanshi tare da ƙara matsota har guiwowinsu na gogan
juna, ganin tana kuma ƙoƙarin matssawane ya ɗan juya fuska ba sauƙi kuma ba zafi yace.

“Tsaya mana”.

Ya ƙare mgnar tare da ɗaga hannunshi na dama tare da ɗaurawa kan goshinta zuwa saman kanta kaɗan
ya riƙe da babbar yatsarsa na kan jijinyan gefen goshinta na dama sai kuma yatsarsa ta tsakiya dake kan
jijiyar kanta na hagu.

“Hhhhhhhm”. Ta fidda sautin daga ƙasan zuciyarta sabida wani irin yam taji tsikar jikinta da zuciyarta sun
amsa a tare.

Shi kuwa Modibbo lumshe idanunsa yayi sabida yadda yaji jijiyar goshinta na harbawa haka yaji A ɗinsa
ya harba da masifarƙafi hankali ya fara karanta Addu'ar da Manzon Allah ya koyarwa maza danyi a
dararen forkonsu.

*“Allahumma inni As'aluka min khairi ha wa khaira ma jabaltaha alaihi, wa a uuzu bika min sharri ha wa
sharra ma jabaltaha alaihi".*

Ma'ana

"Ya Allah ina roƙon ka Al'khairin ta, da Al'khairin da ka Halicce ta akan shi.

Kuma ina neman tsarin ka daga Sharrin ta, da kuma sharrin da ka Halicce ta da shi ko akan shi.

Amfanin Addu'ar

Idan ka yi ta.
Allah zai cike Soyayyar da ke tsakanin ku 100%. Zai tsare Shaiɗanu da Miyagu daga cutar da zaman Auren
ka da ita da sauran su...

*Iyaye muke koyawa yayanmu maza ita musamman in sun tasa dan tana da mahimmanci a rayuwar aure
kuma mazan ba kowa ya iya ba*

A hankali ya koma baya kaɗan ya jingina da jikin gadon,.

A hankali ya buɗe idanunsa da ke lumshe tare dasa hannunsa ya ɗan jawo bowl ɗin fruits din dake
gefenshi sai kuma ya ɗan kalleta ganin alamun zata miƙe yace.

“Ina zakije?”.

“Zan tafi in kwanta bacci nakeji”.

“Zo ki zauna kiyi karatu tukuna inji bitar haddarki”.

Da sauri tace.

“Ai ina muraja'a a gida”.

Ba tare da ya kalletaba yasa hannunsa na dama ya riƙo hannunta tare da jawota, dole ta zauna gefen
damanshi.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya ɗan murza tafin hannuntan dake cikin nasa kana a hankali yace.

“Bismillah kiyi muji”.

Ɗan sunkuyar da kai tayi kana tace.

“Nifa bacci nakeji”.

Matse hanun nata yayi da ɗan ƙarfi har saida ta ɗanyi ƙara.

Hararanta ya ɗan yi tare da cewa.

“Yaushe makika tashi a bacci, baccin awa huɗu cib fa kikayi, dan haka ba bacci ba kam sai dai ko tunda
kuka gama makaranta kin daina muraja'a ko? Shiyasa kike tsoron yi”.

Da sauri tace.

“Wlh inayi fa”.


“Toh kiyi mu ji, in kin bata ki ƙwana kaɗe ɗankalinki”.

Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa kana tace.

“Wacce surar zanyi maka?”.

Yana ɗan matse cinyoyinsa yace.

“Suratul Khaf”.

Cikin sauƙe numfashi ta ɗan yi gyaran murya tare da yin basmala kana ta fara jam ayoyin”.

Wani irin amintaccen nitsuwa salama haɗida shauƙi mai zafine ya fara ziraro mishi, wanda hakan yasa ya
ɗan ƙara matsota da kyau, ita kuwa cikin fesar da numfashi taci gaba da kawo aya ta uku.

“‫مكشين فيه ابدا‬.

Sai kuma ta ɗan yi shiru tare da jan numfashi, tana mai jin wani irin fitunannun abubuwa da idanunsa ke
cusawa nata idanun da ya tsare da kallo, cikin fuzgar numfashi taci gaba da aya ta huɗu.

shi kuwa a hankali ya fara cusa hannunshi cikin hannun rigar ta, wanda haka yasa ta yunƙura da ƙarfi, ta
miƙe tare da nufar ƙofar da ɗan sassarfa.

Cikin wani irin rawan jiki ya miƙe tsaye tare da bin bayanta.

Cikin sauri ta juyo tana kallonshi lokacin da ta isa bakin ƙofar da taja da karfi dan buɗewa, jinsa a
garƙamene ya sata zuba mishi idanu.

Shi kuwa a hankali yake takowa yana nufin gareta, wanda hakanne yasa ita kuma fara ja da baya da
baya.

A hankali ya ƙaraso gaba da ita, sai kuma ya ƙara taku biyu zuwa uku sai ya zama, babu sauran rogowar
fili tsakaninsu, cikin wani irin baƙon yanayin da zuciyarsa ke cusa masa da kuma gaza yiwa zuciyarsa da
gangarjikinsa tawaye, ya sa hannushi na dama ya zagayo ƙugunta tare da jawota ya ruggume ta a jikinsa.

A tare suka sauƙe numfashi ita na tsiro shi kuma na tsananin jin tafasar jini sha'awa.

sai kuma ya ɗan sunkuyo da kanshi, cikin wani irin fitinennen yanayi yake shaƙan ƙamshin fitinennen
kulaccar sirri dake hautsina mishi nitsuwa da kauda haƙurinsa.

cusa kanshi yayi tsakanin wuyanta da kafaɗarta.


Shuuuuuhhhh". Yaja numfashi sai kuma ya ɗan sa hannunsa na hagu ya ja igiyar dake ɗaure akan
ƙugunta daya taimakawa riga.

Da sauri ta rufe idanunta jiki da murya na rawa tace.

“Hhhjjj Uhhmmmmm zan tafi”.

A hankali ya ɗan sa hannunsa bisa kafaɗunta tare da ware wuyan rigar ya fara yin ƙasa dashi.

Yah Salam.

Shine abinda ya furta a saman lips enshi lokacin da yaji santsi da sulɓin fatar jikinta haɗida taushinsa da
yasa jikinsa saki wani irin gigitaccen kerma murya can cikin naƙoshinsa yace.

“Ih hiii in inaha Zaki tafi, da yafi ɗakin mijinki”.

Sai kuma ya ƙara murza rigar da kyau yayi kasa dashi har zuwa kan cikinta.

Ita kuwa Khausar idanu ta zazzaro da iyakar iyawarta da mgnar zuci.

Shin Modibbo lfya yake kuwa, yasan me yakeyi kuwa.

Jikinta ya tsananta rawane a lokacin da taji yana murza after dress ɗin yana ƙara yin ƙasa dashi da ƙarfi
ta rumtse idanunta lokacin da taji rigar ta sule sulub tayi ƙasa.

Ƙanƙame jikinta tayi tare da cewa.

“Innalillah Malam ka cire min rigata”.

Cikin gigitaccan yanayi ya ƙara sunkuyowa tare da cusa kanshi tsankanin wuyanta, yana mai zura...

*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n
nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai
sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan
mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in
kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a
banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account
no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na
faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki
kenan* in dai kayan mata kikeso ko na infection ta wannan number zakimin mhn 08069423567

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito
miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar
infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita
tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a
saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda
yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin
san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo
kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567 sai ki turo min shaidar biyanki,
domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan
ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah
zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce
dai GARKUWAR MA'AURATA.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*
SAKAYYAH

57

*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n
nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai
sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan
mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in
kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a
banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account
no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na
faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki
kenan* _indai maganin mata kikeso ko mgnin infection ko kuma kayan ƙamshi su turarukan wuta humra
kulacca to ta wannan number zakiyi min mgn a WhatsApp 08069423567 shine na masu sayan kaya_

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito
miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar
infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita
tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a
saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda
yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin
san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo
kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567 sai ki turo min shaidar biyanki,
domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan
ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah
zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce
dai GARKUWAR MA'AURATA.

*Littafin Sakayya dai na kuɗi ne in dai har kinaso to ki biya ki karanta cikin aminci da salama 1k ne kacal
0661110170 Gtbank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number
09097853276, in tura Miki ki karanta abinki salamun salaman, ba haƙƙina a kanki dan in dai baki biya ba
kika karanta to na satane kuma na sata na Allah ya isa ne ato*

23

idanunsa dake zazzago da wutar fitina ya zira cikin, tsakanin igiyoyin dake sarƙafe dai-dai kan ƙirjinta,

hannunsa na dama ya ɗan ɗago tare dayi mishi masauƙi kan igiyoyin.

Zuwa yanzu gaba ɗaya jikin Khausar karkarwa yake tamkar mazari ta wani zazzaro idanunta kamar zasu
faɗu ƙasa sabida tsanananin kaduwa.

Shi kuwa Modibbo na mijin duniya, a hankali ya cilla igiyar rigar tata bisa kan gado, sai kuma ya ɗan fara
cusa yatsunshi tsakankanin sarƙafaffun igiyo, wanda cikin hakanne yaji yayi karo da caɓɓullenta dinta na
gefen hagu.

Wani sabon gigitaccen kemar da ta ingiza A ɗinsa yayi miƙewar yan bori.

Ne ya sashi saurin ruggumeta tsam a jikinta.


Cikin rawan jiki da sauri jin sawunshi na shirin butulcewa ɗaukar nauyinshi gangar jikinsa ne yasashi
direta kan gado tare da sa kanta bisa pillow Wanda ya ɗan zarta kaɗan dan har bayanta na kan pillow
haka yasa wuyanta miƙewa.

Wasu irin tagwayen numfarfashi tsoro masu haɗe da gigita Khausar ta fara sauƙewa kai kace zata samu
da tsananin ƙarfi ta rumtse idanunta lokacin da taga Modibbo yayi mata runmfa, ƙara maida numfashin
tayi da karfi wanda yasa ƙirjinta yin up and down.

Cikin salo mai haɗe da ficewar tunani, Modibbo ya manna bakinshi kan wuyanta, a hankali ya zaro
harshensa tare da mannashi kan forkon wuyanta yana mai lasa yana sama dashi har kan habarta, sai
kuma ya fara yi mata wasu hot kiss masu sauti.

Scht! Schtttt da sauri ta juya kanta gefen hagu.

Sai kuma tayi maza ta juyashi gefen dama jin ya maida kanshi gefen hagun.

Kar-kar haka take karkarwa da numfashin wani na korar wani.

Shi kuwa Modibbo cikin tafiya duniyar da ya daɗe yana fatar rissarta da samun ziyaryarta, yaja igiar
gaban rigar baccin ta da karfi.

Ai kuwa sai gashi gaba ɗaya ta ware ƙirjinta ya fito fili.

Caɓɓullenta tade cike pam sun na tsaye cirko-cirko suna zuba wani irin fitinennen shekine yayi wa kallon
Ra'anul ayn.

Wani irin sauti mai kashe jiki da zuciya ya saki lokacin da yayiwa hannunyensa Kekkyawan masauƙi a kan
caɓɓullen nata da taɓasu yasa numfashinsa ɗaukewa.

Ita kuwa Khausar cikin wani irin gigitaccen yanayi ta yunƙura da karfi, sai kuma ta koma lip jin yadda ya
maida ita da ƙarfi ya danneta da faffaɗan ƙirjinsa.

Cikin tsananin ruɗu da tsoro tace.

“Innalillahi Malam me haka, me zakayi min?".

Can sama yake iya jiyo murya tata, haka yasa cikin rawan murya yace.

“Abinda kikayi min alƙawarin cewa ranar Laraba zaki bani, shi nakeso ki bani”.

Cikin tsoro tace.

“Ni kuma? yaushe nayi maka alƙawarin”.


Yanayiwa cɓɓtl ziraya na musamman yace.

“Ke mana, haka kika cemin cikin mafarkina”.

A hankali tayi wani irin fitinennen miƙa mai haɗe da kasala gami da mutuwar jiki, sabida jin yadda yake
sarrafa mata ƙirjinta ya fara sauƙo mata da wasu sabbin ministoci fitina.

A hankali ta cusa yatsunta cikin sumar kanshi lokacin da taji ya manne lips enshi da nata.

inabin da tun ɗazu ya sasu cikin bakinshi ya ɗan.

gyarawa zama sai kuma ya dawo da hannunsa sama ya tallaɓe kanta, a hankali ta buɗe idanunta lokacin
da taji ya cusa harshensa cikin bakinta, yana juyawa tare da ɗan murza mata inabin kan harshenta cikin
wani irin salo mai masifar gigitarwa da gusar da nutsuwa ta saki sautin

Ashhhhhhh. Ta furta da ƙarfi cikin wata kasalalliyar murya mai cike amsar sabbin saƙonninsa ta kai
harshenta da nufin kama inabin da takejin yana murza mata bisa harshen.

Cikin sauri ya kauda inabin wanda haka yasa cikin akasi tayiwa tattausan harshensa wani irin amintaccen
kamu mai gigita tunani, laushin sa da sanyin gami da garɗin ruwan inabin da ya ɗan gasa ne yasa tayi
mishi wani irin fitinennen laluma da fara tsotsa tamkar wacce ta samu lollypop.

A tare suka matse jikinsu sabida ni'imtaccen ƙamshi da sanyi da yayi musu cikekken ƙawanya.

Wani irin raunataccen numfashin mai shirin fidda hayyaci Modibbo yana tare da ƙara tallabe kanta da
kyau, cikin salon ƙwarewa da alamun laƙanta da kuma karantar yadda ake sarrafa mace ya sakar mata
ragamar rayuwarsa.

Ita kam Khausar kissing ɗin shi take tamkar zata haɗiye harshen nasa, yayin da shi kuwa yake ɗan ƙara
gasan ruwan inabin yana ɗan biyo harcensa tana laluma da tsotsa ta haɗiye.

Uhmmmmmmm, hmhyyyyy shhyyyyyyy. Shine abinda yake fiddawa daga cikin zuciyarsa a jere a jere
kuma, ji yake yadda take zuƙan harshensa haka M yake ƙara haɓaka da bayyana matsananciyar
zalamarsa.

Ita kuwa Khausar wani irin fitinennen runguma tayi mishi sabida jin yadda wani abu ke mata yawo cikin
mararata tamkar ana zira mata wani abu mai ƙaiƙayine.
Yayin da bakin Caɓɓulenta suka fara yi mata wani irin fitinennen ƙaikayi.

Shhhhyyyyyyt!!!Ashhhhh Taja sautin da karfi kamar numfashinta na shirin barin gangar jikinta.

Lokacin da taji ya janye harshensa.

Sai kuma tayi sauri riƙo hanunsa tare da ɗaurawa kan karjinta.

Shi kuwa Modibbo shu'umin na miji, hannunshi ya ɗan janye tare da maidashi gefe da gefen cikinta ya
fara yi mata tafiyar tsutsa mai tafiya da nutsuwa,

yanayi yana murza rigar jikinta har yayi nasarar cireta baƙi ɗaya

Cikin ƙarfi ta rumtse idanunta sabida wani irin mayataccen ƙaiƙayi mai masifar nacin da taji asaman
Caɓɓulenta suna ƙarayi.

Cikin wata irin yar raunatacciyar murya ta saki wani irin maraitaccen kuka tare da cewa.

“Malam”.

Wani makirin murmushi yayi fahimtar yarinyar ta fara muradinsa kusantar wani sashinta ne yasa a
hankali ya ɗan sunkuyo kanshi dai-dai kunnenta murya a narke yace.

“Yah akayi?”.

Wani irin saurin juyawa gareshi tayi tare da cewa.

“Ƙaiƙayi”.

Ta ƙare mgnar tana matse jikinta, shi kuwa Modibbo cikin tsuma da jikinsa keyi ya sunkuyo kanta cikin
tsanananin ƙwarewa da iya birkita lissafin duk wata lafiyayiyar mace yayi mata magana cikin raɗa.

“Meh ya yake miki ƙaiƙayin”.

Cikin wani irin azabebben yanayi na tsananin buƙata ta jawo hannunshi a hankali ta ɗaura kan ƙirjinta
kana cikin sanyi tace.

“Nan ne”.

Ta ƙare mgnar da ita kanta bata san iya adadin yadda takejin abubuwa na wanzuwa a jikinta abubuwan
da tunda suka fara ɗirka mata Ingantattun magunguna da aka saya mata wurin AYSHA ALIYU GARKUWA,
lokata da dama suna ziyaryan tata, Amman na yau yafi na duk lokutan baya domin na yau mai fidda
hayyacine.
Shi kuwa Modibbo a hankali ya janye hannunshi zuwa kan lafeffen cikinta cikin hudar cibiyarta ya ziyara
ƴar ƙaramar yatsarshi yayin da sauran yatsun kuma yakeyi mata wani irin fitinennen tausa bisa mararta.

Sai kuma ya sunkuyo kanta a hankali yace.

“Nan ne yake miki ƙaiƙaiyi?”.

Cikin jujjuya kai da murza sawunta Muryanta a narke tace.

“Ƙirji nane fa yake ƙaiƙayin”.

lip ɗinta ya ɗan lasa kana ya kalleta ido cikin ido murya can ƙasa hankali ya furta.

“ In ƙaiƙaiya miki ne?”.

Kai ta rinƙa gyaɗa mishi tare da cewa.

“Shyyuuut ehhhyy”.

cikin wani irin fitinennen yanayi A ɗinsa yayi jiki na rawa yasa hannunsa ya kamo ƙasan jallabiyar sa tare
da zarewa ya cillashi gefe ya rage gashi sai farin boxes sa dake zuba ƙamshi.

Wani irin fitinennen numfashin ya kuma fesarwa a karo na barkatai sabida yadda sanyin A.C da kuma
sanyin garin ya ratsashi.

A hankali ya kife tafin Hannunshi na dama kan caɓullenta na hagu wani irin zillo tayi lokacin da taji
yayiwa Saman ƙirjinta wani irin amintaccen sallama, zir-zir taji wani abu na ratsata.

“Oohhh”.

Ta faɗa da ƙarfi lokacin da taji ya manna bakinshi kan ɗaya cɓl nata.

Far-far haka jikinta ya tsananta rawa, yayin da zuciyarta kuma ya fara bada sautin Dib-dib cusa hannunta
tayi cikin sumar kanshi tare da farayi mishi wani irin cakuɗa mai gigita lissafin duk wanda aka yiwa...

Shhhhyyyyyyt uhmmmm sune sautin dake tashi a tsakaninsu.

Musamman Modibbo so yake ya buɗe idanunsa amman ji yake sun mishi nauyi, ita kuwa Khausar
ahankali ta fara magana cikin Shesh-sheƙan fitinar da yake sauƙar mata.

“M.... AMa... Mal. Mal”.

Ina ta gaza faɗan abinda take son faɗan saboda yanda muryanta ya shaƙe...
A gigice ya taso zaune.

Da sauri ta biyoshi tallaɓeta yayi tare dasa hannunsa ya fara murza boxes ɗinsa dan jin yanda A ɗinsa
yayi masifar bayyana larurarsa.

Kasan cewar a zaune suke bata fahimci yanayi da yake cikiba, ta dai jin fatarta ta manne da fatarsa.

Shi kuwa Modibbo cikin fitar hayyaci jin yau shine a manne jikin da yake cike da muradi tsawon
shekaru,yasa hannunshi ya kamo nata tare da ɗaurawa bisa..ɗinsa dake ta zalama.

Wani irin gigitaccen ƙara ta saki da kasalalelliyar muryar ta mai ƙara ingizashi tace.

“Malam! Mahalam Mhhhaalam”.

Sai kuma ya kwantar da ita tare da ɗan ronƙofowa kanta, a hankali ya manna hannunshi bisa mararta.

“Shyyhhhhhjyyyo". Ya saki makirin sauti mai ɗauke da sarƙewar numfashin lokacin da yaji hannunshi na
kan wani tattausan... Mai santsi da sulɓi, haka yasa bai san lokacin da ya fara murza pant ɗin ba.

Cikin sauri ta riƙo hannunsa tare da tasowa murya na rawa tace.

“Innalillahi Malam ka bari”.

Cikin muryar da bata taɓa zato ko tsammanin ɗan adam nada irinshi ba yace.

“Noo *Minha Vidaa* kii bar mijinki ya raɓeki, ki samu lada kada ki juya min baya kin san ba kyau ko ai”.

Cikin sauri tace.

“Toh me zakayi min?”.

Cikin fesar da wani irin raunataccen numfashiyace.

“Minha zan kusanceki ne, ki aminci ki bani kyautar budurcinki ki kwana cikin amincin Allah da yardar
mijinki,”.

Zuwa yanzu kam tsoron ya fara kauda duk wani feelings din daya sakar mata cikin sarƙewar murya tace.

“Wallahi ina tsoro kayi haƙuri”.

Ta ƙare mgnar tana ƙoƙarin juya mishi baya.

Hannunta ya kamo tare da ɗaurawa bisa kafiyarsa.

Tare da haɗewa da hannunsa ya matsa matse murya na karkarwa yace.


“Kada ki juya min baya in dai bakya son fushin Allah, ai kin san muddin mace ta juyawa mijinta baya
bada izininsa ba, tayi laifi, in kuma kikayi min laifi na kwana da fushinki kin san cikin fushin Allah da
tsinuwarsa data mala'iku zaki kwana ko?".

Wuru-wuru ta farayi da idanunta da suka sake girma suka cika da tsoro kai kace ranta yace ta bashi.

Shi kuwa Modibbo cikin wani irin yanayi na kiɗima yake ƙara shigewa jikinta.

Cikin rawan murya tace.

“Kayi haƙuri, ka barni mana bazan iya juran wannan al'amarin ba Yah Mu'allim lamarin yamin nauyi”.

Shi kuwa Modibbo cikin yana yin da bazai iya jumrewa ba yace.

“Me zan bari?,in bar haƙƙina a kanki zaki iya dakon zunubin?”.

Murya cike da rauni tace.

“Ka yafe min”.

Cikin sanyi da hikimar ƙara rikitata yace.

“Bazan iya yafewa ba Minha vidaa, sai dai in zakiyi dakon zunubin”.

Cikin rawan murya tace.

“Bazan iyaba”.

Zameta yayi ya kwantar da ita kana murya can ƙasa yace.

"Ni kuma J ya bani tabbacin nagartarki da biyayyarki, banyi zaton tirjiyar samun haƙƙina a kanki ba, ko
baki san inada haƙƙi a kanki bane?".

Kuka mai cike da rauni da tsoron abinda bata taɓa fuskanta ba ta farayi a hankali, tayi mgna cikin rauni
tace.

“Na sani”

A hankali ya miƙo hannunsa, ya kamo hannunta ya jawota jikinsa.


Wani irin rugugi akayi mai ƙarfi, tare da walƙi mai jan haske wanda ke nuni da hadarine ya gama
gangami a garin.

Cikin tsoro da razana ta faɗa jikinsa tare da rungumeshi gam-gam, ɓarin da jikinta keyi ya tsananta.

Shi kuwa Modibbo wani irin lumshe idonsa yayi kana yasa tafin hannunsa duka biyu ya tallabo fuskarka,
goshinsu ya haɗe wuri ɗaya, tsinin hancinsa ya goga kan nata tsinin hancin.

A hankali yace.

“Na gama gamsuwa cewa duk duniya, kece sirrina.

Dole ki zamo suturata, kamar yadda nima zan zama suturarki, kamar yadda Allah (S.W.A) ya fadi”.

Ya ƙarashe mgnar yana manna

Bakinshi da nata,

lips ɗin ta duka biyu ya ɗan kamo ya tsotsa a hankali.

sannan ya sake, kiss ya manna mata a goshi kana ya manna mata a tsakanin wuyanta da kafaɗarta,
harshensa ya zaro ya manna bisa wuyanta yana ɗan lasawa, tare dasa hannunsa yana murza ƙirjinta da
ankilta Caɓɓullenta.

hannunshi yasa ya kwantar da ita, kar-kar haka yaji jikinta na rawa,

hannunshi yasa ya danna wani abu dake jikin gadon.

Sai ga wani tattausan labule fari ƙall ya sauƙo daga saman rumfar gadon, yayi wa gadon ƙawanya wanda
yasa duhu mamaye su.

A hankali ya ronƙofo kanta, cikin sanyi murya can ƙasa yace.

“Meyasa jikinki keyin rawa?”.

Cikin rawan murya tasa hannu ta riƙo damatsan hannunsa a hankali tace.

“Tsoro nakeji Yah Mu'allim ina jin tsoron”.

Kanshi ya maida bisa lafeffen cikinta, cikin hudan cibiyarta ya zira harshensa,

da sauri ta rumtse idanunta sabida wani irin masifeffen daɗin da taji yana ratsawa cikin hudan cibiyarta
sai dai tsoronta kuma ƙara hauhawa yakeyi.

Hannunsa ya miƙa ya ɗaurasu kan ƙirjin ta.


yatsunta ta cusa cikin sumar kanshi, tare da fidda sassanyan sauti.

“Ahhhhhhh Umhhhhh”.

Zaro harshensa yayi kana ya fara lasan fatar cikinta tare da kissing cikin.

har zuwa sama.

A hankali ta buɗe bakinta sai kuma ta kasa yin magana saboda, yadda ya zura harshensa cikin bakinta.

Wani irin fitinenne kiss tongue to tongue yake yi mata mai, rikitarwa.

Hannunshi yasa bisa ƙirjinta ɗin ta yanayi mata wani darasi na musamman kanta ta fara jujjuyawa.

A hankali ya zare harshensa ya dawo dashi bisa ƙirjinta,

harshensa ya manna kan. ɗin ta ya, ya fara yi mata wani irin yanayi mai rikitarwa.

Wani irin fitinenne yanayi yaji jikinsa nayi tare da bayyana tsananin muradinsa, tamkar zai kasance da
babu.

Hannunsa ɗaya kuma yana kan ɗaya kirjinta.

Yana matsawa,

gaba ɗaya ya gigitata, ya hautsuna mata lissafi, jikinta yayi weak sai tsuma da yakeyi.

A hankali yayi ƙasa da hannunshi yana shafa cikinta har zuwa kan mararta.

wani irin zillo tayi tare da buɗe baki tace.

“Washhhhh, haahhyyyy”.

Da sauri yayi sama da hannunshi yatsarshi ya zira mata cikin bakinta.

Wani irin cabke yatsar tayi ta fara tsotsa sabida yadda ya rikita mata, lissafi.

A hankali yake murza jikinta daga sama.

Yanayin ƙasa.

A hankali yake shafa ta, yanayi mata wani irin salo.

Kerma jikinta ya fara,

a gigice take jan numfashin tare da tsotsan yatsarshi, hannunta kuwa na bisa wuyansa.
Zare yatsarshi yayi daga bakinta,

kana ya tashi zaune, sabida wani irin masifeffen feelings da yakeji tamkar zai ɗauki ransa,

Moddibo ɗin shi sai wani irin fitinarsa yakeyi tamkar zaici babu.

A hankali ya miƙe zaune

Kana ya matsota sosai.

Gyara zamanshi yayi ya jingina da kan gado, hannunta ya kama, tare jawota jikinshi.

Jiki na rawa manna mata A cikin tafin hannunta,

wani irin zabura mai cike da razani,kana da tsoro suka risketa lokacin ɗaya, murya da jiki na rawa tace.

“Wayyo Yah Mu'allim barni sakeni".

Cikin wata irin murya mai rauni yace.

"Uhhhahhhhhhhh. Minha”.

hannunsa yasa ya haɗe da nata ya matse da tafin hannunta.

Da karkarwa hannunta ya farayi, ganin hakane yasa ya sake hannunta, yajawota ya kwantar da ita
rigingine, a hankali ya sunkuyo da kanshi ƙasa.

Wani irin masifeffen ƙamshi turaren miski ne mai ɗan karen daɗin shaƙa ya bugi hancinsa, cikin rawan
jiki ya manna bakinshi bisa jikin ta.

wani irin yunƙura tayi tare dasa tafin hannunta ta damƙi damatsan hannunsa da ƙarfi.

cikin wata iriyar fitinenneyar murya tace.

"Ahshhhhhhhhyyy Yan Mu'allim. marata zata fashe".

Ta ƙare maganar tana maijin wasu abubuwa masu tarin yawa na yawo a mararta suna sauƙa alamun
sunada muradin abokin tarayya.

Hannunshi yayi sama dashi dai-dai kan marar tata,

Ya fara ɗan shafawa Yayin da ɗaya hannun yana can sama kan ƙirjinta.

Wani tsalle yakeji *A* ɗinsa ta nayi babu sassauci ji yake tamkar zai tsinke yayi ƙasa dan azabar fitina.
Ita kuwa Khausar tuni hawaye keta shatata a fuskarta,

murya na rawa kana jiki na ɓari take cewa.

"Yah Mu'allim ina tsoro ni dai ka barni, bazan iya ba. Ka sakeni zan koma ɗaki na wannan al'amarin ya
wuce tunani bazan iya ba kayi haƙuri ka yafe min sai na girma”.

Cikin rawan jiki da gigita, ya zaro harshensa daga inda yake da tuni take liking mai ƙamshi.

yatsarshi yasa ya ɗan shafa kana ya yi sama da kanshi.

Cikin sanyi yai mata rumfa da faffaɗan ƙirjinsa kana ya kawo bakinshi dai-dai kunnenta a hankali murya
na rawa yace.

“Afwan bazan iya haƙuraba, zan iya rasa rainafa Minha vidaa kotu haƙuri. Ki nutsu zan biki a hankali.
Please ki bani haƙƙina kada ki tauyeni dan bazan iya yafe mikiba”.

Cikin kuka tace.

"Ina tsoro".

Kanshi ya cusa a wuyanta tare da cewa.

"Na sani, nasan baki taɓa yiba Khausar na sani, amman zan biki a hankali ai dai kin san wannan shine
auren ki, ko J bai gaya miki cewa dole zamu kasance hakaba".

Cikin sauri tace.

“Eh ni dai bai gaya minba kuma bansan cewa haka ake kasance wa ba”.

Ɗan matseta yayi tare da cewa.

“Amman ai an karantar daku haka ”.

A hankali tace.

“Eh amman dai ina tsoro Ni bazan iya ba”.

Cikin Tausayawa da yanayin dake fusgarsa yace.

“Bazakiji zafiba”.

Ya ida maganar tare mata rumfa da jikinsa,

Ya kuma nufi mallakinsa da surarsa da bai taɓa sanin zarrarsa ya kai hakaba sai yau, nufar muhallisa yayi
tare da cewa.
_BISMILLAH ALLAHUMMA JANNIBNAL SHAIƊAN WA JANNIBAL SHAIƊANA MARAZAƘTUNA._

Wani irin rumtse idanunta tayi da ƙarfi jin wannan abu mai ban tsoro yana neman inda zai ratsa a jikinta,
murya a hargitse tace.

“Wayyo Yah Mu'allim. fitsari nakeji, zanje inyi fitsari”.

Ina zuwa yanzu bazai iya sahirta mataba burinsa ya tabbatar da aurenshi a kanta.

wanda hakan yasa ta zurma wani gigitaccen ihu mai sauti dai-dai lokacin kuma aka saki wani irin
razanenne tsawa mai firgitarwa da walƙiya mai masifar haske da ƙyalli.

Sai kuma aka kece da ruwa tamkar da bakin kwarya.

Wani irin karkarwa da tsuma jikin Modibbo yakeyi,

burinshi ya rabata da wani abu mai kima da daraja wanda ko wanne Namiji yake bukatar samu a irin
wannan lokacin kana ya tabbatar da ita cikakkiyar mace, ya kusanci duniyarta ya medata cikekkiyar
matarsa abar jin daɗinsa ta zama cikekkiyar suturarsa ya zama cikekkiyar sutarta, shiyasa cikin fitar
haiyaci ya baƙonci rayuwarta da tashi rayuwar ta da masifar ƙarfi da gigin sha'awa.

Ƙanƙameshi tayi da masifar ƙarfi tare da yunƙurowa ta cusa kanta cikin ƙirjinsa sabida wani irin
azabebben zafin rabuwa da abu mafi kima da daraja arayuwarta wacce ko wacce ɗiya mace da takai
Kimarta gidan miji take fuskantar wannan raɗaɗin ji take tamkar yana shirin ɗauke ranta ne kar-kar haka
jikinta ke rawa,

Wata fitinenneyar zufa ce ta karyo mata duk da sanyin da ake ga kuma Ac.da sanyin damuna.

A gigice tace.

"Innalillahi wa innailaihi rajiun.

Wayyoooooooo Allah na Wayyo Mommy na Wayyo Hajja Nana, Wayyo Haiydar na Wayyo Ummi na,
wayyoooooooo Didi,Wayyoooo Asma'u Yah Mu'allim zai kasheni, Ummi kizo ki ceceni, kice ya barni kada
ya cutar da amanar M.Jameel Wayyyyyoohhhh Yah Jameel wlh na fasa”.

Dai dai lokacin kuma Ummi da Hajja Nana da Innayi dake hira akan lamarin Hajia Bunayyah.

Suka kalli juna cike da ƙaruwar jiyo murya Khausar sabida sautin dare kuma da iyakar ƙarfinta take
kukan,Cikin sanyi Ummi tace.

“Kai wlh mace kam ma abar tausayi ce”.

Hajja Nana da jikinta yan ɗanyi sanyi tace.


“Atoh ba ita tace shi take soba, yoh dama wannan tsohon tuzurun ai sai yadda hali yayi ni dai fatana
kada ya yalgacemin jika”.

Innayi kuwa kanta kawai take juyawa kana cikin sanyi tace.

“In sha Allah ba komai”.

Ummi kam miƙa wa tayi ta fito falo haka nan tausayin Khausar yasa idonta zubda hawaye.

Shi kuwa Modibbo Jin yadda take zurma ihu da kiraye kirayene yasa ya manne bakinshi da nata lips ɗinta
duka biyu ya haɗe ya fara yi musu wani fitinenne tsotsa tamkar zai tsinkesu ya haɗiyesu.

Kuka tasa da ƙarfi tare da soma girgiza mashi kanta da takeji tamkar ya kumbura ne.

Wani azabebben ihu ta kurma da iya ƙarfinta, wanda badon ruwan da ake sheƙawa ba, da rugugi da
rabin masararutar Mouley duk sai sun jiyota.

Rahama kuwa da bata jima da fara bacci ba.

A gigice ta tashi cikin zazzare ido ta miƙe tsaye.

Sai kuma ta koma ta zauna jikinta na rawa jin muryar Khausar tana.

“Innalillahi Didi zai kasheni, wayyo Allah Mommy na, wlh na fasa cika wasiyar Yah Jameel dan Allah kuzo
kada ya kasheni”.

Shi kuwa Modibbo cikin duniyar daya faɗane.

Ya ratsa kanshi cikin jikinta yana bin kilatacciyar hanyar yana wucewa birnin fatauci, tare da kekkyawan
fatauci da lafiyar ingarmansa na cikekken namiji tare da ambaton sunan Allah.

"Hhhhhhhhhh, Alhamdulillah, Yah Salam subahanallah! Subahanallah!! Allahu Akbar ohh sorry Im so
sorry Yah Mu'allima Lelelwa.

Afwan Larki J Allah ya maka albarka Allah yayi maka SAKAYYAH da jannatul firdausi J ka gama min komai
na rayuwa ka samamin abu mafi daɗi da daraja".

Sune kalaman da yake iya maimaitawa da alamun a gigice yake.


Iskar damuna mai sanyi da sanyin AC suka haɗe mishi da ƙamshinta suka ƙara zuzutashi suka
hautsunashi suka fiddashi haiyacinsa.

Sai fatauci yakeyi babu sassauci.

Cusa kanta tayi cikin ƙirjinsa tare da riƙo damatsan hannunsa ta saki kuka mai cike da rauni sabida ta fara
galabaita shi kuwa baiji bai gani bare ya sararamata,

wani zazzafan cizo ta datsa mishi a ƙirjin saman nononshi kaɗan tare da fara tuttureshi.

Hannunshi yasa ya jawota jikinsa kana ya sake ratsa jikinta wani irin gigitaccen gamaiya ya kai mata
wanda yasa ta shaƙi wani dogon numfashi tare da koma ta kwanta a sume.

Sai dai baima san ta sumaba.

ita kuwa Khausar kamar yadda wahala tasa ta suma wahalarce ta kuma farfaɗo da ita abu dama da mai
raki.

Sama-sama takejinshi har yanzu tare da ita,

Sai zufarshi mai ƙamshi dake ɗigowa kanta ba sassauci.

Rumtse idanunta tayi da ƙarfi sabida raɗaɗin da takeji tamkar zai kasheta, ƙarfinta ya ƙare duk kuzarinta
ya tafi.

Cikin wahalar da take cikin take jiyo muryarsa can sama yana mgnar da ƙarfi kamar yadda yake fitinarta
da ƙarfi murya na rawa da alamun kuka yake cikin harshen larabci yake cewa.

“Yah Subahanallah, Alhamdulillah Allahu Akbar.

"Khausar As attu li wajattu xawajiki”.

Kuka ta kuma sawa tare da ruggumeshi gam-gam a jikinta, tare da cewa.

“Wash, wash, Wayyo Yah Mu'allim”

a kiɗime yayi mata wata iriyar fitinenneyar kuma gigitacciyar rugguwa da azaban ƙarfi tare dasakun wani
raunataccen muryar kuka dan ji yake kamar daɗin zai kashesa cikin kyarma yace.

“Wayyo Didi hashhhh, Innayi, J J jjjjjjjjjh.”

Da karfi ya kuma fara fidda numfashi tare da maimata wata kalma da larabci.

“Kuntil lagamee! Kuntil lagamee!! Kuntil lagamee Yah Fadimatuzzahrah kuntil lagamee.
Kunti ba'adu jasadi ya Khasy, kunti ba'adu jasadi feeh hayati ana”.

Wani irin karkarwa ya fara da azaban ƙarfi tare da bada himma can ya saki wani irin masifeffen
numfashin tare da kifuwa kanta ya kifa kanshi bisa filo bakinshi na dai-dai cikin kunnenta murya a sake
yace.

"Hashhhh Wahyyyyy Jazakallahu khairan Yah Minha vidaa.

Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Habibteeh kin zama suturata, Ngd kin bani abinda ban taɓa samuba a
duniya kin tabbatar dani cikekken mutun magidanci kana managarci."

Ita kam Khausar da ita da matacciya babbancinsu ba yawa, domin ko yatsarta bata iya motsawa,

tana dai jin duk abinda yake faɗa, na hausa ko fillanci ta gane duka na inɗiyanci da Spanish da yake
zubawa kuwa kaɗan take ganewa tunda ba ji takeba.

wani irin numfarfashi tayi mai rauni lokacin da taji yana raba jikinshi daga nata,

kana ya faɗa gefenta bakinshi ya manna da kunnenta a hankali yace.

“Hazal yaumu huwa a'axamu minna, Khausar Hazal yaumu a'axamu minna”.

Hannunshi yasa ya jawota jikinshi ya kifeta bisa ƙirjinsa.

wani irin masifeffen zafi taji jikinsa yayi har kamar tururi yakeyi, zafine irin mai ratsa jikin nanne.

Ruggume ta yayi tare da lumshe idonsa sabida, wani irin fitinenne zazzaɓi mai masifar zafi da suka yiwa
ƙasusuwan jikinsa daya rufeshi a take a lokacin ɗaya gaba ɗaya jikinsa karkarwa ya fara.

har tanajin hakan, so yake ya tashi da ita a jikinsa ya nufi Bathroom Amman ya kasa sabida abin sai
ƙaruwa yakeyi, ji yakeyi tamkar kansa zai rabe gida biyu.

Cikin rawan jiki ya jawo blanket ɗin ya rufesu da kyau.

sama take jinshi yana sambatu irin na marasa lfy dake jin azabar ciwo da kuma raki.

“J ! Hahhhhh Didi kaina, innayi kaina zai fashe jikina zazzaɓi Abualeey”.

Ya ƙare kiran kamar zaiyi kuka.

Itama kukan takeyi gashi taji shima kukan yakeyi da samɓatun da batasan na menene ba a haka suka
kwanta manne da juna, dukkansu babu wanda yayi bacci.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya fara jin abubuwan da yakeji suna lafawa sai dai sawunshi da yakeji kamar
ba nashi, sabida aikatuwa da abinda basu taɓa yiba.
Kiran sallan forko ne yashi ƙara mannewa jikinta, yayin da ita kuwa Khausar hawaye ne keta xirya daga
idonta zuwa kan damtsen hannunshi da yayi mata fillo, so yake ya tashi amman abin ya faskara.

Rahama kuwa jin kiran Sallah forkon ne, yasa ta kalli time ɗin wayar ai kam huɗu har ta ɗan gota.

Ganin haka ne yasa ta taso a hankali ta buɗe ƙofar cikin sanɗa ta fice ta nufi Side ɗin su.

Ummi kuwa jin kiran sallan ne yasa ta dakata da ziryar da take taje tayi al'wala hakama su Innayi.

A hankali Rahama ta tura ƙofar ɗakin Didi zaune ta hangota bisa salla cikin sanyi ta shiga tare da sallama,
da mamaki Didi ke kallonta lokacin da ta zauna gefenta, cikin kula tace.

“Lfy kuwa?”.

Kai ta ɗan jujjuya murya cike da tausayi tace.

“Didi Aunty Khausar fa, naji tana ta kuka, tana kiranki”.

Cikin tsareta da Ido Didi tace.

“Toh dama ce miki nayi in kinje can ki ƙwana ne?”.

Da sauri ta jujjuya kai tare da cewa.

“Wlh nace zan dawo kuma sai tace, wai dan Allah mu kwana tare, tace zata kiraki ta gaya miki, to kuma
da ta tafi dakin Yah Aleey Bata dawoba, sai ɗazu da naji tanata kuka har tana kiranki fa”.

Cikin sauri Lalla Hafsat da ta fito Bathroom da alamun itama al'wala tayi ta kalli Rahama tare da cewa.

“Toh anji tashi kije kiyi al'wala”.

Jin hakane yasa ta miƙe ta nufi ɗakinta.

Didi kuwa Gwauron numfashi ta fesar tare da ɗan yin ɓoyeyyen murmushi da hamdala ga Ubangji aranta
Aleeyu ta ya zama cikekken Namiji...

Shi kuwa Modibbo jin an kuma kira na biyu ne, yasa ya ɗan ronƙofo kanta, tare da manna mata kiss a
goshinta, sai kuma yasa tafin hannunshi bisa kuncinta yana ɗan shafawa cikin tausayawa da jinƙai gami
da kulawa yace.
“Minha, kiyi haƙuri ki yafe Modibbonki”.

Sai lokacin Shesh-sheƙan kuka ya fara taso mata, shi kuwa a hankali yace.

“Bari inyi wonka ko, ke ma in tayaki kiyi”.

Cikin sauran ɗan rogowar ƙarfinta ta ture hannunsa tare da jan blanket ɗin ta rufe jikinta da kyau.

A hankali ya ɗan janye jikinsa gefe, tare da miƙewa zaune, kana ya ɗan buɗe rumfar gadon ya fito.

Ita kuwa Khausar idonta a buɗe amman bata ganin sosai sabida yawan kuka.

Shi kuwa Modibbo cikin mmki yake kallon jikinsa dake ɓace da jini, kai ya ɗan sunkuyar tare da jawo
jallabiyarsa ya zira a jikinsa kana ya wuce Bathroom

A hankali ya shiga Bathroom ruwan zafi ya haɗa da turaruka wanka, kana yayi wonkan soso da sabulu,
sai kuma ya ƙara haɗa wani ruwan sabida jin yadda ƙafafunshi ke rawa, shiga ciki yayi ya ɗan kwanta na
tsawon 5 minutes kana ya fito, brush yayi tare da sake haɗa wani ruwan yayi wankan Tsarki bathrobe
mai taushin dake gefenshi ya zira.

Sai kuma ya sake haɗa wani ruwa cikin bathtub tare sa turaruka kana ya fito, ana tada iƙama, jin hakane
yasashi kimtsawa sauri-sauri gudu-gudu, turare ya ɗan fesa, kana ya ɗan sunkuyo kanta a hankali yace.

“Afwan Minha, kinji an tada iƙama, jirani yanzu zan dawo kinji”.

Bata kulashiba saima juya kai da tayi, hancinta ya ɗan lakace tare dacewa.

“Hmmm ɗan Didi yayi laifi ko”.

Ya ƙare maganar da juyawa ya fita.

Ita kuma a hankali ta gwada yunƙura wai zata tashi.

Sai kuma tayi saurin komawa zaune, sabida wani irin fitinennen zogi da raɗaɗin daya tsargan mata daga
ƙasanta har maɗigan kanta, sai kuma ta saki sabon kuka, tare da komawa kwance.

Ana idar da salla Didi ta miƙe tare da fitowa ta nufi ɗakin Jakadiya, suna shiga tace.

“Kin haɗa kayannan ko?”. Da sauri ya Jakadiya ta miƙe tare da cewa.

“Eh tsarinma ma tun randa akayi bikin gabatardashi na jiƙamshi, da sauri Didi tace.
“Taho”. Cikin sauri Jakadiya ta ɗauki wata kwarya mai cike da haɗin wasu irin itatuwa na musamman, sai
wani irin fitinennen ƙamshi tuumuwan yake zubawa, sai kuma wasu mayuka da ke kan fefeyin dake rufe
da ƙwaryar sai wata babbar leda dake cike da kaya.

Kai tsaye Side ɗin su Modibbo suka nufa.

Suna shiga cikin corridor Didi ta nuna mata falon tare da cewa.

“Shiga nan, bari in kirawo Ummin Jameel.”

To tace kana ta wuce ta shiga.

Ita kuwa Didi da sallama ta shiga falon su Ummi, da sauri Ummin ta miƙa tsaye tare da kallon Didi dake
ɗan murmushi, ganin yadda Ummi ta tsareta da idone yasa tace.

“Ummin Jameel ina innayi".

“Tana ciki”. Ta ƙare mgnar da nuna mata ƙofar ɗakin da innayi ke ciki.

Da sauri ta nufi can, itama Ummin Binta tayi a baya.

Cikin kulawa Innayi ke kallonta ita kuwa Didi da alamun sauri tace.

“Innayi wa zai iya ɗan taimakawa Khausar?". Murmushi Innayi tayi tare da nuna Ummin Jameel.

“Toh Ummin Jameel ke da waye zamu tafi”.

Da sauri tace.

“Bari a kira Aunty Hajara ƙanwar Maman Khausar”.

Ta ƙare mgnar da kiran Aunty Hajara ba bayani sukabi bayan Didi dan sun lura da gaggawa Didin take
sonsu Hajja Nana kuwa da ido ta rakasu domin ai ita kanta tasan masarautu da tsaraɓe-tsaraɓen al'adun.

Aiko suna isa suka samu Jakadiya a falo, da sauri Didi ta amshi kwaryan ruwan nan ta miƙa Ummi tare da
cewa.

“Idan kun shiga a taimaka mata ta zauna cikin ruwannan in Sha Allah lokaci ɗaya zataji sauƙin jikinta
sosai.
Kai Ummi ta jinjina tare da amsar ƙwarya, ita kuwa Jakadiya cikin alamun tsananin jin daɗin tace.

“Sai tayi wanka zan shigo in shiryata.”

To kawai Ummi tace tare da juyawa suka nufi cikin ɗakin.

Suna shiga sukayi turus suka tsaya a tsakiyar ɗakin tare da juyawa suka kalli juna cikin kaɗuwa ganin
babu kowa a ɗakinma bare Khausar ba ita alamarta...

*Masu son Maganin infection da maganin mata, ku marmatso wannan account no in ne naku ta ciki zaku
turo kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP
NUMBER'N na 08069423567. akwai sabbin kaya masu zafi suna nan bisa hanya, ki turo kuɗinki a saki
cikin lissafi. Kayanen mata masu zafi sadidan daga Chadi akwaisu Garukan daka, gumbunan,
Tsumummuka, cida Ciccibi Abodi cida kaza ci da jan nama kwanon ƙasaitacciyar mace biyar sirri, furar
mata, gumbar madara Gumbar kolli mai ƙyallin al'khairi gumbar uku al'khairi, gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, gumbar riɗi, garin maɗi garin melɗamhi garin ilanwaddihi garin mallaka, tsumin riɗi tsumin
tsirtai tsumin kinfi budurwa, tsumin riɗi, tsumin ta baje Sabaya, matsin maliƙi mai masifar matse mace
matsin daɗi har maɗiga, mai ɗan kare kyau. Kullacar sirri al'ajabu shu'umar Humra, da duk sauran kan
ƙamshi. Haɗin amarya budurwa ko bazawara haɗin mai jego ko uwar gida, akwaisu Available set ɗinmu
hawa hawane akwai manya akwai ƙananan, ƙanan daga 40k ne 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙarami
haɗina na karshe sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar shi 7k ne shine ƙarshen haɗina kenan... Manyan
set ɗin kuma daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k ke zaki faɗi haɗin nawa kikeso anyi miki kana kimin bayanin
yadda kikeso da matsalarki ni kuwa nasan abinda zan haɗa miki, ina araha kam amman ina hana bashi*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

58

Ido suka zuba kan gadon dake hargitse ga jini dake kai sai rigar baccin Khausar da suka gani gefen pillow.

Sai kuma suka kalli juna da mamaki gami da tausayin,

Ummi kama tuni hawaye ya cika mata ido a hankali tace.


“Toh ina take?.”

Da sauri Aunty Hajara ta rumtse idanunta ganin yadda beshid ɗin ya ɓaci da jini, musamman wannan
farin ƙyalle mai heart dake tsakiyar gadon.

Da sauri ta jujjuya kanta sai kuma ta ta kalli ƙofar Bathroom ɗin sabida jiyo mgn can ƙasa-ƙasa da sauri
tace.

“A'a Ummin Jameel kinji fa kamar mgn a cikin Bathroom dinsu”.

Sai kuma duk sukayi kasake alamun kasa kunne cikin mmki Ummin ta sauƙe numfashi tare da cewa.

“Ai kamar ma muryar Babane a ciki".

Shi kuwa Modibbo da duk saurin Didi ya rigasu, iso kuma da suka zo basu shiga cikiba iyakar Jakadiya ma
falo, shiyasa basu san ya dawo ba, a zatonsu yana Masallaci kamar yadda haka al'adarsu take kafin ango
ya dawo salla biyu daga cikin ƴan uwanta da dole al'adar masarautarsunce in an kawo amarya ma sai an
bar mata biyu, masu maidawa iyayen yarinya tukuici in ta kawo budurcinta da kuma kai hatimin mulki da
za'a mallakawa mata shaidar kasantuwarta Gimbiya kenan.

Toh koda ya dawo kawai ciɗak ya ɗagata ya nufi Bathroom da ita, yana shiga ya direta cikin ruwan
ɗumin daya haɗa mata, tun kafin ya tafi.

Jin yadda zafin ruwan ke ratsata ne yasa take yayyarfa hannunta tare da sakin raunataccen kuka murya
adisashe.

A hankali ya ɗan tallaɓe kanta tare da mannawa da ƙirjinsa cikin sanyi mai cike da bayyanar asalin
matsayinta dake cikin zuciyarsa yace.

“Sannu kiyi haƙuri ki zauna zakiji sauƙin ciwon sosai”.

Ya ƙare mgnar da dan ƙara zaunar da ita cikin ruwan ɗumin,

wani raunataccen ƙara ta kuma saki wanda yasa har Jakadiya da Didi dake falo suka jiyota, cikin sauri
Jakadiya ta kalli Didi tare da cewa.

“Inaga sun ɗagata bari mu ɗauko ƙyallen tarihinmu da zanin gadonmu”.

Kai kawai Didi ta gyaɗa mata.


Allah yasani ji take kamar ta shiga to amman ba dama tunda Ita dai surkuwa ce.

A can cikin ɗakin kuwa Ummi da Aunty Hajara kam bushewa sukayi a tsaye kamar wasu sakarkaru, suke
kallon ƙofar Bathroom ɗin fuskoki cike da mamaki.

Da sauri suka juyo suka kalli ƙofar jin a buɗe Jakadiya da yanzu ta shigo, kwaryan dake hannunta ta miƙa
Ummi tare da cewa.

“Gashi ta zauna ciki ammafa kada ta wuce 2 minute”.

Toh Ummi tace tare da amsa kana ta ajiye ƙwarya, sai kuma ta kalli Aunty Hajara dake ruggume da
hannun.

“Inaji mafa kamar tana tare da mijinta ne a Bathroom ɗin."

Aunty Hajara ta faɗa.

Murmushi Jakadiya tayi tare da cewa.

“Ato shike nan ai ni bari in na ɗe..."

Sai kuma suka kalli ƙofar Bathroom jin kamar an buɗe, shi kuwa Modibbo jin alamun surutaine yasa ya
ɗan miƙe tsaye kana ya buɗe ƙofar dan yaji surune da gaske akeyi a ɗakin.

Da sauri yayi ƙasa da kanshi ganin Ummi.

Ita kuwa Ummi cike da kunya ta miƙa mishi kwaryar nan da Jakadiya ta bata tana mai kauda kai tace.

“Gashi ta zauna ciki, Amman kada ta wuce daƙiƙu biyu”.

Cikin tsaanin kunya yayi ƙasa da kanshi tare da amsar kwaryar, ya juya cikin Bathroom ɗin da sauri ya
maida ƙofar ya rufe ba tare da yace komai ba kana bai bari sun haɗa idoba.

Itama Ummi cikin kunya ta kama hannun Aunty Hajara suka fita.

Jakadiya kuwa murmushi mai cike da jin daɗi tayi, tare da shimfiɗa wani farin leda mai taushi a gefen
gadon zai kuma ta ɗan jawo wannan farin ƙyalle mai zanen heart ta sanyashi cikkn ledan kana ta maida
shi ta liƙe ya zama kana iya ganin duk jinin dake jikin ƙyallen sai kuma ta sa hannun ta ɗauko wani ɗan
bugeggen katako mai zagaye da gold a jiki, kana an yishi da marfin glass daga saman an Rubuta MRS
Aleeyu Mouleey, da manyan baƙin larabci.

Sai a ƙasan kuma aka rubuta. Lalla Khausar.


Cikin ta shimfiɗa ƙyallen tare da maida marfin glass ɗin ta rufe, sai ya zama tamkar abun aje hoto, sai
kuma daga ge da gefensa da ke ɗauke da tambarin masarautar Mouley ɗin.

Cikin sauri-sauri ta naɗa beshit ɗin kana ta zaro wani fari mai ɗauke da alamun zanen masarautarsun ta
shimfiɗa tare da sa rigunan pillow da blanket.

Sai kuma ta ɗaukesu tare da fitowa falo da sauri.

Tana fita Lalla Khadijah na isowa da kaskon turaren wuta,

Da sauri ta miƙa wa Didi wannan furem ɗin ƙyallen da kuma sanin gadon, cike da jin dadi Didinta amsa
ita kuwa Jakadiya, amsa kaskon turaren wuta tayi ta koma ɗakin ta ajiye.

Gefen gado kana ta jawo ledan nan, ta fito da wata dandatstsiyar Alƙyabbata irin ta matan masarautar
Mouley ɗin, sai kuma wata tattausar riga mai gajeren hannun, dukansu kolon tutar masarautar sune sai
fararen ondis.

Turarukan data kawo tajera gefen kayan.

Sai kuma ta juya ta koma falo bayan ta ƙarasa kimtsa ɗakin.

A nan cikin Bathroom kuwa, cikin wani irin fitinennen kallo Modibbo ke kallon Khausar da ta tura lip inta
na kasa tare da kwaɓe fuska, har lau hawaye na tsiyaya, cikin sanyi ya ɗan tallabo kanta da hannunsa
duka biyu, manyan yatsunshi yasa tare da fara goge mata hawayen, murya cike da taushi, tausayi, gamin
da jinƙai yace.

“Kiyi haƙuri ko, kin yafewa Yah Mu'allim dinki ko?”. Cikin Shesh-sheƙan sabida jin yadda zafin ruwan ke
ratsa mata jiki, ga wani irin fitinennen zazzaɓi da ciwon kai da sukayi mata taron dangi, murya a disashe
tace.

“Allah zai saka min”. Da sauri ya kauda kanshi gefe jin murmushi na gaba da subce mishi, ita kuwa kuka
ta ɗan saki tare da cewa.

“Ai dama na gayawa Ummi haka zakayi ta cin zalina amman suka ki yarda, Allah zai saka min”.

Cikin sanyi ya ɗan tsuke fuska kana yace.

“Zo nan, zo ki shiga cikin wannan inji Ummi”.

Da sauri ta rumtse idanunta jin ya tallabota ya ɗagota, sai kuma yayi saurin ruggume ta, jin yadda ta saki
wata ƙara mai cike da alamun galabaita.

A hankali ya zaunar da ita cikin kwaryar.


Da ƙarfi ta saki ƙara tare da cakumo wuyanshi ta matseshi gam a jikinta da yake rawa kar-kar sabida zafi
gami da raɗaɗin da jininta ya ɗauka.

Rumtse idanunsa yayi da ƙarfi dan ba ƙaramar shaƙa tayi mishi ba, sai kuma ya fara sauƙe ajiyan zuciya
jin ta fara sassauta cacumar da tayi mishi, ido ya zuba mata jin yadda take ta sauƙe ajiyan zuciya a jere a
jere, sai kuma wani irin fitinennen zufa daya keto mata tako ina a jikinta.

Lumshe idanunta tayi tare da jingina kanta da ƙirjinsa.

Tana mai ci gaba da sauƙe numfashi, a hankali yace.

“Da sauƙi ko?”.

Bata kulashi ba, sai idanunta dake rufe domin duk abinda yake mata bata buɗe idanunta ba.

Sai yanzu da taji ya ɗagota cak daga cikin kwaryar da sauri ta buɗe idan, sai kuma ta rufesu ganin shima
ita yake kallo, ɗan murmushin gefen baki yayi tare da cewa.

“Toh kiyi niyan wankan tsarki”.

Bata kulashi ba, shi kuwa a hankali ya koma gefen bakin bathtub din ya zauna.

A hankali ta buɗe idanunta tare da ɗan kallon ƙofar fita, sai kuma tayi saurin cewa.

“Ni ka daina kallona kuma, ka fita zanyi wanka”.

Bakinshi ya ɗan motsa bata dai ji me yaceba, ta daiga ya rufe idanunshi alamun bazai fita ba kena, ganin
haka yasa tayi niyan wankan, tare da fara yin wonkan a suffatul ijjiza, kawai ruwa ta sakarwa kanta.

Daga zaune ta gama wonkan, kana tayi al'wala, a hankali ta yunƙura ta tashi tsaye ga mamakinta kaso 65
ɗari na zafin da takejin ya tafi.

Zafin da takejin ya tafi har wani tsukewa taji jikinta yayi.

Sai kuma tayi saurin da hannunta ta kare ƙirjinta ɗaya zubawa idanu, da sauri kuma ta maida hannun
nata ƙasa ganin yadda ya tsura wurin ido.

Shi kuwa towel ya jawo tare, da rufe matashi kana ya dauketa suka fito.

Bisa bakin gado ya ajiyeta, sai kuma ya jawo kujerar dressin mirror d mai a fabanta ya zauna.

Tare da lakatan mai ɗin ya murza a tafin hannunsa kana a hankali ya fara shafawa ƙafarta.

Ita kuwa cikin sanyi da rawan jiki tace.


“Yunwa nakeji”.

Yana mai ci gaba da shafa mata mai ɗin yace.

“Toh acici kazar birni, ai ni ya kamata inyi kukan yunwa nida kika kwana ƙwaƙulewa".

Cikin mamaki ta zuba mishi ido tare da mgnr zuci.

“Motar sherri”.

Ga mamakinta sai ji tayi yace.

“Ni ne motar sherri”.

Da sauri ta jujjuya kai, tare dacewa.

“A'a da kaina nake”.

Hannunta ya kamo ya shafa mata mai ɗin kana ya juya ya gaban dressin mirror yana mgna cikin ranshi.

“Komai ma ki, kirani zan amsa, tunda nayi laifi”.

Da sauri ta dauki pant ɗin dake gefenta ta saka.

Sai kuma ta jawo tattausar doguwar rigar nan.

Ta zura, hannunshi yasa ya jawota tsaye, tare da ɗaukar alƙyabar nan.

Ya zira mata.

Sai kuma ya dawo ta gabanta tare dasa hannunshi kan caɓullenta ya ɗan matsa a hankali da sauri ta
rumtse idanunta.

Sai kuma ta fara jujjuya kanta jin abinda yace.

“Yau ma suna miki ƙaiƙayin ne, in sosai miki”.

Murmushi ya ɗanyi ganin yadda gaba ɗaya jikinta ke karkarwa.

Turarrukan ya fesa mata kana yasa mata hulan rigar sai kuma ya jawo hulan alƙyabar ya rufe mata kanta.

Bisa sallaya ya jawota.

Ita kuwa idanunta ta rumtse da karfi sabida yadda in ta daga ƙafarta zafin ke ɗan tsargarta.

A hankali ya dawo bakin gado tare da cewa.

“kiyi salla”.
Ya ƙare mgnar yana dafe kanshi da hannun bibbiyu da shima zazzaɓin yakeji da ciwon kan da yasan
rashin baccine ya jaza mishi.

A hankali ta miƙe tsaye bayan ta idar da sallan

Dai-dai lokacin kuma Jakadiya tayi sallama, ɗan tsaki yaja tare da amsa sallamar kana ya mata izinin
shigowa.

A gefe ta rusuna cikin girmama ta gaidashi ba tare da ya kalleta ya amsa.

“Bisa umarnin Didi tace Lalla Mouley tazo mu tafi wurinsu Ummin Jameel".

Ta fadi tana kallon Khausar, tare da tura kaskon turaren wutan da ta shigo dashi a hannunta da kuma
wata ƴar ƙaramar kwalba dake cike da turaren wutan tsuguno na musamman.

Shi kuwa Modibbo. Cikin tsuke fuska yace.

“Uhm". Ita kuwa hannun ta miƙa Khausar tare da cewa

“Ki tsuguna ki turara jikinki da turaren wutan nan, sai mu tafi.

murya na rawa Khausar tace.

“Bazan iyaba”.

Da sauri Jakadiya ta juya ta fita jin Modibbo yace.

“Kije zan kawota”.

Tana fitowa falon ta gaya musu yadda sukayi hakan ne yasa, duk suka fita Ummi da Aunty Hajara suka
koma masauƙinsu, Didi da Jakadiya da Lalla Khadijah kuma suka nufi kasan.

Dai-dai lokacin kuma Lalla Hafsat da Rahama dake kitchen da kansu suka shiryawa Khausar breakfast mai
rai da lfy, wanda natane ita kaɗai, sai kuma na Abualeey da Modibbo da suka shirya da ban sai kuma
nasu duka.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya miƙa tare da kallonta jin tana cewa.

“Zan faɗi".
Hankali ya jawota jikinshi ya ruggume mata tsam, cikin sanyi ya cusa kanshi a wuyanta yana mai shaƙan
daddaɗan ƙamshin jikinta,

Bakin gado ya ajiye ta, kana ya dawo ya ɗauki kaskon da turaren wutan, ya ajiye gefenta ta inda zai
zauna tattare jallabiyar jikinshi yayi ina ya zauna, hannunshi yasa ya kamo nata tare da jawota gaban shi,
cikin karkarwa da rawan murya tace.

“Ƙafafuna rawa suke bazasu iya ɗaukata ba“.

Kanshi ya ɗan ɗago ya kalleta sai kuma ya ɗan sunkuyo turaren wutan ya danga mai ɗan yawa ya zuba a
cikin kaskon, sai kuma ya jawota gaban shi sosai tare da sa hannun ya ɗan buɗa sawunta, da sauri ya
yawota gaban shi sosai hannunshi ɗaya yasa ya tallabo ƙugunta, kana ya manna kanshi da cikinta yayi
mata Garkuwa Da kyau dan ya lura zata iya faɗin.

Da sauri ta rumtse idanunta tare dasa hannunta ta kamo hannunshi ɗaya da taji ya zira cikin rigar ta
yana jan pant ɗinta yanayin ƙasa dashi.

Jin yadda ta riƙe mishi hannun ne yasashi ɗan jujjuya kanshi murya a tausashe yace.

“Ki bari in cire shi, hayakin zaifi shiga jikinki da kyau yayi miki aiki“.

Ya ƙare maganar da yin ƙasa da shi baki ɗaya.

Sai kuma yasa sawun shi duka biyu tsakanin nata sawun.

Wanda haka yasa dole ta zare ƙafarta ɗaya, sai kuma ta saki ƙara da ƙarfi jin ya ware sawun nashi da
yasa dole ta zauna kan cibiyoyinsa, manna kanta tayi da ƙirjinsa tare da rufe udanunta hawaye na
kwaranyo mata sabida zogin da takeji.

Shi kuwa Modibbo cikin sanyi ya ɗan sunkuyo tare da gyara zaman kaskon sautin jikinta sai kuma ya
tattare rigar nata ya buɗashi ya bazashi bisa guiwowinshi ya zamana ta zama ba komai a jikinta ta ƙasan,
sai kuma ya ƙara ɗanƙo turaren wutan ya saka a ciki.

Ai ko kai tsaye kan jikinta hayakin ke tashi, a take ta fara sakin numfashi da ajiyan zuciya sabida wani irin
daɗin da taji a jikinta sai kuma ta lumshe idanunta sabida jin yadda jikinta ke mata wani irin daddaɗan
ƙaiƙayi alamun ciwon na workewa ne, bisa ƙarfin magungunan dake cikin turaren wutan.

Numfashi mai sanyi ta fesar tare da ɗan buɗe idanunta.

Idonta ta ɗan zubawa lips inshi da yake ɗan motsawa alamun mgn yake sonyi, kuma mishkilanci ya
hanashi, fahimtar hakane yasa ta ɗan tura baki tayi tare da hararanshi ta ƙasan ido.

Da sauri ta kalleshi jin yasa hannunsa duka biyu bisa ƙugunta ya riƙe da kyau kana murya can ƙasan
maƙoshinsa yace.

“Anya kuwa kina son ki rabauta, ki samu jannatul firdausi”. Cikin kwaɓe fuska sabida yanayin yunwa
wahala da bacci tace.
“Ina so mana”.

Kamar cikin raɗa yace.

“Kin san dai sai na ɗaga ƙafa zaki shiga ko?”.

Ya ƙare maganar cikin wata iriyar murya mai nuni da shima zazzaɓin ne a jikinsa kana ya tsareta da
matattun idanunsa, ita kuwa Khausar cikin sanyi tace.

“Eh nasi”.

Kanshi ya ɗan manna da ƙirjinta a saman lips inshi yake

“Toh bakya son shiga kenan?”.

Ya ƙare maganar yana shafa sajenshi kan haɓarta.

Cikin sanyi tace.

“Toh bazaka ɗaga min in shigaba kenan?”.

“Eh in baki bar tura min baki da jujjuya fitinannun idanun nan naki ba kam bazan ɗafaba”.

Da sauri tace.

“Kayi haƙuri bazan ƙaraba”.

Kanshi ya ɗan jujjuya tare da cewa.

“Naƙi”.

Cikin zubda hawaye murya na rawa da alamun tsoro tace.

“Ai dama na sani baka sona ka tsanane kai zakama fi son in shiga wuta”.

Murmushi mai cike da jin daɗi yayi kana a hankali yace.

“Sorry yi shiru in dai kina min duk abinda nakeso, to zan ɗaga miki, ki shiga ba ke ba wuta jinki ko
Minha”.

Ya ƙare maganar tare da manna fuskarshi da tata, a hankali ya ɗan zaro harshensa cikin sanyi ya fara
lasar hawayenta tare da shaƙan ƙamshin jikinta.

Allah ya sani so yake suyi bacci, amman ya lura tana cikin galabaita, ga jikinta zafi kana ko muryarta bata
fita, gashi tun ɗazu take ƙorafin yunwa, kuma ga umarnin Didi.

A hankali ya ɗago kanshi ya kalleta jin tana cewa.

“Yunwa nakeji, kamar zan faɗifa kaina ciwo bayana ciwo, ƙuguna ciwo, idona ciwo”.
cikin wata amintacceyar murya yace.

“sorry Minha vidaa Bazaki faɗiba bari in kaiki kici abinci mu tafi asbiti”.

Sai ya ɗan tsaida ita tare da sa mata pant ɗin kana ta gyara mata rigartan.

Sai kuma ya sunkuyo.

Cak ya ɗagata tare da mannata da ƙirjinsa, sassayan numfashi ya fesar tare da fitowa da ita ya nufi Side
ɗinsu Ummin.

Dai-dai lokacin ɗin da suka iso ƙofar falon dasu Ummin suke tace.

“Ka sauƙeni a nan zan ƙarasa da kaina”.

“Naƙi". Yace yana mai kutsawa cikin falon.

Da sauri ya sunkuyar da kansa dan kusan duk su Ummi suna falon cikin wani irin fitinennen kunya ya
direta bisa 3 sitter kai a sunkuye yayi musu gaisuwar ƴan kasuwa tare da juyawa ya fita.

Yana fita yaci karo da Didi da Lalla Hafsat da Jakadiya, a hankali ya raɓa jikin gini tare da sosa ƙeyarsa.

Cikin kauda kai Didi tace.

“Kaje ƙasa Khadija ta baka abinci”.

Cikin sanyi yace.

“Toh”. Sai kuma ya nufi ƙasan.

Ita kuwa Khausar yana fita ta kife kanta bisa cinyar Ummi da tazo ta zauna kusa da ita, cikin rawan jiki da
muryar data disasha yasa bata fita sosai tace.

“Ummi yunwa nakeji, kaina ciwo zazzaɓi nakeji”.

Sai kuma ta saki sabon kuka.

Dai lokacin kuma Didi suka shigo.

Da sauri ta matso gabansu shafa kanta tayi cike da kulawa so da tausaya take mata sannu tare da
tambayar Ummi me ke damunta.

Kai ta jinjina jin abinda Ummin ta gaya mata, kana cikin kulawa tace.
“Hafsat sauƙa kije ki cewa Ibraahim yaje ya ɗauko Dr Jameel”.

Da sauri tace to kana ta juya ta fita.

Ita kuwa Ummi a hankali tacewa Khausar.

“Tashi kici abincin to”.

Cikin rawan jiki ta tashi zaune da taimakon Aunty Rukayya dake jera mata sannu.

A hankali suka kalli gefen da Hajia Bunayyah take sabida jin wani dogon tsakin da taja tare da juyawa ta
bar falon.

Cikin zubda hawaye Khausar ta kalli Asma'u dake ta sakin murmushin tare da sune kanta.

Sai kuma ta kalli Dija ta kuna kalli Aseeya.

Cikin muryar kukan tace.

“Ummi ki ganifa dariya su Asma'u kemin”.

Da sauri Asma'u da Dija suka nufi cikin ɗaki sabida daƙuwar da Ummi tayi musu, Asiya ma bayansu tabi.

Hajja Nana kuwa cikin dariyar mugunta a fili tace.

“Yar nema ba cewa kikayi Ni Modibbo nake so”.

Cikin Shesh-sheƙan kuka murya na rawa tace.

“Wallahi na fasa, ni dai Wlh ku maidani wurin Mommy na ta kare mgnar da iyakar gskyar zuciyarta”.

Dariya ce ta kubcewa Aunty Hajara da Rukayya Hajja Nana da Innayi kuwa tafa hannu sukayi.

Ummi kuwa da sauri ta jawota jikinta.

Didi kuwa tea mai zafi ta fara haɗa mata.

A can ƙasa kuwa kwance kan 3sitter Lalla Hafsat ta samu Moddibo jikinsa cike da zazzafan kasala gaba
ɗaya yayi so weak baki ɗaya bashi da kuzari saboda yayi abinda bai taɓa yi ba a tsawon rayuwarsa duk
jikinsa amace yake ga wani fitinennen zazzaɓi da yakeji yana ratsa ƙasusuwan jikinsa, yayinda cinyoyinsa
kuwa gaba ɗaya jinsu yake kamar ba nasaba, a hankali ya kishingiɗa da jikin Kujera yayin da ya manna
kansa da jikin Kujeran yasa hannunsa duka biyu ya riƙe sabida zazzafan zazzaɓi yake ji wanda yasa har
jikinsa ke rawa ga kuma ciwon kai wanda alamun kukanda yayi tayine da rashin bacci suka haifar masa
da ciwon kan.

Cikin kula ta isa wajen tare da ɗaura hannunta na dama kan goshinsa jin hannunta agoshinsa ne yasa ya
buɗe Idanunsa dake lumshe ya kalleta.

Cike da kulawa tace.

“Jikin ka zafi,Zazzaɓi kake jine?”.

Kai ya gyaɗa tare da maida idanunsa ya lumshe.

Cikin kulawa ta kalli fuskarsa tare da cewa.

“Subhanallah Sannu”.

Sai kuma ta juya ta kalli Ibraahim da yanzu yake shigowa tare da cewa.

“Yawwa Ibraahim dama yanzu Didi tace in faɗa maka kaje ka kira Dr Jameel yazo ya duba Khausar bata
jin daɗi.

Shima Aleeyu gashi yanzu naji duk jikinsa da zafi ga yanda ya zama wani so week haka nan!”.

Jin abinda ta faɗa yasa Moddibo buɗe Idanunsa ahankali tare da faɗin.

“Dr Jameel kuma?.”

Kai ta gyaɗa mishi alamun eh.

Cikin ɗan rawan sanyin zazzaɓin yace.

“Ba Dr macene? Bana so Dr Jameel ya dubata, a nemi mace”.

Kai Ibraahim ya gyaɗa kana yace.

“Toh Shikenan bari naje na taho da Dr Jameel,Da Dr Isha in yaso Dr Jameel sai ya duba ka ita kuma sai
mace ta duba ta”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana Ibraahim ya juya ya tafi...

Acan ɓangaren su Didi kuwa sauri Didi ta Sanya hannunta ta karɓi plate ɗin da Khausar ta ke miƙawa
Hajja Nana mata alamar ta ƙoshi ita kuwa Hajja Nana harara ta watsa Khausar tare da cewa, nicema zan
karɓi ragowar yunwarki ai shi daya jinyataki sai shi zaiyi jinyarki, Ni ko sannuma zaki samu a wuri nane,.
Murmushi Ummi da Didi sukayi, cikin kulawa Didi tace.

“Ki hutama Hajia ni zanyi jinyar ɗiyata”.

Murmushi suka kumayi baki ɗaya.

Ita kuwa Khausar a hankali ta koma baya tare da jingina kanta da jikin Kujeran ta lumshe manyan
idanunta da suke ɗan kumbure kana sunyi ja saboda yawan kuka da rashin bacci.

Sai kuma ta fesar da sassayan numfashi sabida cikinta yayi mata tib saboda yanda abincin ya mata daɗi
taci sosai musamman ma naman ya dahu yayi lugun gashi yayi yaji yadda take so.

Anutse Didi ta sake miƙa mata kofin tea mai kauri tare da cewa.

“Karɓi ki shanye”.

Sunkuyar da kanta tayi kana tace.

“Cikina ya cika”.

Ummi dake gefenta tace.

“Karɓi ki shanye ki kafa kai kawai ki shanye”.

Cikin lumshe idanu ta karɓa tare da kafa bakinta ta shanye tass.

A take zufa ya shiga tsats-tsafo mata tako ina.

Cike da kulawa Ummu ta kalleta tare da faɗin.

“Sannu”.

Kai ta gyaɗa tare da lumshesu so take ta gyara zamanta amman tsoron yadda zata motsa take, sabida
har yanzu tanaji zogi.

Gajiya da zaman ne yasa ta ɗan kishingiɗa.

Ummi na gyara zamanta tace.

“Kwanciya kike sonyi?”.

Langwaɓar da kai Khausar tayi kamar za tayi kuka ta gyaɗa mata kai tare da faɗin.

“Eh jikina ba ƙarfi,Ummi baki daya jikina amace”.

Numfashi Ummi ta fesar ganin yanda take ciccije baki alamar tana jin ciwo ajikinta tace.

“Toh ki kwanta”.
Kai ta gyaɗa tare da kwanciya.

Zama Didi ta gyara tare da kallon Hajja Nana dake cewa Innayi.

“Dan Allah nikam Innare yau dai kam ki faɗa mana meye ne sirrin Al'amarin tafiyar ku gari ya garire kuka
je kuka zauna har wancan ƙasar”.

Kallon Didi Innayi tayi alamar kin amince in basu labari.

Kai Didi ta Jinjina tare da faɗin.

“Ki faɗa musu”.

Zama Innayi ta gyara tare da juyawa ta fuskancesu baki ɗaya kana ta fara basu labari kamar haka...

Masarautar Mouley ta kasance Masarautace mai girma da ƙarfin iko kana da matsayi a yankin Africa baki
ɗaya, sannan su su Abualeey sarki Youseep kenan su goma ne acikin Mahaifin su suna da ƴan Uba su
kuma su huɗu ne kaɗai acikin Mahaifiyarsu maza biyu mata biyu Sarki Youseep Muhammad Mouleey sai
Haroon Muhammad Mouley, sai Salma Mouley da kuma yar autarsu mahaifiyar Dr Jameel.

Sannan Mahaifiyarsu ta kasance itace Uwar gida mahaifinsu tun yana da rai yayii Murabus aka ɗauki
mulki aka bawa Sarki Youseef kasancewar shine babba sai suka fara fuskantar ƙalubale ƴan Uba sukayi
ca akansu bayan yayi Aure dai duk abin bai bayyana sosai ba, saida suka fara haihuwa, aihuwarsu ta
forko aka samu, Lalla Khadijah lafiya lau aka raineta har aka yayeta. Kana aka haifi Lalla Hafsat lafiya lau
itama aka yayeta, amma tunda aka fara haifan ƴaƴa maza sai ya zama duk Namijin da aka haifa baya
wuce kwana arba'in a duniya tun yana kwana talatin zuwa arba'in ɗin ake sace yaro, baya wuce kwana
uku sai a tsinci gawar yaro a tsakiyar fada, an kashe shi.

Masarautar Mouley gaba ɗaya ta shiga ruɗanin wannan al'amari, sai da Gimbiya Didi ta haifi ƴaƴa maza
uku duk ana kashe su kafin ta haifi Moddibo da aka haifi Moddibo kuma dai-dai lokacin Mahaifin
Moddibo ya kamu da ciwo ya zama kamar irin Kiɗimamme haka ya rasa gane Ainihin abinda ke damunsa
har aka ɗauki Sarauta aka maida ita hannun Ƙaninsa.

Ƙanin shine ayanzu yake kwance kusan shekaru ashirin da biyar bashi da lafiya.

Sanin danayi ana haifar yara basa wuce kwana arba'in ake ɗauke su yasa nayi niyya taimakon uwar
ɗakina da uban ɗakina da kowa yasan yanayin jikinsa akwai alamun sa hannun magauta.

Kasan cewa nice Jakadiyar Didi yawan zama da ita da yaranta da take musu fulatanci yasa na iya yaren
sosai tunda alokacin ma munyi kusan shekaru goma sha uku tare, dan a lokacin shekarun Lalla Khadijah
12 cib Hasfat 10. Haka yasa nayi niyyar ɗaukesa naje wani waje nayi rayuwa dashi ya zama zakaran
gwajin dafi kafin na dawo dashi shiyasa na rubuta wasiƙa sannan na ɗauki sandarsa wanda tsarin
Masarautarne duk Amaryar da aka aura ranar da akayi First night ɗin ta idan aka sameta cikakkiyar
budurwa za'a bata wannan sandar Amma sandar za'a ajiyeta aɗakin Tarihi na Masarautar inda ake ajiye
ƙyallayen budurcin matan masarautar da sarautar ke hannunsu, sai randa ta haifi ɗa Namiji ya kai
shekara ɗaya aduniya za'a ɗauko shi akawo mata shi matsayin sandan godon sarautar, dan haka ne na
ɗauki sandar sannan na shiga ainihin ma adanar masarautasu kasancewata amintacciyar Jakadiya yasa
nasan duk shiga da fitan Masarautar shiyasa na shiga na ɗibi Silalllan Gwal ɗinna kafin na rubuta wasiƙa
da yi musu cikekken bayanin ba sace ɗansu akayiba ni na ɗauleshi na tafi dashi kuma in dai yana raye ina
raye wata rana zan dawo dashi.

Na basu cikekken tabbacin Cewa zan dawo musu da ɗansu in Sha Allah su kwantar da hankalin su nayi
musu alkawarin zan kula dashi sannan zan bashi tarbiyya za kuma yi mishi duk abinda uwa da uwa
zasuyiwa ɗan su bazaiyi kukan rashinsu a kusaba susa aransu zan dawo musu da ɗan su lokacin da yafi
ƙarfin magautan su a kuma lokacin da sukafi buƙatar sa kusa dasu...

Nan'nauyan ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe sai kuma ta juya ta kalli Hajja Nana dake cewa.

“Sai kuma ki rasa inda zaki je sai garin mu”.

Murmushi Innayi tayi kana tace.

“Eh saboda lokacin da aka kawo Didi ƴar Nigeria ce jahar Adamawa sheik Jabeer ya kasance Aminine ga
Sarki Mohammed Aliyu Mouley shiyasa suka haɗa Auren ƴaƴan su.

Shiyasa dana tashi na tafi Nigeria naje na zauna ta yankin dake magwabtaka da yankinsu kuma shiyasa
nake hana Modibbo zuwa Adamawa, sai a sace yaje sau ɗaya nanma da naji nai ta kuka haka yasa yayi
min alƙawarin bazai sake zuwaba Marocco ma nice ke hanashi zuwa da tuni yazo, niko nasan duk wanda
yasan iyayensa to dole in ya ganshi gane ɗansune”.

Murmushi kawai Didi keyi tana sake jin ƙaunar Innayi aranta ta yanda ta riƙe mata amanar ɗanta ta
kuma bashi tarbiyya.

Innayi kuwa idanunta akan Hajja Nana ta cigaba da cewa.

“Daga nan kuma ban san meya faruba a masarautar Mouley bayan tafiyata ba”.

Numfashi suka sauƙe kowa yana sake jinjina girman ikon Allah aransa da yanda al'amarin ya kasance
kana suka haɗa baki wajen cewa.

“Ikon Allah rabo nefa.

Rabon Aurensa da Khausar ne ya jasu”.

Amintaccen murmushi Didi ta Saki kana tace.

“Aikam Al'amarin Ubangji ya wuce wasa sai godiya”.


Sai kuma ta ɗan kalli Innayi tare da cewa.

“Bayan tafiyarku da wata biyu Sarki Muhammad Mouley ya rasu, kana a ranar Unclee Haroon ya cika
shekaru biyu a karagar mulki ƙanin Abualeey kenan. kasancewar jinyar Abualeey gaba gaba kawai takeyi,
to shekarunsa huɗu a kan mulki yayi haɗari shida Baban Jameel da kuma Mamin Jameel ɗin.

A lokacin Yusuf ɗinshi ƙaramine, haka yasa dole aka bawa Unclee Yazidu. Shekaransa ɗaya rak bisa
mulki, a lokacin kuwa wannan dokin Rinƙas yana tsaka da ƙuruciya, abin mamaki dokin nanne ya
kasheshi har lahira a tsakiyar fada, bayan rasuwarsa aka ɗaura ƙaninsa Zarid, shima shekararsa ɗaya
dokin ya kasheshi irin kisar da yayiwa ɗan uwansa zuwa lokacin kuma Allah ya bawa Abualeey sauƙi duk
larurar dake tare dashi haka yasa akace shi zava maidawa mulki, shi kuwa yace shi baya buƙatar mulki a
lokacin jinyar ɗan uwansa shine a gabanshi mu kuma Alhamdulillah an haifi Ibraahim an raine shi lfy
haka yasa,

Yace a bawa ƙanin Zarid Isman abin mamaki ba yadda ba'ayu da isman ya karɓi mulkin nanba fir yace shi
baya so, da aka matsa mishi sai cewa yayi kawai shifa bazaiyi mulkinba tunda sauran yayunsa duk wanda
aka bawa mutuwa yakeyi, kawai sai ya rinƙa faɗin duk abinda sukayiwa Abualeey yace sune suka so
haukatashi kuma sune suke kashe mun yarana uku duka, kuma sunema suka kashe mahaifinsu daga nan
ya zama mahaici yanzu haka shi yana raye ko yaushe yana tsakiyar fada ranar da Aliyu yazo ma Allah ne
ya tsaresa dan Aliyu da dokin ya kashisu dan shi ya kashe mahaifiyarsu ma Lalla Adir tohfa haukacewarsa
da sirrinsu da yake ta tonawa ne yasa muka gane cewa Rinƙas yanayi mana faɗa da magautanmu ne, duk
da ƙanensu mata da suka haɗa uban su dai kamar ba a'lamun cutarwa haka yasa aka matsawa Abualeey
akan ya amshi mulki.

bisa dole dai, ba don yasoba aka sake daurashi kan mulkin Alhamdulillah yanzu dai masarautar Mouley
babu wasu bayyanannun magauta sai dai ɗan abinda ba'a rasaba wanda tsoron yasa suka bari daga
forko dai tsoron Allah bai sa sun tubaba, sai tsoron rinƙas da yasa suka rusuna amman zuwa yanzu sun
gane cewa Allah shine abin tsoro zuƙata sun tsarkaka ko nida abokan zamana bamu da wata matsala
asalima Gimbiya Sahra ita ke shirya komai na Khausar saidai ita batama taɓa haihuwaba sai ta ukun mu
kuma ƴaƴanta duk matane, ta hudun kuma ƴaƴanta yarane amman ita duk mazane mu dai
Alhamdulillah”...

Sai kuma duk suka sauƙe nannauyan numfarfashi Khausar kuwa ido cike da alamun bacci da ciwon ta
lumshesu

Dai dai lokacin kuma Dr Eshaa da Lalla Hafsat suka shigo wacce bisa duk kan alamu tayi mata bayani.

Shogowan sune yasa suka rufe maganar tare da yi mata sannu da zuwa amsawa tayi tare da gaishe su
cike da ladabi.

Cikin kulawa ta zauna kusa da Khausar tare da ɗan shafa gefen fuskarta.

“Sannu Allah ya sauƙa”.


Amin Ummi da Didi suka amsa.

Hajia Bunayyah kuwa baki ta taɓe a ranta tace.

“Allah shi ƙara”.

Ita kuwa Dr Isha cikin kulawa ta muƙawa Didi

Magunguna tare da faɗin.

“Lalla Hafsat tamin bayani, a bata magungunan tasha yanxu In Sha Allah duk wani zugi ko zazzaɓi da
ciwon kai zata daina jinshi”

Amsa Didi tayi tare da fara ɓalla kana tace.

“Ai yanzuma kuwa zan bata”.

Gyaɗa kai Dr Isha tayi tare da sallamansu ta fita.

Didi kuwa maganin ta bawa Khausar tasha kana ta miƙe tabi bayan Dr Isha da bata tsaya duba ko
Khausar ta samu rauni ba, dan tasan ko ta samu rauni tsumin tsarin masarautar da turaren wutan zasu
haɗeta...

Acan Falon Didi kuwa Dr Jameel ne ya bawa Moddibo magunguna kana ya koma gefe yana amsa kiran
da aka masa daga asibitinsu.

Ahankali Moddibo ya miƙe ya nufi ƙofar da sai kashi Side ɗin su, dai-dai lokacin kuma Didi ke dawowa
daga Side ɗin su Khausar.

Kallonsa tayi tare da cewa.

“Ina zaka je?”.

Cikin yanayin zazzaɓin da yake ji ya fesar da numfashi kana ya motsa laɓɓansa tare da cewa.

“Zanje In kwanta ne”.

Tsayuwarta ta gyara kana tace.

“A'a muje dai kaje kaci abinci tukunna”.

Ba musu ya gyaɗa kai kana ya nufi dining tana biye dashi zama yayi tare da ɗan rumtse idanunsa.

Gefensa ta zauna kana tayi serving ɗin sa,

Sai kuma ta kalli Dr Jameel tare da cewa yazo suci abinci.


A hankali Modibbo ya kalleshi jin yana cewa.

“Didi Azumi nakeyi”.

Kai Modibbo ya ɗan jinjina dan zuwa yanzu dai ya fara gamsuwa da sauyawar Dr Jameel, musamman
yadda ya dage da azumi dan daƙushe sha'awarsa.

Ita kuwa Didi kai ta jinjina sannan ta sawa kanta suka fara cin abincin, yana ganawa ya miƙe.

Da sauri tace.

“ina kuma zakaje, kasha maganin ne?”.

Dai-dai lokacin Dr Jameel ya iso wurin kujera yaja ya zauna yana cewa.

“Eh Didi yasha”. Sai kuma ta juyo ya kalli Modibbo tare da cewa.

“Amman fa kamar ba zazzabin kawai ke damunsa ba na lura yana yawan miƙa kamar wanda jikinsa ke
masa ciwo, bini bini ya dafe ƙugunsa”.

Da sauri Didi ta miƙe tare da turawa Dr Jameel ɗin womers ɗin abinci gabansa kana tayi cikin falon dan
tasan ba ƙaramin aikin Dr Jameel bane yayi ɓaram-ɓarama, a gabanta haka yasa ta ma mance yace yana
azumi.

shi kuwa Modibbo wani irin harara ya rabkawa Dr Jameel tare da cewa.

“Ace mutum shi bakinsa baya iya shiru”.

Murmushi Dr Jameel yayi tare cewa.

“Na lura baka taɓa sanin maceba, da alamu jiya kuma kayi yaƙin fatauci shiyasa ƙugu da jinyoyi suke
ciwo, ah aini da na ɗauka kai kam ba abinda zakayi da mace yadda kake wasu abu kamar waliyi, shine
tun ba'aje ko inaba kaje kai ta karya ƙugu ka kwashi Gara, yanzu kuma jiki magayi dan na lura baka
sararawa yar mutaneba”.

Sai kuma yayi saurin dage kansa tare da sakin kara jin yadda Modibbo ya kaiwa bakinsa bugu.

Dariya ya fashe dashi tare da bin Modibbo da ido kana ya dawo tsakiyar falon.

A hankali ya nufi Side ɗin sa saboda wani irin bacci da yake ji ga zazzaɓin ya fara masa yawa alamar
maganin ya fara kokawa da Zazzaɓin yana shiga ya kwanta bisa 3 sitter...

Jakadiya kuwa kai tsaye ɗakin Tarihin Masarautarsu takai ƙyallen budurcin Khausar.
anan aka ajiye wannan frame ɗin kana ta ɗauko sanda da Jigidan Zinare mai tambarin Masarautar
Mouley sai chain na ƙafa shima na Zinare ne kuma munduwa mai tambarin Masarautar, da dai wasu
kaya masu masifar kyau da ɗaukar hankali kai tsaye sashen Didi ta shiga kana ta kalli Didi dake zaune kan
2sitter daga ƙasa Carpet ta zauna tare da faɗin.

“Yawwa Didi gashi an gama haɗawa”.

Sanyayyan Murmushi Didi tayi hakan ganin abin sai ya tuna mata da lokacin da aka kai mata nata cikin
sauƙe ajiyar zuciya tace.

“Toh shikenan mu tafi mu nunawa Niyna daga nan mu tafi da ita”.

Miƙewa Jakadiya tayi suka nufi Side ɗin Niyna daga nan kuma suka shiga sashin abokan zamanta suka
nuna musu kana suka wuce wurinsu Ummi.

Hajja Nana, Innayi da Hajja Umma suka samu azaune suna hira.

Yayin da Ummi Khausar Asma'u Dije da Asiya ke bedroom.

Zama Didi sukayi kana suka sa aka kira su Ummi,Hajiya Bunayya,Aunty Ruƙayya, Aunty Hajara duka suka
fito falon Jakadiya ce tayi musu bayanin cewa.

“Ga wannan Sandar amma yanzu dai an nuna muku ne saboda tabbacin cikekken tukuicin da aka samu
daga Masarautar Mouley ce”.

Wani irin farin ciki ne ya mamaye baki ɗaya ilahirin zuciyoyinsu saɓanin Hajiya Bunayya da take jin wani
sabon kunci da tashin hankali aƙahon zuciyarta.

Jakadiya kuwa cike da alfahari ta cigaba da cewa.

“Kuma yanzu za'a sake mai dashi cikin karagar masarautar tarihin gefenta sai sanda aka samu ɗa namiji
ya cika Shekara ɗaya ranan za'a mallaka mata sandar ahannunta saboda sandar shine zai nuna shaidar
Lalle gadon Masarautar a ɗakinta yake”.

Cike da matsanancin farin ciki Innayi tace.

“Alhamdulillah abinda ake ƙi dai shi ya tabbata in Allah yaso Sarauta dai tana nan ta tabbata a ɗakin
Lalla Didi”.

Niynah kuwa murmushi take tare da faɗin.

“Alhamdulillahi burin magauta bai cika ba”

Acan ɗaki kuwa Asma'u ce ta kalli Khausar tare da ƙyalƙyalewa da dariya kana tace.

“A'a manya gari yane duk bakinki ya mutu. Yah Moddibo yayi aiki kenan”.
Kallonta Khausar tayi tare da tura baki cikin yanayin jin bacci saboda magungunan data sha ta harareta
da kumburarrun idanunta sai kuma ta murguɗa baki.

Ware idanu Asma'u tayi tare da faɗin.

“Eh lallai yarinyar da sauran ki har yanzu Yah Moddibo bai ladab tar dake ba tunda har kika samu idanun
harara da bakin tsiwa”.

Wani kallo Khausar tayi mata cikin dishsheyar murya mai cike da sanyi da rauni alamun ko yanzu tana iya
kuka a hankali tace.

“Hmmm Ladabtuwa na nawa kuma, sai dai kuma in kasheni ya rage yayi”.

Sai kuma ta lumshe idanunta hawaye masu zafi suka zubo ahankali ta taune lips ɗin ta na ƙasa tare da
cewa.

“Naji azabar da tunda Uwata ta haifeni ban taɓa ji ba, salon mugunta kuwa babu wanda Yah Moddibo
bai haddace ba bayan makarantar Hadda da yaje ina ga har da na koyon mugunta da zalumci yaje yayi
Mater's ya iya salon mugunta iri da kala, Ni dai Allah ya sani ba abinda zance sai Allah ya saka min kuma
inyi ta Addu'a Allah ya tsareni da sherrin muguntarsa”.

Ta kare mgnar murya na rawa, da kuma iyakar gskyar zuciyarta.

Wani sabon dariya Asma'u ta ƙyalƙyale dashi harda riƙe ciki kana tace.

“Uhm lallai su Fattanah anji maza wato har Master's Yah Moddibo yayi a fannin mugunta”.

Cikin kauda kai Khausar ta runtse idanunta tare da cewa.

“Ayyah am Asma'u kiyi dariya son ranki kema kwana nawa ne zaki zo irin wannan Matsayin?”.

Murmushi Asma'u tayi tare da miƙa mata wayar kana tace.

“Gashi naga Mommy ke kiran”.

Tana karɓan wayar ta fashe da kuka.

Shiru Mommy tayi tana jin shesh-sheƙan kukanta kusan minti biyu ta ɗauka tana kukan kafin cikin rawan
murya tace.

“Momy ina kwana”.

Ajiyar zuciya Momy ta sauƙe tare da cewa.

“Kin gama kukan?”.

Kamar jira take sai kuma ta sake fashewa da sabon kuka cikin sauƙe numfashi Momy tace.
“Meyesa bakya girma ne Mamana. ai rayuwar nan da kike gani hakuri ake musamman mace dole
abubuwa suzo maka ayanda ba kayi zato ba, ki koyi dauriya Khausar agaban surkunan ki kike fa, kinga
za'a barki agarin da babu kowa naki ki iya dauriya ke macecefa wata rana ma haihuwa zakiyi”.

Kuka ta kuma fashewa dashi cike da rauni tare da cewa.

“Wallahi Mommy ni nafasa Auren zan biyosu in dawo wallahi ni na fasa bazan zauna ba zan biyosu bazan
zauna a garin nan ba kasheni zaiyi”.

Sai kuma taja ajiyar zuciya tare da cigaba da faɗin.

“Dama shi mugune sannan kuma an kawo ni inda ba kowa nawa zai cigaba da yimin mugunta”.

Cikin sauƙe numfashi Momy tace.

“Kul kada In sake Jin kin faɗi haka abakin ki bana so, ce miki akayi aure wasa ne, ina Umminki?”.

Cikin Muryan kuka tace.

“Tana falo”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da faɗin.

“Toh bawa Asma'u ta kai mata”.

Miƙawa Asma'u wayar tayi ta karba kana ta fice ta kaiwa Ummi.

Bayan sun gaisa da Ummi fuska ɗauke da yalwataccen farin ciki Ummi tace.

“Kai Alhamdulillah Momyn Khausar yau muna cike da farin ciki in Sha Allah gobe zamu dawo, zamu dawo
da tukuici mafi tsada da daraja na munduwar masarautar Mouley shaidar yarmu ta kawo budurcinta ”.

Wani banzan kallo Hajiya Bunayya ta watsa mata Ummi kuwa cikin farin ciki ta cigaba da cewa.

“Khausar ɗin mu ta kai budurcinta gidan miji sannan Sarauta wanda muke da yaƙinin in Sha Allah aɗakin
Khausar zai kasance”.

A wannan karon ƙwaffa mai ƙarfi Hajiya Bunayya tayi ta sunkuyar da kanta ƙasa yayin da idanunta suka
kada sukayi Jawur cike da takaici bakin ciki da hassada tace.

“Uhmm ai duk gaggawar asara ta dai jira samu”.

Da kallonta suka bita sabida su dai fulanine ba wata cikekkiyar hausace garesu ba dan haka basu wani
fahimceta ba bare su damu.
Mommy kuwa cikin hayaniyar da take jiyowa tace.

“Naji kamar kina cikin mutane”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin.

“Wallahi ina cikin mutane farin cikine ya hanani in haɗiye abun da zamu tattauna”.

Mommy na murmushin Farin cikin tace.

“Toh ki bari sai kin nutsu zamuyi waya amma ya jikin ƴar taki?.”

Zama Ummi ta gyara tare da faɗin.

“Jiki da sauƙi anzo an bata magunguna yanzuma ina ga bacci zatayi su Asma'u ne suka hanata bacci da
surutu”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da faɗin.

“Toh shikenan Allah ya ƙara sauƙi”.

Ameen Ummi ta amsa kana sukayi sallama.

Acan gadon Khausar kuwa ganin ta samu bacci ne yasa Asma'u, Asiya Dije fitowa.

Fitowar su yayi daidai da ɗaga wayar Lalla Hafsat ta manna akunnenta maganar minti biyu tayi kana ta
janye tare da kallon Asma'u da shigowanta Falon kenan tace.

“Asma'u kizo mu tafi kina da baƙo A Side ɗin Didi”.

Kai ta gyaɗa tare da kallon Ummi batare data bita ba.

Ummi data fahimci tsayuwar da take yasa tace.

“Kije mana”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da bin bayan Lalla Hafsat da ta fara ta fiya tana isa Falon ta saki ɓoyeyyen
ajiyar zuciya ganin Dr Jameel dake zaune kan 3sitter Lalla Hafsat kuwa direct bedroom ɗin Didi ta wuce.

Cikin tsira mata ido da tarin ƙaunarta dake ratsa duk wani magudanan jinin jikinsa wanda yake uzzura
jabarsa ɗaya danne yayi alƙawarin tsakaninsa da Allah bazai ƙara kusantar zinaba, ganinta ya sashi sauke
numfashi mai sanyi tare da lumshe idanunsa kana ya buɗe su akanta tare da cewa.

“Ƙaraso ki zauna anan”.


Ya faɗa yana nuna mata gefensa cikin wani irin yanayi mai tattare da kunya ta nufi gefensa ta zauna kana
ta gaishesa amsawa yayi yana mai tsira mata idanu tare da shaƙar daddaɗan ƙamshin hunran data shafa
Cikin sauƙe numfashi yace.

“Albishir My Asmeey”.

Idanunta aƙasa ta motsa laɓɓanta tare da faɗin.

“Goro”.

Yana binta da wani sihirtaccen kallo yace.

“Fari ko Jaaaaa”.

Murmushi ne ya subce mata asaman laɓɓanta jin yanda yaja kalmar Jaaa ahankali tace.

“Fari ƙall”.

Zamansa ya gyara fuskarsa ɗauke da ƙayataccen murmushi dake bayyana farin cikin dake ciki yace.

“In sha Allah gobe, da Abualeey, Galadima, Waziri da Abban Zakariyya da ƙanin Abbanshi zaku tafi,
saboda za'a je ayi tambayar Aurenmu”.

Tafin hannunta ta sanya ta rufe fuskarta kana ta saki murmushi mai ɗauke da kunya kafin ta ɗago kanta
tare da cewa.

“Allah ya kaimu Allah kuma ya mana zaɓin abinda yafi Alkhairi”.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum amma dai kinyi farin ciki ko?”.

Kai ta gyaɗa still hannunta na saman Fuskarta.

Cikin son janta da hira ya gyara zamansa tare da cewa.

“Kuma harda batun Asiya da Zakariyya ma duk za'a yi tambayar kinsan shi Zakariyya ya riga ya koma
Indi'a amma in Sha Allah yace bazai daɗe ba zai dawo saboda yana so ayi abin cikin ƙanƙanin lokaci in
Allah ya yarda”.

Ahankali tace.

“Ayyah Allah dai ya mana zaɓi mafi Alkhairi”.

Cikin tarin ƙaunarta yace.

“Ameen nan suka ɗan ci gaba da hira”.


Lalla Hafsat da Lalla Khadijah kuwa, duk suna ɗakin Didi hadimai na shirya musu kayansu dan yau da
dare Lalla Khadijah zata koma gidanta. Lalla Hafsat kuwa ƙarfe shida na safe na safen gobe jirnsu zai
tashi zuwa Mexico.

Su Ummi kuwa ƙarfe sha daya zasu tashi.

Wanda kuma da pravate jet zasu tashi so kai tsaye Adamawa jirginsu zai sauƙesu, wanda tunima sun
samu amincewa da sahalewar sauƙansu a Yola international airport, kassn cewar abune na manya ga
kuma su Sheykh Jabeer da sune masu Jihar.

Acan ɓangaren Khausar kuwa bacci ne mai nauyi mai cike da gajiya takeyi.

Yayin da aɓangaren Moddibo ma hakan ne ya kasance sosai yayi bacci kiran sallar la'asar ne ya tashe sa
yana tashi yaji jikinsa yayi sakayau alamar zazzaɓin ya sauƙa, cikin jin daɗi yasa hannunsa bisa mararsa
yana shafawa jin maransa tayi sakayau wani makirin murmushi ne ya subce mishi sai kuma ya lumshe
idanunsa wani irin farin ciki yake ji mara misaltuwa gami da nitsuwa salama kwanciyar hankali da
cikekkiyar lafiya sai kuma zazzafan shauƙi.

Da Zaran ya tuna wasu abubuwa da suka gabata sai ya saki murmushin.

A fili yace.

“Wai Wayyo Didi zai kasheni Yah Mu'allim zan mutu”.

Sai kuma ya ɗan jujjuya idanunsa tare da cewa.

“Farar kura ba, *Minha Vidaa* ga tsoro ga ban tsoro, ga tsiwa ga raki ”.

ahankali ya shiga toilet ya sakaraa kanaa ruwan ɗumi kana ya daura alwala ya fito cikin wani tattausan
yadi fari ƙall ya shirya kana ya feshe jikinsa da turarukansa masu daɗin ƙamshi a bedroom ɗinsa yayi
sallan azahar daya riskeshi yana bacci, kana ya wuce masallaci yana mgnar zuci.

“Sai na hukuntaki da sani makarar samun jam'i da kikeyi kuwa”.

Khausar kuwa kafin akira La'asar ta farka tana tashi Ummi ta sake bata abinci taci kana tace.

“Toh tashi kiyi wonka kiyi salla”.


Kai ta gyaɗa tare da miƙewa tsaye ga mamakinta sosai ciwon yayi sauƙi sai kaɗan-kaɗan da takeji alamun
mgni yayi aiki.

Bayan tayi wanka ta sauya kaya tayi sallan azahar da la'asar ɗin.

Tana bisa sallayar Ummu ta ɗauko mata Magungunan _Aunty Aysha Aliyu Garkuwa_ ɗan bokatjn wata
gumbar madara mai haɗe da kwakwa ta miƙa mata, ba musu Khausar ta karɓa ganin yadda Aunty Hajara
ta tsareta da idanu.

A hankali ta fara ci tana haɗawa da kwakwar gumbar nada ɗan karen daɗi shiyasa ta ci mai ɗan yawa.

Sai kuma ta amshi gorar da take miƙamata wanda na tsumin riɗine da kuma tsimi zuma a cup ta haɗa
mata su.

Cikin tura baki tace.

“Ayyah Aunty Hajara cikina ya cika fa”.

Da sauri ta ɗan sa cup ɗin a baki sabida hararar data watsa mata.

Ajiye kofin tayi bayan ta shanye.

Sai kuma ta kalli Ummi dake cewa ki shiga Bathroom na haɗa miki ruwan ɗumi ki zauna a ciki, kai ta
gyaɗa kana ta shiga.

Toilet ta tayi tsarki da ruwan ɗumi kana ta shiga cikin wanda Ummi ta haɗa matan.

Wanda yaji turaren tsarki ta fito.

Tana baza ƙamshi ita kanta in ta ɗan sunkuyo da kanta sai ta Lumshe idanu sabida yadda take baza
ƙamshi ga kuma kullacar sirri da yafi komai mata daɗi, shiyasa take nace masa wurin shafawa ganin ba
kowa a ɗakin ne yasa ta fita falon tana jin zazzaɓin ya sauƙa kana zugin da ƙasanta ke mata ma ya ragu
sosai.

Haka dai yinin wannan ranan Khausar da Moddibo sukayi yinin jinya kuma Alhamdulillah jiki yayi sauƙe...

Moddibo kuwa yana dawowa masallaci part ɗin Didi ya wuce.

Allah ya sani so yake ya ganta yaga yanayin jikinta amman ya rasa ta yadda zai nematan haka yasa ya
miƙe da nufin zuwa side ɗin dasu Ummin suke kuwa sai ya sauya hanya tare da komawa side ɗinsu Allah
ya sani kunyasu Ummi yakeji, kuma tsoron wannan tsohuwar mai Shegen baki yakeji kada ta kunyatashi.
Bayan sallan isha akazo aka ɗauki Lalla Khadijah ta koma gidanta.

Misalin ƙarfe tara da kwata, Ummi ta kalli Khausar dake kwance gefenta tace.

“Khausar kada kiyi bacci anan fa, tashi ki tafi dakin mijinki”.

Cikin tsinkewar zuciya ta zazzaro idanunta waje, tare da saurin kallon Ummi tana mai girgiza kai kana
tace.

“Na shiga uku Ummi dan Allah, ki barni in kwanan ni bazan koma canba wlh anan zan kwana”.

Kai ummi ta girgiza tare da faɗin.

“Nan kuma Khausar bayan gacan ɗakin mijinki a'a bazai yiwuba. maza tashi ki tafi”.

Da sauri Ummi ta zuba mata ido jin ta fashe kuka tsakaninta da Allah kuwa take kukan. dashi tana yarfe
hannu tace.

“Ni dai dan Allah Ummi ki barni mu kwana anan, wlh tallahi bani da lafiya dan Allah ki barni in kwana
kusa dake”.

Asma'u dake gefe tayi murmushi tare da gyara kwanciyar ta.

Ummi kuwa ganin yanda take kuka da faɗin baza ta je bane yasa tayi shiru...

Sai kuma ta jinjina kai jin Innayi na cewa.

“Ba komai Ummin Jameel barta ta kwana a nan ɗin, gobe ina zata ganku”.

Ita kam Khausar ido ta rufe tana mgnar zuci.

“Yoh ai tarema zamu tafi dan wlh ni dai bazan zaunaba”.

Zuwa lokacin karfe goma harda kota....

Washe gari da asuba ana fita masallaci Aka kai Lalla Hafsat da Hakim Airport.

Bayan ta sallami su Ummi.

Bakwai dai-dai jirginsu ya ɗags zuwa Mexico.


Abujan Nigeria, karfe takwas dai-dai Unclee Naseer ya bar gidan.

Tun fitansa kuwa Amina ke konce a tsakiyar falon bisa Carpet.

A hankali take sauke numfashi sabida ɗan baccin ɗaya fara fizgarta.

Cikin baccin da ya fara nisan, ta rinƙa jin hucin macijin nan, sai kuma tayi saurin buɗe idanunta sabida jin
sanyin jikin macijin yana ratsa cikinta yana ɗan jujjuya kanshi tare dayin sama da kan nashi da ya shigar
ta ƙasar ƴar rigar dake jikinta.

Wani irin fitinennen karkarwa jikinta ya fara, tare da zazzaro idanunta baki ɗaya lokacin da taji macijin
nan ya manna bakinshi kan nimple dinta na hannun dama yayiwa nimple din wani irin damƙa da karf....

*Littafin Sakayya dai na kuɗi ki biya karanta cikin aminci da salama ba haƙƙin kowa a kanki 1k ne kacal
0661110170 gtbank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number
09097853276 in tura Miki ki karanta cikin aminci*

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

59

Tallah !! Tallah !!

Shahararriyar Marubuciyar nan Ikilima Adam (kyauta daga Allah) wacce ta nishadantar daku a littafin ta
mai suna *Kanwata* *kaikajawa kanka , *Rai daya janzaki*.

yau na sake dawowa domin Domin tallata muku Littafaina mai Suna *(RUDANI )* Da kuma *Makauniyar
Shari'a* littafine mai kunshe da Butulci , cin amana ,zagon Kasa , soyayya irin ta gani kasheni , aminci da
saura n su basai n'a cika Ku da surutu ba Hausawa sukace Gani yakori ji.

Karku Manta *Makauniyar Shari'a* sabon littafi ne mai bibiyar Ma'anar sunan sa.

Ya zarce duk littafai na , na baya.


RUDANI littafine mai cike da Rudani da ban Al'ajabi , duk wacce kika fi buƙata zaki biya kudin sa Naira
ɗari biyar kacal.

Farashin kowannen su Naira Dari biyar ne 500 kacal

Domin Karin bayani Ku tuntubeni a lambata kamar haka (09069080725 ko Kuma + 22953726162 ) wacce
Bata shirya Siya ba kada mu batawa juna lokaci.

Domin aikawa da kudi kai tsaye . 3115484026 ikilima Adam first bank

Turo shaidar biya akan wannan 09069080725 sai najiku.

Lokacin daya damƙi nipple ɗin ta akuma dai-dai lokacin itama ta runtse idanunta da masifar ƙarfi jin
yanda yasa harshensa yana ɗo bakin nipples ɗin ta ya mata wani irin zuƙa wanda taji tun daga cikin
Faratun ƙafarta wani irin abu yana biyowa har bakin nipples ɗin ta.

Macijin kuwa zuƙa ya cigaba da yayi.

Ita kam wani irin zogin azaba take ji duk da cewa bata taɓa Shayarwa ba amma ji take zafin yafi ƙarfin
zafin jariri na zuƙan, baki ɗaya ta kasa motsawa dan duk jikinta ya narke koda ya tsanta ta gagara
motsawa bare kuma tayi yunƙurin ceton kanta haka yayita zuƙa tsawon minti biyu da rabi kafin ya zare
harshensa.

Sai alokacin ta iya sunkuyar da kanta ƙasa kaɗan ta kalli bakin nipples ɗin ta jini kaɗan ta gani.

Macijin kuwa harshensa yasa ya fara lashar jinin saida ya lasheshi fes.

Tana gani amma ta kasa taɓuka komai har sai daya lashe jinin duka kafin ya maida kansa kan Breast ɗin
ta na hagu da ƙarfi ta runtse idanunta jin yanda yaja nippes ɗin ta da ƙarfi yake zuƙa kamar zai tsinkeshi.

Wani irin raɗaɗin azaba take ji tun daga ƙasan farcenta abin yana tattura yana bin jijiyoyi da duk wani
magudanan jinin jikinta, wata iriyar fitinenniyar kasala ta fara ji mai masifar yawa bata san lokacin data
runtse idanunta can taji ya sake wanda aƙalla taji ya ɗauki kimanin minti ɗaya da rabi kasa buɗe
Idanunta tayi sai dai tana jin yanda yake lasar saman nipples ɗin ta wanda shima take zaton jinin kaɗan
asama.
Sai kuma taji ya fara zaro kansa zururuuu ya fita daga jikinta lokacin da taji ya fita ajikinta ne ta sauƙe
nannauyan numfashi kana ta buɗe Idanunta ahankali ta bisa da kallo ga mamakin ta sai taga ya koma
wancan dakin daya fito yaje ya kwanta.

Baki ɗaya taji jikinta ya mutu kasala ya rufe ta wani irin Masifeffen baccin da tunda take bata taɓa jin
irinsa ba ne ya rufeta da baya ta koma ta kwanta nan da nan bacci ya ɗauketa awajen...

*Morocco*

A kuma dai-dai lokacin Ummi, Hajja Nana, Aunty Ruƙayya, Aunty Hajara,Hajja Ummah, Hajiya Bunayya,
Asma'u Asiya Dije Zaune suke a falon Didi bisa alamu sun gama baki ɗaya shirin su tafiya ne yanzu zasuyi.

Khausar kuwa zaune take gefen Ummi tana sassayan kuka da shesh-sheƙa tuni. Muryanta har ya dishe
dai-dai lokacin kuma Ibraahim da Haiydar suka shigo.

Ahankali Haiydar ya miƙa mata hannu kana cikin sanyi murya yace.

“Zanyi Missing naki Addah Khausy.

Zamu tafi zan barki inda babu kowa namu.

Zanyi missing naki da halayen ki.

Ina ta tunanin idan na koma wazai min faɗa,

Idan na bar datti a falon Momy?”.

Sai kuma ya lumshe idanunsa hawaye na taruwa a idanunsa cikin sanyi ya cigaba da cewa.

“Wazai yi min masifa idan na buɗe Labule ban gyara ba?.

Wazai min mita idan na ɗauki System ɗin Momy?.

Idan farcena ya taru Addah Khausi Wazai yanke min?”.

Cikin rauni ya ida maganar hawaye na cika kwarmin idanunsa tare da kwaranyowa.

Da sauri ta tashi ta faɗa jikinsa ta rungumesa tare fashewa da kuka tace.

“Wallahi tare zamu tafi Haiydar ni baza Abar ni anan ba tare zamu tafi”.

Ahankali Didi ta jawota tare da cewa.

“Kiyi haƙuri Khausar kinji ko?


Ai bake kaɗai za'a bari ba ba gani ba?

Aini zan zame miki madadin Mommy Sannan ga Rahama zata zame miki madadin Asma'u”.

Sunkuyar da kai Asma'u tayi saboda jin hawaye masu masifar zafi na zubowa a kuncinta tunda suka tashi
da Khausar basu taɓa yin wata ɗaya basu haɗu da juna ba tun suna Nasury koda hutu akayi wanda
ƙawance shiya zama sanadin Mutuntaka sosai tsakanin Momy da Ummi duk da Ummi ta girmi Momy
sosai amma suna mutumtakan da yafi ƙarfin ƙawance.

Jin Kukan Asma'u ne yasa Khausar miƙewa daga jikin Didi ta kifa kanta kan cinyar Asma'u tana kuka.

Haka nan Hajja Nana taji rauni ganin za'a tafi abar Khausar ɗin ta agarin da batasan kowa nata ba.

Akuma dai-dai lokacin Dr Jameel da Moddibo suka shigo atare cikin sanyi Modibbo ya rumtse idanunsa
sabida jin yadda kukanta ya daki ƙahon zuciyarsa, cikin yin ƙasa da kai ya tsira mata idanu, tun da gari ya
waye yake son ganinta amma ya rasa hanyar da zai bi ya ganta.

Runtse idanunsa yayi jin sautin kukanta Ji yake tunda yake bai taɓa jin wani kuka da yasashi baƙin ciki da
ƙunci ba kamar sautin Kukanta Ahankali ya ƙarasa cikin falon tare da zama gefen Ummi dake kan 3sitter
wanda ke fuskantar Asma'u da Khausar sai ya zama na yana fuskantar Khausar.

Cikin sanyin Murya yace.

“Ummi har kun gama shiri kenan ?”.

Cikin sanyi ta gyaɗa masa kai tare da cewa.

“Mun gama shiri Babana”.

Numfashi ya fesar tare da kallon Khausar dake kuka yace.

“Ummi zamuyi kewar ku”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Nima zanyi kewar ka Babana Nasan kona koma Gembila, baza taimin daɗi ba tunda ba kai ba Jamelu
na".

Cikin kula Yace.

“In Sha Allah baza mu daɗe ba zamu zo da izinin Ubangiji”.

Cikin jin kewarsu tace.


“Toh Babana yan zu dai ga amanar ƴata na bar maka amanar Khausi”.

Shiru yayi tare da sunkuyar da kansa ƙasa haka nan yake ji amanar tayi masa nauyi.

Sai kuma ya ɗago kansa ya kalli Hajja Nana da duk tayi sanyi tana matsar ƙwalla tace.

“To ga dai yarinya Khausar nan mun kawo maka amanar kuma bata da kowa anan sai kai sai kuma
Iyayenka wanda su na gamsu da Mutuntakansu, Kararsu, da kuma dattakon su”.

Sai kuma ta share hawayen daya zubo mata ta cigaba da faɗin.

“Nasan su zasu riƙe min Khausar babu haufi kaine dai ban sani ba kana nan kullum fuska babu murmushi
bare fara'a gakanan ga ka nanne ne dai, dan haka ni dai ajihar min da jikata, banda cin zali”.

Kallon ta yayi sai kuma ya sake sunkuyar da kansa bai san wacce kalma zai fada musu ba saboda girman
abinda yake ji acikin zuciyarsa ya kuma lura wannan tsohuwar ya rigimace.

Dr Jameel kuwa kallon Didi yayi cikin yanayinsa na raha yace.

“Didi dan Allah ki ciwa Khausar ta daina kuka gashi tana samin Matata kuka bana so mu rabu tana kuka,
gwara ita tana tare da mijinta Ni kuma zata sa matata ta tafi tana kuka Wazai rarrasa min ita?”.

Baki sake Hajja Nana ke kallonsa kafin ta hararesa da faɗin.

“Oooh Allah Ubangiji ya shirye ku kai kuma wa zai rarrasheta kake tuhuma?Gata da Uwarta kace Wazai
rarrasheta?”.

Murmushi yayi tare da langwaɓar da kai yace.

“Wallahi Hajja Nana ko Ummi bazata rarrasa min Asma'u kamar yanda nake so in rarrasheta ba”.

Dai-dai lokacin Jakadiya tashigo tare da kallon su Ummi kana tace.

“Toh Bismillah ku fito Mazan baki ɗaya sun fito Sarki yace afaɗa muku ku fito jirginku ya kusa tashi”.

Ummi ce ta fara miƙewa kafin Hajja Nana ta miƙe.

Asanyaye Innayi ta miƙe ta rungume Hajja Nana tare da cewa.

“Allah sarki Ƙawata zanyi kewarki”.

Cikin sanyi Hajja Nana tace.

“Ayyah nima zanyi kewan ki ko yaushe zamu sake haɗuwa”.


Innayi na ɗan raba jikinsu tace.

“In sha Allah bazan daɗe ba zamu zo Auren Asma'u zanzo”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da cewa.

“Allah ya kaimu lokacin ya kawo ki lafiya”.

Sai kuma ta kamo hannun Khausar ta sanya cikin na Innayi tare da cewa.

“Toh ni dai ke nafi saninki akan kowa acikin Masarautar nan, dan haka ga amanar Khausar”.

Kai Innayi ta jinjina tare da faɗin.

“In sha Allah zaku same mu masu riƙe amana da kawaici da kara”.

Da sauri Khausar ta janya hannunta acikin na Innayi ganin Ummi ta nufi ƙofan fita yasa ta faɗa jikinta ta
fashe da matsanancin kuka kukan daya sa jikin kowa yayi sanyi cikin rauni take cewa.

“Ummi Ni na fasa mu tafi tare bazan zauna ba, bani da kowa anan fa Ummi, nikam zan koma wajen
Momy na kaifafa Haiydar mafa tafiya zaiyi”.

Cikin shesh-sheƙan ta cigaba da cewa.

“Ba Momy ba Haiydar ba Raudhat sannan ba Asma'u Ummi abarni ni kaɗai ni na fasa”.

Ummi kuwa cikin ƙoƙarin hana kanta kuka da take ji da sauri ta kauda kai dan raunin Khausar yayi yawa a
hankali tace. “Khausar alƙawarin da kika yiwa Yayanki Jameel kenan? Kin fasa cika masa alkawarin
kenan?”.

Cikin matsanancin kuka ta gyaɗa mata kai tare da cewa.

“Na fasa Ni na fasa bazan iya ba, Zanyi tayi mishi addu'a kuma Allah ya bashi haƙuri ni bazan zauna da
Yah Moddibo ba zaita ta cin zalina”.

Ahankali Rahama ta matsa kusa da ita tare da faɗin.

“Ayyah Addah Khausar ki zauna mana muma muna sonki muna son zama kusa dake kuma zan zame miki
madadin Asma'u Didi Madadin Mommy Yah Ibrahim Madadin Haiydar Innayi Madadin Hajja Nana”.

Cikin sauri ta juya ta rungume Haiydar tare da fashewa da matsanancin kuka Haiydar kuwa kasancewar
sa Namiji yasa yashiga share mata hawayen ta yana cewa.

“Kiyi shiru Adda Khausy in Sha Allah muna tare dake duk inda kike”.

Ya faɗa hawaye na zubo masa.


Ajiyar zuciya Ibraahim ya sauƙe tare da riƙe hannun Haiydar yace.

“Haba Haiydar ya haka?.

Kana Namiji kana Kuka ita kuma ya zatayi?Mu tafi”.

Juyawa Haiydar yayi tare da nufar kofar cikin sauri Khausar ta yunƙura da niyyar bin bayansa tana cewa.

“Ni wallahi na fasa zan koma bazan zauna ba Yah Jameel yayi haƙuri bazan iya cika alkawarin saba ni ban
san nan za'a kawoni ba shi yasa”.

Moddibo kuwa wani irin suya da ƙunci yake ji acikin zuciyarsa Kukane da yake saka masa ƙunci
azuciyarsa babu wani abu da yaji baya sonji kamar kukanta.

Didi kanta jikinta yayi sanyi saboda yanda Khausar ke kuka.

A ɗan raunane Aunty Hajara ta kalleta kana tace.

“Khausar ya za'a yi kiyi haka tun safe kike ta kuka sannan har yanzu ba zaki bari ba zaki sawa kanki
zazzaɓi muma haka kike so mu tafi kenan muna kuka?”.

Cikin rauni ta ƙarasa Maganar hawaye na cika mata Ido.

Faɗawa Jikinta Khausar tayi tare da faɗin.

“Yanzu Aunty Hajara sai ku tafi ku barni anan?”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“To ai ko wacce mace haka ta saba ,Aɗauketa daga inda ta sani daga wuraren data sani cikin Mutanen ta
Yayunta, Ƙannenta Iyayenta”.

Kai Khausar ke girgiza wa tana cigaba da riskar kuka.

Aunty Hajara kuwa cikin sanyi da zubda hawaye ta cigaba da cewa.

“Sannan akaita cikin ƴan Uwan mijinta, Iyeyensa, Yayunsa, Ƙannensa su zauna lafiya da ita su zame mata
dangi dan haka kema ki zauna lafiya dasu”.

Sabon kuka ta fashe dashi sai kuma ta kalli Hajja Nana Muryanta na rawa ta kifa kanta kan kafaɗar Hajja
Nana tace.

“Yanzu Hajja Nana kema kin yarda zaku tafi ku barni”.

Hawaye na zuba a idonta tace.


“Toh ya zanyi Khausar ke kika ce kina son Moddibo fa ke kikace kina sonshi sannan yanzu an Aura miki
shi an kawo ki ki riƙa kuka nima ki sani kuka ba gaki ga masoyinki ba”.

Ta ƙarashe maganar tana share hawaye tare da nufar hanya tana cewa.

“Allah ya ƙaddara saduwarmu Khausar”.

Da gudu Khausar ta zabura zata bita ganin haka yasa Moddibo saurin miƙewa wanda shi kansa baisan
lokacin daya miƙe ba.

Hannunta ya kama ya riƙe tare da haɗe tafukan hannunsu wuri ɗaya.

juyawa tayi ta kallesa da fuskanta tayi jazir ga idanunta sun kumbura murya na rawa tace.

“Ka sake ni zan bisu bazan zauna ba”.

Wani irin rawa lips ɗin sa keyi so yake yayi magana amma ya kasa wani irin ƙuna zuciyarsa keyi kukanta
na tayar mishi da hankali.

Hajja Nana na fita Ummi tayi saurin bin bayanta ta fita Asma'u ma cikin rauni ta miƙe ta fita haka Dija,
Asiya, Aunty Ruƙayya, Hajiya Bunayya suka miƙe cikin tashin hankali ta fashe da sabon kuka idanunta
akan hannunta daya riƙe tace.

“Nikam ka sake ni zan bisu”.

Sai kuma ta maida kallon kan Hajiya Bunayya dake ƙoƙarin fita tace.

“Addah Asiya, Dija duk tafiya zakuyi ku barni ba wanda za'a barni ni dashi sai ni kaɗai”.

Jin haka yasa duk sukayi saurin ficewa Didi ma miƙewa tayi tabi bayansu haka Dr Jameel da Rahama duk
suka fice domin yi musu Rakiya.

Ganin duk sun fita yasa ya janyo hannunta suka bi ta cikin Corridor da zai sadasu da Side ɗin sa.

Tana mai ci gaba da kukan suka haura, suna haurawa kai tsaye Falon shi ya nufa da ita suna shiga ya
maida ƙofar ya rufe Falon...

Ahankali ya ajiyeta bisa kujera, ita kuwa Khausar kuka ta kuma fashewa dashi, kukane wanda kasan daga
ƙasan zuciyarta yake fitowa.

Cikin sanyi ya janyota jikinsa ya rungumeta hannunsa na dama ya buɗe ya haɗa da nata tare da tsarkake
yatsun su, kana ya runtse hannu ya ɗago hannun nata ya manna kan sajensa yana shafawa.

Haka nan yake jin wani ciwom kukan ta yayin da hannunsa daya ke shafa bayanta alamun tayi shiru
amma ina kukan ta sai ƙaruwa yake aƙalla sun ɗauki minti biyar ahaka amma Still kukanta ƙaruwa yake
bai tsaya ba...
Adai dai lokacin kuma tawagar motocin su Hajja Nana ya fita daga cikin Masarautar ya nufi Saleh Ramat
International Airport wanda zai kaisu Adamawa kasancewar Private Jet ne yasa suna tashi daga Morocco
kai tsaye Adamawa zasu sauka.

ƙarfe goma dai-dai Jirginsu ya ɗaga daga Rabat Morocco zuwa Adamawa Nigeria...

Acan Side ɗin su Moddibo kuwa cikin sanyi yace.

“Kiyi haƙuri ki daina kukan nan”.

Cikin matsanancin kuka take janye hannunta daga cikin nasa tana mutsu-mutsu da jikinta alamun so take
ta kwace kanta murya a disashe tace.

“Ni zan tafi”.

Ganin haka ne yasa ya kuma ajiyeta akan kujeran kana ya durƙusa gwiwoyinsa agabanta sai kuma ya riƙe
hannayenta tare da buɗa tafin hannunta duka biyu ya daura akan sajensa wanda yake da yaƙinin tana
so, idanunsa ya ɗago ya kalleta cikin wata raunatacciyar murya mai cike da rauni da tausasawa yace.

“Kiyi haƙuri kukan yana samun ciwo da ƙuci azuciyata kiyi haƙuri kibar Kukan”.

Ina kukanta ta cigaba dayi tana cewa.

“Ni zan koma bazan zauna anan ba garin da bansan kowa ba!”.

Lumshe idanunsa yayi kana ya buɗesu akanta yace.

“Ba gani ba ai kin sanni Yah Mu'allim ɗinki nefa, ko dai yanzu kin daina son nawa ne”.

Cikin zubda hawaye tace.

“Ni ba mai sona a nan”.

Tafin hannunshi yasa yana sharce mata hawayen tare da cewa.

“Kiyi haƙuri bana so inajin kukan yana tada min hankali yana samin ciwo azuciyata kiyi haƙuri ki daina
Kuka *Minha Vidaa* bana son ki daina”.

Sai kuma ya taune lip ɗin sa na ƙasa tare da faɗin.

“Idan har ina jin tsoron da takaicin kukan wani ɗan Adam to Kukan kine Yana min suya da ƙuna azuciyata
dan Allah ki daina zubda hawaye ki ki kalleni nine fa Yah Modibbo ɗinki da kikacewa su Lamido shi
kikeso, ko dai kin daina Sona ne *Minha Vidaa?*

Kai ta gyaɗa tare da cewa.


“Ni dai zan koma gida aikaima ba sona kake ba In banda cin zalina babu abinda kake min tunda muke
atsawon rayuwata zalina kake ci, kasa adakeni ka sani kaɗe ɗankwali ka zalunceni kuma yanzu ma in na
zauna mugunta zakai tamin”.

Kai ya girgiza cikin fesar da numfashi yace.

“Bazan miki mugunta ba *Minha* niba mugu bane”.

Cikin shesh-sheƙan kuka ta girgiza kai tare da cewa.

“Baka Sona katsaneni su Momy suka yarda suka kawo Ni wajen wanda baya sona ya tsaneni suka tafi
suka barni”.

Runtse idanunsa yayi tare da faɗin.

“Nine bana sonki *Minha?*”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Eh mana baka sona basai mugunta kake tamin ba”.

Kai ya dafe cikin jin zafin hawayenta yace.

“Yaushe nace miki bana sonki, kuma yaushe nai miki mugunta?”.

Cikin tura baki da shesh-sheƙa ta goge fuskarta tace.

“Shekaran jiya da daddare ba mugunta kayi min ba kakusan ka kasheni, kuma sai Allah ya saka min duk
muguntar da kake min”.

Cikin taushin lafazi mai cike da kulawa cikin muryar da kashe jiki da zuciya yace.

“Toh kiyi haƙuri ki yafe min ki daina yimin Allah ya isa”.

Hawaye na kwaranya daga idanunta ta maƙe kafaɗarta da cewa.

“Wallahi bazan yafe ba”.

Da damuwa asaman fuskarsa ya motsa laɓɓansa tare da cewa.

“Ya Salam mijinki ne baza ki yafewa ba *Minha* ”.

Kai ta gyaɗa cikin tabbatar wa tace.

“Eg bazan yafe ba tunda zalina kakeci”.

Sai kuma ta kifa kanta ahannun kujera ta cigaba da yin kuka.


Duk rarrashin ta da yake taƙi yin shiru.

Ahankali ya miƙe ya nufi bedroom ɗin sa, ganin ya tafine yasa ta yunkura cikin sauri ta miƙe ta nufi ƙofa
tana murɗa handle ɗin taji kofar arufe, komawa tayi ta zauna kan kujeran data tashi kana ta fashe da
sabon kuka fahimtar ya rufe ta yadda bazata iya buɗewa bane.

Moddibo kuwa yana shiga bedroom ya ɗauki wayanta.

Call log yashiga number Momy ya Kira buga ɗaya ana biyu ta ɗauka yana dai-dai bakin ƙofan zai fiti falo
yaji Momy ta ɗauka cikin nutsuwa, girmamawa, Mutumtaka, kara gami da risinar da Kansa ƙasa yace.

“Momy Barka da Safiya”.

“Barka dai Moddibo ko?”.

Cewar Momy.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Eh Momy nine”.

Kai ta jinjina tare da cewa.

“Ya gida yasu Khausar suna lafiya?”.

Cikin damuwa da yanda yake jin shesh-sheƙan kukanta yace.

“Momy tana lafiya amma tunda su Hajja Nana suka tafi take ta kuka Momy nayi-nayi ta daina Kukan
taƙi”.

Cikin raunin Murya irin na wanda ke gab da zubda hawaye ya ƙarasa Maganar saboda har cikin ransa
yake jin kukanta sai kuma ya cigaba da faɗin.

“Momy dan Allah ki rarrasan min ita kukan zai sa mata zazzaɓi Momy ki rarrasheta ki bata haƙuri”.

Cikin sauƙe ajiyar zuciya Momy tace.

“Yanzu ina Khausar ɗin?”.

Ahankali yace.

“Gata nan”.
Dai-dai lokacin kuma ya isa gaban Khausar ɗin durƙusawa yayi agabanta tare da manna mata wayar
akunnenta.

Momy kuwa ahankali tace.

“Hello Khausar”.

Ta buɗe baki da niyyar cewa na'am Momy kenan kuma kuka ya kufce mata cikin rauni tace.

“Momy sun tafi sun barni basu barmin kowa ba babu wanda na sani”.

Sai kuma tayi shiru sakamakon kuka da yaci ƙarfinta kusan minti biyu ta ɗauka tana kuka still wayan na
maƙale kunnenta.

Kallonta kawai Moddibo keyi ya rasa me yake masa daɗi suya yake jin zuciyarsa nayi, hannunta ɗaya na
riƙe da nashi yana shafa sajensa yana kallonta ji yake kamar ya buɗe ƙahon zuciyarsa ya sata acikin ya
rufe kofar koda zata daina kukan.

Ganin yadda hawayenta ke kwaranya ba ƙaƙƙautawane yasashi, ɗan ƙara matsota, tafukan hannunsa
yasa ya tallabe fuskanta tare da matso da tashi fuskar a hankali ya zare harshen sa.

Wani irin dogon ajiyar zuciya Khausar taja a lokacin da taji, sanyin tattausan harshensa yana ratsa
kumatunta.

Shi kuwa Modibbo cikin yanayi na musamman, ya fara lasan hawayenta tare da hanasu zuba.

Ita kuwa Khausar haka nan taji ta gaza barin kukan.

Ganin baza tayi shiru ba yasa Momy cewa.

“Toh yanzu magana zakiyi ko Kuka zakiyi Khausar?”.

Cikin kuka sosai tace.

“A'a Momy”.

Sai kuma ta cigaba da kuka.

Cikin ɗaure fuska Momy tace.

“Idan baki daina Kukan nan ba kashe wayar zanyi”.


Kai ta girgiza tare da faɗin.

“Momy na daina”.

Ajiyar zuciya Momy ta sauƙe kana tace.

“Wai ni kam Khausar kinyi hauka ne? meyesa baki da hankali ne? Nace wai hauka ne a kanki?”.

Cikin ƙoƙarin hana kanta kuka da shesh-sheƙa take girgiza kai.

Modibbo kuwa a hankali ya lumshe idanunsa domin yanajin duk abinda Mommy ke faɗa, sai kuma yaci
gaba da lasar kumatunta da duk ɗigon hawayen da zai ɗiso.

Momy kuwa cikin haɗa fuska tace.

“Waye kika taɓa ganin yayi haka?.

Ke dama kin ɗauka Aure wasa ne?

to ki nutsu ki maida hankalinki cikin jikinki kisan abinda kike yi Aure ba abin wasa bane Aure Sunnar
Manzon Allah (S.A.W) kuma Aure unarnine na Allah da Manzonsa sannan kuma keda kanki kikace zaki
rayu dashi a ko wanne yanayi.

Dan haka babu yanda za'a yi adawo dake kin taɓa ganin anyi Auren ƴa mace ta koma gidansu?”.

Cikin matsanancin kuka ta girgiza mata kai Momy kuwa cikin nutsuwa ta cigaba da faɗin.

“Hakkine da iko da matsayin miji duk inda yaga dama ya ajiye matarsa ya za'ayi Kice ya dawo dake hauka
ne akanki?.

Haka Ummi da muka yi waya take faɗa min Haiydar nata kuka kamar ransa zai fita saboda ya tafi ya barki
kina kuka duk hankalinsa ya tashi zaki sa yaro adamuwa kisa ya dawo min da zazzabi shi kansa mijinki kin
tayar masa da hankali”.

Cikin faɗa ta cigaba da cewa.

“Har mijinki zai riƙa rarrashinki yana cewa kiyi haƙuri amma ki ƙi kiyita kuka kamar ibada”.

Khausar kam shesh-sheƙa ta cigaba dayi so take ta hana kanta kuka amma kukan yaƙi haɗiyuwa.

Cikin damuwa Momy ta cigaba da cewa.

“Ok zakici gaba da kukan kenan?”.


Kai ta girgiza tare da faɗin.

“A'a Momy na dainaaa”.

Irin yanda take kukan har numfashinta na yankewa.

Momy kuwa cikin damuwa ta cigaba da faɗin.

“Mijinki yaita rarrashin ki ki ƙi rarrashuwa hauka ne akanki, Kiyita kuka kina cewa zaki da kowa ba ganan
Maman mijinki ba ai zata zame miki madadina in dai kika mata biyayya zata maye miki gurbina mijinki
kuma dole ki masa biyayya sannan ki bishi sau da ƙafa domin shine komai na rayuwar ki a yanzu saɓa
mishi kamar saɓa umarnin Allah da Manzonsa ne da suka ce Ayiwa miji biyayya”.

Kuka ta cigaba dayi tana jan ajiyan zuciya.

Moddibo kuwa ganin Momy nayi mata faɗa sannan bata daina kukan ba yasa ahankali yasa hannu ya
zaro wayar daga kunnenta kana ya mayar kunnensa cikin sanyi da ƙasƙantar da kai murya a raunace
yace.

“Kiyi haƙuri Momy rarrashinta za'a yi ba faɗa za'a yi mata ba”.

Yana maganar kamar zaiyi kuka.

Kai Momy ta girgiza kana tace.

“Khausar baza taji rarrashi ba idan ta fara kuka batasan bari ba kafita harƙanta ka barta idan tayi Kukan
tagaji da kanta zata bari ka barta na lura Khausar rigima ne da ita”.

Sake ƙasƙantar da muryarsa yayi yace.

“Momy kiyi haƙuri In Sha Allah zan rarrasheta za tayi shiru Mommy bayan iya barinta tana kukaba zai
cutar min da ita”.

Kai Momy ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan sai anjina”.

Ahankali ya sanya hannunsa kan kumatunta ya fara share mata hawaye kana cikin sanyi da taushin lafazi
yace.

“Kiyi haƙuri ni ba mugu bane bazan miki mugunta ba, nifa Mijinki ne ba kyau kada ki sake cewa mijinki
Mugu bakya tsoron Allah ya ƙona kine?”.

Cigaba da kuka tayi wanda yake fitowa daga ƙasan ranta cikin rauni tace.
“Aini ban ce maka mugu ba amma dai kana cin zalina shekaran jiya kusan kasheni kayi kuma Allah zai sa
kamin”.

Sake ƙasa da murya yayi cikin taushin lafazi yace.

“Kiyi haƙuri In Sha Allah bazan sake ba ki yafe min kinji ki yafewa Yah Moddibonki Minha”.

Kafaɗa ta maƙale tare da tura baki da juya kumburarrun idanunta tace.

“Ni dai ban yafe ba sai Allah ya saka min daga duniya har kiyama bazan taɓa yafe maka ba”.

Zare idanunsa yayi sai kuma ya langwaɓar da kansa yace.

“Ayyah Khausar am ki yafemin kiyi min duk horon da zaki min amma kiya femin”.

Cikin shesh-sheƙan kukan ta kallesa kana ta tura bakinta tace.

“Da gaske?”.

Cikin sauƙe numfashi yace.

“Yess kimin duk hukuncin da kikaga ya dace da laifina, Amman banda kuka kuma banda cewa bana sonki
da kuma cewa zaki koma”.

Cikin sauƙe numfashi shesh-sheƙan tace.

“Toh nima yanda kake cin zalina sai na rama ka kaɗe ɗankwali”.

Ba zato yaji murmushi ya sufce masa sabida mgnar tazo mishi a bazata.

Ya kuma lura yadda tayi mgnar kamar hakan shine babban burinta, ɗan ware idanunsa yayi tare da
cewa.

“In kaɗe ɗankwali kuma?”.

Cikin tura baki ta gyaɗa kai tace.

“Eh kaima ba haka kake min duk abinda nayi kaima mugunta da kayi min ka kaɗe ɗankwalin kaji abinda
nake ji”.

Numfashi ya fesar cikin tsira mata ido yace.

“Idan na kaɗe ɗankwalin zakiyi shiru?”.

Da sauri ta gyaɗa masa kai tare da faɗin.

“Eh”.

Sassayan ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.


“Toh kawo ɗankwalin in kaɗe sau nawa zan kaɗe?”.

Kallonsa tayi ta wani tura bakisai kuma tace.

“Da gaske zaka kaɗe?”.

Girarsa ɗaya ya ɗaga mata.

Cikin jin dadi tace.

“Toh Sau hamsin zaka kaɗe”

Ware manyan idanunsa dake narke yayi tare da yarfe hannu da faɗin.

“Wayyo Allah na Ni Aleeyu”.

Sai kuma ya zauna ya kifa kansa akan cinyarta cikin langwaɓar da kai yace.

“To ai zaki kashe mijinkeeh”.

Ya ƙare maganar cikin shu'umar muryar da tasa jukinta mutuwa,

Ƙyafƙyafta idanunta tayi kana tace.

“Ba nima kana sani ina kaɗewa sau 30 ko sau 20 ba?“.

A hankali yace.

“Toh ai ke 50 kikace inyi”.

Cikin sharce hawayenta tace.

“Toh kasan Ai laifin da kayi yafi nawa yawa da zafi ko?”.

Numfashi ya fesar kana yace.

“Toh shikenan kawo ɗankwalin In kaɗe”.

Ɗankwalin abayar kanta ta cire ta miƙa masa karɓa yayi yana ɗan buɗawa.

Baki ta tura tare da cewa.

“Ai wannan ma bashi da nauyi bari In ɗauko maka ɗan kwalin Less”.

Saurin riƙo hannunta yayi ganin ta yunƙura yace.


“Ainima wanda nake saki kike kaɗewa bana Less bane kin manta?,Na Uniform ne na Uniform kuma be
kai wannan kauri ba”.

Baki ta tura tare da faɗin.

“Toh ka kaɗe”.

Cikin tsira mata idanu yace.

“Ina idan na kaɗe zakiyi shiru?”.

Gira ɗaya ta ɗage cikin jin dadi tace.

“Eh mana kai dai ka kaɗe na gani”.

Murmushi yayi kana yace.

“Toh ki share hawayen ki”.

Ba musu ta sanya hannunta ta share hawayen yayin da take sakin murmushi tana tuna yanda take jin
azaba ahannunta idan ta kaɗe sai kuma ta ɗan ɓata fuska da faɗin.

“Toh kaje ka kaɗe mana”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh muje”.

Kallonsa tayi da kumburarrun idanunta tace.

“Ina?”.

“Muje mana kiga yanda zan kaɗe”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.

“Ok”.

Hannunta ya riƙe suka shiga bedroom ɗin kana suka wuce Bathroom.

Bocket ya jawo ya sa ɗankwalin kana yasa ruwa.

Juyawa yayi ya kalleta tana tsaye bakin ƙofa tana murmushi kuma har zuwa lokacin tana sauƙe ajiyar
zuciya na kukan da tayi amma kuma fuskarta ɗauke da murmushi ya lura kaɗe ɗankwalin zai sata farin
ciki ganin itama yau ta samu ƴanci zata sashi aiki cikin langwaɓar da kai ya kwaikwayi muryarta yanda
take roƙon sa abaya yace.

“Ayyah Yah Mu'allim a kiyi haƙuri mana In cire rigar jikina kar in jiƙe”.

Ka faɗa ta maƙe kana ta tura bakinta tace.

“Ai kaima lokacin da kake sani kaɗewa harda hijabi ma ajikina da kuma Uniform ɗina haka kuma nake
kaɗewa”.

Sake langwaɓar da kai yayi tare da narkar da murya yace.

“Kenan yanzu bazan cire Jallabiyar ba?”.

Kai ta gyaɗa tana murmushi tace.

“Yesss Of Course kayi ahakan”.

Ta ƙare maganar tana cilla girarta sama fuska ɗauke da murmushin mugunta.

Kai ya gyaɗa tare da tsugunnawa ya matso ɗankwalin acikin bokitin”.

Cikin sauri ta wani tura baki tace.

“Ai ba'a matse ɗankwalin sosai kaɗan ake matsewa”.

Ta faɗa tana karasa shiga cikin Banɗakin abakin Bathtub ɗin ta zauna shikam cikin wani irin yanayi na
musamman ya fara kaɗe ɗankwalin na farko, hammm ya ja numfashi sabida sanyi ruwan daya watsu a
jikinshi,

sai kuma ya kaɗe na biyu kana ruwan ya watsu a fuskarsa sake kaɗewa yayi Still ruwan ya sake watsuwa
afuskarsa tuni sajensa ya jiƙe.

Ido ta tsirawa Sajensa tana sakin murmushi Allah ya sani sajensa na masifar yi mata kyau musamman
yanzu da fuskarsa ta jiƙe da ruwan sai ƙyallin sajen keyi murmushi kawai take tafi kowa sanin yanda zaiji
a hannayensa idan ya kaɗe.

Moddibo kuwa sau bakwai ya kaɗe sai kuma ya tsugunna zai mayar cikin Bokitin.

Cikin sauri ta kamo hannunsa tace.

“Wallahi sai ka sake kaɗewa ai bai bushe ba”.

Lumshe idanunsa yayi tun lokacin da hannunta ya sauƙa kan nasa jin tsikan jikinsa na tashi saboda laushi
da kuma santsin hannunta haka nan ya tsinci kansa cikin wani irin farin ciki da shauƙi da kuma nishadi
ɗan marairaice fuska yayi kana yace.
“Toh shikenan”.

Sai kuma ya ƙara uku kafin ya kalleta yace.

“Toh yayi In tsoma”.

Cikin jin daɗi ta gyaɗa masa kai sake tsomawa yayi ya matse zuwa lokacin baki ɗaya Fuskarsa ta gama
jiƙewa har ruwan na ɗiga tal-tal-tal kana gaban Jallabiyarsa ma ya jiƙe ahaka dai har ya tsoma sau biyar
ya kaɗe sai kuma ya ajiye ɗankwalin acikin Bokitin ya riƙe ƙugunsa tare da cewa.

“Wayyo Allah ƙuguna”.

Still sajensa na ɗigar da ruwa til-til-til.

Dariya ta ƙyalƙyale dashi harda dafe ciki.

Tsayawa yayi yana kallon yanda dimples ɗin ta ya lotsa da kuma yanda fararen haƙoranta suka bayyana
suna sheƙi duk da cewa ga yanda fuskarta yayi ja da kuma idanunta suka kumbura cikin ƙyalƙyala dariyar
tace.

“Madallah ka dai ji yadda nake ji. Allah ya ƙara ai nima haka nake ji kuma wallahi saura arba'in da biyar”.

Ta ƙare maganar tana mishi signal ɗin daya sashi jin wani irin fitinenne abu na zirya daga tsakiyar kansa
har zuwa tafin sawun shi.

Karya kai yayi tare da langwaɓar da murya yayi kalar tausayi kamar yanda da take masa yace.

“Dan Allah Malama kiyi haƙuri arage min yawansu yayi yawa hannuna ciwo yake”.

Cike da farin ciki ta kuma fashewa da dariya kana ta miƙe ta riƙe ƙugu tace.

“Haka nake ji kaima kayi”.

Sai kuma ta zuba wa sajensa idanu tana kallon yanda ruwa ke cigaba da ɗiga tal-tal-tal.

A hankali yasa babbar yatsarsa na hannunsa na dama ya kwantar da gashin giransa tare da zira mata
idanu.

Ganin ta kifi tafin hannunta kan sanjeshi tana ɗan katse ruwa tare da cewa.

“Bari in gogema maka ruwan”.

Sai kuma ta ƙare maganar da yin murmushin da zuba idanunta kan sajen da kyau.

Ya lura batama sanin lokacin da take kai hannunta kan sajenshi, ganin yadda ya tsira mata idonsa ne
yasa tai saurin janye hannunta.

Shi kuwa Modibbo cikin wani irin fitinenne flenings ya ɗan sake matso ɗan kwalin Abayar ya sake
kaɗewa dake ta miƙe tsaye tana kusa dashi haka yasa ruwan ya jiƙata.
A tare suka saki ajiyar zuciya.

Ita kuwa gira ta kuma ɗaga mai tare da cewa

“Ya akayi?”.

Cikin fitinenniyar murya can ƙasan maƙoshinsa yace.

“Zaki kasheni“.

Murmushin mugunta tai tare da cewa.

“Ba wani mutuwa sai wuya dai, ci gaba, tunda ban mutuba in sha Allah kaima bazaka mutuba”.

Cikin narke fuska yace.

“Uhmmm bayan wuya kuwa zamsha daɗi ba“. Sai kuma ya sunkuya ya cigaba da kaɗewa har yayi na
takwas Kallonta yayi tare da faɗin.

“Wayyo Didi na hannuna ciwo Allah hannuna zogi yake min Minha”.

Dariya ta ƙyalƙyala kana tace.

“Allah ko goma baka yiba kuma sai ka ƙara”.

Juyawa yayi ya fuskanceta kafin yace.

“Kiyi haƙuri ni koma me kike so ki sani amma banda kaɗe ɗankwalin nan yana da wahala”.

Ware Idanunta tayi tace.

“Kaima haka kake yimin ba haka kake sani ba dan haka kaima sai kayi,yau kam sai kayi”.

Yana yarfe hannu yace..

“To ai nayi amma arage min kingani kin ninka min yayi yawa ki bari sai gobe In ƙarasa,in yaso yau inyi 25
gobe inyi 25”.

Ɗan shiru tayi kamar mai nazari sai kuma tace.

“Toh kayi 25 ɗin, kayi na yarda”.

Shafa sajensa yayi tare da cewa.

“Kuma nima ai ashirin nake saki”.

Ƙugu ta riƙe kana tace.


“Toh aini laifina kaɗan ne”.

Kwaikwayon maganar ta yayi yace.

“Toh nima ki bari idan na sake miki lefin sai ki sani”.

Da sauri tace.

“Zaka sake laifinma kenan?”.

Cikin sauƙe numfashi yace.

“Yess sosai ma kullumma kuwa,bai kema kullum sai kin maimaita laifi dan haka nima banyi alƙawari
bazan ƙaraba”.

Cikin kwaɓe fuska tace.

“Wlh komawa zanyi”.

Sai kuma ta kalleshi jin yana cewa.

“Kiyi haƙuri wasafa nake, wanda nayima na tuba ki yafemin”.

Cikin jin dadin cewa yau ita kesa Moddibo irin punishment ɗin da yake sata kuma yanayi harda ƙaramar
murya yake mata cikin jin dadi tace.

“Toh ka kaɗe, Ka kaɗe”.

Kai ya gyaɗa kana yasa ita kam dariya ta cigaba dayi yayin da yake jin wani irin farin cikin ganin
murmushin ta da kuma yanda idan yace ya gaji take dariya yasa duk kaɗewa ɗaya sai yace.

“Wayyo hannuna”.

Ita kuma sai ta fashe da dariya ahaka dai har akayi ashirin tana ƙyalƙyala dariya kamar ba ita ke kuka ba
yanayin yanda ruwan ke sauƙa a fuskarta sai ya zama fuskar ta wanku fes juyawa tayi kan abin alwala ta
wanke fuskarta sai ta juya ta kallesa lokacin daya kade na 25 yana ƙoƙarin maida bocket ɗin inda ya
dauka tare da sanya ɗankwalin acikin kana yace.

“Wayyo Hannu na ya mutuuuuu”.

Dariya ta sanya tare da faɗin.

“Nima haka nakeji duk randa aka sani kaɗe ɗankwalin nan na koma ko rubutu bana iyawa sai dai Haiydar
ya min kaima yau kaji yanda nake ji”.

Juyawa tayi ta nufi hanyar fita.

Da sauri ya tsaya gabanta yace.


“Toh Ni yanzu ko rigana ma bazan iya cirewa ba gashi duk ya jiƙe ki taimaka min ki cire min”.

Kafaɗa ta maƙale tace.

“Um-um nima ai idan ka sani da kaina nake cirewa kacire ka gani kaima idan zaka iya ka dai ji yanda nake
ji”.

Cikin langwaɓar da kai yace.

“Toh shikenan”.

Sai kuma ya tsugunna ya kamo ƙasa Jallabiyar ahankali ya zaro tare da faɗin.

“Wayyo hannuna”.

Cikin sauri Khausar da takai bakin kofa zata fita ta juya jin maganarsa dariya ta ƙyalƙyala dashi.

Yana cire Jallabiyar ya saƙale ahanga dake ban ɗakin.

Ita kuwa ahankali ta zubawa sajensa dake ƙyalli ido sai kuma ta maida idanunta kan gashin ƙirjinsa dake
kwance luf-luf.

Ahankali ya matsa kusa da ita.

Yayinda ita kam baki ɗaya idanunta na kan ƙirjinsa.

Yana isa jikinta ya janyota kana ya rungumeta aƙirjinsa yana saki wani sanyayyan ajiyar zuciya kanshi ya
cusa tsakanin wuyanta da kafaɗarta a hankali ya kai bakinsa saitin kunnenta yace.

*“Minha vidaa* Kin huce ko? Kinji daɗi kinsa mijinki wahala?”.

Kai ta Jinjina tace.

“Eh amma dai zaka ƙarasa saura guda 25”.

Cikin sauƙe numfashi ya shaƙi ƙamshin ta yace.

“In dai zakiyi dariya kaɗewan zai saki farin ciki ko guda dubu kike so zanyi miki *Minha vidaa*”.

Lumshe idanunta tayi.

Shikam ahankali ya riƙa cusa yatsun ƙafansa ƙarƙashin ƙafanta wanda yasa dole ta daura tafin ƙafan ta
akan rumfar ƙafansa yana jin haka ya manna kanta da ƙrjinsa ahankali ya fara ɗaga ƙafansa yana takawa
har suka fito yana tafiya da ita, ɗin yaja ƙofan ya rufe...
Suna shiga tsakiyar bedroom ɗin ya matsa da ita bakin gado akunnenta ya raɗa mata

“Kijifa kema kin jiƙe”.

Baki ta tura cikin kasala tace.

“Uhm toh ba kaine ka jiƙani”.

Yana lumshe idanunsa yace.

“Bake bane kika tsaya kina min dariyar mugunta ba”.

Dariya ta sanya Amma batace komai ba.

Akasalance yace.

“Yanzu ma dariyar kike min ko Minha”.

Cikin lumshe idanu tace.

“Eh mana kaima ba dariyar mugunta kake min ba”.

Yana fesar da numfashi yace.

“Ni na taɓa yi miki dariya ne?”.

Tana tura baki ta ɗan gyara tsayuwar ta akan ƙafarsa tace.

“Baka min dariyar, tunda kasan kayi min Mugunta ai kai kaji daɗi ma nayi maka dariya kai ban taɓa ganin
haƙorinka bama”.

Sanyayyan murmushi ya saki tare da cewa.

“Aikam naji daɗi kiyi min dariya nayi farin ciki, kuma ke yanzu ai ba haƙorina bama, ba gashi harda ƙirjina
da duka jikinama kike kalloba shekaran jiya har kusan tsinkemin lips nafa kikayi Minha vidaa da kyar na
tsira dasu”.

Cikin sauri ta runtse tare da cusa kanta a ƙijinsa.

Sai kuma tayi saurin buɗe idanunta jin ya zuge zip ɗin rigarta yayi ƙasa da ita.

Cikin tura baki tace.

“Sanyi fa”.

Muryansa ashaƙe yace.

“Badole kiji sanyi ba rigar ta jiƙe ki bari In cire miki shi kiji ɗumi”.

Kafaɗa ta maƙale tace.


“Um-um nikam ka barmin rigana”.

Numfashi ya fesar yace.

“Zai saki mura Ni kuma bana son abinda zai cutar *Minha* ”.

Shuru tayi jin yanda ya zuge rigar sannan yayi ƙasa da hannunta ya cire acikin rigar runtse idanunta tayi
lokacin da taji ya zare ɗaya hannun rigar ya zama ta gaba ne kaɗai ya rage baya yaja kaɗan rigar ya faɗi
runtse idanunta tayi.

Cikin sauri da bugawar zuciya ya rumtse Idanunsa jin tudu da taushin Breast ɗin sun sauka kan ƙirjinsa ga
sanyi daya ratsa fatar jikinsa wani sanyayyan ajiyar zuciya mai ƙarfi ya saki atake jikinsa ya fara sharking
Kamar anjona masa Shorking.

Cikin wani irin sauri tasa hannu ta zagaye ƙugunsa da ƙarfi yayin da take jin wani irin abu yana game
jikinta mai cike da shauƙi.

Shikam wani irin abune ya tsiga masa tun daga tafin ƙafarsa har ƙwaƙwalwar kansa yayin da idanunsa
suka sauya lips ɗin sa suka hau rawa hannunsa dake rawa ya ɗaura akan skintied ɗin ta ya fara murzuwa
yana ƙasa dashi.

Da sauri ta tura bakinta ta riƙe kana tace.

“Wayyo Allah ka bari bana so”.

Ahankali ya zauna bakin gado da ita tare da jingina bayansa da jikin gadon ya ɗan ware ƙafafunsa yasata
atsakiyar ƙafansa blanket ɗin ya ware ya rufe su cikin mayatacciyar murya yace.

“Ai kin san ba kyau fa tauye haƙƙin miji, haka zaisa ki faɗa cikin fushin Allah, kina son Allah yayi fushi
dake?”.

Cikin sanyi take girgiza mishi kai tare da lafewa a jikinai tana shaƙan.

Wani irin ƙamshin blanket da taushinsa da kuma sanyinsa ɗakin suka haɗu suka sauƙar mata da kasala
da mutuwar jiki ahankali ta manna kanta da jikinsa dai-dai kan maransa.

Cikin sauƙe numfashi yasa hannunsa duka biyu ya ɗago ta kana ya manna ƙirjinta da ƙirjinsa ya zamana
kanta na dai-dai ƙasan gemunsa yana shinshinan kanta ahankali ya fara shafa bayanta sai kuma ya sauƙe
hannunsa kan skintied ɗin ta yana ɗan tura hannunsa kan mazaunanta.

Da sauri ta runtse idanunta kana tasa hannunta ta rungumo bayansa ɗaya hannun kuma yana kan
sajensa tana shafawa ahankali ya matso da bakinsa kan kunnenta cikin wata kasalalliyar murya yace.
“ *Minha* ”.

Lumshe idanunta tayi zuwa yanzu ta fahimci wani sunane da yake kiranta dashi wanda batasan me
manufar saba may be wani abune daban sai wata zuciyar kuma tace waya sani ko ƴar Iska yake nufi
tunda yace min Fattanah Rigimammiya yanzu kuma yana ce mata *Minha vidaa* wata ƙil ƴar Iska yake
nufi dan yaga yayi abu da ni kuma Allah ya sani nidai ba ƴar Iska bace ta ƙare maganar zucin tana ƙoƙarin
tashi.

Da sauri ta koma ta faɗa jikinsa ganin lokacin data tashi yasa hannu ya tallafe ƙirjinta da hannunsa ɗaya
kana ya kamo hannunta ɗaya kuma ya ɗaura kan mararsa......

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

60

*Masu son Maganin infection set ɗin 10k half 5k sai kuma masu son maganin mata na gani na faɗa na
kece raini da baza ƙamshi na alfarma, ku marmatso kusa wannan account no in ne naku ta ciki zaku turo
kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP
NUMBER'N na 08069423567. akwai sabbin kaya masu zafi suna nan da zafinsu, ki turo kuɗinki a saki
cikin lissafi. Kayane na mata masu zafi sadidan daga Chadi suke na sahihan mahaɗa, akwaisu Garukan
daka, gumbunan, Tsumummuka, cida Ciccibi Abodi cida kaza ci da jan nama kwanon ƙasaitacciyar mace
butar sirri, furar mata, gumbar madara Gumbar kolli mai ƙyallin al'khairi gumbar uku al'khairi, gumbar da
ba'a baiwa mai kishiya, gumbar riɗi, garin maɗi garin melɗamhi garin ilanwaddihi garin mallaka, tsumin
tsirtai tsumin kinfi budurwa, tsumin riɗi, tsumin ta baje Sabaya, matsin maliƙi mai masifar matse mace
wanda bani da haufi kanshi 7k ne kacal matsin daɗi har maɗiga, mai ɗan kare kyau da sauƙo da ni'ima 5k
ne kacal Ni a kayana bani saida abin cushe-cushe duk yawan kayana matsi biyu ne kacal gareni shi
Maliƙin da kuma daɗi har maɗiga, wanda basu da illar komai sai aiki sha yanzu mgni yanzu in zaki saya
anfi son ki haɗa su biyun 12k ne. Kullacar sirri al'ajabu shu'umar Humra, da duk sauran kan ƙamshi.
Haɗin amarya budurwa ko bazawara haɗin mai jego ko uwar gida, akwaisu Available set ɗinmu hawa
hawane akwai manya akwai ƙananan, ƙanan daga 40k ne 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙarami haɗina
na karshe sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar shi 7k ne shine ƙarshen haɗina kenan akwai yajin maza
hajia ke kina lfy oga ba kuzari sayi yaji robar 5k ki mararraka mishi dege-dege nama kisa yajin a ciki
hmmmm ranar dai ki tabbatar kema a shirye kike da dan yadda zaici naman nan tofa ke ma... Manyan
set ɗin kuma daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k ke zaki faɗi haɗin nawa kikeso anyi miki kana kimin bayanin
yadda kikeso da matsalarki ni kuwa nasan abinda zan haɗa miki, ina araha kam amman ina hana bashi
zaki min bayani shin matsi kikeso ko Ni'ima ko sha'awa akwai matsalar infection ke mai jegoce ko
amarya budurwa ko bazawara uwargidace kin ɗan manya to ƙaramace ke ko kuma irin su Garkuwa ne
ƴan saffa-saffa ba taraba ba tsoffiba*😘

Sanyayyan numfashi ya saki tare da rungumeta kana yayi murmushi tare da cewa.

“ *Minha Vaada* Ki tashi mana”.

Baki ta tura cike da shagwaɓa tace.

“Ka cire min rigana kuma kana kallon ƙirjina”.

Yana matsa Caɓɓullenta yace.

“Ba nima bani da riga ba sai ki rama kawai ki kalli ƙirjina kema in kalli naki Kinga munyi one one”.

Ranƙofar da ita yayi ya kwantar da ita kana shima ya kwanta gefenta ahankali ya sunkuyo kanta ya ƙira
ta.

“ *Minha Vidaa*”.

Yanda ya kira sunan ne yasa ta runtse idanunta jin wani irin Feeling da ya ratsa tun daga maɗigar kanta
har babban yatsar ƙafanta sun kuyawa yayi ya kma lips ɗin ta ya mata wani irin kiss mai zafi wanda ya
nakasa duk wani kuzarinta wani irin kasala ne ya rufeta da wani irin yanayi take ji wanda tun randa ya
ruggumeta wurin taron nan take jin wannan yanayin mai wuyar fahimta,

Ji take tana son wani abu wanda bata fahimci me take jiba amma daga shekaran jiya zuwa yau tana ji
kamar akwai abinda take buƙata ajikinsa.

Lips inta dake manne da nashi ta buɗe a hankali tare da lalumar lip unshi na sama ta fara yi mishi wani
irin fitinenne abinda ya gigita nitsuwarsa, cikin rawan jiki ya risa lip inta na ƙasa ya Salam gaba ɗaya
jikinsu rawa ya saki da karkarwa cikin gigita ya janye lips inshi tare da kissing ɗinta tako ina. kissing ɗin
goshinta sai kuma ya ɗago ya kama hannunta ya riƙa Kissing ɗin lallenta ya juya yayi ta gaba kana ya juya
yayi ta baya sai kuma ya riƙe kan yatsun hannun yasa abakinsa yana tsotsa yayin da yake Binta da wani
irin kallo mai kashe jiki.

Lumshe idanunta tayi aranta tace

Kai Yah Moddibo ya cika shu'umin Namiji kallonsa kaɗai ya isa ya kashe maka jiki tsaban masifar kallon
da yake binta dashi da kuma Kiss ɗaya daya mata ya gigita mata tunani haka nan take jin wani abu na bin
ilahirin jikinta kallon daya mata kaɗai yasa taji kamar ta jiƙe.
Shikam Moddibo ahankali ya ɗaura hannunsa a saman caɓɓullenta ɗin ta yana ɗan shafa nmos ɗin ta.

Cikin sauri ta runtse idanunta tare da ƙame jikinta.

A hankali ya ɗago hannunta mai Lallen yasa abakinsa daga kan babban yatsanta ya fara tsotsa har ya
dawo kan ya tsarta manuniya ya dawo kusa da manuniyar ahaka sai da ya tsotse duka yatsun kafin ya
ranƙofa kansa yasa bakinsa kan ƙirjin ta ɗaya kana yasa ɗaya hannun ya riƙe.

Cikin fusgar numfashi ta runtse idanunta yayin da jikinta ya shiga rawa da tsuma kar-kar-kar.

Karkarwan da jikinta keyi yasa ya dakata da abinda yake yana kallon yanda jikinta ke kar-karwa sosai ya
zuba mata ido ganin sosai jikinta ke tsuma.

Ranƙofowa kanta yayi da sauri ta rungumesa kamar zata mai dashi cikin jikinta cikin wani shu'umin
murya yasa bakinsa daidai kunnenta yace.

“ *Minha* ya dai me kike so?”.

Cikin wata fitinenniyar murya me cike da kasala wanda ita kanta batasan tana dashi ba ta motsa
laɓɓanta dake rawa tace.

“I don't know”.

Ranƙofowa kanta ya sake yi tare dasa hannu ya shafo ƙasan maranta.

Atake kuma jikinta ya fara rawa kafin wani lokaci ya tsananta fiye da farko cikin wani sexy voice yace.

“Ya dai Minha vidaa?”.

Ahankali ta buɗe Idanunta da suka canza launi su ba ja sukayi ba amma sun koma kalan bacci alamun
tsananin feeling yana damunta.

Ajiyar zuciya ya sauƙe aƙasan zuciyarsa yace Alhamdulillah ta kasance irin macen dana ke buƙata
tunanina akanta ya zama gaskiya ta kasance irin matar da nake muradi.

Khausar kuwa damatsan hannunsa ta riƙe da karfi tana sakin ajiyar zuciya.

Sanyayyar iskan bakinsa ya hura mata bisa fuskar ta kana yace.

“ *Minha* ya dai ?”.

Cikin sakin Ajiyar zuciya ta fesar da numfashi tare da cewa.

“Yah Mu'allim ina jin tsoro”.

Yana lasan saman lips ɗin ta yace.


“Tsoron me kike ji?”.

Cikin alamun tsoro take girgiza masa kai kana tace.

“Nikam tsoro nake ji kabarni”.

Ta faɗa tana tuno azaba da zafin da taji a haduwar su ta farko.

Kai ya girgiza cikin yanda jikinsa ya gana mutuwa yace.

“Zan kaɗe ɗan kwali fa ko sau 100 kikeso”.

Cikin rauni da kasala tace.

“A'a ina tsoro”.

Gefen fuskanta ya shafa tare da faɗin.

“Kona miki ba zakiji zafi ba kinji ko *Minha Vidaa* ba zakiji zafi ba”.

Numfashi ta fesar tare da cewa.

“Ni dai ina tsoro”.

Sai kuma tayi saurin runtse idanunta jin yanda yakai hannunsa kan maranta jin yana mata wani irin
abinda yasa bakinta mutuwa wanda baza ta taɓa iya mishi gardama ko kuma wani abu ba sai dai
tsananin tsoron da yasa jikinta tsuma yayinda tuni tayi zuru-zuru da idanunta kai kace zasu faɗo ƙasa..

Moddibo kuwa cikin wani irin salo mai rikitarwa yake mata wasu irin abubuwa masu wuyar fahimta
abubuwan da babu wata lafiyyar mace mai jini ajiki da zata iya juresu batare data mayar masa da
martani ba.

Cikin haka ta ɗago kanta ta kama Lips ɗin sa ta manna da nata ta fara yi masa wani irin kiss da ita kanta
batasan ta iya ba lokaci ɗaya ta gigitasa ta gigita masa tunani.

Jin kiss ɗinta ɗaya yakeji yaji kamar ta tsotse ruwan dake jikinsa ne baki ɗaya.

Cikin rawan jiki da tsananin buƙata suka fara romance ɗin juya.

Lokaci ɗaya ta saki ƙara da ƙarfi kana ta ɗago ta rungumesa da ƙarfi lokacin data ji yana ratsa jikinta jin
zafi baki ɗaya sai jikinta ya fara rawa musamman cinyoyinta sassayan kuka ta saki jin zafin yana nan
yadda ta zata, kasan cewar su hutun kwana ɗaya wurin ya samu, danma Allah yayi jikinta da
wadacecciyar ni'ima da kuma taimakon magungunan da tai ta shiga, shi yasa taji zafin bai kai yanda take
tunani ba.

Amman duk da haka ta gaza hana kanta kuka.

Ajiyar zuciya ta fara saukewa jin yanda yake sarrafa ta yayin da take jin hawaye yana kwaranya daga
idanunta sai kuma ta fara shesh-sheƙan kuka tana ɗan bubbuga ƙrjinsa tana cewa.

“Yah Mu'allim zafi! Zafi!!zaaafeeehh”.

Ta ƙarashe mgnar da sassayan sautin kuka.

Moddibo kuwa zuwa yanzu bazai iya saurara mata ba saboda baya jinta baya iya fahimtar duniyar ma
shiyasa ya kasa sararawa yabita ahankali wanda hakan yasa ta sake tsananta kukanta duk da cewa be kai
zafin da taji a farko ba.

Cikin kukan da take yi take jiyo Muryasa a sarƙafe yake wasu zantuka masu kurman baƙi.

“J kayi min komai a duniya ka zama sanadin mallakar wannan ni'ima da jin daɗin duniya, J zan rayu cikin
yi maka addu'ar Allah ya jiƙanka ya baka jin dadi makwancinka kamar yadda ka sama min wannan jin
daɗin makwancina, j kayi sanadin samamin cikekken jin daɗin duniya ka cika amini na gsky J Allah yayi
ma gafara. Wayyyyyoohhhh J..... Wow Minha vidaa, thanks Minha vidaa Jazakillahu khairan wa yatta
ƙinallahu jami'an Yah Mu'allima”.

Sai kuma tayi saurin buɗe idanunta sabida jin sauƙan hawayeshi bisa fuskar ta yana faɗin.

“Minha Vidaa Allah ya jiƙan iyayenki yasa ki kasance mu al'wadussaliha Mommy tamin komai a duniya
data haifa minke, Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!”.

A ƙalla ya kai kusan minti arba'in kafin ahankali ya jawota jikinsa ya rungumeta da karfi tare daci gaba da
yiwa J da iyayenta addu'ar neman rahamar Allah.

Cikin wata sanyayyar murya mai cike da kwanciyar hankali Salama nutsuwa aminci yace.

“ *Minha Vidaa* Allah ya miki albarka Allah yasa ki gama da duniya Lafiya Allah ya faranta miki fiye da
yanda kika faranta min ya Ubangji yajiƙan J da Abbanmu ya musu Rahma Allah yasa sun huta”.

Ita kam kuka kawai take sabida radaɗin da takeji cikin shesh-sheƙan kuka tace.

“Ba gashi ba yanzu ma ka sake min Mugunta Ni wallahi tafiya zanyi bazan zauna ba zan koma wurin
Mommyna kuma sau 360 zaka kaɗe ɗan kwali”.

Ranƙofowa kanta yayi cikin yanayin farin cikin da yake ji yace.


“ *Minha Vidaa* ba mugunta bane abin daɗi ne fa *Minha* ahaka zaki saba idan na barki bazaki saba ba
shiyasa zan riƙe wuta, ɗan kwali kuma na yarda Amman duk kaɗewa ɗaya yi ɗaya ko“.

Cikin muryan kuka tace.

“Kana tayi min Mugunta nace maka kuma yana min zafi amma ba ka bari kullum haka zaka yita azabtar
dani Ni dai zan koma”.

Miƙewa ya ɗan yi ya zauna kana ya janyota jikinsa ya rungumeta cikin wata tattausan murya yace.

“ *Minha* kin sani kinyi karatu aikin karanci Ahallari bakisan me zaman Aure bane!”.

Tana jan ajiyan zuciya tace.

“Na sani mana”.

Cikina sanyi ya shafi gefen fuskarta yace.

“Toh kiyi ki rage raki shin kin mata cewa wannan shine Auren?”.

Cikin tura baki tace.

“Toh ba kaine ka kaƙi min ahankali ba”.

Idanunsa ya lumshe tare da buɗesu akanta cikin sanyi da wani irin yanayi mai wuyar fassarawa da yake ji
agame da ita yace.

“Daga yanzu baza ki sake jin zafi ba yanzu muje muyi wanka”.

Muskutawa tayi ajikinsa tare da faɗin.

“Nikam na gaji bazan iya ba gaba ɗaya jikina rawa yake”.

Hancinta ya ɗan kama da yatsunsa biyu ya ɗan ja tare da faɗin.

“Raguwa kawai daga first round ba'ayi na biyu ba kike cewa kin gaji”.

Kukan gajiya tasa kana tace.

“Wani second round kuma?”.

Da murmushi afuskarsa ya kuma lakace mata hanci kana yace.

“Wuce dai muje kiyi wanka kinsan ba kyau zama da janaba ko?”.

Kai ta gyaɗa kana ya ɗauketa suka shiga toilet itakam tunda ya ɗauke ta ta rufe ido kasancewar babu
komai ajikinsu cikin raɗa yace.
“Muyi wanka”.

Kafaɗa ta maƙale tace.

“Ka fita dai zanyi wanka”.

“Mu dai yi tare ina so inga ko kin iya”.

Cikin tura baki tace

“Yah Mu'allim ai kasan na iya tun dai kam kun karantar damu”.

Ɗan murmushi yayi tare da faɗin.

“Ohh haka fa na manta ashe Malama ce toh Bismillah Amma dai ki fara”.

Kai ta gyaɗa kana ta shiga cikin Bathtub ɗin shikam tsayawa yayi daga gefe ya buɗe ruwan ya fara wanke
cinyoyinsa da suka wadatu da ni'imar jikinta, aransa kuma yana jinjina ni'imar yarinyar yarinyace ƙarama
amma tana da wadatacciyar ni'ima mai gamsarwa.

A haka sukayi wanka suna fitowa daga wanka ya jawota jikinsa suka kwanta kan gadon ta gefe ɗaya
suna kwanciya ya rungumeta ahaka bacci mai masifar daɗi ya ɗauke su...

Misalin ƙarfe ƙarfe 3:00pm dai-dai Jirginsu Hajja Nana ya sauƙa a Yola suna sauƙa a Adamawa Yola aka
turo manya manyan motoci na Alfarma,girma,isa, kamala, mutuntaka daga Fadar Masarautar Joɗa aka
zo aka ɗauke su bisa jagoranci Jabeer bin Jabeer da Umarnin sheikh Jabeer aka zo aka ɗauke su suna isa
aka kaisu masauƙi me kyau kana aka kawo musu abinci na alfarma bayan sun ci abinci sun Aish ɗin Yah
Sheykh tazo tayi musu godiya ita da Sheykh ɗinta.

Bayan sun gama komai aka kawo msu motoci na Alfarma daga Adamawa wanda direct zai kaisu Taraba
ƙarfe huɗu daidai suka nufi Taraba.

Karfe goma dai-dai suka isa Membila kai tsaye gidansu Lamiɗo suka nufa.

Wanda a dai-dai lokacin kuma tuni Momy ta gama shirya musu abinci da komai zasu buƙata duk ban
ɗakin gidan ta saka musu ruwan zafi.

Ƙarfe 10 dai-dai Motocinsu suka shiga coumpund cike da matsanancin farin ciki Momy tace.

“Sannun ku da zuwa,Marabanku”.
Cikin farin ciki da gajiyar tafiya suke amsawa kana suka nufi Side ɗin Momy dukan su yayin da Hajiya
Bunayya ta wuce Side ɗin ta cikin ƙunan zuciya da matsanancin hassada da ƙyashi.

Lamido kuwa da kansa ya kai su Abualeey da Galadima da Waziri da Baban Zakariyya masauƙi na
musamman a cikin gidan nasa wanda tuni an gyara komai.

Aunty Ruƙayya,Ummi Hajja Nana,kao tsaye Momy tayi musu iso zuwa ɗakinta Yayin da Aunty Hajara,
Asma'u, Asiya, Dija aɗakin Khausar suka nufa.

Cike da farin ciki Momy ta kallesu tare da cewa.

“Sannun ku kunsha hanya”.

Sai kuma ta fita ta kawo musu abin motsa baki kallon Hajja Nana tayi tare da cewa.

“Hajja Nana Bismillah ko zaku shiga kuyi wanka akwai ruwan zafi ku shish-shiga kuyi wanka kafin na
ƙarasa kawo muku abinci kun dai yi sallah kam ko Ummin Jameel?”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh munyi sallah a hanya”.

Ummi kuwa bayan sunyi wanka Momy ta kawo wa Hajja Nana, Ummi,Aunty Ruƙayya, Hajja Umma
bedroom ɗin ta.

A can ɗakin Khausar kuwa Aunty, Hajara, Asiya, Dija, Asma'u abinci kala-kala Momy takai musu tuwo
miyan yakuwa da yaji tantaƙwshi, ga kunun nono daya damu ga kuma tea Mai zafi da yaji kayan ƙamshi
sannan

Ga indomie da yaji gesha da soyayyen ƙwai a cewar ta tasan su Asma'u shi zasufi so, sai Jollof ɗin
spaghetti Mai zafi wanda yaji busheshshen kifi da nama...

*Morocco*

Akuma dai-dai lokacin Khausar ce zaune afalon Didi, Didi na gefenta yayin da Moddibo ke zaune daga
can gefe sai kuma Rahama data zo ta mikawa Khausar wani kula bisa ga duk kan alamu nama ne agashe
sai kuma ta kalli Didi tare da cewa.
“Didi gashi na gama amma naji kamar ya ɗan yi yaji”.

Cikin sauri Didi ta kalleta tace.

“Yayi yaji kuma? bayan kinsan Yah Aleey ku baya son yaji kuma sai da na gargaɗeki Rahama”.

Cikin sanyi Rahama tace.

“Amma baiyi yaji sosai ba Didi nasa vegetables aciki ya kashe zafin yajin be fito sosai ba”

Kai ta gyaɗa cikin sauƙe numfashi tace.

“Toh da sauƙi”.

Khausar kam ahankali tace.

“Nikam ma na ƙoshi”.

Sai kuma ta ɗan gyara alamar zata kwanta awajen.

Kallonta Didi tayi tare da cewa.

“A'a Khausar dare nayi tashi kije kisa masa Abinci naga tunda kuka zo da yamma kuka ci abinci baku sake
zuwa ba”.

Ɗan juyawa Khausar tayi ta kalli Moddibo

daya zuba mata ido kana tace.

“In sa maka ne?”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Muje kisa min”.

Baki ta tura kana cikin kasa da murya tace.

“Mu tafi kuma?,Ni anan zan kwana zan kwana tare da Rahama”.

Dai dai lokacin kuma Didi ta nufi bedroom ɗin ta jin alamun ana kiranta awaya kuma Yau itace da girki za
tayi wanka ta tafi turakan mijinta takai masa abinci ganin Didi ta shiga ɗaki yasa ya jawo hannunta yace.

“Mu tafi”.

Cikin tura baki tace.

“Ni wallahi anan zan kwana da Rahama”.


Wani kallo ya mata sai kuma ya tsuke fuska yace.

“Ki kwana da Rahama kuma? Rahman ce mijinki?”.

Baki ta tura amma batace komai ba yatsunsa biyu yasa ya kama Lips ɗin ta tare da cewa.

“Mu tafi”.

Rahama kam cikin sauri ta maida idanunta kan waya.

Da hannun yayi mata alamun su tafi ganin yadda ya tsuke fuska yasa tayi gaba kana ya bita a baya.

Suna isa ta nufi falonta,

cikin sauri yabi bayanta cikin wata kasalalliyar murya yace.

“Yau anan kike son mu kwana kenan?”.

Fuska ta shagwaɓe tare da tura bakinta gaba tace.

“A'a ni ka tafi ɗakin ka Ni zan kwana anan”.

Yana ƙarasa shiga ciki yace.

“Shegen tsoro kamar farar kura dare-dare zaki tashi kina lalubemin jiki da Ihu kina sawa mutanen gida
suyi tunanin kamar na miki wani abun ne”.

Cikin kasala tayi miƙa kana tace.

“To ai kana yi min wani abin ma”.

Matsawa daf da ita yayi yace.

“Toh yanzu dai kawo mu gani danni yunwa nakeji gaba ɗaya kin ƙwaƙule min ciki”.

Asangarce ta kallesa tace.

“Kamar ya na ƙwaƙule maka ciki?”.

Shafa cikinsa yayi yace.

“kin ƙwaƙule min ciki mana baki san cewa duk tattalin lafiya da kuzarin namiji na tsawo kwana uku a
dare ɗaya mace ke kwaƙuleshi ba”.

Juyawa tayi ta nufi kichen taɓa tura baki, plate ta ɗauko kan ta dawo.

Gefen ta zauna tare da zuba gashesh-shen naman mai ɗan ruwa da romo-romo yaji albasa,da kayan
haɗi.

Ganin ta ajiye masa agabansa yace.


“Kici mana”.

Kai ta girgiza tare da faɗin.

“Na ƙoshi bana jin yunwa”.

Cikin sauƙe numfashi yace.

“Na lura fa tun safe ba kici abincin kirki ba tun safe kuka kika tayi da rana ma babu abinda kika ci da
yamma na da muka sauka ina kallo ba wani abin kirki da kika ci sannan yanzu ma Kice baza kici komai
ba”.

Kusa da ita ya matsa ya ɗauki tsokan naman tare kai mata b....

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 08069423567
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

61

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar
gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku
nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta
ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki
zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin
mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi
mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai
masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar
goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai
tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai
maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze
gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai
Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma
Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato
khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da
sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin
kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja
anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma
sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata
kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar
kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 08069423567
muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki
shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,


😘

Abun ya zomata abazata da kuma Mamaki sosai take mamakin wasu abubuwan da yake mata ahankali
ta ɗago Manyan Idanunta masu haske ta kallesa ganin yadda ya tsare fuska babu alamar wasa atare
dashi yasa ta kawar da kanta.

Cikin tsare fuska yace “buɗe bakin ki”.

Jin yanda yayi magana da kuma yanda fuskarsa ke tsuke yasa ta buɗe bakinta yasa mata ahankali take
tauna tana juya tsokan a bakinta, ido ya zuba mata har ta cinye wani ya ɗauka ya sake samata ta kuma
amsa tana jujjuyashi kusan one minute kafin ta haɗiye.

Ba tare da ya kalleta ba ya kuma ɗauko wani ya muƙa mata, a hankali ta riƙe hannunsa tace.

“To kaima kaci mana”.

Yana ƙoƙarin cire hannunsa dake cikinta yace.

“Me ruwanki cikin ki ko cikina?

aina fiki sanin wahalar cikina ke kici mana”.

Langwaɓar da kai tayi tare da cewa.

“Ni na ƙoshi bana jin yunwa ya isheni haka”.

Fuska ya kuma tsukewa tare da faɗin.

“Sai kinci fa”.

Ya faɗa tare da kai mata bakinta aransa kuwa mamaki yake yana da tabbaci ita ko ciwo take tana cin
abinci amma kuma yau tunda gari ya waye bataci komai ba ya fahimci hakan baya rasa dalili da tafiyarsu
Ummi data sa aranta ne.
Ɗagowa yayi ya kalleta kana yace.

“Tunda gari ya waye bakici komai ba sai kuka da kika tayi sannan yanzu ma Still Kice min zaki kwanta da
yunwa ya za'a yi na yarda? ki kwanta da yunwa ai yunwar sai ta cutar dake nima ta cutar dani”.

Fuska a narke ta kallesa sai kuma ta langwaɓar da kai tana cewa.

“To ai bana jin yunwa aƙoshe nake”.

Zamansa ya gyara da faɗin.

“Sai kinci fa ki buɗe baki”.

Bai jira cewartaba ya ɗauko wani tsoka mai laushi yasa mata abaki lumshe idanunta tayi kafin ta fara
tauna ahankali ahaka yaci gaba da bata taci ɗan dai-dai bada yawa ba.

Wata tsokan ya sake ɗauka yakai mata baki tayi saurin girgiza masa kai tana rau-rau da idanu tace.

“Allah banaso Wallahi na ƙoshi”.

Cikin tsira mata a ya girgiza kai tare da cewa.

“Baki ƙoshi ba”.

Idanunta dake lumshe ta ware tace.

“Allah nikam na ƙoshi cikina ya cika”.

Numfashi ya fesar tare da faɗin.

“Inga cikin?”.

Baki ta tura tare da faɗin.

“To ai ya ƙoshi sai ka gani ne?”.

Kai ya jinjina kana yace.

“Um idan kina so in yarda cikin ya ƙoshi tona ga cikin”.

Ya ƙare maganar yana kallon dogon rigar Abayar dake jikinta wanda daga ƙasa abuɗe yake daga sama
kuma atsuke cikin tura baki tace.

“Ba gashi ba ka gani”.

Tayi maganar batare data ɗaga rigar ba.


Idanunsa ya lumshe kana ya buɗe akanta yace.

“Ɗaga rigar na gani”.

Ware ido tayi sai kuma ta sake langwaɓar da kai tace.

“In ɗaga riga kuma?”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa

“Eh idan kin tabbatar ɗaga in gani”.

Ahankali ta ɗan matsa kana ta fara tattare rigan idanunta akansa tace.

“Toh ba gashi ba”.

Lumsassun Idanunsa ya zubawa santala-santalan cinyoyinta dake cikin wani farin skintied kafin ahankali
ya maida idanunsa kan cikinta dake lafe tabbas bata ƙoshi ba kamar yanda yake zato amma ya rasa
dalilin da yasa batason cin abinci.

Ahankali ya matsa gefenta kana ya daura hannunsa na dama kan cikinta ya shafa a hankali ya cusa ya
tsansa cikin ramin cibiyar.

Cikin sauƙe numfashi ta lumshe idanunta tare da sakin ajiyar zuciya cikin wata sanyayyar murya ta motsa
laɓɓanta tare da cewa.

“Kaji na ƙoshi ko?”.

Sanyayyan ajiyar zuciya ya sauke tare da girgiza mata kai kana yace.

“Um-um baki ƙoshi ba, Baki ƙoshi bafa, Baki ƙoshi ba, Baki ƙoshi bafa³”.

Kallonsa tayi jin yanda yake ta maimaita maganar ba ƙaƙƙautawa numfashi ta fesar tare da faɗin.

“Toh ai naci kai ne fa bakaci komai ba”.

Kai ya girgiza yana yawo da hannunsa ashafeffen cikinta yace.

”Ni a ƙoshi nake, kin gani ɗazu da yamma naci abinci”.

Tana ɗan sakin ajiyar zuciya akai-akai tace.

“Kuma kace na ƙwaƙule maka ciki?”.

Kai ya jinjina yana ɗan lasan lips ɗin sa yace.


“Eh kin ƙwaƙule min ciki mana baki san cewa duk tattalin lafiya da cin abinci mai kyau da gina jiki da na
miji yayi na kwana bakwa guda a dare ɗaya matarsa take zuƙeshi ba.

yanzu ma gudun Nasan zaki ƙara ƙwaƙulemin cikine yasa zan sake ci”.

Rau-rau tayi da idanu kana tace.

“Wallahi ba ruwana da kai”.

Bai ce komai ba ya sake ɗauko naman yakai mata baki aƙalla ya ƙara mata kusan tsoka biyar kafin yace.

“Bari na haɗa miki tea kisha”.

Kasancwar Flaks ɗin tea na gefe.

Kofin ya jawo da Gongomin madara dana milo cikin sauri tace.

“Ayya kaɗan zaka samun kuma kar kasa min madara ka bani Empty zansha ”.

Kai ya gyaɗa kana ya zuba mata ya mika mata ya ɗan ci naman.

Bayan ya gama ya jawota jikinsa ya rungumeta ajikinsa ita ma lafewa tayi ajikinsa yayin da wani irin daɗi
da nutsuwa da Salama dake bin ko wani magudanan jinin jikinta muddin zata kasance atare dashi haka
takeji.

Irin dai nitsuwar nan da duk macen duniya takeji muddin tana manne da mijinta nitsuwace da nasani
kun sani yana samawa ko wacce mace aminci da yaƙini ayayinda take manne da jikin mijinta.

Shiru sukayi ajikin juna ko wannensu yana shaƙan numfashi ɗan uwansa shi kansa bai san wani irin
yanayi yake ciki ba idan yana tare da ita.

Cikin shirun ne ta tsinkayo muryansa na cewa.

“Allah yayi wa J albarka Allah ya masa Rahma Allah ya gafarta masa”.

Cikin sanyi da nutsuwa tace.

“Ameen ya Allah”.

Sunkuyo kanta yayi tare da cewa.

“Kina masa addu'a?”

Kai ta gyaɗa kana tace.


“Eh ina masa”.

Kai ya jinjina tare da hura mata iskar bakinsa akan idanunta wanda yasa ta ƙyaf-ƙyafta ido sai kuma yace.

“Toh kina masa godiya?”.

Ɗagowa tayi ta kallesa tare da faɗin.

“Godiyan me?”.

Murmushi yayi tare da ɗage mata hira ɗaya yace.

“Godiyar baki ni da yayi mana”.

Ware idanunta tayi sai kuma tayi murmushi tace.

“Baka ni kai ko kuma dai bani kai?”.

Shima murmushin yayi jin yanda tayi maganar kamar mai raɗa da alamu in tana jikinshi haka muryarta
ke narkewa.

Cikin tsareta da ido yace.

“Bakini dai?,ke ai kinyi Sa'a da J ya baki babban Amininsa mafi tsada”.

Da sauri tace

“Hmmm wlh kai dai kayi Sa'a daka sameni”.

Yana murmushi yace.

“Allah ko?”.

Kai ta ta gyaɗa tace.

“Eh mana”.

Murmushi yayi tare da lakace mata hanci yace.

“Baki, Baki, Bakinki baya mutuwa toh na yarda”.

Cinno baki gaba tayi kafin tace wani abu ya tallafo kanta ya haɗe lips ɗin su ahankali ya kamo lips ɗinta
na ƙasa ya fara tsotsa .

Sishhhhhhh taja yaji tana sakin ajiyar zuciya.

Sake Lips ɗin yayi tare da kallon yanda idanunta suka koma cikin cikin raɗa yace.

“Fitinanniya”.
Sai kuma yaja hannunta tare da cewa.

“Tashi muje mu kwanta”.

Kai ta girgiza tare da faɗin.

“Bana jin bacci”.

Ahankali yace.

“Nima bana jin bacci ai kwanciya nace muyi ba bacci nace zamuyi ba”.

Tana ƙoƙarin miƙewa ta furta.

“Toh”.

Hannunta ya riƙe acikin nasa suka nufi bedroom ɗin ta suna shiga ya kalleta tare da faɗin.

“Jeki yi Alwala”.

Kai ta gyaɗa kana ta shiga Bathroom tayi alwalan tana fitowa shima yashiga yayi yana fitowa ya sameta
zaune gaban dreesing mirrow.

Yana yarfe ruwan dake sajensa yace.

“Muje mu kwanta mana”.

Ya ƙare maganar yana fesa musu turare a jikinsu.

Kallonsa tayi sai kuma tace..

“Toh ai banajin bacci”.

Yana gyara tsayuwar sa yace.

“Na sani bakya jin bacci kizo nace”.

Ahankali ta miƙe lallausan tafin hannunsa yasa ya riƙo nata kana ya jawo ta suka zo bisa gado, kana ya
kwantar da ita agefensa.

Tana ɗan tura baki gaba tace.

“Yah Mu'allim wai ni kam lefin me Zip ɗina ya maka?”.

Cikin ɗan tsira mata ido ta cikin hasken Deam light ɗin yace.
“Zip ɗin kine zakice lefin me yamin?”.

Idanunta ta lumshe tare da gyada masa kai ta furta.

“Um”.

Cikin sauƙe numfashi yace.

“Zip ɗinki yamin shamaƙi yashiga hakkina, ya shiga rayuwata”.

Langwaɓar da kai tayi tace.

“Kamar ya?”.

Muryansa akasalance ya fesar da numfashi tare da cewa.

“Shiya min katanga da mallakina”.

Numfashi ta fesar tare da faɗin.

“Nikam sanyi nake ji dan Allah kar ka cire min rigata”.

Wuyanta ya shafa kana yace.

“Kada ki damu ba zakiji sanyi ba zan rufeki”.

Langwaɓar da kai tayi tare da cewa.

“Da me zaka rufeni”.

Bakinsa ya kai saitin kunnenta yace.

“Zakiji ɗumin jikina”.

Khausar kam duk wani abu da yake mata sannan yake faɗa mamaki take yayin da duk wani sautin
muryarsa da zai fita yake haifar mata da kasala da tashin tsikar jikinta sosai take ji mmkin lakuransa...

Ahaka ya zare mata rigar jikinta ya haɗe lips ɗinsu.

Haka dai awannan daren ma Moddibo bai bar Khausar ta sarara ba ya riƙe mata wutane sosai saboda so
yake ya saba mata ya kuma tabbatar da ita cikakkiyar mace ta yanda zata saba dashi ta daina gudun
kasancewa dashi ta fara mararin tarayarsu.

Sai da ya ɗauki kimanin minti arba'in kafin ya ɗan ɗago ya koma gefenta ya kwanta yana maida numfashi
sai kuma ya rungumeta tsam ajikinsa yana sauƙe numfashi so yake ya ɗan hutu kamar minti biyu zuwa
uku sai suyi wanka kafin su kwanta ahaka kuma bacci me nauyi ya ɗauke su...
*Gembila*

Acan gidan Lamiɗo kuwa Hajja Nana da Hajja Umma ce kwance akan gadon Momy yayin da Aunty Aunty
Ruƙayya da Ummi ke kwance tsakiyar bedroom kan katifa data shimfiɗa musu Momy dake zaune gefen
katifa ta kalli Ummi tare da cewa.

“Ummin Jameel ku kwanta kun ɗebo gajiyar hanya”.

Murmushi Ummi tayi kana tace.

“Ai Momyn Khausar bazan iya bacci ba yau sai na baki labari”.

Murmushi Momy tayi tana gyara zamanta tace.

“Allah ko?”.

Ɗagowa Aunty Ruƙayya tayi tare da faɗin.

“Ai dai kam Momyn Khausar sai mun baki labari ,Muna tafe da labarai kala-kala munga alfarma, Isa,
Wadata, Kawaici, kara, Mutuntaka, Munga iyayen Moddibo, Mahaifinsa, Mahaifiyar sa,Yayunsa,
Ƙannensa, Kakarsa, munaga baki ɗaya Family sa masu mutunci kamala da kawaici”.

Zama Momy ta gyara tare da cewa.

“Abin al'ajabi yaron nan suka zo suka rayu da Innayi anan babu wanda ya taɓa tunanin yana da dangi”.

Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.

“Kin ganni nan Momyn Khausar koni kaina ban taɓa sani ba Jameel dai kusan rasuwarsa ya fara cemin ya
samu labarin inda ƴan Uwan Moddibo suke amma be faɗa min ba ni kaina na shiga mamaki”.

Juyawa Momy tayi tare da kallon Ummi tace.

“Allah Ubangji ya rufa asiri Allah ya basu zaman lafiya, amma yau hankalina gaba ɗaya ya tashi yanda naji
Khausar nata kuka, kawai daurewa nayi na rufeta da faɗa saboda Kukanta yana son sakani kuka”.

Sai kuma ta sauƙe Numfashi fuskarta ɗauke da damuwa ta cigaba da cewa.

“Bare kuma acan bata da kowa sannan Mijinta ba sonta yake ba ita ta daurawa kanta da kanta Ni abinda
yake tayar min da hankali kenan Moddibo bawai son Khausar yake ba”.

Cikin sauri Hajja Nana da bacci ya fara fusgarta ta miƙe zaune idanunta akan Momy tace.

“Waya ce miki baya sonta in faɗa miki Aysha kiyi shuru da bakinki babu Munafukai aduniya sama da
wannan yarinyar da yaron bata nuna mana saboda Jameelu zata Auresa ba to ƙarya take suna soyayya
wannan abin nasu ƙaryane ace babu soyayya ke kinga abinda suke wlh ita kanta Khausar tana matuƙar
sonshi so na gaskema kuwa bare shi uban gayya kam ai ko tattabara sai haka”.
Cikin mamakin maganarta Ummu ta zuba mata idanu sai kuma ta juya ta kalli Aunty Ruƙayya da take
cewa.

“Kai gaskiya Momyn Khausar al'amarin Moddibo ya sunce min ƙwaƙwalwata da tunani idan kinga abinda
Moddibo ke yiwa Khausar wallahi ³ gaba ɗaya sai kin faɗa Duniyar da bakiyi zato da tunani ba”.

Cikin mamakin kalamanta Momy ta gyara zama tana sauraren ta Aunty Ruƙayya kuwa cikin farin cikin
yanda Moddibo ya karɓi Khausar hannu bibbiyu ta cigaba da faɗin.

“Abinda Moddibo ke yiwa Khausar ya wuce akirasa da so sai dai Ƙauna kai baza ma kasan da me zaka
Misalta shiba saboda ko kallon Khausar yake yi kallone da yake cike da tsantsar soyayya,kulawa da
tausayi Momyn Khausar ki cire tunanin da kike yi ba cewa wai Moddibo baya son Khausar ni inaga akwai
abinda M Jameel ya sani shiyasa yace a haɗa Auren khausar da Moddibo”.

Ummi ce ta gyara zama tare da cewa.

“Nima abinda nayi tunani kenan ina ga tabbas Jameel yaga Moddibo nasan Khausar ne Shiyasa ya haɗa
abin domin gaskiya abinda Aliyu ke yiwa Khausar soyayya ce mai zafi da zurfi atare dashi”.

Baki sake Momy ke kallonta cikin mamaki tace.

“Moddibon yake son Khausar?”.

Cikin tabbatar Ummi ta gyaɗa mata kai tace.

“Babu shakka babu tantama babu Haufi acikin wannan al'amarin wallahi akwai soyayya mai ƙarfi
tsakaninsa da yarinyar nan ita kanta bata sani ba shi kuma bai fito fili ya faɗa mata ba al'amarin su
soyayyace mai ƙarfi”.

Ajiyar zuciya Momy ta sauƙe kana tace.

“Ikon Allah amma abinda Mamaki”.

Hajja Umma dake kwance tayi murmushi tare da faɗin.

“A akwai soyayya kam dan lamarinsu yafi ƙarfin ace wanzar da wasiyyane kawai bama so bane soyayya
ce ta gefe duka biyu”.

Cikin sauri Ummi tace.

“To ai shi Aliyu idan yasan wasiyyar ma daga baya ya sani don har aka ɗaura Auren nan har muka je
baisan da batun wasiyyar ba”.

Kai Aunty Ruƙayya ta jinjina tare da faɗin.

“Kinga kuwa ran farko da yaga Khausar irin rungumar daya mata?”.

Murmushi Momy tayi tare da sunkuyar da kai tana jin wani irin sanyi nutsuwa da Salama.
Aunty Ruƙayya Kuwa ahankali tace.

“Wallahi rungumar daya mata sai da gaba ɗaya falon ya ɗauki tafi zaki rantse da Allah uwace da ɗan ta
ya ɓace tsawon shekaru ta gane sa haka ta rungumeta kamar ma ya manta da akwai mutane acikin Falon
itama Khausar ni har taban kunya yadda ta lafe a jikinshi kai kace furanninesu”.

Fuska ɗauke da farin ciki Momy tace.

“Moddibon?”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.

“Tabbas kuwa Moddibon shi ɗin dai”.

Hajja Nana dake jinsu tace.

“Tabbas Moddibon kuwa bakisan fitsaran yaron bane ya tsefe idanunsa yo wannan ƙasurgumin tuzurun
ai sai abinda Allah yayi”.

Zama suka gyara suka cigaba da bata labarin abinda ya faru Hajja Nana ma cikin gyara zama ta riƙa basu
labarin yanda yaje dining ya same su da Khausar filla-fillah duk abubuwan da suka faru acan sai da suka
bata.

Haka nan Momy taji wani irin nutsuwa da Salama har misalin ƙarfe biyu suna zaune suna hira juyawa
Ummi tayi tare da kallon Momy tace.

“Nikam Momyn Khausar kina zaune Lamiɗo fa kin barshi shi kadai”.

Dariya tayi tare da faɗin.

“A'a haba yau kam ai nace masa Hajiya Bunayya taje ta sameshi nikam ai ina tare da baƙi”.

Da mamaki Aunty Ruƙayya tace.

“Kamar ya Hajiya Bunayya taje ta sameshi ba tare sukayi tafiyar ba?”.

Still Murmushi tayi kana tace.

“Inma tare da ita akayi tafiyar ba ai bata gan shiba bai gan taba ko?”.

Haɓa Ummi ta riƙe tare da cewa.

“To ai kema baki ganshi ba”.

Momy na dariya tace.

“A'a duk da haka dai suje na turata ni kuma inji da baƙina mana”.

Ƴar dariya Ummu tayi tare da faɗin.


“Eh lallai kam hakane”.

Daren wannan ranan haka suka rabata cikin hira.

Acan Side ɗin Haiydar kuwa kwance suke da Sulaiman yana ta bashi labarin Morocco da kuma Family
Moddibo da irin abubuwan da aka gabatar acikin Masarautar.

Acan ɓangaren su Asma'u kuwa bayan ta gama waya da Dr Jameel ne ta juya ta kalli Asiya dake waya da
Zakariyya sai kuma ta maida idanunta kan Dija dake kwance ba tayi bacci ba cikin sanyin murya tace.

“Nayi kewan Khausar bari In kirata inji”.

Ajiyar zuciya Dija ta sauke tana gyara kwanciyar ta tace.

“Wallahi kuwa nima nayi kewarta kira mana ita muji”.

Ɗaukar waya Asma'u tayi tare da dearling Number Khausar har tayi ringing biyu ta gama bata ɗauka ba
kallon Dija tayi kana tace.

“Ki gani fa har kira biyu bata ɗaga ba”.

Wayar Dija ta ɗauka ta duba lokaci ɗan ware idanunta tayi tace.

“Kina gani ƙarfe biyu na dare nefa ya za'a yi ki sameta kina ganin wannan mijin nata maƙale mata mam-
man-ne mata ai da wuya idan ba suna can suna maƙale da juna ba”.

Asma'u kuwa kirji ta dafe tare da ɗan zaro ido sai kuma tayi saurin cewa.

“Haka fa”.

Sai kuma ta janyo wayar ta kashe tare da kallon Dija tace.

“Ai Yah Moddibo duniya ne wani irin kallon da yake yiwa Khausar kamar zai mai da ita cikin zuciyarsa”.

Dija na gyara kwanciyar ta tace.

“Aikuwa Soyayya ce mai ƙarfi Moddibo Namijin Duniya ne”.

A wannan daren haka suka kwana hira.

Acan ɓangaren su Khausar ma suka kwana maƙale da juna.


Washe gari da safe

*Abujan Nigeria*

Bayan fitar Uncle Naseer da kimanin minti talatin Amina ta fara jiyo gurnanin macijin na fitowa tana
zaune Jingine jikin kushin wanda tun jiya daya shata jikinta ke mace ta kasa da faɗawa kowa aranta tana
ji tana so ta faɗawa Ummanta amma ta gagara tayi waya da Samira Sani ma tayi niyyar faɗa mata amma
sai taji bakinta yayi nauyi ta kasa sanar mata tana kwance taji gurnanin Macijin kusa da ita cikin sauri ta
miƙe daga kwance ta zubawa Micijin Ido yana isowa kusa da ita kamar jiya ya shiga rigarta ya kamo kan
Nipples ɗin ta ya-shash-sha kafin ya kama hanya ya fita tun jiya daya sha bata sake dawowa dai-dai ba
tana jin kasala bata da kuzari yanzu ma daya sake tsotsa sai taji gaba ɗaya jikinta ya sake mutuwa
ahankali ta kalli bakin Nononta na dama kana ta kalli na hagun taga ɗigon jini kamar na jiya wani irin
nauyi jikinta yayi mata ahankali ta sulale ta kwanta wani irin bacci ya ɗauketa...

Acan gidan Lamiɗo kuwa Abualeey, Waziri, Galadima Baban Zakariyya tun da sassafe aka kai musu
abinci da komai na buƙata na alfarma kuwa su Asma'u ne suka kai musu Breakfast da komai ba buƙata.

Bayan sun kammala Breakfast Ummi ta kalli Momy tare da cewa.

“Momyn Khausar mufa zamu tafi”.

Da sauri Momy tace.

“Da wuri haka Ummin Jameel?”.

Ummi na murmushi tace.

“Gidan ba kowa nayi missing ɗin ɗan Autana Bashiruna Nasan tun jiya yake tsammanin zan koma yaji
shiru yayi ta kirana ma ban ɗauka ba nafi so ma sai naje ya ganni”.

Kai Momy ta jinjina tare da cewa.

“Ayyah Asma'u am ki riƙa ɗan leƙoni kafin kema a ɗauke mana ke kinga ƙawarki kam an ɗauke ta zakuje
can ku haɗu”.

Asma'u kam kanta ta sunkuyar ƙasa tana murmushi tace.

“Momy gobe ma zanzo in Sha Allah”.

Cikin sanyi Momy tace.


“Allah ya kaimu”.

Miƙewa Aunty Ruƙayya tayi tana kallon Momy tace.

“Toh nima zan tafi”.

Kai Momy ta gyaɗa kafin duk sukayi mata Sallama suka tafi bayan ta basu komai na biki.

Acan ɓangaren Mazan bayan sun kammala Breakfast Lamiɗo yai musu jagora suka tafi gidan su Malam
Ahmad sukayi tambayar Auren Asma'u wa Jameel gaba ɗaya malam Ahmad da yaji lbrin Jameel sai da
yashiga ruɗu da tashin hankali jin tsananin kamarsa da Jameel bayan sunyi tambaya sun dawo da
tabbacin Anbasu kasancewar Lamiɗo ne ya musu Jagoranci.

Bayan sun dawo Hajja Nana, Hajja Umma Baffa Jimeta suka tafi Jauro Yaya daidai lokacin da Motarsu
Hajja Nana ya fita akuma dai-dai lokacin

Text ɗin Yah Ali ya shigo wayar Dija, cikin tsananin mamaki take karanta sakon nasa.

“Tun jiya da dare jikina da zuciyata suke gaya min kun dawo Nigeria kun shigo jihar Adamawa sabida
wani irin ni'imtaccen ƙamshi da isaka mai sanyi da nakejin wanda ya tabbatar min kin kusa dani, shiyasa
nake fata da burin in ɗaukeki daga Jauro yaya in dawo dake kusa dani a matsayin matar aurena in kin
amince Dija”.

Wasu irin tagwayen murmushi take saki ba ƙaƙƙautawa ta karanta sakon a karo na uku kana ta turawa
Khausar tare dayi mata bayanin wanda ya turo saƙon da kuma neman shawara, haka dai sukaci gaba da
tafiya.

Motarsu Hajiya Lami da Samira Sani yayi Parking sunzo wajen Hajiya Bunayya dan jin cikekken bayanin
da tsara batun tafiyarsu.

Zuwa lokacin su Abualeey sun gama komai Lamiɗo ya musu Jagoranci zuwa gidan Abban Jameel Lokacin
da Hajiya Turai da Hajiya Karima suka kalli hoton Dr Jameel dasu Abban Jameel da kuma lbrun kakannisu
da Jameel da kuma lbrin dangin Modibbo sosai suka shiga mamaki, musamman kamannin Dr Jameel da
kuma M Jameel abin yayi masifar basu mamaki ya kuma girgiza su a washe gari suka je Juuro yaya suka
gaida Hajja Nana.

Kwanan su biyu acikin Taraba suka koma Adamawa kwana ɗaya sukayi a Adamawa ya zama kwanan su
uku sukayi suka shirya komawa Morocco...
A Morocco kuwa rayuwa ta fara tafiya Khausar da Moddibo sun fara samun shaƙuwa na musamman
wanda su kansu basu fahimci haka ba aranan dasu Abualeey zasu dawo Khausar ce zaune a falon Didi
bayan sun gama girki wanda bisa alamu sun yiwa baƙi da zasu dawo ne sun gama komai sun shirya a
dining.

Ahankali Didi ta kalli Khausar tare da cewa kizo ki zauna kici abinci”.

Anutse Khausar ta ɗago Idanunta tare da shafa cikinta kana tace.

“Didi na ƙoshi bana jin yunwa”.

Juyawa Didi tayi tare da kallon Moddibo dake zaune gefe da system a gaban shi bisa alamu aikin da ya
shafi campanny Abba ne yake duba, cikin kula tace.

“Taci abinci tunda gari ya waye?”.

Kai ya girgiza cikin alamun damuwa ya kalli Didi kana ya maida kallonsa kan Didi yace.

“Babu abinda taci ni kaina bansan meyesa bata son cin abinci ba kuma ba haka take ba”.

Langwaɓar da kai tayi tare da cewa.

“Nifa bana jin yunwa nasha tea ɗaxu”.

Didi na girgiza kai tace.

“Toh tea Abinci ne? Khausar ai tea ba Abinci bane.

Rahama maza ɗebo min abinci a plate”.

Miƙewa Rahama tayi ta ɗebo abincin ta kawo mata aplate karɓan abinci tayi tare da kallon Khausar tace.

“Sa hannu kici”.

Kai ta girgiza tare da faɗin.

“Allah Didi banjin yuwa cikina aƙoshe yake”.

Kai Didi ta girgiza kana tace.

“Bana son zamanki da yunwa Khausar koda bakya jin yunwa ki karɓa kici”.

Kai ta sunkuyar ta ɗauki cokali saboda batason yiwa Didi gardama.

Moddibo kuwa ahankali ya ɗago ya kalleta tare da faɗin.


“Wallahi Didi tunda gari ya waye bata ci abinci ba idan kinga taci abinci sai na matsa mata dole² bansan
meyesa ba”.

Dai-dai lokacin Ibraahim dake shigowa yace.

“Toh ko dai bata da lafiya ne?,Idan baki da lafiya ne mu kaiki asibiti aje aduba ki”.

Tana cakalan abincin tace.

“Wallahi lafiyata ƙalau bana jin komai abinci kuma ina ci ina yawan shan Fruit nake gama shine yake
hanani cin abinci”.

Ajiyar zuciya Didi ta sauƙe tare da cewa.

“Toh yanzu dai kici bari kuma akawo miki fruit ɗin”.

Cokali biyu zuwa uku ta sake tsakura kana ta tura plate ɗin gaban Rahama tace.

“Toh muci mana”.

Ɗan ware Idanu Rahama tayi tare da faɗin.

“Ai kina gani ɗazu naci”.

Sake langwaɓar da kai tayi tace.

“Ni ma Wallahi na ƙoshi”.

Cikin sauƙe numfashi Didi tace.

“Kici mana Khausar am”.

Ahankali ta sunkuyar da kanta tare da faɗin.

“Allah Didi na ƙoshi”.

Kai Didi ta gyaɗa kana tace.

“Toh shikenan Rahama jeki ɗauko mata fruits”.

Kai Rahama ta gyaɗa sai kuma ta miƙe ta dauko mata wani kekyawan Bowl wanda ke cike da

Inabi, Apple, Banana, Pineapple, Water millo wanda yake a yayyanki an yarayarɗa madara akai.

A hankali ta gyara zamanta tare da ɗaukan fork ɗin jin Didi na cewa.

“Bismillah”. A hankali tai Bismillah tare da soka yankan kankana kana ta buɗe bakinta a hankali tasa,
lumshe udanunta tayi sabida zaƙi da garɗin madarar da ya game mata baki, a hankali take taunan
kankanan tare da haɗiyewa, sai kuma tattare ƴaƴan kankanan ta haɗesu gefen bakinta.
Shi kuwa Modibbo ta gefen idonshi yake kallonta,

yanka na biyu ta kuma kaiwa bakinta ba tare da ta haɗiye ƴaƴan kankanan ba, sai kuma ta sake harhaɗe
ƴaƴan kankanan ta tarasu gefen bakinta sabida bata iya haɗiyesu, sai kuma ta jujjuya kwayar idanunta
alamun tana neman wurin da zata zuba ƴaƴan kankanan ne.

A hankali ya miƙo mata hannunshi tare da buɗe mata tafin hannunshi, cikin fidda idanunta waje ta ɗan
jujjuyasu alamun tambaya.

“In zuba?”.

A hankali ya ɗan juyo ya ɗan kalleta tare da ɗaga mata girarsa ɗaya alamun yess zuba ya ƙare ɗaga girar
da ƙara manna hannunsa ƙasan bakinta kaɗan a hankali ta tattarosu tare da ɗan sunkuyowa ta zuba
mishi su cikin tafin hannunshi.

Cike da mamaki Rahama ta buɗe baki da hanci tana kallon su kamar wasu tattabaru.

Ibraahim ma ido ya zuba musu, ita kuwa Rahama kai ta kuma juyawa ta kalli Didi data kauda kanta gefe
tana mgnar zuci.

“Uhmmm ai in dai ya ɗauki mahaifinku zai yi abinda yafi hakama”.

ta ƙare mgnar zuci da kallon Ibraahim da ya saki baki yana kallon Modibbo ganin ya afa ƴaƴan kankanan
cikin bakinsa tare dasa hannunsa ya tsinki inabi guda ɗaya ya haɗa da ƴaƴan kankanan ya ci.

Ita kuwa Didi murmushin tayi tare da maida kanta kan TV.

Shi kuwa Modibbo hannunshi ya kuma miƙa mata a karo na biyu ta kuma sa mishi ƴaƴan kankanan.

A nutse taci gaba da ci, a hankali ta juya ta kalli Ibraahim dake cewa.

“Yah Aleey in Sha Allah nima gobe zan koma Turkey”.

Kallonsa Moddibo yayi kana yace.

“Ha'a har zaka koma kuma?”.

Ya ƙare maganar da sawa Khausar tafin hannunshi ƙasan bakinta sabida ganin ta kuma tara wasu ƴaƴan
kankanan, zuba mishi su tayi tare da zuba mishi idanu,

Shi kuma shu'umin murmushin gefen baki yayi tare da watsa ƴaƴan kankanan a baki domin shi yasan
amfanin ƴaƴan kankanan a jikin namiji, domin babu wani abu cikin fruits dake ƙarawa wa maza ƙarfin
kamar ƴaƴann kankanan shiyasa duk wani mgnin ƙarfin tattalin lafiya mazantaka zaka samu da sinadarin
ƴaƴan kankanan a ciki.
Ya tabbatar bata san amfanin da zasuyi mishi a jikinsa bane da bazata bashi ba.

Yoh shida ko azumin rage ƙarfin sha'awa yayi muddin ya kuskura yayi buɗa baki da kankana to ranar ba
bacci, bare ba azumin yayi ba, kuma gata kusa dashi.

Shi kuwa Ibraahim cikin kallon yadda yayan nashi ke amsar ƴaƴan kankanan daga bakin matarsa yana ci
ya ɗan gyara zama yace.

“Eh wasu kaya zan sake kaiwa kasan ban cika zama anan ba saboda yanayin kasuwanci na”

Murmushi yayi tare da faɗin.

“Yaro Ƙarami da neman kuɗi”.

Yaaje mgnar yana kallon Khausar data tura baki alamun ya kawo hannunshi ya amshi ƴaƴan kankanan,
miƙa mata hannun yayi tare da lasar gefen lip inshi na sama.

Didi dake sauraron tace.

“Wallahi fa kadai faɗa masa kayi masa faɗa ko zai rage Ibraahim da zirga-zirga firr yaron nan yaƙi zama
sai jaraban son Kuɗi”.

Murmushi Ibraahim yayi yana mai lallon salon so mai zafi da darasi a wurin ustzun yayansa da ya dasa
mai son aure farat ɗaya cikin fesar da numfashi yace.

“Toh Didi Idan ban nemi kuɗi ba mai zanyi nayi karatu na gama kuma Ni ba ayi min Aure ba sannan kuma
abubuwan nan abune daya kamata asame su a inda babu tunda dabino ne mutane da dama suna
bukatar shi acan shiyasa muke kai musu”.

Kai Didi ta girgiza tana gyara zamanta tace.

“Toh lallai kam wato ba'ayi ma aurena ba?”.

Kanshi ya ɗan sosai tare da sunkuyar da kai dan baisan mgn ta subce mishi ba.

Ita kuwa Didi cikin kulawa tace.

“Toh Amman ai bashi kaɗai kake yi ba inka dawo nan ɗinma komai na hotel ɗin Mouldy ka ciki”.

Ƴar dariya yayi tare da faɗin.

“Toh Didi ba dole inne mi kuɗi ba sune abokan rayuwa”.

Murmushi tayi tace.

“Yanzu kayi magana”.

Cikin sauƙe numfashi yace.


"Da Yauma nayi niyyar tafiya amma ina jira su Abualeey su dawo ne Shiyasa”.

“Allah ya dawo dasu lafiya”.

Cewar Moddibo.

Da ya kuma miƙa Khausar hannun a karo na barkai ita bashi ƴaƴan kankanan da sai yanzu ta cinye sai
kuma ta kalli bowl ɗin tuni ya cinye mata inabi.

Zama Didi ta gyara tare da faɗin.

“Aima In Sha Allah nan da awa biyu zasu iso”.

Atare suka hada baki wajen cewa.

“Masha Allah Allah ya kawo su lafiya”. Kana sukaci gaba da hirarsu Rahama kam zama ta gyara tana bin
Modibbo da Khausar da kallo domin Ita dai darasi take ɗauka.

Aranan su Abualeey suka dawo sun dawo kuma da labari mai daɗi cewa Mahaifin Asma'u ya bawa Dr
Jameel Aurenta sannan Mahaifin Asiya ma ya bawa Zakariyya wanda ansa bikin Auren nanda wata uku
ne masu zuwa.

A daren ranar misalin ƙarfe biyu da rabi.

A hankali Khausar ta saki wani irin raunataccen kuka mai cike da gajiya kasala gamida fara galabaitar da
ita da Modibbo yayi.

Wanda tun sha ɗaya ya rsitsata, hutun awa ɗaya ya bata tana cikin bacci ta kuma jin ya kwaƙumeta.

Shine har yanzu bai sararamata ba kusa 50 minutes kenan, cikin yarfe hannun ta kuma saki sassayan
kuka bawai dan zafiba sai dan gajiya duk da kuma cikekkiyar nitsuwa da yake samar nata.

“Wasshhhhhhhhh Yah Mu'allim na gaji”.

Cikin tsananin farin ciki gamsuwa salama da wadatacciyar ni'amarta ya tallabota jikinshi tare da fara sa
mata albarka da yiwa J ɗinsa addu'a da Abbanta.

“Wow Minha vidaa Jazakillahu khairan wa yatta ƙinallahu jami'an kin bani dukkan jin daɗi da na miji
kema, Allah yayi miki albarka Yayiwa Mommy gafara duniya da ƙiyama ya killace mata farin ciki ta kamar
yadda ta killace min budurcinki Allah yayi mata tukuici da jannatul firdausi”.

Cikin gajiya da narkewa a jikinsa da jin daɗin addu'ar da yake wa iyayenta tace.
“Amin Yah Mu'allim”.

Sai kuma ya tallabota suka shiga bathroom sukayi wanka kana suka fito liƙe da juna.

Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya wani shaƙuwa na musamman ne yashiga tsakanin Khausar da
Rahama wacce ta zame mata kamar Asma'u, sannan Didi na nuna mata soyayya na musamman mai
nutsarwa da kwantadar da hankali Hakama Niyna, Innayi kuwa tuni ta dawo ɗaya daga cikin ɗakunan
dake falonta, kana an kawo mata komai na girki tare da hadimai uku, biyu masu girki ɗaya kuma maiyi
mata dan gyaran ɗaki.

A banƙaren Modibbo kuwa sosai yake baza hutun amarcin da aka bashi, sai dai time to time yana leƙa
fada, domin Abualeey nada burin yin murabus nan kusa shiyasa yake nuna mishin komai na masarautar
Alhamdulillah kuma yana gane komai sosai.

Alhamdulillah Abban Jameel kuwa ya ɗauki Yah Ali aiki a Company sa wanda yakeso shi zai maye mishi
gurbin Modibbo, sosai karar da Abban Jameel yayiwa su Bappa jimate ya sasu farin ciki ya kuma ƙara
dangon zumunci

Aɓangaren Amina haka rayuwa ta cigaba da tafiya tsakaninta da Macijin nan kullum zai fito yasha
Nononta wanda zuwa yanzu ta fahimci jininta yake ɗan zuka kasancewar duk sanda yasha nono taɓa
ganin jinin kaɗan tana so ta faɗa amma ta kasa idan ta fadawa Uncle Naseer cewa tana ganin jininta
yake zuƙa sai cewa yayi ai da jininki yake zuƙa da tuntuni kin mutu kawai yana tayani shan abu nane,
ahaka yake sha-shantar da ita.

Haka tsakanin Dr Jameel da Asma'u soyayyarsu ke tafiya gwanin ban sha'awa.

Haka ma Dr Zakariyya da Asiya soyayyarsu ke tafiya cikin kwanciyar hankali.

Hakama Yah Ali da Dija.

Wanda tuni mgnar ta isa ga Bappa jimate.

Tuni shirye-shiryen aure ya kankama sosai dan Abualeey da kanshi yace ya ɗauki nauyin gidan Jen
angawaye da komai na amare Abban Jameel kuwa shine ya ɗauki nauyin komai na auren Yah Ali da Dija
tuni yasa an fara gyara gidan cikin sama kuwa Yah ɗauki Yah Abba ma aikin sabida shima CB inshi sunyi
kyau.

Aɓangaren Hajiya Bunayya da Hajiya Lami ma sun shirya zuwa Niger wajen sabon bokan da suka samu...

Yau kwanan su Ummi goma sha biyu kenan da tafiya.

Ahankali Khausar ta tura ƙofan Falon Moddibo ta shiga saboda tana so tayi wasu da Ummi dan tunda
suka tafi ba tayi waya da kowa ba kasancewar Moddibo ya riƙe wayarta shiyasa ta shiga ahankali saboda
tana so zata roƙesa ya bata wayarta ta kira Ummi Momyn ta harma da Hajja Nana in tayi sa'a ta sameta.

A hankali ta shiga tsakiyar Falon sai kuma ta ɗan jujjuya idanunta ganin ba kowa,

ha yasa ta nufi cikin bedroom ɗinsa tana shiga ta hango wayoyinsa da nata akan dreesing mirrow cikin
sanɗa ta ƙarasa jikin dreesing mirrow jin alamun yana wanka a ban ɗaki.

Da sauri ta ɗan sunkuya ta ɗauki wayar dai-dai lokacin kuma, ya buɗe ƙofar tare da fito ƙugunsa ɗaure
da towel cak ya tsaya yana kallonta ganin yanda take sanɗan ɗaukar wayar tana juyawa ta ganshi tsaye a
gabanta,

cikin sauri ta runtse idanunta ganin faffaɗan ƙirjinsa awaje cikin wata sanyayyar murya yace.

“Mene?”.

Cikin tura baki tace.

“Baka da riga”.

Da mamaki ya kalli yanda ta runtse idanunta ya lura ganinshi na tsokanon kuran karfenta cikin yin
murmushin gefen baki yace.

“Yau kika fara ganina bani da riga ne?”.

Muryanta na rawa tace.

“Ni dai ka rufe jikinka”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Ok na rufe”.
Ya ƙarashe maganar tare da since towel ɗin ta ya ɗan murzashi ƙasa kaɗan har sai da jikinshi ya bayyana.

Da sauri tace.

“Da gaske?”.

Cikin tsareta da ido yace.

“Yess da gaske buɗe idonki ki gani”.

Cikin sanyi ta buɗe Idanunta a hankali, wani irin tsalle tayi tare da fara yarfa hannunta tana ihu.

Lokacin da ta buɗe idon,

Gaba ɗaya ta zazzaro idanunta waje tamkar zasu zubo ƙasa, sai kuma tasako ihu kana ta juya da sauri
alamun zata gudu.

ya janyota tare da rungumeta ahankali yace.

“Ba jiya guduwa kika yiba, kika ƙi kwana a nan ba, kika kwana aɗakin Didi ba, toh gashi yanzu kin shigo
hannuna”.

Ya ida maganar yana jawota jikinshi tare da rungumeta a jikinshi....

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

62

Tallah! Tallah! Tallah!

Shahararriyar Marubuciyar nan mai suna IBNATU-UMAR data rubuta ALAƘA, FANSA, RUHI BIYU ZUCIYA
ƊAYA, GAGGARARU yanzu ta kawo maku littafi mai suna HANTA DA JINI, free book ne bata sai kin biya
koh sisi ba, littafine dake kunshe abubuwa da dama cin amana, domestic abuse da wasu matan ke fama
dashi a gidan aure, kiyayya da kuma zazzafar soyayya.

Ku danna link dinnan dan kuyi joining group din https://chat.whatsapp.com/J9OJOK93SFt7inXdfmSa3t


Ahankali ya Kai bakinsa saitin kunnenta kana yace.

“Wato dama yau ma niyyar ki guduwa za kiyi baza kizo mu kwana tare ba? Wai ayi mace tai ta gudun
Mujinta bata tsoron fushin Ubangiji da tsinuwan mala'ikun Allah ta'ala”.

Tana shaƙan ƙamshin jikinsa ta ɗan turo baki tare da faɗin.

“Toh ba kai bane idan nazo kusa da kai sai kai ta damuna kai yita hanani bacci”.

Ta ƙare maganar cikin yanayin kasala

Cikin sauri ya rufe bakinta tare da cewa.

“Bakya son lada ne?“.

A hankali tace.

“Ina so mana”.

Cikin hikimar yadda yake sarrafa tunaninta yace.

“A'a bakya so tunda gashi kina gudun aikin lada, ga lada ga salama fa amman kike gudu sabida ba
kyason ladane?, Kinsan jiya da kika kwana a ɗakin Didi kika gujeni kinsan Malaikun Allah kwana sukayi
suna tsine miki?”.

Cikin sauri da tsoro ta zare idanunta kana tace.

“Astaghfirullah!! Astagfirullah Wa'atubu ilaik!!! Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un kamar ya kuma?”.

Cikin sauƙe numfashi ya lumshe idanunsa kana yace.

“Toh ba kin guji mijinki ba ai bada Izinina kika tafi kikaje kika kwana acan ba”.

Asanyaye ta sake lafewa ajikinsa kana tace.

“Toh kayi haƙuri ka yafemin bazan ƙara ba In Sha Allahu”.

Cikin ƙara nusar da ita tsoron Allah da hakkin miji yace.

“In dai baki so Allah da Mala'ikunsa su tsine miki toh ki daina gudun Mijinki”.

Kai ta Jinjina tare da cewa.

“In sha Allahu na daina to amma kayafe min ai ko?”.


Kai ya gyaɗa kana yace.

“Bazan yafe miki ba sai naga baki sake ba”.

Cikin tabbatarwa tace.

“In sha Allahu nayi alƙawari bazan sake ba bana son fushin Ubangji”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da lumshe idanunsa ya sake buɗe su akanta yace.

“Idan bakyason fushin Ubangji kada ki yarda da fushina minjiki ko?,Kina sane da hakki da girma da
darajar miji ko?”.

Ahankali ta gyaɗa kai tare da cewa.

“Na sani”.

Yana yawo da hannunsa awuyanta yace.

“Toh meyesa kika gudu jiya?”.

Rau-rau tayi da idanu tare da faɗin.

“Na gaji ne nasan kuma idan na zauna zaka hanani bacci”.

Kai ya girgiza tare da faɗin.

“Bazan hana ki bacci ba ki kwantar da hankalin ki sannan ki nutsu ai kinsallameni da yamma dole kuma
in kin gaji in barki ki huta”.

Ya ƙarashe maganar yana zama bakin gado itama ya zaunar da ita.

Akunyace ta ɗan kawar da kanta gefe tace.

“Toh ka jawo towel ɗin ka mana ka rufe”.

Ɗan murmushi yayi ganin yanda ta kawar da kanta kana ta ɗan runtse idanunta ahankali yace.

“Toh”.

Tare da jan towel ɗin ya daura saman ƙugunsa sai kuma ya daidaita nutsuwarsa tare da cewa.

“Kinci abinci?”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Eh”.

Cikin ɗan ɗaure fuska ya girgiza kai tare da cewa.


“Ƙarya kike baki ci abinci ba”.

Kanta ta sunkuyar ƙasa tace.

“Allah naci Didi ta bani naci”.

Hannunsa yasa ya shafa cikinta tare da faɗin.

“Amma kaɗan kika ci ko”.

Saurin girgiza masa kai tayi tace.

“Amma nasha Tea Mai yawa”.

“Yanzu taso muje kici abinci”.

Kwaɓe fuska tayi tare da langwaɓar da kai tace.

“Allah Yah Mu'allim na ƙoshi bana jin yunwa”.

Da wata irin murya me ɗauke da kulawa tausayi jin ƙai yace.

“ *Minhaaa* bana son kina zama da yunwar nan na rasa meyesa kike yin haka?, Kinga Didi ma abun
yana damunta dan jiya Abualeey da kansa yake cemin wai ko dai za muje asibiti ne saboda Didi tace
masa bakyason cin abinci”.

Zamanta ta ɗan gyara tare da cewa.

“Wallahi fa ina ci kune kuke ga kamar bana ci, kuma wallahi ni lafiyata lau”.

Cikin gamsuwa da lafiyarta ƙalau yace.

“Toh shikenan”.

Haka dai yaita lallaɓanta adaren ma bai barta ba...

Washe gari da safe agarin Gembila Hajiya Bunayya ce a falon Hajiya Lami suna zaune sai Samira Sani
dake gefensu cikin sauƙe numfashi Hajiya Bunayya tace.

“Na yiwa Lamiɗo maganar tafiyar mu amma yace dole sai nan da sati biyu kinga tafiyar nesa baza kace
zaka saci hanya ka tafi ba”.

Kai Hajiya Lami ta jinjina tace.


“Hakane kam nima na faɗawa Alh zamu yake tambayata wai me zamuje nace ai yasan kina da ƴan Uwa
acan toh sune zamuje dubawa”.

Zare ido Hajiya Bunayya tayi tace.

“Ikon Allah nima fa haka na cewa Lamiɗo kece kike da ƴan uwa acen zamu je”.

Ƴar Dariya Hajiya Lami tayi tare da faɗin.

“Toh Allah ya rufa mana asiri kar dai asirun mu ya tonu”.

Hajiya Bunayya na gyara zama zama tace.

“Nikam ma cewa nayi Goggonki ce ta rasu zamu je Ta'aziyya”.

Kai Hajiya Lami ta jinjina tare da faɗin.

“Nima kuma cewa nayi wani Baffanki ne ya rasu zamu je muyi Ta'aziyya”.

Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta sauke kana tace.

“Toh shike nan dai tunda mun tambaya sunce sun barmu ai magana ya ƙare”.

Hajiya Lami na Kada kafa tace.

“Nikam ma Babansu Samira cemin yayi sai juma'a mai zuwa kinga sati ɗaya kenan ke kuma gashi yace
har sai sati biyu to amma dai ba damuwa zai zo kamar yau”.

Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa tace.

“Hakane kam”.

Cikin sauƙe ajiyar zuciya Hajiya Lami tace.

“Ya labarin Amina kuna waya”.

Hajiya Bunayya na murmushin tace.

“Eh muna waya sosai ma?”.

Samira dake gefe wacce tunda suka fara magana kanta ke ƙasa ta ɗago ahankali tace.

“Nima ɗazu munyi waya da ita”.

Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh nima munyi waya da ita”.


Da damuwa Samira tace.

“Amma fa ni naji Muryanta yayi sanyi acikin kwanakin nan duka”.

Kai Hajiya Bunayya ta jinjina tace.

“Nima naji Muryanta yayi sanyi gaskiya ta canza sosai amma ina ga ciki ne”.

Cike da farin ciki Hajiya Lami tace.

“A'a Kice kwalliya ta biya kuɗin sabulu abin har ya samu?”.

Hajiya Bunayya na dariya tace.

“Gaskiya kam idan ba ciki ba sanyin nata yayi yawa kuma kona tambaye ta lafiya zata ce min eh lafiya
babu komai”.

Cikin jin daɗi.

Hajiya Lami ta jinjina kai da faɗin.

“Aikam ga duk kan alamu wannan ciki ne”.

“Sosaima nima abinda nace kenan?”.

Bayan sun gama maganarsu Hajiya Bunayya ta kalli Samira data zabga tagumi tace.

“Amma ya jikin Samira abin nan har yanzu yana zuba?”.

Shiru tayi sai kuma tace.

“A'a har yanzu dai abin yana zuba sai wani abu ne yake fita min agabana guda guda”.

Hajiya Lami ta karba da cewa.

“Ai shiyasa ma na matsu mu tafi Niger ɗin nan saboda wasu yanzu guda gudan abu ke fito mata”.

Atsorace Hajiya Bunayya ta dafe ƙirjinta tace.

“Guda guda kuma to na mene?”.

Kai ta jinjina tare da cewa.

“Wallahi kuwa idan wajen ya fara yi mata ƙaiƙayi kamar za tayi hauka sai ta shiga ruwan zafi da gishiri sai
kiga abu na fitowa daga gabanta kamar duwatsu”

Cikin tashin hankali Hajiya Bunayya tace.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un mun shiga uku wannan wani irin masiface?”.
Da damuwa Hajiya Lami tace.

“Wallahi kuwa gashi Boka Kar'uzu har yau bai dawo ba”.

Da damuwa Hajiya Bunayya tace.

“Lafiya kuwa bai taɓa tafiya yayi dadewa irin wannan bai dawo ba”.

Cikin sauƙe ajiyar zuciya da jimami Hajiya Lami tace.

“Nima dai wannan abin ya daure min kai”.

“Aikam dai dole muje Niger ɗin nan asamo mata magani”.

Cewar Hajiya Bunayya.

Kai Hajiya Lami ta jinjina da faɗin.

“Munje asibiti ma abanza likitoci sun kasa ganewa menene waɗanan abun”.

Haka Hajiya Bunayya tayi ta mamaki Amma duk da haka basu san Annabi Yafaku ba haka dai suka ci-
gaba da labarinsu akan zasu tafi wajen Bokansu...

*Morocco*

Washe gari da safe

Khausar ce zaune tana riƙe da wayarta ta kira Momyn.

Acan ɓangaren Momy kuwa zaune take a Falonta yayin da Haiydar ke zaune gefenta suna hira tana ganin
kiran Khausar tayi picking tare da cewa.

“Mamana na kaina sai yau kenan?”.

Aɓangaren Khausar kuwa kallon Moddibo dake kwance ya ɗaura kansa kan cinyarta yana fuskantar ta
kana hannunsa na cikin rigarta yana zagaye Hudar cibiyar cike da farin ciki tace.

“Wallahi Momy na nayi kewar ku kwana nawa ba muyi waya ba?”.

Murmushi Mommy tayi tare da cewa.

“Khausar am Nima nayi missing ɗin ki nace Khausar kam ta manta Momynta ta samu Moddibon ta”.

Murmushi tayi tare da faɗin.


“Momy na isa In manta dake Momy na kina cikin raina Yah Moddibo ne ya karɓi wayana ai be bani ba sai
yau ya bani shine yace wai bazai bani ba kada In kira ki inyi ta kuka ina tayar miki da hankali”.

Cikin sauƙe ajiyar zuciya Momy tace.

“Toh amma dai yanzu kin daina kuka ko?”.

Kai ta gyaɗa kamar tana gabanta tace.

“Eh Momy na daina.

Yanzuma nayi waya da Ummi da Asma'u ma harda cewa wai har yanzu ina kuka ko na bari?”.

Murmushin mai ɗan sauti Momy tayi tare da cewa.

“Dagaske kin daina ko?”.

Kai ta gyaɗa tace.

“Eh Momy na daina?”.

Zama Momy ta gyara tare da cewa.

“Kuna lafiya dai”.

Khausar na Kada ƙafa tace.

“Muna lafiya,Momy ina Haiydar?”.

Kallon Haiydar Momy tayi tare da faɗin.

“Gashi nan ma yana jinmu”.

Cikin kewarsa tace.

“Ayyah nayi kewarsa”.

Haiydar na murmushi ya gyara zamansa tare da cewa.

“Nima nayi missing naki Addah Khausi yanzu babu mai mana faɗa babu mai sharewa Momy ɗakinta
Momy ita da kanta ke share ɗakinta”.

Kai ta langwaɓar tace.

“Ayyah toh Haiydar ka fara share mata mana”.

Cikin sauri yace.


“Toh ai ban iya ba Addah Khausy”.

Sake langwaɓar da kai tayi cike da tausayin Momy tace.

“Toh ka koya mana”.

Dariya Momy tayi tare da cewa.

“Toh ya za'a yi namiji yayi shara Khausar?”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.

“Gaskiya nikam Momy ki samu me yi miki aiki ta riƙa yi miki sharan daki, da wanke-wanke tunda Raudhat
ƙarama ce baza ta iya ba”.

Kai Momy ta jinjina tace.

“Raudat baza ta iya ba amma idan an kwana biyu tana shiga dakin ki tace bari ta sharewa Addah Khausi
ɗakinta kafin ta dawo”.

Dariya Khausar tayi kana tace.

“Allah sarki Raudhat ai zanzo nan kusa in Sha Allah”.

Sai kuma tace.

“Momy abawa Raudat wayar”.

Da sauri Raudhat ta karɓa wayar tare da faɗin.

“Addah Khausy yaushe zaki dawo?”.

Cike da ƙaunarta da kuma kewarta tace.

“Gobe zan dawo”.

Cikin sauri ta sunkuyar da kanta jin yanda Moddibo ya zira harshensa cikin hudar cibiyarta ɗan hararanta
yayi sai kuma ya zaro harshensa yace.

“Gobe zaki dawo kike faɗa?”.

Sai kuma yayi ƙasa da murya yace.

“Raudhat ƙarya take miki baza ta dawo ba”.

Ga mamakinsa sai yaji Raudhat na cewa.

“Ayyah Malam Moddibo yaushe zaku dawo ne?”.

Karɓan wayar yayi kana yace.


“Ke dai yaushe zaki zo mana?”.

Cike da farin ciki tace.

“Momyna tace zamu zo Auren Addah Asma'u”.

Murmushi yayi yace.

“Toh shikenan sai kinzo me kike so in ajiye Miki?”.

Murmushi tayi sai kuma tayi shiru alamar tunani da sauri tace.

“Ina so ku siya min Teddy”.

Ƴar dariya yayi tare da cewa.

“Toh shikenan za'a siya miki Teddy Raudhat”.

Sai kuma ya miƙawa Khausar wayar karɓan tayi tana ƙoƙarin warware rigarta daya nannaɗe saurin riƙe
hannunta yayi yace.

“Meyesa zaki rufe min abu na?”.

Ashagwaɓe ta kallesa sai kuma ta cinno baki tace.

“Abinka ko abuna?” .

Gira ɗaya ya ɗaga mata tare da cewa.

“Abuna dai?”.

Cikin sauri Momy data karɓi wayar ahannun Raudhat ta miƙawa Haiydar wayar Haiydar kuwa ahankali
yace.

“Addah Khausy idan farcena ya taru Wazai yanke min?”

Da murmushi afuskarta tace.

“Allah sarki ɗan Uwana nayi missing ɗin ka yanzu toh wa zai yanke maka?”.

Kallon Momy yayi sai kuma yace.

“Zan bawa Momy ta yanke min”.

Kallonta Moddibo yayi sai kuma yasa harshensa yana lasar hudar cibiyarta da sauri tace.

“Ka bari mana”.

Haiydar dake riƙe da wayar yace.


“Me zan bari kuma?”.

Baki ta cunno tace.

“A'a Ni bada kai nake ba.

Moddibo kuwa wayar ya karɓa ya katse kiran cikin tsira mata ido yace.

“Kina magana dani kuma kina magana da Haiydar kina so ki faɗa masa abinda nake miki ko?”.

Langwaɓar da kai tayi ta shagwaɓe murya tare da faɗin.

“Toh ba kai bane ka cika neman tsokana wallahi Yah Mu'allim”.

Yana mutsu-mutsu da kansa akan cinyarta yace.

“Neman tsokana ne? Nida abuna hakkina ne fa? halal ɗina ne fa.

Kina so ki faɗa fushin Ubangji ne?”.

Saurin girgiza masa kai tayi tare da cewa.

“Toh Ni kabarni in gama waya dasu mana”.

Yana yawo da hannunsa kan maranta yace.

“Ki bari idan na fita sai ki kirasu ki sake waya dasu”

Tana lumshe idanunta ta fesar da numfashi ta motsa laɓɓanta tare da cewa.

“Kai yaushe zaka fita?,Bayan ko yaushe kana gida”.

Ware idanunsa yayi yace.

“Au kin gaji da zamana agida ne?”.

Kai ta girgiza tace.

“A'a Ni dai bance ba amma kai baka fita ko ina ma?”

Murmushi yayi yana cigaba da shafa hudar cibiyarta yace.

“Zan fara fita ma sai kinso ganina fada ta rikeni kuma idan ina damunki ba matsala zan gayawa innayi a
san abinyi”.

Sai kuma ya daura harshensa ya cigaba da lasar hudar cibiyarta cikin sauƙe numfashi tace.

“Yah Mu'allim ka bari mana”.


Ta faɗa tare da manna hannunta kan sajensa tana shafawa.

Muryansa anarke yace.

“Toh nima ki bari mana Yah Mu'allima”.

Idanunta alumshe tace.

“Me nake yi?”.

“Kina shafa min saje kina cewa me zaki bari”.

Dai-dai lokacin kuma aka kira Sallar la'asar miƙewa yayi yace.

“Bari In tafi masallaci kafin ki fara cewa bana zuwa masallaci ma”.

Ware ido tayi tace.

“Na isa?, Ai duk shedar da zan bayar akan ka bazan bada shedar baka zuwa masallaci ba”.

Cikin ɗan hararanta yace.

“Bayan ma tunda kika zo sau biyu ina makara bana samun zuwa jam'i”.

Murmushi tayi tare da faɗin.

“Kaine dai ka makarar da kanka da kanka”.

Miƙewa yayi yace.

“Ni kika ce ina makarar da kaina ko?”.

Cikin ƙasa da murya tace.

“Kwaɗayinka dai ya makarar da kai”.

Ɗan ware ido yayi yace.

“Nine ma me kwadayin?”.

Cikin sauri ta nufi ƙofan Falon tana murmushi.

Ahaka dai rayuwa ya cigaba da tafiya baki ɗaya yanayin Khausar ya fara canzawa sosai Moddibo ke
mamakinta yawan rawan kanta da rakaɗinta ya ragu yana mamakin ashe dama haka Aure ke nutsar da
mace.

Yau kimanin satinta biyar da tarewarta a Side ɗin Moddibo


Kuma sai wannan ranan Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka samu tafiya Niger.

Yau suna cikin ƙasar Niger yankin Damagram suna isa Damagram bisa jagoranci wani daga cikin Mutimin
Ƙasar wanda wacce tayi musu hanya zuwa wurin bokan ta haɗa su dashi yayi musu Jagoranci.

Akan mashin ya ɗauke su 3in1 sunyi tafi ta kimanin tsawon Klmt 200 sun wuce ramuka da kwazazzabu
da Sahara kafin suka isa gidansa dake can cikin Sahara wajen shiru ba kowa sai wannan gidan shi kaɗai
wanda yafi kama da shuri suna isa daf wajen bukka ya fito cikin rawan jiki da mamaki suka shiga ga
mamaki su sai suka ga sun fito akan ruwa.

Suna shiga Boka ɗan Gillaw ya kece da wata irin dariya mai kama da haushin kare cikin wata Gaggausan
murya mara daɗin amo da sauti yace.

“Hajiya Bunayya daga Ƙasar Nigeria Jahar Taraba yankin Gembila kinzo ne akan ƴar kishiyarki wacce ta
kasance agola agidan mijinki kina so akashe Aurenta da Sarki Aliyu Youseep Mohammed Mouley ki
kwantar da hankalin ki idan har kinbi dokokin mu da sharaɗan mu da ƙaidarmu burinki zai cika mu
mutum baya zuwa wajen mu burinsa bai cika ba sai dai in bebi ƙai'ida ba”.

Cikin rawan jiki tsoro gami da farin ciki Hajiya Bunayya ta gyara zamanta tare da cewa.

“Zanbi Boka Ɗan Gillau in Sha Allah”

Cikin wata razananniyar murya Mai furgitarwa ya ɗaga mata hannun kana yace.

“Kar ki sake kiran sunan Allah anan in ba so kike aikinki yaƙi samuwa ba idan Allah kike son kibi ai banan
zaki zo ba sai kije ki samu Malaman Sunnah malaman Addini kana ki tsarkake zuciyarki ki cire hassada,
munafurci, Zamaba cikin aminci, Manaƙisa da shiga rayuwar mutanen da babu ruwansu dake”.

Wani yawu mai ɗaci ta haɗiye still jikinta na kyarna ta gyaɗa masa kai tare da faɗin.

“Tuba nake Ɗan Gillau nayi shiru bazan sake ba”.

Hannunsa ya ɗaga sama kana ya fara wasu irin maganganu da tsatsuba irin na matsafa sai ga wani ƙurtu
jajawur ya fito wani ƙullin magani ya cire acikin shima yana naɗe cikin jan ƙalle atake idanunsa sukayi
wani irin Ja cikin wata murya mai cike da tabbatarwa yace.

“Ya rantse da Shu'umi uban shu'umai shugaban su wanda babu Sheɗan abin dogoron su kina amfani
dashi yanda gaya miji matsala ta ƙare buƙatar ki zata biya”.

Cikin rawan jiki ta amsa tare da cewa.

“Toh Boka baka faɗa min kuɗin ba”.

Kai ya girgiza tare da kallonta da Jajayen Idanunsa masu furgitarwa da ban tsoro yace.
“Idan kuɗi ne nasan zaki iya baki da matsala dashi amma ƙaidan aikina sai buƙata ta biya za'a biya dole
sai kinje kinyi amfani da maganin idan buƙata ta biya kizo ki biya idan kuma baki zo kin biya ba mu da
kanmu zamu je mu nemi hakkinmu akan ki idan kuma baki biya ba muyi maganinki”.

Kai ta gyaɗa tana kallon Hajiya Lami dake murmushin samun nasara tace.

“Baka da matsala damu Boka Ɗan Gillau zaka same mu masu cika alkawarin”.

Ƙullin magani yasa mata atsakiyar tafin hannunta na hagu yace.

“Ki kwance,da yatsun biyu na hannun hagu ki gani”.

Jiki na rawa ta gyaɗa kai tare da sun cewa kamar yanda ya faɗa garin magani ta gani da wasu ƴan ƙwallo
guda uku kamar na aduwa kallonsa tayi tana jiran karin bayani.

Dariya ta kece dashi wanda yasa bukkan girgiza kana yace.

“Kinga wannan?”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Na gani Boka Ɗan Gillau ko me kake so in dai burina zai cika zanyi ko kwanciya kakesonyi dani”

Murtuƙe fuska yayi kana ya mata wani kallo tare da cewa.

“Ni bance ki kwanta dani ba,Ina zanyi Jima'i da bil'adama inji daɗi Ni da nake jima'i da Aljanu ko jakuna
bani da lokacin yin Jima'i da bil'adama dan haka kije kisa wannan abin cikin bayanki yayi kwana uku”.

Saurin kallon abin tayi sai kuma ta maida kallonta kansa jin ya cigaba da cewa.

Idan yayi kwana uku sai ki cire ki shanyasa ya bushe sai ki haɗa da garin maganin ki ɗibi ƙasar tsakiyar
gidanku ki haɗa ki watsar iska ya ɗiba, duk inda take a duniyar nan sihiri zaije ya sameta kuma ya
kamata. yanda kika san kashi nada baƙin jini awajen ko wani ɗan Adam toh haka za tayi baƙin jini a idon
mijinta da dangin mijinta ke dama duk wani makusancinta aduniya hatta uwar data haifeta sai tayi baƙin
jini a idanunta yanzu ke kanki idan ki kaga kashin ki kina sha'awar ki sake kallonsa?”.

Cikin matsanancin farin ciki da jin daɗi ta girgiza masa kai kai ya gyaɗa ya cigaba da faɗin.

“Toh yanda kashi keda baƙin jini kowa ke ƙyamansa ba wanda ke son ganinsa atsakiyar mutane haka
zata kasance tamkar mujiya, babu wanda zaiso kasancewa da ita har yawu sai an fara zubarwa akanta
yanda kika san duk wani baƙin jini na kashi to haka zata kasance.

Sai tafi mujiya bakin jini ai mujiya ana zama da ita kashi fa ana iya zama dashi?”?

Dariya ta ƙyalƙyale dashi har wani irin tsuma jikinta keyi na farin ciki kallonsa tayi tace.

“Boka an gama kuma in nayi na ƴar yayi zan dawo ayi min na uwar ma”.
Shima dariya ya ƙyalƙyale dashi wanda yafi kama da kukan alade kana yace.

“In kin gama kudin da zaki biya kuɗi dubu dari uku da hamsin da uku da ɗari uku da Naira uku da
karnuka uku alade uku jakuna mata wanda zanji dadin kwanciya dasu zaki biya mu”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Boka wannan magana tazo da sauƙi”.

Kai ya jinjina tare da maida Jajayen idanunsa kan Hajiya Lami yace.

“Kee kuma kinzo batun ƴar kice?”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Eh Boka Ɗan Ilu Ina nenan temakon ka daka temaki ƴata”.

Wani ƙullin magani ya acikin baƙin ƙyalle ya miƙa mata kana yace

“Gashi ki jiƙa ki bata tasha idan har ta warke ku biya idan bata warke ba ku bari magana ta ƙare basai
kun biya ba”.

Muryanta na ɗan rawa ta risinar da kai tare da cewa.

“Boka abinfa na zuba sosai”.

Kansa ya jinjina kana yace.

“Kada ki damu kije kiyi yanda na faɗa idan tasha ta samu sauƙi abiya idan bata samu sauƙi ba kada ku
sake zuwa inda nake da buƙatar ku”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Nagode da muna ta jiran wanda yayi mata aikin ai”.

Wani wawan dariya yayi tare da cewa.

“Ai wannan shima yana fama da kanshi ko kun gashi bazaku ganeshiba ya fara girbar abinda ya shuka
ne”.

Cikin mamaki suka zuba masa ido suna nazartar kalaman sa.

Cikin sauƙe ajiyar zuciya Hajiya Bunayya tace.

“Yanzu Boka batun auren ƴata Asiya ɗin nan yanzu saura wata ɗaya da mako uku ina so idan aka raba
Auren Khausar da Moddibo mai zai hana ya Auri Asiya tunda ita Amina tuntuni anyi Aurenta da wannan
Jarabebben Yaron”.
Wata mahaukaciyar dariya ya kece dashi wanda yasa suka shiga nutsuwarsu kana yana nuna ta da yatsa
ya cigaba da dariya kusan minti biyu kafin yace.

“Ai Amina kam ba maganarta kwatakwata kibar batun maganarta ki daina kira min sunanta anan saboda
waɗan da suke tare da ita Aminaina ne babu yanda zanyi in shiga tsakaninta dasu shin baki ga gidana
kamar curuba toh ai muhallin waɗanda ke tare da Aminane”.

Hajiya Bunayya kuwa cikin rashin fahimtar abinda yake faɗa tace.

“Yanzu ba za'a samu idan Moddibo ya saki Khausar ya Auri Asiya”.

Fuska ya ɗaure tamkar na tsohuwar biri kana ya buga mata tsawa tare da cewa.

“Asiya wannan miji shine ya dace da ita ke dai kawai tunda ga abinda kike so kije kiyi Moddibo zai sake
ta magana ta ƙare”.

Kai ta jinjina tare da cewa.

“Nagode yaushe zan dawo?”.

Idanunsa ya ɗaga sama kana yace.

“Duk randa buƙatarku ta biya bukatar ku yana biya washe gari ku shirya kuzo ku biyani idan kun ki koda
second ɗaya kamar inuwa haka zan biku Nasan duk motsin ku sannan in tona muku asiri a inda baku zata
ba”.

Kai suka gyaɗa har suna haɗa baki wajen cewa.

“Zaka same mu masu cika alkawarin”.

Sai kuma suka miƙe zasu fita cikin tsawa yace.

“Ku fita da baya da baya sannan ku cire kayan ku tsirara zaku fita daga ciki ba'a fita da sutura anan dan
kayanku shine mahadin bibiyarku”.

Jiki na rawa suka cire kayansu kana suka fita tuɓutur-tuɓutur.

Suna fita Mutumin daya rakasu ya miƙa musu kaya kasancewar yasan ƙai'idar wajen karɓa sukayi suka sa
kaya ya goya su amashin kamar yanda suka zo aranan suka koma cikin Damagram suka samu masauki
suka kwana washe gari suka kama hanyar dawowa Nigeria ƙarfe uku dai-dai Jirginsu ya sauka cikin
Abuja, A Abuja suka kwana karfe tara Jirginsu ya tashi daga Abuja zuwa Adamawa daga nan suka hau
mota zuwa Taraba.

Bayan sun dawo da kwana biyu sun huce gajiyarsu.


Yau Hajiya Bunayya ta shirya fara aikin cikin yaƙini da gamsuwa, rashin imani, da bushewar zuciya, ta
shiga ban ɗakinta kana ta tsugunna ta kware takashinta ƙwallon aduwar ta ɗauka tare da turawa acikin
da ƙarfi ta runtse idanunta jin wani irin azabebben zogi daya amsa cikin dauriya ta runtse idanunta tare
da cewa.

“Ai ranan biyar buƙata rai ba abikin komai yake ba”.

Sai kuma ta ɗauki na biyu ta cusa shima zugine ya ratsata wanda yafi na farko atake wasu ƙwallan azaba
suka zubo mata tayi saurin gogewa tana murmushin ƙeta kana ta ɗauki na ukun ta cusa da ƙarfi tana ciro
ya tsar taga yatsar yayi datti da sauri ta ɗauki Morning Fresh dake ajiye ta wanke hannunta afili tace.

“Wannan ya tsata ne ma da kaina nake jin ƙyamarta ina ga Khausar?,da zatayi baƙin jini awajen mijinta
da dangin ta babban farin ciki na ma ance a idanun duniya duka za tayi baƙin jini duk yanda Yayun
mijinta da ƙannensa ke rawan jiki akanta duk zasu tsaneta su koreta fata-fata Ni banƙi ma ace daga
Morocco ta dawo har Nigeria da kafa ba shegiya ƴar Bororon daji tana nan kamar Sadaka yalla”.

Tana gamawa ta fito tare da zama gefen gado wayarta ta ɗauka tare da dearling Number Amina tana jin
ta ɗaga tace.

“Hello Amina”.

Acan ɓangaren Amina kuwa cikin sanyin murya da rauni ta sauƙe Ajiyar zuciya kasancewar dai-dai
lokacin macijin ya gama shanta araunane tace.

“Umma”.

Hajiya Bunayya na gyara zama jin muryan Amina tace.

“Amina am kinyi sanyi da yawa”.

Cikin lumshe idanu da rauni Amina ta girgiza ji kai tare da cewa.

“Bakomai Umma”.

Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta sauƙe kana tace.

“Ko dai cikin ne yake wahalar dake haka?”.

Numfashi Amina ta fesar tare da cewa.

“Hmmm”.

Kasancewar baza ta ita cewa komai ba duk da kuwa yanda zuciyarta ke son faɗa amma bakinta ya gaza.

Murmushi Hajiya Bunayya tayi tare da faɗin.

“Kin san shekaran jiya muka dawo daga Niger?”.


Kai ta gyaɗa tace.

“Eh munyi waya da Samira take cewa kun dawo har an bata magani ta fara sha”.

Kai Hajiya Bunayya ta jinjina tare da faɗin.

“Haka dai munje mun dawo in Sha Allah burin mu zai cika Khausar za'a korata zata baro Morocco da
baƙin jini yanda babu wani ɗa namiji da zai sota kowa zai ƙyamaceta”.

Cikin sanyin Amina tace.

“Hmmmm Ummah kenan? dama dai kin haƙura ni yanzu bana son hakan ma cutarwa da wani bayi da
wani riba abuma ko mun yi ba Kamasu yakeba saboda sun yarda da Allah suna da kekyawan yaƙini da
riƙe ibada”.

Baki ɗaya yanzu bata da kuzari tsoro ya kamata kwata-kwata bata cikin nutsuwarta da haiyacinta tana so
ta buɗe bakinta ta faɗawa mahaifiyarta amma bazata iya ba.

Hajiya Bunayya kuwa cikin bushewar zuciya da rashin fahimtar halin da ƴar tata ke ciki tace.

“Ki kwantar da hankalin ki In Sha Allah kwanan nan burinmu zai cika in Allah yaso ya yarda wannan aikin
shi yafi na Kar,zu”.

Ahankali Amina tace.

“Ba komai ɗazu munyi waya da Addah Asiya ashe dai batun Aurenta ya matso har an fara shiri Abba yazo
yace mata wani irin Furnitures take son a shirya mata wai baban Modibbo ne da kanshi zai mata komai
ko?”.

Dariya Hajiya Bunayya tayi kana ta gyara zama tare da cewa.

“Sosai ma kuwa ayanda suka yanke bikinma ai saura wata ɗaya da mako biyu nema za'ace kin san shina
Zakariyya mahaifiyarsa da baban Modibbo uwa ɗaya uba ɗaya suke”.

Cikin sanyi da lumshe Idanu Amina tace.

“Allah yasa muna raye zuwa lokacin”.

Kai ta gyaɗa Tare Da cewa.

“In sha Allahu ma muna raye yaushe zakizo”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Allah yasa haka in lokacin yayi muna rayen bikin saura mako ɗaya zanzo”.

Ahankali tace.

“Amina naji kamar bacci kike ji bari in barki kiyi bacci”.


Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh sai da safe”.

“Allah ya kaimu ta amsa daga nan suka katse kiran...

*Jauro Yaya*

Acan ɓangaren Hajja Nana adai-dai lokacin suke zaune da Baffa Jimeta wanda tunda ya koma Adamawa
bai zoba sai yau cike da kulawa da kuma girmamawa ya kalli Mahaifiyar tasa da Ƙannenta yace.

“Tunda ga yanda al'amarin Auren khausar ya kasance ga kuma Dija da Aliyu sun haɗa kansu sun fahimci
juna kunga kenan abu yazo da sauki“..

Murmushi Bappa Jauro yayi cikin jin daɗi yace.

“Alhamdulillah nayi farin ciki da wannan al'amarin”.

Cikin jin daɗi da girmamawa Baffa Jimeta ya gyara zamansa tare da cewa.

“Nima naji daɗin haka saboda munyi magana da Alh Bashir Mai Dala cewa tunda Aliyu da Abba duk ya
ɗaukesu aiki a Company sa acan dan haka yana so Aliyu ya Jagoranci Company's sa acan zai koma can
Morocco da zama shiyasa nace In Sha Allah Aliyu bazai tafi Morocco ba sai da Matashi”.

Murmushi Hajja Nana tayi cike da ƙasaita ta gyara zamanta tana kallon ɗan nata Baffa Jimeta kuwa cikin
sauƙe numfashi ya cigaba da cewa.

“Shiyasa nazo akan atsaida batun maganar Aurensa da Dija ya ɗauki matarsa su tafi kunga itama Khausar
ta samu ƴar Uwarta sannan ga Asma'u da take Aminiyarta za tayi Aure su koma can kana ga Asiya da
suka zauna gida ɗaya yanzu ma kafin nazo nan sai da na biya ta wajen Alh Bashir Mai Dala na bashi
mukayi mgnar”.

Cike da gamsuwa Baffa Liman ya jinjina kai tare da cewa.

“Wannan abu yayi munyi farin ciki, abu ya zama tuwonmu Manmu magana yaƙare in Sha Allah nan kusa
kuma za'a yi ɗaurin Aure”.

Baffa sadu dake gefen Hajja Nana ya sauke ajiyar zuciya yace.

“In sha Allah kuwa In yaso Auren mu ajiyeshi nan da wata ɗaya mana”

Ajiyar zuciya Baffa Jimeta ya sauƙe tare da cewa.


“A'a da yake Alh Bashir ɗin yace Modibbo ma zasu zo Auren Asma'u mu bari ya kasance ahaɗa bikin gaba
ɗaya idan an tashi sai atafi da Amaren”.

Cikin gamsuwa Baffa Jauro yace.

“Haka ma yayi Allah ya nuna mana da rai da lafiya”.

Daga nan suka ci-gaba da tsara bikin yanda zai kasance”....

Bayan kwana uku Hajiya Bunayya ce tsugunne a Bathroom ɗin ta yayin da ta cika Bocket da ruwan ɗumi
ahankali ta sanya tsarta ta zaro wannan abu mai kama da ƙwallon aduwa ta ɗaura akan Tissue data ajiye
gefenta ahankali ta sake cusa ya tsanta ta zaro na biyu ta ajiye ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta sake danna
yatsarta da niyyar ciro na uku taji babu sake cusa wa tayi bata jiba akiɗime tare idanunta tare da faɗin.

“Ha'a to ina yake?".

Sai kuma ta sake danna yatsarta akaro na uku da ƙyar taji kansa cikin sauri ta cusa yatsanta da ƙarfi ta
fisgoshi.

Ajiyar zuciya ta sauƙe da karfi ba ƙaramin tsorata tayi ba domin tayi zaton koya ɓace acikinta tana cirowa
kuwa wani irin azabebben ƙaiƙayi na fitar hankali ya game wurin cikin sauri ta shiga kwara ruwan zafi
ahankali taji ƙaikayin ya ragu miƙewa tayi tare da naɗe su acikin Tissue ta fito kana ta shanya a Balcony
inta ƙasan dish ɗin ta yadda ba wanda zai lura dashi komawa ɗaki tayi ta zauna tana sakin ajiyar zuciya
jin har yanzu ƙaiƙayin na damunta.

Bayan kusan kwana biyar ya bushe ƙermes ne ta ɗaukoshi ta daga a turmi ƙarfe tare da haɗawa da garin
maganin kana ta haɗa da yashin tsikayar gidan nasu sannan ta watsashi tsakiyar dare yadda bokan yace
mata a hankali ta turo ƙofar falonta ta shigo cikin jin daɗin ta gama haɗa aikinta tana sauke numfashi ta
zauna bakin gadonta sai kuma tayi saurin miƙe da masifan sauri sabida wani irin masifeffen ƙaiƙayin da
taji takashinta ya fara yi irin kaiƙayin da yayi mata randa ta zaresu da gudu ta nufi bathroom sai kuma ta
kwaye zanenita tare da cusa yatsarta ciki tafara mishi wani irin kwakwasusa.

“Shhhhuuuwwwyyyooo Allah na wayyyyyoohhhh duwawuna ƙaiƙayi-ƙaiƙayi”.

Sai kuma maza ta haɗa ruwan zafi still dai tana yagunan wurin wanda tuni yayi jazir.

Koda ta shiga cikin ruwan zafin kuma sai ta daka tsalle tare da miƙewa tsaye sabida yadda taji wasu
abubuwa suke cin takashin nata wanda sunfi ƙarfin a kirasu da cucuka ko mude.

A wannan ranar dai haka ta kwana a tsaye tana susa har farshen yatsar ya karye sai asuban fari taji
kaiƙayin ya lafa sannan ta samu bacci.
*Morocco*

Yau kwanan Khausar hamsin Cif da tarewarta sashen Moddibo bayan sallar Asbah Khausar ce zaune a
bedroom ɗin Moddibo tun da ita idar da Sallar Asbah bata motsa ba tana kan sallayar yayinda gaba ɗaya
jikinta ke a saluɓe kasalar data zame mata abokin rayuwa a jiya da yau ta tsananta mata wata ƙil hakan
baya rasa nasaba da rashin cin abinci wanda ta kai kwana biyar sai ruwa tea da fruits domin abin ƙaruwa
yakeyi.

Bayan Moddibo ya dawo daga Masallaci kai tsaye bedroom ɗin sa ya wuce ganinta zaune kan sallaya
yasa ya nufeta tare da zama gefenta ya zuba mata ido gaba ɗaya ta rame ta ɗanyi fiyau sai wani irin fari
mai kamar yellow da tayi wanda har jijiyoyin jinin jikinta suka ɗanyi kore kaɗan suka bayyana.

Ganin kamar azkar takeyi ne yasa shina ya janyo Alkur'aninsa dake kan Starm.

Cikin lumshe idanu da nutsuwa yayi A'uziyyah kana ya fara karatu cikin Suratul Ibrahim daga forko.

Yayinda ita kuma taci gaba da yin azkar ɗinta bayan ta gamane ta shafe jikinta da addu'ar kana a hankali
ta ɗan yunƙuro ta matso kusa dashi a dai-dai lokacin kuma yazo aya ta (39)a hankali ya ɗan juyo ya
kalleta tare dasa hannunshi ya kamo nata, cikin sanyayyar muryansa yaci gaba da karantun kamar haka.

_“Alhamdulillaziy wahabli alalkibri Isma'iyla Wa Ishaƙ,Inna rabbi lasami,Uddu',a.”_

Sai kuma ya janyota jikinshi a hankali ya rungumeta,

Ita kuwa Khausar cikin kasala ta daura kanta akan kafaɗarsa hannunta ɗaya na bisa ƙirjinsa idanunta na
kan Alkur'anin tana mai jin zazzaƙan sautin muryarsa.

Shi kuwa Modibbo hannunsa na dama na kan Kur'anin na hagu kuma na rungumeta da ita yana cigaba
da karatun,

A hankali ta kuma manna kanta da ƙirjinsa sai kuwa ta lumshe Idanunta jin yana karanto aya ta(40)
yanda sautin karatun ke ratsa dodon kunnenta yasa itama buɗe bakinta muryarta a sanyaye a hankali ta
fara binshi suna karatun a tare sai dai muryarshi ya ɗanfi nata fita a jere suke karanta harufan ayata 40.

_“Rabbij Alniy Muƙiymassalati wamin zuriyyatie.Rabbana wataƙabbwl du'aaa”_.

Cikin lumshe idanu da sauƙe numfashi ta kuna zamewa ta kwanta kan cinyarsa tana fuskantar qura'an
ɗin sabida duk yadda tayi bata jin daɗin jikinta ga azabar yunwa da kasala ga alamun zazzaɓin da take ji,

Shi kuwa Modibbo still dai yana karatu ya ɗaura hannunsa aƙugunta yana shafawa yana cigaba da
lumshe idanunsa yayinda ita kuwa Khausar tayi lamo a jikinsa, sai kuma ta miƙe zaune tana ɗan
fuskantarsa, cikin sanyi ya ɗaura bayan tafin hannunshi bisa kuncinta na dama yana ɗan shafa har lau
kuma idanunsa na kan qura'an ɗin.

Cikin narkewan jiki ta langwaɓar da kai tare da ƙara matsoshi sosai ganin haka ne, yasashi sa hannun
tare da ɗan tura katakon da Qura'an yake a kai, kana ya jawo ta ya rungumeta tsam a jikinshi da
hannunsa duka biyu a hankali yake ɗan shafa bayanta da hannunsa na dama da yake saman na hagun
alamun yana son ta samu nitsuwane yasa yaci gaba da karatun cikin zazzaƙan muryansa ya ɗauko ayata
(41) kamar haka.

_“Rabbanagfirliyy,Walilwalidiyya Walilmu'uminiyna Yauma Yaƙuumulhisab”_.

Ahankali ta ƙara rungumesa tare da ɗan ɗago kanta ta kalleshi idanu cike da alamun hawaye sai kuma ta
sauƙe numfashi mai zafi, wanda yake sauka acikin kunnensa.

ba tare daya kai ƙarshen Surar ba kasancewar yazo ƙarshen Ayar ya rufe Kur'anin tare da gyara mishi
zama kana ya janyota jikinsa ya rungumeta da kyau yana goga sashen sa afuskarta ya motsa laɓɓansa
tare da cewa.

“Ya dai?”.

Ahankali tayi miƙa tare da lumshe idanunta wani irin kasala da yunwa takeji baki ɗaya jikinta yayi nauyi
ba tada kuzari ko kaɗan zuwa yanzu ta gama fahimtar baki ɗaya yanayinta ya canza ta rasa meyesa meta
cikin sanyi ta girgiza masa kai tare da cewa..

“Ban sani ba”.

Yayin da idanunta suka canza launi saboda yanayin da take ciki.

Sake jawota jikinsa yayi kanaya cusa kansa tsakanin wuyanta muryansa can ƙasa cike da kasala yace.

“Minha yau baki da lfy me yake damunki ne?”.

Kai ta girgiza tare da cewa.

“A'a nima ban sani ba fa?”.

Cikin rauni, kulawa, tausayi, gami da jinƙai da damuwar yadda yaga yauɗin gaba ɗaya ta sake yace.

“Minha Vidaa yunwa cefa take son lahanta min ke”.

Bai jira jin abinda zata ce ba ya mike tare da ɗaukarta cak a jikinsa, batayi musu ba, sabida bata da ƙarfi a
hankali ta lumshe udanunta ganin side ɗin Didi ya nufa da ita.

Da sauri Didi dake tsaye a dinning area ta zuba mishi ido cike da tsoron da yasa jikinta mutuwa tace.

“Aliyu lafiya kuwa”.


Ta ƙare maganar tana nufi tsakiyar falon ganin ya kwantar da ita bisa kujera murya cike da damuwa
yace.

"Didi yau kusan kwana biyar bataci abinciba yau kuma kinga duk ta sake na rasa meke damunta Didi”.

Ya ƙare maganar yana zama gefenta, ita kuwa Didi da sauri ta koma dinning ta haɗa tea mai zafi kana ta
dawo,

Cup ɗin ta miƙa shi tare da cewa.

“Gashi bata”. Da sauri ya tallabota ya zaunar da ita tare da amsar cup ɗin yasa mata a baki, ba musu ta
kafa kanta ta fara sha saida ta shanye a janye cup ɗin dai-dai lokacin kuma Innayi ta shigo da sauri ta
ƙaraso gabanta kusan a tare suke mata sannu ganin wani irin zufa daya keyi mata.

Ita kuwa Khausar cikin wani irin gigitaccen yunƙurin amai daya taso nata, ta damƙi hannun Modibbo tare
da niyar miƙewa wanda tuni ta fara kakari da sauri Didi ta maida ita zaune, shi kuma ya tallabota.

Aiko nan take ta fara zuga.....

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

63

Tallah! Tallah! Tallah!

Shahararriyar Marubuciyar nan mai suna IBNATU-UMAR data rubuta ALAƘA, FANSA, RUHI BIYU ZUCIYA
ƊAYA, GAGGARARU yanzu ta kawo maku littafi mai suna HANTA DA JINI, free book ne bata sai kin biya
koh sisi ba, littafine dake kunshe abubuwa da dama cin amana, domestic abuse da wasu matan ke fama
dashi a gidan aure, kiyayya da kuma zazzafar soyayya.

Ku danna link dinnan dan kuyi joining group din https://chat.whatsapp.com/J9OJOK93SFt7inXdfmSa3t


*Masu son Maganin infection da maganin mata, ku marmatso wannan account no in ne naku ta ciki zaku
turo kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP
NUMBER'N na 08069423567. akwai sabbin kaya masu zafi suna nan bisa hanya, ki turo kuɗinki a saki
cikin lissafi. Kayanen mata masu zafi sadidan daga Chadi akwaisu Garukan daka, gumbunan,
Tsumummuka, cida Ciccibi Abodi cida kaza ci da jan nama kwanon ƙasaitacciyar mace biyar sirri, furar
mata, gumbar madara Gumbar kolli mai ƙyallin al'khairi gumbar uku al'khairi, gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, gumbar riɗi, garin maɗi garin melɗamhi garin ilanwaddihi garin mallaka, tsumin riɗi tsumin
tsirtai tsumin kinfi budurwa, tsumin riɗi, tsumin ta baje Sabaya, matsin maliƙi mai masifar matse mace
matsin daɗi har maɗiga, mai ɗan kare kyau. Kullacar sirri al'ajabu shu'umar Humra, da duk sauran kan
ƙamshi. Haɗin amarya budurwa ko bazawara haɗin mai jego ko uwar gida, akwaisu Available set ɗinmu
hawa hawane akwai manya akwai ƙananan, ƙanan daga 40k ne 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙarami
haɗina na karshe sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar shi 7k ne shine ƙarshen haɗina kenan... Manyan
set ɗin kuma daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k ke zaki faɗi haɗin nawa kikeso anyi miki kana kimin bayanin
yadda kikeso da matsalarki ni kuwa nasan abinda zan haɗa miki, ina araha kam amman ina hana bashi*

Amai kamar ba gobe, wasa wasa dai amai yaƙi tsaya, ganin hakane gaba ɗaya Modibbo ya birkice kawai
sai ya rungumeta a jikinshi tanata kakarin wanda ba abinda take hararwa sai miyau da ɗan ruwa kaɗan
sabida ba abinda taci shiyasa gaba ɗaya ta galabaita.

Cikin sauri Didi ta shiga ɗakinta alƙyabbata ta sako kana ta dawo tare da cewa maza.

“Maza ɗauketa mu tafi asibiti”.

Cikin ruwan jiki ya ɗauketa suka fito harabar side din Didi suna fita hadimai na buɗe musu mita Didi da
Innayi mota ɗaya suka shiga shi kuma mota ɗaya da Rahama da tazo shigowa ne ta gansu.

Kai tsaye Mouldy hospital suka nufa.

Wanda tuni Didi ta gayawa Abualeey da kanshi ya gayawa Dr Jameel shiyasa tun kafin su isa an shirya
komai.

Suna isa aka amsheta tare da bata taimakon gaggawa wani ɗan karamin ruwa suka ɗaura mata da allurai
kana suka nufi ɗakin gwaje-gwaje da ita.

Wanda duk inda sukayi Modibbo na biye dasu a baya.

Cikin iyawa da ƙorewa Dr Isha ke ɗan jujjuya na'urar dake saman cikin Khausar yayinda Dr Jameel kuwa
yana ɗaya gefen yana haɗa ruwan allura.
Cikin murmushin Dr Isha ta kalli Modibbo fuska cike da jin daɗi tace.

“Alhamadullah Mrs Aliyu Youssef Mouldy nada ciki na tsawon kwanaki arba'in da biyar”.

Ya Salam shine abinda Modibbo yayi ya faɗi a fili da kuma ƙarfi sai kuma ya juya da sauri ya fuskanci
alƙibla yayi sujudushukur, yana ɗagawo kuma ya dawo bakin gadon da sauri ya yasa hannunsa da nufin
zai ɗagota sai kuma ya kalli Dr Jameel da ya riƙe hannunsa tare da cewa.

“Malam barta bakaga bacci tayiba”.

Kawai sai sunkuyo kanta bisa goshinta ya sakar mata amintaccen kiss sai kuma a kunatu daga nan sai
haɓarta kawai sai ya rinƙa bin duk jikinta da sumbatar dake nuni da tsananin farin cikine ya gigita shi, ita
kuwa Khausar bacci takeyi cike da wahala.

Ganin alamun Modibbo zai takura tane yasa Dr Isha cewa.

“Afwan a barta tai vacci”

Jin hakane yasa ya juya da sauri ya fita.

Yana fitowa ya nufi Didi itama ɗin shi ta nufa, yana isa inda take kawai sai ya rungumeta cikin tsananin
farin ciki jin daɗin mara musaltuwa na yadda labarin yazo mishi a bazata yace.

“Didi Minha vidaa nada ciki Didi ciki nanefa a jikin Khausar Didi ɗa nane a jikinta fa”.

Cikin tsananin jin daɗi Didi da dama ta daɗe da fahimtar cikine da Khausar kanshi ta fara shafawa tana
cewa.

“Kayi sujja ka godewa Allah”.

Da sauri yace.

“Didi nayi”.

Sai kuma ya saki Didi ya kama Innayi da yanzu ta ɗago kanta daga yin sujjadar godiya ga Allah ruggemeta
yayi yana cewa.

“Innayi kinji ko?”.

Kai ta gyaɗa mishi dan da alamu yama rasa me zauce.

Sai kuma ya kamo hannun Rahama dake rawa da juyi da waya a kunneta da alamun Lalla Khadijah take
gaya cikin jin daɗin yace.

“Kinji kin kusa zama Goggo ko”


Sai ta ruggumeshi.

Kan kace kobo Abualeey da Waziri Galadima da Niyna suna sunzo.

Haka dai ranar suka wuni a asibiti wanda ita kam Khausar batama san meke faruwa ba dan bacci ta wuni.

Nigeria

Ana kiran sallan Magrib Hajiya Bunayya dake kwance tayi zumbur ta miƙe tsaye tare da sakin ƙara ta
rugawa a guje ta nufi bathroom sabida wannan azabebben ƙaiƙayin da ta kwana dashi daran jiya da tayi
ya dawo.

Ai kuwa susa takeyi harda hawaye data fito bazata wuce 15 minute ba ƙaiƙayin zai dawo sai kuma ta
koma ciki.

Kafin zuwa lokacin sallan Isha har jini ke zuba sabida masifar

Kaikayawa datake.

Ganin Jini na zuba yasa ta mike azabure,

ruwan dumi ta hada a Baho kana tasa gishiri ta shiga ahankali tafara Jin masifar kaikayin na raguwa
zaman minti goma tayi kana ta fito falon kan 2sitter ta zauna tana Maida numfashi wayarta ta janyo tayi
dealing number Hajiya lami ringing biyu ana uku ta dauka tare da sallama cikin matsanamcin tashin
hankali gami da tsoro Hajiya Bunayya tace.

“Hajiya Lami nifa nashiga cikin Masifa ƙaiƙayine yake addabata na faɗa Miki jiya kwana nayi banyi bacci
ba da asuban farine na samu sauƙi yanzu gashi Maghiba nayi ƙaiƙayi ya dawo”.

Zazzafan Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauƙe tana gyara zama ta girgiza Kai tare da cewa.

“Ke dai bari Hajiya Bunayya nima Ina cikin tashin hankali tunda muka dawo yarinyar Nan ta fara Shan
magani wannan abu guda² suka fara fitowa kamar masu Rai”.

Aruɗe Hajiya Bunayya ta dafe ƙirjinta da hannunta na hagu sai Kuma ta ɗago ta yarfe tare da faɗin.

“Yau mun shiga Uku wannan wace irin masiface ta tun kuramo?”.

Zazzafan Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauƙe kana tace.

“Hmmmm ni nama rasa kalar tunanin da zanyi Baki ɗaya hankali na atashe yake”.

Haka dai suka cigaba da tattaunawa.


Morocco Acan ɓangaren Khausar kuwa bayan an idar da sallar Isha'i Moddino ne da Dr Jameel cikin
sauƙe numfashi Dr Jameel yace.

“Ruwanta ya ƙare yanzu zan sallameku ku koma gida sannan zan haɗa maka magungunanta”.

Numfashi Moddibo ya fesar tare da cewa.

“Toh shikenan Babu laifi”.

Sai Kuma ya juya Inda su Didi ke zaune Ganin Basu nan yasa ya Maida kallonsa Kan Dr Jameel yace.

“Ina su Didi?”.

Ɗan gyara tsayuwa Dr Jameel yace.

“Ni nace su tafi tunda zan sallameku”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Ok”.

Ya Ida maganar tare da tura ƙofan ɗakin da take kwance yana shiga Idanunsa suka sauƙa akanta tana
zaune kan sallaya bisa alamu ta idar da Sallah Dr Ishaa na gefenta sai Kuma Rahama yayin da Dr Ishaa ke
riƙe da Plate ɗin Indomie Wanda yaji yajii Dr Ishaa na miƙa mata kanta ta kawar gefe alamar bata so.

Kallonsa Rahama tayi kana tace.

“Yah Aleey kaga yanzu abinci kusan kala huɗu muka kawo mata Kuma duka taƙi taci”.

Ta ƙare maganar suna miƙewa ita da Dr Isha ɗin suka nufi ƙofar fita.

Shi kuwa Modibbo

Zama yayi gefenta tare da rungumeta aƙirjinsa sai Kuma ya manna Kansa a wuyanta yana shaƙan
ƙamshin wajen yayin da ya Sanya hannunsa na dama yana shafa cikinta cikin wata sanyayyar murya Mai
cike da aminci, tausayi jin ƙai gami da shaƙuwa yace.

“Minhaa cikin nan yana wahalar min dake sosai, nayi alƙawarin duk randa yazo duniya saina sumbacesa
kana na Sanya mishi Albarka sannan nayi mishi adduar shiriya saboda wahalar min dake da yake yi”.

Jin haka ne yasa Dr Ishaa da Rahama saurin fita.

Bayan sun fita ta ɗaga kanta ta kallesa cikin wata kasalalliyar murya Mai sanyi tace.

“Waye ɗin Kuma?”.


Amintaccen murmushi ya sakar mata Wanda ya fito daga ainhin ƙoƙon zuciyarsa still Kuma hannunsa na
cikinta yana shafawa yace.

“Minhaa kina da ciki fa”

Fuskanta ɗauke da mamaki ta kallesa sai Kuma ta lumshe Idanunta cikin kasalar daya game jikinta tace.

“Ciki Kuma?,Dama Ina da ciki ai”.

Ɗan shafa cikin yayi sai Kuma ya sassauta murya cike da matsanancin farin yace.

“Ba irin wannan cikin ba,Ciki na Haihufa”.

Cikin mamaki ta buɗe Idanunta dake lumshe ta kallesa giransa ɗaya ya ɗaga mata da faɗin.

“Wallahi dagaske”.

Cikin wani irin yanayi ta faɗa jikinsa hannunsa duka biyu yasa ya rungumeta itama hannunta tasa ta
rungumesa tana Jin wani irin yanayi na tsananin farin ciki sai Kuma ta ɗaura hannunta asaman cikinta
tana shafa muryanta ɗauke da farin ciki tace.

“Yah Mu'allim da gaske?”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Eh Wallahi da gaske”.

Ahankali ta Kuma ɗago Kai ta kallesa cikin sanyi tace.

“Allah yasa mu samu Mai kama da Ramadan idan ya girma sai mu bawa Momyna shi ya maye mata
gurbin Ramadan”.

Sake rungumeta yayi ajikinsa tare da faɗin.

“Allah ya sauƙeki lafiya Allah ya ingantashi ya masa Albarka Amma Khausar bazan iya bada gudan
jininmu ba kiyi haƙuri ba zan iya ba.

Ya karashe maganar cikin tabbatarwa da Kuma gaskiya da gaskiya ahankali tace.

“Baza ka iya ba?”.

Kai ya gyaɗa yana shafa cikinta ya fesar da numfashi tare da faɗin.

“Bazan iya ba,bazan iya ba kiyi haƙuri ban Miki alƙwariba kada ma in Miki ƙarya”.

Ɗan ware Idanunta dake lumshe kamar na Mai jin bacci tayi sai Kuma tace.

“Ido da ido?”.
Ɗan murmushi yayi Jin yanda tayi maganar cikin shaƙan ƙamshin ta yace.

“Um kada in Miki ƙarya ne”.

Tana sake shiga jikinsa ta ɗan cunno Baki tare da cewa.

“Ni Kuma Ina so idan na samu Mai kama da Ramadan in bawa Momy ya maye mata gurbinshi shiyasa
naji daɗi”.

Cikin fahimtar har yanzu rashin Ramadan na ranta yasa yace.

“Toh shikenan in kin dage kin Haifa mana Dozen Mai yuwa in bawa Momy ɗaya”.

Zare Idanunta tayi tare da faɗin.

“Har Dozen?”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Eh mana”.

Cikin sauƙe numfashi tace.

“Wannan ɗayan ma ga yanda nake ji”.

Cikin Jin taisayinta ya tallafe fuskarta kana ya motsa laɓɓansa tare da faɗin.

“In Sha Allahu zanyi Miki addu'a Kuma Ubangiji zai kawo Miki da sauƙi ”.

Sai Kuma ya tallafo ta tare da miƙar da ita yace.

“Tashi mu tafi sai mu biya restaurant idan akwai abinda kike so in siya miki”.

Kai ta girgiza cikin sanyi da game mata jiki tace.

“Nikam ma banajin yunwa cikina aƙoshe yake”.

Dai-dai lokacin Dr Jameel ya shigo Idanunsa akan Moddibo yace.

“Eh ko bata ci abinci ba bazata damu ba saboda ƙarin ruwan da aka mata zai taimaka.

Kuma in Sha Allahu duk bayan makonni zanke ɗan ƙara mata ruwa tunda dai bata samun cin abinci”.

Ya Ida maganar tare da miƙa masa ledan Magungunan kana ya ɗaura da cewa.

“Rahama tana jiraku amota”.

Ahankali Moddibo ya tsugunna ya tallafo ta kamar Baby muryanta cike da sanyi tace.

“Yah Mu'allim kabarni zan iya tafiya naji ɗan sauƙi fa”.
Kai ya girgiza tare da cewa.

“Um-um fa bana so”.

Ya faɗa yana gyara mata zama ajikinsa.

Baki sake Dr Jameel ke kallonsa tare da faɗin.

“Ikon Allah”.

Harara Moddibo ya watsa masa kana yace

“Ɗan sa ido”.

Murmushi Dr Jameel yayi tare da bin bayan sa suna Isa jikin Motar Dr Jameel ya buɗe masa gidan baya
yasata kana Shima ya shiga Rahama na ɗaya gefen ya zama sun sata tsakiya kana Driver yaja.

Suna ƙoƙorin fita cikin asibitin Moddibo yayi saurin Kallon Driver tare da cewa.

“Kai ya kake gudu irin haka da ƙarfi?”.

Cike da girmamawa Driver yayi ƙasa da Kansa tare da faɗin.

“Kayi haƙuri”.

Kai Moddibo ya girgiza Idanunsa akan Khausar Dake lumshe Ido yace.

“Um-um bani baza ka iya ba”.

Murmushi kawai Rahama tayi al'amarin Yah Aleey da Khausar na masifar burgeta.

Kai Drive ya gyaɗa tare da fita Moddibo kuwa mazaunin driver ya koma har ya shiga sai Kuma ya fito
yana Kallon Khausar ya miƙa mata hannu kana yace.

“Fito ki koma gaba”.

Kai ta gyaɗa, tare da miƙa mishi hannun a gefensa ya ajiye ta.

Yana ƙoƙorin saita Motar kan kwalta ya janyo Khausar ya ɗaura kanta kan kafaɗarsa ahankali yake
driving tafiyar da zasuyi cikin minti talatin Saida suka dauki awa ɗaya da ƴan mintuna sunayi.

Sunzo dai-dai wani restaurant ya fara ƙoƙorin parking yana cewa.

“Mushiga in siya Miki duk abinda kike so?”.

Idanunta ta buɗe ta kallesa sai Kuma ta girgiza Kai tace.


“Ni Babu abinda nake so kawai mu koma gida inyi wanka in samu in huta”.

Rahama kuwa tana gyara zamanta ta Kalli Khausar da duk jikinta Babu kuzari tace.

“Lalla Khausar idan akwai abinda kike so ki faɗa min ko meye idan munje gida zan dafa miki”.

Kai ta girgizawa Rahama tare da cewa.

“Ayyah Rahama ni Babu ma abinda nake so bana Jin yunwa”.

Moddibo kam ahankali yaci gaba da driving har suka Isa gida yana parking ya fito ya ɗauketa Kai tsaye ya
side ɗin Didi ya wuce da ita.

Didi na ganinta ta sauƙe Ajiyar zuciya tare da cewa.

“Sannun ku da zuwa

Ɗiyata ya jikin?”.

Murmushi Khausar tayi ahankali tace.

“Da sauƙi".

Sai Kuma ta juya dinning abinci kala-kala ta ɗebo ta jere mata agabanta tace.

“Toh Maza sauƙo kici”.

Langwaɓar da Kai tayi muryanta asanyaye tace.

“Ayyah Didi na ƙoshi fa bana Jin yunwa”.

Da damuwa Didi ta kalleta tare da faɗin.

“Wannan al'amari yana damuna Khausar am duk laulayi laulayine Amma Wallahi laulayin dake hana cin
abinci yafi jikkatarwa da wahalar wa”.

Cikin sauƙe numfashi da tarin tausayinta Moddibo ya fesar da numfashi Idanunsa akan Khausar yace.

“Yanzu Didi Babu abinda za taci Kenan?”.

Kai Didi ta girgiza tace.

“In dai jininka ya ɗauka zaiyi wuya, taci abinci sai dai Ina tunanin in Sha Allahu akwai abinda zan dafa
mata zata ci Dan haka nayita fama lokacin da cikin ka”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da cewa.

“Toh Didi menene?”.

Tana ƙoƙarin miƙewa tace.


“Toh ba matsala bari in shiga kitchen”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Toh kafin ki gama bari tayi wanka”.

Kai ta gyaɗa tare da shiga kitchen shi Kuma ya ɗauketa ya haura samansu wanka tayi da ruwan ɗumi
kasancewar lokacin har goma yayi kafin ta fito.

Ya fito mata da kayan bacci masu masifar taushi Pink color da ratsin farin da Kansa yasa ka mata kana ya
cusa mata gashin kanta a hular net ruwan da aka ƙara mata yasa jikinta ya ɗanyi ƙarfi sai dai fuskarta tayi
fayau alamar rama sai dai Kuma ta sake haske sosai yana gyara mata gashinta cikin hular yaji ana
knowking ajiyeta yayi bakin gadon kana ya tafi ya buɗe ƙofan Didi da kanta ya gani tsaye iso ya mata
suka shiga falon tana kallonsa tace.

“Ina Khausar ɗin”.

Yana ƙoƙarin karban warmer dake hannunta yace.

“Tana ciki”.

Kai ta gyaɗa tare da bin bayan sa suka shiga bedroom ɗin stool ta janyo ta zauna tare da faɗin.

“Sannu Khausar”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Yawwa na warkefa”.

Didi kuwa Warmer ta buɗe Dambun Shimkafa da yaji zogale da gyaɗa kana yaji Vegetables sosai sai
tashin ƙamshi yake.

Khausar na gani taji yawunta ya tsinke Didi na kallonta tace.

“Zaki ci ko?”.

Kai ta gyaɗa murmushi Didi tayi Khausar kuwa ahankali ta ɗan gyara zamanta tare da faɗin.

“Didi asamin kadan”.

Kai ta gyaɗa kana ta zuba mata da ɗan yawa ahankali Khausar ta karba ta faraci murmushi Didi tayi tana
kallon Moddibo tace.

“In Sha Allahu Zata ci da yawa”.

Murmushi tayi tare da ci gaba da cin dambun Alhamdulillah kuma taci kusan cokali tara kana a hankali ta

ta miƙawa Didi plate ɗin tare da faɗin.


“Na ƙoshi”.

Didi na Kallon Plate ɗin tace.

“Kin ƙoshi Kuma?”.

Moddibo kuwa ahankali ya kalleta tare da sassauta murya yace.

“Ki ƙara mana”.

Kai Didi ta girgiza kana tace.

“A'a barta tunda taci wanna an samu ya zauna acikinta ya Isa kaima haka nayi ta fama da Kai”.

Cike da rauni ya kalleta yana Jin ƙaunarta Aransa yace

“Oh Didi Kiya femin haka nayita wahalar dake”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Na yafe maka tuntuni Babana.

Kai ma bari na Saka maka kaci”.

Bata Jira cewarsa ba ta ƙara masa akan plate ɗin Khausar anutse ya karba ya fara ci ba laifi yaci da yawa
Dan sosai ya masa daɗi bayan ya gama Didi tayi musu sallama kana ta ta dauki warmer da kanta ta tafi
dasu.

Bayan ta tafi Moddibo ya Mike tare da komawa gefen Khausar ya zauna ya jawota jikinsa ya
rungumeta....

*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n
nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai
sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan
mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in
kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a
banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account
no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na
faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki
kenan*
Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito
miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar
infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita
tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a
saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda
yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin
san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo
kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567 sai ki turo min shaidar biyanki,
domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan
ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah
zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce
dai GARKUWAR MA'AURATA.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*
SAKAYYAH

64

*SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!*

*PART OF OUR DESTINY*

*Shin ko kunsan shahararriyar marubuciyar nan me suna *FATYMASARDAUNA* marubuciyar


*SHU’UMIN NAMIJI* *SOORAJ* *LAYLERH MALEEK* *MAJNOON* ta sake kawo muku sabo kuma
dadd’an littafinta dake cike da tarin zazzafar soyayya me gigita hankali, sadaukarwa, k’addara, da kuma
hamshakiyar Kaunar dake gudana acikin jinin jikin mazaje guda biyu da suka kasance y’an uwan juna,
duk acikin littafin nata me suna *PART OF OUR DESTINY* kada ku sake abaku labari domin samun
karantawa da kuma shiga cikin group din marubuciyar zaku biya 500 ne kacal ta wannan account
number din 2268498748 Fatima Abubakar UBA bank, ko ku tuntub’eta ta WhatsApp number dinta
kamar haka 07069917168.

Kada ku Bari abaku labarin wannan littafi me suna *PART OF OUR DESTINY* littafine dake cike da tarin
zazzafar soyayya....

64

Ahankali ya kwantar da ita kan cikinsa, tare da yi mata pillow da ƙirjinsa, sai kuma ya jawo blanket ya
ɗan rufe su. ahankali ya haɗa tafin hannunsa waje ɗaya tare da karanta addu'oin bacci _Falaƙi, 3 Nasi 3,
Ƙulhuwa 3, Ayatulkursiyyu, 1 kana ya haɗa da Amanarrasulu1 Laƙadja'akum_ yanayi yana hura hucin
numfashi nai cikin tafukan hannunsa.

Cikin kulawa ya shafa mata kana.

Yayi kansa shima ya shafa ajikinsa yana mai lumshe Idanunsa, hakanan yake jin wani irin farin ciki wanda
tunda yake a iya tsawon rayuwarsa bai taɓa riskan labarin da yasa shi farin ciki da jin daɗi ba kamar
wannan labarin ba, ko labarin kasancewar su Didi iyayensa baisa shi farin ciki kamar wannan labarin cikin
nasa ba, ya rasa ya aka yi labarin ya kasance masa baƙon lamari abin yazo masa abazata, sabodaai kawo
hakan a ransa da sauriba, shi ganima yake ai Khausar ɗin ƙaramace.

Haka ya kwana cikin tsananin jin daɗi da farin ciki kusan a zaune ya kwana da zaran ta motsa zai gyara
mata kwanciya.

A gefen Hajiya Bunayya ma ita ma haka ta kwana da azabebben ƙaiƙayin dake addabar rayuwarta
Rayuwa tayi mata ƙunci haka ta kwana ƙaiƙayi ya hanata kataɓus.

Ana kiran Sallar Asbah ta fara sauƙe numfashi saboda jin ya fara lafawa, kamar abin Jaraba ƙaiƙayin ya
daina wunin ranan haka tayi tana rama bacci da bata samu ta yi shi a daran ba.

Ana kiran Sallar Maghriba ƙaiƙayin na Assalamu alaikum yana sake dawowa haka wannan ranan ma haja
ta kwana ƙaiƙayi, gaba ɗaya ta rasa inda zata sa kanta jin ƙaiƙayin ya gallaza mata yasa ta haɗa ruwan
zafi da gishiri ta cika Baho da ruwan ɗumi da gishiri ta shiga cikin.

Numfashi wahala ta fara sauƙewa jin abin ya fara lafawa,

Sai kuma tayi saurin sunkuyar da kanta jin yadda wasu abubuwa caccakarya a wurin.

Ido ya kuma fiddawa sosai saboda ganin wasu ƙananan tsutsotsi masu baƙin baki suna fita ta gabanta
asaman ruwa bisa alamu sune suke sa mata ƙaiƙayin kuma suke hanata bacci.

Shiyasa idan ta shiga ruwan zafi sai take jin sauƙi idan ta fita kuwa ko awa ɗaya bazai kai ba zai da meta..

Haka dai take fama da wannan rayuwar da zaran dare yayi tayi sallama da kwanciyar hankali da bacci sai
kuma safiya.

Haka ta rayu tsawon Makonni biyar tana fama da wannan azabebben ƙaiƙayin da bai nuna alamun akwai
sauƙi ko sassauci ba.

A gefen Samira Sani ma ita baki ɗaya rayuwa ta sake yi mata ƙunci da duhu abin ba a cewa komai.
Morocco Acan gefen su Khausar kuwa rayuwa tayi daɗi Khausar na samun kulawa na musamman daga
gefen uwar mijinta da kuma Kakar Mijinta Niyna kana da Innayi.

Hadimanta nayi mata komai daya kama na rayuwa har zuwa yanzu bata iya wani cin abinci amma ko
yaushe cikin Hidima suke mata haka Didi nayi mata komai na sungullan rayuwa takowa mata wannan ta
kawo mata wancan, amma bata iya cin komai yau tsawon kwana goma shabiyar da jin labarin Khausar
nada ciki, wanda haka yayi dai-da cika wata biyu kenan da cikin yayi.

Kwance take akan 3sitter yayinda tayi pillow da cinyarsa.

Cikin sanyi ya shafa kumatunta tare da juyiwa ya kalli plate ɗin abincinta kwata-kwata ko cakali shida
mai kyau bata yiba.

Cikin takaicin rashin cin abinci ya shafa cikinta dake lafe kamar bata da komai cike da damuwa yace.

“Minha”.

A hankali ta ɗan ɗago kanta ta kalleshi jin yadda ya kirata da alamun damu cikin kula yace.

“Rashun cin abinci kinnan yana damuna,

ina ga zan kira Momy in faɗa mata matsalar rashin cin abinci nan koda shawarar da zata bamu”.

Ware manyan Idanunta dake lumshe kamar na mejin bacci tayi tare da cewa.

“Momy kuma?”.

Kai ya jinjina mata, cikin sauri tace.

“Bana ce maka mubar maganar faɗa wa Momy nan ba”.

Yana shafa gashinta yace.

“Gsky ni dai inaga gwara mu gaya mata wata ƙil kiga mun samu mafita?”.

Kai ta girgiza tare da cunno bakinta gaba tace.

“Kenan me zaka ce mata?”.

Kallonta yayi tare da tallafo kanta ya juyo da ita suna fuskantar juna cikin sassauta murya yace.

“Ce mata sanyu Minha bata cin abinci ni kuma rashin cin na damuna”.

Lumshe Idanunta tayi tare da buɗe su akansa cikin yanayin irin mata masu fama da laulayi tace.

“ Idan tace maka me ya hanani cin abinci ke zaka ce mata?”.


Matsota yayi sosai kana yace.

“Ce mata zanyi kina da cikine kuma yana hana ki cin abinci?”.

Zare idanu tayi kamar wacce tayi wani laifi sai kuma ta kife kanta akan ƙirjinsa.

Lallausan murmushi ya saki kasancewar tun washe garin ranan da akace tana da ciki yace zai faɗa wa
Momy amma fir taƙi yarda wai tana kunya, sosai ta sake mannuwa ajikinsa kana ta manna kanta da
faffaɗan ƙirjinsa cike da kasala tace.

“Nikam Yah Mu'allim Ina kunya taya zaka faɗawa Momy wannan magana Taya zaka faɗa wa Momy cewa
ina da ciki Fisabilillahi yanzu sai ka iya faɗa?”.

Murmushi yayi tare da cewa.

”Toh mene cikin nan fa halartacce ne, cikine mai gata mai daraja gashi da mahaifinsa na rasa kunyar me
kikeji?”.

Kallonsa tayi da mamaki sai kuma ta langwaɓar da kai tace.

“Yanzu Yah Mu'allim baza kaji kunyar cewa Momy ina da ciki ba?”.

Idanunsa ya buɗe tare da karkata mata kai kana yace.

“Toh me aciki?,me abin kunya aciki don kina da ciki?”.

Wani kallo ta masa mai tattare da shauƙi da yanayi na musamman ahankali ta motsa laɓɓanta kamar mai
raɗa tace.

“Yanda aka samu cikin shine abin kunya kowa fa yasan me muka yi”.

Ta ida maganar tana rufe fuskarta janyota jikinsa yayi tare da rungume ta kana yayi murmushi tare da
faɗin.

“Toh shikenan tunda baki so, Sarkin kunya zanga yanda zakiyi kuma idan munje Auren su Dr Jameel ai
zata ga cikin kafin nan”.

Cikin sauri ta girgiza masa kai tare da narke fuska sai kuma ta janyo hannunsa ta ɗaura akan cikinta tace.

“Toh ai cikin baya wani girma".

Yana ƙunshe dariyarsa yace.

“Ai kafin nan zai ƙaru tunda zuwa lokacin ya cika wata uku tunda kinga an ƙara wata biyu a asalin date
ɗin kinga har zai shiga wata na huɗu ma kafin nan”.

Kanta ta ɗan jujjuya sai kuma ta tsirawa sajensa dake ƙyalli Ido tace.

“Ha'a sai dai-dai lokacin Auren yayi zamu tafi ne?”.


Kai ya girgiza tare da cewa.

“A'a sai bikin ya rage saura sati zamu tafi kinga kafin nan cikin ya cika wata uku har ya shiga na huɗu
ma”.

Ganin yanda ta narkar da fuskarta ne yasa ya janyonta jikinsa ya sake rungumeta cikin tura baki tace.

“Nikam gaskiya ina jin kunya wallahi”.

Sosai ta bashi dariya amma baiyi ba yace.

“Uyumm idan kina jin kunya ki riƙa cin abinci”.

Narai-narai tayi da idanu tare da faɗin.

“Yah Mu'allim toh bana jin yunwa kaga kuma yanzu nasha fruit Alhamdulillah na ƙoshi”.

Janyota yayi ya rungumeta daga haka bacci ya ɗauke su.

Acan ɓangaren Amina kuwa yanzu baki ɗaya rayuwa tayi mata ƙunci gani take kamar rayuwarta yazo
gangara.

Cikin sauƙe numfashi ta kalli Uncle Naseer Dake gefenta kana tace.

“Uncle Naseer bani da lafiya”.

Wani kallo ya mata sai kuma tayi murmushi tare da faɗin.

“Ba wani nan lafiyarki ƙalau”.

Cikin sanyi da kasala daya gama baibaye rayuwarta ta fesar da numfashi kana tace.

“Allah da gaske bani da lafiya Ni nasan yanda nake ji ajikina”.

Yana ɗan latsa wayarsa yace.

“Kada ki damu”.

Araunane tace.

“Ji nake kamar zan mutu”.

A wannan karon ma murmushi yayi yana gyara zamansa yace.

“Baza ki mutu ba yarinya ki kwantar da hankalinki”.

Kanta ta jinginar da jikin kushin tare da cewa.


“Uncle Naseer to yaushe zamu tafi gida naga Auren Addah Asiya ya matso du-du-du saura wata ɗaya da
sati ɗaya”.

Juyawa yayi ya kalleta sai kuma ya ɗaga kansa sama alamar tunani yana sauke kansa ƙasa yace.

“Auren saura sati ɗaya zamu tafi kinga yanzu kenan saura 1month zamu tafi”.

Cikin sanyi ta gyaɗa kai tare da faɗin.

“Shikenan Toh Allah ya kaimu”.

Kafin yace wani abu wayarsa ta hau ruri ahankali ya miƙe ya fita tare da picking call ɗin.

Daga ɗaya bangaren akace.

“Ranka yadaɗe nan Veazer ka na komawa India zai fita”.

Cike da farin Yace.

“Alhamdulillah Nagode bari zuwa anjima zan kiraka”.

Kana ya katse wayar tare da komawa Falon ya zauna gefen Amina ahankali ta ɗago Idanunta ta kallesa
tare da cewa.

“Uncle Naseer ya batun tafiyarmu Indi'a ne?”.

Still da murmushi afuskarsa yace.

“Sai mun dawo bikin Asiya”.

Cikin sanyi tace.

“Toh Allah ya kaimu”.

Acan gefen Hajiya Bunayya kuwa rayuwa tayi mata tsanani abubuwan ta kullum gaba-gaba yake da safe
zuwa rana zata yini cikin kwanciyar hankali sai dai da dare yana yi bata da kwanciyar hankali zuwa yanzu
ƙyanƙyamin kanta da kanta ta keyi.

Cikin sauƙe numfashi ta kalli Hajiya Lami Idanunta cike da ruwan hawaye tace.

“Na lura ko ɗana Sulaiman ƙyamar zama kusa dani yake yi sannan Lamiɗo koda abinci na kai masa sai
yace in tattara in fita dashi shi ya ƙoshi.
Hankalina ya tashi Hajiya Lami kaddai mugun abinda naje yiwa Khausar ya dawo kaina ya addabi
rayuwata?

Ji nake kamar ƙaiƙayin yasa gabana ya haɗe da bayana”.

Zare idanu Hajiya Lami tayi cikin yanayin tashin hankali tace.

“Mun shiga ukun mu Hajiya Bunayya wannan wani irin abu muke fuskanta a rayuwar ki kalli haka Samira
fa yanzu yanda ta bushe ta rame duk ta lalace sannan nima bana bacci dana kwanta da daddare sai
muggan mafarkai na rasa yanda zanyi da rayuwarta”

Cike da damuwa Hajiya Bunayya ta girgiza kai tare da cewa.

“Ke koni?,Auren Asiya sai matsowa yake gashi Lamiɗo ko zama kusa dani muyi maganar Auren nan baya
yarda sai kyara da hantara ina ga baƙin jinin da Boka yace Khausar za tayi ya tabbata nice nayi shi”.

Cikin mamaki Hajiya Lami ta tallafe kuncin ta tana sauraron masifar daya riskesu lokacin ɗaya duniya tayi
musu atishawar kaji.

Hajiya Bunayya kuwa da damuwa ta cigaba da cewa.

“Ƴaƴana ma duk sun fita harƙana dama Asiya ita tun can ba shiga harƙana take ba.

Kuma abin mamaki itace take ɗan daurewa tana zama kusa dani shekaran juya da taga ina ta fama da
ƙaiƙayin nan ina zirya da sintiri shine ta faɗa wa Lamiɗo aje asibiti koda ta faɗa masa ma cewa yayi shi
bazai samu damar kaina ba inje in Kai kaina idan na kuɗine in faɗa masa ko nawa ne magana ta ƙare”.

Tallafe kunci Hajiya Lami tayi kana tace.

“Ohhh Mukam munga ta kanmu wannan al'amari wacce irin Musifa da fitinace ta Kunno mana kai”.

Kafin Hajiya Bunayya tace wani abu Asiya ta fito daga cikin Bedroom ɗin ta kana ta zauna gefen su tare
da girgiza kanta sai kuma ta kallesu ahankali ta sunkuyar da kanta Idanunta na cika da ruwan hawaye
murya cike da rauni tace.

“Umma ku koma ga Allah ku nemi gafarar waɗanda kuka cutar sai kuga Allah ya kawo muku sauƙi
wannan ishara ne Ubangiji yai muku Allah ya soku da Rahma ne daya kama ku tunda ranku baku mutu
ba dan haka kunemi yafiyar wa'anda kuka cutar tun kafin lokaci ya ƙure muku”.

Kallonta suke tunda ta fara magana har ta dasa aya basu katse taba kamar yadda suka sqba.

Karo na farko a rayuwar su da suka ji jikinsu ya mutu akan abinda suke aikatawa kana kalaman ta ya
ratsa su.

Ganin yanda jikinsu yayi sanyi alamar nadama tare dasu yasa cike da girmamawa matsayinsu na iyaye
taci gaba dayi musu nasiyya mai ratsa jiki kana ta nuna musu kuskuren su da basu shawarar su nemi
gafarar waɗanda suka cutar kana su nemi yafiyar Allah da yardarsa...
Morocco bangaren Khausar sosai al'amura ke tafiya yau ya kama Auren Asma'u da Dr Jameel saura mako
biyu haka Auren Asiya da Zakariyya da kuma Yah Aliyu da Dija saura mako biyu Cif-cif sukuma a shirye-
shiryen su saura Mako ɗaya su tafi Nigeria.

Ahankali ta ɗaga kanta tare da zubawa ƙofar falonta Ido jin sanyayyan kamshin turaren Moddibo wanda
da alama ya dade da dawowa harma ya shiga side ɗin sa yayi wanka kai tsaye gefenta ya nufa ya ya
kwanta kana ya ɗaura kansa kan cinyarta kasancewar tana kan 3sitter sai kuma yasa hannunsa ya shafa
cikinta kafin ahankali ya maida hannunsa kan cikinta yace.

“Baby ya kake kana lafiya?”.

Murmushi Khausar tayi amma bata ce komai ba.

Sake manna kansa da cikin yayi tare da cewa.

“Meimei ta baka abinci Kaci?”.

Still shiru tayi sai kuma ya ɗago ya kalleta tare da cewa.

“Kinci abinci ko?”.

Kai ta gyaɗa masa tare da faɗin.

“Eh wallahi da gaske naci”.

Cikin tsira mata idanu yace.

“Da gaske?,Me kika ci?”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Nayi wainar Fulawa kuma naci guda uku”.

Kai ya jinjina tare da faɗin.

“Masha Allah Alhamdulillah haka yayi kyau ai naga cikin ya ɗan tashi”.

A hankali ta ɗan ɗaura hannunta bisa sajenshi tana shafawa a hankali tace.

“Yau ina ka tafi tunda safe baka dawo ba”.

Saman hannunta ya shafa tare da cewa.


“Mun fita ne da Dr Jameel da Zakariyya kinsa ya dawo tun shekaran jiya sunje sun nuna min gidansu an
tsara musu komai masha Allah.

Dan su bikin saura kwana goma ma zasuyi gaba”.

Cikin sauri ta kallesa sai kuma ta langwaɓar da kai tace.

”Toh muma mu tafi dasu mana Yah Mu'allim”.

Kai ya girgiza tare da faɗin.

”Tafiyarsu da ban tamu da ban”.

Sake marairaice murya tayi tace.

“Allah mu tafi dasu na ƙagu naga Raudat nayi kewar Momyna sosai”.

Cikin kwantar mata da hankali yace.

“In sha Allah zakije ki ganta”.

Kallonsa tayi sai kuma ta make kafaɗa tace.

“Ni dai wallahi da zamu tafi tare nafi so".

Yana gyara kwanciyarsa yace.

“Suɗin ma ina ga zance su haƙura kawai mu tafi tare, tunda saura sati ɗaya zamu je gwara su haƙura mu
tafi”.

Cikin sauƙe ajiyar zuciya tace.

“Toh Allah yasa su haƙura mu tafi".

“Ameen”.

Sai kuma yayi saurin miƙewa daga jikinta jin wayarsa na ruri ɗagawa yayi ta kalli screen ɗin, sunan
Sheikh Jabeer ya bayyana da murmushi afuskarsa ya dauka tare da cewa.

“Kaka”.

Daga ɗaya bangaren Sheikh Jabeer dake zaune cikin falonsa A'ish ɗin sa na zaune gefe ya saki murmushi
tare da cewa.

“Na'am Jikalle Barka da yamma”.

Moddibo na gyarawa Khausar zama ajikinsa yace.

“Barka dai ya gida?".


Ahankali Sheykh yace.

“Lafiya lau”.

Ya ƙare mgnar yana gyara zama yace.

“Kwanaki munyi magana da kai akan ɓatan Jameel da plate number motar ɗin da muke magana akai?”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da faɗin.

“Hakane”.

Anutse Sheikh Jabeer yace.

“Masha Allah idan ban manta ba cikin mutanenku akwai wacce tasan number motocin da ake zargin
suna yawan binbiyarku gab da ɓacewan Jameel ”.

Kai Moddibo ya jinjina yana mai tuno J dinsa yace.

“Eh Khausar ce ma ”.

Cikin sauƙe ajiyar zuciya Sheikh Jabeer ya gyara zamansa tare da faɗin.

“Toh ba matsala idan har yanzu tana riƙe da number ka turo min saboda akwai ƙungiyar da Tabital Fulani
suka kama a Taraba.

Wanda an kamasu da motoci tawaga guda kusan guda goma wanda gaskiya muke zaton motoci ne da
suke harkan Kidnapping dasu saboda a dokar adaji aka kama su da kuma makamai kana da tarin
kuɗaɗe".

Numfashi Moddibo ya fesar kana yace.

“Toh shikenan In sha Allah bari muyi maganar da ita”.

Bayan ya katse wayar ya maida kallonsa gare ta ahankali ya riƙe hannayenta cikin nasa cikin natsuwa ta
zuba masa ido.

Cikin fesar da numfashi yace.

“Minha batun number motar nan da Asma'u tace kin riƙe,har yanzu kina riƙe dashi akan ki?”.

Kai ta gyaɗa cikin tabbatar tace.

“Tabbas kuwa har abada bazan manta number motar nan ba saboda na ganta alokuta uku maban-banta
na ganshi a Jauro Yaya.

Na ganshi a bakin Makarantar mu.


Sannan ranan da muka yi rabuwa ta ƙarshe da Yah Jameel na ganshi yana bibiyarmu”.

Numfashi ya fesar tare da faɗin.

“Yanzu zaki iya faɗa min?”.

Kai ta gyaɗa mishi.

Ganin hakane yasa ya

ɗauki wayarsa ya danna kan number Sheikh Jabeer ya shiga wajen text yace.

“Gashi sa”.

Karɓa tayi ta rubuta number motar da komai da komai harda collor ta miƙa masa number ya tsirawa
idanu sai kuma ya kalleta yace.

“Kin tabbatar shine dai-dai?”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Na tabbata shine babu shakka ko Haufi ko yanzu na rufe Idanuna ina kallon number motar”.

Kai ya jinjina kana yace.

“Ok ba laifi”.

Ba ɓata lokacin ya yiwa Sheikh Jabeer sending.

Ahankali ya maida hannunsa kan cikin nata wanda zuwa yanzu ya fara bayyana kallonta yayi tare da
langwaɓar da kai yace.

“Minha yunwa nake ji mai zan samu?”.

Tana lunshe Idanunta cikin nasa tace.

“Mekake so?".

Muryansa cike da kasala ya sake narkewa jikinta tare da cewa.

“Me kika yi min?”.

Manyan Idanunta ta juya sai kuma ta sakar masa da murmushi tare da cewa.

“Nayi maka abinda kake so?”.

Ɗan ware idanunsa yayi yana cigaba da shafa cikinta yace.

“Mene?”.
Langwaɓar da kai tayi tace.

“Nayi dambu a tunanina zan iya ci sai kuma naji bazan iya ciba”.

Wani kallo ya mata me cike da tarin tausayi da jin ƙai yace.

“Ke kuma me yake miki daɗi In banda Fakala ba”.

Da sauri ta sanya tafin hannunta ta rufe fuskarta tare da cewa.

“Kai Yah Mu'allim”.

Kai ya jinjina kana yace.

“Ehem sai an jima da daddare zaki ce min kina son pakala”.

Marairaice fuska tayi kana tace.

“Ni dai wallahi kabar faɗa min haka kar kayi min sharri”.

Idanunsa ya buɗe kanta tare da faɗin.

“Sharrine ma?,Toh bari zan kama kine?”.

Murmushi tayi tare da faɗawa jikinsa amma bata ce komai ba.

AnanTaraba shirye-shiryen biki ya kankama tuni aka fara gyara amare an killace su.

Momy da kanta je gyara Asma'u Asiya ita ke mata Dilke sai wani ƙyalli suke sunyi kyau gwanin ban
sha'awa soyayyar ta da Dr Jameel ɗin ta kuwa na tafiya hakama su Asiya.

Yau ya kama Auren saura kwana goma wanda ya rage saura kwana uku Moddibo su taho da Angwaye da
ƴan ɗaurin Aure.

Yau tun safe Ummi da kanta da Asma'u suka tafi gidansu Innayi kasancewar key na hannunta Ummi da
kanta ta shiga Side ɗin Moddibo da kanta ta gyara masa ta killace Asma'u kuwa gefen Innayi ta gyara ta
killace ko ina yayi gonin ban sha'awa.

Ga kuma sabbin part guda biyu da ake ƙenƙesa sabon gini, na alfarma wanda tuni an gama komai nasu,
wanda bisa shawarar inanayi aka tsara da umarnin Abualeey tare jagorancin Abban Jameel abune na
kuɗi shiyasa tuni an gamsu wanda nanne masauƙinsu in sun iso.
Morocco Khausar ce kwance akan kujerar bisa alamu da Momy take waya cike da farin ciki ta gyara
kwanciyarta tare da cewa.

“Momy In sha Allah mun kusa zuwa".

Murmushi Momy tayi kana tace.

“Toh Khausar me kike so in shirya miki idan kin zo.

Ga Raudhat baki ɗaya lissafinta da tunani Adda Khausy ta kusa daeowa.

da an taɓa ta sai tace sai Addah Khausy tazo, wanka ma ƙinyi tayi yau wai sai Addah Khausy tazo tayi
mata”.

Dariya Khausar ta sanya tare da faɗin.

“Yau mun bonu kafin inzo ai datti zai kashe ki Raudat ”.

Ta ƙare faɗin haka jin muryan Raudat ta amshi wayar Raudat kuwa itama cikin dariya tace.

“Addah Khausy datti bazai kashe niba fa zan riƙa fesa turare sannan insa humran Momy saboda nayi
kamshi sai kinzo ki min wanka”.

Dariya suka sanya Dukansu daga nan suka cigaba da hira.

Suna gama waya dasu Momy ga Mamaki ta sai ga kiran Hajja Nana ya shigo tana ɗagawa tace.

“My Kakus”.

Baki Hajja Nana ta taɓe tare da faɗin.

“Ƴar tselen Uwa tunda muka dawo sau ɗaya mukayi waya dake baki sake kirana ba”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Kai Hajja Nana kuma abin harda Sherri ne?

kin manta cewa garin ku babu network in baku kuka kira ba baya shiga, kullum fa kina raina”.

Dariya Hajja Nana tayi tare da faɗin.

“A yayi kyau yaushe zaku zo?”.

Cikin sauri tace.

“Next week”.

Cikin so da ƙauna Hajjaj Nana tace.


“Yau da kaina na ɗibo ƙafana har bidhiyar ƙare zancenka saboda inji Labarin Ƴar jikata dan nayi kewarki
ina so in San yaushe zakuzo”.

Khausar na murmushi me ɗauke da ƙaunar Kakar tata tace.

“In sha Allah nan da kwana uku dai muna cikin Nigeria”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.

“Toh Allah Ubangiji ya kawo ku kafiya”.

Bayan ta gama wayar ne ta miƙe ahankali kasancewar tun safe bata leƙa Didi ba kallon jikinta tayi ganin
dogon riga ce budadde da mayafinsa babba yasa ta sauƙa falonta ta wuce Side ɗin Didi.

Tana shiga Falon ta samu Didi zaune da ahlinta, Modibbo Sai Zakariyya da Dr Jameel, Sai kuma Lalla
Khadijah da Lalla Salma da Hafsat wanda ga duk kan alama sunzo tafiya bikin ne Didi na ganinta ta miƙa
mata hannu idanunta akan cikinta,.

Sai lokacin itama ta kalli cikin ta ga Mamaki ta sai taga cikin nata har ya tura rigar ta kaɗan cikin jin kunya
ta zauna gefen Didi cike da kulawa Didi tace.

“Barka da yamma?”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Yawwa Barka dai Didi”.

Didi na gyara zama tace.

“Yau tun safe nake ta zuba ido zan ganki ban ganki ba ki shigo ba, nace Rahama taje ta du baki data
dawo sai tace kina bacci”.

Tana kallon Moddibo tace.

„Eh Didi ina bacci ban daɗe da tashi ba shine nayi wanka sai kuma na ɗanyi waya da Momy na Momy
tace in gaishe ki ma”.

Fuska a sake Didi tace.

“Ina amsa wa Masha Allah fatan suna lafiya?".

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Lafiya ƙalau”.

Ita kuwa Khausar kallonta ta mayar kan Lalla Khadijah da Lalla Salma da Hafsat cike da girmamawa ta
gaishesu cikin sakin fuska suka amsa mata suna tambayar jiki.
Kallonta ta mayar kan Didi jin tana cewa.

“Khausar ya shirye-shiryen tafiya?”.

Dariya Khausar ta sanya tare da faɗin.

“Aini har na gama shirya wa ma”.

Ahankali Moddibo ya ɗago Idanunsa ya kalleta kana yace.

“Toh da kika gama shirin ma ai ke ba zuwa zakiyi ba”.

Zare idanunta tayi sai kuma ta kwaɓe fuska ahankali ta maida kallonta kan Didi dake murmushi tace.

“Didi kiji fa abinda yake cewa".

Ɗan dariya Didi tayi ganin yanda ta kwaɓe fuska yasa tace.

“Rabu dashi waya isa ya hana ki zuwa Mamana ai kece agaba idan baki zoba amaren ma baza su zoba”.

Ware idanu Dr Jameel yayi tare da sanya dariya yace.

“Anya kuwa Didi wannan zai saɓu dan bata jeba ace Amare baza su zoba ai ita ta zauna gidan mijinta mu
muje mu ɗauko Matan mu". Cikin murmushi Zakariyya cewa.

“Gaskiya dai kam”.

Dariya Didi ta sanya kana tace.

“A'a Zakariyya har kaima wato zama da Jameelu ya dawo da kai mai surutu da baki”.

Dariya Lalla Khadijah ta sanya tare da faɗin.

“Aikam Didi Hausawa sunce zama da maɗaukin kanwa shi ke kawo farin kai".

Dariya suka sanya Lalla Hafsat ta karɓe da cewa.

“Aikam dai ko kurma ne ya zauna da Dr Jameel Sai ya koyi magana".

Zakariyya kuwa ƙeya ya sosa tare da sunkuyar da kai...

Ɗago kansu sukayi atare tare da kallon Ibraahim dake shigowa cikin mamaki suka haɗa bakin cewa.

“A'a Ibraahim kuma”.

Kai ya gyaɗa tare da buɗawa Rahama hannu wacce ta nufo kansa da gudu da murmushi afuskarsa yace.
“Surprise dama bazata na shirya muku Yah Jameel ba jiya muna waya kana zaton bazan zoba, har kana
fushi”.

Ya ƙare maganar tare da ƙarasawa gefen Lalla Khadijah ya zauna kana ya ɗaura kansa kan kafadarta Dr
Jameel cikin murmushi yace.

“Aikam da har nayi fushi da kai”.

Jujjuya idanu yayi yace.

“Amma dai yanzu ka huce ko?”.

Kai Dr Jameel ya gyaɗa tare da cewa.

“A na huce tunda kazo”.

Lalla Salma ce tace.

“Toh dama taya za'a yi Auren Yayun ka har biyu baka nan ai dole saida babban ƙanin ango za'a ɗaura
Aure”.

Dariya yayi tare da faɗin.

“Aikuwa dai Lalla Salma kin gane”...

Haka dai suka cigaba da hiransu.

Ana gobe zasu tafi da misalin karfe goma na dare Moddibo ne kwance a gefen Khausar yana romance
ɗin ta tare da shafa cikinta ahankali ya ɗago Idanunsa ya kalleta tare da cewa.

“Gobe idan munje Nigeria gidan Innayi zamu sauƙa” .

Idanunta dake shanye kamar na mai jin bacci ta buɗe tare da tura baki tace.

“Yah Mu'allim gidan ku kuma? Nikam dai inje gidan Momyna ”.

Da sauri ya ware idanunsa tare da dafe ƙirjinsa kana yace.

“Na isa ki tafi kibarni da waye idan kin tafi gidan Momy?”.

Cikin tura baki tace.

“In barka da Innayin ka mana”.

Kissing ɗin goshinta yayi tare da cewa.

“Innayi zata bani abinda kike bani ne Minha?


Innayi bazata bani abinda kike bani ba Minha sabida duk duniya babu wanda yake bani abinda kike bani
fa Minha ya za'a yi kice dan ina tare da wasu za kiyi nesa dani ai bazan iya jura ba”.

Ahankali ta fesar da numfashi tare da cewa.

“Kai Yah Mu'allim Kuma fa kasan nayi missing na Momy”.

Tafin hannunta ya riƙe cikin nasa yana matsawa yace.

“Nayi miki alƙwari idan munje kullum zan na kaiki ki wuni amma kwana bazan barki ba.

Babyna ma bazai iya ba saboda yana son ɗumin jikin Abbansa”.

Ta buɗe baki da niyar magana ta fasa jin wayarsa na ruri ahankali ya miƙe tare da janyota jikinsa yana
shafa bayanta ganin number Sheikh Jabeer yasa ya dauka muryansa can ƙasa yace.

“Kai baka san dare yayi bane?".

Ware idanu Sheikh Jabeer yayi tare da cewa.

“Ƙaniyarka ne ni kake faɗawa dare yayi?”

Cikin kwaɓe fuska Modibbo yace.

“Toh Amman dai kasan inada iyali ko?”.

Wani irin murmushin mai cike da tuna baya Sheykh Jabeer yayi tare da cewa.

“Hmmm yaro man kaza da kake cemin bansan dare yayi bane shin baka san cewa duk abinda ɗanyen
ganye ya sani ya kuma ganiba bushesh-she ya riga saba".

Murmushi Moddibo yayi tare da cewa.

“Can maka dai da karin maganar ka Ni ban fahimci me keke nufi ba".

Dariya Sheikh Jabeer yayi kana yace.

“Ai baza ka fahimta ba,

amma dai kasani duk abinda kake tunanin kasan shi na fika sanin shi kai abayana kake”.

Moddibo kuwa hannu ya cusa cikin sumar kan Khausar yace.

“Toh naji Ni dai yanzu ka faɗa min me yake tafe da kai ina da abinyi”.

Cikin so na kaka da jika Sheykh Jabeer yace

“Eh Ya maka kyau.


Dama akan batun number motar da kuka turo min ne tun jiya nayita kiranka baka ɗauka ba bansan me
kake ba”.

Cikin sauri Moddibo ya dai-daita nutsuwarsa tare da cewa.

“Kuma banga Miss call ɗin ba”.

Cikin fesar da numfashi Sheik Jabeer yace.

“An samu motar cikin motocin da aka kamo sannan acikin mutanen ana so gane su waye ke amfani da
motar dan mutanen kusan su ashirin da biyar aka kama.

Toh muna so mu gane su waye ke amfani da wannan motar sannan su waye suka sace Jameel suka
kashe sa”.

Cikin fesar da numfashi da kuma rauni Moddibo yace.

“Alhamdulillah in Sha Allahu Jinin J bazai tafi abanza ba”.

Kai Sheikh Jabeer ya jinjina tare da faɗin.

“Yanzu shine abinda muke so tunda har ita mai ɗakin ka ta gansu tasan Fuskarsu tunda jibi kuna hanya
idan kun iso kafin ku wuce sai munje kun gan su”.

Cikin sauri Moddibo ya runtse idanunsa yace.

“Yah Sheikh bana son ganinsu”.

Ahankali Sheikh Jabeer yace.

”Meyesa?”.

Araunane ya girgizar kai tare da cewa.

“Bana son ganin waɗanda suka kashe min J idan na gansu bansan me zanyi musu ba, kar nazo nima nayi
abinda bashi bane, bansan mai zan musu ba, na tabbatar dai in na zan ga wanda ya kashe J.

Bazan iya barinshi arayeba zan iya yi musu komai”.

Cike da nutsuwa da dattako Sheikh Jabeer yace.

“In sha Allah babu abinda zaka musu dole zaku zo ku gansu ”.

Idanunsa na tara hawaye yace.

“Bazan gansu ba bazan iya ba har abada bana ƙaunar ganinsu.

Babu wa'anda na tsani gani a duniya sama dasu”.


Ahankali Khausar ta miƙe ta zauna Sheikh Jabeer kuwa ahankali yace.

“Toh ba laifi ku dai ku shirya idan kun zo sai kun biya nan”.

Kai ya gyaɗa tare da katse kiran sai kuma ya maida kallonsa kan Khausar cike da rauni lokaci ɗaya
mutuwar Jameel ya dawo masa sabo idanunsa muryansa cike da sanyi da kuma rauni yace.

“Kinji fa waifa cewa yayi inje in Kalli waɗanda suka kashe min J.

Ina zan iya kallonsu?”.

Hannunta tasa ta tallafo kansa tare sa ɗaura aƙirjinta kana tace.

“Yah Mu'allim zamuje ko domin mu tabbatar da cewa suɗin ne suka kashe sa sannan mu tabbatar da
cewa suɗinne an kamasu, sannan ayi musu hukunci dai-dai da laifinsu.

Ni na tabbatar muddin na gansu wallahi zan gane su da Izinin Ubangiji”.

Araunane ya girgiza kai tare da cewa.

“Muje kuma Minha?, Minha bazan iya ganin suba fa”.

Kansa ta tallafe tana ɗan shafa bayansa alamar kontar da hankali tace.

“Yah Mu'allim zamu iya zamu iya ganinsu kodan ahukuntasu abinsa cutar damu da sukayi”.

Zuciyarsa na ƙuna yace.

“Minha zan iya musu abinda basuyi tunani bafa”.

Sake tallafo kansa tayi tare da cewa.

“Yah Mu'allim babu abinda zaka musu hukumane za tayi aiki akansu kamar yanda Shari'a ta tsara”.

Ta ida maganar tana shafa kansa ganin yanda mutuwar Jameel ya dawo masa sabo ahankali ta haɗe lips
ɗin su waje ɗaya wani gauron numfashi ya saki tare da janyo jikinsa ya fara shafa sassan jikinta ahankali
ya ɗago kai ya kalleta tare da yin murmushi kana yayi ƙasa da rigar baccin jikinta muryansa ashaƙe yace.

“Minha kina ganin gaba ɗaya abin nan sai sake girma suke”.

Shanyayyun idanunta ta ɗago ta kallesa tare da sakin murmushi hannunta na shafa kansa tace.

“Yah Mu'allim ba dole su sake girma ba gaba ɗaya ka buwaye su ka gigita su sannan ka hanasu nutsuwa
da kwanciyar hankali ”.

Hancinta ya lakace yace.

“Ba dole ba waɗan'nan kayan marmarin ai ba'a barinsu Minha suna da matsayi babba dama rashin
samun hannu ne shiyasa basa girma sosai yanzu kuma kinga sun samu”.
Dariya tayi haka tayi ta yi masa abubuwan da suka mantar dashi damuwa da kuncin daya shiga haka suka
kwana cikin farin ciki...

Ranan dasu tafi Misalin 12:00pm jirginsu ya tashi daga kasar Morocco zuwa Nigeria.

Kasancewar Private Jet ne shida Khausar suna First class daga can ƙarshe Zakariyya,Dr Jameel, Abualeey,
Galadima, Waziri, suma na cikin First class daga gaba sai Innayi kana Didi, Lalla Khadijah da Lalla Hafsat
duk suna baya.

Misalin ƙarfe biyar dai-dai jirginsu ya sauka a Adamawa kai tsaye motoci suka zo suka ɗauke su daga
Airport zuwa fadan Mai martaba sarki Jabeer Nuruddeen Bubayaro.

Kyakkyawan masauki na musamman aka basu anan suka kwana bayan anyi musu tarbar na mutuntaka
Didi takasance ga Mahaifiyarta da Mahaifinta sannan ga Ummi Kakarta Ummei Jakadiyarsu.

Washe gari da safe Misalin ƙarfe bakwai na safe Sheikh Jabeer da kansa ya wuce Masauƙin da aka bawa
Moddibo da Khausar yana shiga ya samu Moddibo na haɗa mata tea.

Juyawa Moddibo yayi ya kallesa tare da faɗin.

“Wai ya kake shigo mana haka ba neman izini”.

Kallonsa Sheikh Jabeer yayi tare da cewa.

“Ka manta nan Fada tace ba Fadar kuba da zaka ce sai na nemi izini”.

Murmushi Moddibo yayi yana mikawa Khausar tea ɗin yace.

“Toh me kake nema da sanyi safiyar nan da kazo mana?”.

Sheikh Jabeer na gyara tsayuwar sa yace.

“Tashi zakuyi mu tafi inda zamuje”.

Langwaɓar da kai Moddibo yayi tare da faɗin.

“Ni bazan jeba”.

Cikin sauri Khausar tace.

“Kayi haƙuri Yah Mu'allim muje”.

“Gwara kam ki faɗa mishi muje mu tabbatar dan kada aɗaurawa wasu laifin da bana su ba”.
Haka dai suka ta lallaɓa Moddibo har ya amince suna fita sai ga Amintaccen Hadimin Sheikh Jabeer ya
ɗauke su a mota suka tafi kurkukun dake cikin Yola suna isa bisa sirri akayi musu jagora da iso, aka wuce
da ciki.

Duna shiga Khausar tayi saurin komawa bayan Modibbo tare da riƙe hannunsa gama, cikin rawan jiki ta
ɗago hannunta tana nuna wasu ƙattun mutum biyu da babu alamun imani tare dasu, shiyasa aka ɗan
waresu gefe suna zaune sai kuzurai suke.

Cikin tashin hankali gami da tsanarsu ta fashe da kuka murya narawa tace.

“Ga sunan wallahi Yah Mu'allim sune, sukayi ta bin motarmu da Yah Jameel randa aka sace shi, kuma
sune suka je Jauro Yaya sannan kuma sune suka je bakin Makarantar.

Wallahi tallahi sune suka bibiye mu aranan da muka rabu da Yah Jameel na ƙarshe har da muka tsaya a
suma suka tsaya”.

Cikin Tsananin tsana takaici da ƙunar rai Modibbo ke binsu da wani irin kallo mai nuna jin zafin illar da
sukayi mishi.

Shi kuwa Sheikh Jabeer nan take yasa aka killace su waje na musamman da kansa ya tsananta bincike
Matsayin sa na SS mai zaman kansa wanda yasan kansa da aikinsa da ƙirewa.

Bisa jagorancin Jalal yasa aka musu ɗan banzan bugun da ya karya ƙarfin zuciyarsu.

Kana yacewa su Modibbo su shiga.

Cikin tsaresu da ido ya nuna musu Khausar tare da cewa.

“Kunsanta?”.

Agalabaice suka ce.

“Eh mun santa itama an bamu kwangilar kashe ta”.

Aruɗe ta zare ido kana ta ɗaura hannunta aƙirji tace.

“Kasheni kuma nima? me nayi muku”.

Kai Sheikh Jabeer ya jinjina kana ya nuna Moddibo dake binsu da wani irin kallon tsana gaba ɗaya jikinsa
rawa yake shi kuwa Sheikh Jabeer cikin sanin makamar aikinsa yace.

“Wannan fa kun san shi”.

Kai na farkon ya gyaɗa tare da faɗin.

“Eh ai dama shi tare aka bamu kwangilar karshe sa da Malam Jameel”.
Zama sheikh Jabeer ya gyara tare da faɗin.

“Waya baku kwangilar kashe su?

Sannan akan me zaku kashe su?”.

Ɗayan da yafi galabaitane ya ɗago fuskarsa da duk halittarsa ta canza saboda azabebben bugu da ya sha
yace.

“Mu mutanen garin dake gefen Jauro Yaya ne, kuma manyanmu ne suka bamu kwangilar karshe su".

Akai Khausar ta ɗaura hannu tare da faɗin.

“Ai kune ma na gani a Jauro Yaya ”.

Cikin tsawa Sheikh Jabeer yace.

“Me ya kaiku Jauro Yaya kuma?”.

Na farkon ne ya karɓi zancen da cewa.

“Mu muka kashe Garkuwan Rugar Jauro Yaya Umaru”.

Wani irin raunataccen kuka ne ya kubcewa Khausar yayinda gaba ɗaya jikinta ya ɗauki rawa.

Jalal kuwa a hankali ya gyara riƙon da yayiwa wayarsa saboda video'nda yake yi musu.

Zama Sheikh Jabeer ya gyara tare da ci gaba dayi musu tambayoyi.

Shi kuwa Moddibo gaba ɗaya ilahirin jikinsa rawa yake ji yake duniyar tayi masa ƙunci ji yake tamkar ya
fisge bindigar dake hannun Sheikh Jabeer ya kashe su kowama ya huta”.

Amma ya kasa motsa wa saboda Khausar dake rungume dashi ita ta hana shi motsi.

Dayan ne ya karɓi maganar da cewa.

Kamar haka uuna ɗaya daga cikin mutanen dake Maƙoftaka da Rugar Jauro Yaya wanda sun kasance
arna ne sannan manyan sune suka bamu umarnin su kashe Garkuwan Rugar Jauro Yaya saboda shine
yake shiga cikin Sabgoginmu yana hana mu Kidnapping yanda suke a yankin, dan da in sun sato mutane
a nan cikin tsaunukan dake zagaye dasune suke zuwa su ɓoye mutane, sai an biya su kuɗi wanda in za'a
samu mutane a wurin kai tsaye cewa za'ayi Fulani wurin ne suke satosu.

saboda haka ne in sunje sunyi kidnapped shi yake hana su sakewa, kuma basu isa su ɗauki dabbobi
yanda suke so saboda kasancewar mutum mai sa ido da kuma Jarumta”.

Cikin tafarfasan zuciya Sheikh Jabeer ya dasa masa bindiga akansa kana yace.
“Shi kuma Malam Jameel meya muku?,”.

Cikin haki da fusgar numfashi yace.

“Shima Malam Jameel manyan mune suka bamu kwangilar kashe sa Saboda shine mutum na farko daya
buwayi al'ummar mu da wa'azi wanda yake zama sanadin da matasanmu da yawa suke Musulunta
shiyasa manyan mu suka bamu umarni shi da Moddibo mu haɗa su mu kashe su shine abinda zai fi mana
sauƙi da kwanciyar hankali idan ba haka ba zasu janye mana ra'ayi da tunanin matasan mu”.

Dafe kai Sheikh Jabeer yayi tare da cewa.

“Innalillahi wa'inna alaihi raji'un”.

Cikin tashin hankali Moddibo ya dafe kansa tare da faɗin.

“Hasbunallahu wani'imal wakin".

Sai kuma ya koma ya zauna yana dafe kansa da hannun ɗaya yayinda ɗaya hannun kuma ke tallabe da
Khausar cikin kaɗuwa yace.

“Ana zaton wuta amaƙera sai gata a masaƙa ina zaton kashe J akayi tunda aka kamasa na tabbatar cewa
magautane acikin kashe sa amma duk atunanina akwai sa hannun ɗaya daga cikin Yadikkonsa ashe babu
su Astagfirullah Allah na tuba ka yafe min da zargin da Nai ta yiwa Hajia Turai da Karima Allah na tuba”.

Cike da rauni da tausayinsa Khausar ke zubda hawaye, shi kuwa Modibbo cikin rauni ya cigaba da cewa.

“Manzon Allah (S.A.W)da kansa yace _Azzhana zhambu Walau kana haƙƙun_ sai naje na nemi yafiya da
gafarar Hajiya Karima saboda duk tunanina ko ita ko Hajiya Turai akwai sa hannun ɗaya daga cikinsu
aɓacewan J ashe suma ba abinda suka sani waɗan nan kafiran maƙiya Allah da Manzonsa suka sa aka
kashe min J ɗina”.

Sosai Sheikh Jabeer yasa aka azabtar dasu suka faɗi duk laifinsu daga nan aka tura su waje na daban aka
killace su domin jiran yanke musu hukunci.

Jalal kuwa nan take ya tura Modibbo video da yayi musu na cikekken bayanansu da sukayi.

Sheykh Jabeer kuwa da kansa ya tara su Abualeey yayi musu cikekken bayanin, ya ƙara da cewa, sai yazo
ɗaurin auren su Dr Jameel shi da kansa zai yiwa Ummi da Abban Jameel dukkan bayani.

Aranan ƙarfe goma dai-dai na safe suka kama hanyar tafiya Membila da rakiyar motoci na musamman.

Ƙarfe huɗu dai dai ya musu acikin garin Gembilan...


By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

65

KAZAURE COLLEGE OF NURSING SCIENCES (KCONS)

Lafiya Uwar jiki, Kuma sai da lafiya ake morar rayuwa. Kazaure College Of Nursing Sciences (KCONS) ta
kawo muku ingantaccen tsarin koyar da jinya da unguwar zoma, mun himmatu wajen samar da
kwararrun ma'aikatan jinya da unguwar zoma a fadin Nigeria da ma matakin duniya baki daya, a KCONS
mun tanadar muku kwararrun malamai, ingantaccen yanayi da tsarin koyo da koyarwa kai harma da
tsarin e-learning, ka zalika akwai tabbataccen tsaro a dakunan kwanan dalibai maza da mata, bugu da
kari kudin makaranta dai-dai aljuhu ne, KCONS munanan a lamba 5 layin fadar sarki dake kan hanyar
kano zuwa daura a Kazaure jahar Jigawa, za'a iya samummu a shafikanmu na facebook da instagram
@KCONsciences domin bayani, za'a iya tuntubanrmu a wadannan lambobin, 07066542055,
08035298851, ko shafin mu na yanan gizo @ http://kcons.edu.ng/admission KCON sciences kan turbar
aiki da kwarewa muka shahara.

https://chat.whatsapp.com/HCji7xLpR1VEJGYcZJMP6k

65

Ajere-Ajere motocinsu suka fara shiga harabar gidan Innayi. Moddibo kuwa sassayan numfashi ya fesar a
hankali ransa cike da mamakin, shin meyesa Abban Jameel yace su sauƙa anan duk da yasan cewa ba
wasu wadatattun ɗakuna bane a gidan, kasancewar daga ɗakin Innayi sai Side ɗin sa dake da 2 bedroom
sai single room a bakin ƙofar falon, yace wa Abba su sauƙa a hotel daya musu booking Amma yace a'a
yaƙi masa musu ne, saboda bai san mai ya shirya ba duk da yafi tunanin Abba yace hakane ko sai sunci
abinci kafin su tafi Masauƙinsu.

Akuma dai-dai lokacin motocinsu sukayi Parking a farfajiyar gidan.


Daga can waje kuma cikin sassarfa Haiydar da Bashir suka nufo gidan wanda har sun dauki hanyar
komawa gida kasancewar sun jira su basu zoba sai kuma suka hango motocin su.

Acan harabar cikin gida kuwa cike da matsanancin mamaki da al'ajabi Moddibo ke bin baki ɗaya ilahirin
gidan da kallo wanda aka tsara shi yayi masifar kyau wasu dan ƙara dan ƙaran Side ne akayi su guda biyu
wa ɗan da kusan komai nasu irin nasa ne sai dai basu da wadatan flowers kamar nashi cikin fesar da
numfashi da mamakin dake kwance saman fuskarsa ya ziro ƙafarsa na dama kafin ahankali ya gama fito
da gangar jikinsa daga motar, hannunsa na riƙe cikin na Khausar still Idanunsa na bin harabar gidan da
kallo.

Akuma dai-dai lokacin Idanunsa suka sauƙa kan Abban Jameel, Lamiɗo da Malam Ahmad suna sauƙa
daga kan barandar ɗaya daga cikin Sabon Side biyu da aka gina still da mamaki ya maida kallonsa kan
Innayi data fito daga Motar da suke.

Murmushi Innayi tayi ganin kallon mamakin da yake bin gidan dashi kana tace.

“Bismillah ku shiga side ɗinka”.

Kallon yaushe akayi wannan ginin yayi mata, fahimtar kallon da yake mata yasa ta jinjina masa kai tare
da cewa.

“Tun kwanaki ai aka fara ginin saboda sanin cewa zamu zo Auren su Jameel, kana lokaci zuwa lokaci
zamu buƙaci zuwa nan tunda ni da kai dai ba zamu manta garin Membila ba”.

Sanyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe kana yayi murmushin gefen baki sosai yaji daɗin hakan saboda bawai ya
tsani garin Membila bane saboda ya samu nasa garin, kawai dai Membila ta fita a ransa ne saboda rasa
amininsa, Amman duk da haka yasan gari Membila garine wanda yake da tarihi arayuwarsa yana jin
Membila na cikin garin da yake tamkar tsagin jikinsa, ya sani bazai manta garin arayuwarsa ba, ko ina
yaje a duniya watara zata faɗo masa arai kuma dole zai buƙaci jin yana son zuwa cikin garin.

Anutse Didi ta fito kana Lalla Khadijah, Lalla Hafsat, Sai Rahama tana fita ta nufi gefen Khausar fuskarta
ɗauke da murmushi tace.

“Woww Lalla Khausar haka garinku yake daɗi?,Masha Allah kina jin weather Mai daɗi haka Masha Allah i
like it”.

Murmushi Khausar tayi kana ta gyaɗa mata kai da faɗin.

“Aikuwa zaki sha sanyi”.

Idanu Rahama ta lumshe sai kuma ta buɗe tace.


“Aikam akwai sanyi kam, duk da muma A Morocco ana mana sanyi but time to time ne amma bai kai
wannan ba sanyin nan daban ne”.

Ta ƙarashe maganar tana ƙanƙame jikinta waje ɗaya jin yanda sanyi ke ratsata.

Kallon Khausar dake ɗan lumshe idanu Didi tayi kana ta maida kallonta kan Moddibo cike da kulawa
tace.

“Aleeyu ku shiga ciki yarinyar ta gaji da zaman motar nan ”.

Kai ta gyaɗa Tare da cewa.

“Toh”.

Sai kuma ya damƙe hannun Khausar cikin nasa tare da ɗan janyota jikinsa suka nufi Side ɗin sa.

Gaba Innayi tayi tana mai cewa.

“Didi, Lalla Khadijah Lalla Hafsat Bismillah”.

Kai suka gyaɗa tare da bin bayanta suka nufi ɗaya daga cikin Side ɗin.

Akuma dai-dai lokacin Ummi ta fito daga Side ɗin fuskarta ɗauke da farin ciki da mamakin ganinsu tace.

“Masha Allah sannunku da zuwa, sai yanzu kuka iso, da naji ku shiru-shiru har nake cewa barin tafi wata
ƙil zaku kai dare”.

Ta ida maganar tare da rungumar Didi itama Didi rungumeta tayi tana cewa.

“Masha Allah fatan mun sameku lafiya”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da riƙo hannun Lalla Hafsat tace.

“Alhamdullah. Bismillah mu shiga daga ciki”.

Cike da farin ciki suka bi bayanta...

Abban Jameel kuwa shi yayi wa Abualeey, Waziri, Galadima, Baffan Zakariyya, Dr Jameel Zakariyya
jagora zuwa Side ɗin da suka fito ko wanne yana ɗauke da 3bedroom manya,-manya wanda aka shirya
su da kaya na alfarma da kawa ɗaya daga cikin ɗakunan Dr Jameel, Zakariyya da Ibraahim ne aciki.

Sai kuma na biyun Abualeey ne da Waziri, Sai kuma Baffan Zakariyya, Galadima.
Acan Side ɗin su Ummi kuwa Didi da Rahama ta nunawa ɗakin farko inda zasu zauna kana bedroom ɗin
gaba ta kai Lalla Khadijah, Lalla Hafsat,da Niyna.

Sai da ko wannensu yayi wanka kana suka canza kaya zuwa mai ɗan nauyi amma ba can ba saboda
yanayin sanyin garin kafin suka gabatar da sallolin suka ɗan huta tare da taɓa hira sai kuma suka fito Falo
Ummi da kanta tayi musu iso zuwa dining.

Didi na murmushi ta shaƙi sanyayyar Iskar garin da kuma wanda bishiyoyi da flowers ɗin gidan ke
kaɗawa tace.

“Kai Alhamdulillah Masha Allah weather garin nan akwai daɗi ”.

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.

“Aikam sai dai akwai sanyi”.

Sai kuma tayi serving ɗin su da lifiyayyan abinci iri iri na alfarma da suka musu.

Akuma dai-dai lokacin Haiydar da Bashir suka shigo bayan sun fito daga ɓangaren su Abualeey Haiydar
na bin Falon da kallo yace.

“Ummi ina Addah Khausy?”.

Ɗan Murmushi Ummi tayi tare da faɗin.

“Tana side ɗin Moddibo”.

Cikin sassarfa ya juya da niyyar fita sai kuma yayi saurin juyawa ya kalli Didi cikin girmama ya ɗan
rusunar da kanshi yace.

“Ayyah Didi kuyi haƙuri na manta bamu gaisa ba ina yininku fatan kunzo lafiya?”.

Dariya tayi tare da faɗin.

“A' lafiya lau anyi kewar ƴar uwa ko?”.

Dariya yayi tare da kama hannun Bashir da yake gaida su daga nan suka ficewa kai tsaye Side ɗin
Moddibo suka nufa.

Acan Side ɗin Mazan ma haka ya kasance Abban Jameel da kansa yagabatar musu da abinci na alfarma
da girmamawa sosai Abualeey suka jinjina mutunci da karramawarsu...

Haiydar da Bashir kuwa tun daga kan step ɗin Side ɗin Moddibo suke ƙwalawa Khausar kira suna cewa.

“Addah Khausy! Addah Khausy!!, Addah, Khausy!!!”.


A kuma dai-dai lokacin Khausar da Moddibo ne tsaye Dining hannunsa na cikin nata cikin taushi ya
ranƙofa kanta tare da sassauta murya yace.

“Me zaki ci?”.

Kanta ta langwaɓar tare da tsirawa jerin abincin dake dining ɗin ido lumshe idanunta tayi tare da fara
buɗe womers ɗin cikin yanayin jin sanyi ta motsa laɓɓanta tare da cewa.

“Ga nan tuwo miyan kuka kasa min kaɗan zanci ”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da faɗin.

“Masha Allah zauna toh bari na zuba miki”.

Da dan sauri ta juya jin Bashir da Haiydar na cewa Addah Khausy Addah Khausy hannunta dake cikin
nasa ta janye ta juya cikin sassarfa ta nufi ƙofan anufinta tayi gudu.

Da wani irin sauri Moddibo ya riƙo tsintsiyar hannunta yace.

“Kiyi haƙuri Minha na tuba dan Allah kada kiyi gudu”.

Ɗan ware idanunta tayi tare da faɗin.

“Su Bashir da Haiydar ne fa”.

Kafin ta ƙarasa suka ƙara so cikin falon tare da rungumeta shima Bashir cikin sauri ya rungumeta ta gefen
Haiydar.

Murmushi Moddibo yayi tare da harɗe hannunsa aƙirji yana kallonsu da tattausan murmushi bisa
kekkyawar fuskarsa.

Khausar kuwa kallon Bashir tayi tare da cewa.

„Bashir ina Asma'u?”.

Murmushi yayi kana yace.

“Ba tazo ba wai ita kunya Amarya baza ta zo ba”.

Dariya mai tauri ta sanya tare da faɗin.

“Don Allah yanzu baza tazo ba haka zata min kenan?”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Wallahi fa taƙi zuwa tun safe taƙi zuwa ayi shara da ita wai Ummi tayi haƙuri”.
Dariya Khausar ta sanya tace.

“Lallai dai kam”.

Haiydar kuma hannunshi yasa cikin nata.

Cikin mamaki ta kamo hannun tare da kallon faratunsa hararansa tayi tare da cewa.

“Me haka zaka wani tare farce kamar mace?”.

Cikin lingwaɓar da kai yace.

“Na gaza koyan yanke wa nefa, Mommy kuma tace in dai bazan koyaba bazata yanke minba”.

Murmushi tayi tare dasa hannunta ɗaya ta dungure ƙeyarsa tare da cewa.

“Shine daga isowata zaka haɗani da aikin yankewa”

Ta ƙareshe mgnar tana jawosu suka zauna bisa kujerun Dinnin table ɗin.

Moddibo kuwa a kujerar dake fuskantar Khausar ɗin ya zauna, yana maiyi mata wani arin amintaccen
kallo ya fahimci akwai tsananin shaƙuwa da so tsakaninta da Haiydar duk da yawan faɗan da suke a da.

Anan sukaci abinci tare.

Kana sukayi ta hira kiran sallan Magrib ne yasa duk mazan sunka tafi masallaci.

Kana basu dawoba saida sukayi sallan Isha sannan suka dawo nan kuma suka sake dasa sabon hira.

Hakama Abban Jameel dasu Abualeey.

Suma su Didi da Ummi haka ta kasance a wurinsu.

Misalin sha ɗaya su Lamiɗo suka yiwa su Abualeey saida safe kana suka tafi.

Su kuma duk sukayi shirin bacci suka kwanta.

Ummi dake tare da Malam Ahmad ta nufi sashen Khausar tana faɗin.

“Bari in je in jawo su Haiydar dan na lura su yau in zasu samu a nan zasu kwana”.

Kai ya jinjina mata tare da jingina jikin motarsu ya tsaya jiran fitowarta.

Ummi na shiga ta kalli Haiydar dake zaune gefen Khausar tace.


“Ku tasa mu tafi”.

Da sauri Khausar ta miƙe tare da cewa.

“Toh Ummi bari in ɗauko mayafina mu tafi”.

Juyawa Ummi tayi jin Moddibo na cewa.

“Ina zaki je?".

Idanunta ta narkar kana tace.

“Zanje gida mana”.

Yana tsuke fuska yace.

“Da Izinin wa?".

Murmushi Ummi tayi tare da kallon Haiydar da Bashir tace.

“Haiydar kuzo mu tafi dare yayi mu barsu su huta”.

Saurin kallon Ummi Khausar tayi tace.

“Ayyah Ummi dan Allah ku jirani ya za'a kuma ace bazan jeba don Allah kayi haƙuri”.

“Da Izinin wa?”.

Ya maimaita tambayar yana mai tsuke fuska.

Kamar za tayi kuka tace.

“Da Izinin ka mana”.

Kai tsaye yace.

“Toh ban bada Izini ba”.

Ummi kam hannun Haiydar da Bashir taja suka fice.

Sai da suka sauƙe Haiydar agida kafin suka wuce.

Haiydar na shiga Falon Momy ya shiga da sauri ya zauna gabanta kan lallausan Darduma da take bisa
alamu shafi da witri tayi.

yayin da ta jingina kanta jikin kushin cike da matsanancin farin ciki yace.
“Momy".

Cikin tsira nasa ido ta gyara zamanta tare da cewa.

“Na'am”.

Murmushin fuskarsa ya faɗaɗa tare da faɗin.

“Kin ga yanda Addah Khausy ta dawo kuwa Momy?”.

Kai Momy ta girgiza kana tace.

“A'a ya ta dawo?”.

Zama ya gyara yace.

“Wallahi idan kika ganta zakice Balarabiya ce Masha Allah Subhanallah, tayi wani irin fari mai masifar
kyau farinta har wani ƙelli takeyi”.

Ɗan ware idanu Momy tayi tare da faɗin.

“Allah ko?”.

Kai ya gyaɗa yace.

“Wallahi fa”.

Daga nan suka cigaba da hira.

Acan ɓangaren su Moddibo kuwa cikin tura baki Khausar tace.

“Haka kawai ahanani zuwa gidan mu yanzu Fisabilillahi muna ƙasa ɗaya gari ɗaya ace bazan ga Momyna
ba?”.

Kansa ya ɗaura bisa kafaɗarsa yace.

“Na isa? Ai ban isa in hana ki ganin Momyn kiba? waya isa ya raba uwa da ɗa? ban isa in ra Baki da
Momy ba.

Kawai dai nima bana so ara bani da ɗana akusa dani ne shiyasa”.

Cunno baki tayi tana kallonsa cike da shagwaɓa hanci ya lakace mata kana ya cigaba da cewa.

“Kuma ina so ki huta nasan in kunje hira zaku tayi baza ki huta ba kiyi haƙuri ki kwanta kiyi bacci ki huta
gobe da kaina zan kai ki muje mu gaida Momy”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.


“Da sassafe”.

Kai ya gyaɗa cikin tabbatar wa yace.

“In sha Allah in dai mun karya”.

Lallausan murmushi ta sakar mishi tare da riƙe tafin hannunsa tace.

“Toh shikenan”.

Bedroom suka wuce sosai tsarin ɗakin yayi kyau komai yayi yanda ake buƙata kana agyare tsaf-tsaf sai
tashin ƙamshin roomfteshner yake, zama tayi kan gadon tare da jingina kanta da jikin gadon.

Moddibo kuwa gefenta ya zauna yana ɗan matsa mata ƙafafun yace.

“Kinga tafiyar nan da akayi mai ɗan tsawo sai nake ga kamar ƙafarki ta kumbura”.

Idanunta dake lumshe ta ɗan buɗe ta kalli ƙafan sai kuma ta gyaɗa masa kai tace.

“Eh dama Ni haka nake in dai na ɗanyi tafiya mai tsawo amota Normal haka yake min, zuwa safiya zaka
ga ya watse”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da faɗin.

“Kuma ahaka kike so ki tafi kije ki zauna ba kiyi bacci ba”.

Ya ƙare maganar yana jan yatsun ƙafar tata tare da ɗan mammatsa mata su, sassayan numfashi ta fesar
tare da muskutawa, da sauri ya ɗan tallabota tare da gyara mata kwanciyar saboda ganin duk ta sake
alamun bacci mai nauyi takeji.

Ahaka ya cigaba dayi mata massage suna hira jefi-jefi har bacci ya ɗauketa.

janyota jikinsa yayi ya haɗa hannunsa waje ɗaya ya tofa musu addu'a ajikinsa ya fara shafawa kana ya
shafa mata.

Washe gari bayan sun kammala breakfast da duk wani abu da za suyi Kai tsaye sashen su Didi suka shiga
bakinsu ɗauke da sallama suka shiga bayan sun gaigaisa Moddibo ya kalli Didi tare da cewa.

“Didi zamu je wurin Momy”.

Kai Didi ta gyaɗa kana tace

“Ok sai munzo muma yanzu Ummin Jameel zata zo mu taho tare”.

Kai ya gyaɗa yana ɗan matsa hannun Khausar yace.

“Toh shikenan sai kun zo”.


Daga nan suka miƙe suka fito da kansa ya shiga mazaunin driver, kana ta shiga gefen mai zaman banza,
cikin nitsuwa yaja suka tafi anutse yake driving yana Jin wani yanayi na daban.

Titinan garin ya zubawa ido lokaci ɗaya kuma tunanin J ɗinsa ya faɗo masa sai kuma yake tuna Lokuta
da dama Idan yana tuƙi J na gefensa ko kuma J na tuƙi shi yana gefensa jikinsa ne yayi sanyi, tafin
hannunta ya riƙo tare da mannawa kan cikinta yayi shiru kwayar idanunsa na tsats-tsafo da ruwan
hawaye.

Tuni ta fahimci yanayin da yake ciki cikin sanyi da rauni tace.

“Allah ya jiƙan Yah Jameel Allah ya mishi Rahma Allah ya gafarta masa”

Araunane yace.

“Ameen Ya Allah Minha”.

Tana matsa hannunsa dake cikin nata tace.

“Yah Jameel yanzu baya buƙatar kukan nu addu'ar mu yake buƙata”.

Cikin ƙoƙarin hana hawayen sa zuba yace.

“Nima haka nakeso ina ta ƙoƙarin hana zuciyata da Idanuna kuka akan J sai dai muyi ta mishi addu'a
Amman wasu lokutan ina gaza hana kaina hawaye a kanshi saboda nayi rashine da har yau ban samu
madadinsa ba”.

Cikin tausasawa tace.

“Na sani Yah Mu'allim to Amman Allah ya fimu sonshi, kuma dama shi ya bamu shi dan haka addu'a
kawai zamuyi ya mishi”.

Cikin sanyi yace.

“In sha Allah za muyi masa”.

A kuma Dai-dai lokacin mai gadi ya buɗe musu gate ɗin gidan Lamiɗo Parking yayi kana suka fita da sauri
ta nufi harabar gidan da nufin gudu,

saurin riƙo hannunta yayi cikin tsira mata idanu ya langwaɓar da kai yace.

“Kar kiyi gudu mana wai ke bakya jin tsoron ki faɗine”.

Kai ta ta gyaɗa tace.

“Toh ai sauri nake inje inga Momy".


Sake langwaɓar da kai yayi yace.

“Ai zaki ganta Minha ba sai kinyi gudu ba tun da gaki cikin gidan”.

Ko gama rufe baki baiyi ba ta hango Raudat riƙe da Comb da kifiya bisa alamu kitso zata tafi.

Da sassarfa ta nufeta tana kiranta,

Ita kuwa Raudat jin muryar Adda Khausy tane yasa ta ɗago kanta aiko ganinta ne yasa ta buga tsalle cike
da matsanancin farin ciki tace.

“Addah Khausy”.

Da wani irin sauri Khausar ta janye hannunta dake cikin nasa ta ruga da gudu.

Atsorace ya sanya tafin hannunsa biyu ya dafe kansa kana ya motsa laɓɓansa tare da faɗin.

“Ya Salam ki daina gudun nan”.

Ina bata saurareshi ba da gudu ta rungume Raudat Raudat kuwa tsalle ta riƙa yi ajikinta tana cewa.

“Oyoyo! Oyoyo Addah Khausy!, Mommy Addah Khausy!! Tazo Addah Khausy!!!,Oyoyo”.

Cike da matsanancin farin ciki Khausar ta ɗaga ta sama ta riƙa juyawa da ita a tsakiyar gida wanda hakan
ne yasa baki ɗaya mutanen gida suka san cewa Khausar tazo.

Dai-dai lokacin kuma Haiydar ya fito daga ɗakinsa.

Da gudu Sulaiman ma ya fito daga sashen Hajiya Bunayya atare suka rungumeta suna faɗin.

“Oyoyo Addah Khausy ”.

Khausar kuwa cike da matsanancin farin ciki take jujjuyawa atsakiyarsu ruggume da Raudat tsam a
jikinta.

Jin sowarsunw yasa Momy dake zaune falonta ta miƙe da sauri ta fito jin sautin muryansu na tashi cak ta
tsaya ta riƙe ƙafan Falon tare da tsirawa Khausar idanu tana kallonta cike da so, ƙauna, bege, kewa irin
na uwa da yarta.

Khausar kuwa sai juyawa take dasu tana ƙyalƙyala dariya sai kuma tayi saurin sake su ta nufi Momy tana
gudu tare da faɗin.

“Oyoyo Momyna”.
Runtse idanunsa yayi sai kuma ya ɗan ɗaga saitin muryansa yace.

“Dan Allah Momy kice mata ta daina gudun nan zata yiwa kanta Illah fa”.

Murmushi Momy tayi tare da kallon Khausar kallo ɗaya ta mata ta fahimci tana da ciki wanda har ya ɗan
tasa ga wani irin kyau da tayi sai ƙelli take zubawa ga ɗan cikinta daya turo gwanin kyau ya zauna a
jikinta cib da cib sai ƙugunta da ya ƙara faɗi.

Cikin sauri da bege Minti ta rungumeta asanda ta isa gareta sau kuna tace.

“Ke meyesa bakya girmane. Khausar wannan guje-guje har yanzu baki barshi ba”.

Murmushi tayi tare da sake Momy sai kuma ta sake rungumeta kana ta sake ta ta kuma sake rungumeta
ɗan turata Momy tayi tare da faɗin.

“Ni matsa ahanya Bismillah Moddibo shigo".

Sai alokacin Haiydar ya miƙawa Moddibo hannu kana yace.

“Yah Moddibo Bismillah mu shiga”.

Kai Moddibo ya gyaɗa suka shiga bayan sun zauna a falo Momy da kanta ta kawo musu Drinks da Snacks
da ruwa ta ajiye musu agabansu.

Raudat kam cike da farin ciki ta kwanta kan Khausar tana ta nuƙurƙusata,

ahankali Moddibo ya riƙo tafin hannunta yace.

“Kiyi haƙuri Aunty Raudiy adaina danne Adda Khausy kar aji mata ciwo”.

Cikin jin daɗi Momy ta kawar da kanta jin yanda yake mata magana cike da kulawa sai kuma ta miƙe
tace.

“Bismillah kusha ruwa bari nazo ”.

Ta ƙarashe maganar tana fita kai tsaye bedroom ɗin ta ta wuce.

Acan ɓangaren Hajiya Bunayya kuwa a dai-dai lokacin zaune take aruwan zafi idanu ta tsirawa ruwan
tana kallon ƙananun tsutsotsin farare masu jajayen kai wanda ga duk kan alamu sune suke addabar ta da
jarabar ƙaiƙayi wanda zuwa yanzu tsakaninta dubaranta da gabanta ya wawake tuni sun fafeta ta kashin
ta da gabanta ya haɗe saboda masifar ƙaiƙayi da yanda suke cinta taje asibiti har ta gode Allah abanza
kana ta kira matar data haɗa su da Boka Gillaw.
Taje ta faɗawa Boka Gillaw ga abinda yake faruwa yace wannan sakamakon aikin su suke girba babu
abinda zai iya kada su sake kiransa, dama shi ya gaya musu idan buƙata ta biya su biya kuɗi idan kuma
bai biya ba shikenan suji da kansu.

Matar ta tambaye shi mai zai basu amma yace babu abinda zai basu wannan Sakayyar sune babu wanda
ya isa ya kawar da Sakayyar zunubansu ne ya sauka akan su Babu ruwansa suji da kansu shima yaji da
kansa.

Tuno waɗanan maganganun ne yasa ta fashe da marayan kuka mai cike da nadama mara amfani, tana
cikin kukan ta jiyo sautin muryoyi ana cewa Oyoyo Addah Khausy ahankali ta juye ruwan tana kallon
tsutsotsin masu masifar gudu da ƙaiƙayi dole sai ta shiga ruwan ɗumin ne take ɗan jin sauƙi.

Tana fitowa daga Bathroom ɗin ta zaune gefen Amina dake kwance kan gadon wacce ta rame ta zama
wata halitta daban kamar ƙwarangwal tana nan tamkar wacce babu numfashi ajikinta kuka ta fashe
dashi tare da cewa.

“Amina kinga Sakayyar abinda mukayi ko. Ubangiji ya kama mu tun a duniya Allah ya kamu da Sakayyar
tarin zunubanmu Amina ya zamuyi?”.

Araunane Amina ta ɗago kanta cikin muryanta da baki ɗaya ya koma na wata halitta ta kalleta duk ta
disashe baki ɗaya kamanninta da siffofinta ya fara zama na maciji ne ko menene dai ho da kyar ta buɗe
bakinta tace.

“Umma munemi gafarar wa'anda muka cutar tun kafin dare ya mana ”.

Cikin rauni da zubda hawaye Hajiya Bunayya tace.

“Dole ma mune mi gafarsu su yafe mana nasani wannan Sakayyar abinda nata yiwa wannan baiwar Allah
ne, da abinda nayi wa ƴarta da kuma yanda nayi ta zubar mata da ciki sannan nasa aka kashe Ramadan
yanzu shine Allah ya jarabceni da wannan abin”.

Kuka sosai Amina ta fashe dashi tana ji kamar adawo mata da lokacin baya ta gyara kuskurenta.

Ita ma Hajiya Bunayya kuka ta fashe dashi Asiya ce ta shigo ta zauna gefen su ta shiga rera kuka cikin
rauni da tausayinsu tace.

“Umma ku nemi gafarar Momyn Khausar da Khausar duk wanda ku kasan kun cutar kunemi gafarar su
Allah gafururrur rahim ne shima zai yafe muku sai kuma ku nemi gafarar Allah akan shirka da kuka yi
Allah ya yafe muku ”.

Cikin raunin Murya da shesh-sheƙa Amina ta gyaɗa mata kai tare da faɗin.

“In sha Allah zamu nema amma Addah Asiya ki taya mu basu haƙuri ”.
Kai Asiya ta gyaɗa tare da cewa.

„In sha Allah yanzu ma mukayi waya da Samira Sani take cemin itama jiya baki ɗaya Momyn ta kwana
tayi tana ta ihu acikin gida gaba ɗaya tazama kamar mahaukaciya, ita tana jin tsoro yanzu zata dawo nan
ma”.

Atsorace Hajiya Bunayya ta dafe kuncinta tace.

“Yau sun shiga ukunsy Hajiya Lami fa ta haukacene”.

Cikin sanyi da zubda hawaye Asiya tace.

“Haka dai alamu suka nuna Umma Allah ya yaye muku ya dubeku da idon Rahama”.

Cikin rauni da tarin tsoro Hajiya Bunayya tace.

“Ameen”.

Amina kam sai hawaye take tana nadama da danasanin abinda ta aikata.

Acan Falon Momyn kuwa bayan Moddibo yasha ruwa kana yaci Snacks da Drinks Momy ta fito suka gaisa
bayan sun gaisa ta kallesa da kulawa tace.

“Ina su Didi kuma?”.

Sake sunkuyar da kansa yayi tare da cewa.

“Momy su Didi suna gida amma sunce zasu ɗan fito zuwa azahar, sannan zasu fara ta gidan su Ummu
kafin suzo”.

Dai-dai lokacin kuma Asma'u ta shigo Falon bakinta ɗauke da sallama kasancewar Haiydar ya kirata ya
sanar mata Khausar tazo gida.

Khausar na ganinta ta miƙe da tsalle kana ta haɗa da gudu suka rungume juna da Asma'u suka fara
juyawa atsakiyaar Falon.

Cikin tsuke fuska Moddibo ya kalli Asma'u tare da faɗin.

“Asmau me haka ki sake ta?”.

Ahankali Asma'u ta sunkuyar da kanta ƙasa sai kuma ta saki Khausar ta tsugunna gefen Moddibo cike da
ladabi tace.

“Yah Moddibo sannu da zuwa Ina yini”.

“Lafiya”.
Ya faɗa yana ɗan sake Fuskara sai kuma yace.

“Ke baki ga yanayin yanda ƙawar taki take bane kike mata irin wannan rungumar?”.

Dariyar dake cinta ta danne ganin yanda Khausar ta Cunno baki kana tace.

“Yah Moddibo ayi haƙuri”.

Yana murmushi yace.

“In sha Allah yanzu dai akiyaye”.

Kai ta gyaɗa tare da miƙewa ta riƙe hannun Khausar suka nufi bedroom ɗin ta.

Ganin haka yasa ya miƙe tare da cewa.

“Momy bari in fita dan su Dr Jameel na jirana zamuje gida Abban Jameel ”.

Mommy na gyara mayafinta tace.

“Ayyah ai nima Jameel ɗin nan ina so akawo minshi in ganshi Haiydar yata bani labarinsa”.

Cike da girmamawa yace.

“In sha Allahu Momy za'a kawo miki shi”.

Murmushi tayi tare da faɗin.

“Toh ka gaishe su”.

Amsawa yayi kana ya fita.

A dai-dai lokacin kuma Didi, Lalla Khadijah, Lalla Hafsat, Suna gidan Ummin Jameel duk sun gaisa da ƴan
Uwanta wanda suka fara taruwa saboda bikin bayan sun gama suka fito zuwa gidansu Momyn Khausar.

Suna shiga Falon dai-dai lokacin Asma'u da Khausar na kitchen Khausar har mamakin kanta take saboda
ƙosai da kunun gyaɗan da taci da safe, kana yanzu kuma Asma'u da kanta ta tuƙa mata tuwan Semovita
da miyar ɗanyen kuɓewa aƙaramin dining Dake kitchen ɗin suke zaune.

Khausar kam ta kasa daina mamakin kanta yanda take cin tuwon sosai kallon Asma'u da itama tayi wani
irin kyau na ban mamaki tayi ta fito a asalin amarya tace.

“Wallahi Asma'u har mamakin kaina na keyi rabona da abinci hakafa nafi wata huɗu”.

Murmushi Asma'u tayi tare da cewa.


“Ikon Allah baby ɗan albarka yasan yazo garinsu kenan”.

Murmushi Khausar tayi tare da sunkuyar da kanta ta ɗan kalli cikin,

dai-dai lokacin kuma suka jiyo sallamarsu Didi sun shigo gidan cikin wani irin...

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

66

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/HCji7xLpR1VEJGYcZJMP6k

KAZAURE COLLEGE OF NURSING SCIENCES (KCONS)

Lafiya Uwar jiki, Kuma sai da lafiya ake morar rayuwa. Kazaure College Of Nursing Sciences (KCONS) ta
kawo muku ingantaccen tsarin koyar da jinya da unguwar zoma, mun himmatu wajen samar da
kwararrun ma'aikatan jinya da unguwar zoma a fadin Nigeria da ma matakin duniya baki daya, a KCONS
mun tanadar muku kwararrun malamai, ingantaccen yanayi da tsarin koyo da koyarwa kai harma da
tsarin e-learning, ka zalika akwai tabbataccen tsaro a dakunan kwanan dalibai maza da mata, bugu da
kari kudin makaranta dai-dai aljuhu, KCONS munanan a lamba 5 layin fadar sarki dake kan hanyar kano
zuwa daura a Kazaure jahar Jigawa, za'a iya samummu a shafikanmu na facebook da instagram
@KCONsciences domin bayani, za'a iya tuntubanrmu a wadannan lambobin, 07066542055,
08035298851, ko shafin mu na yanan gizo @ http://kcons.edu.ng/admission KCON sciences kan turbar
aiki da kwarewa muka shahara.

66

Zare idanu Asma'u ta miƙe tare da kallon Khausar tace.

“Kamar su Didi ce suka shigo?”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da cewa.


“Ehem sune ya akayi?”.

Yarfe hannu tayi sai kuma ta girgiza kai kana tace.

“Wayyo Allah nikam zan fita ta ƙofar kitchen bana zaton zan iya haɗa ido da ita”.

Dariya ce taso kufcewa Khausar amma sai ta daure bata yiba tace.

“Meyesa?”.

Cikin sauƙe ajiyar zuciya Asma'u ta ɗan kalli ƙofar tare da faɗin.

“Wallahi kunyar su nake ji”.

Baki sake Khausar ke kallonta kafin tace.

“Dallah tafi daga nan muje ki gaishesu idan yaso sai mu tafi gidan Ummi tunda su suna nan”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Toh shikenan ”.

Kana suka fito Falon Khausar ce agaba Asma'u na biye da ita cike da kunya.

Didi na kallon Asma'u ta miƙa mata hannu tare da faɗin.

“A'a ɗiyata ƴar Albarka Masha Allah fatan mun same ku lafiya?”.

Kai Asma'u ta gyaɗa batare data kalleta ba kana ta gaishesu ɗaya bayan ɗaya.

Anutse Khausar da cikinta ya ƙara bayyana dabida samun cin wadataceccen abinci ta juya jin Lalla Hafsat
na cewa.

“Ƙanwata ya dai an samu anci abinci kuwa?”.

Murmushi Momy tayi tana kallon Lalla Hafsat tace.

“Dama bata ci abinci ko?”.

Kai Didi ta gyaɗa cike da tausayi tace.

“Ina kuwa take cin abinci sai dai tai ta shan fruits”.

Mommy na kallon Khausar dake sunne kai kana tace.

“Ikon Allah nan kuwa tunda tazo cikinta bai huta ba haba ashe shiyasa take ta ci ba sausauci”.

Asma'u ce ta karɓi zancen da cewa.

“Yanzu ma tuwo da miyar kuɓewa tana ɗa a kitchen kamar me”.


Khausar kuwa ɗan hararan Asma'u tayi.

Didi kam da mamaki ta kalli Khausar tare da faɗin.

“Ikon Allah Alhamdulillah ai haka akeso”.

Murmushi Lalla Khadijah tayi kana tace.

“Ai dama wani cikin hakane in Kaje unguwa sai kiga Kaci abinci idan kuma agidanka ne ba zaka iya ba”.

Ahankali Khausar ta sake kasa da kanta cike da kunya wani irin masifeffen kunya ne ya mamaye ta jin
yanda ake ta maganar tana da ciki.

Batare data ɗago kanta ba ta riƙe hannun Asma'u tare da cewa.

“Mu tafi”.

Miƙewa Asma'u tayi kana suka shiga bedroom ɗin Khausar ta dauko mayafinta kallonta Momy tayi tare
da cewa.

“Ina zaki je?".

Tana ƙoƙarin gyara mayafinta tace.

“Zamuje gidan Ummi ne”.

“Toh kin tambayi mijinki ne?".

Cewar Momy.

Murmushi Didi tayi kana tace.

“A Babu Matsala ai taje tunda ziyara ne”.

Miƙewa sukayi suka fita kai tsaye Side ɗin Hajiya Bunayya suka shiga bakinsu ɗauke da sallama.

Falon shiru ba kowa sake sallama Khausar tayi da ɗan ƙarfu.

Asiya dake bedroom ɗin tun ɗazu suna kukane tashin hankali d suke cikine ya hanata fitowa, jiyo muryar
Khausar ɗin ne yasa tayi saurin miƙewa ta fito idanunta cike da hawaye ga kumburar da sukatu Khausar
ta rungumeta tare da cewa.

“Oyoyo Khausar sannu da zuwa fatan kunzo lafiya? ya gida yasu Didi da kowa da kowa?".

Khausar na sake ruggume ta tace.

“Duk lafiya lau".

Ta ƙare maganar tana kallon idanunta da Fuskanta da suka kumbura alamar taci kuka da damuwa tace.
“Addah Asiya lafiya kuwa?”.

Ɗan Murmushi tayi tare da cewa.

“Lafiya lau Khausar ”.

Kai Khausar ta girgiza tana nazartan yanayinta tace.

“Amma Addah Asiya kamar kuka kika yi fa dan Allah ki faɗa min dakuwarki na tabbatar akwai abinda ke
damunki”.

Araunane Asiya ta maida hawayen dake ƙoƙarin zubo mata tace.

“Amina da Umma ce babu lafiya shiyasa hankalina yake tashe”.

Da damuwa Khausar ta kalli Asma'u da itama ita take kallo kana tace.

“Subhanallah me ya sami Aminan?”.

Ahankali Asiya tace.

“Bata da lafiya ne”.

Da sauri Khausar ta ɗan kalli Falon tare da cewa.

“Toh Ina take?”.

Bedroom ɗin Hajiya Bunayya ta nuna mata tare da faɗin.

“Tana ciki”.

Cike da kulawa da tarin tausayi tace.

“Toh mu shiga mana”.

Kai Asiya ta gyaɗa kana tayi gaba Khausar da Asma'u na biye da ita.

Suna shiga Idanunsu ya sauƙa kan Hajiya Bunayya dake zaune gefen gado tana sharɓan Kuka cikin sauri
Khausar ta ƙarasa shiga kana ta zauna gefen Amina ta riƙo hannunta acikin nata cikin raunin ganin halin
da Amina ke ciki tace.

“Innalillahi wa'inna alaihi raji'un Amina meyesa meki?,me yake damunki?,Ya ilahi ya mujibud da'awati ya
hayyu ya ƙayyum meye haka yake damunki?”.

Ƙasa furta komai Amina tayi sai hawaye dake ambaliya saman fuskarta kallonta ta mayar kan Asiya kana
ta cigaba da faɗin.

“Addah Asiya meke damunta?”.


Kai Asiya ta girgiza tare da cewa.

“Muma bamu san meke damun Amina ba”.

Muryanta na rawa tace.

“Yaushe taxo to?”.

Kai Asiya ta girgiza tare da faɗin.

“Abin sai ahankali Khausar am”.

Cikin matsanancin Kuka Amina ta damƙe hannun Khausar dake cikin nata kana muryanta cike da rauni
tace.

“Khausar ki yafemin”.

Da sauri Khausar tace.

“Ni kuma me kikayi min”.

Cikin rawan murya Amina tace.

“Ai ba abinda ban mikiba na cutar dake arayuwa Khausar ki yafemin”.

Cikin sauri Khausar ta girgiza mata kai Idanunta na zubda hawaye.

Hannunta ta ɗaura akan bakinta ta datake wani irin zaro harshe waje kana tace.

“Ba kiyi min komai ba Amina ki daina kuka Allah Ubangiji ya yaye miki abinda yake damunki Allah ya baki
lafiya Amina”.

Kallonta ta mayar kan Hajiya Bunayya jin yanda shesh-sheƙa kukanta ke tashi tace.

“Ummu kema kina kuka toh ita kuma ya zata yi aike zaki ƙarfafa mata guwwa!”.

Amaimakon tayi magana sai ta zame ƙasa ta gurfana gwiwoyinta gaban Khausar tare da riƙe hannunta
cikin wata raunatacciyar murya mai sanya tausayi tace.

“Khausar ki yafe min nasan na cutar dake a rayuwata na cutar da mahaifiyar ki nasan kin sani na cutar
daku”.

Ahankali Khausar ta cije gefen bakinta kana ta jujjuya kanta still hawaye na bin fuskarta tace.

“Bakomai Umma Allah ya yafe mana”.

Kuka sosai Hajiya Bunayya ta fashe dashi tare da cewa.

“Khausar na cutar daku da cutarwa mafi muni azaman da mukayi nasan ke kina zargina ”.
Kai Khausar ta girgiza tare da faɗin.

“Astagfirullah ai nima zargi nake Umma Allah ya yafe min kan zargin dana miki saboda Manzon Allah
Sallallahu alaihi Wasallama ya ce. _Azzannah Zhambu Walau kana haƙƙun_”.

Araunane Hajiya Bunayya ta girgiza kai tare da cewa.

“Ba zargi bane Khausar dagaske ne tunanin ki akaina, ina cutar daku gashi Allah ya muku Sakayyah
alokacin da bakuyi tunani ba ba kuma san ina yiba. Allah yayi muku Sakayyah alokacin da banyi Aune ba
don Allah Khausar ki roƙamin gafarar wurin Momynki ku yafemin”.

Asma'u kuwa cikin yanayin tsoro take kallon Amina data kasa tantance yanayin da take ciki.

Hajiya Bunayya kuwa cikin tarin nadama ta cigaba da faɗin.

“Kiga yanda Allah ya jarabceni kiga yanda Amina ta dawo kiga abinda Naseer ya mana Naseer yaje ya
cutar min da yarinya.

Jiya da yamma yazo ya wurgar mana da ita ya tafi ko shigowa cikin gidan nan baiyi ba.

Ya juya ya tafi yau ya tafi Indi'a yabar mu da jidali Uwarsa da Ubansa sai binmu sukayi da rashin
mutunci”.

Nan ra kwashe duk labarin da Amina ta basu na macijin da yake fitowa yasha nononta da yadda ta kasa
faɗawa kowa da kuma yadda yake hanata faɗa ta kara da cewa.

“Ashema shine yake juyawa ya zama macijin yayi ta shan nononta sai jiyan duk yake gaya mata ya aureta
ne dan tayi tsafi da ita ya samu biyan buƙatar rayuwar duniyar sa, yanzu kuma buƙatarsa ya biya ya
haɗota da takardar saki uku yazo ya wurgar mana da ita”.

Hawayen da yaƙi tsayawa Khausar ta share tare da faɗin.

“Innalillahi wa'inna alaihi raji'un Uncle Naseer”.

Sai Kuma ta juya ta kalli Asma'u da itama ita take kallo Asma'u kuwa cikin sanin muguwar ɗabi'arsa tace.

“Hmmmm Uncle Naseer zaiyi abinda yafi haka ma”.

Hajiya Bunayya kuwa cigaba da cewa.

“Khausar nasan Sakayyar abinda nayi miki ne nayi muku sihiri na biku da bita da ƙulli”.

Daga nan ta tsinke da surutai duk wani abu data aikata musu saida ta faɗa.

Khausar kam baki ɗaya ilahirin jikinta rawa ya fara cikin tsananin kiɗima mamaki da al'ajabi gami sa
tsoro.

Duk da cewa tana zarginta bata taɓa tunanin abin nata yakai haka ba.
Hajiya Bunayya kuwa miƙewa tsaye tayi sai kuma ta durƙusa tana ƙoƙarin naɗa zaninta tace.

“Khausar kiga yanda tsutsotsi suke cina yanda na dawo”.

Cikin sauri Khausar ta riƙe hannunta tare da cewa.

“Innalillahi wa'inna alaihi raji'un Umma kada ki nuna min Ummu kiyi addu'a Allah ya yaye miki kuma in
Sha Allahu nima zan miki addu'a nikam na yafe miki”.

Idanunta ta mayar kan Amina kana tace.

“Amina Allah ya baki lafiya Ubangiji ya yaye miki zan faɗa wa Yah Moddibo ya miki addu'a Allah yaye
miki kuma zan sa Dr Jameel zai zo ya duba ku in Sha Allahu Allah yaye muku ya baku lafiya mai amfani
mai albarka Allah ya yafe muku shurkar da kukayi”.

Da karfi Hajiya Bunayya ta fisge hannunta dake cikin na Khausar kana tace.

“Um-um Khausar ki bari in nuna Miki abinda ke cina kiga *Sakayya* data diromin”.

Cikin sauri Khausar ta girgiza kai tare da cewa.

“A'a Umma basai kin nuna min ba wannan bai kamata ba ai”.

Ta ƙarashe maganar hawaye na cigaba da kwaranya daga idanunta ganin ta da Amina ke wani irin
numfashi tana hura yayin da take zazzaro harshenta waje tana kaɗawa kamar yanda maciji keyi”.

Asiya kuwa ta gaza cewa komai sau wani irin kuka mai cike da ƙuna da ƙuncin zuciya da take yi tamkar
ranta zai fita.

Asma'u kuwa cikin yanayin tsoro ganin abinda Amina keyi ta shiga jan hannun Khausar dake zaune tana
cewa.

“Khausar mu tafi”.

Cikin dashewar murya da rauni Amina ta kalli Asma'u tare da faɗin.

“Ayyah Asma'u am ki barni in nemi yafiyarta”.

Kai Khausar ta girgiza cikin sake jin tsoron Allah da tsoron hakkin mutum tace.

“Amina wallahi na yafe miki duniya da lahira”.

Cikin sauƙe ajiyar zuciya tace.

“Toh kicewa Momynki ma ta yafemana”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da cewa.


“In sha Allah Momy zata yafe muku Momy kam ma bata riƙe ku ba”.

Asma'u kam.da ƙarfi taja hannun Khausar suka fita daga bedroom

Khausar kam wani irin tsoro gami da mamakine ya mamaye mata zuciya ganin yanda rayuwa ta juye
dasu suna fitowa compound ɗin gidan Samira Sani da Hajiya Lami na shigawo.

Samira na ganin Khausar ta nufeta tare da fashewa da kuka kana ta rike hannunta tare da cewa.

“Khausar! kece haka?”.

Cikin sanyin jiki Khausar ta gyaɗa mata kai tare da faɗin.

“Eh nice Samira ya gida”

Ta ida maganar tana kawar da kai gefe saboda wani irin masifeffen wari da take ji Samira kuwa cikin
rauni tace.

“Khausar ki yafe mana Khausar dubi yanda Allah ya dawo dani”.

Idanunta ta mayar kan cikin Khausar daya fara tashi kasancewar rigar jikinta lafaffiya ce cikin sanyi ta
cigaba da cewa.

“Ayyah Khausar dubi yanda Allah ya miki gata arayuwa sabida kin bishi, mukuma dubi yanda Allah ya
mayar mana da mugayen aiyukabmu damu”.

Hajiya Lami dake gefe wacce duk yanda Samira taso gudu ta barta batare data biyo taba sai da ta manne
ta biyota ta fashe da wani irin dariya mai firgitarwa kana ta tafe hannu tare da faɗin.

“Iyyeee sukam ai sunbi Allah sun samu yanda suke so mu da muka bi Bokaye baga nan sakamakon mu
yanda ya dawo ba Itama Hajiya Bunayya Stuliya ta ruɓe tsutsotsi na zuba ke kuma gaki nan kinata Yoyon
ruwa mai ɗoyi Ni kuma gani nan gani nan dai Ni ba mai hankali ba niba mara hankali ba”.

Cikin zubda hawaye Samira tace.

“Dan Allah Momy ki daina surutan nan”.

Ta wani zare idanu tana kallon Samira tace.

“Wani irin surutai zan daina ai gaskiya nake faɗa abinda muka aikata ne yoh tunda ma Allah ya ɓallomin
waɗanan sutura akwai wanda ya isa ya hanani zubasune ai nice nan mai tona asirinmu”.

Bisa alamu dai yadda take maganganu ƙwaƙwalwarta ya fara taɓuwa ne ta dawo sha tara sha tara haka
hankalin ya zama tara da indagi.
Khausar kam baki ɗaya ilahirin jikinta rawa ya fara Allah ya sani tana masifar tsoron Mahaukaciya ga
kuma Hajiya Lami dake nan atsaye ƙam kaman ƙiran Samudawa ga tsawo ga jiki da uban zuguda.

Asma'u kam cikin sauri taja hannunta suka fita dai-dai lokacin Haiydar da Bashir suka zo akan mashin
Bashir ya goyi Asma'u kana Haiydar ya goyi Khausar suka nufi gidan Ummi.

Suna isa Falon Ummi suka gaishe da Goggonayen Asma'u ƙannen Malam Ahmad da ƴan uwan Ummu
kana suka wuce bedroom ɗin Asma'u...

Suna zama dai-dai lokacin kira ya shigo wayar Khausar ahankali ta ɗaga ganin sunan Moddibo yasa tayi
picking.

Daga ɗaya ɓangaren ta tsinkayo sanyayyar muryansa na cewa.

“Minha”.

Cikin sanyi ta gyara zamanta murya cike da rauni tace.

“Na'am Yah Mu'allim”.

Cike da kulawa yace.

“Lafiya kuwa ya naji kinyi sanyi”.

Kai ta girgiza tare da cewa.

“Bakomai Yah Mu'allim?”

Da damuwa yace.

“Ina kike yanzu?”.

Ahankali ta ɗan lumshe Idanunta tare da cewa.

“Ina gidan Ummi ”.

Ɗan tsuke fuska yayi kana yace.

“Minha meyesa kike son yawo ne?.

Toma tukun meyasa da zakije baki kirani kin faɗa min ba”.
Still asanyaye tace.

“Yah Mu'allim kayi haƙuri nida Asma'u muka taho kuma Haiydar ne ya kawo mu”.

Da sauri ya zare idanunsa yace.

“Ya za'a yi Haiydar ya kawo? ki akan me ya kawo ki?”.

Numfashi ta fesar tare da faɗin.

“Akan Mashin ya kawo ni”.

Cikin bada umarni yace.

“Bana so kada ki sake hawa Mashin banaso”.

Kai ta gyaɗa tace.

“Yah Mu'allim kayi haƙuri bazan sake ba”.

Ahankali ya sassauta muryansa tare da gyara zamansa acikin mota yana kallon Dr Jameel da Zakariyya
yace.

“Tukunna ma yanzu menene matsalar ki naji duk kinyi sanyi”.

Muryanta na rawa irin na wanda ke gan da zubda hawaye tace.

“Yah Mu'allim Amina da Umma ce basu da lafiya sai kaga yanda suka dawo”.

Cikin rashin fahimta ya shafa sajensa tare da faɗin.

“Wacece Amina?”.

Cikin sauri tace.

“Yah Mu'allim ya za'a yi kace min wacece Amina ka manta Amina?”.

Ɗan shiru yayi sai kuma yace.

“Gaskiya na manta ta”.

Tana jinginar da kanta jikin gadon Asma'u tace.

“Wannan wacce muke zuwa makaranta tare Yah Mu'allim ya za'a yi kace baka santa ba”.

Numfashi ya fesar tare da cewa.

“Ok na tuna ta”.

Cikin sauƙe numfashi tace.


“Wallahi bata da lafiya”.

Ba yabo ba fallasa yace.

“Ayyah Allah yaye musu”.

“Ameen”

Ta amsa sai kuma tace.

“Ayyah Yah Mu'allim kayi ta musu addu'a Allah ya basu lafiya”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Toh Allah Ubangiji ya yaye musu ya basu lafiya”.

Ahankali ta gyara zamanta kana tace.

“Kuma inso samu ne dan Allah kasa Dr Jameel yazo ya duba su da jiki”.

Yana lumshe Idanunsa yace.

“Yanzu dai tukunna muyi Abin dake gabanmu Ni naji gaba ɗaya kinyi sanyi shine matsalata”.

Cikin tabbatarwa tace.

“Wallahi lafiya ta lau kawai dai jikin sune”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Ok toh Allah ya basu lafiya in Sha Allahu za'a yi musu addu'a kuma Dr Jameel zai zo ya duba su
hankalinki ya kwanta”.

Kamar yana gabanta ta gyaɗa masa kai.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da cewa.

“Toh yanzu bari muna zuwa dan Dr Jameel ma yana son ganin Asma'u”.

Kai ta gyaɗa kana sukayi sallama.

Ba daɗewa suka isa a waya Moddibo ya kirata tare tare da sanar mata sunzo yana dakin Bashir kana
Asma'u kuma ta samu Dr Jameel a mota.

Acan ɗakin Bashir kuwa cike da tarin kulawa taysayawa Moddibo ya jawota jikinshi tare dayi mata
sahihin rugguma, sai kuma yasa hannunsa duka biyu ya tallabo kanta wani irin amintaccen lasa tayi lips
inta duka biyu sai kuma ya fara yi mata wani irin amintaccen kiss mai saukar da nitsuwa salama da
mantar da ita duk damuwar dake tare da ita.

Hannunta tasa bisa sajenshi tana ɗan jujjuya yatsunta, mirginata yayi a kan jikinshi tare da gyara
kwanciyarsa bisa tattausar katifar Bashir dake zuwa amintaccen ƙamshi da watar tsabta.

Hannunshi ya cusa cikin rigartan tare da fara shafa cikinta.

Cikin tarin farin ciki ya zare harshensa daga bakinta tare da kallonta itanma shi take kallo cikin zare ido
saboda jin yadda cikinta ke wutsul-wutsul, da sauri ta fara nannaɗe rigar ta tare da turashi sama cikin ya
bayyana a fili, ido suka zubawa cikin baki ɗayansu, sai kuma tayi saurin kamo tattausan rafin hannunsa
tana mai ɗaurawa akan dai-dai inda cikin ke wutsulniya tare da cewa.

“Yah Salam Yah Mu'allim kaji yadda yake ta motsi irin motsin da Dr Jameel yake cewa zan fara ji da zaran
ya shiga wata na huɗu”.

Cikin tsananin farin ciki mara musaltuwa ya sunkuyo kan cikin tare da fara manna ma hot kiss tako wani
sashin na cikin bisa alamu jin daɗin ya hanashi mgn, ita kuwa Khausar hannunta ta cusa cikin sumar
kanshi tana cakuɗawa.

Sai kuma ta lunshe udanunta saboda jin sautin muryansa yana rero addu'o'in na musamman na kariya
yana tofawa cikin tare dasa mishi albarka.

Murmushin takeso ciki da jin daɗi tana mai ƙara shafa sajenshi da tuni ta fara rabashi sa nitsuwarsa.

Da sauri ta buɗe idanunta jin ya naɗe rigarta har sama har caɓɓullenta sun bayyana faresa, wanda zuwa
yanzu sun gama cika sunyi tamtsam-tamtsan dasu gwanin kyau.

Shyyyht taja wani irin amintaccen numfashi lokacin da taji ya manna sassayan tongue ɗinsa bisa kan
caɓɓullenta na dama kana yayiwa hannunsa na hagu masauƙi a kan na hagunta.

Wani irin amintaccen kana fitinennen salon sa bazata iya ƙi ko bujurewa ba ya fara yi mata, tuni ta fara
amsar saƙonninsa tare da maida masa amsar da tasa ya zare rigarta ya dire gefe kana ya zare tasa rigar
cin mancewa da inda suke ya fara ida nufinsa sosai ta amshi baƙocinsa gami dayi masa kekkyawar tarbar
da tashi sambatu da sanya mata albarka da yiwa J ɗinshi Addu'a.

Bayan kamar 50 minutes ne ya sahirta mata tare da jawota jikinshi yayi mata kekyawan rugguma cikin
sauƙe numfashi yace.

“Kai Minha Vidaa kwaɗayi yanzu a ɗakin Bashir ma, baki barniba saida kika tsotse min ɗan ruwan jiki”.

Cike da kunya tace.

“Yah Mu'allim banda sharri fa, ba kai bane ka fara”.

Da sauri yace.
“A'a ni kawai gaisawa nayi da Babyna nasa mata albarka, ke kuma kwaɗayi irin rabonki da abin daɗinki
tun a marocco, shine kakayi ta min kuka a waya to nazo na baki hankali ya kwanta ko”.

Cikin zazzafan shaƙuwa tace.

“Zan rama ai”.

Cikin yin murmushi yace.

“Ƴar al'barka matar aljanna ai uwar ƴaƴana gari na tuba kada arama”.

Cikin kwaɓe fuska tace.

“Toh Amman zaka tura Dr Jameel ya duba su Umma ko?”.

Ganin yadda duk tai sanyi ne da alamun sosai abin ya bugeta cikin sanyi ya,

rika kwantar mata da hankali har ta saki fuskarta kana cikin sanyi ta gyara zama tare da zayyane
Moddibo duk abinda ke faruwa.

Kansa ya girgiza tare da cewa.

“Ai dama haka rayuwa take Minha Duk wanda ya saki Allah ya kama wani yana tare da wahala
mabayyani.

Fatanmu Allah yaye musu zan sashe addu'a kuma batun asibiti yanda kika ce ɗin nan zaiyi wuya ai
maganin asibiti ya musu aiki sai dai suyi na Islamic sannan kuma a dage da addu'a kana ki yafe musu
domin Ubangiji yana son masu yafiya kinji Minha tunda dai Allah ya rufa min asiri basu samu damar
lalatamin duniyar jin daɗinaba abu ya komai kansu ai ni sai dai ince Alhamdulillah yanzu da ace suhirinsu
yaci ai da bamuji wannan daɗin da mukajiyar da juna yanzu”.

Cikin yin ƙasa da kai tace.

“Uhmmm da tuni ka sakeni dai ka koroni Nigeria na dawo da ƙafa”.

Cikin gsky da gaskiya yace.

“Wannan kuma duk rintsu duk wuya bazai taba faruwaba in sha Allah, da haka ta faru ina mai roƙon
Allah gwara in mutu kiyi takabana, shima kuma in Allah ya bani dama kafin in mutu sai na roƙi alfarma na
bar Miki watsiyar ko bayan raina kada ki sake aure dan bana son wani ɗa na miji yaji abinda nakeji a
jikinki bana son ko wani ɗa na miji ya kallemin abinda nake gani inji daɗi kayan marmarina nawa ne ni
ɗaya. Har abada babu wani mai mallakarsa, tunda J ya sadaukar min dashi, dama shi kaɗai ne a duniya
na iya yakicewa abin sona na sadaukar mushi dake”.

Cikin wani irin amintaccen so ƙauna da kuma ganin wutar kishinta a ranshi da idanunsa tace.

“Ni kuwa alfarma ɗaya nakeso in zan samu”.


Da sauri yace.

“Faɗi inji in zaki samu”.

Cikin tsananin bayyanar tsananin sonshi da kishinsa murya na rawa tace.

“Ni iyakar in ina rayene kaɗai bani son inga wata ya mace ta raɓeka, ta ganka a suffar da in na ganka a
haka nakejin cewa duk duniya ba macen da ta kaini dace, kana na tabbatar muddin nasan zakayiwa wata
ɗiya mace abinda kakemin a duk dare da muke kasance a muhalli ɗaya na sani zan mutu wlh zuciyata
zata buga na mutu”.

Wani irin amintaccen numfashi mai tafe da murmushin mai cike da tsananin farin ciki ya saki saboda
fahimtar kalamanta da ganin tsananin so da kishinsa cikin kwayar idanunta, sai kuma tayi saurin kallonta
jin ta saki sassayan kuka murya na rawa taci gaba da cewa.

“Amman idan har rigaka barin duniya ni na amince Yah Mu'allim kayi aure saboda nasan zamanka ba
mace, zai cutar da kai sabida nasan mijina inƙarman namijine ma buƙaci, Amman indai ina raye kada ka
haɗani da wata nayi alkawarin zan ɗauki dukkan buƙatar ka don mallakar ka ni ɗaya, shiyasa nakeso kayi
min alkawarin bazaka haɗani da ko wacce ya maceba a fagen mallakarka”.

Cikin sanyi yasa rafin hannunsa bisa kuncinta yana share mata hawaye sai kuma ya ɗaga mata girarsa
ɗaya cikin sahihiyar murya yace.

“Sai nayi nazari zan baki amsa sarkin”.

Cikin rauni tace.

“Sai kayi nazari kuma ni yanzu nakeso kayi min alkawarin”.

Cikin kauda mgnar yace.

“Da fari ki yafewa su Umma tunda basu samu damar rabaki da mijinki ba, muna nan tare zanyi ta baki
abin daɗinki”.

Ya ƙare maganar cikin son kauda tunaninta da waccar mgnar alkawarin.

Kai ta gyaɗa kafin tace.

“Ai dama Ni na yafe musu Yah Mu'allim Kuma zan faɗawa Momyna ma ta yafe musu”.

Cikin son sama mata nitsuwa da sassauta zazzafan kishinta daya motso yace.

“Toh yanzu ki kwantar da hankalinki in Sha Allahu zasu samu lafiya ai babu abinda yafi ƙarfin Allah”.

Kai ta gyada tare da faɗin.

“Hakane”.
Haka dai ya cigaba da kwantar mata da hankali da kauda mgnin ta.

Acan ɓangaren Dr Zakariyya kuwa shima yana tare da Asiyansa.

Bayan Sallar la'asar Moddibo ya maida Khausar gidan Momy.

Akuma dai-dai lokacin Didi dasu Lalla Khadijah Lalla Hafsat suka tafi hakan ya bawa Khausar daman ke
ɓancewa da Momynta kasancewar kowa ya watse cikin sauƙe numfashi Khausar ta kalli Momy tare da
cewa.

“Momy ashe Amina da Umma basu da lafiya?”.

Zama Momy ta gyara tare da faɗin.

“Ke dai bari Khausar Rayuwar Nan abin tsoro ne jiya-jiyan nan Naseer yazo ya kwantar da Amina a ƙofar
gida abakin gate fa ko ciki bai shigoba ya juya barta”.

Da sauri Khausar ta dafe ƙirjinta Momy kam cikin sanyi ta cigaba da cewa.

“Babu ma wanda yasan ya kawo ta Haiydar ne ya dawo ya ganta akwance da Ghana Masgo ɗin ta da
yake tana iya magana ne shine tace shi ya kawo ta ya ajiyeta ya juya ya tafi kuma taji yana waya kan
cewa yau zai koma Indi'a kuma ma ya tashi ya tafi”.

Zuwa lokacin kam hawaye sunƙi tsayawa akan kuncinta.

Cikin sauƙe numfashi Momy ta cigaba da faɗin.

“Koda Lamiɗo yaje wajen Mahaifinsa sai cewa yayi ina ruwansa tunda shi da Naseer ƴan Uwa ai shine
bare a ciki, kar a wani sashi a ciki, kar kiga yanda Amina ta dawo Khausar Rayuwar Nan wanda bai ji
tsoron Allah ba ya wahala Kinga dai wannan ya ishe ki ishara”.

Khausar na zubda hawaye ta gyaɗa kai tare da faɗin.

“Momy da naje duba su sunata bani hakuri tare da faɗe-faɗe abubuwan da nake faɗa Miki ina zargin
Umma ita da bakinta tayi ta min faɗe-faɗe Hajiya Lami kam naga kamar ma ta haukace”.

Cikin sanyi da al'amarin Momy tace.

“Hmmm sosai ma tayi ta ife-ife daga bisani mijinta yazo ya ɗauketa yace gata ɗaya zaiyi mata ya Kaita
gidan mahaukata.
daƙyar aka samu aka ɗauke ta aka fitar da ita ƴarta ma cewa tayi tana tsoronta.

Lamiɗo kuwa kullum binshi nake yakai su asibiti yaƙi ance kuma ya ɗaga Auren Asiya tun da ga jikin
Mahaifiyarta da ƴar uwarta ba lafiya yace babu wanda ya isa ya hana suje can su ƙarata da zunubin su”.

Cikin jimami Khausar ta tallafe kuncinta tare da cewa.

“Kai Rayuwar Nan Allah dai yasa mu cika da imani” .

Cikin sanyi jiki Momy tace.

“Amin ya Allah, haka rayuwa take dan kayi abu a ɓoye Allah na ganin ka gashi yau yaya da kanta ta fito
take ta faɗamin abubuwan da tayi ta min da bakinta, wai harda cewa ita ta kashe min Ramadan nace a'a
ni karya ɓatamin gawar ɗa, dan dama tunda yayiwa wannan haɗarin garin gwaje-gwajen aga kanshi bai
buga aka gane cewa yana da cutar brean Cancer.

A lokacin ma sunce ya cinye kaso biyu cikin uku kanshi shiyasa ko mgnin basu bashi ba.

Ni nasan kuma Abbanku ma ya sani kune dai bamu faɗawaba.”

Cikin zubda wa Khausar tace.

“Allah Sarki Ramadan Allah ya jiƙanshi”.

Cikin sanyi Momy tace.

“Amin ya Allah kinga

ni dai na yafe mata kema ki yafe mata”.

Tana shafa cikinta tace.

“Na yafe mata Mommy, kuma in sha Allah duk randa na haifi mai kama da Ramadan tun asibiti zan
bakishi ya meye Miki madadin Ramadan ɗinmu ki raineshi”.

Murmushin jin daɗin Momy tayi tare da cewa.

“Allah ya sauƙeƙi lfy Khausar am ki raini abinki da kanki Mamana”.

Cikin kunya ta ce

“Amin ya Allah”.

Sai kuma ta kalli Momy jin tana cewa.

“Wata nawa ne yanzu”.


Kai ta ɗan sunkuyar tare da cewa.

“Wata uku ne ya shiga na huɗu”.

Kai Momy ta jinjina.

A wannan ranan haka Momy da Khausar suka yi yammacin suna hira.

Da daddare bayan an idar da Sallar Isha'i Moddibo yazo ɗaukarta.

Bayan Moddibo yazo suna hira Momy ta kalli Khausar tare da cewa.

“Khausar kawo masa abinci”.

Kai Khausar ta gyaɗa kana ta miƙe ta shiga kitchen ta kawo masa.

Gabanshi ta zauna tare da matso da warmars ɗin.

Tuƙeƙƙen tuwon shinkafa da miyar kase wanda yaji man shanu, da kifi haɗi da nama.

A plate ta zuba masa mai ɗan yawa kana ta ajiye masa agabansa tare da sa kishi sassayan kunun ayan da
Momy tayiwa su Didi cika cup ɗin tayi kana ta koma bisa kujerar.

Gyara zamansa tare da cewa.

“Toh saƙƙo muci”.

Kai ta girgiza tare da shafa cikinta tace.

“Um-um ai na ƙoshi”.

Ɗan ware idanunsa yayi tare da faɗin.

“Kin tabbatar?”.

Cikin gaskiya da gaskiya tace.

“Wallahi naci Yah Mu'allim”.

Kai ya girgiza yana mai tsirawa cikinta idanu yace.

“Ban yarda ba”.

Raudat dake shigowa ta kallesa tare da cewa.

“Wallahi taci da yawa Yah Moddibo Addah Khausy yau tunda tazo sai tuwo take ta ci”.
Cikin mamaki ya kalleta tare da faɗin.

“Da gaske?”.

Daidai lokacin kuma Momy ta fito daga bedroom ɗin ta cikin shiri wanda da alamu Side ɗin Lamiɗo zata
tafi, cikin yin ƙasa da Moddibo ya kalleta kana yace.

“Momy wai dagaske taci abinci?”.

Murmushi Momy tayi tare da gyaɗa masa kai tace.

“Wuuuu ai Khausar yau ko Gara nan ya barta acin abinci ai daga safe zuwa yanzu taci abinci ya kai sau
bakwai”.

Cikin mamaki yace.

“Ikon Allah Momy bata cin abinci a gida fa”.

Momy na ƙoƙarin fita tace.

“Aikam haka su Didi suka faɗa amma nan kam tana ciki inaga duk yunwar data tara take sauƙewa”.

Cikin farin cikin daya kasa ɓoyewa yace.

“Alhamdulillahi”.

Bayan fitan Momy yafara cin abinci suna ɗan taɓa hira.

Suna cikin hirar Momy ta dawowa zuwa wannan lokacin already Moddibo ya gana cin abincin har
Khausar ta kwashe kayan kallon Khausar yayi tare da cewa.

“Toh mu tafi dare yana yi momy zamu tafi dare yayi”.

Ya ƙare maganar yana kallon Momy.

Ɗan murmushi Momy tayi tare da faɗin.

“Toh Allah ya bamu Alkhairi”.

Kallon Khausar dake zaune yayi kana yace.

“Minha mu tafi ko?”.

Kallonsa tayi tare da faɗin.

“Ba anan zan kwana ba?”.

Yi yayi kamar bai jita ba sake langwaɓar da murya tayi cike da shagwaɓa tace.

“Ayyah ka barni in kwana mana”.


Still yi yayi kamar bai jita ba ya ma Mai da kallonsa kan Momy yace.

“Momy zamu tafi dare yayi”.

Kai Momy ta gyada tare da faɗin.

“Allaj ya bamu Alkhairi ku gaida su Didi”.

Cikin sauri da lumshe ido Khausar tace.

“Dan Allah kabarni in kwana mana”.

Juyawa yayi ya kalleta kana ya kalli Momy da tayi shiru alamar tana son ƴartata ta kwana.

Har ga Allah baison barinta ta kwana amma ganin yanda Momy tayi shiru tana Murmushi yasa shi kallon
Khausar data langwaɓar da kai da kuma yanda akace tana cin abinci yasa shi fesar da numfashi tare da
faɗin.

“Shikenan zo muje ki rakani”.

Da sauri ta ɗan ware idanunta tace.

“Kenan ka barni in kwana?”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Eh ba damuwa amma muje in Baki saƙo amota”.

Cike da farin ciki tace.

“toh”.

Kana ta miƙe tabi bayansa.

Cikin tsananin jin daɗi momy ta rakasu da ido domin ta samu cikekkiyar gamsuwa akan mutumunci da
kulawar Modibbo da iyayensa akan ɗiyar tata.

Mazaunin Driver ya zauna yayin da ta zauna gefen mai zaman banza janyota jikinsa yayi kana ya ɗaura
hannunsa akan cikinta tare da faɗin.

“Minha bana son barinki ki kwana awani waje batare dani ba amma yanda kika nuna agaban Momy ba
yanda zanyi”.

Cikin sanyi tace

“Kayi haƙuri Yah Mu'allim nayi kewar Momyne”.


Cikin lumshe idanu yace.

“Shikenan ba komai”.

Ya ƙarashe maganar yana ɗaura hannunsa akan cikinta ahankali tace.

“Kayi haƙuri ”.

Kai ya girgiza tare da cewa.

“Bakomai”.

Cikinta yake shafawa kafin ya buɗe tafin hannunsa ya karanta _Ƙulhuwa³ Falaƙi³ Naasi³ Ayatulkursiyyu¹
Amanarrasulu ¹ Laƙadja'akum¹_ ya shafa mata cikinta tare da faɗin.

“Toh Allah ya kare ki ya kare min Babyna saboda banason Maƙwabtakanki da Hajiya Bunayya tsoronta
na keji akan abinda tace ta miki”.

Kai ta girgiza tana sake lafewa jikinsa tace.

“Bakomai in Sha Allahu ba abinda zai samemu tunfa addu'o'inka na tare damu”.

Cikin sanyi yace.

“Dan Allah Minha kada ki kwanta bakiyi alwala ba kuma kiyi addu'a Kinga Bama tare bare inyi miki”.

Cikin shaƙar ƙamshin jikinsa tace.

“In sha Allah zan yi kuma Momy nayi min yadda kake min”.

Cikin jin gamsuwa yace.

“Ayyah Mommy Allah ya bar mana su ”.

Amin. tace tana shafa sajenshi.

Bayan sun sake taɓa hira ya rakata har ƙofan Falon Momy sai da ta shiga kana ta juya ya koma.

Ita kuwa Momy hannun Khausar ta kalla.

Ummmmm tace saboda ganin ba wani saƙo kawai so yake ya kebe da matarsa fahimta haka ya sata
mgnar.

“Uhmmm kaddai in shiga haƙƙinshi shi da matarsa”.

Sai kuma ta kalli Khausar dake matsar da Raudat gefe tare da kwantawa kusa da Momy tana cewa.

“Yau dai ke zaki koma gefe ni zan kwanta kusa da Mommy na”.
Murmushi Momy tayi tare da cewa.

“Je kiyi alwala tukun”.

Toh tace kana taje tayi alwala kana tazo ta kwanta nan sukayi ta hira.

Washe gari bayan an idar da Sallar Asbah duk su Abualeey sun koma gida.

Moddibo kuwa karatun ƙur'ani ya fara daga bisani yayi Azkhar.

Takwas dai ya miƙe ya nufi gida.

Har ya nufi bedroom ɗinda sai kuma ya fasa key ɗin motarsq dake kan Dinnin table ta ɗauka, kana ya fito
kai tsaye mota ya shiga.

Tare da nufan gidan Momy haka nan yake ji yayi mugun missing ɗin ta ji yake kamar ya ɗauki wasu
kwanaki bai ji ɗumin baby nai ba.

Yana Parking motar aharabar gidan ya hango Haiydar da Bashir wanda yanzu ya dawo gidan da kwana
saboda baƙin da suka cika gidansu.

Suna ganinsa suka isa wajensa tare da cewa.

“Yah Moddibo Barka da safiya”.

Cikin sakin fuska yace.

“Yawwa Haiydar Barka dai”.

Su Haiydar ne sukayi nasa jagora zuwa Falon Lamiɗo bayan sun gaisa Lamiɗo yace.

“Nima yanzu nake shirin zuwa wajensu Abualeey”.

Anutse Moddibo ya ɗan sunkuyar da kansa ƙasa tare da cewa

“Ayyah ai suna na tare da Abban Jameel ma da Malam Ahmad”.

Kai Lamiɗo ya gyaɗa tare da kallon su Haiydar kana yace.

“Ku isa dashi”.


Kai suka gyaɗa tare da fita kana ya miƙe yabi bayansu.

Dai-dai lokacin kuma Momy na kitchen.

Yayin da Khausar ke kwance kan 3sitter.

Suna isa bakin Falon Haiydar ya kalli Moddibo tare da faɗin.

“Yah Moddibo ka shiga ”.

Kai ya gyaɗa kana yace .

“Ok”.

Sai kuma ya kalli Bashir tare da cewa.

“Ina zakujo”.

Cikin shaƙuwa Bashir yace.

“Adda Asma'u ce ta matsa mana da kira wai muje mu amso mata ɗinkunanta”.

Kai jinjina musu, daga nan ya nufi cikin ɗakin.

Kana suka juya da alamu aikan zasu tafi.

Ahankali Moddibo ya shiga Falon bakinsa ɗauke da sallama.

A hankali ya lumshe idanunsa kana ya buɗesu sabida hango Khausar kwance bisa 3 sitter. Falon shiru ba
kowa sai sassayan ƙamshi da sautin TV can ƙasa da ake addu'o'in azkar.

A hankali idanunsa suka suke yawo a kanta tana bacci cikin kwanciyar hankali wanda ga duk kan alamu
tana jin dadin bacci..

Sai kuma plate dake gabanta da cup wanda ke da guntun tea a ciki sai plate ɗin dake da alamun indomei
ne taci a ciki kafin tayi baccin.
Anutse ya ƙara sa tsakiyar Falon tare da zama agefenta daga ƙasa ahankali ya ɗaura hannunsa dai-dai
kan fuskarsa kana yasa babban yatsansa kan gashin girarta ya kwantar.

Ahankali ta fara jin alamunsa akusa da ita yayin da take zuƙan ƙamshinsa ahankali ta buɗe ido ta kallesa
fuskar ya shafa cikin wata sanyayyar murya yace.

“Barka da safiya me kyau ko Babu kwalliya”.

Idanunta ta sake lumshe jin yanda sautin muryansa ya ratsa ainihin ƙoƙon zuciyarta.

Moddibo kuwa ahankali ya kamo tafin hannunta tare da ɗaurawa asajensa kana ya motsa laɓɓansa tare
da cewa.

“Na kasa juriya rai kin ka kwana tun jiya”.

Da wani irin sauri Khausar ta damƙe hannunsa dake cikin nata jin wani irin nutsuwa da farin ciki. cikin
nutsuwa da zaƙin muryansa ya cigaba da faɗin.

“Ko rufe ido nayi kece kaɗai nake gaaaani kin wadaci zuciyata ba wacce zata rarrafo”.

Hannunsa ya mayar kan lips ɗin ta yana shafawa ya cigaba da cewa.

“Tattalinki zan kamar ya ƙwai”.

Cikin jin daɗi ta matso da kanta ta ɗaura asaman tafin hannunsa cikin tarin ƙaunarta ya kashe mata ido
ɗaya tare da cewa.

“Duk abinda kin kaso akwai, babu wacce zata ji da kai gareni dan ni ina da Gimbiya”.

Da hannu ta nuna kanta alamar Ni ya gyaɗa mata kai yana shafa sumar kanta yace.

“In kiraki Layla ne ko Majnuniya”.

Ahankali ta ɗan mike tana jin wani irin farin ciki da nutsuwa yayin da wani irin ƙaunarsa ke fusganta
ganin yanda ta kwanto jikinsa ya sanya shi kuma ahankali ya janyota tare da rungumeta tare da man....

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

67
Tallah !! Tallah !!

Shahararriyar Marubuciyar nan Ikilima Adam (kyauta daga Allah) wacce ta nishadantar daku a littafin ta
mai suna *Kanwata* *kaikajawa kanka , *Rai daya janzaki*.

Yau na sake dawowa domin Domin tallata muku Littafaina mai Suna *(RUDANI )* Da kuma *Makauniyar
Shari'a* littafine mai kunshe da Butulci , cin amana ,zagon Kasa , soyayya irin ta gani kasheni , aminci da
saura n su basai n'a cika Ku da surutu ba Hausawa sukace Gani yakori ji.

Karku Manta *Makauniyar Shari'a* sabon littafi ne mai bibiyar Ma'anar sunan sa.

Ya zarce duk littafai na , na baya.

RUDANI littafine mai cike da Rudani da ban Al'ajabi , duk wacce kika fi buƙata zaki biya kudin sa Naira
ɗari biyar kacal.

Farashin kowannen su Naira Dari biyar ne 500 kacal

Domin Karin bayani Ku tuntubeni a lambata kamar haka (09069080725 ko Kuma + 22953726162 ) wacce
Bata shirya Siya ba kada mu batawa juna lokaci.

Domin aikawa da kudi kai tsaye . 3115484026 ikilima Adam first bank

Turo shaidar biya akan wannan 09069080725 sai najiku.

67

Ahankali ya shaƙi ƙamashin jikinta tare da kallon plate da cup dake gabanta wanda da alama akwai
abinda taci kafin ta bin ba ba kwanta.

A dai-dai lokacin kuma Momy ta fito daga Kitchen idanunta suka sauƙa akan Moddibo dake zaune a
hannun kujeran Khausar na zaune gefensa ta manna kanta da kafaɗarsa yayin da hannunsa ɗaya ke
bayanta yana shafawa ganin haka yasa Momy saurin komawa kitchen.

Ahankali Moddibo ya ɗago kansa tare da kallon ƙofar Falon jin sautin muryan da ko agigin bacci ya farka
zai gane ta muryan Hajja Nana.
Khausar kuwa cikin yanayin baccin da take ji ta buɗe idanunta ta kalli Hajja Nana sai kuma ta maida
idanunta kan Moddibo ahankali ta sake maida idanunta kan Hajja Nana tare da cewa.

“Da sassafen nan?Wannan wani irin sammako kika yi?”.

Cikin sauri Hajja Nana ta kallesu tare da faɗin.

“Toh ƴar nema wato karota ma kike yi?,Ni ina nan tunda kuka zo na gaza bacci ina ta begenki ina son
ganin ki shiyasa ana fitowa masallaci nace wa Baffa Liman da Abba su kawoni amma shine kike cewa nayi
sammako toh ai ba gidanki naje ba sai ki bari idan gidanki naje kiyi min iyaka da zuwa”.

Murmushi Moddibo yayi kana yace.

“Toh ki zauna mana kina tsaye”.

Kai ta gyaɗa tare da ƙarasawa tsakiyar falon madadin ta zauna kan kushin sai ta zame ƙasa ta zauna tare
da kamo ƙafafuwan Khausar ta fara jan yatsun sai kuma ta maida idanunta kan cikinta cikin mamaki ta
riƙe haɓa tare da faɗin.

“Ohhh Allah mai iko, Allah mai kyauta da daɗi”.

Sai kuma ta maida kallonta kan Moddibo.

Moddibo kuwa kansa ya ɗan jujjuya kana ya juya ƙwayar idanunsa sai kuma ya sanya hannunsa na dama
ya shafa sajensa ya fahimci kallon cikin Khausar yasa take yi masa kallon irin sannu. Jarabebbe
mayatacce har ka ɗirka mata ciki? fahimtar hakan yasa ya kauda kansa.

Hajja Nana kam ganin yanda ya jujjuya idanunsa yasa ta jinjina kai tare da faɗin.

“Hmmm Allah Ubangiji ya shirye ka ke kuma Allah ya sauƙeki lafiya”.

Cike da kunya Khausar ta sake manna kanta da kafaɗan Moddibo kana ta motsa laɓɓanta ta furta.

“Ameen”.

Cikin ɗan ɗaga sautin murya Moddibo yace.

“Amin Amin Ameen ya Allah, Allah ya amsa addu'ar ki mun gode da addu'a”.

Kallonsa tayi tana mamakin yanda zamani ya sauya sukam a zamaninsu ko kusa da makamancin wannan
ba'a yi ga yadda ya wani ƙwaƙumeta a farkon surka.

Momy dake kitchen kuwa jiyo kaman muryan Hajja Nana yasa ta leƙo.

Ganin tabbas Hajja Nana ce yasa cikin sauri ta fito tare da cewa.

“A'a Hajja Nana, dama naji kamar Muryar ki na dan kasa kunne ashe dai ke ɗin ce”.
Murmushi Hajja Nana tayi kana tace.

“Wallahi fa tun randa mukayi waya kika cemin tazo nake ta son zuwa washe garin ranan kuma Mashin
ɗin Abba ya samu matsala shine malam Liman yace na bari sai yasa mai a mota kafin muzo, tunda zai zo
ya marabci su Abualeey yanzu ma tare muke suna falo da Lamiɗo”.

Kai Momy ta gyada tare da faɗin.

“Kai Masha Allah sannun ku da zuwa.

Ahankali Moddibo ya juya da naiyyar gaisheta

Sai ya ga har ta shige kitchen Momy kuwa already ta gama haɗa breakfast Sultan Cheaps ta soya wanda
yaji Vegetables da naman rago mai laushi sai kuma Ƙosai data soya wanda keta tururi wanda Khausar ce
tace tana so sai kuma Koko wanda duk zaɓin Khausar ne sai kuma tea dake ƙamshin Kanunfari, Citta
Na'a'na'a ta fito dasu.

Anutse. Moddibo ya sunkuyar da kansa kana yace.

“Momy Barka da safiya".

Cike da kulawa tace.

“Barka dai Moddibo ka iso?”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Eh Momy ina kwana”.

“Lafiya lau Alhamdulillah ya gida”.

Kallonta ta mayar kan Khausar tace.

“Ki tashi ki samu ku abinci kuci”.

Juyawa Khausar tayi tare da kallon Momy kana tace.

“Momy kinyi min ƙosan?”.

Kai Momy ta gyaɗa cike da tarin ƙaunarta tace.

“Nayi miki mana ai dole na inyi miki”.

Hajja Nana dake cigaba da matsawa Khausar Kafa tayi dariya tare da faɗin.

“Aikam dole kiyi mata naga abin na musamman ne”.

Baki Khausar ta ɗan tura tare da hararan Hajja Nana kana ta ɗan janye jikinta daga na Moddibo wanda
shi har ga Allah yama manta Momy na wajen jin ta ɗan matsa ne yasa ya kalleta.
Ganin yana kallonta yasa ta juya mishi ido alamar yaga Momy na nan.

Fahimtar hakan yasa ya gyara zama sai kuma ya zame ya zauna akan tattausan Carpet ɗin ya zamana
suna fuskantar juna yayin da Hajja Nana ke gefensu.

Kulan farkon ta jawo ta buɗe idanunta suka sauƙa akan ƙosan dake zuba wani irin tururi da ƙamshi ajiyar
zuciya mai sanyi ta sauƙe irin yanda duk wata mai ciki keji asanda ta samu abinda take so.

Flaks din dake gefe ta jawo ta buɗe sai taga tea.

Fuska ta kwaɓe kamar za tayi kuka tace.

“Momy kunun fa?”.

Momy na ƙoƙarin janyo Flaks din gabanta tace.

“Gashi nan ki buɗe mana ki gani ke kina da ci da zuci”.

Ɗan Murmushi tayi kana ta buɗe tare da cewa.

“Kai Momy Ubangiji Allah yabar min ke Allah ya miki Albarka Ubangiji ya miki sakayya da gidan Aljanna”.

Murmushi momy tayi tare da faɗin.

“Ameen ya Allah Mamana”.

Murmushi Hajja Nana dake gefe tayi kana ta kalli Khausar sai kuma ta kalli Momy ahankali tace.

“Ubangiji Allah ya rabaku lafiya”.

Cikin sanyi Khausar tace.

“Ameen”.

Moddibo kuwa fuskarsa ɗauke da murmushi ya gyara zama tare da cewa.

“Ameen ya Allah aini ina ga yau tukuici na musamman zan banki tunda kika zo kike mana addu'a da
fatan Alkhairi ”.

Baki Hajja Nana ta taɓe tare da cewa.

“Allah yasa dagaske kake”.

Cikin tabbatar wa yace.

“Dagaske nake mana ai ina ga ke tare zamu tafi dake kiyi ta mana addu'ar nan sannan kiyi ta kula mana
da ita”.

Ɗan zare idanu Hajja Nana tayi kana ta hararesa tace.


“Kunyi ƙarya nikam bazan zama mai aikin kuba kuda gacan innare kuna tare da ita ai magana ta ƙare duk
kular da kuke buƙata zaku samu”.

Kai ta jinjina kana tayi Murmushi tare da faɗin.

“Aikam itama munzo dasu jiya ma take cewa tana son zuwa wajen ki sai Khausar ke cewa ai kema zaki zo
shiyasa bata jeba”.

Ɗan gyara zama Hajja Nana tayi tare da faɗin.

“Aikam toh shikenan”.

Khausar kuwa ƙosai ta zuba kusan guda goma kana ta zuba Kokan sai kuma ta zuba wa Moddibo Sultan
Cheaps da Perpe Chicken mug ta ɗauka ta haɗa masa tea mai kauri.

Hajja Nana ma ƙosan Khausar ta zuba mata tana kallon ƙosan da yayi kyau a ido ta kalli Momy tace.

“Ƙosan ya isa haka, asamin shayi sai ahaɗa min da biredi”.

Kai Momy ta gyaɗa kana ta miƙe ta ɗauko Bread Mai yanka-yanka Karɓa Hajja Nana tayi ta shiga haɗa
breading, ƙosai da tea tana sha.

Khausar kuwa Ƙosai da Kokon ta shiga sha cikin tsananin mararin abin.

Ahankali ta gutsiri Ƙosan da cikin tsakiyarsa ke ɗauke da diddigin nama kana ta kuma kurɓan kokon daya
sha kayan ƙamshi yawun bakinta sai tsinkewa yake saboda yanda ya mata masifar daɗi.

Moddibo kam cike da mamaki yake kallon yanda Khausar ke cin ƙosai da Koko tsakaninta da Allah.

Hajja Nana dake kai biredi da Ƙosai baki ta kalli Moddibo daya zubawa Khausar idanu yana cew.

“Ni mamaki nake bata cin abinci fa agida”.

Murmushi Hajja Nana tayi tana kallon yanda Khausar ke shan Koko tsakaninta da Allah tace.

“Ai dama haka wani yake in dai yana da ciki baici agidansa amma da zaran yaje unguwa zai ci abinci”.

Kansa ya girgiza tare da cewa.

“To ai can ko munje gidan Lalla Khadijah bata cin abinci amma kinga tunda muka zo nan cin abinci fa
takeyi”.

Momy dake fita zata kaiwa Abba da Man Liman nasu tayi Murmushi tare da faɗin.
“Sosai ma kam tunda aka zo nan abinci take ci babu kama hannun yaro taci ta ƙara ɗayan daren ma
munyi hira mun gama tace min yunwa take ji sai da naje na dama mata Quaker oats tasha kafin tayi
bacci”.

Cike da farin Moddibo ke sakin murmushi yana kallon Khausar dake ɗan Cunno baki gaba Momy kuwa
idanunta akan Hajja Nana ta cigaba da cewa.

“Sannan da safe kafin ta kwanta plate da kuka zo kuka samu shima indomei taci tasha tea kafin ta
kwanta tayi bacci anan gashi yanzu ma tana ta ɗurawa”.

Langwaɓar da kai Khausar tayi tare da faɗin.

“Toh Momy yunwa nake ji na daɗe bana cin abinci fa”.

Dariya Momy tayi kana tace.

“Keee dama haka kike da cin abinci nayi mamaki ma da akace wai ciki ya hanaki cin abinci.

Don banyi tunanin akwai abinda zai hana ki cin abinci ba, tunda ke ciwo ma baya hana ki cin abinci”.

Kanta ta sunkuyar ƙasa ta cigaba da cin ƙosanta kallonta Moddibo yayi ganin ta gama cinye duk ƙosan
hannu tasa ta sake janyo kular ɗan ware idanunsa yayi tare da faɗin.

“Minha bazai Miki yawa ba?”.

Kallonsa tayi sai kuma ta girgiza kai tace.

“Um-um kaɗan zan ƙara naji cikina ya ƙoshi amma bakina bai gaji dashi ba”.

Yana rufe kulan yace.

“Toh ki bari sai anjima”.

Marairaice fuska tayi ganin haka yasa Momy cewa.

“Ki bari na rage Miki ƙullu a fridge idan kina so anjima zan sake soya miki ”.

Gyatsa tayi kana ta gyaɗa kai tare da faɗin.

“Toh shikenan”.

Ta ida maganar tana jingina bayanta da jikin kujera.

Ahankali Moddibo ya matsa kusa da kujeran da take ya ɗan jawota jikinsa tare da cewa.

“Zo, Zo zonan kada ki kwanta, ki ɗan zauna tukun mu samu abincin yabi jikinki”.

Ya faɗa yana manna kanta da kafaɗarsa yayin da hannunsa ɗaya ke kan cikinta yana shafawa shi kuma
yana cigaba da cin abinci da hannunsa na dama.
Ahaka suka gama cin abinci suna taɓa hira jefi-jefi.

Suna gama cin abinci Momy ta shigo idanunta akan Khausar tace.

“Toh tashi ki tattare wurin”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Toh”.

Kana ta yunƙura zata miƙe.

Ahankali Moddibo ya kalli Momy kana yace.

“Momy bari na tattare”.

Ɗan ware idanu Momy tayi kana tace.

“Ta isa tana zaune ka tattare mata kwanika”.

Cikin sanyi yace.

“Momy toh ta gaji ne kuma ta cika cikinta da yawa bata son motsi”.

Kai Momy ta girgiza tare da faɗin.

“Aikuwa dole tayi motsi maza tashi ki tattare su”.

Ta ƙare maganar tana kallon Khausar.

Hajja Nana dake kallonsu ta ɗan taɓe baki tace.

“Kai dai kai dai kam wannan akwai ka da tsirfa iri-iri yo in Mai ciki bata motsa jiki ba mai za tayi!? Ko
kaine zakayi mata naƙudar”.

Ɗan hararan Hajja Nana Khausar tayi sai kuma ta kalli Momy tare da cewa.

“Nima fa bance yayi ba shi yace zaiyi”.

Ta ƙarashe maganar tana kwashe kwanukan ta kai kitchen kana ta dawo ta zauna bayan ta dawo sun
zauna Momy suka gaisa da Hajja Nana bayan sun gaisa suna cigaba da hira.

Asiya ta shigo cikin sassarfa kamar an jefota cikin yanayin tashin hankali tace.

“Momy dan Allah kizo kiga Ummana baki ɗaya yau tunda gari ya waye atsaye take bata zauna ba kona
minti ɗaya fa gaba ɗaya yau jikinta ya tashi!”.
Da damuwa Momy ta miƙe cikin sauri tabi bayan Asiya suka nufi Side ɗin Hajiya Bunayya.

Khausar kam ahankali ta juya ta kalli Hajja Nana itama Hajja Nana kallonta tayi sai kuma ta juya ta kalli
Moddibo cikin sanyi tace.

“Yah Mu'allim nace maka batun jikin Umma da Amina ayi musu addu'a sannan ka turo Dr Jameel yazo ya
duba su amma Yah Mu'allim har yanzu baka ce komai akai ba”.

Ahankali Moddibo ya dafe kansa da hannunsa na hagu yace.

“Wallahi na manta, koyie haƙuri mantawa na keyi Minha”.

Kamar za tayi kuka tace.

“Yanzu fa kaji abinda Asiya tace”.

Hajja Nana da batasan meke faruwa ba ta kalli Khausar tare da cewa.

“Meke damunta?”.

Cikin rauni Khausar tayi ƙasa da kanta kana ta kwashe labarin duk yanda ta faɗawa Moddibo ta faɗawa
Hajja Nana.

Ajiyar zuciya Hajja Nana ta sauƙe tare da jinjina kanta tace.

“Ai dama haka duniya take idan kace tukunyar wani bazai tafasa ba naka ko ɗumi bazai yiba arayuwa ka
taka ahankali kada ka shiga hurumin da bana kaba duk lokacin daka shiga hurumin da bana kaba sai ka
samu abinda zai shiga huruminka”.

Araunane Khausar ta risinar da kanta Hajja Nana kuwa cikin jimami ta cigaba da faɗin.

“Ya hanaka zaune ya hana ka tsaye yanzu wa gari ya waya ita wancan ta haukace ƴarta ta zama mai wari
ita gata nan ƴarta ta zama wata halitta daban gashi ita kuma yanzu ƴarta tazo tana cewa tunda gari ya
waye bata zauna ba ta isa ta zauna tsutsotsi na cinta”.

Ahankali Khausar ta rausayar da kanta hawaye na kwaranyowa daga idanunta tace.

“Hajja Nana Ni tausayi suke bani musamman Amina tana bani tausayi gaba ɗaya sai kinga yanda ta dawo
ita ma Umman na ban tausayi bata isa ta zauna bafa Hajja Nana wlh ko jiya data shigo nan mu gaisa
tsutsotsin har bin ƙafarta suke yi sai in taji kiga tana ta buge-bugen ƙafart kamar itama so suke su
haukatata gaba ɗaya ”.

Cikin sauƙe numfashi Hajja Nana ta gyara zama tare da cewa.


“Dama haka duniya take”.

Still idanunta na zubda hawaye ta kalli Moddibo tare da faɗin.

“Ni dai ina so a samar mata magani ayi mata addu'a ane ma mata sauƙi awajen Allah”.

Acan Side ɗin Hajiya Bunayya kuwa Momy na shiga ta sameta atsaye sai bubbuga ƙafa take saboda
yanda tsutsotsin ke cinta yayin da Amina ke gefenta tana zazzaro harshenta waje.

Da sauri Momy ta ƙarasa wajenta ta riƙe hannunta kana tace.

“Yaya ki zauna mana”.

Kai ta girgiza cikin tarin damuwa tace.

“Ina Momyn Khausar bazan iya zamaba idan na zauna ji nake har cikin hanjina tsutsotsin suke ci suna
gigitani na rasa yanda zanyi na cutar dake arayuwa gashi nima yanzu na samu abinda yake cutar dani na
rasa yanda zanyi a rayuwata”.

Cike da tarin tausayinta Momy ta girgiza kai tare da faɗin.

“Bakomai in sha Allah zaki samu lafiya”.

Kai ta girgiza tana cigaba da buga ƙafarta kana tace.

“A'a nikam nasan na nemowa kaina abinda yafi ƙarfina Momyn Khausar ki yafe min ki cewa Khausar ta
yafe min”.

Cikin sauri momy ta juya tare da faɗin.

“Ki kwantar da hankalinki Yaya bari naje na kira Lamiɗo yazo ya kai ki asibiti ”.

Ta ida maganar tare da nufar Side ɗin Lamiɗo.

Cikin kiɗima tace.

“Wallahi Lamiɗo Yaya ce babu lafiya gaba ɗaya ta kasa zaune ta kasa tsaye ta kiɗime ta gigice ga Amina
ma ita ma baki ɗaya yau jikinta nata abin ya sake motsa wa”.

Anutse Lamiɗo ya juya ya kalleta kana yace.

“Hmmm shine baki ɗaya kika gigice haka?, Mutanen dake suka cutar Sakayyah ce ta sauƙa akan su shine
zaki gigice haka?”.

Kai ta girgiza kana tace.


“Nikam basu cutar dani ba kuma koda sun cutar dani na yafe musu Duniya da lahira”.

Gyaran murya Man Liman yayi tare da cewa.

“Wayene ba lafiya?”.

Zama Momy tayi muryanta ɗauke da damuwa tace.

“Uwar gidata ce babu lafiya Baffa Liman jinyan kuma ya kiɗima mu”.

Kai ya jinjina yace.

“Toh kunje asibiti ne?”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Munje asibiti. Likitocin da kansu sunce bana asibitinba ne na gidane sai kaga yarinyar mijin da aka Aura
mata ne bisa duk kan alamu tsafi yayi da ita ita kuma Yayan dai baza ka tantance ba”.

Zama Lamiɗo ya gyara kana yace.

“Ki daina cewa ba za'a tantance ba ki fito kice sihiri tayi Miki keda Khausar ya dawo kanta haka zaki faɗa
masa ki fito fili ki faɗa masa abinda ta miki Saboda ko baki faɗa ba Allah ya sani kuma taga Sakayyar
abinda ta aikata”.

Kai Momy ke girgiza masa shikam cikin tsanar Muguwar ɗabi'ar Hajiya Bunayya ya cigaba da cewa.

“Ita kuma Amina dama ai ƙulle ƙulle sukayi Ni kaina tsoron Al'amarin Naseer nake yi suka nuna dole-dole
sai Naseer ya auri Amina yaje yayi tsafi da ita ya dawo da ita me zance musu su suka jawa kansu jiki
magayi.

Ai dama sai dana ce duk abinda ya faru babu Ni aciki ba hannuna bare ƙafata aciki”.

Cike da nutsuwa Man Liman ya kalli lamiɗo tare da faɗin.

“A'a Lamiɗo baza ayi haka ba ai ita rayuwa rai da lafiya ita ake bibiya ake duban Lamarinsu kuma komai
lalacewan Amina jinin kace tsatsonka ce kana Hajiya Bunayya komai lalacewan ta Matarka ce Uwar
ƴaƴan kace”.

Da sauri ya girgiza kai yace.

“Uwar ƴaƴana ne babu yanda na iya amma Ni na saketa na saki Hajiya Bunayya tun wata ɗaya daya
wuce Ni yanzu babu alaƙa tsakanina da ita na barta dai ta sauna a gida nane albarkacin Asiya da
Sulaiman, taje can rayuwarta da ban rayuwata da ban”.

Mommy kam kallonsa take cike da matsanancin mamaki jin cewa ya saki Hajiya Bunayya ko kaɗan batayi
farin cikin jin haka ba sai ma damuwarta ɗaya karu.
Man Liman kuwa cike da nutsuwa yace.

“Ai baza ayi haka ba yanzu idan babu matsala kayi min jagora muje in gansu Babu abinda yafi ƙarfin
Ubangiji zanyi musu abinda Allah Ubangiji ya sanar dani”.

Kai Lamiɗo ya girgiza kana yace.

“Baffa Liman ka barsu baka san su bane”

Cikin rauni Momy ta kallesa kana tace.

“Dan Allah Lamiɗo kayi haƙuri ka taushi zuciyarka”.

Ahankali Lamiɗo ya ɗago ya kalleta kana ta girgiza kai ganin yanda ta tashi hankalinta yace.

“Kina jifa da bakinta tace ita tayi sihiri ta kashe Ramadan ”.

Cikin sauri Momy tace.

“Innalillahi wa'inna alaihi raji'un yanzu kai Lamiɗo sai ka yarda ita tayi sihiri ta kashe Ramadan?”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Ehem ita ta faɗa da bakinta ai ”.

Cikin sauƙe numfashi ta kalli Man Liman ta kalli Lamiɗo tace.

“Amma ka manta tun lokacin da Ramadan yayi accident an gaya mana cewa yana da brein Cancer tun
lokacin daya karye ka manta cewa Likita ya faɗa mana kuma ko kai kanka kasan cewa ciwon kan da
Ramadan yayi dare ɗayane sannan kuma an tabbatar mana da cewa ciwon ne ya kashe sa”.

Kai Abba dake gefe ya jinjina Momy kuwa cikin rauni ta cigaba da faɗin.

“Ko Sihiri da tace tayi Ni banyi Imani Sihirinta da tayi shi ya kashe min ɗana ba imma shine ya kashesa
tsakaninta da Ubangijinta kuma ko cikina da take cewa ita tayi sihiri ya zube wallahi bata isa tayi Sihiri
cikina ya zube ba face dama Allah ya ƙadarta waɗanan cikin bazan haifesu su taka doron ƙasa ba, shine
kaɗai amma Ni bata isa ta kashe min ɗa ba bata isa zubar min da ciki ba wa'adin sa ne yayi”.

Cikin sanyi ta ƙare maganar tana mai zubda hawaye ta cigaba da cewa.

“Kuma ai ita in tayi zalunci mu bai kamata mu saka mata da zaluncin ba sai mu barta da Allah shi yasa
Sakayyar da zaiyi mana”.

Jikin Lamiɗo ne yayi sanyi jin abinda ta faɗa sai kuma ya kalli Man Liman dake cewa.

“Kayi haƙuri muje mu dubata”.


Ahankali Yah Abba ya gyara zamansa tare dasa baki acikin tattaunawar su yace.

“Ayyah Lamiɗo ayi haƙuri adubasu ai rai da lafiya ake dubawa”.

Kai ya gyada tare da cewa.

“Shikenan”.

Momy ce ta fara miƙewa ta fita Lamiɗo na biye da ita sai kuma Man Liman da Yah Abba Abaya.

Suna shiga falon Hajiya Bunayya suka sameta atsaye sai bubbuga ƙafanta take tana tsalle ga ƴan mili-
milin tsutsotsin nan na bin ƙafafunta yayin da Amina ke kwance kan 3sitter tana karkata kanta tare da
zaro harshenta Man Liman na ganinta yace.

“Innalillahi wa'inna alaihi raji'un”.

Juyawa yayi ya kalli Hajiya Bunayya kana ya kalli Amina sai kuma ya sake juyawa ya kalli Momy tare da
faɗin.

“Momyn Khausar akwai Zam-zam?”.

Kai ta gyaɗa tace.

“Eh akwai”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da faɗin.

“Toh ki temako min dashi”.

Da sauri tace.

“Toh”.

Kana cikin hanzari taje ta dauko Zam-zam Babban gora ta kawo karɓa yayi kana yace.

“Allah yasa kuna da ganyen Magarya ko ɗanye ko bushesh-she amma idan akwai ɗanye anfi buƙatar
shi”.

Ajiyar zuciya Momy ta sauke kana tace.

“Alhamdulillah akwai ɗanye abayan window na adan kwai bishiyarsa”.

Cikin sauke numfashi yace.

“Toh Alhamdulillah aje atsinko akawo min”.


Cikin sauri ta juya taje ta tsinko ganyen Magarya ta kawo masa tana kawowa ya karɓa kallon Asiya dake
kuka yayi kana yace.

“Asiya idan akwai sabon roba mai haske ki kawo min”.

Cikin sauri tace.

“Toh”.

Kana ta shiga kitchen ta ɗauko roba mai ɗan girma karɓa yayi yasa rabin Zam-zam ɗin aciki zama yayi ya
Tofa Ayatul Shifaa gaba ɗaya aciki idan ya gama tofawa yasa ganyen Magarya guda bakwai aciki kallon
Asiya yayi yace ta kawo masa karamin kofi cikin minti ɗaya ta kawo kofin ruwan addu'ar ya ɗebo ya
bawa Amina yace.

“Karɓi kishi”.

Akarkace Amina ta miƙe tare da kauda kai gefe.

Cikin tausasa murya ya sake cewa.

“Karɓi kisha”.

Still juyawa tayi alamar bazata shaba.

Kallon Lamiɗo Man Liman yayi tare da cewa.

”A danneta Abata tasha”.

Cikin takaici Lamiɗo ya girgiza kai kana yace.

“Ta karɓa tasha sai adanneta ai jiki magayi lafiyarta ne ko lafiyanmu”.

Man Liman na gyara alkyabbarsa yace.

“Ayi haƙuri Abata ai sihirin da aka yi mata ne an haɗa mai tafiya da siffar maciji bayin kanta bane bazata
sha ɗinba”.

Cikin rauni Asiya ta kalli Lamiɗo tace.

“Ayyah Abba don Allah Abata ”.

Ta ƙare maganar tare da karban kofin ta matsa kusa da Amina.

Amina na ƙoƙarin ture kofin Lamiɗo yayi saurin kama hannayenta kana ya rike kanta Asiya ta ɗura mata
ruwan Tofi da ganyen Magaryan tasha mai ɗan yawa amma sauran ya zube.
Ahankali ta fara yin gyatsa lokaci ɗaya jikinta ya saki ta koma ta kwanta kan kujeran atake bacci ya ɗauke
ta.

Tana yin Bacci Man Liman ya sauƙe ajiyar zuciya yace.

“Alhamdulillah tunda har tayi bacci in Allah yaso ya yarda zata rabu da abinda ke tare da ita amma
wannan yaron da kuka Aura mata ya cika taƙadirin Jahili makirin mutum mushirki”.

Kai Lamiɗo ya girgiza tare kana yace.

“Su suka siyawa kansu”.

Cikin kuka da nadama Hajiya Bunayya ta durƙusa gaban Man Liman tace.

“Dan Allah nima ataimaka min mana abani abinda zansha inji sauƙi atemaka min”.

Kai Man Liman ya gyada yace.

“Ba matsala in Sha Allahu”.

Sai Kuma ya tsiyayi ruwan Zam-zam daban akofi yasa ganyen Magarya aciki yayi mata Tofi kana ya bata
yace ta taune ganyen Magarya Zam-zam ɗin shi kai ta gyaɗa kana tayi kamar yanda yace tana gama yi
taji kamar fitsari take ji cikin sauri ta nufi bedroom ɗin ta ta wuce Bathroom.

Man Liman kuwa kallon Asiya yayi tare da cewa.

“Idan ta farka wannan ruwan daya rage ta samu tayi wanka dashi awajen da babu najasa”.

Kai Asiya ta gyaɗa tare da faɗin.

“Toh In Sha Allahu”.

Yana kallon Aminan dake bacci yace.

“Kuma in sha Allah akwai tofin da zan mata amma da Zam-zam ɗin ne sai dai zai ɗauke Ni tsawon kwana
biyu in sha Allah idan anyi shi in zamu zo daurin Auren su Jameelu zamu zo dashi da izinin Ubangiji zata
samu sauki”.

Kai Asiya ta gyaɗa kafin cikin sanyi tace

“Umman mufa?”.

Ɗan gyara tsayuwar sa yayi kana yace.

“Toh bamu san mai Ubangiji zaiyi ba amma itama in sha Allah muna kyautata zaton Allah zai bata lafiya”.
Cikin sanyi da ɗan jin nutsuwa tace.

“Allah yasa mun gode”.

Nan Lamiɗo da Man Liman da Yah Abba suka fita.

Momy kuwa cikin jin sassauci tace.

“Alhamdulillah Amina ta samu sauki”.

Kai Asiya ta gyaɗa.

Momy kuwa ganin Hajiya Bunayya ta tafi daki yasa tayi zaton sauki ta samu tana kallon Asiya tace.

“Barin tafi ina da baƙi kinsan Hajja Nana nacan”

Cikin ƙaunarta da sake jinjina kyawun halinta Asiya tace.

“Toh Mun gode”.

Lamiɗo Man Liman da Yah Abba kuwa Side ɗin Lamiɗo suka koma...

Momy na shiga falon Moddibo ya mike kana yace.

“Toh Momy Ni zan wuce”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh mun gode”.

Khausar kuwa cikin sanyi ta kallesa kana tace.

“Dan Allah Yah Mu'allim kada ka manta Dr Jameel yazo ya duba Umma”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“In sha Allahu bazan manta ba Minha baza ki rakani bane”.

Kanta ta langwaɓar tare da ƙyafta ƙwayar idanunta ciki nasa sai kuma ta daura hannunta na dama kan
ƙafarta tace.

“Ayyah kayi haƙuri baki ɗaya Ƙafafuna rawa suke”.

Lallausan murmushi ya sakar mata tare da motsa laɓɓansa cikin ƙasa da murya yanda ita kaɗai zata ji
yace.

“Toh sai nazo da daddare”.


Kallonsa tayi da sauri tace.

“Me kuma za kazo yi da daddare?”.

Yana ɗan lumshe Idanunsa cikin nata yace.

“Bakyaso in kawo Dr Jameel ɗin ne?”.

Ahankali tace.

“Ina so mana”.

Kai ya gyaɗa yana gyara tsayuwar sa yace.

“Toh idan nazo kuma ki shirya zamu tafi tare”.

Langwaɓar da kai tayi tare da faɗin.

“Ayyah Yah Mu'allim ka barni in kwana mana”.

Kai ya girgiza tare da faɗin.

“Bazan iya ba dole fa yau zamu tafi muje mu kwana tare”.

Sake langwaɓar da kai tayi tare da marairaice fuska tace.

“Dan Allah Yah Mu'allim ”.

Cikin sauri ya ɗan tsuke fuska yace.

“Kada ma ki haɗani da Allah ki cuceni”.

Shiru tayi ganin kallon da Momy ke mata me nuni da alamun gargaɗi.

Shi kuwa Modibbo Hajja Nana ya kalla jin tana cewa.

“Idan Allah ya kaimu gobe ko jibi in ba matsala zamu tafi jahar Gombe muje kaga asalin masarautar su
Khausar kuna mahaifarta”.

Cikin murmushi Khausar tace.

“Gobe dai zaifi dan Allah Yan Mu'allim kace gobe”.

Kai ya jinjina cike da jin yana son yaje yaga Masarautar su yace.

“Allah ya kaimu goben in ya samu in kuma bai samuba sai jibi, za dai muje kafin ayi bikin”.

Amin suka amsa kana shi kuma ya juya fita.


Yana isa gida kai tsaye Side ɗin su Dr Jameel ya shiga nan yasa masu suna ta maganar abinda za'a yi
kasancewar yau saura kwana huɗu ne ɗaurin Auren kasancewar yau ya kasance Litinin.

Talata Laraba Alhamis juma'a za'a ɗaura Auren.

Nan dai suka cigaba da hiransu.

Acan gidansu Asma'u ma shirye shiryen biki ya kankama.

Alhamdulillah washe gare suka tafi Gombe.

Harda Dr Jameel da Lallai Khadijah da Rahma harda Didi da Innayi da Galadima suka je dan ya gabatar da
masarautar su.

Kwana su biyu suka dawo Gembilan.

Alhamdulillah zuwa yanzu Amina ta fara samun sauyi dan yanzu ta daina zare harshenta.

Hajia Bunayya kuwa abu kam sai gaba gaba.

Samira Sani kuwa jin Amina ta samu sauƙine da yadda akayi yasa itama ta zo ta kokawa Momyn kuma
Alhamdulillah yau dasuka dawo daga Gombe.

Man Liman yayi mata tofi, ya bata ya bawa Amina.

Alhamdulillah cikin kuɗirar Ubangiji kafin zuwa la'asar Samira ta fahimci zuban ruwan nan ya ragu sosai.

Amina kuwa sosai itama mummurɗewa da jikinta keyi ya fara raguwa.

Nan ya sake yi musu tofi cikin zam-zam ɗin na wasu keɓantattun ayoyi da sauri kamar haka.

*Al-araf ayata 117, 118, 119, 120, 121 da kuma 122. Sai Suratul Yunus daga ayata 79, 80, 81, 82, Sai
kuma suratul Ta-ha aya ta 65 66, 67, 68, 69, 70, Sai kuma suratul al-Kafurune gaba ɗayanta, da kuma
suratul al-ikhlas dukanta sai suratul al-falaq itama dua da kuma suratul An-nas itama dukanta da forko
zaki samu zam-zam ki zuba mai yawa a tsabtacecen mazubi ko roba ko kwarya, ki tabbatar zam-zam ɗin
zai ishe ki sha da kuma yin wanka, sai zuba a robar kana kisa kanyen magariyar guda bakwai an fison
ɗanye Amman busheshenma ba matsala zaki daka guda bakwai in ɗanyen nema ki daka bakwai, sai ki
zuba a Zam-zam ɗin kana ki karanta ayoyin Alkur'ani mai tsarkin dana lissafa Miki da surorin ki ɗan
motsashi zakiga ya ɗan buga kumfa sai ki ɗiba a cup wanda zakisha ki ƙoshi kuyi gyatsa, sai ki zauna bisa
yaƙini da niyar Allah ya yaye Miki matsalarki ko wacce iri yace Sihiri, ko tsafi, Sammu, ko kambun baka,
ko cutar da ba'a gane kantaba ko sharrin iska. Kisha koyi hamdala kana ki ɗauki sauran na cikin robar ki
samu sarkakekken wurin da babu najasa kiyi niya da duk matsalarki kiyi wanka. Wlh da izinin Ubangiji
zakiji sauƙi ki samu sauyi anaso na farko dai kiyishi da Zam-zam inda hali duk bayan wata shida ko
shekara ɗaya kiyi kiyiwa yaranki da mijinki dan makarine mai girma in ba hali saboda tsadar da Zam-zam
keyi in kinyi na forkon da Zam-zam to na biyu kiyi da ruwan sama na uku da duk ruwan da ya sauwaƙa
gareki, inda hali ko yaushe da Zam-zam in ba hali ayi na forkon da Zam-zam in bai samuba ayi da ruwan
sama na roƙon da na biyun da na ukun, kiyishi maƙo maƙo ko wata wata ana dai son duk bayan wata
shida ko shekara ɗaya kiyi, yar uwa ko ɗanki, ƴarki mijinki ƙanwarki ƴaƴan yar uwa ki ko ɗan uwa duk
inda kukaga yaro ko yarinya sun cika rashin ji gagara rawan kai gardama da alamun kwaucewa hanya
kuyi masu yanada matuƙar fa'ida da falala, sadakace fisabilillahi idan kinji daɗinshi kiyi niya kiyiwa
Mahaifiyata Fatima Dedde na ƙu'huwa ƙafa uku da fatan Allah ya jiƙanta ya kai haske da ni'ima
Qabarinta. Ni kuma inada wata buƙata mai girma da falala da daraja a wurin Allah kuyi min addu'a kisa
yaranki suyi min addu'a kice su roƙawa Aysha Aliyu Muhammad Garkuwa Allah ya biya mata buƙatarta
akan alkhairi, ya raya mata ƴaƴanta Muhammad Jabeer da Maimuna Ikhram da Ibraahim ya shirye su ya
basu ilimi mai amfani da albarka yasa su zama abin alfahari ga Musulunci da Musulmai mazan ya basu
mata na gari da zuraya ɗaiyi ba, macen ya bata miji na gari da zuri'a ɗaiyiba, kana Allah ya bani wasu
ƴaƴan masu albarka da nisan kwana tagwaye inyiwa Deddena takwara da Babana in samu Aliyu Haiydar
da Fatima Khausar in samu auta A'isha takwarar kakata mafi soyuwa*

Man Lima da Hajja Nana ma bayan sunyi sallar la'asar da Baffa Liman da Yah Abba suka kama hanyar
komawa Jauro Yaya.

Acan ɓangaren Hajiya Bunayya ma tunda tasha wannan ruwan tofin sai tsutsotsin suka yawaita fita yayin
da suke cinta da gasken gaske sai dai tana shiga ruwan ɗumi zai lafa amma bazai wuce awa biyu zuwa
uku ba zai sake dawowa haka tayi wannan yinin ranan zunibi da sakayyan aikinta na bibiyarta.

Daddare bayan sallar Isha'i Moddibo ne da Dr Jameel zaune afalon Hajiya Bunayya tana zaune Sai
murtsukuku take yi akan kujeran jin yanda tsutsotsin ke cinta yayin da Amina ke zaune gefenta bisa duk
kan alamu Alhamdulillah ta fara samun sauƙi har nishinma duk ta daina .

Anutse Dr Jameel ya kalli Hajiya Bunayya kana yace.

“Akwai tests ɗin da za'a Miki.

Sai kiyi ƙoƙari kije asibitu aduba ki acan”.


Cikin sanyi tace .

“Nagode Nagode Dr Jameel Allah ya saka da Alkhairi ”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Bakomai”.

Kana suka miƙe suka fita dai-dai lokacin kuma Dr Zakariyya da Asiya ne zaune amota suna hira fitowa su
Dr Jameel ne yasa Asiya yiwa Dr Zakariyya sallama ta fita kana Dr Jameel ya shiga Motar.

Moddibo kuwa bayan Khausar dake shiga Side ɗin Momy ya nufa yana shiga falon yaga ba kowa sai
Raudat dake kallon Catoon yace.

“Raudy ina Addah Khausy?”.

Hankalinta na kan kallon tace.

“Tana ɗakinta”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Momy fa?”.

Still idanunta na kan tv tace.

“Tana gidan Ummin Jameel Yah Haiydar ya kaita”.

Kai ya gyaɗa kana ya shiga ɗakin Khausar zaune ya sameta agaban Weldrop ɗin ta gabanta littafaine tana
ta duddubawa.

Da mamaki ta kallesa kana tace.

“Yah Mu'allim har nan kuma?”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Eh ai gidan mune”.

Kai ta gyaɗa hannunta na kan littafin tace.

“Eh nasani ai yanzu in Momy tazo ta same mufa?”.

Murmushi yayi tare da shafa sajensa kana yace.

“Eh dai-dai kenan idan Momy tazo ta ganni zata san ina buƙatar matata zata kora min ke mu tafi tun da
ke yanzu kin iya gardama da taurin kai ”.
Kanta ta langwaɓar tare da cewa.

“Ayyah Yah Mu'allim ba gardama da taurin kai bane kaga idan mun koma kafin na sake ganin Momy fa
zai daɗe ”.

Yana gyara zamansa gefenta yace.

“Amma Ni bakya jin tausayina tunda muka zo fa kike bari na ina rayuwa Ni kadai kamar Maraya Babu
kowa kusa dani”.

Kallonsa tayi tace.

“Yah Mu'allim aima mun kusa komawa dai kayi haƙuri kwana nawa ya rage”.

Ta ƙare maganar tana cigaba da dudduba littattafan sai kuma ta ajiyesu ta gefensa kallon yanda ta
hargitsa Littattafan yayi kana yace.

“Me kike nema?”.

Tana cigaba da abinda take tace.

“Wani littafi na nake nema?”.

Da mamaki yace.

“Littafi kuma?”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh”.

Kamar mai raɗa ya sake matsawa kusa da ita yace.

“Toh me zakiyi dashi?”.

Kanta na kan tulin littattafan tace.

“Wani abu ne aciki?".

Da mamaki yace.

“Wani abu ne kuma aciki?,ki bari gobe sai ki duba”.

Kai ta girgiza tare da faɗin.

“Ina so ne in tabbatar yana nan ko baya nan saboda da nazo na samu Raudat tana wasa takarduna da
jakar makarantana ta bubbuɗe min ban sani ba ko ta jefar min da littafin ”.
Cikin mamakin yanda take neman littafin yace

“Toh littafin na wani Subjects ne?”.

Tana ɗan tura baki tace.

“Um-um fa littafin bana karatu bane?”.

Yana ɗan ƙara matsota yace.

“Ikon Allah toh littafin na menene?”.

Ya ƙare maganar yana dudduba littattafan data tutturo gefensa yayin da take sake zaro na cikin jakar
ganin basu cikine yasa ta jawo durowan ƙasan Weldrop ɗin tare da cewa.

”Toh ban sani ba bari in duba ko suna cikin nan ne”.

Dai-dai lokacin yaga wani note Book An rubuta *SPECIAL MAN* da manyan baƙi Aransa ya maimaita
Special Man ahankali ya jawo littafin yana ɗan jujjuyawa Khausar kuwa baki ɗaya hankalin ta na cikin
durowan Weldrop ɗin.

Ahankali ya buɗe shafin farko na littafin.

ga mamakinsa sai yaga Drawing ɗin hoton fuskarsa ne rauɗau ba abinda aka bari har sajensa.

Cikin tarin wani irin mamaki al,ajabi da kuma kaɗuwa ya kalli gefen shafin.

A gefen kuwa Drawing ɗin fuskarsa ne acikin aji hannunsa na kan Black board kamar yana rubutu cikin
sauri ya kalli rubutun da akayi da kalo wanda akayi musu design yanda ya kasance na musamman haka
sunansa ya kasance na Musamman _Aliyu Youseef Mohammed Mouley (Moddibo)_

da mamaki ya kalli inda aka rubuta sunansa anyi zanen ❤️sai kuma ya maida idanunsa inda akayi
Drawing ɗin fuskarsa yaga date and time ɗin da akayi rubutun Drawings ɗin.

Idanunsa ya jujjuya ya kalleta amma baki ɗaya hankalinta na kan tarin himilin sauran littafan.

Kallonsa ya mayar kan date ɗin idan har baiyi kuskure ba toh shekaru huɗu kenan ranan dasu Khausar
suka fara zuwa SS3 cikin mamaki da wani irin yanayi ya buɗe page ɗin gaba sai yaga Drawing ɗin
Fuskarsa ne amma ba'a fitar da fuskan sosai ba sai sajensa aƙasan ta rubuta.

_One's if I remember your face, my actionable will be change to cool, is your Breed brightly my heart
always yo be sunshine , i really love you with deep voice. Uncle Aliyu Youssef Mouldy (Modibbo)_

Ahankali ya motsa laɓɓansa ya furta.

“Ya salam”.

Wani irin amintaccen numfashi ya fesar saboda jin kalaman suna Barka duk kan lakar jikinsa.
Fahimtar da yayi baki ɗaya littafin kamar akansa yake magana haka nan yaji wani abu yana sauƙa tun
daga ƙwaƙwalwar kansa har zuwa babban yatsarsa a iya shafi biyu daya buɗe ya fuskanci gaba ɗaya
Khausar ta rayune da soyayyar shi acikin zuciyarta shi kansa baisan meyesa ba ya dai tsinci kansa da
naɗe takardan yasa cikin aljihunsa.

tare juyawa yayi mata wani amintaccen rugguma yana mai kallonta yace.

“Wai wani littafi kike nema ne?”

Batare data kallesa ba tace.

“Wani Littafina ne na musamman, nasan da wuya in Raudat bata ɓatar min da shiba dan haka taɓatar
min da ɗan uwanshi da Nai ta rubutawa tun daga JSS one to 3”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Ko dai Diary kine?”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Kusan haka amma shi babban littafine ai yama fi Diary daraja awajena”.

Gira daya ya dage tare da faɗin.

“Toh tashi mu tafi da safe sai muzo na tayaki dubawa”.

Kai ta langwaɓar kana tace.

“Allah ina so ba mamaki yanzu Raudat ta ɓatar min dashi. In dai ta baddashi wlh sai na daketa dan yana
tunamin abubuwa da yawa a rayuwata”.

Kai ya girgiza tare da faɗin.

“In sha Allah ma bai ɓata ba kada ki damu kizo mu tafi da safe za'a zo mu duba”.

Ya ƙare maganar da ƙaguwar so yake ya ga su ƙeɓe daga shi sai ita.

Kai ta girgiza tana cigaba da hautsina littattafan tace.

“Um-um.ni dai ina son gani ”.

Fuska ya tsuke tare da cewa.

“Mu tafi nace ko?”.

Ganin yanda ya tsuke fuska yasa ta gyaɗa kai tare da faɗin.

“Toh”.
Kana tattare littafan ta mayar cikin drawer.

Hannunta ya jawo ya riƙe kana ya kalli gyalen jikinta ganin babu laifi yasa yace.

“Mu tafi toh”.

Suna fita motarsu Dr Jameel na fita agidan motarsu suka shiga kana suka tafi gida.

Suna shiga Falonsu ya rufe ƙofan kana ya ɓalle botir ɗin wuyan rigarsa ya zare ya ajiye kana ya jawota
jikinsa ya rungumeta ajikinsa cikin sanyi ya kai bakinsa saitin kunnenta kana ya shiga raɗa mata abinda ta
rubuta yana cewa.

“ _One's if I remember your face, my actionable will be change to cool, is your Breed brightly my heart
always you be sunshine , i really love you with deep voice Aliyu Youssef Mouldy (Modibbo)_”

Cikin sauri ta ɗaga ido ta kallesa tare da wani irin fiddo idanun duka tamkar zasu faɗo ƙasa, ido ɗaya ya
kashe mata kana yace.

“Tukuocin soyayyar da kike min nake son baki a daren yau”.

Baki ta tura tare da kwaɓe fuska kana tace.

“Waye ɗin?”.

Ido ya kashe mata tare da cewa.

“Keɗin mana”.

Ɗan ware idanunta tayi akansa kana tace.

“Kamarya tukuicin soyayyar da nake maka kuma?”.

Ta ƙare maganar cikin kunya da son waskewa.

Cikin wani irin yanayi yace.

“Shekara nawa kika yi kina dakon soyayyata azuciyarki?”.

Kallonsa tayi da mamaki sai kuma ta lumshe Idanunta tace.

“Kamarya kuma nayi dakon soyayyar ka azuciyata?”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Littafin da kike nema yana hannuna fa?”

Still kallonsa tayi tace.


“Wani littafi kuma?”.

Ɗan murmushi yayi kana ya hura mata sanyayyar iskan bakinsa yace.

“Littafinki da kike nema”.

Littafin ya zaro acikin rigarsa ya nuna mata cikin mamaki ta kallesa kafin tace.

“Yaushe ka ganshi?”.

Dariya yayi tare da cewa.

“Tun ɗazu har na karanta shi ma”.

Da sauri ta kife kanta akan ƙirjinsa cike da kunya murmushi yayi kana ya shiga tura yatsunsa ƙasan
ƙafarta jin haka yasa ta ɗaura ƙafanta kan rumfar ƙafansa.

A hankali ya fara tafiya da ita har suka isa bedroom.

Cikin sanyi ya kwantar da ita akan gado.

Kana yayi kissing ɗin goshinta da lips ɗin ta ahankali ya fara cire mata rigarta cikin wata kasalalliyar
murya yace.

“Khausar da shin da gaske kina min soyayyar da baza ki iya furta min ita abaki ba Khausar?Meyesa baza
ki faɗa min ba inji sanyi raina sai kiyita dakon soyayyata tsawon shekaru meyesa baki faɗa min ba
meyesa baki nuna min ba? Da gaske kece kika rubuta littafin nan”.

Ahankali taja numfashi mai tsawo hannunta na cikin sumar kansa tana shafawa kana manyan yatsunta
guda biyu na kan sajensa tace.

“Ni ba ni na rubuta ba.

Haka kawai ka'ida basona kake ba kalen ince ina sonka ka kashe ni?”.

Cikin sauƙe numfashi ya gyara ta ajikinsa tare da cewa.

“Wayace miki bana sonki? Minha”.

Idanunta ta lumshe zuciyarta na bugawa tace.

“Nasan baka soma kuma nima ba nice na rubutaba”.

Yana shafa sumar kanta yace.

“To amma tunda ke kina sona ai da kin faɗa min munyi ta cutar da juna tsawon lokaci?,bamu sani ba”.

Muryan cike da sanyi ta ɗan cije gefen bakinta tace.


”Ni dai bance ina son wanda baisona”.

Saurin girgiza mata kai yayi tare da faɗin.

“Ki daina cewa bana sonki Minha”.

Sai kuma ya shiga romance ɗin ta yana shafa saman Breast ɗin ya cigaba da cewa.

“Kinsan dalilin zamana aƙasan nan kuwa?

Naƙi na koma Jami'atul Madina nayi aikin dana samune saboda ke tun lokacin dana fara sauke idanuna
akan ki Allah ya jarabceni da sonki na soki alokacin da bakisan kanki ba Minha”.

Da wani irin sauri mai nuni da zallan farin ciki Khausar ta tallofo kansa tana kissing ɗin dogon hancinsa
cikin kasala da shauƙi kana da yanayin da yake ji yaci gaba da cewa.

“Sanadinki na zauna anan nasoki soyayyar da bazan iya yiwa kaina ba duk Drawing da kike yi na ki wasa
ne ni duk wani motsin da kikayi a duniya idan na dawo sai nayi Drawing ɗin sa na ajiye babu abinda yake
sani farin cikin gani a duniya kamar fure da kuma ke saboda furanni kansu kin fisu kyau sai dai suna ɗebi
min kyewar rashin ganinki ne, kana suna cike min gurbin kallonki”.

Cikin mamaki Khausar ta ɗago ta kallesa ido cikin ido tace.

“Yah Mu'allim kenan kana sona da gaske?”.

Kai ya jinjina tare da faɗin.

“Minha ina sonki son da bansan adadinsa ba nayi Miki son da ba yiwa kowacce ƴa mace irinsa a duniya
ba”.

Sai kuma ya miƙe da sauri, ya buɗe durowar dake jikin gadonshi, wasu manyan takardu masu kana da
kalandu ya ja, a kan kadon ya zubasu.

Da sauri ta zubawa na forkon idanu.

Sai kuma ta kalleshi domin ta tuno yanayin da suka kasance a cikin mota a ranar daya rage mata hanya.

Da sauri yaja mata na ƙasashi.

Wani irin murmushin ne ya subce mata ganin zanenta tana rawa a gaban motarsu ranar da suka haɗu
gidan Ummi.

Baki ta turo ganin na ƙasanshi ranar da take kakkaɓe ɗan kwali ne sai kuma wani da bazata manceba na
ranar data fara ganinshine da ta tsaya tana kallonshi harda karkata wuya ranar da ta fara zuwa JSS one
kenan sai kuma wanda ta diƙo kan bishiyar ranar da suka zo da Asma'u sai wanda suka haɗu a rugar
Jauro yaya.

Ya Salam sai kuma wasu wanda bisa alamun nashine da Yah Jameel.
Kawai sai ta faɗa jikinsa.

Ture takardun yayi tare da ruggumeta da kyau.

Kanta ta kwanta ajikinsa tana jin yanda hannunsa ke yawo a sassan jikinta tace.

“Amma kuma Yah Mu'allim kullum dukana kake yi ya za'a yi na yarda dagaske cewa kana sona”.

Yana sakin ajiyar zuciya yace.

“Dole ne yasa nake Miki wannan yanayin saboda na fahimci kamar J yana sonki so kuma irin na aure”.

Saurin kallonsa tayi ya jinjina mata kai yana cigaba da cewa.

“A duniya ban taɓa son abu J yaƙi shiba.

Kana J bai taɓa son abu naƙi shiba sai nazo na fahimci akan mace ma zamuyi tarayya akan soyayya kuma
hakan zai zame mana masufa a amintakarmun shiyasa nasawa raina hantarar ki da nisantarki da ƙin
kasancewa kusa dake saboda in yakice ki azuciyata J ya mallake ki dan nayi alkawarin mace bata isa ta
shiga tsakanin amintakarmu ba”.

Idanunta ta lumshe tana jin wani irin ƙaunarsa na huda duk wani magudanan jinin jikinta ahankali ya
cigaba da cewa.

“Abinda J ya faɗa min kenan a voice ɗin sa na ƙarshe yace min ya fahimci ina sonki yamin voice da ace
alokacin yana raye zance J ai kaima kana sonta amma tun a voice ɗin yace min kana tunanin kamar ina
son Khausar ko? Shiyasa kake hantararta dan ka yakiceta a zuciyarka.

Wai sabida zaka bar min ita ko?.

To ni ba sonta nake ina taya ka son abinda kake sone A.J ka Aureta dan naga zanenta da kayi a takardu,
in su ka ɓoyesu shin zaka ita ɓoye na zuciyarta da ƙwaƙwalwar kane, AJ. Ka aureta. abinda J ya faɗa min
Kenan ”.

Duk da nasan ya faɗane kawai Amman J ya soki Minha ya soki irin so na aure ashe ya gane ina sonki”.

Idanu ta tsira masa kana tace.

“Dagaske Yah Mu'allim?”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Sosai ma”.

Daga nan ya cigaba da romance ɗin ta ya dauki Kimanin minti arba'in da biyar akanta kafin ya jawota ya
rungumeta yana sa mata albarka tare da cewa.
“Alhamdulillah ashe son da nake baso bane soyayya ce?”.

Tana sauƙe Ajiyar zuciya tace.

“Kamar ya?”.

Murmushi yayi tare da faɗin.

“Eh so na gefe ɗaya shi ake cewa so amma tunda kema kina sona kinga soyayya ce”.

Sake shiga jikinsa tayi kana tace.

“Dagaske Yah Mu'allim maganar daka ke faɗa?".

Cikin tabbarwa yace.

“Ki daina kokonto Minha Vidaa Ana uhubbuki kubban axeem”.

Wani irin farin cikine mara misaltawa ya mamaye gaba ɗaya ilahirin zuciyarta.

Awannan daren haka suka kwana cikin farin ciki da kwanciyar hankali...

Alhamdulillah haka rayuwa ta cigaba da tafiya ranan Alhamis akayi walima ranan juma'a aka ɗaura
auren.

Malam Liman da yazo ɗaurin Aure ya kawowa Amina da Samira magani da yayi alƙawar kamar yanda ya
faɗa zuwa yanzu Alhamdulillah jikinu da sauƙi amma dan Amina har abinci takeci.

Samira kuwa ruwan ya rage zuba sosai a wuni haifi sau uku zai zuboba.

Hajiya Bunayya kam abin nata babu sauƙi kullum gaba-gaba yake.

A ranan jumma'a akayi Dinner mai rai da lafi.

Alhamdulillah ranar Litinin sufa dawo Adamawa da amarensu Zakariya da Aseeya Asma'u Da Dr Jameel
Dija Yah Ali Su Didi sunje har falon bappa Jimeta.

Washe gari talata jirginsu ya ɗaga zuwa Morocco.


Misalin ƙarfe 2:00pm suka sauƙa acikin Morocco anan suka samu motoci daga Masarautar Mouley na
jiransu suka shish-shiga kana suka tafi motocin ajere ajere suke tafiya a sai da sukayi nisa Khausar taga
motarsu ta fita cikin sauran tawagar motocin ahankali ta kalli Moddibo dake gefenta kana tace.

“Yah Mu'allim ya naga su sunyi can mu munyi nan?”.

Yana ɗan shafa cikinta yace.

“Gida zamu tafi”.

Idanunta ta zare kana ta langwaɓar da kai tace.

“Yah Mu'allim gida kuma?

Baza muje inga gidansu ba? Ai kamata inyiwa Asma'u rakiya aminiyata fa”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Za kije amma ba yau ba sai kin huta”.

Kai ta gyaɗa direct motarsu Masarautar Mouley ta nufa.

Yayin da Amare aka wuce dasu gidajen su batare da rakiyan kowa ba daga Nigeria kasancewar ga Didi da
Innayi sun sai Goggo Asma'u ta wadatar dan a cewarsu ai Asiya ga Khausar dijama ga Khausar ga Yah
Abbanta.

Khausar kuwa suna isa abinci suka ci kasancewar an shirya musu komai kana ko wanne yayi wanka ya
kwanta dan huce gajiya.

Bayan kwana biyu Moddibo ne zaune akan sallaya gabansa ɗauke da starm da Kur'ani ke kai, bayan ya
dawo daga sallar Asbah yayin da Khausar ke gefensa ahankali ta ɗago kanta jin ringing ɗin wayarta kallon
Moddibo tayi kasancewar ya fita kusa da wayar da ido ta mishi alamar ya dai wake kira?.

Juyawa yayi kana ya kalli screen ɗin wayar sai kuma ya kalleta yace.

“Asma'u ce”.

Da ɗan sauri ta miƙe ta karɓi wayar tare da amsawa takai kunnenta tare da cewa.

“Hello Besty na kiyi haƙuri laifin yayanki ne. Yah Mu'allim ne ya hanani zuwa wai in barku ku gurji
amarc...
Sai kuma tayi shiru ba tare da ta ƙarasa mgnar ba, sabida jin muryan Asma'u a disashe kana yayi sanyi
alamun taci kuka ta godewa Allah cikin raunin murya tace.

“Khausar”.

Da damuwa Khausar ta ɗan jingina bayanta da kafaɗar Moddibo kana tace.

“Subhanallah Asma'u meke faruwa”.

Cikin rauni da zubda hawaye Asma'u tace.

“Khausar zan mutu dan Allah ki cewa Yah Mudibbo kuzo ki ɗaukenu, wannan mutumin mungu ne ya
kasheni ”.

Dariya mai sauti Khausar ta fashe dashi har tana ɗan bubbuga kanta da jikin kafaɗar Moddibo kana tace.

“Ya kashe ki kuma kike magana?”.....

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

68

https://chat.whatsapp.com/Ke5tcPxlatRGeO2qeSdR8s

Group ne na musamman na Ƙasaitattun mata da suka san darajar gyara. Kana group na mata na
musamman masu daraja.

Hajia ko sau ɗaya kika taɓa sayan kayana, ina maraba dake.

Please idan kin san baki da ra'ayin sayan kayan ɗa'a ko na ƙamahi bi ma'ana baki bukatar gyara kada ki
shigo group na domin na kayyakin Matana dana ƙamshi.
Kamarsu. Set ɗin uwar gida, Amarya, budurwa ko bazawara, mai jego, mgnin infection sadidan kayyakin
ƙamshi kamarsu Humra kala-kala kullacca kala-kala Turaren wuta kala-kala Turaren wanka turaren
carpet, na kujeru da labulaye hodar hammata mai hana zufa.

*Idan dai kina buƙatar kayan to ƙofa a buɗe take ki shigo group ɗin ina maraba da tsoffin Customers na
da kuma New Customers, ina lale marbin da kuma masu sayan ƙanana set da kuma masu sayan manya,
domin da rarrafe taro ke tashi tsaye.

Set ɗina hawa hawa ne, akwai manya daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k sai ƙananan set ɗin daga 40k 35k
30k 25k 20k 15k 10k sai ɗan ƙaramin haɗina na ƙarshe Hajia 5k bani da haɗin ƙasa da haka Amman zaki
samu na ɗan dubunki biyar ina saida mgnin infection sadidan ba haufi set 10k half 5k akwai daɗi har
maɗiga 5k maliƙi mai masifar matsewa 7k in son samune ki haɗasu biyu, akwai kwanon Ƙasaitacciyar 7k
akwai sahuwar zuciyar farin rago 25k akwai haɗin dahuwar kaza da rubutu 20k akwai mara rubutu 15k
akwai ɗayan 12k ku'accar siri 7k shu'umar Humra 5k ƙanan roba kenan duk gumbunana ƙananan roba 3-
3k ne sai na riɗi da uku alkhairi da gumbar kwalli ƙanan robar su 5k ne sai ƴan botikayen gumbunan su 9-
9k ne hakama garuka, haka tsumuka sai dai a garuka akwai na roba ɗaya 5k akwai kuma na 2,500 da 3k
ɗin, ina araha kam Amman bana bada bashi.

Farashin kayana duka biyu kenan kayan Ɗa'an na mata da kuma na ƙamshi.

Sayan
😘 na gari maida kuɗi gida, dan Allah yar uwa ko bazaki sayi kayan mataba, ki sayi na infection ki
raba kanki da cuta, set ɗin na na infection yana maaifar kyau duk naci sanyi koda na cikin mahaifane, da
izinin Ubangiji zaki rabu dashi, mgnin infection ɗina na gargajiya ne mai aminci.

Mai ciki babba ko ƙarami na iya sha lfy Lau ba abinda zai mata, budurwa, matar aure, bazawara, yara,
manya, maza, mata, maijego. Duk suna sha, dan Allah ki saya ki sayawa yaranki in dai kinada abokiyar
zama kisa ogo ya saya muku tare, dan infection mugun cutane mai masifar naci so dole muma mu nace
masa da mgnin. In dai kin san kinada infection dan Allah kadama kice zaki say mgnin Matana, dan bazan
saida mikiba kizo kuna cewa kayana ba inƙanci, kuma in set ɗinki ya kai 35k zuwa sama dama dole sai na
sa Miki dana infection ɗin.

68

Cikin dariya sosai ta ƙarshe Maganar, sai kuma tayi saurin sa tafin hannunta na dama ta rufe bakinta,
sabida jin yanda muryan Asma'u ya fito tana shesh-sheƙa.

Tare da saki sanyayyan kuka tana cewa.


“Dariya ma kike min Khausar?,Baki san halin da nake ciki bane wallahi zai kashe ni fa!”.

Da sauri Khausar ta gyara zamanta cike da tausaya wa tace.

”Kiyi haƙuri My Besty babu abinda zai kashe ki in Sha Allahu, wahala ce dai anshata kuma in sha Allah
baza amaimaita irin taba”.

Sai kuma ta kalli Moddibo da idanunsa ke lumshe yana motsa laɓɓansa amma bisa duk kan alamu yana
sauraron tattaunawar wa tasu tace.

“Kin manta nima lokacin haka kike ta min dariya idan kin tuna alokacin har ce miki nayi kema kwana
nawa ya rage Miki amma kika cigaba da dariyar ki”.

Araunane Asma'u taja dogon numfashi tare da cewa.

“Baza ki gane bane Khausar Ni ba maganar dariya nake Miki ba Ni dai yanzu dan Allah ki daina yimin
dariya,yanzu ina Yah Moddibo yake ki bashi wayar”.

Cikin tausayinta da kuma yanda take jin shesh-sheƙan kukanta Khausar tace.

“Menene? me zaki ce masa?”.

Asanyaye Asma'u tace.

“Ni dai dan Allah ki bashi wayar”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh”.

Kana ta sanya wa Moddibo wayar akunnensa.

Ahankali ya juya ya kalleta kana ya ɗaura hannunsa akan nata ya riƙe wayar.

Asma'u kuwa da muryanta ya gama dishewa da kuka tace.

“Yah Moddibo”.

Ahankali ya ɗan runtse idanunsa yana mai jin tausayinta, rauninta, damuwarta, domin jinta yake tamkar
jininsa tsatsonsa yana jinta tamkar yanda yake jin Rahama Aransa, cikin sanyi da tausasawa yace.

“Na'am Asma'u me ya faru? Me yake damunki?”.

Kuka ta fashe dashi cikin dashewar murya tace.

“Yah Moddibo bani da lafiya ni dan Allah kazo ka ɗaukeni”.

Cikin fesar da numfashi Moddibo ya ɗan gyara zamansa tare da cewa.


“Kiyi haƙuri Asma'u, Kwantar da hankalinki ki daina kukan ki faɗa min meke damunki!?,Mene matsalar
ki?”.

Cikin son danne kukan dake taso mata tace.

“Bani da lafiya zazzaɓi nake ji ƙafafuna, bayana, kaina, duk ciwo suke min”.

Ahankali yace.

“Toh kiyi haƙuri Yi shiru yanzu me kike so?”.

Tana shesh-sheƙan kuka tace.

“So nake ka kawo min Khausar kuma kaima kazo”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Toh kiyi shiru in Sha Allahu zan kawo miki ita”.

Cikin muryanta da bai fita sosai tace.

“Yanzu fa?”.

Kai ya gyaɗa mata kamar tana gabansa yace.

“Eh in Sha Allahu yanzu”.

Ya ƙarashe maganar yana mai jin matsanancin tausayinta kasancewar yasan wanene Dr Jameel mutum
ne mai shegen fitina kana yasaba neman mata ya saba ko yaushe rayuwarsa da mata sannan yasan
tunda sukayi maganar Aurensa da Asma'u ya daina neman mata, tun lokacin yake fama da Azumi yasan
ya tara fitinar da tafi ƙarfinsa shi kansa shiyasa yake jin tausayinta dan ya san ya mata wawan riƙone.

Cikin sanyi ya fesar da numfashi kana ya cigaba da cewa.

“Kiyi haƙuri ki share hawayenki kuma ki daina kuka, kukan da kike yi zai sa kiki zazzaɓi da ciwon kai”.

Kai ta gyaɗa kamar yana ganinta ta share hawayenta tare da cewa.

“Toh ka bawa Khausar ”.

”Toh”.

Yace kana ya miƙawa Khausar wayan tare da faɗin.

“Tashi, tashi ki shirya mu tafi”.

Khausar kuwa cikin sanyi da tarin tausayin aminiyar nata tace.

“Asma'u kiyi haƙuri ganin nan zuwa ki daina kukan dan Allah ”.
Ba tare data tsaida kukan nata ba tace .

“Nikam dan Allah kizo kuma idan akwai magani ki kawo min”.

Murmushi Khausar tayi kana ta kalli Moddibo da fuskarsa ta nuna damuwa numfashi ta fesar tare da
cewa.

“Kamar ya in kawo kiki magani Asma'u!,Keda kike tare da Likita?,Ai ke kece gidan magani”.

Sabon kuka ta fashe dashi kana tace.

“Baza ki gane bane yanzu ma yamin allurai sannan yaban magunguna kuma duk nasha”.

Ajiyar zuciya Khausar ta sauke tare da cewa.

“Toh kiyi haƙuri in Sha Allahu zaki ji sauƙi ”.

Kai ta gyaɗa tare da katse kiran kana ta mike suka fito.

A Corridor sukayi kiciɓis da Innayi wacce bisa alamu taje ta gaida Didi ce ta dawo cike da kulawa ta
kallesu kana tace.

“Lafiya ina zaku je?”.

Kallon Khausar Moddibo yayi kana cikin sauri yace.

“Zamu je tayi Anti nytel ne”.

Kai Innayi ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan amma da sassafe haka?”.

Yana kallon Khausar data ɗan lumshe Idanunta yace.

“Eh”.

Kai ta jinjina kana tace

“Ok kuma naga wancan zuwan nata da daddare kuka je wannan kuma da sassafe?”.

Yana riƙe hannun Khausar acikin nasa suka nufi hanyar fita kana yace.

“Eh”.

Kai ta gyada tare da shigewa ta nugi kitchen.

Nan ta samu Hadimai da already sun fara girki.


Dr Jameel ne zaune dafe da kansa fuskarsa ɗauke da Murmushi.

Cikin kasala da alamun rashin wadataccen bacci ya muƙe a saɓule jin ana knowking ɗin ƙofar.

A hankali ya buɗe ƙofar ganin Khausar ce agaba yasa ya ɗan ja baya cikin sauri Khausar ta wuce cikin
falon tare da cewa.

“Barka da safiya Dr”.

Fuskarsa ɗauke da ƙayataccen Murmushi yace.

“Barka dai Bestynmu”.

Sai kuma yayi saurin juyawa tare da rungume Moddibo cikin matsanancin farin ciki yace.

“Ka gama min komai Aminina kuma ɗan uwana ka bani abinda ban taɓa samun irinsa ba arayuwata ta
duniya”.

Ya lumshe idanunsa yana tuna irin garar daya kwasa awajen Asma'u kana ya cigaba da faɗin.

“Dukk biye-biyen neman Matana ban taɓa samun gamsuwa, nutsuwa, da kwanciyar hankali ba kamar
akan wannan ƙanwar taka kagama min komai”

Ɗan tsuke fuska Moddibo yayi kana yasa hannunsa na dama ya make ƙeyensa tare da rike ƙunnensa
yace.

“Ka kuwa san abinda kake faɗa?,”.

Still fuska ɗauke da murmushi Dr Jameel ya gyaɗa masa kai tare da cewa.

“Na sani mana, nasan me nake faɗa kawai dai na rasa ta ya zan nuna farin cikina ne.

Ji nake kamar in kira Ummi in sa mata albarka saboda ta bani abu mafi daraja da daɗin samuwa
arayuwar duniya”.

Zare idanu Moddibo yayi kana yace.

“Baka da hankali fa”.

Kai Dr Jameel ya gyaɗa yana lumshe idanunsa kana har zuwa lokacin fuskar na ɗauke da Murmushi yace.

“Sosai ma bani da hankali, Wallahi bani da ishesh-shen hankali saboda tun jiya da hankalina ya tafi cikin
gajimare har yanzu bai dawo ba.

Ni kaɗai nasan irin daɗi da shaukin dana kasance”.


Da ɗan ƙarfi Moddibo ya matsa kunnensa wanda yasa Dr Jameel sakin ƙaramin ƙara.

Moddibo kuwa yana cigaba da matsa kunnensa yace.

“Shine ka azabtar min da ƙanwata da fitinar da baka kasheta ba na tsawon watanni ko?

shine yanzu dare ɗaya zaka sauke akanta ko?”.

Langwaɓar da kai Dr Jameel yayi tare da cewa.

“Ƙanwar taka ce tafi zuma daɗi baki ɗaya ta gigitani ta gigita min lissafi duk ta rikitani”.

Ƙeyensa Moddibo ya kuma makewa da karfi kana ya wuce cikin falon.

Da sauri Khausar da tuni tayi ciki, ta juya ta kallesu kana tace.

“Dr ina Asma'u take?”.

Da hannu ya nuna mata Corridor da bedroom ɗin su yake.

Da sassarfa ta wuce.

Moddibo kuwa zama yayi akan kujeran kana Dr Jameel ya zauna gefensa.

Asma'u kuwa cikin yanayin baccin daya fara ɗibarta ta fara jiyo sautin muryan Khausar cikin sauri ta
yunƙura da niyyar tashi.

Da sauri Khausar ta tura ƙofa ta shiga Asma'u kuwa da wani irin sauri ta runtse idanunta kana ta koma ta
zauna tare da sakin ƙara tana yarfe hannunta.

Cikin sauri Khausar ta matsa ta zauna kusa da ita kana ta riƙe hannunta tare da cewa.

”Allah sarki Asmeeyn Ummi an girma”.

Harara Asma'u ta galla mata da kumburarrun idanunta tace.

“Wani an girma?,An dai zalinceni!, Kawai ai wannan zalincine ba girma ba”.

Murmushi Khausar tayi wanda ya bayyanar da hoƙoranta tace.

“Kema kiji abinda ake ji, kiji abinda ko wacce ƴa mace take ji fatan mu dai Ubangiji Allah yayiwa
iyayenmu albarka ya kuma saka musu da mafi kyawun sakamako da tarbiyyan da suka bamu Ubangiji
Allah ya bamu zaman lafiya a gidajen aurenmu”.

Cikin shesh-sheƙa Asma'u tace.

“Ameen ya Allah amma Ni dai wallahi tare zamu tafi”.


Zare idanu Khausar tayi tare da cewa.

“Tare zamu tafi?,Na isa? A,a ni kam ba isa in ɗauke wa Dr Mata ba”.

Ɗan hararanta Asma'u tayi kana tace.

“Idan ke baki isa ba Yah Moddibo ya isa?”.

Sai kuma ta fara yunkurin miƙewa tana cewa.

“Ina Yah Moddibo?”.

Ganin yanda take ciccije bakinta yasa Khausar faɗin.

“Ki zauna mana bakya jin zafi ne”.

Tana goge hawayen fuskarta tace.

“Ai nasha magunguna na fara jin yana raguwa sosai yanzu”.

Kai Khausar ta gyada tare da cewa.

“Toh yanzu ina zaki je”.

Tana cije gefen lip inta na ƙasa tace

“Zanje wajen Yah Moddibo”.

Dariya Khausar ta sanya tare da faɗin.

“Iyeee wai ke bakya jin kunya ne?”

Hararanta Asma'u tayi kana tace

“Eh ɗin bana ji,Ke lokacin da aka miki kunya kika ji?,Ina gaban su Ummi kika je kika rinka Zuba taɓara son
ranki”.

Dariya Khausar ta sake fashewa dashi ganin yanda Asma'u ke wani ciccije baki alamar har yanzu bata
gama warware ba tace.

“Eh amma ai agaban mata nayi ba Maza ba”.

Shiru Asma'u tayi kana ta fara ƙoƙarin miƙewa har ta mike ta fara tafiya miƙewa Khausar tayi tabi
bayanta tare da riƙe hannunta ahaka suka fito falon kallonsu Moddibo yayi ganin yanda Asma'u ke
tafiyar yasa ya sunkuyar da kansa ƙasa ya kalli gefe tare da cewa.

“Asmeeyn Ummi kin fito?,”.

Cikin da shashshiyar muryanta tace.


“Eh Yah Moddibo ”.

Akuma dai-dai lokacin suka ƙarasa cikin falon zama sukayi akan 2sitter ahankali Asma'u ta zame ta
kwanta kana ta ɗaura kanta akan cinyar Khausar.

Ahankali Khausar ta gyara zamanta kana ta tallafo kanta.

Moddibo kuwa ba tare da ta kuma sallonta yace.

“Asmeey zaki danne Baby fa”.

Murmushi Asma'u tayi duk da yanayin da take ciki saboda ya bata dariya ta lura Yah Moddibo yana
masifar tattalin cikin nan juyawa Asma'u tayi ta kalli tudun cikin Khausar hannunta na dama tasa kan
kitchen tare da cewa.

“Baby kayi haƙuri nima yau ina buƙatar cinyar Mamynka”.

Murmushi Khausar tayi kana tace.

“Yama isa tun kafin ya fito,ai tare ya ganmu ma”.

Ahankali Moddibo ya shafa sajensa yace.

“Adai barshi kar ta kura mishi”.

Dr Jameel dake Murmushi ya kalli Moddibo yace.

“Iyeee komai yaya dai yau zai bari ayi tattalin Umminsa”.

Murmushi suka baki ɗaya kafin Moddibo ya kalli Asma'u yace.

“Ya jikin?”.

Asanyaye tace.

“Da sauƙi Yah Moddibo ”.

Kallonsa ya mayar kan Dr Jameel tare da cewa.

“Ya baki magunguna ko? Kuma kinci abinci?”

Kai ta girgiza tana ɗan lumshe Idanunta tace.

“A'a banci ba”.

Shiru yayi kafin yace.

“Toh yanzu me zaki ci insa akawo Miki daga gida?.

Cikin sauƙe numfashi Khausar tace.


“A'a bari in shiga kitchen in girka mata”.

Da sauri Moddibo ya girgiza kai tare da faɗin.

“A'a bana so”.

Kai ta langwaɓar tare da cewa.

“Yah Mu'allim zan iya mana agida ma ina shiga inyi girki ”

Cikin sauƙe numfashi yace.

“Toh shikenan”.

Asma'u kuwa miƙewa tayi tare da cewa.

“Toh mu tafi kitchen ɗin tare”

Kai Khausar ta girgiza tare da cewa.

“A'a ke kam ki wuce bedroom ki kwanta naga kamar bacci kike ji”.

“A'a muje dai”.

Cewar Asma'u tana lumshe Idanunta.

Numfashi Khausar ta fesar tare da kallon yanda take lumshe idanu tace

.“A'a ke dai kije kiyi baccin”.

Ahankali tace.

“Toh”.

Hannunta Khausar ta riƙe suka wuce bedroom ɗin kwanciya Asma'u tayi kana Khausar ta zauna gefenta
tace.

“Amma kinyi amfani da Ruwan ɗumi sosai?”.

Kai Asma'u ta gyada tare da cewa.

“Eh ya sassani kuma ya ban magunguna sannan yamin allurai kuma ya shafa min wani ma a wurin
Alhamdulillah naji sauƙi sosai yanzu ɗazun fa ko numfashi nayi zafi nake ji kamar raina ake zarewa”.

Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe kana tace.

“Toh ba komai yanzu dai bari na miki abinda zaki ɗan ci mai zan dafa Miki?”.
Idanunta ta juya tare da taune lips ɗin ta tace.

“Nikam ma bana jin yunwa”.

Cike da kulawa Khausar ta dafa kafaɗarta tace.

“A'a ki dai fadi me kike so adafa miki?”.

Rau-rau tayi da idanuna tare da cewa.

“Nifa bana jin kwaɗayin komai”.

Shiru Khausar tayi na tsawon minti ɗaya alamar tunani kafin ta mike tace.

“Bari dai naje kitchen in ga abinda zan Miki.

Ko dai in gasa Miki nama?

Dan nasan ki”.

Tana gyara kwanciyarta tace.

“Eh”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da wucewa kitchen.

Kallon Moddibo Dr Jameel yayi kana yace.

“Yanzu kusan 1month fa kenan da Khausar taje anti nytel ya kamata ace gobe ko jibi ku samu ta sake
zuwa”.

Cike da gamsuwa Moddibo ya gyara zamansa yace.

“Eh nima dama gobe ko jibi nake so muje,dama tun bayan 2weeks ma naso muje toh ya kama bikin
nanne da muka tafi amma in sha Allah gobe ma zan kawo ta”.

Kai ya jinjina kana yace.

“Toh Allah ya kaimu”.

“Ameen”.

Ya amsa kana suka cigaba da hira...

A gefen Khausar kuwa cikin sauri sauri ta gasawa Asma'u nama mai ɗan romo-romo sai tashin ƙamshi
yake kana ta dafa Cous-cous da yaji Carrot da grean beans daya ƙawata kyawunsa gashi yayi wasar-
wasar abin sha'awa sai kuma tayi miyar hanta da yayi kyau sosai bayan ta gama ta zuba a Warmer
kasancewar duka ayyukane masu sauƙin yi ta ɗauki na Moddibo da Dr Jameel ta kai musu Falo kana ta
koma ta ɗauki nasu ta wuce bedroom ɗin Asma'u.
Tana shiga ta samu Asma'u na bacci jin alamun tana jin yunwa yasa ta zauna a tsakiyar ɗakin kana ta
zuba a plate ta fara ci.

Tana cikin ci ta ɗago kanta ta kalli Asma'u jin alamun Asma'u tayi motsi.

Asma'u kuwa cikin baccinta taji kamar sautin ƙaran cokali tare da yunwar daya murɗeta ne ta mike ta
zauna.

Dan ɗan murmusu tayi sai kuma ta miƙe ta zauna.

Khausar dake kallonta tace.

“Ya dai”.

Cike da farin ciki ta shafa cinyoyinta kana tace.

“Zafin ya tafi fa”.

Ajiyar zuciya Khausar tayi tare da kai spoon ɗin bakinta tace.

“Haba dai”.

Cikin tabbatarwa ta gyada mata kai sai kuma ta sakin sanyayyar ajiyar zuciya tace.

“Wlh kuwa”.

Ta ƙare maganar tana gyara zamanta.

“Masha Allah magunguna sun kama aikinsu”.

Cewar Khausar na Murmushi.

Asma'u kam cikin jin daɗi tace.

“Wlh kam".

Warmer Khausar ta janyo tana ƙara musu abincin tace.

“Toh saƙƙo muci abinci”.

Kai ta gyada kana ahankali ta saƙƙo ta zauna suka fara cin abinci bayan sun gana Khausar tace.

“Akwai magungunan da zaki sha yanzu ne?”.

Kai ta girgiza tare da cewa.

“A'a sai bayan Azahar zan sake shan wasu”.


Tana tattara plate ɗin waje ɗaya tace.

“Toh shikenan”. Daga nan sukaci gaba da hira.

Wunin ranan dai haka Khausar ta yini agidan Asma'u koda Moddibo yace su tafi cewa tayi yayi haƙuri sai
bayan Sallar Isha'i yazo ɗaukar ta.

Tsaye suke a abakin gate kallon Asma'u Khausar tayi tare da cewa.

“In sha Allah daga nan zamu wuce gidan Addah Asiya”.

Cikin sanyin Asma'u tace.

“Wallahi nima ina son zuwa”.

Dr Jameel da baki ɗaya nutsuwarsa ke kanta tace.

“Ki bari idan kin sake warware wa in Sha Allahu zan kai ki”.

Langwaɓar da kai tayi tare da cewa.

“Toh ba ance kwanan nan zasu tafi ba?”

Kai Khausar ta girgiza tace.

“A'a ance dai kwanan nan zasu koma kuma naji ance anan zai gama hutunsa”.

Kai Asma'u ta gyada tare da cewa.

“Toh shikenan In sha Allahu kafin su tafi zamu sake zuwa mu wunin mata ko?”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da faɗin.

“Eh in sha Allah”.

Daga nan sukayi sallama suka fita.

Suna fita kai tsaye gidan Asiya suka nufa.

Dai-dai lokacin kuma Asiya ce da Dr Zakariyya ke zaune a falo suna hira jin ana knowking yasa Dr
Zakariyya miƙewa ya buɗe.

Khausar ce agaba Asiya na ganinta ta miƙe da gudu taje ta rungumeta Moddibo kuwa cikin Murmushi
yace.
“Addah Asiya abi ahankali”.

Murmushi tayi kana ta riƙe hannun Khausar tare da cewa.

“Adda Khausy tun shekaran jiya nake ta zuba ido ina so in ganki ban ganki ba”.

Cunno Baki Khausar tare da kallon Moddibo da suke magana da Dr Zakariyya tace.

“Yah Mu'allim ne ai”.

Murmushi Moddibo yayi kana ya marairaice fuska yace.

“Komai dai Ni ko wani laifi nawa ne komai ace Yah Mu'allim toh naji na ɗauki laifina”.

Cikin narke fuska tace.

“Ato ai kasan hakane”.

Murmushi yayi.

Asiya kuwa kitchen ta shiga ta kawo musu abubuwan motsa baki taɓa ka lashe.

Khausar ce dai ta ɗanci Amman shi Modibbo ko ruwa bai sheba.

Bayan sun gama hira kusan karfe goma na dare sukayi musu sallama suka tafi.

Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya Khausar na samun kulawar Uwar mijinta da danginsa Innayi ma na
iya bakin ƙoƙarin ta kana suna waya da Momy, Ummu, Hajja Nana, akai-akai hakama Aunty Ruƙayya da
Aunty Hajara.

Bayan sati Uku Asma'u da Khausar suka je gidan Asiya suka yini mata bayan sati ɗaya da zuwa su Asiya
da Dr Zakariyya suka koma Indi'a...

Washe garin ranan da suka tafi a Nigeria Amina ce zaune a falo yayin da Hajiya Bunayya ke tsaye tana
bubbuga ƙafa tare dasa hannunta tana bubbuga mazaunanta jin yanda masifaffun tsutsotsin nan ke
addabar rayuwarta wanda da ƙanane suke fita yanzu kuma manya ne Amina kuwa Alhamdulillah bisa ga
duk kan alamu jikinta yayi sauƙi sosai kasancewar har ta fara maida ƴar ƙibanta alamun ta samu sauƙi
sosai-sosai.

Ahankali ta tallafe haɓarta tana kallon Mahaifiyarta ta zuwa yanzu ta fahimci tsutsotsin nan sun haukata
mata mahaifiya saboda ko yaushe ƙoƙari take ta cire zaninta ta yasar ita take ƙoƙarin hanawa kamar dai
yanda yanzu ma take ƙoƙarin cirewa.
Cikin sauri Amina ta miƙe cikin rauni da zubda hawaye tace.

“Dan Allah Umma kada ki cire zanin”.

Alalace ta juya ta harareta tare da cewa.

“Kada in cire zani in zauna kenan su cinyeni ke kin san abinda nake ji kuwa? baki ga tsutsotsin nan yanda
suke cina ba ko kuma dan ke kin samu lafiya bake kike shan azaba yasa zakice haka, ai dacan da kike
zazzaro harshe waya ce ki daina”.

Ta ƙare maganar tana kwayewa Amina ɗuwawunta tare da cigaba da faɗin.

“Ki ga fa”.

Cikin sauri Amina ta runtse idanunta kana tace.

“Innalillahi wa'inna alaihi raji'un”.

Ganin manya-manyan tsutsotsin dake cin Mahaifiyarta cikin matsanancin tashin hankali ta saki ihu dai-
dai lokacin da Lamiɗo ya hau Farandar falonta saboda yanda Amina tayi ta kuka daren jiya akan cewa ya
kai Hajiya Bunayya asibiti cikin sauri ya karaso Falon yayin da Momy ke biye dashi abaya ganin haka yasa
Momy saurin ɗaukan zanin ta daura mata.

Ga mamakinsu sai suka ga Hajiya Bunayya ta fara buge-buge tare da ɗaga hannu zata daki Momy
cikin sauri Lamiɗo ya kamo hannayenta ya riƙe.

Dariya ta fara ƙyalƙyalawa alamun hauka ta tabbata tuburan ziraran.

Kuka sosai Amina ta fashe dashi.

Dai dai lokacin Haiydar da Sulaiman suka shigo ganin haka yasa Sulaiman rungume Haiydar suka fashe da
kuka cikin rauni da shesh-sheƙa Sulaiman yace.

“Haiydar kaga Ummana yanda ta koma”.

Shiru yayi ganin yanda take ƙoƙarin ƙwace hannunta Momy kuwa duk da yanda take ƙoƙarin kawo mata
duka sai da ta jawo zanin ta ɗaura mata ta baya.

Wani irin abu ta fara kamar rawa kamar tsalle alamun dai hauka Muraran ziraran.

Kai Lamiɗo ya girgiza tare da juyawa ya kalli Gimbiya Dadu da tazo wacce hayaniyar dake faruwa ne yasa
taxo tana shigowa taga Hajiya Bunayya keyi ta saki ƙara ta faɗi awajen atake a wurin ɓarinta ɗai ya
shanye tun, kafin aɗagata ɓarin jikin ta ya mace.
Cikin gigita da Kiɗima Lamiɗo ya kalli Haiydar kana yace.

“Haiydar jeka kira min bappanka”.

Cikin rawan jiki Haiydar ya juya ya fita yaje ya kirasa.

Hajiya Bunayya kuwa ƙoƙarin duka take kai masa ɗankwalin kanta ya since ya ɗaure hannunta.

Dai-dai lokacin da ƙanin nashi ya shigo cikin tashin hankali Lamiɗo yace.

“Yusuf ka ɗauki Hajiya Bunayya ka Kaita Sycatry na cikin Taraba”.

Cike da damuwa yace.

“Innalillahi wa'inna alaihi raji'un Sycatry kuma?”.

Araunane Lamiɗo ya kalli Hajiya Bunayya dake wani irin fusga tana ƙyalƙyala dariya yace.

“Toh ya zamuyi Yusuf?Bata da wani amfani daya wuce mu Kaita Sycatry dama arayuwa duk abinda
mutum zai yi yabi ahankali”.

Kuka sosai Bashir keyi tamkar ransa zai fita Lamiɗo kuwa cikin sanyi ya cigaba da cewa.

“Gashi tun ba aje ko ina ba Ubangiji Allah ya haɗa mata sakamakon aikin ta ya liƙa mata su atsakiyar
kanta sun zame mata matsala, muma sun zame mana matsala tun da komai yaya zukatanmu nada Imani
zamuji tausayinta”.

Cikin azabebben kuka Amina ta kalli Lamiɗo tare da faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Ummana yanzu Sycatry za'a kai ta?”.

Cikin sauƙe zazzafan ajiyar zuciya yace.

“Yanzu Amina anan za'a barta tayi ta hauka?,Mutane suna kallonta tana since zani idan mun barta anan
cikin gari zata shiga tayi ta yawo tana bayyana tsaraici kinga ai baiyi ba”.

Cikin matsanancin kuka da shesh-sheƙa Amina ta gyada kanta tare da faɗin.

“Hakane kam Abba”.

Alh Yusuf kuwa janta yayi ya sata a mota.

Lamiɗo kuwa sai alokacin yaje ya ɗaga Gimbiya Dadu da tuni ta sume.

Cikin kiɗima ya Kaita asibiti, inda duk binciken da akayi likitoci suka tabbatar masa da cewa ta kamu da
ciwon ɓarin jiki awanna ranan dai haka suka yini a asibiti koda ta farfaɗo gefen bakinta ya karkace tana
magana yawu na zuba cikin zubda yawu da magana irin na wanda suka samu shanyewar ɓarin jiki tace.
“Ohhh nima dai ga karshena nayi ta cin ƴaƴan mutane ina ta zubar da cikin ƴaƴan mutane idan naga ɗan
da yamin maiƙo in lashe in naga mai ciki inlamushe”.

Cikin sauri da matsanancin mamaki da tashin hankali Lamiɗo ya rufe mata baki tare da cewa.

“Dadu Ki daina faɗan haka dan Allah ki dai na faɗa ”.

Bakinta na tsulalar da yawu tace.

“Ai dole in faɗa ayyukana ne in ban faɗesu ba ya zanyi.

Ni na aikata kana ganin kamar zargina mutane suke da suke cewa Ni mayyace.

Tabbas ni mayyace da gaske amma kai Allah ya tsare ka da ƴan Uwanka dama nida ƴar uwata siya
mukayi bawai tsatson mu bane”.

Araunane Lamiɗo yace.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un hasbunallahu wani'imal wakin”.

Haka yaita addu'oi wai ko zai samu ta bar tone-tone ta kama addu'a amman a banza.

Washe gari da safe aka sallamosu a asibiti suka dawo gida saboda Likitoci since babu abinda zasu iya
mata dole yasa Lamiɗo ya nemo masu aiki wanda zasu riƙa kula da ita.

Yayin da Hajiya Bunayya da Hajiya Lami ke can asibiti suna can suna buga wash-shagare wallensu a
haukace.

A kuma dai-dai wannan ranan Khausar ce zaune a falonta kunnenta maƙale da waya tana hawaye cikin
rauni tace.

“Yanzu Momy haka Umma da Hajiya Lami suka dawo?

Ita ma Gimbiya Dadu haka ta dawo?”.

Cikin sanyi da damuwa Momy tace.

“Wlh Khausar am ai rayuwar nan mu bita a sannu”.

Cikin zubda hawaye Khausar ta gyara zamanta tare da cewa.

“Dama Momy ina faɗa Miki kallon da Gimbiya Dadu take yimin yana ban tsoro kullum cikin kareta kike”.

Ajiyar zuciya Momy ta sauke kana tace.


“Toh Khausar baka da tabbaci ka isa ka tuhumi mutum ne?

ba kiji Manzon Allah (S.A.W.)yace _Azzhana zhambu Walau kana haƙƙun_ ai zato zunubi ne koda ya
kasance gaskiya amma yanzu da taxo ta faɗa da bakinta ai taga *SAKAYYAR ta*”.

Kai Khausar ta jinjina tare da faɗin.

“Allah ya rufa mana asiri ya kare mu”.

Dai-dai lokacin Moddibo ya shigo ganin tana hawaye yasa yayi saurin shigowa ciki, tare da zama a
gabanta kana ya sanya hannunsa ya share mata hawaye.

Yana mai kallonta, sai kuma ta ɗan sauƙe ajiyan zuciya, ganin yanda ya zuba mata idanu yasa tace.

“Toh Momy sai anjima”.

Kana suka katse kiran.

Ahankali ya janyota jikinsa ya ɗaura hannunsa akan cikinta yana shafawa saboda yanzu cikin yashiga
wata na biyar zuwa na shida haka yasa cikin ya ɗan bayyana ya girma yayi ɗas a jikinta gwanin ban
sha'awa ganin yanayin fuskarsa yasa tace.

“Ya akayi Yah Mu'allim?”.

Fuska ya narkar da damuwa atare dashi yace.

“Minha kuka fa kike yi ya za'a yi kintam bayeni ya akayi?”.

Asanyaye ta bashi labarin da Momy ta bata ta faɗa mata sai abinda take ga sirrinsu ne bai kamata ya
saniba ta ɗan sakaya.

Jikinsa ya sake janyota ya rungumeta kana yace.

“Mu godewa Allah, Allah ya sake tsarkake zuciyanmu Allah ya hanamu samun damar da zamu cutar da
wani, Allah ya hana wani ma samun damar da zai cutar damu.

Cikin sanyi da rauni ta gyara zamanta ajikinsa tare da cewa.

“Ameen”

Yana shafa gadon bayanta yace.

“Kuma ki daina damuwar nan ki riƙa yi musu addu'a Ubangiji Allah ya gafarta musu”.

Tana ɗan lumshe Idanunta tace.

“In sha Allahu ”.


Sake janyota jikinsa yayi, bakinsa ya kai saitin kunnenta cikin wata kasalalliyar murya mai cike da shauƙi
da bege yace.

“Minha babu matsala ban takura ki bako?”.

Cikin lumshe idanu da yanda hannunsa ke yawo a sassan jikinta ta fesar da wani sanyayyan numfashi
tana sake shiga jikinsa tace.

“Ya zanyi Yah Mu'allim tunda kana da buƙata?Kuma dole in ɗauke buƙatar ka tunda bana so wata ta
raɓeka”.

Ya tsarsa manuniya da babba yasa ya kamo tsinin hancinta ya jijjiga tare da cewa.

“Kishi! Kishi!! Kishi!!!”.

Cikin Cunno baki ta langwaɓar da kai kana tace.

“Toh ba dole inyi kishi ba,

Idan banyi kishin kaba waye zai yi kishinka a duniya”.

Sai kuma ta marairaice fuska tace.

“Ka ƙi kayi min al'ƙwarin baza kayi min kishiya ba”.

Jawota jikinsa yayi ya rungumeta kana ya haɗe bakinsu waje ɗaya daga nan yashiga sarrafa ta cike da
bege da tarin ƙaunarta...

Bayan wani ɗan lokacin Alhamdulillah yanzu cikinta ya cika wata bakwai Cif-cif.

Ahankali take sauka kan tsep ɗin sauƙa Falon Didi.

Didi dake zaune tayi saurin miƙewa hangota da tayi kana ta riƙe hannunta cike da kulawa tace.

“Ba nace miki sauƙan nan idan yana wahalar dake ki bari ba?,Idan kina son ganina ki riƙa kirana in zo
ba”.

Murmushi tayi tare da faɗin.

“Toh ai Didi Likita ma da kansa yace na riƙa motsa jiki na zaman bazai yiba”.

Kai Didi ta jinjina tare da cewa.

“Haka ne kam ƴata zo ki zauna me kike so in dafa Miki?”.

Murmushi tayi kana ta maida kallonta kan Moddibo da Ibraahim dake shigowa cikin langwaɓar da kai
Ibraahim yace.
“Toh koma menene za'a dafa adafa dani”.

Dariya Didi tayi tare da cewa.

“Wannan ba naku bane ”.

Murmushi Moddibo yayi tare da shiga Falon kana ya zauna agaban Khausar tare da janyo ƙafarta ya
ɗaura akan cinyarsa yana ɗan jan yatsunta sai kuma ya maida kallonsa kan Didi yace.

“Didi kalli ƙafafun tan nan kamar kumbura sukayi?”.

Juyawa Didi tayi ta kalli ƙafafun kana tace.

“Eh nima naga kamar kumbura sukayi amma Dr Eshaa tace bakomai dan tun shekaran jiya da naga
kumburin na kirata tazo ta duba ta tace bakomai wannan Normal ne mafi akasari wasu na fuskantar
haka daga ciki wata Bakwai kuma kaga kumburin bamai yawa bane”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe yana cigaba da matsa ƙafafun yace.

“Toh shikenan ”.

Didi kuwa Kitchen ta shiga ta ɗauko Pride rice da yaji Vegetables da naman zabbi sai Perpersoup ɗin Kifi
da yaji kayan ƙamshi ta kawo fitowa dasu tayi da plate guda biyu ta zubawa Khausar kana tasa mata kifin
agefe.

Kana ta zuba aɗaya plate ɗin tasa spoon biyu aciki ta ajiye atsakanin Moddibo da Ibraahim.

Daidai lokacin Rahama ta fito daga ɗakinta ware idanunta tayi tare da cewa.

“Didi anyi Babu Ni ko?”.

Murmushi Didi tayi kana tace.

“Na isa ƴar Autana bata ciba ɗauko plate kizo ki ɗibi na ki”.

Kai ta gyaɗa kana ta juya ta shiga kitchen ta ɗauko plate tazo ta zuba suka fara ci suna hira...

Yayinda hadimai keta zuryan aikace-aikacen yau da kullum.

A haka rayuwa ta cigaba da tafiya Alhamdulillah Khausar na samun wadatacciyar kulawa daga wajen
tako wani sashin, sosai rayuwa take tafiya zuwa yanzu cikinta ya cika wata tara Cif-cif amma dai na ƙuda
har yanzu bai zoba kuma.
Cikin kulawa Asma'u da tazo mata yini, ta zuba mata ganin ta yunƙura ta nufi bedroom cikin sauri
Asma'u tace.

“me kike so in kawo Miki?”.

Kai ta girgiza tare da faɗin.

“Bakomai kawai ina so in shiga bathroom ne yau tunda gari ya waye fitsari da yaƙi ƙarewa nake tayi”.

Ɗan zare idanu Asma'u tayi tare da cewa.

“Fitsari kuma?,Kin fa ɗawa Dr?”.

Kai ta girgiza kana tace.

“A'a ban faɗa masa ba bakomai ai”.

Cikin cikin kulawa Asma'u tace.

“Toh bari in tai maka Miki?”.

Ƴar dariya Khausar tayi tare da faɗin.

”Laaa da kin bari babu inda ke min ciwo fa”.

Cike shaƙuwa Asma'u ta gyaɗa kai tace.

“Toh shikenan ”.

Khausar kuwa ban ɗakin tashiga.

Asma'u kuwa wayarta ta dauka tare da kiran Dr Jameel yana ɗauka tace.

“Hello Dr”.

Daga ɗaya ɓangaren cike da begenta yace.

”Na'am dear ya akayi?”.

Cikin sauƙe numfashi da da kulawa tace.

“Kaga tun daga ɗaxun da muka zo zuwa yanzu bai wuce awa ɗaya zuwa biyu ba ko?”...

Kai ya gyaɗa mata tare da faɗin.

“Eh”.

Numfashi ta fesar tare da cewa.


“Toh wallahi daga lokacin zuwa yanzu Khausar ina ga tashiga ban ɗaki tayi fitsari ya kai sau biyar nace ta
faɗa maka tace wai babu matsala kawai yau yawan fitsari ne take fama dashi”.

Da mamaki yace.

“Ha'a ikon Allah kuma tace ba abinda yake mata ciwo?”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Eh”.

Cikin sanin makamar aiki da yanayin masu ciki yace.

“Alamun na ƙuda ne yana iya tashi ko yaushe”.

Cikin sauƙe numfashi tace.

“Kuma fa tace babu abinda yake mata ciwo”.

Ajiyar zuciya ya sauke tare da faɗin.

“Eh ba komai bari idan ta fito sai ki haɗa Ni da ita”.

Kai ta gyada kana ta katse wayar, jim kaɗan Khausar ta fito.

Tana fitowa Moddibo na shigowa kasancewar Dr Jameel ya kirasa ya faɗa masa yana shiga ya kama
hannunta ya zaunar da ita akan kujera kana ya zauna aƙasan lallausan Darduma tare da k...

Littafin Sakayya dai na kuɗi ne, 1k ne, ki biya ki rabu da haƙina a kanki.

0661110170 Gtbank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number
09097853276.

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH
69

*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n
nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai
sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan
mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in
kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a
banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account
no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na
faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki
kenan*

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar
zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan
manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har
budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har
baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari,
da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum
buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a
idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in
kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki
kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda
kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da
sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba
miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki
wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama
yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki,
ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa
Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito
miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar
infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma
maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi
ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita
tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a
saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana
ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda
yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin
san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo
kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567 sai ki turo min shaidar biyanki,
domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan
ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah
zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce
dai GARKUWAR MA'AURATA.

69

A kan ƙafafunsa ya durƙusa ya zama na kansa na dai-dai kan cikinta ahankali ya dafa cikin, cikin
amintacciyar murya mai ɗauke da nutsuwa da tarin kulawa ya fara yi mata addu'a na tsawon minti
bakwai sai kuma ya ɗago ya kalleta ita ɗin ma shi take kallo muryansa ɗauke da Amintaccen kulawa da
jin ƙai yace.

“Minha Viddaa meke damunki?”.

Numfashi ta fesar kana ta girgiza kai tare da cewa.

“Bakomai fa”.

Juyawa yayi ya kalli Asma'u dake kallon Khausar cike da tausayi yace.

“Asma'u menene matsalar ta?”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da faɗin.

“Yah Moddibo daga zuwa na zuwa yanzu fa tashiga ban ɗaki yakai ƙafa bakwai tana fitsari”.

Da sauri ya kalleta kana yace.

“Ba abinda yake Miki ciwo?”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Yah Mu'allim nifa ba abinda ke min ciwo”.

Da damuwa asaman fuskarsa yace.

“Toh ba abinda kikeji?”.


Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Wallahi ba abinda ke min ciwo”.

Yana cigaba da massage ɗin ƙafanta yace.

“Yanzu kuma Dr Jameel ya kirani yace muje asibiti”.

Langwaɓar da kai tayi tare d cewa.

“Nifa ba abinda ke yimin ciwo Yah Mu'allim ai da akwai zan faɗa muku amma wallahi babu?”.

Numfashi ya fesar kana yace.

“Toh amma dai bari na sanarwar Didi halin da ake ciki”.

Ganin yanda ya damu yasa ta gyaɗa masa kai tace.

“Toh shikenan ba laifi kaje ka faɗawa Didi”.

Dai-dai lokacin kuma wayar Asma'u ta hau ruri ahankali Asma'u ta ɗauka ganin Ummi yasa tayi saurin
Picking ta kai kunnenta suka gaisa da Ummi sai kuma taji kamar muryan Momy tana gyara zamanta tace.

“A'a Ummu ina kike?”.

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.

“Ina gidan Momyn Khausar ne na kwana biyu banji labarinta bane shine nazo kuma dana zo ma muke ta
hiranku sai nace bari in kira ku inji Labarin ku”.

Murmushi Asma'u tayi kana tace.

“Nima kuma yau ina gidan Khausar ce ki bawa Momy wayar”.

Wayar Ummi ta bawa Momy suka gaisa Ahankali momy tace.

“Ya dai Asma'u ya jikin Ƙawar taki lafiya ko?”.

Kallon Khausar dake lumshe Idanu Asma'u tayi tare da cewa.

“Momy lafiya lau sai dai yau tunda gari ya waye take ta yawan fitsari dai take tayi banfi awa biyu da
zuwaba fa, amma tayi fitsari yakai sau bakwai”.

Ahankali Momy tace.

“Ikon Allah toh kuje asibiti mana”.

Tana gyara zaman wayar akunnenta tace.


“Eh na kira Dr na faɗa masa yace dai yanzu babu wata matsala tunda Babu abinda yake mata ciwo amma
Yah Moddibo yace zai je ya faɗawa Didi yaji mai zata ce”.

Cikin sauƙe Ajiyar zuciya da fargaba irin na duk wata Uwa ke shiga idan ƴarta na fama da ƙaratowan
naƙudan tsohon ciki tace.

“Ikon Allah toh bata wayar”.

Wayar Asma'u ta miƙa mata karɓa Khausar tayi tare da faɗin.

“Momy ya gajiya?”.

Cikin sanyi Momy tace.

“Lafiya lau Khausar meke ke damunki?”.

Langwaɓar da kai tayi tace.

“Momy Nifa ba abinda ke yimin ciwo”.

Ahankali tace.

“Toh amma kuma iya fitsarin kike?”.

Kai ta gyada kana ta ɗaura hannunta ɗaya akan cikin tace.

“Eh fitsarin ne kawai sai dai yanzu dana shiga ina ganin har da wani ruwa yake fito min”.

“Ok ki faɗawa Dr toh”.

Cewar Momy suka katse kiran.

Dai-dai lokacin kuma Moddibo ya shigo bayansa Didi,Niyna Innayi ce ke biye dashi abaya cikin sauri Didi
ta zauna kusa da ita hakan yasa Asma'u ta ɗan matsa gefe tace.

“Ɗiyata me yake damunki?,Ba abinda yake Miki ciwo?”.

Kai ta girgiza tare da faɗin.

“A'a abinda yake min ciwo”.

Cike da kulawa Didi tace.

“Duk da haka dai mu tafi asibiti”.

Kai Khausar ta gyaɗa.

Nan take suka tafi asibiti kafin su isa ma Already an shirya komai.
Suna isa aka karɓesu aka shirya komai kana akayi duk kan abinda ya kama na gwaje-gwaje.

Bayan an gama gwaje-gwaje Dr Jameel ya fito zuwa lokacin kuma ruwan dake zuban nan zubansa ya
ƙaru sosai shigowa yayi kana ya kalli Niyna ya kalli Didi kallonsa Didi tayi kana ta miƙe tabi bayansa zuwa
office ɗin sa tace.

“Jameel ya akayi?”.

Ƙofan ya ɗan tura tare da zama kan kujera kana ta zauna gefe sai kuma Moddibo dake biye dasu yazo ya
zauna gefen Didi gyaran murya Dr Jameel yayi tare da kallon Didi yace.

“Kinga Didi tun cikin nan yana da wata bakwai munyi Sikaynin komai lafiya sannan ko kwanan nan bai
daɗe ba still munyi Sikaynin komai lafiya”.

Cikin bugawar zuciya Moddibo ke kallonsa cikin sauƙe numfashi ya cigaba da cewa.

“Kuma ko yanzu ma Alhamdulillah zaman yaro lafiya to Amma kuma kinga yanzu ruwa yana ta zuba
mata kuma ba alamun naƙuda tare da ita”.

Numfashi Didi ta sauƙe tare da cewa.

“A wannan Normal ne in dai wannan ne ruwan zaƙine”.

Kai Dr Jameel ya jinjina kana yace.

“Eh nima ina ga kamar Normal ne?”.

Cike da gamsuwa ta gyaɗa masa kai tare da faɗin.

“Eh dan nima wani lokaci yana kai kusan sati kafin naƙuda yazo ya tashi idan na ƙuda ya tashi kuma baya
wuce awa ɗaya ko biyu shikenan na haihu”.

Cikin rauni da tarin tausayi Moddibo ya juya ya kalleta yace.

“Didi Amma ba matsala?”.

Kai ta gyada tare da cewa.

“In sha Allahu ba matsala wannan ana ce mishi zaƙi zaƙine yake zuba”.

Numfashi Dr Jameel ya fesar kana yace.

“For now dai zaƙine yake zuba amma yanzu zaku tafi gida, tunda ba haihuwar bane amma kullum da
daddare kafin ku kwanta azo in duba ta saboda kada ruwan ya canza ya zama wanda yaro ke rayuwa a
cikine ke zuba, amma for now ba matsala”.

Hararansa Moddibo yayi tare da faɗin.

“Toh munji”.
Murmushi Dr Jameel yayi tare da cewa.

“Ha'a Yayanmu laifin me nayi kuma?”.

Murmushi Didi tayi daga nan dai suka tattara suka koma gida.

Haka Khausar suka yini da Asma'u sai dai har zuwa lokacin ruwan nata zuba sai dai ba sosai yake zuba ba,
da daddare bayan sunje asibiti Dr Eshaa ce ta duba ta tace in sha Allah babu wata matsalar komai kuma
ba haihuwa bace...

Kwance Khausar take agefen Moddibo yayin da hannunsa ke kan cikinta yana tofa mata addu'oi.

Ahankali ta juya ta kallesa tare da cewa.

“Yah Mu'allim!”.

Idanunsa dake lumshe ya buɗe kana yace.

“Na'am Minha ya akayi?meke damunki meke kiki ciwo”.

Ya ƙare maganar cikin tsananin kulawa, tausayi, jin ƙai.

Kai ta girgiza tare da faɗin.

“Babu abinda ke yimin ciwo amma Yah Mu'allim dan Allah don darajar Annabi ka cewa Momyna tazo
mana”.

Cikin sauri ya miƙe ya zauna ya kalleta tare da cewa.

“Meyesa kika ce haka Minha?”.

Kai ta girgiza asanyaye tace.

“Ni dai kawai nafi so Momyna tazo ina son ganinta kaga bata taɓa zuwa ba kuma ina so in na haihu tazo
kaga ga abin na zuba kuma Dr Jameel yace in sha Allah nan da sati ɗaya zan haihu kaga ai tazo yafi”.

Kai ya jinjina kana yace.

“Amma dai ba abinda yake Miki ciwo ko?”.

Tana riƙe tafin hannunsa acikin nata tace.

“Um bakomai kawai ina so Momyna tazo kuma dan Allah in zata zo taxo min da Raudhat in yaso in na
haihu kafin suna Hajja Nana ma tazo kaji ko Yah Mu'allim”.

Cikin sanyi yace.


“An gama Minha in Sha Allahu Momy za tazo”.

Cikin jin daɗi tace.

“Yaushe za'a faɗa mata?”.

Kallon haɗeɗɗen agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa yayi ganin 10pm yayi ya sanya shi sauƙe
numfashi yace.

“Kinga karfe goma tayi sai gobe zan faɗa mata”.

Marairaice fuska tayi tare da cewa.

“Um-um Yah Mu'allim a faɗa mata yanzu mana”.

Kai ya girgiza kana yace.

“Minha idan na faɗa mata yanzu kinga dai lafiyarki lau, toh Amman in taji zatayi zaton baki da lafiya ne
karshe muzo mu hanata bacci”.

Idanunta ta narkar acikin nasa tare da cewa..

“A'a Yah Mu'allim baza ta tsorata ba ai zanyi waya da ita zata fahimta”.

Sake kallon agogo yayi yace.

“Mu dai bari har sai da safe”.

Kamar za tayi kuka tace.

“Ni dai Um-um mu faɗa mata yanzu”.

Ganin yanda ta damu yasa yace.

“Toh shikenan”.

Ya ƙarashe Maganar tare da ɗaukar wayarsa yayi dearlin number mommy.

A can Nigeria kuwa dai-dai lokacin Momy ce tare da Amina zaune a falonta cikin sanyi Amina tace.

“Momy kinji ɗazu an kirani ko?”.

Kai Momy ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh Amina naji".

Cikin fesar da numfashi da kuma yanda nutsuwa da nadama ya baibaye rayuwarta tace.
“Kin san waye ne ya kirani”.

Cikin sanyi gami da rauni ta gyara zamanta tare da faɗin.

“Baban Samira Sani ne fa yazo wajena”.

Da mamaki Momy tace.

“Kai haba dai?”.

Araunane ta gyaɗa kanta tare da cewa.

“Wallahi”.

Ajiyar zuciya Momy ta sauke tace.

“Lafiya dai?”.

Kanta ta sunkuyar ƙasa idanunta na ciko da ruwan hawaye tace.

“Wai cewa yayi yana sona zai Aureni”.

Shiru Momy tayi kana ta ronƙofar da kanta kafin sai kuma ta ɗago kanta ta kalleta.

Amina kuwa cikin sanyi ta cigaba da cewa.

“Momy nikam kuma da zama hakan nan tunda ya sanni kawai zan Aureshi kawai yafi min tunda tuntuni
na gama iddah kuma babu wanda yake zuwa wajena”.

Cike da tausayinta Momy tace.

“In dai har kin gamsu kinga zaki Aureshi ai babu laifi, tunda dama mun sanshi mutum ne mai mutunci da
kamala da daraja”.

Tana wasa da yatsun hannunta tace.

“Hakane kam Momy kuma ma kinga ya bada hujjan cewa zamu zauna cikin aminci, tunda dama nida
Samira mun saba zanje in zauna in maye mata gurbin Mahaifiyarta sannan kuma muyita mata addu'a
Allah ya fito mata da mijin Aure na Alkhairi ”.

Kai Momy ta jinjina cike da gamsuwa tace.

“Toh shikenan Amina Allah ya tabbatar da abinda yafi Alkhairi ”.

Ahankali tace.

“Dama shine nace bari na faɗa Miki saboda ki faɗawa Abbana, nikam na yarda shiɗin in Aureshi dama
Momy Ni yanzu waye zai kalleni ya Aureni in ba tsohon ba?”.
Cikin kwantar mata da hankali Momy ta ɗan muskuta tare da cewa.

“Bakomai Amina in Sha Allahu zan faɗawa Abbanku Allah kuma ya sanya Alkhairi kuma ai mutum ne mai
mutunci”.

Cikin sanyi Amina tace.

“Ameen ya Allah”.

Suna cikin hiran ne kira ya shigo wayarta da mamaki tace.

“Toh Moddibo kuma”.

Sai kuma ta amsa kiran ta kai kunnenta tare da faɗin.

“Assalamu Alaikum ”.

Anutse Moddibo yace.

“Wa'alaikum Salam Barka da dare Momy kina bacci na tashe ki ko?”.

Murmushi tayi tare da faɗin.

“A'a idona biyu muna hira da Amina ce ma”.

Kai ya gyaɗa yana shafa cikin Khausar yace.

“Masha Allah”.

Sai kuma yayi shiru cike da kulawa tace.

“Lafiya kuwa Moddibo?,Me yake faruwa faɗa min mana?”.

Kansa ya sunkuyar ƙasa tare da ɗagowa ya kalli Khausar sai kuma ya maida hankalinsa kan wayar yace.

“Momy Khausar ce kin san yau tun da safe”.

Sai kuma yayi shiru ya rasa ta ina zai fadi maganar.

Ganin haka ne yasa Khausar ta karɓi wayar tasa akunnenta tare da faɗin.

“Momy”.

Cikin sauƙe ajiyar zuciya Momy tace.

“Na'am Mamana lafiya kuwa?”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Lafiya lau Momy?”.


Tana ɗan jingina da jikin kushin momy tace.

”Toh me yake faruwa?”.

Tana gyara zamanta tace.

“Bakomai fa Momy kinga yau munje asibiti an duba ance ba matsalar komai, kuma in sha Allahu nan da
sati ɗaya ko kwana biyar zan haihu shiyasa nake so ki tambayi Abba in ya barki kizo”.

Da damuwa Momy tace .

“Amma dai kin tabbatar Babu komai”.

Idanunta ta lumshe tare da buɗe su akansa tace.

“Allah Momy ba komai kawai dai ina so kizo ne kuma dan Allah Momy kizo da Raudhat yanzu ki tura
mana hoton Passport ɗinki amiki booking”.

Murmushi Momy tayi tare da cewa.

“Da gaggawa haka Mamana?,Ba dai abinda kike ji?”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Bafa abinda nake ji”

Cikin ɗan radaɗine Mommy tace.

“Ok toh shikenan zan faɗawa Abbanku idan ya amince zanzo, tunda ga Amina da sauƙi zata zauna da
ƙannen ku kafin mu dawo”.

Tana ɗan lumshe Idanunta tace.

“Toh shikenan Momy ina Aminan?,Ki bata mu gaisa”.

Momy na ƙoƙarin miƙa wa Amina wayar tace.

“Gata nan”.

Jin Amina ta karɓi wayar Khausar tace.

“Amina ina yini”.

Asanyaye Amina tace.

“Lafiya Khausar ya gida ya labarin Addah Asiya ”.

Khausar na jinginar da kanta kafadarta Moddibo tace.

“Munyi waya ma tace kwanan nan zasu zo hutu akwai bikin abokinsa da za'a yi zasu zo”.
Ahankali Amina ta gyara zaman wayar akunnenta tare da cewa.

“Allah ya kawo su lafiya ya jiki?”.

“Alhamdulillah”.

Cewar Khausar tana lunshe idanu.

Cike da kulawa Amina tace.

“Toh Allah ya raba lafiya”.

Daga nan sukayi sallama.

Nan take Momy ta mike taje ta faɗawa Lamiɗo ba gardama Lamiɗo ya amince tare da yi mata fatan
Alkhairi kana ya fara yi mata booking ɗin tafiya cikin ikon Allah ya ga nan da kwana huɗu akwai jirgin da
zai tashi daga Abuja zuwa Morocco direct cikin Rabat zai sauƙa nan take yayi mata komai da komai a
online kasancewar ranan juma'a ce kuma jirginsu zai tashi ranan Laraba

Ranan Lahadi da yamma Khausar da Moddibo ne zaune a Falon Didi suna hira Ahankali ta yunƙura ta
miƙe jin kamar tana jin fitsari ta nufi bedroom ɗin Rahama cak ta tsaya tare da juyawa ta kalli Didi dake
cewa.

“Ha'a lafiya?”.

Ganin wani ruwa daya tsinko mata yake bin ƙafafunta cikin sauri Moddibo ya matso kusa dasu tare da
cewa.

“Lafiya?”.

Kallon Didi tayi kana ta kalli Innayi sai kuma ta maida kallonta kan Moddibo da damuwa ya bayyana
asaman fuskarsa Ahankali tace.

“Nima ban sani ba”.

Cikin wani irin yanayi Moddibo yace.

“Ya salam”.

Ganin yanda ruwan ke gudu akasa cikin sauri Didi tace.

“Ɗaukwta mu tafi asibiti”

Da sauri ya ɗauketa ya sata Amota Didi na gidan gaba tare da Ibraahim dake mazaunin Driver sai kuma
Moddibo dake rungume da Khausar baya.

Sai kuma ɗaya motar da hadimai ne aciki sai Innayi da Niyna da kuma jakadiya direct suka nufi asibiti.
Bayan anyi mata gwaje-gwaje bayan wani lokaci Dr Eshaa ta fito tare da Kiran Didi bayanta Didi tabi cikin
sauri Moddibo yabi bayanta yana cewa.

“Dr Lafiya meke faruwa?”.

Zama tayi akan kujeranta tare da kallon Moddibo sai kuma ta kalli Didi tace.

“Toh gaskiya da farko dai ba muyi tunanin haihuwar Nan zai zo da gardama haka ba saboda komai naga
da baby lafiya lau Toh amma kuma daga ɗazu zuwa yanzu ruwan da yaro yake rayuwa aciki ne yake
zubowa wanda kwata-kwata naƙuda bai tashi ba bare ta iya haihuwa dole sai an nata C'S”.

Cikin sauri gami da wani irin azabebben bugawan zuciya Moddibo ya dafe kansa tare da cewa.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Theater Kuma?".

Cikin sauri da son kwantar masa da hankali Dr Eshaa tace.

“Bakomai fa ai Theater ba wani abu na tashin hankali ko kiɗima bane”.

Still hannunsa na dafe da kansa yace.

”Allah ko?”.

Kai ta jinjina cikin tabbarwa tace.

“In sha Allahu bakomai babu abinda zai faru sai alkhairi wasu ma da yawa basu bari suyi naƙuda kawai
sai ayi musu Theater”.

Cikin sauri da damuwa Didi tace.

“Toh yanzu yaushe za'a Theater?”.

Juyawa tayi ta kalli agogon hannunta kana ta maida kallonta kan Dr Jameel dake shigowa cikin sauƙe
numfashi ya gyara tsayuwar sa tare da cewa.

“Gaskiya Theater zai kai kamar ƙarfe biyu na ranan gobe za'a yi”.

Cikin Jimami Didi tace.

“Toh amma ba matsala zuwa goben ko?”.

Kai ya gyaɗa yana gyara zaman farin glass ɗin idanunsa tare da cewa.

“Eh in Sha Allahu bakomai saboda ba wani ciwo take jiba ruwan ne dai kuma already kafin lokacin zai
ɗan ƙara sa zubowa ne gaba ɗaya zai kuma iya riƙe yaron”.

Still da damuwa atare da ita tace.


“Allah ya kaimu lokacin”.

Sai kuma ya ƙarasa gefen Moddibo ya dafa kafadarsa ganin kamar duk ya rikice cike da kulawa ya ɗan
bubbuga tare da cewa.

“Eh in Sha Allahu ba komai sai alkhairi ”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.

“Toh amma babu matsala zan iya sanar mata C's za'a yi mata ”.

Kai Dr Jameel ya gyada tare da cewa.

“Of Cause ya kamata ka faɗa mata sannan ka kwantar mata da hankali.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da fita kana ya ciro wayarsa tare da dearlin number Mommy Jin ta ɗaga yasa
cikin sanyi yace.

“Momy yaushe Jirginku zai taso?”.

Ahankali tace.

“Yanzu ma ina Abuja idan Allah ya kaimu gobe Jirginmu 9:00 zai tashi”.

Cike da girmamawa yace.

“Toh Momy Allah ya kaimu”.

Da ɗan damuwa atare da ita tace.

“Lafiya dai Babana”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Lafiya lau dama naƙudan ne ya tashi kuma ance”.

Sai kuma yayi shiru shin ya faɗa mata C's za'ayi wa ɗiyarta,

Sai kuma ya katse mgnar sabida tunanin kada ya faɗa mata ya tsinka mata zuciya tare da tayar mata da
hankali da sauri Momy tace.

“Ance me?”.

Da sauri yace.

“A'a ance ba matsala in Sha Allahu yanzu haka ma muna asibiti”.

Anutse tace.
“Masha Allah yanzu ina Khausar ɗin?”.

Yana gyara tsayuwar sa yace.

“Ni ina office ɗin Dr ita kuma tana ɗakin da aka kwantar da ita tare da Innayi da Niyna Ni kuma ina tare
da Didi”.

Cikin sauke numfashi tace.

“Toh abawa Didi”.

Miƙa wa Didi wayar yayi Didi tace.

“Maman Khausar ”.

Cikin sanyi Momy ta gyaea zaman wayar akunnenta tare da cewa.

“Na'am ya gida ya yara?”.

“Lafiya lau Alhamdulillah ya hanya”.

Cewar Didi Momy kuwa Ahankali tace.

“Ya jikin ƴar taki”.

Didi na kallon Moddibo da idanunsa ke lumshe kana ta maida hankalinta kan wayar tare da faɗin.

“Ba damuwa Maman Khausar in Sha Allahu ki kwantar da hankalinki gobe kina isowa Mai gidanki ko
Amarya na bisa hanya”.

Cikin jin karfin gwiwa tace.

“Toh Allah ya kaimu rai da lafiya ”.

Cikin kwantar mata da hankali Didi tace.

“Kiyita mata addu'a Allah ya kawo mata da sauƙi”.

Kai Momy ta jinjina tare da cewa.

“In sha Allahu ina mata kuma zan cigaba dayi mata”.

Daga nan sukayi sallama bayan sun fito office ɗin Dr Jameel Moddibo ya wuce ɗakin da Khausar ke ciki.

Yana shiga ya hangota kwance akan gado tayi shiru Ahankali ya ƙara sa ciki kana ya riƙo hannunta tare
da cewa.

“Minha”.
Idanunta ta ɗago ta kallesa kana tace.

“Na'am”.

Yana matsa hannunta dake cikin nasa yace.

“Minha Me yake Miki ciwo?”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta jujjuya masa kai tare da cewa.

“Babu inda yake min ciwo Yah Mu'allim ”.

Ahankali ya zauna bakin gadon tare da janyo hannunta ya daura kan cinyarsa kana ya cire pillow ya
ɗaura kanta akan cinyarsa yace.

“Minha naƙuda akwai zafi ko?”.

Idanunta ta zuba masa sai kuma ta girgiza kai tare da cewa.

“To ai ban fara bama Yah Mu'allim bare inji?”.

Murmushin karfin hali yayi kana yasa ya tsansa yana kwantar da gashin girarta tare da faɗin.

“Toh ai ma bazan bari kiyi naƙudan ba”.

Cikin sauri tace.

“Toh ai Yah Mu'allim ance dole sai mutum yayi naƙuda kafin ya haihu”.

Cikin rauni da rawar murya ta ƙare maganar lokacin ɗaya tsoro da fargaba ya mamaye mata zuciya.

Cikin sauri ya tallafota kanta tare da manna mata kiss agoshi yace.

“Bakomai kinga yanzu muka gama magana da Dr Eshaa ai kinsan Momy ma Theater akayi mata a
haihuwar Ramadan da Raudhat ko?”.

Cikin sauri ta gyaɗa masa kai tare da cewa.

“Eh”.

Yana shafa kanta yace.

“Momy bata taɓa faɗa Miki cewa ba wahala ba?”.

Cikin lumshe idanu ta fesar da sanyayyar numfashi tare da faɗin.

“Haka dai take cewa haihuwa yafi Theater wuya”.

Sake janyota jikinsa yayi kana yace.


“Toh shiyasa na zaba Miki mai sauƙi Minha ayi C's kawai lafiya lau kar wani abu ya samu Babynmu ya
cutar dashi”.

Da sauri ta ɗaura hannunta akan cikin ta shafa tare da cewa.

“Yah Mu'allim”.

Cike da tsantsan so da kulawa yace.

“Na'am amma dai ai Baby lafiyarsa lau kina jin motsinsa?”

Dai-dai lokacin tayi saurin kamo hannunsa ta ɗaura akan cikin tace.

“Kaji yanzu ma yana motsi ko?”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Tabbas naji Allah ya mishi albarka ya kawo shi kafiya”.

Kallonsa tayi cikin sanyi ta langwaɓar da kanta kana tace.

“Amma Yah Mu'allim ai Theater ma da zafi”.

Ɗan ware idanunsa yayi cikin son kwantar mata da hankali yace.

“Inji waye ba wani wuya munyi magana da Dr Eshaa, tace ayi Miki Theater kin san itama tana sonki bata
so ki wahala, kuma itama Didi tace ayi kiki Theater yafi sauƙi”.

Dai-dai lokacin Didi ta shigo tana shiga ta riƙe hannunta tare da kallonta tace.

“Kada kiji tsoron Theater ba komai ɗiyata ai kinga Lalla Hafsat ma, haihuwar Hakeem ɗin ta Theater
akayi mata kuma gashi nan lafiya lau itama lafiya lau kuma bayan shi duk yaranta da kanta take
haifarsu”.

Shiru tayi tare da lumshe idanunta.

Cikin jin sanyi tace Didi taci gaba da cewa.

“Ki kwantar da hankalinki in Allah ya kaimu gobe za'a yi Miki Theater”.

Idanunta ta lumshe tare da cewa.

“Toh Allah ya kaimu bisa rai da lafiya ”.

Sai kuma ta maida kallonta kan Didi tace.

“An faɗa wa Momy na”.

Kai ya jinjina yace.


“Eh an faɗa mata gobe-gobe ma tana hanya in Sha Allahu yanzu ma haka tana Abuja kafin a shiga dake
Theater jirginsu zai iso”.

Ahankali tace.

“Toh Allah ya kawo ta lafiya”.

Ameen ya amsa dai-dai lokacin kuma Dr Jameel da Dr Eshaa suka shigo.

Khausar na kallon Dr Jameel tace.

“Dr kuma zamu koma gida ne ko kuma zamu yita zama anan ne?”.

Hannunsa na cikin aljihu yace.

“Eh zaku zauna anan saboda ki kasance cikin kulawarmu”.

Kai ta jinjina cikin gamsuwa.

Dai-dai lokacin Asma'u kuma ta shigo, ganin Khausar ɗin zaune ras ana hira da itane yasata saki ajiyan
zuciya tare da zama gefenta.

Daga nan sukaci gaba da hira kamarsu saboda bata jin komai.

*Masu son Maganin infection da maganin mata, ku marmatso wannan account no in ne naku ta ciki zaku
turo kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP
NUMBER'N na 08069423567. akwai sabbin kaya masu zafi suna nan Available ki turo kuɗinki a saki cikin
lissafi. Kayanen mata masu zafi sadidan daga Chadi akwaisu Garukan daka, gumbunan, Tsumummuka,
cida Ciccibi Abodi cida kaza ci da jan nama kwanon ƙasaitacciyar mace butar sirri, furar mata, gumbar
madara Gumbar kolli mai ƙyallin al'khairi gumbar uku al'khairi, gumbar da ba'a baiwa mai kishiya,
gumbar riɗi, garin maɗi garin melɗamhi garin ilanwaddihi garin mallaka, tsumin riɗi tsumin tsirtai tsumin
kinfi budurwa, tsumin riɗi, tsumin ta baje Sabaya, haɗin sabon budurci 40k matsin maliƙi mai masifar
matse mace matsin daɗi har maɗiga, mai ɗan kare kyau. Kullacar sirri al'ajabu shu'umar Humra, da duk
sauran kayan ƙamshi. Haɗin amarya budurwa ko bazawara haɗin mai jego ko uwar gida, akwaisu
Available set ɗinmu hawa hawane akwai manya akwai ƙananan, ƙanan daga 40k ne 35k 30k 25k 20k 15k
10k 5k shine ƙarami haɗina na karshe sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar shi 7k ne shine ƙarshen
haɗina kenan... Manyan set ɗin kuma daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k ke zaki faɗi haɗin nawa kikeso anyi
miki kana kimin bayanin yadda kikeso da matsalarki ni kuwa nasan abinda zan haɗa miki, ina araha kam
amman ina hana bashi*
By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

70

*Masu son Maganin infection da maganin mata, ku marmatso wannan account no in ne naku ta ciki zaku
turo kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP
NUMBER'N na 08069423567. akwai sabbin kaya masu zafi suna nan bisa hanya, ki turo kuɗinki a saki
cikin lissafi. Kayanen mata masu zafi sadidan daga Chadi akwaisu Garukan daka, gumbunan,
Tsumummuka, cida Ciccibi Abodi cida kaza ci da jan nama kwanon ƙasaitacciyar mace biyar sirri, furar
mata, gumbar madara Gumbar kolli mai ƙyallin al'khairi gumbar uku al'khairi, gumbar da ba'a baiwa mai
kishiya, gumbar riɗi, garin maɗi garin melɗamhi garin ilanwaddihi garin mallaka, tsumin riɗi tsumin
tsirtai tsumin kinfi budurwa, tsumin riɗi, tsumin ta baje Sabaya, matsin maliƙi mai masifar matse mace
matsin daɗi har maɗiga, mai ɗan kare kyau. Kullacar sirri al'ajabu shu'umar Humra, da duk sauran kan
ƙamshi. Haɗin amarya budurwa ko bazawara haɗin mai jego ko uwar gida, akwaisu Available set ɗinmu
hawa hawane akwai manya akwai ƙananan, ƙanan daga 40k ne 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙarami
haɗina na karshe sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar mace shi 7k ne shine ƙarshen haɗina kenan...
Manyan set ɗin kuma daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k ke zaki faɗi haɗin nawa kikeso anyi miki kana kimin
bayanin yadda kikeso da matsalarki ni kuwa nasan abinda zan haɗa miki, ina araha kam amman ina hana
bashi*

70

Haka dai yinin ranan Didi suka yini da ita kana suka kwana Asma'u kuwa sai da Dr Jameel ya gama duty
inda suka tafi tare da barin Dr Esha.

Washe gari da sassafe Asma'u ta zo hannunta riƙe da wani madaidaicin Basket Dake ɗauke da Warmer
masu kyau bisa ga duk kan alama abinci ne tayi kana kafadarta maƙake da waya ta ƙara sa shiga ɗakin
alamar waya take yi sai kuma tace.

“Eh Ummi gata nan ma yanzu na shigo”.


Ta ƙare maganar tare da miƙa wa Khausar wayar kana ta ajiye Basket ɗin hannunta tana mai gaida
Moddibo dake magana da Dr Jameel.

Khausar kuwa cikin sanyi tace.

“Ummi”

Cike da kulawa Ummi tace.

“Khausar lafiya dai kike jin jikin ki ba abinda yake Miki ciwo?”.

Kai ta gyaɗa kamar tana gabanta tare da cewa.

“Ummi ba abinda. Yake min ciwo fa”.

Cikin jin sanyi da tausayinta Ummi tace.

“Toh Allah ya rabaku lafiya ”.

Tana ɗan lumshe Idanunta ta gyara zamanta tare da cewa.

“Ameen ya Allah Ummu kuyi min addu'a”.

“In sha Allahu muna miki kuma zamu ci gaba daya miki yanzu ma mukayi waya da Momynki tace min
yanzun jirginsu zai tashi”.

Juyawa Khausar tayi ta kalli agogon wayanta tare da cewa.

“Yanzu ma ai sun tashi tun da gashi har tara da rabi kuma tara dai-dai ma jirginsu ya tashi”.

Cikin sauƙe numfashi Ummi tace.

“Toh Allah ya kawo su lafiya”.

Ameen ta amsa suna cikin waya da Ummi taga kiran Hajja Nana ya shigo ta wayarta cikin sauri ta miƙa
wa Asma'u wayarta kana tayi picking nata takai kunnenta atake muryan Hajja Nana ya ratsa kunnenta
tana cewa.

“Khausar”.

Ahankali Khausar tace.

“Na'am”.

Cike da so irin na Kaka da Jika Hajja Nana tace.

“Ya jikin naki?”.

Tana ɗan lumshe Idanunta ta gyara zamanta tare da cewa.


“Da sauƙi”.

Cikin sauke ajiyar zuciya Hajja Nana tace.

“Jiya mukayi waya da Momy take cewa baki jin daɗiba ma tana kan hanya zata zo”.

Kai ta gyaɗa tana kallon Asma'u dake cire warmers cikin Basket tace.

“Eh lafiya lau ba abinda ke damuna Hajja Nana amma wai ance Theater za'a min”.

Cikin son kwantar mata da hankali kana da son sama mata nutsuwa tace.

“A'a kada ki damu ki kwantar da hankalinki ai Theater ba abinda yake yi nima in Sha Allahu da izinin
Ubangiji zanyi ƙoƙari in zo”.

Murmushin tayi cikin jin daɗi ta gyara zamanta tare da cewa.

“Allah ya kawo min ke lafiya Allah yasa ki same ni araye”.

Cikin rashin walwala Hajja Nana tace.

“Wani irin magana ne wannan in Sha Allahu ma araye zan sameki kar ki karya min zuciya”.

Murmushi tayi tare da faɗin.

“Toh Allah ya kawo ki lafiya”.

Ameen ya Allah ta amsa kana sukayi sallama.

Kallonta ta mayar kan Moddibo dake riƙe da hannunta cikin rauni yace.

“Kina so ki karya min zuciya ko Minha? wani irin kalma ne kike faɗa haka”.

Ɗaya hannunta ta ɗaura akan nasa tare da cewa.

“Bakomai Yah Mu'allim”.

Dr Jameel kuwa kallon Asma'u dake tsaye gefensa yayi wacce tunda ta cire Warmers cikin Basket bata
zauna ba yace.

“Toh ki zauna mana”.

Ahankali tace .

“Toh bari in sa mata abinci”.

Idanunsa ya zare tare da cewa.

“Dear wa yace Miki idan za'a yiwa mutum Theater yana cin abinci ai baza taci abinci ba sai bayan an fito
da ita”.
Kallonsa Khausar yau cikin langwaɓar da kai tace.

“Kuma wallahi yunwa nake ji Dr”.

Idanunsa akan Asma'u yace.

“Ki ƙara haƙuri in Sha Allahu ana fito dake ba daɗewa zaki samu ki ɗanci wani abu”.

Rau-rau tayi da Idanunta tare da faɗin.

“Toh shikenan”.

Bayan zuwan Asma'u ba daɗewa Niyna da Innayi suka iso wanda hakan yasa Didi ta samu ta koma gida
tayi wanka ta sake shiryawa.

12:30pm dai-dai suka fito da niyyar komawa Asibitin wanda kuma yayi dai-dai da Jirginsu Ummu ya kusa
sauƙa hakan yasa tace da Ibraahim dake driving ya wuce da ita Airport kana sai motar Hadimai dake biye
dasu wanda sun kai huɗu motar Ajere-Ajere suke tafiya motar Hadimai ɗaya agaba saina su Didi sai
kuma sauran ukun abaya ƙarfe 1:05pm dai-dai suka shiga cikin airport Akuma dai-dai lokacin jirginsu
Momy yayi Landing.

Bayan Fasinjoji sun fiffito Momy ta fito hannunta riƙe da Raudhat yayinda wani yaro daga cikin
ma'aikatan wurin ke gabanta da troling su.

A hankali take tafiya tana ɗan jujjuya ido alamar tana neman ta inda zataga fuskantar da ta sani, sai
kuma tayi saurin juyawa jin Raudhat na cewa.

“Oyoyo Didi Yah Ibraahim Oyoyo”.

Murmushi Momy tayi kana tace.

“A'a gasu can ma”.

Ibraahim kuwa sunkuyawa yayi tare da buɗewa Raudhat hannu da gudu tajeta ta rungumesa tare da
cewa.

“Ina Addah Khausy?”.

Yana ɗan Sharking ɗin hannunsa acikin nata yace.

“Addah Khausy na asibiti”.

Cike da zumuɗin son ganinta tace.

“Toh mu tafi inganta ina son ganinta ”.


Miƙewa yayi tana riƙe hannunta yace.

“Toh shikenan ”.

Cikin sassarfa Didi ta rungume Momy tare da cewa.

“Momyn Khausar Barka da zuwa”.

Fuska ɗauke da Murmushi Momy tace.

“Barka dai ya mai jikin?”.

Suna tafiya Didi tace.

“A'a Alhamdulillah mai jiki tana can anata hira da ita amma yanzu nan da minti arba'in za'a shiga da ita
sai muyi ƙoƙari mu tafi asibiti kafin a shiga da ita”.

Momy ta gyaɗa kai tare da cewa.

“Toh shikenan”.

Daga nan suka shiga motoci Madadin su wuce gida kai tsaye asibiti aka wuce dasu.

Dai-dai lokacin kuma Lalla Khadijah da Rahma ne da Asma'u ke tare da Khausar, cikin kulawa Lalla
Khadijah ke kallon Khausar ɗin jin yadda tayi mgnar a yunwace.

“Ayyah Rahma kije ki tambayi Dr Jameel, zan iya shan tea ne”.

Cikin kula Rahama tace.

“Ai ɗazuma naje Lalla Khausar cewa yayi ki ɗan ƙara haƙuri”.

Gyara zama Lalla Khadijah tayi tare da cewa.

“Kiyi haƙuri ko Khausar ba komai zuwa yamma dai zaki samu kici wani abu”.

Ɗan kwaɓe fuska tayi tare da kallon Asma'u dake cewa.

“Toh ni bari inje in kira Dr suzo su shiga suyi mata mana ta samu taci abinci”.

Ta ƙare maganar tana fita.

Su Momy kuwa da Didi tafe suke suna hirarsu, duk da dai duk karfin hali suke.

Raudat kuwa sai surutu take zubawa Ibraahim.


Acan asibitin kuwa lokacin da Asma'u take ta kira Dr zuwa lokacin 1:30pm yayi, haka yasa suka fara
shirya komai, nan da nan suka gama shirya komai da komai na asibiti kasancewar ƙarfe 2:00 dai-dai za'a
shiga da ita ahankali Dr Eshaa ta shiga ɗakin hannunta riƙe da wani riga da hula irin wanda ake sawa idan
za'a shiga da mutum ɗakin C's miƙa mata rigar tayi tare da cewa.

“Gashi zakisa wannan ɗin”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da karɓa kana ta juya ta kalli Moddibo cike da tarin ƙaunarta da kuma
tausayinta Moddibo yace.

“Insa Miki ne?”.

Langwaɓar da kanta tayi tana rau-rau da Idanunta tace.

“Nikam tsoro nake ji zuciyata bugawa take Yah Mu'allim”.

Kamota yayi kana ya ruggumota jikinsa cikin wata amintacciyar murya mai cike da jin ƙai da tausayi yace.

“Bakomai Minha, ba abinda zai sameki sai alkhairi kinji ko Minha”.

Ya ƙarashe Maganar cikin sanyi haka nan yake jin jikinsa ya mutu kana zuciyarsa na tsinkewa ya rasa mai
yake masa daɗi a duniya.

Ganin haka yasa Dr Jameel da Dr Eshaa juyawa suka fita Ahankali Asma'u ta yunƙura da niyyar fita da
sauri Khausar ta riƙo tsintsiyar hannunta tare da cewa.

“Asmeey ina zaki je?,Ki tsaya mana”.

Cikin rauni da karyewar zuciya Asma'u ta kalleta kana tace.

“Khausar abinda kike faɗa yana tayar min da hankali ance Miki bakomai a Theater Nan Amma sai wasu
maganganu kike masu tarwatsa lissafi da hargitsa mana nitsuwa”.

Araunane ta sunkuyar da kanta tare da cewa.

“Toh ya za muyi da abinda Ubangiji ya tsara mana Asma'u”.

Cikin ƙarfafa mata gwiwa tace.

“In sha Allahu Alkhairi Ubangiji ya rubuta mana”.

Kallonsu tayi sai kuma tace.

“Hmmm Allah yasa”.

Asanyaye Asma'u tace.


“Ameen”.

Shiru ɗakin yayi na wasu mintuna katse shirun Khausar tayi ta hanyar cewa.

“Gashi kuma har yanzu Momyna bata zoba”.

Kallon time Asma'u tayi tare da faɗin.

“Ai zata zo kafin a shiga dake in Sha Allahu yanzu naji Didi na waya da Innayi tana cewa sun taho asibiti”.

Sake jingina bayanta da jikin Moddibo tayi kana tace.

“Allah ya kawo su lafiya ta ganni inganta koda ma na karshene waya sani!?”.

Cikin sauri Moddibo ya sake janyota jikinsa ya rungumeta haka nan yaji wani irin rauni tausayi jin ƙai
baisan lokacin da shesh-sheƙan kuka ke taso masa daga ƙasa ba yace.

“Minha meyesa?”.

Kai ta girgiza tare da cewa.

“Bakomai fa Yah Mu'allim”.

Haka yaita rarrashinta tare da kwantar mata da hankali yace.

“Bakomai Minha babu abinda zai sameki sai alkhairi lafiya za'a shiga dake afito dake lafiya”.

Ɗan Murmushi tayi tare da cewa.

“Ameen Yah Mu'allim in Sha Allahu ya Mu'allim na daina damuwa amma ina neman yafiyarka iya tsawon
rayuwar da mukayi tare tun daga makaranta har zuwa dana kasance ƙarƙashin Inuwar Aurenka idan
akwai abinda nayi maka ka yafe min kayi min aikin gafara”.

Cikin sauri ya sake ƙanƙameta ajikinsa kana yace.

“Babu abinda kika yimin Minha.

Ni kuma me zakiyi kin aduniya Ni babu abinda kika yimin kuma koma akwai na yafe miki duniya da
kiyama”.

Kanta ta sake mannawa da ƙirjinsa tare da cewa.

“Nagode Yah Mu'allim”.

Ahankali Dr Eshaa ta sake turo ƙofar ta shigo tare da kallon Moddibo tace.

“Asa mata rigar yanzu fa sauran minti goma a shiga da ita kunga har 1:50 yayi”.
Kai ya gyaɗa kana ya cire mata rigar jikinta ya zira mata na asibitin sai kuma ya tsugunna ya zare mata
skintied dake jikinta ya cire ya ɗaura akan gadon da take kwance ya riƙo hannunta yayin da ƙafanta ke
sanye cikin wani takalmin roba mai taushi Ahankali ya kama gashin kanta ya nannaɗe kana ya tura
acikin hular rigar sai kuma ya sakar mata da lallausan murmushi yace.

“Kin kuwa ga yanda kika yi kyau cikin kayan nan kuwa?”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Hmmm”.

Matsowa jikinta yayi tare da tallafo kanta ya manna da ƙirjinsa kana ya mata kiss agoshi yace.

“Kinyi kyau sosai tare dani za'a shiga ayi Theater dake kinji Minha”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Toh Yah Mu'allim”.

Yana ɗan janta jiki yace.

“Ana Miki Theater za'a cire mana ɗan mu kina gani muna hira”.

Saurin kallonsa tayi sai kuma ta zaro idanunta tace.

“Yah Mu'allim wani irin Theater ne ina kallo”.

Yana matsa hannunta acikin nasa yace.

“Kawai za'a Miki alluran kashe zafi ne sai ayi Theater kina ji kina gani muna kuma hirarmu Yah Mu'allim
ɗinki a kusa dake”.

Cikin sauri ta girgiza masa kai idanunta na tara hawaye tace.

“Um-um nikam bana son wannan Yah Mu'allim a cire min hankalina kawai ayi min Theater”.

Ganin alamar hankalinta ya fara tashi ya sassauta murya tare da cewa.

“Haka kike so?”.

Kai ta gyaɗa dai-dai lokacin Dr Jameel ya karaso yace.

“Bakyaso amiki kina kallo?Idan kina so na sai a jawo Mirror a sama Anuna Miki kina kallo”.

Da sauri ta runtse idanunta tare da manna kanta a dantsen hannun Moddibo tace.

“Nikam ina tsoro nice zan tsaya har acire ɗa ajikina?,Nikam bana so wallahi Dr Jameel kawai dai ayi min
alluran da zai cire min hankalina gwara ayi min shi ina bacci in na farfaɗo in ganni da yaro na”.
Moddibo na shafa bayanta ya kalli Dr Jameel tare da cewa.

“Ayi mata yanda take so”

Kai Dr Jameel ya Jinjina kana yace.

“Toh shikenan ba matsala haka za'a yi mata”

Fita sukayi dai-dai lokacin kuma su Momy suka shigo cikin sassarfa taje ta rungume Momy.

Momy kuwa cikin sauri ta lumshe Idanunta jin hawaye na tsats-tsafowa cikin sanyi da rauni tace.

“Ubangiji Allah ya rabaku lafiya Khausar Allah yasa ayi aikin nan cikin lafiya akan alkhairi Allah ya fitar
dake lafiya ".

Araunane ta kalli Momy tare da faɗin.

“Ameen ya Allah Momy Allah ya amsa kiyita min Addu'a Momyna kiya femin idan akwai abinda na taɓa
yi Miki na cutar wa ko ɓacin rai”.

Da ɗan sauri Momy ta mari kumatunta kadan kana tace.

“Me kikayi min?,Ni babu abinda kika yimin Mamana Ubangiji Allah ya fito miki dashi da sauƙi”.

“Ameen ya Allah” ta faɗa tare da sakin Momy jin muryan Raudhat wacce suka shigo da Ibraahim da sauri
ta risina ta rungumo Raudat cike da farin cikin ganinta Raudat tace.

“Oyoyo Addah Khausy ”.

Rungumeta Khausar tayi tana Murmushi cike da farin ciki Raudat ta cigaba da cewa.

“Addah Khausy wannan kayan fa”.

Kallon jinkinta tayi sai kuma tace.

“Raudat Theater za'a yimin”.

Cikin rashin fahimta Raudat tace.

“Addah Khausy menene kuma Thearter?”

Ɗan murmushi tayi tare da cewa.

“Abinda aka yiwa Momy lokacin haihuwar ku keda Ramadan”.

Jim tayi sai kuma tace.

“Toh Addah Khausy Allah ya kawo miki sauƙi da lafiya”

Cikin sanyi da rauni tace.


“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.

Moddibo kuwa Ahankali ya kamo hannunta ya tsayar da ita sai kuma ya juyo da ita gaban Momy yace.

“Momy ayi mana addu'a Allah ya fito damu lafiya ”.

Ahankali Momy tace.

“Ameen ya Allah Moddibo”.

Ahankali Khausar ta sake janye hannunta ta rungume Momy sai kuma ta rungume Didi Dr Eshaa ce ta
ƙaraso tare da cewa.

“Lokaci yayi fa kizo mu tafi Khausar”.

Cikin sanyi ta kamo hannun Asma'u.

Ita kuwa Asma'u tuni take zubda hawaye hakanne yasa ta kauda kanta gefe tare da ruggumeta.

Ganin hakane yasa Modibbo ya kamo hannun Khausar ɗin suka juya suka nufi cikin ɗakin.

Anutse Khausar ta juya ta fara tafiya Ahankali tana waiwayen su cikin ƙarfin hali Momy tace.

“Mene kike tafiya haka kamar Kazar da ƙwai ya fashewa aciki, kiyi maza kishiga ayi Miki minti nawa kin
fito hankalin ki kwance Mamana kike tafiya kina sanɗa”.

Juyawa tayi ta kalli Momy cikin sanyi da langwaɓar da kai tace.

“Momy ba sanɗa nake bafa yunwa nake ji shiyasa bani da ƙarfi”.

Jin haka yasa Moddibo ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.

“Shikenan toh tunda yunwa kike ji”.

Ya ida maganar tare da tsugunnawa ya ɗauke ta cak kamar Baby ya rungumeta.

Raudat dake kallonsu ne ta sanya dariya kana ta buga tsalle tare da faɗin.

”Iyeeee Addah Khausy kin lale kinji daɗin ki Yah Moddibo ya ɗaga ki”.

Ibraahim dake bayanta ya matsa kusa da ita tare da ɗagata sama kana yace.

“Toh kema kiji daɗi an ɗaga ki”.

Cike da farin ciki ta riƙa ƙyalƙyala dariya tana cewa.


“Addah khausy Bye bye sai kin fito”.

Juyawa Khausar tayi ta kalleta kana tace.

“Toh Raudy na”.

Su Momy kuwa shiru kawai sukayi tare da rakasu da ido.

Suna shiga ɗakin direct kan gado Moddibo ya kwantar da ita Dr Jameel kuwa gefen kanta ya tsaya yana
Murmushi yace.

“Mrs Mouley Ya kike?”.

Idanunta akan Moddibo tace.

“Lafiya”.

Yana kallon Norse biyu dake tsaye gefe hannunsa riƙe da wani ɗan tiren silver yace.

“Ina yake Miki ciwo?”.

Baki ta Cunno gaba still idanunta na kan Moddibo tace.

“Nifa babu inda yake min ciwo”.

Murmushi yayi tare da faɗin.

”Masha Allah”.

Sai kuma ya matsa kusa da Dr Eshaa ya miƙa mata alluran yace.

“Gashi kiyi mata”.

Karɓa Dr Eshaa tayi kana tayi mata.

Dr Jameel kam sake matsawa kusa da ita yayi tare da cewa.

“Mrs Mouley me kike ji yanzu?”.

Cikin wani irin yanayi data fara tsintar kanta ta lumshe Idanunta tare da cewa.

“Wani irin bacci mai daɗi nake ji Yah Mu'allim ”.

Ta ƙare maganar tana sauƙe sassayan numfashi.

“Masha Allah”.

Cewar Moddibo yana matsa hannunta cikin nasa.


Dr Jameel kam Murmushi yayi kana yace.

“Asha bacci lafiya”.

Ahankali tace.

“Toh”.

Sai kuma ta sake lumshe Idanunta tare da buɗe su ta kalli Moddibo sai kuma ta juya ta kalli Dr Jameel
Ahankali ta sake kallon Dr Eshaa.

Cikin wani irin murya na magagin bacci tace.

“Dr Eshaa”.

Cike da kulawa tace.

“Na'am Mrs Mouley”.

Cikin yanayin baccin dake fusgar idanunta tace.

“Bacci nake ji”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Toh gaki ga Mijinki akusa dake kiyi bacci”.

Ɗan jujjuya idanunta tayi tare da faɗin.

“Ta ina yake?”.

Da hannu ta nuna mata gefenta kana tace.

“Ba gashinan kusa dake ba”.

Ƙyafƙyafta idanunta dake cike da bacci tayi tace.

“Ina yake ban ganshi ba bacci nake ji”.

Dai-dai lokacin kuma alluran ya gama fara aiki ajikinta ta narke idanunta suka tafi luuuuu.

Moddibo kuwa Ahankali ya ɗan sun kuyo kanta tare da faɗin.

“Minha! Minha!! Minha!!!”.

Yi tayi kamar zata buɗe idanunta kuma ta kasa kasancewar alluran ya gama game jikinta ya saki sai kuma
ta buɗe idanunta cikin magagin bacci tace.

“Yah Mu'allimmmmm”.
Shikenan kuma sai bacci.

Sake sunkuya kanta yayi tare da cewa.

“Minha”.

Dr Jameel dake kallonsa yace.

“Kai ka daina ma kiranta allura ya fara aiki ajikinta bari muzo mu fara aikin mu”.

Momy kuwa toilet dake cikin ɗakin da aka kwantar da Khausar ta shiga tayi alwala kana tayi sallar Azahar
kasancewar su Didi already sun idar.

Momy kuwa koda ta idar addu'a ta shiga yiwa Khausar kan Allah ya fito da ita lafiya haka ma su Didi,
Innayi, Niyna ke tayi.

Ahankali Moddibo ya juya ya kalli Dr Jameel tare da cewa.

“Wai da kai za'a yi Theater ne?Dr Eshaa baza ta iya bane?”.

Kai Dr Jameel ya jinjina kana yace.

“Zata iya amma dole sai da taimakona”.

Ya ƙare maganar yana kallon Norse biyu dake tsaye.

Cikin sanyi Moddibo yace.

“Toh shikenan”.

Ahankali Dr Eshaa ta zuge zip Dake gaban rigar yanda baza aga al'amuran ta ba sai cikinta daya bayyana
a fili,

cike da kwarewa suka fara Thearter cikin abinda bazai gaxa minti goma sha biyar zuwa ashirin ba suka
cire yaro fari ƙall kyakkyawan jariri gwanin ban sha'awa.

Dr Jameel na ɗago shi ya cilla ihu Yararai-yararain alamar lafiyayyan yaro cikin sauri Dr Eshaa ta miƙa
hannu zata karɓe shi sai kuma tayi saurin ja baya tana Murmushi ganin yanda Moddibo ya buɗe rigarsa
ya tallafi yaron ya manna shi da jikinsa.

Murmushi Dr Jameel yayi tare da yin ƙasa da murya a hankali yace

“Wai kai ma ka zama Likita ne?”.

Cikin matsanancin farin ciki da wani irin azabebben ƙaunar yaron daya mamaye ilahirin jikinsa yace.
“Ba dole ba”.

Dariya Dr Jameel yayi tare da faɗin.

“Aikam toh yanzu dai a bawa Likitarmu ta gyarashi tukunna”.

Moddibo na sake ƙanƙame shi jikinsa yace.

“Wani gyarawa sai na kaiwa Didi ta ganshi”.

Dr Jameel na saka hanglove acikin wani ɗan silver dake riƙe hannun Norse's dake tsaye yace.

“Zaka kaisa amma ka bari agyara shi tukunna”.

Kai Moddibo ya gyada tare da miƙawa Dr Eshaa jaririn ta amsa tare da miƙawa Norse's ɗin karɓa sukayi
kana suka je suka fara gyara jaririn.

Su kuwa Dr da Dr Eshaa nan take suka cigaba da aiki bayan sun gyara sun gama komai suka sa mata
plaster kasancewar ba ɗinki bane atake suka ƙarasa mata komai kana suka balle wani abu daga jikin
gadon ya zama dai-dai yanda suke buƙata,

kana Norse's ɗinsu suka fara tura gadon yayinda ƙarin ruwan ke maƙe a hannunta.

Cikin sauri Moddibo ya matso ta gefenta ganin kamar ta buɗe Idanunta sai kuma tayi saurin rufe su
Ahankali yabi bayan gadon.

Dr Eshaa kuwa juyawa tayi ta koma bayan Norse's ɗin dake gyara jaririn karbansa tayi ta cigaba da gyara
shi da kanta...

Su kuma suna fita kai tsaye wajen Didi da Momy suka nufa.

Momy, Didi, Innayi, Niyna kuwa cikin sauri suka mike hangosu ta window da sukayi Norse's kuwa dakin
hutu suka nufa kafin su shiga ma sun buɗe musu ƙofa kawai shiga sukayi.

Akuma dai-dai lokacin Lalla Khadijah da Rahama suka shigo harabar Asibitin wanda dama sunje sun
saukowa Khausar da Baby abin buƙatarsu ne.

Khausar kuwa Ahankali ta sake buɗe idanunta sai kuma tayi sauri ta rufe ganin kamar Mutanen da Kai
suke tsaye bada ƙafafunsu ba kasancewar har zuwa lokacin alluran bai gama sake taba Ahankali ta sake
buɗe idanun tana ɗan jujjuya kanta Ahankali.
Cikin wani irin matsanancin ƙaunarta da matsayin mai girma da take dashi a zuciyarsa ya matsa daf da
ita ya riƙe hannunta cikin wata sanyayyar murya mai cike da aminci da sadaukarwa yace.

“Minha”.

Idanunta ta sake buɗe wa sai kuma ta sake rufe wa.

Norse's ɗin kuwa zaman gadon suka gyara kana suka gyara mata ɗaurin ruwan dake jikinta kana suka
juya suka fita.

Kujeran dake gefenta ta wajen kafafunta Momy ta zauna.

Moddibo kuwa kujeran dake gabanta daf da kanta ya zauna yayin da Asma'u Rahama, Lalla Khadijah
suka ɗaya gefenta.

Ibraahim kuwa bayan Moddibo yake tsaye

Niynah da Innayi kuwa zaune suke bisa carpet dake shinfiɗe.

Fuskarsu ko wannensu ɗauke da matsanancin farin ciki.

Anutse Moddibo ya ɗaura hannunsa na hagu akan gashin girarta yana ɗan kwantarwa yayin da yake
motsa laɓɓansa yana mata addu'a.

Didi kuwa cikin sauri ta nufi waje jin Dr Eshaa na cewa.

“Didi ga mai gida ya ƙara so”.

Cikin sauri da matsanancin farin ciki Didi ta karɓesa kana tace.

“Masha Allah Fatabarakallahu Fi Ahsanil Khaliƙin Masha Allah”.

Sai kuma ta rungumesa Momy kam baki ɗaya hankalinta na kan ƴar ta.

Da sauri Rahama taje ta karɓi Yaron ta zuba masa idanu tana kallon baiwar kyau da Allah ya zuba masa
yaro ɓulɓul dashi fari ƙal.

Rungumesa tayi tana cewa.


“Alhamdulilah Alhamdulillah nayi yaro Ni zan riƙa masa wanka ina rainonsa”.

Murmushi duk sukayi kana Innayi ta karɓesa ta kalla tare da miƙawa Lalle Khadijah cikin matsanancin
farin ciki take masa addu'oi.

Cikin matsanancin farin ciki Asma'u ta leka fuskar yaron tare da shafa kansa tace.

“Baby ka wahalar mana da Maminka bazan ɗauke kaba har sai taci abinci tukunna”.

Dariya suka sanya Kana Niyna ta karbi yaron sai kuma duk suka koma suka zauna akan Lallausan
Darduma Asma'u kam gefenta ta koma ta zauna.

Ibraahim ne ya amshi yaron tare da rugumeshi tsam a jiki yace.

“Welcome to the world *Keyan*. “.

Ma'ana King kenan.

Murmushi Didi tayi tare da cewa.

“In sha Allah kuwa”.

Khausar kuwa Ahankali ta motsa laɓɓanta a hankali murya can ƙasa tace.

“Yah Salam, Yah Mu'allim”.

Kasancewar da sunansa ta tafi kana kuma bayan sunan Allah data kira da sunansa ta fara farfaɗo wa.

Da sauri ya sunkuya kanta yace.

“Na'am Minha”

Still idanunta na lumshe tace.

“Yah Mu'allim”.

Ahankali ya sake sunkuyar da kansa daf nata har suna shaƙan numfashin juna yace.

“Na'am Minha”.

Hannunta ta yunƙura kamar zata ɗaga sai kuma taji ta kasa fuska ta narke tare da cewa.

“Yah Mu'allim ka ɗaga min hannuna”.

Dai-dai lokacin Dr Jameel ya shigo cikin sauri yace.


“Kada ka ɗaga mata hannunta ka bari sai ta ɗaga da kanta”

Kallonta Moddibo yayi cike da tausayi sai kuma ya gyaɗa masa kai yace.

“Ki ɗaga hannunki mana Minha ai zaki iya”.

Idanunta ta rufe kana ta sake buɗe su cikin narkewan murya da sanyi tace.

“Yah Mu'allim ta ina kake?”.

Cikin tsira mata idanu yace.

“Gani nan Minha gani kusa dake”.

Rufe idanunta tayi ta buɗe tare da cewa.

“Ina Momy”.

Cikin sauri Momy tace.

“Gani nan Mamana gani nan kusa dake ki kwantar da hankalinki”.

Ƙyafƙyafta idanunta tayi tare da cewa.

“Yah Mu'allim ka zauna daidai mana meyesa kake zaune da kan ka?”.

Da mamaki yace.

“Zaune da kai kuma?”.

Murmushi Dr Jameel ya masa kana ya masa alamar alluran ne bai sake taba har yanzu.

Muskutawa yayi tare da faɗin.

“Toh Minha na gyara”.

Motsa idanunta tayi tare da cewa.

“Toh”.

Sai kuma ta buɗe idanunta ji tayi kamar alluran ya fara saketa ahankali ta ɗago hannunta sai kuma tayi
saurin sakewa tace.

“Yah Mu'allim ka tayani in ɗaga hannu na mana”.

Kai ya girgiza tare da cewa.

“Ki ɗaga da kanki mana”.

Momy kam na zaune gefenta ta tsira mata Idanu.


Didi kuwa wayane maƙale kunnenta cikin jin daɗi da girmamawa tace.

“Alhamdullilah Abokinka, Amininka, Jikanka Kuma Sarki mai Jiran gado ya fito duniya”.

Abualeey dake zaune cikin Fada ya gyara zamansa cike da matsanancin farin ciki yace.

”Masha Allah Alhamdulillah Allah ya raya mana shi bisa Imani”.

Cike da jin daɗi tace.

“Ameen”.

Kana ya katse kiran.

Abualeey kuwa cikin jin daɗi ya juya ya kalli Waziri, Galadima da sauran fadawa yace.

“Alhamdulillah an cirewa Matar Aleeyu ɗa namiji lafiya lau ”.

Cikin sauri da jin daɗi Galadima yace.

“Alhamdulillah”.

Waziri kuwa juyawa yayi kana yayi Sujudur Shukur tare da cewa.

“Alhamdulillah abu duk yanda ake fata haka ya tabbata magauta basu sami yanda suke soba”.

Kai Abualeey ya jinjina kana yace.

“Idan munyi sallar la'asar sai muje asibiti Mu duba ta”.

Amsawa sukayi daga nan suka ci-gaba da zaman fada.

Agefen Khausar kuwa zuwa yanzu ƙarfin jikinta ya fara dawowa Sai dai har yanzu alluran bai gama saketa
ba bisa duk alamu maganar da take Sambatune.

Ahankali ta ɗago hannunta kana ta ɗaura kan cikinta ta shafa ɗagowa tayi ta kalli Moddibo tare da cewa.

“Yah Mu'allim”.

Kallon hannunta yayi tare da faɗin.

“Na'am Minha”.

Idanunta alumshe tace.

“Ina cikina”.
Juyawa yayi ya kalli Kyakkyawan Jaririn dake hannun Ibraahim yace.

“An cire mana Baby”.

Idanunta ta rufe kana tayi Murmushi tare da cewa.

“Yah Mu'allim”.

Hannunsa ya ɗaura kanta tare da faɗin.

“Na'am”

Tana shafa cikin tace.

“Ka ganshi?”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Eh na ganshi?”

Murmushi tayi kana tace.

“Momy na ta ganshi?”

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Eh”.

Murmushi ta sake yi still tana shafa cikin tace.

“Didi da Asma'u fa su ganshi?”

Kai ya sake gyaɗa wa tare da cewa.

“Kowa ya ganshi”.

Baki ta tura gaba cike da shagwaɓa kamar za tayi kuka fuskanta ta shafa kana yace.

“Minha ya akayi”.

Fuska ta sake narkarwa cikin mayen allurar tace.

“Yanzu shikenan kowa ya rigani ganin ɗana”.

Murmushi yayi kana Didi ma tayi Murmushi Asma'u kam dariya tayi tare da cewa.

“Aikam dai kece karshen kallo duk mun riga ki”.

Baki ta Cunno gaba.


Didi kuwa sake matsawa kusa da ita tayi kana tace.

“Kiyi haƙuri Ɗiyata In sha Allahu zakiga ɗan ki”.

Sake narke fuskarta tayi tare da cewa.

“Hmmmm”.

Sai kuma ta jinjina kanta tare da juya kanta gefe tace.

“Yah Mu'allim”.

Ahankali yace.

“Na'am”.

Lallausan Murmushi ta saki tare da cewa.

“Yah Mu'allim ina sonka”.

Kansa ya sunkuyar ƙasa tare da sakin Murmushi kana ya ɗago ya manna mata kiss agoshi.

Ahankali ta cigaba da kiransa.

“Yah Mu'allim! Yah Mu'allim!! Yah Mu'allim!!!”.

Duk kiransa da take yi yana amsawa.

Cikin sanyin murya da shagwaɓa ta cigaba da cewa.

“Ina sonka! Ina sonka!!,Ina sonka!!!Yah Mu'allim Kasan ina sonka ko?”.

Dariya Asma'u ta sanya tare da cewa.

“Dan Allah kar ki dame mu ai mun san kina sonshi”.

Ta ƙare maganar tare da ciro wayarta tana mata video Khausar kuwa jin abinda Asma'u ta faɗa yasa ta
Cunno baki gaba har lau kuma cikin mayen take.

Moddibo kuwa wani Amintaccen Murmushi mai cike da jin daɗi gami da shauƙi ya saki Sambatu take
yi amma yana masifar jin daɗin su.

Aƙage da kuma shauƙi yace.

“Na sani Minha?”.


Sake Cunno baki tayi tace.

“Yah Mu'allim kaima kana sona?”.

Tafin hannunta ya matsa tare da cewa.

“Ina sonki Minha Ina sonki ina sonki Minha”.

Cike da kunya Didi ta koma kan Darduman ta zauna.

Momy dake zaune gefensu kuwa sunkuyar da kanta ƙasa tayi.

Lalla Khadijah Rahama Asma'u Dr Jameel kam Murmushi kawai suke suna sake jaddada ƙauna da
shaƙuwar dake tsakanin su sun lura Moddibo yama mance da suna wajen.

Khausar kuwa cikin Sambatu da azabebben ƙaunarsa tace.

“Ina matuƙar Ƙaunarka Yah Mu'allim tun ina JSS one fa nake sonka kasan kafi duk malaman makarantar
mu kyau ko ina ka sani ko?”.

Cikin jin daɗin gami da farin ciki yace.

“Uhmmm”.

Cikin narkekkiyar murya tace.

“Da gaske fa kafi duk mazan duniya kyau, sajenka mai kyau, ai kasan ina son sajenka ko Habibeeey”.

Lallausan Murmushin mai cike da farin ciki yayi tare da cewa.

“Yesss na sani”.

Cikin tsokana Ibraahim yace.

“Toh ashe fa tsohuwar soyayyace, ashe nima sai in fara aje saje”.

Murmushi sukayi baki ɗaya, Asma'u kuwa gefen Dr Jameel daya riƙo hannunta yaja ta ɗan matso still
tanayiwa Khausar video.

Ita kuwa Khausar Jujjuya kai tayi tare da tura baki sai kuma tace.

“Ina sonka har rainafa, kuma ina tsoron kayi min kishiya bana son rayuwa da kai da kishiya Yah Mu'allim
kayi min alƙwarin baza kayi min kishiya ba, kuma ka ƙi kayi min alƙwari Yah Mu'allim”.

Gashin girarta ya shafa kana ya kwantar kanta ya sunkuya ya kai bakinsa saitin kunnenta ya raɗa mata.
“Minha aike ta musamman ce arayuwata koda wata mace takasance kusa dani Babu wata mace da zata
kai ki matsayi da daraja akusa dani”.

Idanunta ta buɗe ta kallesa kana cikin wata sanyayyar murya mai cike da shauƙi da bege ta ƙyafƙyafta
idanunta tare da cewa.

“Yah Mu'allim ina son ka”.

Murmushi yayi kana yace.

“Naji”.

Kanta ta juya ɗaya gefen tare da cewa.

“Didi?,Didi!!”.

Didi dake gefe tace.

“Na'am Khausar ”

Baki ta tura kana ta marairaice fuska tare da cewa.

“Didi ki faɗa masa ina son shi Dan Allah kar ya yimin Kishiya”.

Murmushi Didi tayi kana tace.

“Shikenan ɗiyata kwantar da hankalinki kin ji”.

Sake tura bakinta tayi tace.

“Ina Momyna?,”.

Kallon Momy Didi tayi tare da cewa.

“Gata nan”.

Ɗan buɗe idanunta tayi tace.

“Momy ki matso ta nan mana”.

Miƙewa Momy tayi kana ta matsa kusa da kanta ta tsaya jin alamun ta kusa da ita tace.

“Momy”.

Anutse Momy tace.

“Na'am”.

Tana ɗan Murmushi tace.


“Momy kinga Babyna?”.

Kai Momy ta gyaɗa tace.

“Eh”.

Kwanciyanta ta gyara tare da cewa.

“Momy kinga yaro na ko?,Didi tace namiji ne?”.

Kai Momy ta gyada kana tace.

“Eh”.

Murmushi ta saki tare da faɗin.

“Momy dawa yake kama?”.

Murmushi Momy tayi tare da juyawa ta kalli Jaririn dake hannun Niyna kana ta juya ta kalleta tare da
cewa.

“Da Ramadan yake kama Khausar”.

Wani Amintaccen Murmushi ta saki mai cike da jin daɗi kana tace.

“Alhamdulillah Momy na samu mai kama da Ramadan".

Kai Momy ta jinjina tace.

“Sosai ma”.

Fuskarta ta shafa tare da faɗin.

“Momy Kyakkyawa ne kenan?”.

Ta ƙarashe Maganar da alamar tambaya kana da Murmushi afuskarta.

Kai Momy ta gyada tare da cewa.

“Kyakykyawane Mamana ɗan ki kamar Balarabe”.

Tana Murmushi tace.

“Ai tunda aka ce da Ramadan yake kama nasan kyakkyawane Momy”.

Sai kuma ta Maida idanunta kan Moddibo tace.

“Yah Mu'allim kaji wai ɗan mu da Ramadan yake kama, kyakkyawane ko?”.

Kai ya jinjina kana yace.


“Kyakykyawa ne yama fiki kyau ai?”.

Baki ta tura gaba tace.

“Ni dai bai fini kyauba”.

Murmushi yayi yace.

“Toh naji bai fiki kyau ba Rigimatu, ki Kwantar da hankalinki”.

Asma'u kam sai dariya suke mata.

Haka ta cigaba da surutu da Sambatu har kusan karfe huɗu zuwa lokacin already alluran ya gama saketa
ta dawo hayyacinta.

Kallon Moddibo tayi tare da cewa.

“Yah Mu'allim zan tashi zaune”.

Sumar kansa ya shafa tare da cewa.

“Toh ki taushi ki zauna mana”.

Fuska ta narke tare da cewa.

“Ka tayani”.

Cikin yi mata kallo mai haɗe da zazzafan yanayi yace.

“Toh ki tashi ki zauna mana ai likitoci sun hana in tayaki, ki tashi da kan ki mana”.

Baki ta tura tayi ta ƙorafi misalin 4:15 ta mike ta zauna da kanta kasancewar ta tashi ta zauna da kanta
yasa Dr cewa Moddibo ya tallafa mata amaida ta ɗaki ta taka da ƙafanta.

Da ƙafanta ta taka aka canza mata ɗaki wanda akwai step agabansu suna komawa ɗaki Asma'u ta zauna
ta gabanta Moddibo kuma nata bayanta.

Kallon Dr Jameel Asma'u tayi tare da cewa.

“Dr”.

Yana gyara abin karfen gadon yace.

“Na'am my Dear”.

Kai ta langwaɓar tare da faɗin.


“In bata abinci?”

Kai ya dafe kana yayi Murmushi tare da cewa.

“Kai ke dai baki ɗaya na lura bama ta ɗan mu kike ba ta Ƙawarki kikeyi”.

Dariya Momy tayi kana tace.

“Da gaskiyar ta wa yake ta ɗan ku”.

Murmushi Moddibo yayi tare da faɗin.

“Momy harda kema bata ɗan mu kike ba wato ta ita kike ”

Cikin sauri Dr Eshaa tace.

“To ai har kaima bata ɗan ka kake ba ta ita kake tunda ka ɗauke sa aɗaki baka sake ɗaukar saba kana
riƙe da hannunta yanzu dai lokacin sallar la'asar yayi atafi ayi Sallah.

Zuwa biyar a ɗan asa mata abinci.

Cheaps kaɗan da tea rabin cup”.

To sukace kana su tafi masallaci, su kuwa matan sukayi salla a nan.

Sai ƙarfe biyar dai-dai

Asma'u ta ɗan sa mata cheabis ɗan kaɗan sai tea rabin cup, kamar dai yadda sukace mata.

Bisa jagoranci likitoci ta matsa ta riƙa bata taɓa ci.

Moddibo kuwa kanta ya riƙa shafawa tare da cewa.

“Minha kinga muje muyi alwala muyi sallah na roki Allah ya baki lafiya ya raya mana ɗanmu”.

Lallausan murmushi ta sakar masa kana ta gyaɗa kai shi kuma ya zauna gefe, nan dai ta gama ci, kana ta
ɗan gyara manta.

Dai-dai lokacin kuma Abualeey suka iso, bisa jagorancin Ibraahim m suka nufi dakinta dai-dai lokacin da
suka shiga a kuma dai-dai lokacin Khausar ta fara wani irin....

By
*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

71

*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son
k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman
lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun
matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa
ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki
tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones
dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da
tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da
ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda
ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya
wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka
kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki
da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 08069423567 kimin mgn ta whatsApp
in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta,
muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina
nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a
ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.

0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta
wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije
gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.
GARKUWAR MA'AURATA

71

Tana wani sassayan tari, wanda take ta son danneshi, cikin sauri suka ƙara sa cikin ɗakin da sauri Dr
Jameel yace.

“Ha'a ya dai?”.

Momy ce ta ɗago kanta tare da cewa.

“Kamar ƙwaruwa tayi”.

Cikin tsoro gami da damuwa Moddibo ya kalli Dr Jameel kana yace.

“Jifa tari take ba matsala ko?”.

Kai Dr Jameel ya girgiza tare da faɗin.

“A'a ba matsala bari nasa akawo mata wani magani tasha tarin zai bari”.

Ya ƙare maganar tare da kiran Line-line dake cikin wayar ya kira Pharmacy ya faɗa musu su kawo
maganin jim kaɗan Norse ta kawo maganin karɓa yayi ya bata tasha cikin ikon Allah atake tarin ya bari.

Sai alokacin ta samu nutsuwa numfashi ta fesar kana ta maida kallonta kan Abualeey tare da cewa.

“Abu ina yini”.

Cike da kulawa yace.

“Lafiya lau ya jiki?”.

Ahankali tace.

“Da sauƙi ”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Masha Allah Allah ya raya abinda aka samu”.

Karɓan Jaririn yayi tare dasa mishi albarka kana ya miƙawa Waziri da Galadima dai-dai lokacin kuma kira
ya shigo wayar Khausar Momy anutse ta duba ganin sunan Hajja Nana yasa ta ɗauka muryanta cike da
farin ciki tace.
“Hajja Nana Alhamdulillah anyi Theater ancire ɗa namiji”.

Cikin jin daɗi da sauke ajiyar zuciya Hajja Nana tace.

“Alhamdulillah amma tana lafiya ko?”.

”Eh lafiya lau gata nan ma”.

Cewar Momy na miƙa wa Khausar wayar karɓa Khausar tayi suka gaisa cike da farin ciki Hajja Nana tace.

“Ƴar tsele da zaki kasheni azaune”.

Murmushi Khausar tayi cikin rashin jin karfin jikinta tace.

“Yaushe zaki zo?”.

Fuska ɗauke da farin ciki Hajja Nana tace.

“Kwanan nan in sha Allah kafin ayi suna”.

Murmushi Khausar tayi tare da maida kallonta kan Moddibo da idanunsa ke kan Jaririn tace.

“Ayiwa Hajja Nana shiri in Sha Allahu tana kan hanya zata zo”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.

“In sha Allahu”.

Akuma dai-dai lokacin Dija da Yah Aliyu suka shigo Murmushi Khausar tayi tare da cewa.

“Dija”.

Cike da farin ciki Dija tace.

“Na'am Khausar ai mu bamu sani ba Khausar baku faɗa mana ba”.

Still da Murmushi afuskarta tace.

“Kiyi haƙuri Dija gaba ɗaya abin ne yazo min atsorace”.

Dariya Yah Ali yayi tare da faɗin.

“Raguwa gaba ɗaya kin gigice kin gigita bayin Allah”.

Langwaɓar da kai tayi kana tace.

“Hmmm ba dole inji tsoro ba Yah Ali abinda ance wasu da yawa idan an musu kafin afito dasu ta can
suke wucewa”.

Murmushi yayi tare da cewa.


“A'a ke kam in Sha Allahu kina nan sai kin kawo wasu ƙannensa goma sha ɗaya sun zama Dozen”.

Idanunta ta zaro tare da faɗin.

“Goma sha ɗaya”.

Baki ɗaya ɗakin suka sanya dariya.

Raudat dake zaune gefen Asma'u ta ƙyalkyale da dariya kana tace.

“Addah khausy idan kika haifi Dozen sai ki bani biyun saman na riƙa kulawa dasu kar suyi Miki yawa ai
Yah Moddibo zaku bani ko?”.

Ta ƙare maganar tana kallon Moddibo kai Moddibo ya gyaɗa yana Murmushi.

A ranan haka suka yini suna kula da ita.

Bayan sunyi kwana uku aka sallame ta suka koma gida.

Haka Didi da Momy suka cigaba da kula da ita suna bata kulawa na musamman...

Washe gari da safe Misalin ƙarfe 7:30 Asma'u ta zo zaune ta samu Lalla Khadijah, Rahama, na zaune kan
lallausan Darduma Yayin da Didi,Momy,Innayi ke zaune gefe ɗaya Hajja Nana kuwa na gefen Khausar da
Moddibo dake riƙe da Jaririn yana masa addu'a kana su kuma suna hira.

Ahankali Asma'u ta ɗago fuskarta ɗauke da Murmushi ta miƙa wa Khausar wayarta tare da cewa.

“Kalli wani special abu dana ajiye Miki wanda nake da yaƙinin sai kinyi min kyauta na musamman”.

Ɗan ware idanu Khausar tayi tana kallon Rahama dake cewa.

“Aikuwa dai Addah Asmeey muma dake gefe muna sa ran samun khauta”.

Dariya Khausar ta sanya kana tace.

“Aikam dai zanso gani”.

Ta ƙare maganar tana playing video

Da sauri ta zaro Idanunta waje ganinta kwance kan gado tana surutai.

Moddibo kuwa wani Amintaccen Murmushi ya saki ganin yanda ta zaro Idanunta waje sai kuma tayi
saurin ɗaga kanta cike da kunya jin yanda suka ƙyalƙyale da dariya cikin tura baki ta kalli Asma'u tare da
cewa.

“Asma'u Ni ko?,Aikuwa kin ci bashi sai na rama”.


Ta ƙare maganar cike da kunya ganin yanda suke maimaita maganar.

Asma'u kuwa Gwalo Asma'u tayi mata tare da cewa.

“Aikuwa sai dai ki rame yarinya dama can abinda ke Ranki kika faɗa”.

Khausar kuwa juyawa tayi jin Hajja Nana na cewa.

“Yoh ai gaskiya Asma'u ta faɗa ke da wannan mijin naki duk ba kunya ne daku idan ke baki cikin hayyacin
ki kika faɗa ai shi yana sane bare keɗin ma kina sane”.

Rau-rau da idanu Khausar tayi ta shiga bubbuga ƙafa daga zaune tace.

“Didi kiji fa abinda Hajja Nana ke faɗa wai bani da kunya”.

Murmushi Didi tayi tare da faɗin.

“Rabu da Hajja Nana am Khausar ɗina kina da kunya sosai ai bada sanin ki kikayi ba”.

Momy kam Murmushi kawai takeyi.

Daidai lokacin Jakadiya ta shigo tare da sanarwa Didi tayi baƙi ƴan Barka.

Miƙewa Didi tayi kana tace.

“Toh ganan zuwa”.

Sai kuma ta kalli Momy dake cewa.

“Mu tafi”.

Atare Didi Momy Innayi,Niyna suka fice.

Kallon Rahamah kalla Khadijah tayi kana tace.

“Rahama muje ki tayani haɗa Alawar Madara da gullisuwa tun jiya naso yi kuma ina zirga-zirga”.

Murmushi Rahama tayi tare da miƙewa Lalla Khadijah kuwa har taje ƙofa ta juya ta kalli kana tace.

“Ƙanwata kema zo muje”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare da miƙewa suka fita.

Falon ya rage daga Khausar, Moddibo sai Hajja Nana da itama ta miƙe ta fita falon.

Cikin shagwaɓa Khausar ta kalli Moddibo tare da narke fuska kana ta tura baki tace.

“Yah Mu'allim”.

Murmushi yayi kana ya kwantar da jaririn ya janyota jikinsa bakinsa ya kai saitin kunnenta yace
“Na'am Minha Viddaaaa ya akayi?”.

Ya ƙarashe yana jan sunan.

Cike da shagwaɓa tace.

“Jifa yanda na saki baki naita faɗan magana gabansu Momy da Didi kuma baka hanani ba”.

Murmushi yayi yana shafa bayanta yace.

“Ya za'a yi in hanaki fallasa min sirrin dake Ranki?,Taya kike tunanin bakina zai iya dakatar da zinaren
kalaman da suke fitowa daga bakinki suna ratsa kogon zuciyata?,Kin kuwa san farin ciki da shaukin dana
kasance alokacin?”.

Ya fesar da sanyayyan numfashi mai cike da zallan so da shauƙi yace.

“A lokacin ji nake tamkar ina yawo a gajimare ji nake tamkar nafi Mazan duniya Sa'a da samun
Nagartacciyan mace irin ki kin nuna min so tun baki san menene so ba shin mai zanyi in biyaki”.

Cikin wani irin yanayi na musamman tace.

“Ka ƙaunaceni ka kuma soni fiye da yanda nake son kaina kada ka haɗa ni da kowa atare da kai idan kayi
min haka kaga yimin komai Yah Mu'allim”.

Ahankali ya ɗago kanta tare da ɗaura lips ɗin sa asaman nata yashiga kissing ɗin ta...

Alhamdulillah zuwa yanzu jikinta yayi ƙwari bazama ace Thearter aka mata ba kullum Asma'u da Dija
anan suke yini ana I gobe suna Dr Zakariyya, Asiya Hajja Nana, Abban Jameel, Lalla Hafsat suka zo.

Hajja Nana da Innayi ce zaune da Khausar aɗaki yayin da Innayi ta zuba mata abinci ta bata taci Momy
kuma na riƙe da jiriri tayi masa wankan Yamma ta saka shi cikin wasu fararen kayan sanyu masu masifar
taushi pink and white collar.

Anutse Moddibo ya shigo ya same su Kai tsaye bakin gadon ya wuce gefenta ya zauna.

Kallonsa hajja Nana tayi tare da cewa.

“Wai kai kam baka jin kunya ne?”.

Juyawa yayi ya kalleta kana yace.

“Kin iso da sa ido ko? Idon ki be iya gani bakinki yayi shiru ko?”.

Hararansa tayi tare da faɗin.


“Ba dole ba idan bani nake taka maka birki ba babu mai taka maka birki”.

Kallonta yayi tare da cewa.

“Toh sai kiyi mugani in birkin zai taku”.

Anutse Khausar ta kallesa kana ta kalli Hajja Nana tace.

“Yah Mu'allim rabu da ita”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Aima na rabu da ita?”.

Khausar kuwa nutsuwarta ta tattara kana tace.

“Yah Mu'allim gashi har gobe suna in Allah ya kaimu”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Eh”.

Ahankali ta langwaɓar da kai tare da cewa.

“Kuma banji ka faɗa min sunan yaron ba”.

Murmushi yayi kana yace.

“Kuma tun a asibiti kafin ayi mishi wanka na masa huɗu ba tun kafin ki farfaɗo”.

Murmushi tayi kana ahankali tace.

“Kuma Yah Mu'allim baka faɗa min ba".

Juyawa yayi ya kalli Asma'u kana ya kalli Asiya dake cewa.

“Ai dai kam bamu san sunan yaro ba gashi har gobe Suna”.

Didi kam ido ta zuba mishi tana kallonsa Momy kuwa sunkuyar da kanta ƙasa tayi tana sawa Jaririn safan
hannu tace.

“Toh menene sunan”.

Sunkuyar da kansa ƙasa yayi kana ya motsa laɓɓansa tare da cewa.

“Sunan shi Jameel”.

Cikin tsananin jin daɗi Asma'u ta kallesa tare da cewa.


“Allah sarki Yah Moddibo Ubangiji Allah ya saka da Alkhairi Allah yabar zumunci ayyah Yah Jameel ɗina
Allah ya raya shi Allah ya mishi Albarka”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Ameen ya Allah Asma'u, Allah yasa ya biyo halin takwaransa”.

Ya ƙare maganar yana Murmushi.

Innayi ce ta amshi zancen da cewa.

“Naji Ibraahim kuna na kiranshi da *Keyan*”.

Kai Modibbo ya jinjina tare da cewa.

“Eh laƙanin kenan. Amman asalin sunan Jameel, Allah ya raya mana shi yayi nagarta irin ta mai
sunanshi”.

Cikin tsananin jin daɗi Asma'u tace.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum ”.

Khausar na Murmushi tace.

“Ameen ya Allah yasa ya biyo halin takwaransa Allah yasa yayi Ilimin takwaransa”.

Cikin jin daɗi Didi tace.

“Ka kyauta Babana Allah Ubangiji ya raya mana Jameelu”.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum ”.

Cikin tuno da Jameel Hajja Nana tace.

“Ameen ya Allah ai Jameelu mutumin kirki ne”.

Asma'u kuwa cikin sauri ta ɗauki waya tare da kiran Ummi Ummi na ɗauka tace.

“Ummi albishir”.

Daga ɗaya ɓangaren Ummu tace.

“Goro”.

Cike da farin ciki Asma'u tace.

“Yah Jameel ya samu takwara”.

Murmushi Ummi tayi tare da faɗin.


“Hmmm Asma'u kenan kece baki sani ba amma ainin tun ranan Aliyu ya faɗa min”

Murmushi Asma'u tayi kana tace.

“Ummi shine baki faɗa min ba ranan muna hira ina cewa Ala'andi wani suna za'a sawa yaron kikayi shiru
ashe duk kin sani”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Na sani mana tun ranan ya faɗa min”.

Murmushi Moddibo yayi tare da cewa.

“Ai TOH na rigaki yin albishir ɗin”.

Dariya ta sanya tace.

“Wallahi Yah Moddibo Ina sauri in rigaka ashe ka rigani”.

Haka sukayi yinin ranan anata shirye-shiryen suna, nan washe gari suna akayi raɗin suna da hidindimu
kamar yanda al'adan masarauta take.

Bayan sallar la'asar manyan Fada ne a zaune saboda Aranar Abualeey yake son yin Murabus ya barwa
Moddibo sarauta.

Bayan an zauna an cika a Fada anyi komai an taru Sarkin Al'adun Fada ne ya juya ya kalli Moddibo dake
cikin wani irin shiga na alfarma da kawa da yayi masifar fitar da ainihin kyawunsa da ƙwarjinsa kana
yace.

“Alhamdulillah kamar yanda al'adun Fada take sarki yana da dama da iko da zai yi Murabus tun yana da
rayuwarsa ya danƙa Mulki a hannun ɗan sa da yake ganin zai iya gadon mulkinsa kana zai iya kula da
Masarauta yanda ya kamata dan haka Sarki Youseef Mohammed Aliyu Mouley ma yayi alƙawari zai
maida Sarauta ahannun ɗan sa Aleeyu Youseef Mohammed Aliyu Mouley”.

Cikin jin daɗi Manyan cikin Fada da Manyan Masarautu na gefe-gefe wanda baki ɗaya sun san da
Maganar an samu sa hannunsu tun watanni hudu da suka wuce kowa cikin jin daɗi da farin ciki yake
faɗin Alhamdulillah.

Cike da girmamawa Sarkin Fada ya juya ya kalli Moddibo tare da cigaba da cewa.

“Kuma a wannan ranane za'a ƙara wa Sarki Aleeyu Youseef Mohammed Aliyu Mouley mata kamar yanda
atsarin Masarauta sarki bai kasancewa da mace ɗaya sai an masa biyu aranan da za'a danƙa mulki a
hannunsa”.
Cikin sauri Moddibo ya ɗaga kansa ya kallesu sai kuma ya saki wani Murmushi dashi kaɗai yasan ma'anar
sa juyawa yayi ya kalli Abualeey dake cikin matsanancin farin ciki kana ya kalli Sarkin Fada tare da cewa.

“Ina son magana da mahaifina”.

Kai Sarkin Fada ya gyaɗa kana yace.

“Toh shikenan ba damuwa”.

Kana suka shiga ɗakin Sirri Shida Abualeey, Waziri, Galadima Wambai Garkuwa...

A dai-dai lokacin kuma acikin gida Khausar ce cikin shiga ta alfarma sanye take cikin wani lafiyayyan
Abaya Pinch colour mai masifar taushi da santsi da yasha duwatsu kana ta ɗaura Alkyabba ta Masarauta
fari ƙall mai masifar taushi wanda al'ada ce ta Masarauta wanda ranan da za'a naɗa mijinka a Masarauta
zaka sa.

Shima Jaririn sanye yake cikin shiga na alfarma wasu picnh colour kayane tausasa kana aka daura masa
ƙaramin Alkyabba fari irin na jarirai.

Sai hotuna suke ta ɗauka dasu Lalla, Khadijah Lalla, Hafsat Asiya, Asma'u, Dija, Rahama, Raudat Asma'u
kuwa kai tsaye take turawa cikin group ɗin su na class mate ɗin su da suka gama makaranta.

Nan da nan cikin group ɗin ya kace me da surutu kala-kala kowa na tofa albarkacin bakinsa wata
ƙawarsu wacce lokacin da suke makaranta bencinsu ke kusa da nasu Khausar mai suna Hawwa Idris ne
tace.

“Ikon Allah wai Khausar ce haka🤔 girma yazo rawan kai ya gudu?”.

Tayi typing da emotion na mamaki dariya Asma'u ta tura mata tare da cewa.

“Gashi kuwa kinga zahiri”

Cikin Mamaki tayi voice dan gani take typing ɗin bai mata sauri kana tace.

“Masha Allah shiyasa akace arayuwa kada ka taɓa wulakanta mutum domin baka san baiwar da Allah ya
mishi ba wai yau Khausar ce matar Sarkin Morocco kuma Malam Moddibo?”.

Hoton dariya Asma'u ta sake tura musu tare da faɗin.

“Aikam ikon Ubangiji yafi gaban haka?”.

Wata mai suna Jidda ce tace.

“Aikuwa dai muma Allah yasamu Adamshin ku Asma'u ku kam kunji daɗin rayuwarku”.

Murmushin Samira Sani ta turo tare da cewa.


“Uhmmm kuma ku godewa Allah a yadda kuke ɗin”.

Da sauri Khadijah Sule tace.

“Sosai ma kam Samira am”.

Amin kuwa cikin sanyi da nadama tace.

“Alhamdulillah ai in Allah ya baka lfy ka gode masa”.

Haka dai suka cigaba da hira acikin group ɗin kowa na faɗin albarkacin bakinsa.

_Daga can gefe kuwa su ne Rafi'a,Tutus kitchen, Mom sayyeed&Noor Tatti Dija chiroma, ne da suka
halarci wajen sunan ne suke ta Video da hotuna suna turawa cikin Group ɗin SAKAYYA Team Moddibo
da Khausar kam baki yaƙi ruhuwa duk farin ciki ya cika su ganin irin gift da Khausar ta bayar akawo
musu._

_Daga can gefe kuma ƴan karatun bati siddan na Allah ya isa kenan da basu biya kuɗi ba suke wiƙi-wiƙi
da ido duk hakki ya hanasu sakewa da samun nitsuwa..._

Asma'u dake cigaba da hotuna da wayar Khausar wayar ya ɗauki suwwa ganin sunan Yah Mu'allim na
yawo yasa da sauri ta nufi Khausar dake tsakiyar Didi da Momy suna hoto tayi saurin isa gareta kana ta
tsugunna zata miƙa mata wayar kasancewar azaune suke haka yasa ta fito a hoton da yayi masifar kyau.

Asma'u kuwa cikin raɗa takai bakinta kunnenta tace.

“Gashi fa Yah Moddibo yana kiran ki”.

“Mu gani”.

Cewar Khausar tana karɓan wayar tare da kaiwa kunnenta tace.

“Assalamu Alaikum Yah Mu'allim”.

Cikin wani irin yanayin na musamman yace.

“Minha kizo ki sameni aɗakina”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh”.
Sai kuma ta miƙe tare da rungume jaririn kai tsaye ta nufi sashen bakinta ɗauke da sallama ta shiga falon
nan ta samu Dr Jameel, Dr Zakariyya, Ibraahim,Yah Ali, da Yah Abba da sauran yan uwansa.

Yah Abba na ganinta yayi Murmushi tare da cewa.

“Mai jego kin sha ƙamashi”.

Murmushi tayi kana tace.

“Ai dai kam”.

Kallonta ta mayar kan Ibraahim tare da cewa.

“Ibraahim Yah Mu'allim fa?”.

Da hannu ya nuna mata bedroom ɗin kana yace.

“Yana ciki”.

Ahankali ta nufi bedroom ɗin kwance ta gansa akan gadon yana ganinta ya saki sanyayyar ajiyar zuciya
tare da buɗe mata hannunsa.

Cike da begensa ta zauna kusa dashi miƙewa yayi ya haɗa ta da jaririn ya rungumesu ahankali ya riƙa
kissing ɗin goshinta zuwa wuyanta da kuma sassan jikinta baki ta ɗan tura tare da cewa.

“Yah Mu'allim ka matsaneni kuma ɗanka ya matse min wajen Theater na”.

Cikin sauri ya saketa kana ya karɓesa ya kwantar dashi tare da jawota jikinsa ya rungumeta sai kuma ya
saki sanyayyar numfashi kana ya ruggumeta tsam cike da kulawa da kuma ganin yanayinsa ta shafo
sajensa tare da cewa.

“Yah Mu'allim lafiya meke faruwa?”.

Kanta ya tallofo kana ya kalleta ido cikin ido da mamaki take kallonsa ganin yanda idanunsa suka kaɗa
sukayi jawur dasu cike da kulawa tace.

“Yah Mu'allim lafiya?”.

Sunkuyar da kansa ƙasa yayi kana ya ɗago ya kalleta tare da cewa.

“Minha na yiwa Abualeey laifi kuma har yayi fushi dani”.

Cikin sauri ta zare idanunta tare da faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Yah Mu'allim laifin me kayiwa Abualeey?”.

Araunane yace.

“Minha nayi mishi babban laifi naƙin bin Umarninsa”.


Cikin tsoro da kaɗuwa tace.

“Ya Ilahi Yah Mu'allim akan me baza kabi umarnin Abualeey ba?”.

Langwaɓar da kansa yayi kan wuyansa yace.

“Saboda kece ban bi Umarnin Abualeey ba!”.

Cikin sanyi da rauni tace.

“Ya Ilahi bana son jin wannan maganar sam maganar babu daɗin ji Yah Mu'allim Kabi Umarnin
mahaifinka shine abinda ya dace kuma shine *SAKAYYAR* da zamuyi masa”.

Cikin rauni da karyewar zuciya yace.

“Bazan iya ba”.

Cike da mamakin shin wani irin abu ne me nauyi da girma agaresa da yasa har ya yiwa mahaifinsa
gardama tace.

“Haba Yah Mu'allim ya za'a yi kace baza kayi abinda mahaifinka keso ba shin wani irin abu ne?”.

Cikin sanyi ya kalleta kana ya lumshe Idanunsa tare da cewa.

“Saboda yau yake so a bani mulkin Masarautar Mouley ahannuna”.

Cikin sauri da jin daɗi kana da Jimamin yanayin da yake ciki tace.

“Toh mene Yah Mu'allim mulkin ne baka son rikewa ko me meyesa zaka yi mishi gardama?Kuma ai
nikam ma ina son mulkin nan meyesa baza ka karɓi Sarautar ba? Kawai ka karɓi mulkin shine abinda ya
dace”.

Kai ya jujjuya tare da juya ƙwayar idanunsa acikin nata kana ya riƙo hannunta acikin nasa tare da cewa.

“Ba karɓan mulkin bane matsala Minha”.

Cikin rashin fahimtar abinda ke damunsa tace.

“Toh ka karɓi mulkin mana kayi mishi biyayya akai”.

Hannunta ya damƙe kana yace.

“Ki bari kiji ko menene”.

Fuska ta tsuke tare da cewa.

“Nikam babu abinda zanji Yah Mu'allim kawai kayi mishi biyayya akan abinda yake so ka karɓi mulki
Allah ya tayaka riƙo ya baka ikon Adalci kai masa biyayya ka samu lada”.
Cikin sanyi da rauni yace.

“Cewa yayi an bani mulki bisa sharaɗin za'a bani Auren wata mata ya zama ina da mata biyu!”.

Da wani irin sauri ta dafe ƙahon zuciyarta da yayi wani irin harbawa cikin rauni da fusgar magana tace.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”.

Atake jikinta ya fara rawa kar-kar-kar tamkar wacce aka watsawa ruwa ƙanƙara atsakiyar hunturun sanyi
kana idanunta suka kaɗa sukayi jawur tamkar garwashin wuta lokaci ɗaya taji numfashinta na Up and
down alamar yana shirin barin gangar jikinta jawota yayi ya riƙe ta da damuwa atare dashi yace.

“Kee ki tsaya mana ki nutsu me haka!?”.

Gaba ɗaya ta rikice numfashinta sai fusga yake alamun tana gab da suma saboda tsabar masifar kishi,
cikin fusgar numfashi da ficewar hayyaci ta dafe ƙahon zuciyarta tare da cewa.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Yah Mu'allim Aure kuma?,Wata matar za'a Aura maka?,ita?”.

Sai kuma ta tsaya da Maganar jin numfashinta na shirin barin gangar jikinta alamar zata iya rasa
numfashinta.

Moddibo kuwa cikin matsanancin mamaki tsoro gami da ruɗu yake kallonta tabbas yasan tana da kishi
amma bai taɓa tunanin kishinta yakai wannan matsayin ba.

Cikin sauri ya rungumeta tare da riƙo hannayenta kana yana jijjiga fuskarta yace.

“Khausar Khausar ki nutsu mana ki buɗe idanun ki dan Allah ki tsaya ki fahimci abinda zan faɗa miki”.

Da ƙyar ta iya buɗe idanunta.

Cikin sauri da tsoro ya sake tallafe Fuskarta ganin yanda ta zazzaro idanunta sukayi wani irin ja.

Ahankali ya fara bubbuga kumatunta tare da cewa.

“Dan Allah Minha ki nutsu kiji abinda zan faɗa Miki”.

Cikin rauni murya da bugawar zuciya tace.

“Yah Mu'allim yanzu mata zasu ƙara maka innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”.

Sai kuma ta kife kanta akirjinsa ta saki marayan kuka mai masifan cin rai da zafi kukan data sakene ya
temaka wajen daidaiton numfashinta ya tsaya.

Ahankali ya tallafota jikinsa yace.


“Minha shine laifin da nace Miki na yiwa Abualeey saboda nace masa, in dai har sai an ƙara min mata
za'a bani mulkin, ni na yafe bana buƙatar mulki abawa Ibraahim nayi alƙwari zan rayu daga Ni sai ke sai
kuma ɗan mu da kuma wa'anda zamu haifa nan gaba”.

Khausar kam wani irin kuka mai tsuma zuciya da tsananin kishi take yi.

Moddibo kuwa cikin gaskiya da gaskiya ya cigaba da cewa.

“in dai akan mulkine zan yi Miki kishiya abawa Ibraahim in yaso a Aura mishi Mata huɗu a rana ɗaya,
nayi alkawarin bazan yimiki kishiya a kan mulkiba Amman ban miki alkawarin cewa wai bazan Miki
kishiyaba dan bansan ne Allah zai tsara a kanmuba a gaba”.

Da sauri ta tashi kana ta buɗe Idanunta cikin rauni da shesh-sheƙa tace.

“Mata fa kace zasu Aura maka”.

Cikin kwantar mata da hankali yace.

“Ba kiji mai nace Miki bane indai mulki ne na haƙura dashi a bawa Ibrahim abarni Ni in rayu dake da
ɗana da abinda zaki haifa agaba”.

Ahankali ta shiga sakin ajiyar zuciya Moddibo kuwa cike da tarin ƙaunarta ya cigaba da faɗin.

“Na tabbar kun isheni farin ciki kun isheni jin daɗin rayuwa kun isheni komai batare da mulkin nan ba Ni
na yarda zan kasancewa Ibraahim mai bada shawara abawa Ibraahim mulki shine abinda yafi min
kwanciyar hankali hakan ya miki kinji daɗi akan haka”.

Cikin matsanancin jin daɗi da farin ciki tace.

“Na yarda in dai har Abualeey ya yarda Bama son mulkin mun bar musu mun yafe musu mulkinsu
Mukam Bama so”.

Akuma dai-dai lokacin Jaririn yasa kuka cikin sauri ta kallesa cikin shesh-sheƙan kuka tace.

“Abu J ba ka jiba yana kuka shima baya so a yiwa Mimeeinsa kishiya”.

Cikin sauri ya rungumota jikinsa kana ya haɗa da jaririn ya rungumesu tare da cewa.

“Mu bar musu mulkinsu Minha ba ruwanmu suje can su ƙarata da mulkinsu, su riƙe abinsu abarmu haka
mu cigaba da jin daɗi da kwanciyar hankali yafi mana”.

Dai-dai lokacin Ibraahim yayi knowking kana ya sanar masa zuwan Momy da Didi.

Suna shiga Didi ta kallesa Babu walwala atare da ita tace.

“Yanzu Aleeyu ka kyauta kenan ɓacin ran da kasa Mahaifinka”.

Cikin sauri ya mike kana ya tsugunna gaban Didi tare da cewa.


“Didi dan Allah kuyi haƙuri”.

Cikin sauri da rashin walwala Didi tace.

“Shi ya gama yanke hukunci amatsayin sa na Mahaifin ka Sarautace an riga da an baka ita sai kayi abinda
kaga zaka iya akai”.

Da sauri cikin shesh-sheƙa Khausar tace.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Didi yanzu kuma harda Mata za'a ƙara mishi?,”.

Cikin tsuke fuska momy ta harareta tare da cewa.

“Dan Allah rufe mana baki, sokuwar banza sokuwar wofi, in ba'a Aure ke aka Auro ki baza ki taya mijinki
yanda zai yiwa iyayensa biyayya ba, sai ki tsaya sokonci kina kuka kina cewa an ƙara masa mata matar
kashe ki zata yi, ko kuma akan ki zata zauna?”.

Cikin rauni ta fashe da kuka kana ta jingina kanta da bakin gado cikin shesh-sheƙan tace.

“Momy ba zaki gane bane bazan iya rayuwa da wata mace tare da Yah Mu'allim ba”.

Ahankali Didi ta ɗagota kana ta dafa kafaɗarta tare da cewa.

“Kiyi haƙuri Sarauta ce an bashi Mata kuma tunda yace baiso da ɗaya zai zauna shikenan tun da dama
bawai shariya ɓace ta tsara haka, al'adace”.

Ajiyar zuciya mai sanyi ta shiga saki tana jin nutsuwa na diran mata shi dai Moddibo kan sa na ƙasa Didi
kuwa cikin kwantar mata da hankali ta cigaba da faɗin.

“Allah da kansa ya basu Umarni suyi Huɗu, Uku, Biyu idan kuma ba zasuyi adalci ba suyi ɗaya tunda yace
ba zai yi adalci ba laifi.

Mahaifinsa ya yarda an bashi Sarauta batare da anƙara mashi mata ba”.

Cike da matsanancin farin ciki ta mike ta rungume Didi kana tace.

“Nagode Didi Ubangiji Allah ya miki Albarka”.

Cikin sauri ta saki Didi kana ta tsugunna ta fuski Alƙibla tare da yin Sujudur Shukur ta godewa Allah
kallonta ta mayar kan Moddibo dake Murmushi ta miƙa masa hannu tare da cewa.

“Yah Mu'allim Alhamdulillah ”.

Martanin Murmushi ya mayar mata yana mai jin wani irin nutsuwa na ratsa sassan jikinsa ganinta cikin
farin ciki ahankali yace

“Alhamdulillah”

Murmushi Didi tayi tare da riƙe hannun momy kana ta kalli Moddibo tace.
“Idan ka gama murnan ka tashi ka tafi Fada ana damƙa maka sarauta”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh”.

Momy kuwa kallon Khausar tayi kana tace.

“Wuce mu tafi ”

Ta ƙare maganar suna fita.

Cikin sauri Khausar ta miƙe tare da faɗawa jikin Moddibo tayi masa wani Amintaccen runguma sai kuma
ta tallafo kansa ta haɗe bakinsu ta shiga kissing ɗin sa ahankali ta zare harshenta cikin nasa tare da riƙe
hannunsa Fuskarta ɗauke da maɗaukakin farin ciki tace.

“Ina ƙaunarka Abu J My life is nothing without you”.

Murmushi yayi kana ya lakace mata hanci tare da cewa.

“Shikenan kuka ya ƙare ko?”.

Dariya ta sanya tare da ɗaukan Jaririn tabi bayansu Momy da tuni suka fice kana shi kuma ya fita ya
samu su Ibraahim suka wuce Fada.

Aranan aka naɗa masa Sarautar Mouley kana aka ɗaura auren Rahama da saurayinta kana matar da za'a
Aura masa aranan aka Aura wa Ibraahim ita Ibraahim kam. baki har kunne cikin jin daɗi da farin ciki aka
gama Shagali da daddare aka kaiwa Ibraahim matarsa.

Tun aranan Lalla Hafsat da wasu daga cikin baƙi suka tafi da Rahama kasan cewar ƙanin mijin Lallai
Hafsat ne mijinta yasa aka wuce Mexico da ita baƙin suna kuma duk an watse lfy...

Haka rayuwa ta cigaba da tafiya Khausar na samun kulawa mai kyau.

ranan da ta cika sati Uku Alhamdulillah Thearter yayi gwaɓi sosai suka je asibiti aka sake dubawa a
ranan sukaje asibiti Alhamdulillah aka duba akace babu matsala yayi kyau saboda jikinta yana da kyau
yaro yayi kuɓul-kuɓul gwanin sha'awa Masha Allah.
A ranan da suka cika wata ɗaya da yammaci Khausar bayan ta fito daga wanka ta shirya cikin wani riga
da skirt na less me kyau jikinta sai ƙamshi yake ɗan ta yayi kuɓul-kuɓul Masha Allah yayi ƙato gwanin
ban sha'awa.

Zaune suke Khausar Innayi da Hajja Nana suke a bedroom.

Yayin da Momy da Raudat ke zaune Side ɗin Didi tana ta shirye-shiryen tafiya nan da kwana biyar masu
zuwa.

Ahankali Moddibo ya shigo bedroom ɗin hannunsa riƙe da Jaririn dake tsala kuka kusa da Khausar ya
zauna kana ya ɗaura mata yaron akan cinyarta kai ya langwaɓar cikin wata amintacciyar murya me cike
da kulawa tare da tsantsar soyayya yace..

“Minha yunwa fa yake ji”.

Ashagwaɓe ta tura baki kana ta langwaɓar da kai tare da cewa.

“Yah Mu'allim ɗazu fa yasha kuma sai yaita tsotseni”.

Akasalance yace.

“Ki ƙara mishi”.

Fuska ta narkar tare da faɗin.

“Toh tunda ya daina kuka a bari sai anjima”.

Ahankali ya girgiza kai kana yace.

“A'a ki bashi yanzu”.

Miƙewa Innayi tayi tare da cewa.

“Khausar bari inje inyi Miki ɗan wake naji kina cewa kina son ɗan wanke tunda kika haihu baki ciba”.

Murmushi tayi kana tace.

“Yawwa Innayi na ayi min shi yaji yaji yayi daɗi sosai sannan asa min da ƙwai da lemun tsami akai”.

“Toh".

Innayi ta amsa tare da ficewa.

Hajja Nana kuwa ido ta zubawa Moddibo lokacin daya zuge zip ɗin rigar Khausar ta baya.

Cikin Mamaki tace.


“Ohhhh ikon Allah”. Ta faɗa asanda taga yayi ƙasa da wuyan rigar Nonon fito, kan yaron ya tallabe ya
sawa yaron abakinsa.

Ta cigaba da cewa.

“Gwara ma ni in tattara mu koma in bar muku gidanku. hankalin mu ya kwanta wai nan kai Sarki ne
guda".

Juyawa yayi ya kalleta kana yace.

“Toh ce Miki akayi Sarauta anayinsa atsakanin Iyalai ne?

Ai sarauta iya kacinta Fada”.

Cikin taɓe baki Hajja Nana tace.

“Ohhh Allah ya kawo mu zamani ai kai ko A Fada idan zaka samu za kayi musu taɓara”

Murmushi yayi yana shafa sajensa yace.

“Toh Matatace fa,Ko ba matata bace?

Sadaki fa na biya”.

Hararansa tayi tare da cewa.

“Ka biya ko aka biya maka?”.

Dariya maganar nata ya bashi amma sai ya murmusa yace.

“Eh koma dai menene Matatace ni wlh kin isheni da gorin biya min sadaki akayi dan haka ni yau zan biya
nawa sadakin”.

Ya ƙare maganar yana jan wayarshi tare da ƴan danne-danne.

Dariya ta sanya tare da cewa.

“Ohhh baki baya mutuwa ai da kai da ita duk bakin ku ɗaya ne”.

Khausar Murmushi take musu tana cigaba da bawa yaron Nono.

Sai kuma ta kalli wayarta jin sautin shigowar saƙo.

Hannunta na hagu tasa ta ɗauki wayar tare da buɗe saƙon.

Cikin tsananin mamaki ta zaro ido ganin alert ɗin 10 million da Modibbo ya tura nata da rubu a jiki.

*Minha ga sadaki na*.

Cikin kaɗuwa tace.


“Yah Mu'allim 10 million fa ka turo min me sanyi dasu, million goma”.

Sai kuma ta ƙare maganar da kallon Hajja Nana dake cewa.

“Da gaske”. Cikin tsananin jin daɗi Khausar tace.

“Wallahi kuwa gasu kin gani”.

Ta ƙare maganar tana miƙa mata wayar da kuma yaron sai kuma ta ruggumeshi tana saki kishi sassayan
kiss tako ina a jikinsa.

Ganin yadda ta ruɗene yasa Hajja Nana yarda bawai dan ta fahimci rubutun alert ɗin ba.

Haka tai ta murna tare da godiya, kukan da Keyan ya sakan ne yasa ta saki uban ta karɓi ɗan kana taci
gaba da bashi Nono.

Cikin dariya Hajja Nana tace.

“Daga yau ka huta da gori, kuma dole a bani million ɗaya a ciki”.

Murmushin yayi tare da cewa.

“Kawo account inki in baki naki sadakin tunda jikarki na gudun kishi sai in haɗata dake”.

Cikin dariya tace.

“Yoh ina ni ina aure ai na gama aure kam”.

Dariya sukayi baki ɗaya.

Bayan ta gama bashi da kansa ya mayar da Nonon kana ta mike tare da faɗin.

“Kizo muje ki gyara min Siff ɗina ya hargitse”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Toh”.

Tare da miƙewa tabi bayansa da kallo Hajja Nana ta bisu sai kuma ta saki Murmushi tare da ɗaukan
Jaririn tana mishi wasa.

Suna shiga tsakiyar bedroom ya jawota jikinsa ya rungumeta yana shaƙan ƙamshin Kwalaccan Sirri da
Humran _Aunty Aysha Aliyu Garkuwa_ da tayi amfani dashi sosai ƙamshinta ke zautar dashi yana masifar
son ya riƙa shaƙar ƙamshin jinta yana masifar gigita masa tunani cikin wata kasalalliyar murya me cike da
shauƙi da fitina yace.

“Minha yanzu dan Allah tsawon kwana nawa kika fara Sallah?”.
Cikin lumshe idanu da yanda lallausan tafin hannunsa ke yawo asassan jikinta ta fesar da sanyayyan
numfashi tare da cewa.

“Yah Mu'allim nafi sati biyu da fara Sallah ”.

Ɗan ware idanunsa yayi kana muryansa can ƙasan maƙoshi yace.

“Kina tsoron kishiya kuma kina tsoron kyautatawa mijinki da ɗauke bukatarsa”.

Ashagwaɓe ta ƙyafta ƙwayar Idanunta cikin nasa tace.

“Yah Mu'allim nifaaaa”

Da sauri ya sake ƙanƙameta yana sakin ajiyar zuciya yace.

“Minha kin san dai ina da buƙata bazan iya jiran abinda Likitocin nan suka faɗa ba”.

Cikin sanyi da ɗan tsoro tace.

“Thearter na fa kada ya ɓalle”.

Yana yawo da hannunsa aƙugunta yace.

“Bazai ɓalle ba”.

Ya ida maganar yana zama bakin gado kana ya zaunar da ita kan cinyarsa tare da zuge zip ɗin rigar ta
yayi ƙasa dashi kana shima ya cire nashi blanket ya jawo ya rufe su tare da ɗaura bakinsa akan dogon
hancinta yana tsotsa kana ya mayar kunnenta yana hura mata sanyayyar iskan bakinsa.

Sai kuma ya tsaya jin tana cewa.

“Yah Mu'allim ina tsoron Theater nafa”.

Muryansa can ƙasan maƙoshi irin na wanda ke cikin tsananin buƙatuwa yace.

“Na sani zan biki ahankali”.

Bai jira jin Abinda zata ceba ya shiga sarrafa ta cike da bege da kuma shauƙi yayin da ya shiga Binta
hankali cikin shagwaɓa da tsoro tace.

“Wayyo Yah Mu'allim wajen Theater na zafi fa ina tsoro kar ka ɓalle min ɗinki?”.

Cikin ficewar hayyaci yace.

“Minhaaaaa bazan ɓalle Miki ba ki nutsu dan Allah”.

Ita kam cigaba da zuba masa shagwaɓa da raki tayi tana cigaba dace masa wajen Theater ta sai da ya
ɗauki kusan awa ɗaya akanta kafin ya janye jikinsa daga nata ya janyota jikinsa ya rungumeta yana sa
mata albarka sai kuma yayi Murmushi yace.
“Matsoraciya sai raki ɗinki ɗinki ɗinki sai raki da tsoro".

Cikin sauƙe ajiyar zuciya tace.

“Yah Mu'allim Allah tsoro nake ji kar ya ɓalle”.

Yana shafa shafeffen cikinta yace.

“Ba abinda zai ɓalla shi Minha”.

Miƙewa sukayi suka shiga toilet sukayi wanka atare bayan sun fito suka fara jiyo muryan Raudat na
cewa.

“Assalamu alaikum.

Addah khausy”.

Da sauri Khausar ta ƙarasa jan Zip ɗin rigar ta ta nufi ƙofa kallonta Moddibo yayi tare da cewa..

“Kamar Raudat ko?”.

Kai ta gyada kana tace.

“Eh Itace kuma kamar Naji kukan Keyan”. atare suka fita yana gyara wuyar rigarsa yayin da take naɗe
ƙasan rigarta.

Suka fita falon idanunsa ya sauƙa kan Raudat dake rungume da jaririn.

Ware idanu Moddibo yayi tare da faɗin.

“Ya Salam Aunty Raudhiy yanzu ke aka bawa Yaron nan?”.

Murmushi tayi tare da kallon fuskar Keyan tace.

“Yah Moddibo ai na iya riƙewa bazan kada shiba”.

Murmushi yayi tare da faɗin.

“Aikam ba zaki kada shiba kawo shi nan”.

Karbansa yayi ya bawa Khausar ta zauna tana bashi Nono suka zauna gefenta suna ta hira...

Bayan kwana biyar Momy suka wuce Saudi ita da Hajjaj Nana dan Modibbo ya biya musu umra, bayan
sun gama aikin umrarsu ne suka koma Nigeria bayan komawar su da sati ɗaya akayi.
Auren Amina da Baban Samira Sani cikin ikon Allah mai gadin gidansu Samira yace yana sonta fahimtar
yanayin da take ciki kuma zuwa yanzu Alhamdulillah jikinta yayi sauki arana ɗaya aka ɗaura Auren
Babanta ya bashi gida da jari kana ya nemi wani sabon mai gadi.

Haka suka tare abinsu Samira da maigadinsu.

ita kuma Amina tana rayuwarta da tsoho.

Hajiya Bunayya da Hajiya Lami kuwa na can Sycatry suna gallar rayuwarsu da girban abinda suka shuka.

Haka dai Rayuwa ta cigaba da tafiya Khausar kam Alhamdulillah yaronta ya kai wata shida yayi ɓul-ɓul
dashi yana zama kana yana wangale baki yana dariya sosai.

A wannan lokaci kuma suka tafi aikin hajji, Ita da Modibbo da ɗan Jaririnsu da Hadimar dake kula dashi
da kuma innayinsu, Asma'u da Dr Jameel, Asiya da Dr Zakariyya, Dija da Yah Ali, Yah Abba da matar daya
aura wata biyu ɗaya wuce.

Sai Didi da Innayi da Abu Ali, da kuma Ibrahim da matarsa.

Watansu ɗaya a can suka dawo, bayan sun dawo da mako biyu suka je Mexico.

Sosai Lalla Hafsat da Rahama sukayi daɗin sosai.

Itama kanta Khausar Mexico tayi mata daɗi sosai.

Makonsu uku suka dawo.

Taraba. Nigeria Gembilan

Yau ya kasance labari cikin ɓadda kama Uncle Naseer ya shigo cikin garin Gembila da niyyar kwashe
Mahaifiyarsa da Mahaifinsa su koma Indi'a da zama.

Cikin dare ya shiga cikin unguwar su da sauri ya buɗe musu mota tare da cewa Mamansa da Babansa.

“Kuyi sauri kushi ga mu tafi”.

Kai Maman ta gyaɗa kana tace.

“Toh ai gwara ka kwashe mu mu tafi mu huta da jaraba da Sa idon mutanen gari da gulmace-gulmace”.
Ta ƙarashe Maganar tana shiga motar.

Shikam Uncle Naseer cikin sauri ya shiga motar yaja su.

Suka fara tafiya suna gab da fita garin Gembilan motarsu tayi tambul ta riƙa juyawa tana bugawa da
tsaunukan gefen titi kafin ta kama da wuta sukayi mugun ƙonewa sai ya Fuskarsu ce ta rage kana kuma
b....

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

SAKAYYAH

72

*_Last Page_*

Uncle Naseer kuwa, daga ƙugunsa zuwa ƙafafunsa ya ƙone ƙurmus kana bai mutuba yayin da fuskarsa
yayi baƙiƙƙirin yanayin halittar fuskarsa ta sauya tamkar an babbaka kare. Mamansa, Babansa kuwa
atake rai yayi halinsa Uncle Naseer kuwa cikin ƴan kawo agajine suka daukesa suka kaisa asibitin cikin.

Taraba.

Daga ƙarshe dai dole Lamiɗo aka kira Lamiɗo kam lokacin da akace Uncle Naseer yayi hatsari sosai yayi
mamaki kasancewar baisan zuwansa garin ba kana yayi mamaki da akace iyayensa sun mutu...

Lokacin da Lamiɗo ya isa asibitin ya samu ina baki ɗaya Uncle Naseer babu abinda yake Banda jujjuya
kai cikin tsananin azaba da Kiɗima sosai Lamiɗo ya tsorata da ganin yanda halittarsa ta sauya baki ɗaya
jikinsa yayi sanyi ya sake jin tsoron Allah da kuma tsoron saɓawa Ubangiji.

Uncle Naseer kuwa Cikin matsanancin kuka da radaɗin azabar daya game jikinsa ya kalli Lamiɗo kana ya
riƙe hannunsa tare da cewa.

“Na ƙulla sharri na kulla rashin imani na ƙulla shirka da riya da yawa gashi Allah ya kamani lokacin da
banyi zato ba lokacin da nake tsaka da shirya makirci na zama abin tausayi kuma abin ƙonawa cikin
wanan azabebuyar wuta”.
Kai Lamiɗo ke girgiza wa cikin tsananin tausayi da son kwantar mishi da hankali Amman ina.

Cikin ihu da kururuwa Uncle Naseer ya cigaba da cewa.

“Gashi tun daga nan duniya Allah ya fara ƙonani da wuta ina ga naje lahira nayi tsafi na sadaukar da
mutane da yawa nasha jini”.

Kai Lamiɗo ya girgiza cikin sanyi da mamaki yace.

“Babu amfanin wannan maganar Naseer kawai ka tuba zuwa ga Allah kayi ta Istigfari”.

Cikin kururuwa da azaba Naseer ya girgiza kai tare da faɗin.

“Bazam iya ba bana jin zan iya tuba Ni mushrikine na haɗa Allah da wani saboda duniya wayyo nashiga
uku na lalace kaicona wayyo Ni wayyo kaina”.

Kallonsa Lamiɗo yayi cikin mamaki yace.

“Baka iya tuba kuma toh kana so ka mutu da zunubi ne?”.

Kai kawai Uncle Naseer ke girgizawa ya gaza buɗe bakinsa ya nemi gafarar Ubangiji alamar Allah ya hana
shi samun rahamar sa haka sai ya cigaba da surutai yana kururuwa tare da faɗe-faɗe da kuma abinda
yake aikatawa cikin azaba da zugin da jikinsa ke masa yace.

“Ni nake zama Maciji na tsotsa jinin Amina naso in kashe ta Allah bai ƙaddara ba kwananta yana gaba
ita. Asirinta ya ruhu naso in cutar da ita Allah bai nufa ba amma laifin Mahaifiyarta su suka nuna
kwaɗayin kuɗinsu ga yanda rayuwa ta zamo mini”.

Ya ƙare maganar cikin tsananin kururuwa da firgita yayin da yake fisge-fusge yana zabura kana idanunsa
suka zazzago cikin ihun azaba yace.

“Ka gani ko zan mutu kuma in na mutu cikin wuta zan shiga kaga wutar da ake nuna min kalletafa sai ci
take tamkar ba abinda zai kashenta”.

Cikin rashin sanin madafa da tarin tsoron Allah Lamiɗo yace.

“Naseer ka daina kururuwa ka tsaya kayi salati da istigfari”.

Yana cigaba da ihu tare da firgita yace.

“Inyi salati kana ganin wutar da ake nuna min cikin wutar nan wai za'a jefani? Kuma kace inyi shiru”.

Haka dai ya ci gaba da tona wa kansa asiri ɗa'a fade-faɗe abubuwan d yake ganin, yinin wannan ranan ya
mutu aka tattarasu dasu da iyayensa aka binnesa...
A cikin wannan kwanakin kuwa Baffa Jimeta yace Hajja Nana ta tattara kayanta su koma Yola ya gaji da
zamanta a Jauro Yaya haka ya ɗaukota ta dawo Adamawa da zama ba don ta soba, Amman bini-bini
zatace ya kawota haka kuwa dole yake kawotan tai kwanaki azo a ɗauleta tana komawa bazata rufa
wataba zatace a Kaita.

Amina kuwa Alhamdulillah rayuwa ta cigaba da tafiya mata cikin kwanciyar hankali tana ta Istigfari tana
zaune Lafiya da Mahaifin Samira wanda har ta samu ciki.

Wata rana ta fito daga gidan Samira kasancewar basu da nisa tayi mata rakiya kasancewar aminaine har
zuwa yanzu suna Aminanta kansu.

Suna fitowa suka ga wani mahaukaci yara na binsa suna ta ihu yana cewa.

“Nine dai Boka Kar'uzu na aikata shirka na ɓatar da mutane na shuka zunubai da yawa Ni nariƙa yiwa
mutane Sihiri!”.

Cikin tsananin mamaki da rawan jiki Samira ta kalli Amina tare da cewa.

“Amina wanna Boka Kar'uzu ne fa”.

Da sauri Amina ta dafe ƙirjinta tace.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un wallahi Samira shine rayuwa ba tabbas duk wanda ya saki Allah ya kama
waninsa ya shiga uku”.

Cikin sanyi Samira tace.

“Wallahi kuwa Allah ya yafe mana Ubangiji yajiƙanmu ya gafarta mana zunubanmu”.

Cikin kaɗuwa da rauni Amina tace.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum ”.

Boka Kar'uzu kuwa cikin ihu irin na ƙazamai lalatattun mahaukata da ƙarshen su ya munana ya cigaba
da ihu yana faɗe-faɗe yaje zai tsalle ke kwalta wata ƙatuwar Mota ta buge kansa atake yayi daga-daga
akan kwaltan mai motar kuwa ko tsayawa baiyi ba ya gudu.

Irin ƴan iskan samarin nan ne suka sa Shebir suka kwashe Jejjegen naman gawarsa suka tura aƙaton
kwalbet da ruwa ke gudu ruwa yaja gawarsa ya wuce ya kai sa cikin Fadamar Gembila kifaye suka samu
abinci.
Haka dai Rayuwa ta cigaba gaba da tafiya mai aikata Alkhairi ya fuskanci Alkhairi mai aikata sharri ya
fuskanci sharrinsa ra'anul aiyn...

Morocco rayuwa ta cigaba da tafiya cikin daɗi da kwanciyar hankali Keyah yayi kuɓul-kuɓul dashi ya
shiga wata na takwas har ya fara tsayuwa Moddibo ne zaune a tsakiyar falon Didi yayin da Keyah ke
rarrafe cikin Murmushi Moddibo yace.

“Iyeeee Toyi manga toy-toy Toyi manga toy-toy manga”.

Yana ɗan tafa hannunsa Keyah kuwa ƙoƙarin miƙewa yake yana ƙyalƙyala dariya.

Didi dake gefe tayi Murmushi tare da cewa.

“Ohhh zai fa haukataku in baku nutsu ba fa”.

Dariya Moddibo yayi kana yace.

“Didi kin gani dai ya fara tsayuwa ko”.

Kallon Keyah dake tsaye ya dafe jikin kujera tayi tare da faɗin.

“Toh Barka tunda ya fara tsayiwa yayi kyau anyi Sa'a Barka”.

Matar Ibraahim dake gefen Didi tayi Murmushi tare da cewa.

“Wallahi kuwa Didi kallifa ya tsaya fa”.

Sai kuma ta juya ta kalli Khausar tace.

“Ba ina faɗa Miki ba shekaran jiya ya riƙe kujera ya tsaya ba. cewa kin dai ji baki yardaba tunda ba ki
gani ba Lalla Khausar”.

Murmushi Khausar tayi tare da cewa.

“Ato yanzu kam na gani da idona Oum Keyah”.

Cikin sauri Matar Ibraahim ta rungume Keyah tare da faɗin.

“Allah ya raya mana kai da Imani Keyah”.

Murmushi Moddibo yayi kana yace.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.

Miƙewa tayi ta ɗauki Keyah tana masa wasa ta nufi Side ɗin sa.

Khausar kuwa Ahankali ta juya ta kalli Moddibo cikin sanyi tace.


“Yah Mu'allim na kwana biyu banji labarin Asma'u ba tun ranan sunan Addah Asiya fa bamu sake
haɗuwa ba”.

Cike da kulawa Moddibo ya gyara zamansa yace.

“Toh badamuwa in Sha Allahu da daddare zamu je”.

Bayan Khausar sun idar da sallar Isha'i suka tafi gidan Asma'u afalon suka same su zaune Dr Jameel na
zaune ƙasa Asma'u na saman kujera kallon Khausar Dr Jameel yayi tare da cewa.

“Yawwa gwara ma da kika zo”.

Cikin kula Khausar tace.

“Toh meke faruwa?”.

Ta ƙare maganar tana miƙawa Asma'u Keyah data miƙo hannu”.

Karbansa Asma'u tayi cikin sanyi murya take masa wasa tare da cewa.

“Keyah ɗan Albarka”.

Wangale baki yayi yana ƙyalƙyala mata dariya ƙyal-ƙyal-ƙyal rungumesa tayi tare da sumbatar sa kana
tace.

“Allah ya maka albarka”.

Khausar na Murmushin yanda Asma'u ke nunawa Keyah soyayya tace.

“Ameen!”.

Moddibo kuwa ido ya ɗan zubawa Asma'u dan ya lura kamar fuskantar na ɗan kumbere kaɗan more
especially eyes ɗinta.

Ajiyar zuciya Dr Jameel ya sauƙe kana yace.

“Ki ganta nan wai ita tana ga bata da rabon haihuwa tunda duk gwaje-gwajen da za'a yi anyi lafiyanta
ƙalau nima lafiyata lau, amma gashi har yanzu bata da ciki shine take ta kuka b'na faɗa mata lokacine, ta
kwantar da hankalinta”.

Cikin sanyi tayi Murmushi hawaye na zuba a idanunta tace.

“Ka gani fa Addah Asiya ta haihu Dija ma ta haihu amma Ni har yanzu ko ɓatan wata ban taɓa yiba ina so
in haifawa Keyah Mata”.

Murmushi Khausar tayi tare da faɗin.


“Ai zaki haifa masa lokacine fa Asma'u yaushe ma akayi Auren badan haihuwar wuri da ake yiba”.

Lumshe Idanunta hawaye suka zubo kana ta taune lips ɗin ta na kasa tare da faɗin.

“Hmmm Khausar yanzu fa kusan shekara biyu muke nema tunda mun cika shekara ɗaya da wasu
watanni da yin Aure har na biyu muke nema”.

Araunane taci gaba da cewa.

“Khausar am har yanzu fa ban haihu ba ko ɓatan wata ban taɓa yiba kuma duk gwaje-gwajen da za'a yi
anyi ance lafiyata lau shima Dr bashi da matalan komai”.

Gyaran murya Moddibo yayi kana yace.

“Kiyi haƙuri Asma'u lokacine idan ban manta ba Ummi ta faɗa mana sai da tayi shekara bakwai ana
takwas ta samu cikin J ɗina.

Tace mana a randa ta cika Shekara tara ta haifi Jameel dan haka kema ki kwantar da hankalinki, in sha
Allahu Babu abinda zai faru sai alkhairi kinji ko My dear”.

Ya ƙare maganar cikin kulawa a matsayinsa na babban yayanta.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan Yah Moddibo yana iya amma dai ku sani a addu'a Allah ya kawo min masu albarka ”.

“In sha Allahu zakmu yita Miki addu'a ”.

Sai kuma ta juya jin Khausar na cewa.

“Kima kwantar da hankalinki daga Yaye in kawo Miki Keyah shikenan zan bar miki ɗanki”.

Murmushi tayi tare da kallon Moddibo tace.

“Allah dagaske Yah Moddibo zaku bani?”.

Zamansa ya gyara tare da cewa.

“Toh me aciki Asma'u ɗana ai ɗan kine, kuma ɗan Khausar ɗan kine”.

Cikin jin daɗi tace.

“Toh Allah ya raya mana shi da Imani ”.

Atare suka amsa da Ameen ya hayyu ya ƙayyum.

Haka dai ranan sukai ta hiransu suna bata ƙarfin guiwa sai karfe 12 suka tafi.
Bayan wata biyar Khausar ta yaye Keyah kana ta kaiwa Asma'u kamar yanda ta mata alƙwari satinsa
uku agidan Asma'u ya saba da yaye ya daina tambayar Nono.

Inda ya zamana mafi akasarin zamansa a tsakanin su koda Moddibo ya matsa aje a ɗauko sa Khausar
zata danne sa akan abarwa Asma'u.

Bayan Yaye Keyah da wata Uku Allah ya sake baiwa Khausar wani cikin.

Bayan shekara watannin tara da kwana tara ta haifan ɗa namiji aka sa masa sunan Abualeey Youseef ana
kiransa da Ayman haka ranan sunansa aka ta biki da hidindimu bayan ta haihu da wata biyu matar
Ibraahim ma ta haihu hakama Dija da Asiya da Matar Yah Abba duk sun haihuwa, Ameena ma ta haifi
ƴan twagaye duka maza, Samira Sani ma ta haifi yarta mace Masha Allah itama Khausar ta kuma
haihuwa Uwar ƴaƴa maza.

Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya akwana a tashi asarar mai rai.

Keyah yana da shekara takwas Ayman nada shekara shida sun girma sunyi kyau gwanin ban sha'awa
sunyi kuɓul-kuɓul dasu zuwa lokacin ƴaƴan ta maza Uku Keyah, Ayman, Haiydar mai shekara huɗu daga
nan bata sake haihuwa ba sai yanzu da take rainon ciki na huɗu wanda yama ɗan girma.

Ahankali Khausar dake zaune a babban Falonsu na ƙasa ta ɗan ɗago kanta ganin yaran na sauƙowa daga
matakalan Benin Keyah na gaba Ayman na biye dashi Jikinsu sanye da wani Gezner Fari ƙall ƙafafunsu
sanye da half covel golden color na maza mai masifar kyau yayin da kansu ke dauke da hula Zhanna
bukar blue mai ratsin fari daya dace da kayan jikinsu sosai sukayi nasifar kyau tamkar ka sace su ka gudu.

Anutse Moddibo da shigowar sa kenan daga Fada ya durƙusa tare da buɗe musu hannayensa alamar
suzu ya rungumesu.

Da gudu yaran suka rungumesa.

Sai kuma suka maida kallonsu kan Ibraahim kana suka haɗa baki wajen cewa.

“Uncle Ibraahim mun gama”.

Ibraahim dake riƙe da ƴa mace Kyakkyawa mai suna Mifra wacce bisa alamu ƴar sace da sauri Ayman
yace.

“Mifra Oyoyo zo?”

Da sauri tazo ya rungumeta sai kuma suka kalli Moddibo dake cewa.

“Ina zakuje?”.
Keyah na Murmushin yace.

“Zamu tafi gidan Ummina”

Kasancewar da Ummi suke kiran Asma'u.

Yana murmushi yace.

“Toh ku gaida Ummin ku” ya ida mgnar yana kamo hannun Haiydar dake ƙoƙarin kwanciya a jikin
Khausar yace.

“Tashi kuje kaima”.

Cikin lingwaɓar da kai yace to kama ya miƙe.

Kai suka gyaɗa kana suka fice tare da nufar gidan Asma'u.

Suna shiga gidan suka sameta kwance a falo ta lulluɓe jikinta da bargo tana rawan sanyi cikin sauri da
kulawa Keyah ya ɗaura hannunsa kan Fuskarta tare da cewa.

“Ummina meke damunki?”.

Cikin alamun zazzaɓi da rawan jiki tace.

“Zazzaɓi nake ji Keyah”.

Da damuwa atare dashi yace.

“Uncle ya sani?”.

Kai ta girgiza tare da cewa.

“Bai sani ba ɗazun ne ya fara min”

Cikin sauri ya juya gudu kna yace.

“Bari naje na faɗawa Uncle Ibraahim yazo ya ɗauke ki mu tafi asibiti”.

Ya ƙare maganar yana fita dai-dai lokacin kuma Ibraahim ke reverse ɗin motar yana shirin fita cikin ɗan
ɗaga murya yace.

“Uncle Ibraahim ka tsaya”.

Ahankali Ibrahim ya tsaya cikin damuwa Keyah yace.

“Ummina bata da lafiya Uncle Ibraahim ka Kaita asibiti”.

Kai ya gyada tare da cewa.


“Toh”.

Kana ya yayi Parking tare da zaro wayarsa ya kira Dr Jameel ya sanarmasa.

Shi kuwa Keyan da gudu ya koma cikin gidan hannunta ya kamo tare da cewa.

“Ummi tashi mu tafi asibiti”.

Ahankali ta gyada kai tare da miƙewa ta gyara mayafinta.

Kama ta tasasu a gaba duka fita.

Tun suna mota ta kira Dr Jameel ta faɗa masa gasu ahanya Ibraahim ya kawo mata yara yanzu zai
kawota asibitin nan yake cemata ai Ibraahim ɗin ya gaya mishi.

Suna isa asibitin Dr Jameel da kansa ya karɓeta kana yayi mata duk gwaje-gwajen daya kamata nan yaga
ashe tana da ciki har na tsawon uku batare da sun sani ba cike da farin ciki ya ɗagata sama ya riƙa juyata
kafin ya sauƙeta cikin matsanancin farin ciki yace.

“Sweetheart albishir”.

Tana ɗan lumshe Idanunta tace.

“Goro”.

Wani kallo ya mata still fuskarsa ɗauke da Murmushi yace.

“Wani kalla”.

Ɗan ware idanunta tayi da kuma yanda zazzaɓin ya fara sauƙa tace.

“Fari ƙall”.

Sake rungumeta yayi kana yace.

“Ciki ne fa dake Sweetheart?”.

Cikin mamaki da wani irin farin ciki data kasa tantance yanayin da take ciki tace.

“Ciki?da gaske?”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.

“Wallahi da gaske Sweetheart kina ɗauke da cikina ajikin cikin da muke muradi da mararin samu”.

Ahankali tace.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un?wata nawa?”.


Cikin farin cikin daya kasa ɓoyuwa asaman fuskarsa yace.

“Har wata uku fa”.

Da wani irin sauri ta ɗauki waya ta kira Ummi Ummi na ɗagawa tace.

“Ummi Ummi ina da ciki har na wata uku”

Cike da matsanancin farin ciki da jin daɗi Ummi tace.

”Alhamdulillah³ nayi farin ciki Ubangiji Allah ya raba lafiya kice na kusa zuwa”.

Murmushi Asma'u tayi kana tace.

“Yawwa Ummi dama kin daɗe baki zoba tun sunan Ayman baki sake zuwa ba dan haka kima fara shiri kin
kusa zuwa”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh Allah yakai mu da lokacin rai da lafiya”.

Ameen ta amsa tare da katse kiran ta kira Khausar ta sanar mata murnan da Khausar tayi ba a cewa
komai.

Ummi na gama waya da Asma'u ta kalli Bashir da Haiydar dake zaune gabanta wanda zuwa yanzu sun
zama manyan Samari sun mallaki hankalin kansu.

Wanda tuni an gama maganar Auren Raudat da Bashir.

Haiydar kuma ya auri ƴar Aunty Ruƙayya.

sosai sukayi farin ciki jin Asma'u nada ciki kana atake awajen suka kirata suka tayata murna...

Zuwa yanzu kuwa Khausar ta haife cikinta, an samu ɗiya mace, ansa mata sunan Didi suna kiranta Eeman

Bayan watanni Allah ya sauƙi Asma'u lafiya ta samu ƴa mace wacce taci sunan mahaifiyar Dr Jameel
A'isha suna kiranta Ishmah.

Anyi suna lafiya an gama Alhamdulillah Ummi da Mommy sunzo wajen suna.

*BAYAN SHEKARU ASHIRIN*


Alhamdulillah ƴaƴan su sun girma sun mallaki hankalin kansu an haɗa Auren Keyah da Ishmah ƴar
Asma'u.

Sai Ayman da Mifra ƴar Ibraahim.

Alhamdulillah Raudat ma ta haifi ƴaƴanta mata biyu duk sun girma Hakeem ɗan Lalla Hafsat ya Auri
Fatma ƴar Dija Haiydar kuma ya Auri Ruƙayya yarinyar Rahama.

Alhamdulillah rayuwa ta cigaba da tafiya tamkar yanda ake buƙata.

Bayan anyi biki an watse.

Ahankali Khausar ta shirya cikin shiga ta alfarma sai baza ƙamshi take sanye take cikin wasu tausasan
rigar bacci masu masifar kyau da santsi idan ka ganta zaka yi zaton yau akayi Aurenta duk da cewa sun
Aurar da ƴaƴan su amma tana da kyakkyawan jiki wanda Babu wanda zai ce ita ta haifi wannan yaran ga
autarma Eeman an zama manyan ƴan mata wacce ba abinda ya bari na mahaifiyarta har rawan kan.

Anutse ta tura ƙofan bedroom ɗin ta ta shiga idanunta suka sauƙa akan Moddibo daya sake zama
magidanci baza kayi zaton ya wuce 45years ba saboda kyawun jikinsa nutsuwa, jin daɗi kwanciyar
hankali sun sake wanzuwa acikin rayuwarsu yana ganinta ya buɗe mata hannunsa anutse ta ƙara sa
tsakiyan tare da faɗawa jikinsa ya mata wani Amintaccen runguma ahankali yake cusa yatsun ƙafansa
aƙasan nata ganin haka yasa ta ɗaura ƙafafunta asaman rumfar ƙafansa anutse ya riƙa tafiya da ita har
yaje bakin kofa yana isa ya rufe ƙofar saurin kallonsa tayi tare da cewa.

“Yah Mu'allim ya zaka rufe ƙofa”.

Goshinsu ya haɗe waje ɗaya still ƙafafunta na kan nasa yace.

“Um Minha Vidaa (My life) rufe wa zamuyi saboda kada _Aysha Aliyu Garkuwa_ ta shigo ta samu abin
rubutawa Fan's ɗinta”...

Acan gidan Dr Jameel kuwa Asma'u ce zaune tare da ƴaƴanta wa'anda ta haifa bayan ta haifi Ishmah
ƴaƴa maza guda biyu wanda ɗaya an yiwa Moddibo ta kwara suna kiransa da Moddibo sai takwaran
Abban Jameel suna kiransa da Abba ahankali tace.

“Yah Moddibo”.

Anutse ya kalleta cike da girmamawa yace.

“Na'am Ummina”.

Tana gyara zamanta tace.


“Yaushe zakaje Nigeria ne?”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Ummi kwanan nan dai nake son zuwa amma nafi son mu tafi da Abba idan ya gama exams ɗinsa”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Toh ba matsala nima dama nayi kewar Ummina idan yaso zamu tafi tare”.

Dr Jameel dake gefe yai mata wani kallo mai cike da so kauna yace.

“Nima ɗin dani za'a je saboda nayi kewar Abbana da Ummina”.

Hira suka cigaba dayi mai cike da farin ciki da ƙaunar junansu...

Acan bangaren Ibraahim rayuwa tayi musu daɗi da matarsa.

Haka bangaren Asiya ma Alhamdulillah rayuwa na tafiya cikin farin ciki da kwanciyar hankali ɗan ta ya
Auri ƴar Amina da suka haifa da tsohonta...

Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya hankali ya kwanta ya kowanne ɓangaren...

_TAMAT BIHAMDULILLAHI..._ Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Na godewa Allah daya


bamu aron rai da lfy da lokaci da dama ya nuna mana forkon littafin nan lfy tare da aramana daman
ganin ƙarshensa lfy dani daku masu karatu. Toh Alhamdulillah. Yah Allah mun gode maka, muna kuma
neman yafiyarka da gafararka da rahamar ka, Yah Allah ka yafe min kurakuran dake cikin wannan littafin
ka shafe zunubaina kayi min gafara da rahama da jinƙai dani da masu karatu. Abinda mai dai-dai Ya Allah
ka haɗamu a kan ladan, ya Allah ka nuna mana forkon wanda zan fara lfy da ƙarshensa duk lfy, ya hayyu
ya ƙayyum kasa al'ummar Annabi su amfana da alkhairan dake cikin littatafai na ka tsaresu da sharrin
dake ciki.

*Yafiya! Yafiya!! Yafiya!!!*

*Ina mai neman yafiyarku makarantan littatafai na, mace ko namiji babba ko yaro wacce muka taɓa mgn
da ita da wacce bamu taɓa mgn da ita, na kusa dani dana nesa. Wala Allah akwai abinda nai Miki ko nai
maka ko cikin rashin sani ko ajizanci ko kuma yanayin gajiyawa da raunin ɗan adam ki kuma yanayin ɗan
fusatan lissafi ko gaza danne fushi, Ka! Ku! Ki! Haƙuri ku yafe min, kuyi min azurun na fama da yawan
jama'a, ni na yafewa duk wacce taimin abu cikin rashin sani, Amman wlh ban yafewa masu fitarmin
littafina su tura a wasu groups ɗin ba domin misali ka bawa ɗan uwanka mutum ɗaya biyu wannan da
banner da turawa a groups mutum dari ko sari biyu ko uku ku dari hudu ai wannan kai kankama kasan
me sunanka madadin samun wani suyi Murmushin group a kuma kwashi zunubi*

*Littafin Sakayya dai kowa ya sani na kuɗine, in ma kin ganshi a wani wurin to na satane kika karanta 1k
ne kacal, 0661110170 GTBANK Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyanki ta Whatsapp number
na 09097853276. In tura Miki littafin complete Kisha karatun ki ba haƙin kowa a kanku*

*Gareku masu son kayan mata ko turarukan wuta da kulacca da su Humra a wannan no ɗin ne zakuyi
min mgn 08069423567 in kuma kuɗi zaki tura to ta account in na na Jaiz bank zaki tura. 0005388578 Jaiz
bank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta Whatsapp number na na 08069423567, in
haɗa Miki kayanki in tura Miki shi duk state da kike nama lfy fata lfy*

You might also like