Kuskure Na by Feenerh
Kuskure Na by Feenerh
_*KUSKURE NA*_🙆
_Love & Destiny_
*Written by Fenerh*
✍✍✍✍✍✍✍
*GOLDEL PEN WRITER'S ASSOCIATION*
✍✍✍✍✍✍✍
❄_We are bearers of sooo golden a pen We write assidiously percieven no pain Sooo
magical Our creative golden pen Be hold our words A product of our pen Savour our
words, for it will cause you no pain_❄
********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery,
Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from
our blog.
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa
novel ko kuma post.
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search
na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
_Am back again my fan's , da fatan anyi Salla lfy ina Addu'ar Allah ya karbi ibadun
mu Albarka cin Annabi da Al Qur'ani Ameen_
_"Kamar koda yaushe Na kuma dawo muku cikin wani sabon littafi Na mai suna
KUSKURENA Wanda yake kunshe da zazzafar soyayya da kuma kaddara, dukkan cikakken
musulmi dole ya dauki kaddarar rayuwar shi mai kyau ko Mara kyau sai dai muce Allah
ya bamu i kon cinye namu jara bawoyin Ameen'_
1➡1⃣ 1
"Ummu Ummu""""' shine kiran da yayi sanadi yar farka warta da ga d'addad'an baccin
da takeyi mai cikeda mafarkai masu dad'in gaske'
"Cikeda shagwaba tace " kai Hajiya yanzu bazaki barni inyi baccin ba bayan jiya
dak'yar mutanen ki suka barni na runtsa"
"Hajiyar tace " ke wai bakya gajiya da bacci ne A rayuwar ki Ummu? Ta turo dan
bakinta "Hajiya Ummu Ruman meye wani Ummu? Bawani dadi Kamar tsohuwa'
" toh naji yanzu dai kitashi ki shirya ko bazakije maka rantar bane yau?
"wani irin zaburowa tayi Kamar zata tun tsira tunawa da yau tanada lecture karfe
bakwai kuma lecturer din ba mutunci ko kadan'
" Ta dubi a gogo ' na shiga uku Hajiya kika ki tashina da wuri gashi zanyi latti.
" sarkin mita yanzu inace cewa kikayi bana son ki huta ?
"Nidai ki zabomin kaya kafin in watsa ruwa ta cire hijabin dake jikinta ta wurgar
tareda kwasawa a guje tayi waje Hajiya na faman cewa'
" kinsan Akwai jama'a ko idan wani ya ganki Kamar diyar arna fa Gaki tubarkalla
duwaiwai Kamar masaki 'daga wajen tace " wurin ki na gada ai keda ke tafiya dakyar
saboda kiba'
"Nagode kya fito ki zabo kayanki shiryayya ' bata dai fitaba ta zabo mata Riga da
zani shiga dai ta hausawa tareda hijabin da zai shiga da kayan ta fara gyara mata
gadon tareda nannade hijabin data wurgar a kasa
" A guje ta shigo daure da towel Wanda ko haduwa bai gama yiba a kirjinta " Hajiya
tace " Amma Ummu kun raba hanya keda kunya ' yanzu a haka kika ratso tsakar gidan
nan?
"Idan wani ya ganki fa kuma kinsan gidan mu kowa shigowa yakeyi tunda ina Sana'a'
" toh ni ina ruwana da mutane nida gidan mu zanrika kame kame' ""aa Ummu gidana dai
gidanku ai kinsan inda yake'
" Ni dai nan ne gidan mu tunda gidan kakata ne mai sona " ta rungumota cikeda so
irin na jika da kakan da suka shaku '
"Cikin minti da bai wuce biyar ba ta shirya tareda daukar Jakarta ta rataya ta kuma
zura hijabin ta
Hajiya ta zaro kudi a gefen zaninta ungo ki hau achaba Allah ya tsare ki daga
sharrin mutum da Aljan
Ta karba tareda godiya bata tsaya wata kwalliyaba mai kawai ta shafa tadan murza
powder tafito abinta shar Kamar ba jami'a zata ba takalminta plat ta zura tafita
cikeda sauri duk da tasan tayi latti batason lecture ya wuceta'
"A kofar gidan kuwa mutane ne dankam masu jiran Abinci kasan cewar sana'ar kakar
tata kenan wadda da ita suke samun rufin Asiri kuma Allah yasa ma lamarin ta hannu
komai basu nema sun rasa ba'
*JIGON LABARI*
Hajiya kaka mai Abinci tsohuwa ce da Allah ya jarabceta da haihuwar da daya tilo
Wanda shine mahaifin Ummu Ruman Wanda mahaifin shi yarasu tun yana karami Hajiya
kaka ita tayi ta dawai niya da danta batareda gazawa ba tayi wani Auren bayan
rasuwar mijinta Wanda suka dauki kusan Shekara Ashirin batareda ta kuma haihuwaba
har Allah ya dauki ranshi shima A lokacin ta Aurar da tilon d'an nata hadin zumunci
ne da y'ar kanwarta wadda itama Allah ya dauki rayuwarta a sanadiyyar haihuwar Ummu
Ruman '
Sunji mutuwar baiwar Allahr nan sosai kasan cewarta mace mai hakuri domin mijinta
yayi Alfahari da Aurenta mace mai tawakkali da kaunar mahaifiyar shi'
Alhaji Muhammad saida ya dauki shekaru kafin ya kara Aure don gaba daya kaurace ma
Garin nasu yayi wato Zaria ya koma Kaduna da zama yaci gaba da kasuwancin shi kafin
daga baya ya samu wata mata sukayi Aure A halin yanzu yana da yara kusan biyar
tareda ita
"Tun lokacin da Alhaji Muhammad ya Auri bilkisu komai ya canja A rayuwar Hajiya
kaka don gaba daya mantawa yayi daita da tilon marainiyar y'ar shi,
A dole ta mike tafara Sana'a domin cikawa jikanyar ta burin ganin tayi karatu mai
zurfi,
" Hajiya kaka tana zaune ne a layin Banaden dake kusa da kwango A cikin tudun wadan
Zaria
Gidane mai dan girma irin na talaka mai daukeda da kuna kusan goma Wanda take zuba
dalibai suna biyan haya Amma dakunan duk suna kallon waje ba sosai sukan shigo
cikin gidan ba kasan cewar su dalibai sukuma suna zaune a ta cikin gidan mai
daukeda ciki biyu da falo Wanda daya Ummu Ruman ke zama daya kuma na Hajiya kaka
Ba laifi komai suna samu najin dad'in Rayuwa da sana'ar Abincin da takeyi tanada
tsofaffi masu tayata yin komai suma tana biyansu
Arayuwa Ummu Ruman ta tsani wannan Sana'a ta Abinci domin irin kattin dake taruwar
musu akofar gida wai su suna siyan Abinci saboda Akwai runfa an jera kujerun katako
tako ina Kamar wani restaurant
"A kullum Addu'ar ta tazama wani Abu idan tagama karatu ta taimaki y'ar kakarta
Ummu Ruman yarinyace mai diri chocolate colour mai tsada tanada dan tsawo fatar ta
sumul sumul Kamar mai Rayuwa a cikin A.c ga wani dimple mai zurfi Wanda ko motsa
bakinta tayi sai ya zurma kyakkawa ce tubarkalla wadda mafi yawan cin kawayenta ke
kiranta da African Queen saboda kalar fatar ta mai sheki,
" Tayi karatunta a zenith primary & secondary dake unguwar kaya cikin ikon Allah
tasamu sauke qur ani kafin ta fara zuwa F.c.e Zaria
Abu biyu yake ci mata tuwo a kwarya A rayuwar ta rashin kulawar mahaifinta da kuma
rashin mijin da zata iya Aure ita kadai tasan irin damuwar datake ciki bawai ta
rasa masu sonta bane aa ita kawai har yau bataga irin mijin datake buri bane don
ita Sam ta tsani Auren karamin yaro gwara dan talatin da wani Abu zuwa Arba'in
"don gani n take yi tafi karfin karamin yaro ita kam shiyasa duk Wanda ya nemi
kulata bata bashi fuska Sam saboda gudun raini
" Damuwar ta babbace domin Allah ya jarabceta da muguwar jaraba wadda ba kowace ya
mace bace zata' iya daurewa ba ta kuma kame kanta musamman ita dake goyon kaka Ummu
nada tsananin kula da kuma kiyayewa domin tana gudun Abinda zai janyoma kakarta
shiga damuwa,
Karfin feelings dinta bai janyo mata fadawa cikin halaka ba saima kara kusanto ta
da ubangiji Wanda a kullum take kokarin yin Azumi tareda Addu'ar Allah ya yaye mata
wanna damuwar da ba maiyimata maga ninta sai Allah
"wann matsalar ko Hajiya kaka bata San ta da itaba domin duk rashin kunyar datake
nuna mata bazata iya bari tasan wannan ba'
*Cigaban labari*
Allah ya taimake ta har ta isa bai shigoba tafada cikin kawayenta masu faman kwala
mata kira Queen"""
"Daya daga cikin su wadda duk kusan sa anni ne da Ummu duk bazasu wuce Shekara
Ashirin ba mai suna hajara tace " kai guys yau naga wani lafiyayyan yaro under
twenty ya jiku da kudi da kuma tsantsar kyau kana ganin shi kaga Hutu da kuma
class ina fada muku gayen first class ne wlh kai banma tunanin bahaushe ne dan
nijeriya ,
"Gaba dayansu suka juyo domin jin zancen saurayi dan karami mai kuma kyau da kudi
suna rige rigen tanbayarta " kai Sumy A ina don Allah ita dai Ruman juya musu baya
tayi don basuda zance saina kana nan yara masu sauke wando a duwawu'
"Kudai kubari wlh a kofar shigo wata nan naganshi ya tsaya a jikin wata Arniyar
mota harda body guard dinshi kai wallahi yaron ya hadu ban Masan irin kwatancen da
zan muku ba gashi a lambar motar an rubuta *J 3* wlh nayi karshen gani yau"
"Shigowar malamin yasasu yin shiru domin baya wasa ko kadan suka fara daukar
lecture
" Ana gamawa ta mike cikin sauri domin tasan halin kawayen nata basuda aiki sai
zancen kananan yara bare sun samu sabon labari yau ai ba sauki
Tana fitowa taga duk su napep din sun ciccika gashi da yake Antashi ko ta ina ba
mashina gudun kar su kuma biyota da zancen yasa tafara takawa tafe take tana
nazarin Rayuwa da kuma damuwar ta kanta a kasa tafara jin kanshin wani Azababben
turare
Batareda ta damuba taci gaba da takunta still kamshin na karuwa bata damu tasan ko
na wayeba domin tasan tana kusa da Congo Akwai dalibai kala kala yayan masu da shi
'
"Dady pls I don't want to stay in the hotel'and pls Dady tell ur body guard to stop
following me I don't like it
" Taji wata irin murya mai dadi tana fada tasan kuma a waya ne ake maganar haka
kawai taji tanason ganin mai muryar domin muryace mai dad'in sauraren
"Tana dagowa tayi saurin dauke kanta domin ganin exact gayenda hajara kebada
labarin kamannin shi dazu ta ya tsina fuska saboda tana ganin shi tasan yarone
saidai ace girman Hutu da kuma jin dadi '
Tayi wucewarta batareda ta kuma wai wayo shiba shikuwa saida ya katse kiran domin
irin fuskar da ya gani a kusa dashi irin fuskar da yake mafarki a kullum take
hanashi sukuni har tayi sanadi y'ar barowar kasarshi zuwa nan ko zai samu matsuwa
fuskar da sanadinta yafara balaga yau a gabanshi ""
Wani irin juyowa yayi "Amma me bai ga koda inuwar ta ba ta bace bat
" wata irin razana yayi tareda bugawa bodyguard din dake kusa dashi tsawa " ware is
she???? Yafada cikin karaji'
"Who are you talking A bout? "My dream girl " she is here right now we're did she
go?
Ya buga musu tsawa ""find her 'tareda dafe kamshi ya jefar da wayar hannun shi
hankalin shi yayi mugun tashi '
" Haka suka gama dube dube suka hakura don ta bace musu bat cikin motarshi yafada
tareda dafe kanshi dake mugun bugawa "shikadai yasan halinda zuciyar shi take ciki"
"Umma kuwa mashin ta haye batareda bata lokaci ba yakarasa da ita gidan su'
" tundaga nesa tafara hango jama'a a kofar gidan su ranta yafara baci domin itadai
ta tsani sana'ar abin cin nan gashi ba halin ta wuce sai sun samata idanu"
"Daga nesa ta sauka ta sallami mai mashin din sannan ta karasa kanta a kasa
batareda ta kalli kowaba tayi shigewar ta cikin gidan"
"Cikin ma masu Aikin Hajiya kaka sunata hidimar sallamar mutane suka fara gaishe
ta'
" Cikin falon kawai ta fada ta samu Hajiya nata kirgar kudin cinikin ta gefen ta
kuma wani kaninta ne da Ake kira magaji dan uwanta ne na jini duk wani Abu shi
yake yimata itama tana taimakon shi sosai"
" Kamar kinsan yunwa nakeji wlh banci komai ba yau a makaranta" ta bude kular ta
fara cin Alkubus dinta datake bala in kauna'
"Hajiya tace " magaji yanzu dole sai an hade mai da kuna biyun zai zauna? eh yaya
kawai ki y'arda tunda ga dan fili har bayan gida sai Ayimin taciki na fada miki
bature ne ba karamin kudi zai saki ba "
"Tunda kinga su kulu zasu tashi sai a hade ginin kuma bako kwandalar ki " toh
magaji Allah ya taimaka na Amince"
"Ita dai Sam bata fahimci me suke fada ba ' Abincinta kawai takeci don bata wani
son yin magana da magajin'
" Sai bayan tayi Salla tayi wanka tareda zura yar wata doguwar Riga mai Kamar rigar
bacci don mugun zafi takeji yau ta sanya hular net a kanta domin kan yasha iska don
ta jikoshi da ruwa bai gama bushewa ba"
"Ta karaso kusa da Hajiya " wai ni kaka me Magaji ke magana akai?
"Kedai wai wani bature ne ya nace inbashi hayar daki biyu yanaso ya zauna nadan
lokaci ba yason zaman hotel" kuma zai gyara da kanshi ni banaso kinsan magaji da
naci da kuma shegen son kudin tsiya "
"Kudai wallahi bazaku bar mutane su hutaba yaushe muka samu muka kori inya muri
yanzu kuma bature "?
" Shima idan yace zai mana rashin hankali ai dole yabarmin gidana "
"Shiru kawai Umma Ruman tayi domin Abin nasu yafara isarta daga wannan sai wannan"
"Washe gari kam da wuri ta tashi ta yi musu gyare gyaren dakunan su don ba ruwanta
da tsakar gidan don Akwai masu Aikin Abinci ga kuma yan hayar Hajiya
" Tayi wanka ta fito tsab tareda karbar kudi wurin Hajiya sannan ta wucewarta
F.c.e'
"Yauma daga isarta kawayen ta suka fara tarar ta da zancen wannan saurayin " tayi
kicin kicin " Kudai wlh kunaban kunya dan wannan yaron ne kuke wa wannan rawar
jikin?
"Ke yaro da kudi babbane Nidai na mato wlh " inji hajara "Sumy tace " nima dai tun
banganshi ba naji a gaskiya ya burgeni kinsan ni da kaunar sabon jini "
"Allah ya kyauta soyayya da kana nan yara ko raini nifa wlh natsani kula jarirai "
suka sheke da dariya harda tafawa "hajara tace " wlh ki bar raina Allura karfe ce
ke baki karanta littafi da nace kije ki karanta labarin namiji baya kadan"
"Na Aisha Ali garkuwa kiji Aikin yara " Kudai kula sani da yawarku baruwana da
shirme "
"Yau kuwa suna tashi suka ce binta zasuyi domin suna son suci Abin cin Hajiya kaka
dama hakan sukeyi wani lokacin " Sumy tace Hajara kinsan bazata hau motar ki ba
muje ta same mu
"Tace toh gobara yau zan hau muje kawata " baki suka saki gaba dayan su suna kallon
ta domin tun tsawon zaman su bata taba y'arda ta hau motar kowace kawa"
"Kuma yanada nasaba da irin hudubar Hajiya da kullum take fadamata ta kiyaye bin
yaran masu maiko don gujewa wulakanci Amma a gaskiya. Ta fahimce hajara na matukar
kaunar ta sosai'
" Hajara iyayenta masu haline sosai mahaifin ta na aiki a karkashin matatar mai
dake Kaduna wato NNPC Allah ne ya hada kaunar su da Sumayya da kuma Ummu Ruman,
Sumy itama ba laifi mahaifinta dan kasuwa ne sunada nasu rufin Asirin '
"Suna isowa kofar gidan ta bude ta fito Sumayya ma haka hajara ce ta karshen gaba
daya sa idawan kofar gidan Hajiya suka watso masu ido suna mamakin daman kawayen
wannan mai girman kanne?
" Sudai wucewarsu sukayi cikin gidan suna tafe suna raha irin ta kawaye,
Wani daga cikin yan zaman kashe wando yace " a gaskiya Allah yayi halitta a nan
kasan saboda kawai inrika ganin Babyn nan nake zama kofar gidan nan'
Shima na kusa dashi yace wlh nima haka nifa ganinta kawai ya wadatar dani can ma
wani yaci "ai Hajiya ta ajiye Diamond wlh irin wannan kayan ai mutum dole ya huta
" Kaifa dan iska ne ina zaka kai wannan mai girman kan tsiyar wlh ko iya tunkarar
ta bazakayi ba domin Allah ya mata kwarjini da yawa'
Anan dai sukayita surutan su sukuwa sunkule cikin dakin Hajiya sai kwasar gara
sukeyi don Abin cin gargajiya yayi a Rayuwa'
"Sunata zabga shaftar su " Hajiya na gefen su tana dariya domin tana kaunar su har
cikin zuciyar ta don suna son tilon jininta Hajara tace " kakus don Allah Kice
Ruman taje gidan mu '
"Saidai mu muyita zuwa Amma ita bata taba leka gidan mu ba " toh Kuyi hakuri kawar
takuce murdaddiya kunsani sai hakuri
"Toh Nidai Hajiya yayana zai dawo daga America next week wlh dole tazo domin zamu
hadamai walimar kammala karatu nshi idan bata zoba zanyi fushi da ita
" toh ai kunfi kusa nawa idone, saida suka yi kat suka sauke farali Ruman ta
rakasu suka wuce domin Sumy na kofar doka ne ita kuma hajara GRA saita sauke Sumy
zata wuce gida"
"J kuwa Kamar yadda nagani a jikin motar shi yau ma ya dade a wurinda yaga dream
girl dinshi jiya Amma har yamma shiru haka dole ya hakura ya kara gaba tareda
damuwa mai tarin yawa
" Domin jiya baiyi bacci ba kwana yayi yana tunanin fuskar ta da yagani a fisge
tafi kyau a reality she is damn beautiful ya dafe saitin zuciyar shi yana mai hango
tsantsar kyanta da yagani ga wani kallo data aikomai mai tsaya wa a zuciya'
Juyi kawai yakeyi yana dafe cikin shi Wanda yazamar mai farilla a duk lokacin da
zai tuna dream girl dinshi "
Bayan kwana biyu an gama gyara ko ina na gidan Hajiya kaka ita kanta mamaki takeyi
waye wannan yake hasarar kudin shi shida ba dadewa zaiyi ba"
An baza tile's har tsakar gidan hardasu A.C ga wata solar da suka wani kafa gudun
matsalar nefa Ruman ma cewa tayi hasa rarre ne kowaye '
"Yau da wuri suka tashi kasan cewar jumu'a ce tana sauri ta sallami su hajara domin
tanaso ta danyi shopping a inna idea shopping complex Hajiya ta bata dubu biyar
"tundaga bakin plaza din taga wasu motoci a Jere guda uku masu matukar daukar ido
farare tas bata kuma bi takansu ba ta shige wajen Cosmetic's Tafara siyan
turarukanta da kuma manta a kullum'
Ta gama ta biya tareda daukar ledarta ta fice " kanta a kasa take tafiyar ta domin
ta tsani hada ido da mutane don ana yawan fada mata wai idanunta na daukar hankalin
mutane'
"Jin kawai tayi tayi karo da mutum har ledar ta tafadi kasa " cikeda masifa ta dago
tafara zazzaga balai "
"are you blind? Kuna tafe bakwa kallon gabanku sai shegen kallon mata tun baku
tafasa ba zaku kone gari' tunda tafara magana bakinta kawai yake kallo da gefen
kuma tun ta dake lobawa ga sexy eye's dinta har wani sheki sukeyi gaba daya ya
shagala da kallon ta
" Har ta duka ta kwashi kayanta tayi gaba bai dawo hayya cin shiba "wani irin
firgita yayi ya fisgo numfashi tareda waiga wa yau ma Kamar walkiya ta bace'
Ita kuwa tagane shi sarai shine mutumin hajara kuma w'anda tagani ranar nan " mai
shegen kallo ta yi tsaki mtswwww ......✍
_*MATAR SOJA*_
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
_*KUSKURE NA*_🙆
_Love & Destiny_
*written by Fenerh*
~Dedicated to~
All my fan's
✍✍✍✍✍✍✍
_GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION_
✍✍✍✍✍✍✍
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
2 2
➡2⃣
"Tunda ya fito yake waigen inda zai ganta Amma ko walkiyarta bai gani ba "
Cikin motar shi kawai ya fada tareda dafe goshin shi yana mai fitar da hawaye masu
zafi'
Saida ya dade yana jinyar zuciyar shi kafin kafin yabasu umarnin tafiya'
I pad dinshi ya bude tareda dialing number wadda naga an rubuta *Momy me*
"Tana received ya saka mata kuka gashi suna ganin juna da yake video call ya
kirata"
Wata mace nagani kyakkyawa duk da a cikin waya ne ina ganin ta nasan ta gama haduwa
tareda mallakar Hutu na garari"
"Kuka kawai ya saka mata kamar wani jariri " gaba daya rikicewa tayi tafara
tanbayar shi " what's wrong my baby??
"Why are you crying? Da kyar ya saita kanshi tareda furta" I saw her a gain Momy ""
"Then why are you crying ? "She is gone again momy I lost her again """
"Cikeda kulawa tareda karfafa mai guiwa take tausar shi da cewar kar ya damu zai
ganta "
*Ummu Ruman*
" Tana fitowa mashin ta haye ta wuce gida Abinta hankali kwance batareda tunanin
komai ba"
"Tana isa ta samu mutanen nata wato sa idawan unguwar kamar kullum ta shige warta
cikin gida batareda tace musu tak ba "
Masu Aikin Abincin Hajiya sai sannu suke yimata tana Amsawa, ta shige falo tasamu
Hajiya na sana'ar wato girga kudin cinikin ta"
"Tayi sallama tareda karasa wa da gudu ta rungume ta " ta manna mata kiss a kumayi
" I love you my kakus"
"Ta furta cikeda tsokana " aa Nidai dagani kar ki karya ni " da wannan manyan
katarorin naki da kika A jiye " tasa dariya "
"Hajiya hips ba katarori ba " ai ni banida jiki saidai diri mai kyau irin na kakus
dina "
"Tasa dariya cikeda kaunar jikan yar ta tace " to kiyi Addu'ar Allah ya rabaki da
idanun bata gari " don wannan karuwan jikin naki Ruman harma kin fini ai tubarkalla
"
"Shiyasa nake dinka miki hijabai banason fitan ki da gyale " nima bana sha'awar
gyale n ai "
"Ta fito da siyayyar da tayi ta nuna mata " Hajiya tace " sarkin turare kedai bakya
gajiya " ai kamshi yayi ne Hajiya "
"Toh ku naku ai zamanin daban namu da ban mu lokacin mu ai sai dan duwala kawai da
kuma miski yanzu kuwa turare har da,mai warin bunsuru"
"Ba Abinda takeyi sai dariyar wai warin bunsuru in banda sharrin Hajiya"
Cikeda kulawa tace " ke dai Ruman bansan irin kiba " tace me kuma nayi yanzu kakus
muna hira mai dadi"
"Yanzu a ce ko yar wayar zamanin nan baki ra ayin mallakar ta? " Hmm Hajiya mai
zanyi da waya ? Wazan kira ? Baban ki " shi idan ya y'arda ni ke banaso ki y'arda
shi'
"Ina so ki bashi hakkin shi na mahaifin ki nan take I don ta ya kawo ruwa domin
tasan Hajiya na cikin damuwar rashin kulawar yaronta"
"Tace Hajiya ki daina sa damuwa da izinin Ubangi " Baba zai zo ya ganki kuma ni
banida damuwa Sam tunda inada ke ban rasa komai ba sutura ko yar masu kudi bazata
nunamin ba saboda kintsaya min a Rayuwa "
"Ta kuma rungume ta " ina son ki kakata Allah ya barmin ke har inyi Aure ingudu
inbarki" cikin tsokana".
"Ta kai mata duka " matsa can Mara kunya tana zancen Aure in banda zamani "
"Haka sukayita raha a tsakanin su daga baya take bata labarin ai mai hayar su ya
tare "
"Dazu yazo yagai sheta yaro kamar baya taka kasa baki ganshi ba bature sak Amma
Yanajin hausa sosai" .
"Ta mike zunbur um " wallahi Saura kuma India tunda kinzauna da beyerabe kin zauna
da Igbo yanzu kuma bature to Saura Aljani "
"Ta kai mata duka ta kwasa daki da gudu ita da kayanta tana dariya"
"Tunda sabon mai hayan su ya tare bata taba sa shi a,idoba saboda ba wai damuwa
tayi da sha anin mutane ba"
Kuma gashi tana fita school abinta idan ta dawo bata zuwa ko ina kuma "
"Yau tun da ta tashi takejin cikin ta naciwo tun tana daurewa har ta kasa ta kira
Hajiya " gaba daya hankalin tsohuwa ya tashi ganin Ummu Ruman dinta na faman juyi"
"Bata tsaya bata lokaci ba ta kira magaji yasamo musu napep sai Asibiti "
"Kafin wani lokaci tafara fita hayya cin ta cikin gaggawa likita ya karbeta ya fara
bata kulawa "
"Sai kuka takeyi domin tasan damuwar ta tana tsoron kar likita ya gano yace zai
fadawa Hajiya ko magaji tanajin bala in kunyar hakan tafaru"
"Tayi sa'a kuwa ya bata magun guna " yanemi da su basu wuri zai yimata tanbayoyi "
"Ta dukar da kanta kasa domin irin kallon da yake aika mata "
"Hajiya Ummu Ruman " yakira sunan ta a natse yana mai binta da kallo da kuma wani
irin sihirtaccen murmushi "
"Kinsan kinada matsala? Tayi saurin dagowa tana mai zubamai idanu' eh that's means
kinsani"
"Meyasa bazaki nemi solution ba " nasan Hajiya bata saniba kuma a Al adar bahaushe
mace bazata iya kallon iyayen ta da irin wannan zancen ba"
"But u have to do something " kinada isashshiyar lafiya ' don haka Bawani Abu bane
"
"Kinsan cewa irin ki a cikin mata sunada wuyar samu " da Watace da tuni ta fada
sabon Allah "
"Bakida saurayi ne" tayi saurin kallon shi " saurayi kuma? " eh I mean boy friend
"ta girgiza kai " aa "
"Wata irin Ajiyar zuciya ya sauke " zan iya samun numbar wayarka?
"Banida waya ni' tafada atakaice domin ta matsu ya sallame ta " haba Hajiya Ummu
Ruman kamar ki a wannan zamani Bakida waya?
"Ba Abinda zanyi da itane " tafada cikin zakuwa " Hmmm ya janyo drower gefen shi "
wata sabuwar waya ya zaro ya mika mata " gashi Akwai layi a ciki"
"Ta dago kai tana mai kallon me yake nufi? " ina nufin ki rike a wurin ki zamuyi
magana " " wace irin magana kuma? Kedai ki karba'
"Aa nidai banason waya ta mike tsaye " zan iya tafiya? Toh ki taimaka ki gayamin
Address dinki'
"Gaba kawai tayi domin yafara bata haushi don ta gama ganoshi " ko ledar magun
gunan ta bata d'auka ba ta wuce
"Mikewa yayi da sauri ya d'auka ya biyota yasamu zasu wuce " yace ga maganin ta ta
kula da Amfani dasu akan lokaci ":
" Hajiya tayi godiya " tace magaji nemo mana keken toh "
Har ya juya yace " Hajiya bari inkaiku kawai ina zuwa " batareda ya jira amsa ba ya
koma ciki
"Nidai Hajiya bazan hau motar shi ba " kibani na mashin kawai ma hadu a gida" toh
saboda me? Mutum da Aikin shi ya ajiye saboda ya taimaka mana sai mu watsa mai kasa
a ido"
"Toh badani ba" ya fito tareda bude musu wata mota mai kyau Hajiya da Ummu suka
shiga baya magaji kuma a gaba
"Saita madubin motar shi yayi daidai saitin ta yanayi yana kallon kyakkyawar fuskar
ta yana tasbihi a cikin zuciyar shi '
" gaba daya ya gama bata haushi " shiyasa taki dago kanta " saboda yasan matsalar
ta shine zai nemi ya shige mata ' ko Anfada mai ita y'ar iska ce ?"zatayi maganin
shi kuwa"
"Suna tsaya wa Hajiya tafara koro godiya magaji ma nayi " tace Dan nan ka shigo
daga ciki kaji " Allah yayi Albarka "Ruman kuwa tuni ta shige ciki tana mai jin
haushin Hajiya"
"Har cikin falon su ya zauna masu Abinci suka kawo mai lafiyayye n tuwon shinkafa
da miyar Agushi " ya zake ya kwashi tuwo harda santin shi " A gaskiya zanrika zuwa
ina cin Abin ci kullum Anan Hajiya "
"Tayi dariya tareda cewa Matar ka fa' " Ai Hajiya ban da Aure kuma aiki ne yakawo
ni nan iyayena na Kaduna kuma sun dade suna damuna akan zancen Aure ban samu Matar
da ta dace dani ba sai yau "
" ina fatan Hajiya zaki bani jikar ki don bada wasa nake sonta ba ganin ta kawai
danayi yau naji nasamu iyali na nima"
"Hajiya taji dadi sosai har cikin zuciyar ta domin tana kaunar duk mai kaunar
Ummun ta " Allah yasa ku daidaita idan Matar ka ce "
"Toh banji sunan mijin nawa ba? Hajiya sunana Sulaiman Abubakar mahaifina dan
siyasa ne mu biyar ne a wurin mahaifin mu nikadai ne namiji sai kuma kanni na mata
guda hudu a halin yanzu ina cikin shekara biyu da kammala karatuna a India inda na
karanci Aikin likita"
Ruman dake kwance cikin dakinta tanajin zancen su sai taji ya burgeta kadan saboda
dama irin shi takeso bawai kananan yara ba under thirty "
"Don ita daga farko ta d'auka bai wuce shekara Ashirin da biyar ba saboda yanada
jiki mai kyau Ashe hutune ya boye shekarun kuma gashi kamar Fulani "
"Ba laifi ya hadu daga fuska har zuwa wankan shi har ma y'anda yake abubuwan shi
straight for word ba wata kwana"
Saida ya mata bayanin magun gunan sannan yace daga yau idan taji ciwo basai Ankawo
ta Asibiti ba kawai su kirashi yazo"
"Yace toh kuma nabata waya taki karba" kyaleta kaidai koni nayita fama da ita in
sai mata taki "
"Yayi dariya tareda karbar yar Nokia Hajiya ya yi plashing number shi yayi mata
serving "
"Yaron ya shiga ranta farat daya Haka suka sha hirar su harda magaji saida aka
nemeshi sannan ya tafi ".
" Cikin yan kwanaki kadan sukayi mugun sabo da Doctor Sulaiman kullum yana gidan
Hajiya idan yataso aiki "
"Mutu miyar ma ta dan fara sakewa dashi har suna dan hira idan har tana gida Amma
" taki bashi fuskar abin da yake nema wato soyayyar shi gareta '
"Yau tana zaune a falo tareda Hajiya suna hira Magaji yashigo tareda sallama" suka
Amsa ya dan fara zolayar ta " yau banga mutumin nakiba ?
"Hajiya ta Amshe zancen " wai likita? " eh. " yaje Kaduna yau wai Ana neman shi a
gida"
" tana gefe batareda ta tanka musuba ta mike zuwa cikin dakin ta"
"Yaya yau bature zai dawo fa. " bangane bature ba da waye a cikin dakin? Yaron shi
ne Ashe sai yanzu yake mun bayanin ogan na zuwa wai yadan yi tafiya ne "
"Toh Allah yakawo shi Sannan yanzu bana bukatar wasu masu hayar bayan shi sauran
dakuna biyun a barma masu Aikin surika zama a ciki"
"Kamar kullum kofar gidan na Hajiya kaka yana cike d'ankam da mutane " wasu masu
siyan Abinci wasu kuma yan zaman kashe wando "
Suna faman sana'ar wato tsegumin da suka saba' " wani yafara magana " ba_ba kwana
biyu banga Babyn nan ba ' dayan yace " kai ai kallo ya wuceka "dazu ma tafito "
wallahi kullum kamar ana kara k'erata "
"Ai kaidai bari " Wannan ta manyan yara ce " ina ma inama.......
"Maganar su ta tsaya ne dai dai lokacin da wata irin Arniyar mota ta kunno kai zuwa
kofar gidan " A tunanin su wucewa zatayi domin sun San duk mamallakin wannan motar
wani ne a Nigeria "
"Duk da kasan cewar duk Wanda yake Rayuwa a wannan unguwar yasaba ganin motoci kala
kala Amma wannan ta daban ce "
"Saida aka dauki mintico kafin mamallakin motar yabude ta " a hankali yake zuro
kafafunshi zuwa waje " wasu irin takalma ne irin na matasan yanzu sawu ciki farare
tas "
"Fitowar shi ya mugun fadar min da gaba don ni Kaina bankawo shi bane " yau ina
body guard din sukaje? Saboda tsegumi na da gudu naleka numbar motar domin gasgata
zargina"
*J5* na gani a jikin motar gaba daya Kaina ya kunce " me hakan yake nufi?
"Shi din ne kuwa Amma meya kawoshi gidan Hajiya kaka? Kaddai Ace shine zai kasan ce
a cikin wannan dakin da aka gyara ?
" Kara kallon shi nakeyi yana Amsa waya cikeda izza dakuma yanga kamar bayason
magana "
"Gaba daya gayun dake wurin sun raina Kansu duk da sun San cewar sun girme shi nesa
ba kusa ba Amma yaron yanada k'warjini da kuma cika ido ga kuma kare zance wato
masu gida rana"
"Suna ganin shi sun San cewar ba bahaushe bane kodai bature ko kuma balarabe " ya
karaso da earphone a kunne yana maganar "
"Wani mai shegen salo a cikin su yayi saurin cewa" Can I help u ? "Yace yes please"
Am looking for .... Saida ya kalli faskekiyar wayar hannun shi sannan yace " Hajiya
kaka" Hause,
"Cikin rawar jiki yake cemai ai ga gidan nan " jikin shi narawa yayimai jagora
kasan cewar gidane da kowa yakan shiga "
"Shikuwa yana kallon unguwar da kuma kofar gidan A zuciyar shi yake aiya nawa "
Anan zai zauna ?
"Cikin ya tsuna fuska yake takawa yana shiga cikin gidan " first ting da yafara cin
karo dashi shine wani Almajiri dauke da kwanon sauran tuwo miyar kubewa da wani ya
rage aka juyemai '
"Wani irin kauce wa yayi tareda cewa" goodness wat tha hell " ai da sauri ya juya
batareda ya shiga ciki ba " fadawa kawai yayi cikin motar shi yafara danna wayar
shi"
"Batareda bata lokaci ba yafara ruwan bala'i " AK wat the he'll is that? are
kidding me?
Batareda naji Amsar dayan da yake kira da A k ba yayi hangin wayar shi tareda
fisgar motar shi yabar unguwar ya hau babban titi kenan ya uban wani burki
Wanda yayi kusan hada dan karamin hatsari "
"Gaba daya mutane suka fara duramai Zagi Wanda shi Sam hankalin shi baya jikin shi
burin shi kawai ya kara ganin wannan kyakkyawar fuskar da ta hana rayuwar shi
sukuni fuskar dake hanashi bacci fuskar dake sanyashi ciwo a duk lokacin da ya tuna
ta "
"Wani irin juyawa yayi domin bin mashin din da take kai ya koma inda yafito " domin
yayi Alwashin bazai kuma bari ta kubce mai ba again don zai iya mutuwa muddin ya
bari ta bace mai a yau'
"Tabbas zuciyar shi zata buga " duk surutun mutane bai dameshi ba "burin shi
kawai yau yaga farin cikin shi wato his dream girl"
"Dai dai kofar gidan da yabari ta sauka tareda biyan mai mashin din tafara takun ta
cikin natsuwa batareda tunanin komai ba"
"Saurin sauka yayi batareda ya tsaya kulle kofar motar ba cikin sauri yabita
lokacin har tasa kanta zuwa cikin gidan "
"Tsaya wa tayi domin jin wannan kamshin da bata mance mamallakin shi kafin tagama
wani tunani yafado cikin gidan "
"" wani irin mugun karo suka gabza Wanda yayi sanadi yar tayi baya tana shirin
zubewa kasa " cikin zafin naman shi ya fisgota " batareda bata lokaci ba ya
Rungume ta cikin kirjin shi "
"Ita kuwa ta gama sadakar wa zata zube kasane war was " jinta a cikin wani kirji
mai bala'in kamshi da kuma ni'ima " yasata bude idanunta "
"Sai akan fuskar shi mai cikeda da Annuri da kuma tsantsar yarinta" tayi saurin
tureshi tareda fara koro ruwan bala'i"
"Au saboda rashin kunya biyoni kayi gidan mu ? Har kake kokarin Hada jikin ka da
nawa " wallahi Allah ya isa " batareda ta jira komai ba ta shigewar ta"
"Sukuwa yan tsegumi tuni sunyi cin cirin do suna kallon wannan dramar ta Ruman da
kuma kyakkyawan gayen " tareda tanbayoyi masu yawa a zukatan su"
"Biye yake da ita kamar gaula har zuwa cikin falon Hajiya batareda damuwar komai ba
yake binta kamar jela..........✍
*Akwai cakwakiya kenan jama'a Ruman da Bature Wanda zan warware muku waye shi idan
har kuka ci gaba da biyoni A cikin wannan littafi nawa mai suna KUSKURE NA*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA*🙆
_Love & Destiny_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*
~Dedicated to~
All my fan's
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA*🙆
_Love & Destiny_
*Jama'a don Allah duk w'anda yaga kuskure a cikin rubutu na hanya Abud'e take'
domin dan Adam ajizi ne tara yake bai cika goma ba, nagode*
3 3
➡3⃣
"Tafara tsorata da lamarin wannan Aljanin yaron " cikin zare ido ta waigo shi jin
takun shi a bayanta cike da masifa tafara " waikai dakikin wane garine ?
"Wane irin jakanci ne haka? Dabba ne kai da zaka shigo cikin gidan mutane batareda
izini ba " koda yake idan nayi la'akari da yanayin ka nasan kasar da kafito Akwai
karan cin Addini da kuma tarbiya"
"Jin hayaniyar ta yayi sanadi yar Fitowar Jama'ar dake gidan har ma Hajiya dake
sanye da hijabin ta hannun ta rike da carbi tana istigifari da Alamar Salla ta idar
"
"Kowa yakasa cewa komai ganin irin wannan had'add'en gayen yaro a tsaye ba Abinda
yakeyi sai kallon ta "
"Hajiya tayi saurin taron ta ganin irin zagin da take shekawa bawan Allah"
"Haba Ummu " wannan ai batarbiya bace ' kin saki baki kinata zagin d'an mutane " ba
irin tarbiyar da na baki ba kenan "
"Hajiya idan ba raini ba ya zai rika bina sai kace ni sa'ar shi ce?
" Salati Hajiya ta saki domin jin son girman na Ruman ya girmama " yo wannan Zatace
ta girma?
"Shikuwa tuni ya dawo cikin natsuwar daga dogon tunanin da ya tafi " ya kalli
tsohuwar mai cikeda kwarjini da kuma haiba "dattijuwa mai kyau da kuma kyan hali
tareda ta wakkali"
"Karasa wa yayi cike da ladabi " Mama ina wuni? Cikeda lafiyayyar hausar shi mai
hade da wani irin salo irin na Wanda yatashi cikin harshen nasara "
"Nine w'anda zai zauna a nan gidan, muryar shi cikin natsuwa ga wani irin salo mai
dad'in saurare "
"Ita kanta tayi mugun jin mamakin wai hausa yakeyi " ta zaro ido tana kare mai
kallo y'anda ya tsuguna gaban Hajiya "
"Ko zagin da tayi mai da hausa tayine da gangan bata taba kawo yanajin hausa ba"
"Kuyi hakuri don Allah bata sani bane shiyasa " ya juya cikeda wani irin kallo mai
tattare da fassarori daban daban"
"Na farko wahala ta takare nabiyu tausayin kanshi na uku tsantsar so mai cikeda
damuwa.
" Cikin gaji yawa tareda sanyin jiki yace " Aunty kiyi hakuri ba ke nake bi ba '
"Ita kanta jikinta yayi sanyi sosai Amma hali irin na Ruman tayi wucewarta batareda
ta kuma furta komai ba "
"Binta yayi da kallo harta shige cikin falon su" ya kara matsawa kusa da Hajiya "
mama Don ALLAH Kuyi hakuri da abinda ya faru"
"Aa yaro kai zanba hakuri da irin Abinda jikata tayi maka ka yi hakuri kaji ba haka
halinta yake ba An samu kuskure ne ALLAH ya huci zuciyar ka "
Isowar Ak ya tarar da wannan dramar " domin yazone da zancen sun Fasa zama domin
ogan baya son gidan kuma ya sameshi a ciki "
"Ya karaso Yace "Oga' yayi saurin daga mai hannu " Ware is the room?
"Cikin rawar jiki ya nufi kofar da shi Sam tun zuwa nshi bai lurada itaba wato
itace farkon shigowa gidan "
"Ya bude mai tareda cewa" hare is the room sir.
"Ya shiga tundaga falon dan madai daici ba laifi sofa guda dayace a ciki Wanda Ak
ne yasakata hade da dan center table karami sai dan madai daicin plasma A.c da dan
karamin firij duka a cikin falon
" cikin inner room din kuwa katuwar katifa ce irin hutadda gadon ka din nan taji
duvet da kuma pillows gefen ta kuma harda mirror cikeda kayan kayan kanshin da yake
Amfani dasu masu matukar tsada da kuma kamshi mai tsaya wa a rai"
" sir' hannu yayi saurin dagamai " atakaice yace " just go I will call you.
"Yana fita ya fada kan katifar mai dauke da lallausan kamshin room freshener Wata
irin Ajiyar zuciya ya sauke tareda fitar da hawaye masu mugun zafi da radadi '
"Ruman kuwa tana shiga cikin daki taji gaba daya ranta baya mata dad'i yanzu wannan
ne zai zauna musu a gida?
" Hajiya na shigowa ta rufeta da fada " Ummu banson rashin tunani yanzu saboda
Allah me yayi miki banson rashin da'a fa'
"Cikeda dauriya ta taso ta rungume ta " yi hakuri my kakus nayi laifi '
" Shine. "sai yaya? " tab a she Akwai aiki kenan, " babba kuwa " kuma ba ruwan ki
da shi ki kiyayeni'
"Don nafi kowa sanin halin ki, " halina mai kyau ne ko Hajiya ta? Eh amma watarana
Akwai gyara a ciki ki kiyaye wulakanta mutum ko yaya yake'
"Kinga wannan bawan Allah bakisan ko waye shi ba Meya kawo shi dan gidan waye oho
don haka ki kula "
"Banason ki yi sanadin jefa mu cikin wata damuwar muna zaman mu cikin rufin Asirin
Allah'
" A gaskiya tayi nadamar Abinda tayi sosai ita kanta tasan ta zake da yawa haka
Hajiya ta cigaba da Jan kunnen ta tareda nasohohin da 'ya kamata duk wata uwa
tagari tabawa y'ay'anta,
"Ta tafi ta barta cikeda nadamar zagin da tayi mai ta tuna irin kallon da yake
aika mata lokacin da take surfa mai Ashar Ashe duk yanajin ta "
" kiyi hakuri Aunty shine Kalmar da tafi komai tsaya mata a zuciya "
"Ta dade a kwance cikin tunani kafin ta mike tayi Wanka tareda dauro Alwala "
"Tun Fitowar ta tasamu kanta da kallon kofar dakin nashi " ko yana ciki?
"Ita take wannan tunanin " to ina ruwana ko yana ciki?wata zuciyar ta kuma cewa,
" ya dade a kwance yana tunani kala kala daga karshe yafara jero murmushin shi mai
kayatar wa
"Yana tuna y'anda take magana muryar ta very sweet her lips wow ya wani irin rintse
idanu nshi tareda cije lips dinshi kadan ' tunawa dayayi da irin kirar jikinta
" he never imaging her structure kullum fuskar ta kawai yake gani a mafarkin shi ko
haduwar da yayi da ita sau biyu fuskar ta kawai yake kallo but today """""""""
Hmmmmm.
"Yasan His dream girl is Awesome she is very sexy she have everything he wants her
Boob's hip's her kissable mouth " more especially her expensive colour
"Ruman ta hadu iya haduwa shiyasa takejin tafi karfin kula duk wani karamin yaro
bawai don kudi ba aa nata ra ayin kenan.
" yana tausayawa zuciyar shi da ta jarab ce shi da sonta juyi kawai yakeyi tareda
shakar kamshin jikin ta da ya manne a jikin shi wani irin tashi tsigar jikin shi
keyi
"Sakamakon tunawa da yayi da irin rungumar da ya yimata " Ashhhh ya furta da dan
karfi tareda danne marar shi
"Oh my God ya furta a hankali' wayar shi ya janyo da kyar tareda neman numbar Ak "
"Cike da wahala yake magana a wayar " yace " zanturo maka sunan wani magani please
ka kawo min yanzu "
" cikin mintin da bai wuce sha biyar ba Ak ya kawo mai maganin " cikeda kulawa
yafara tanbayar shi me ke faruwa ?
"Cikin jarumta da kuma karfin hali yace ' am OK please don't tell any one am going
to be Alright"
"Yace " OK sir but please take care of ur self " I will don't worry "
"Bayan yasha maganin bacci mai dadi hade da mafalkai masu dad'i ya dauke shi "
"Washe gari da wuri ta shirya ta bar gidan domin sun shirya dasu hajara zasuje wani
waje kafin lokacin lecture.
" Sun fara shirye shiryen dawowar yayan hajara daga outside country har anko suka
buga na wani tsadadden code less su uku Wanda hajara ta dauki nauyin dinka musu '
"Sumy kuwa wasu irin tsadaddun jakun kuna designers da takalmin su ta siyo musu "
ba yadda zatayi dasu domin ta San tanakin Amsa zasu fara complained
"Shiri sukeyi na musamman Hajara na cikin tsananin farin cikin dawowar d'an uwanta
" ya makara sosai yau saboda rashin baccin da bai samu ba jiya da wuri sai kusan
Asuba ya samu ya rintsa a gurguje ya fada bathroom
"Ya dad'e a tsaye yana tunanin y'anda zai fara wanka a tsaye " yasaba da kwanciya a
cikin jacuzzi ruwan dumin ya ratsa shi Amma gashi shine da wanka da wannan ,
"Rashin mafita yasashi runtse ido tareda fara wankan shi cikin natsuwa da kuma kyal
kyale jikin shi ta ko ina
" karfe kusan goma yafito cikin shigar shi a koda yaushe wato kana nan kaya yana
sanye cikin wandon Jean's baki tareda farar rigar T-shirt wadda aka rubuta *COOL*
a gabanta
"Kafarshi na sanye cikin takalmin shi kamar kullum wato canvass fari ga wani
Annurin kyau da fuskar shi ke fitar wa daka kalle shi zaka hango tsantsar kuruciyar
shi
" cikeda natsuwa yake takawa zuwa cikin gidan " tunda yafito ma aikatan Hajiya kaka
duk suka zubo mai idanu har mada masu siyan Abinci suna kallon Hutu da kuma wayewa
"
Kofar falon nasu yayi sallama " w'anda Hajiya ce zaune a gefen ta kuma doctor
Sulaiman ne suna hira kamar y'anda suka saba"
"Cikeda fara a tace ' shigo ciki dan nan Ak kaima kazama na gida " ya kutsa kanshi
cikin falon " kamshin shi mai matukar tsada ya musu sallama " shi kanshi doctor
Sulaiman kallon shi yakeyi "
"Yasan daga ganin wannan Ajebo ne " Amma meye dalilin shi na zama cikin wannan
gidan duk irin hotels din dake cikin Garin na Zaria "
"Tuna nin shi ya tsaya ne a dai dai lokacin da ya mika mai hannu cikeda ladabi
sukayi musa baha da lallausan hannun shi mai kamar Auduga
" Ya gaida Hajiya yana mai bin ko ina na falon da kallo " ba laifi ko ina fes domin
Hajiya kaka Akwai tsafta sosai ga falon su ba laifi Akwai kayan more Rayuwa dai dai
na mai karamin karfi tundaga firij TV da kuma kujeru "
"Wani irin ni shad'i yakeji a cikin zuciyar shi " yanzu Anan my dream girl take
Rayuwa ? Yana mai Addu'ar dama tafito yasata A idanun shi '
"Hajiya ta katse mai tunani lokacin da take magana da Sulaiman" mutu miyar taka ko
batasan kadawo ba " kuma da wuya yau ta dawo da wuri don suna taya kawar su shirye
shiryen wata hidimar da zasuyi gobe'
"Wani irin faduwa gaban shi yayi " tareda kallon gefen da doctor Sulaiman yake" to
shi wayene nata? Mutu miyar shi? What was that means?
"Oh no yayi saurin kawarda tunanin shi domin jin zuciyar shi na wani irin har bawa
" ya runtse idanun shi tareda tattaro natsuwar shi ,
"Mama Aunty fa? Tafita ne? " wai Ruman? Ai tun karfe takwas ta bar gidan nan "
Ruman""" Ruman''' A cikin zuciyar shi yake nanata sunan " what a name
"Mikamai hannu da Sulaiman yayi ya dawo dashi daga duniyar thinking " Abokina
have a nice day' tanks ya furta a hankali '
"Ya fita tareda yima Hajiya sallama da kuma Alkawarin dawo wa da dare "
"Wata irin wa wuyar Ajiyar zuciya ya sauke bayan fitar doctor Sulaiman haka kawai
yaji bayason gayen
" Hajiya sarkin sabo har ta saki jiki dashi tana bashi labarin yar jikar tata da
kuma irin son girman ta " wani irin farin ciki yakeji kamar yayi tsuntsu ya ganshi
a gabanta " cikin dubara ya tanbayi sunan makarantar su"
"D'an nan ka ko ci Abinci? Aa bana break fast da wuri, "a'a kaidai kace Bazaka
iya cin irin Abincin mu ba'
" No ba haka bane idan nadawo zanci a ajiye mun. ya mike tare da fita yana mai
yimata sallama.
"Kamar koda yaushe kofar gidan d'ankam yake da mutane " batareda ya ko kalli gefen
su ba ya fara takawa har zuwa wurin da motar shi ke fake "
"Ga badaya sun zuba mai ido har ya bar unguwar,gulma cike da zukatansu
" Yana fita a unguwar direct G.R.A naga ya nufa yafaka kofar wani lafiyayyen gida
mai tangamemen gate "yayi horn yakai kusan sau uku kafin a bude gate din'
" A zuciye ya fito ko kashe motar baiyiba ya fito yayi shigewar shi cikin gidan
batareda da yako kalli mai yimai magana ba "
Gaba daya body guard din shi suka taso cikin girma mawa " welcome sir"
"Hannu kawai yake daga musu cikeda izza da kuma yanga ya shigewar shi cikin wani
lafiyayyan falo mai kofar glass w'anda saida yayi Amfani da hannun shi ta bude
" Subuhanallah falon ya hadu iya haduwa komai najin dad'in Rayuwa Akwai Kamar a
Dubai kujerun ma kawai Abun kallo ne ga wani irin plasma mai kamar cinema a jikin
bangon falon
" Wata hanya naga ya nufa ya zuge kofar da ita ma glass ce ya shiga cikin wani
hadadden bedroom Wanda yaji wani irin lafiyayyan gado batareda ya tsaya bata lokaci
ba ya fara kwabe kayan jikin shi yana mai cilli dasu a kasan dakin "
Yarage dagashi sai short Hmmm " kallon shi nafarayi tundaga kasa har zuwa saman shi
ina mamakin wannan wane irin yarone mai kwarjini da kuma cikar zati ko ta ina
jikinshi gashine akwance mai daukar hankalin duk wata lafiyayyar mace "
"Ga wani irin fadi da yayi daga sama kirjin ma cike yake da suma " bathroom ya
fada saida ya cika shi da ruwa sannan yashiga daga ciki ya dauki kusan rabin hour
ruwan na ratsashi kafin yayi wanka yafito
"Wurin shafe shafen kuwa ai ya dauki kusan hour daya " shafa wancan shafa wannan "
"Saida ya shirya cikin shirin nashi wato kananan kaya wannan karon fari ne Jean's
din harda rigar itama da rubutu ajiki *SHE IS MINE* yafito cikin shigar farare har
takalmin shi
" yana baza kamshi ya fito tareda nufar wani irin dining table Wanda aka jera
Warmer's masu daukar ido "
"Dagudu kukun ya iso tareda fara serving dinshi Abinci daban daban irin naturawa
yafaraci cikeda yanga " bai wani ci dayawa ba ya mike ya nufi hanyar waje '
"Ak yataso da sauri yana yana rikeda wayoyin shi " who call? Yafada cikin
natsuwa kuma atakaice " shima yabashi Amsa " your Dad and Momy ' yayi saurin Jan
birki " ya karbi wayar " what did you tell my parents?
"Jikinshi narawa yafara dialing number Dady " yana picking yafara yimai fada " ina
yashiga tunjiya baka dauki waya naba ?
"Am sory Dady ya fada cikeda shagwaba " I was busy yerstaday " busy? Yes Dady I
saw her and I no ware she is now "
"Dady katayani Addu'a kar Momy ta hanani Auranta. " saboda me? ur Momy is
supporting u " no Dady she is a Muslim.
"What? Yafada cikin karaji " Don't let ur mother hear that "
"Wasu irin hawaye ne suka biyo kuma tun shi ya janye wayar a fuskar shi " zuciyar
shi na mugun bugawa ya fada motar shi Ak kawai ya shiga tareda tayarda ita Aka
wangale musu get
"Sai bayan sunfita ya tanbaye shi ina zamuje? " F.C.E kawai yafada "
"Karfe shabiyu da kusan rabi suka danna motar cikin makarantar ' gabadaya dalibai
sukabi lafiyayyar motar da kallo sunaso suga waye wannan a cikin wannan motar?
" Suna gefe sai hirar su sukeyi "Hajara Sumy da kuma uwar gayyar Wato Ruman " gefen
su wani couse mate dinsu ne Abokin hajara sunata hira dashi duk da ba ruwanta da
rayuwar samari Amma suna shiri sosai da Abdul sosai yana taimaka musu ta fannin
karatu'
"Idanun shi ya sauka a lokacin da Ruman ta zauna a gefen Abdul tana mai nuna mai
hand out dinta " wani irin mashi ya kuma cakar zuciyar shi " dama yana cikin
damuwa "
"Batareda ya tsaya bata lokaci ba ya bude motar ya fito idanun shi jawur ya nufi
wurin da suke Zaune " Wanda sai Alokacin Idanun su Hajara yakai kanshi
"Cikeda kaduwa suka zuba mai idanun ganin su yake nufowa jikin su na rawa tareda
jin dadi sosai saidai suna ganin yanayin shi sun San cewa a kidime yake "
"Idanun shi a rufe ya tsaya akansu kamshin turarenshi kawai ya sanarda ita cewar
Akwai mutum akusa da ita Amma bata kawo shi bane "
"Yana huci ya riko hannun ta a firgice ta dago kanta domin jin wani irin shock a
jikinta w'anda shima saida ya kusa faduwa saboda jin laushin hannun ta'
" you have to understand baby u are mine " banason ganinki da kowa ke tawa ce ki
fahimci haka mana '
Ya fada cikin taushin murya irin ta gaji yawa gaba daya baki suka saki suna kallon
shi har ita kanta tsoro ya kamata "
"Toh nima dai nace ba ayi komai ba Akwai aiki don haka muje zuwa ✍
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*
_godiya cikin barrack fan's da irin comments dinku Amma ina neman kari, saboda inji
karfin yi muku typin kamar yadda kuke bukata,ina mugun yinku masoya Fenerh_
4➡4⃣ 4
"Wani irin kallo take aika mai mai cike da fitinu kala kala ga shi idanun jama'a ta
ko ina Kowa ya natsu yana kallon su " ranta yayi mugun baci "
"Meye matsalar ta da wannan yaron? Zai zo ya y'ar fata a gaban students har ma da
kawayen ta " cikin masifa ta fisge hannun ta batareda tunanin komai ba ta zabga mai
lafiyayyan mari '
"W'anda atake hawaye suka biyo fuskar shi ya dafe gurin ya nabin ta da kallo.
" A rikice su Sumy suka taso suna me rike hannun ta da take shirin watsa mai wani
marin "
"Hajara tace " haba Queen meye haka don Allah ? " ya zaki tanbaye ni meye haka
bayan kina kallon irin renin da ya nunamin A gaban mutane.
"Ina nasan shi impact meye had'i na dashi? Saboda kana haya a gidan mu " that's
doesn't give you the right to hold my hands "
"Gaba daya ta sakasu a cikin duhu suna bukatar bayani. A ina tasan shi? Haya a
gidan su? Wannan dan gayun bature ?
" Abdul kuwa ai shi tuni ya ware "kowa mamakin karfin halin ta yakeyi ,
Kwasar kayanta kawai tayi ta yi wu cewar ta Jikin hajara na rawa ta fara bashi
hakuri domin yaron yayi mata kwarjini sosai da bazata iya kallon idon shi ba"
"Ashe ranar kallon tsoro tayi mai Ashe duk zancen da sukeyi Ruman ta sanshi shiyasa
take musu masifa"
"Hakuri suka ci gaba da bashi " ya share hawayen da kebin kuncin shi " Kuje karta
hau bike please banaso '
"Maganar shi a takai ce kamar tana yimai wuya da sauri Sumy ta bita ita kuwa hajara
bata gama kallon wannan baturen ba"
"Tareda mamakin bature da jin hausa ? " ki bata Hakuri please friend,
"my name is Hajara and the other one Sumayya but we call her Sumy " nice to meet
you Hajara yafada cikin wani irin salo tareda mika mata hannu kamar y'anda Al
adarsu take'
"Ta noke tareda girgiza kai ta fara tafiya cikin sauri ya bita " tell me more About
your friend please ""
"Tsaya wa tayi cike da mamaki " Eh kifada min Ina son inji komai a kanta " ya fada
cikin shagwaba " ita mamakin shi ma takeyi namiji da saurin kuka kuma gashi
shagwababbe "
"Ina jinki ' Am sory kaga yanzu muna Sauri zamuje gidan sune munada party gobe na
taron brother na so till next time in mun kuma haduwa "
"No problem muje gidan nima a can nake zama, idanun ta a waje " kafin tace wani Abu
yayi gaba tabishi cikeda tan bayoyi "
"Suna tsaye a jikin motar Hajara sai ruwan masifa take zubowa tana ganin su tare
tayi saurin bude gaban motar ta shige Sumy sai ido kawai take binsu da shi saida ya
karaso kusa da su ya dan duk'a yana kallon fuskar ta ta glass din windown motar "
"Ya dauki lokaci a haka Sannan ya mikawa Hajara hannu Give me the key. Jikin ta na
rawa ta mika mai "
"Hannu kawai Yama Ak ya taso da gudu " drive them. Cikin bada umarni su basu ma
fahimci mai yake nufi ba saida ya bude motar hajara ya shiga " tayi saurin jiyowa
"
"Kafin tayi wani Abu yayi lock din motar tafara ruwan bala'i ya fisgi motar
batareda ya saurareta ba ya harba ta" suma ganin ba suda zabi dole suka bi Ak
"Instead of ya kaita gida aa hanya ya d'auka saida sukayi nisa da gari sannan ya
faka a gefen titi still tana kan rabtaba mai masifa "
"Ya kife kanshi jikin sitiyarin motar Ya saki kuka mai tsaya wa a zuciya,
" Gaba daya wuta dauke mata tayi ta tsaya tana mai kallon shi saida yayi mai Isar
shi San nan ya dago idanun shi farare da suka canja kala zuwa kalar ja'
"Jikinta yayi sanyi sosai' juyowa yayi dakyau yana mai fuskan tar ta, cikin kwantar
da murya yafara magana.
"Me yasa bakyajin y'anda nakeji a zuciyata' ya dafe k'irjin shi " my heart is
beating very fast, zan iya mutuwa idan ta cigaba
"Am begging you Roman"" yafadi sunan ta cikin wani irin salo,
"Ki taima keni I no u hate me but please Roman Am begging you please Allow me to be
with you I love you mothern my oun life
" baki San tsawon lokacin da na d'auka ina wahala ba tun ban ganki ba am here only
bcos of you help me " ya karasa maganar shi cike da gajiya wa
"Wani irin kallo take yimai " ni kakeso ? Yes I love you and I can do Anything for
u please"""'"
" wani irin murmushi yayi mai dan sauti ya kalleta dakyau don yasan me take nufi da
hakan ,
" saboda raini zakace kana sona bayan na girmeka da kusan shekara daya " ko dan
kaga kayi girman jiki ka kuma Ajiye wani irin munafukin saje a fuska shi zai baka
damar cewa kana sona"
"Ni kece mate dina kece dai dai dani ke nake so Roman ke kadai saboda ke na baro
kasata batareda nasan cewa kina nan kasar ba
" that is our destiny ke kaddara ta ce tun lokacin da nafara zama namiji nafara
mafarki dake zuciya ta na fadamin zan ganki zamuyi Rayuwa tare zaki soni zaki Haifa
min yara"
"Dariya kawai ya bata ta wani kalle shi irin kallon ka raina ni "
"You are dreaming. Kallonta yake cikin idanunta kallo irin mai cikeda tsananin so
da kuma sa daukar wa
"Am not dreaming, my dream has Already come true u are in front of my eyes "
"Cike da takai ci " you no what ? Just take me home before I do something stupid
"Ban sanka ba bansan sunan ka ba daga ina kafito kawai naganka ne a hanya sai kuma
a cikin gidan mu da sunan haya ,
" Me kake nema a wurina? Nasan ba sona kakeyi ba don ALLAH ka fita a Rayuwa ta
kaga jinsin mu ba daya ba shekarun mu ba daya ba ban San kuma Addini ba"
"Gaba daya jikin shi yayi sanyi" mu samman y'anda tafara zubar da hawaye " jikin
shi na rawa yakai hannun shi zai share mata hawaye tayi saurin bugemai hannu "
don't touch me,
"Listing to me please " kina maganar shekaru " ni nasan zan Isar miki k'arki raina
namiji
" wani irin kallo ya ke yima ta "Roman u will regret your word's
" Kaine zakayi dana sani bani ba kuma Sunana Umma Ruman ba Roman ba,
" Hmmm Roman ki kula ina sonki magana da wani namiji kamar kinamin wasa da Rayuwata
ne bakiji y'anda najiba da bayanki da wannan yaron ba
"Ki rike wannan tunda na iya barin iyayena masu matukar kaunata saboda sonki to ba
Abinda bazan iya yiba ki kiyaye wannan
" Bai kuma kallon gefen ta ba ya Yata yar da motar sai gidan su tunda ya fara
tafiya take kallon shi domin ya bata tsoro " to wai shi meyake nufi da ita ne?
Yana fakawa ta bude motar ta fito ko kallon gefen shi batayi ba ta shige cikin
gidan fuuuu kamar iska " tun a tsakar gida ta cire hijabin ta saboda tsabar jaraba
ta fada falon Hajiya bako sallama " tasamu su hajara sun mimmike kafa sai hira suke
kwasa da Hajiya gefe kuma Doctor Sulaiman ne har sun saba dashi saboda yanada
saurin sabo"
"Batareda ta tsaya ba ta shigewar ta cikin dakinta ta fada kan gadon tareda Sakin
kuka mai karfi
" Hajiya tace ALLAH ka taimake ni " waya tabomin ita yau ? Suna rige rigen shiga
dakin ita da su Sumy " kowa sai faman tanbayar ta yakeyi lafiya?
"Ba Amsa saida tayi mai Isar ta sannan tayi shiru tareda saita kanta " Umma lafiya
waya tabaki ? Hajiya ta tanbaya
"Kaina ke ciwo ta fada cikeda shagwaba tana sharbe" mtsww Hajiya ta ja tsaki tayi
ficewar ta tana mita" ALLAH ya shirye ki wallahi sai kace Karamar yarinya"
"Doctor Sulaiman kuwa duk ya rude ganin y'anda ta shigo cikin gidan ya d'auka ko
ciwon ta ne ya tashi saida Hajiya tamai bayani ya natsu tareda yin dariyar ta "
"Yaji takara shiga ranshi saboda yana kaunar mace mai shagwaba A rayuwar shi "
"Ita kuwa Hajiya na fita ta mike zaune " duk suka haye gadon suna son jin bayani "
lafiya kuka zuba min idanu haka?
"Lafiyar kenan ki fada mana Meke faruwa mu bamu gane komai ba ki sanar damu kawai
muna jira.
" A hankali tayi musu bayanin komai tundaga ranar da tafara ganin shi har zuwa
ganin shi da tayi a gidan su da kuma Abinda ya fada mata A yau"
"Gaba dayan su suka runkun kumeta dakyar take numfashi " ku sakeni meye haka ?
"Ai dole mu rungume ki mu shafi tabaraki ko ALLAH zai bamu baturen mai son mu Kamar
haka "
A Gaskiya ke mai sa'a ce Queen " tana musu kallon kun hau kace " wace irin sa"a ?
Karamin yaron ne sa'a kuma daga gani ba musulmi bane
" aa ba kyau k'arki yi saurin kafirta mutum haka kawai" hajara tafada "
"OK yana ina? Oh zuwa zakiyi? " Sumy muje " tayi saurin rikesu " ku wuce gida sai
mun hadu gobe please banaso Hajiya ta sani "
"Sun sallami Hajiya ta rakosu Sulaiman sai binta yakeyi da ido Ita kuwa ko kallon
gefen shi bata yiba
" Suna fitowa tsakar gidan suka same shi a tsaye " cike da iya yi hajara ta matsa
kusa dashi '
"Hy friend. " Hy" ya fada yana kallon Ruman kamar ya had'iye ta
"Ta Ciro wani dan karamin I v ta mika mai " u are invited' hope u will come " ya
fara duba wa tareda cewa " sure.
"Ya kalli gefen Sumy " hy Sumy how are you? Cike da jin dad'in ya kira sunan ta ta
washe baki " _Am cool_
" Ya mika ma Hajara key din motar ta tareda cewa tank's " tace u are well come.
"Sun rabu tareda sabo mai karfi ya shige cikin dakin shi ita kuwa bata kuma lekowa
waje ba tana son yin wanka Amma saboda kar ma ta hango shi ta hakura ,
" misalin karfe takwas na dare ta leko domin Gaskiya ta matsu ta yi wanka " A
hankali ta shigewar ta " tana fitowa ta daura Alwala sannan ta shigewar ta tareda
Ajiyar zuciya'
"Shikuwa tun Fitowar ta yake kallon ta don kar ta koma yasa ya boye karta gan shi
har tayi Alwala ta shige "
"Koma wa yayi cikin dakin domin yayi jin yar zuciyar shi da kuma gangar jikin shi
" Wani iri yakeji a duk lokacin da ya ganta A Gaskiya idan har ba a mallaka mai ita
ba Akwai matsala
"Yana mugun jin feelings akanta ba karamin kai zuciyar shi nesa yakeyi ba a duk
lokacin da take kusa da shi ya tuna moment ago y'anda ta ke komai a natse ga tsab
ta'
" Wani irin mur mushi yayi lokacin da ya tuna da irin son girman ta bayan ita
kanta kuruciya na damunta "
"Ruman kuwa yau marar ta taki bari ta runtsa tun tana daurewa har ta fara birgima
akan gado " ganin Abin yafi karfin ta tafara hawaye tareda Addu'ar Allah ya yaye
mata wannan jarabawar
"Tanason yin Azumi Amma tasan gobe ba halin yin haka saboda hidimar dake gaban su
Gashi yin Azumin shine yafi mata sauki domin yana rage mata damuwar
" Ni shin da take fitar wa yasa Hajiya shigowa dakin domin tana zaune a falo "
" tana dafe da Mara tace " Cikina Hajiya zan mutu" .
"Jikin Hajiya na rawa tace na shigesu ni yar nan wannan wane irin Abu ne haka?
" ta fita ta rarumo wayarta tafara laliben numbar doctor Sulaiman Amma shiru bai
daga ba " ganin Wankin hula zai kaisu tsakar dare yasa ta ruga waje " Wanda yayi
dai dai da Shigowar shi " A kidime ta fara cewa dan nan katai makeni kar in rasa ta
ita kadai ta rage min ita kadai nake gani inji dadi"
"Cikin rudu yafara tanbayar ta Mama waye ? Ummu,,, Ai bai ko gama jin baya nin ba
ya fada cikin falon
" Tun daga shigar shi ya jiyo kukan ta dakin kawai ya fada mai dauke da sassanyar
sanyin ta da kuma na turaren wuta
"Batareda tunanin komai ba ya rikota " w'anda saida sukayi Ajiyar zuciya a tare duk
da tana cikin ciwo.
Jikin shi narawa batareda ya damu da Hajiya ba yafara kiranta " baby" what
happened?
"Hajiya ma sai salati take duk ta rude A hankali ya kwantar da ita ya fita da
saurin shi sai gashi dauke da wata yar Karamar Akwati ya bude tareda Sanya mata
wata irin na ura akan yatsan ta ya kunna Hajiya na tsaye tana kallon ikon ALLAH"
"Ya dauki lokaci sannan ya cire ya Cire ya kalleta sai juyi takeyi tana rike cikin
ta " Ya Ciro sirinji ya zuko ruwan Allura Hajiya ta fita da Sauri domin ita kanta
ta tsani ganin tsinin Allura "
"Ya Ajiye agefe tareda dagota cak kamar wata y'ar baby ya rungume ta sannan yasa
hannun shi ya yaye Hijabin dake jikin ta "
"Wani irin mugun bugawa kirjin shi yayi domin daga ita sai towel wannan hijabin ne
dama ya rufe jikinta tun Fitowar ta daga wanka ko Salla batayiba tafara jin ciwon ,
"Dakyar ya iya dai dai ta kanshi ya dan kawar da kanshi ya zame towel din tareda
janyo hijabin sannan ya laluba yayimata Allura Wanda saida tayi wani irin zillo ta
shige jikinshi
" w'anda yayi sanadi yar daukewar numfashin shi na kusan min tuna sai dakyar ya
jawo shi ya samu ya mike cikin tangadi ya tattara kayan Aikin shi ya fito bai ko
iya yima Hajiya bayani ba tana godiya ko iya Amsata batayi yayi waje
"Dakin shima kasa komawa yayi " yana fita wayar Ak ya kira " yace suzo yanzu'
"Cikin minti goma suka iso harda body guard din shi yace su kai shi G.R.A
" Ita kuwa bayan yimata Allura bacci ne mai dadi ya dauketa Hajiya a kusa da ita ta
kwanta tareda zare mata Hijabin tana mai yimata mitar rashin sa kaya"
"Gaba daya ranar bai runtsaba ciwon shi ya dawo danye sharab dama shi kadai yasan
irin famar da yake yau gashi yayi ganin Abin da zai dameshi
" laps dinta kawai yagani hankalin shi yatashi Inaga yaga mai gaba dayan
"Ranar tsabar fitina har kuka yayi gashi ciwon yafi na kullum" ai Ak da gudu ya
fita ya kira numbar MAMAN shi " yamata bayani domin gudun faruwan wani Abu yasan
idan har wani Abu ya sameshi tsab za akulle shi saboda tsaron lafiyar shi yake tare
dashi"
"Gaba daya ta tashi hankalin ta cikin daren taso ta biyo private jet dinsu Amma
Dadyn shi ya bata hakuri ta jira Gari ya waye shima zai je "
"Sam bata cikin hankalin ta shi yasa bata tsaya tunanin komai ba ta hakura da
maganar shi
" Kafin safe kuwa har suma yayi gaba daya hankalin Ak ya tashi
"Ganin Wankin Hula zai kaishi dare yasa suka kwashe shi sai Asibiti " cikin gaggawa
suka Amshe shi tareda daura mai drip "
"Koda gari ya waye garau ta tashi Abun ta kamar ma batayi ciwo ba Hajiya tafara
cewa " kai nagode wa wannan yaron ya taimake ni ALLAH ya mai Albarka "
"Cikin kidima tafara tariyo Abinda ya faru jiya " ranta yayi mugun baci domin ta
tuna komai "
Shi kenan zaiji dad'in rainata dakyau ya shigo har cikin dakinta yaga gadon baccin
ta✍
*ku taromin Ruman fa my fan's tanada matsala babba mutumin da ya taimake ki?*
_*Matar Soja*_
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
~Dedicated to~
_*XUMUNTA @ NOVEL FAN'S GRP*_
_kuna bani nishad'i A Gaskiya naji dad'in comment dinku keep it up_
5 5
➡5⃣
Karfe goma ya farka na safiya har lokacin dafe yake da cikin shi Ko mikewa baya
iya yi da kyau " yayi saurin duba time " cikin rawar jiki ya zare Karin ruwan dake
hannun shi,
"Wanda yayi dai dai da Shigowar Ak " cikin sauri ya rike shi " what are you doing?
U have to rest .
"No Am OK I want to go and see her she is not fine" Allow me to go "
"Kafin ma ya gama rufe baki Likitan ya shigo " cikin tsananin girma mawa yafara
duba shi tareda bashi hakuri Akan yayi hakuri ya karasa sauran drip din y'anda
zaiji karfin jikin shi sosai,
"Ranshi bai soba haka nan ya koma ya kwanta Likitan ya mayar mai da ruwan yana fita
ya bude ida nun shi
" Ya fara zuwa G.R.A domin taron iyayen nashi saboda bai sanar mai da zuwan su ba "
kuma a dai dai lokacin suka diro Motoci ne sun kai kusan bakwai a Jere suka fara
fakawa a kofar gidan
"Jikin Ak na rawa ya karasa ya fara bude motar da yasan iyayen gidan shi na ciki '
" wa iya zubillah shine kawai na iya fada domin wata mace ce kyakywa fara tas da
ita kana ganin ta kasan baturiya ce kuma ko a cikin turawan ta jiku da Hutu da kuma
masu gida rana"
"Ta na sanye da kwamemen glass jikinta sanye da suit na mata baki Riga da wando ga
wata irin jaka wadda kana ganin ta kasan naira ta koka a wurin iri daya da takalmin
ta have cover masu masifar tsini"
"A Gaskiya ko a turawa wannan ta hadu " Hmm Anan na gano da wa yake kama baturen
Ruman'
"A dayan side din kuwa Namiji ne w'anda ina ganin shi nasan shine me gidan duk da
shi ba fari bane Amma kalar shi mai kyau ce ya jiku da Hutu da kuma naira
" Yana rike da wata faskekiyar waya letest shima cikin suit din yana Amsa call"
"Shine Abinda naji yana fada cikin natsuwa har suka isa cikin gidan da shi da
kanshi ya danna lambobin kofar ta bude gaba daya body guard din shi suna biye
dasu ,
"He is in the hospital mah ya fada yana dukar da kanshi kasa kuma jikin shi na rawa
"
"Tayi wani irin mikewa " tafara zazzaga mai bala'i " yaron ta na Asibiti zai sa
akawo su nan Ita akaita Asibitin taga danta kawai if possible a yau zata juya dashi
America "
"Me gidan na tausar ta " please sweetheart came down take it easy noting will
happened to our boy "
"Dakyar yasamu tayi shiru tareda warning Ak duk Abinda yasamu danta sai ya fuskanci
hukunci mai tsanani'
" Direct Asibiti suka wuce w'anda still idanun shi a bude yana jiran kiran Ak domin
yaji lafiyar Ruman din shi'
"Kamar daga sama yagan su Hankalin shi ya tashi ganin Momyn shi a Nigeria kasar da
ta tsana har ma da mutanen cikin ta
" Yayi saurin Ajiye wayar hannun shi yana bin iyayen shi da kallo ita tafara
matsowa hawaye na bin kuncin ta ganin shi zaune ya dan fada
"Tafara fada dama shiyasa batason ta bar yaron ta gashi zai mutu ba a gaya mata ba
ita bazata y'arda ba ina likita ya basu sallama ita zata kaishi waje Aduba mata shi
" Murmushi yayi tareda rungume ta " Am fine Momy don't worry your self it's just a
Minor sickness Am going to be Alright'
"Ak ya kira Likitan yana shigowa yafara rawar jiki domin idan ba gizo idanun shi
suke mai ba kamar Ambassador yake gani A gaban shi mutumin da saidai ya ganshi a TV
tvn ma saidai irin su CNN ko Aljazera yau shine a cikin a Asibitin su?
"Jikin shi na rawa yafara zubewa yana Kwasar gai suwa ya Amsa shi tareda tanbayar
matsalar yaron shi cikin natsuwa yafara koro musu bayanin cewar sparm yayi mai yawa
Amma sunyi iya kokarin su sai dai yayi kokari ya rage shi kafin ciwon ya kuma tashi
don Gaskiya Akwai matsala'
" Cikin rawar jiki ta kara rungumo yaronta cike da tausayi Abinka da baturiya
tafara tanbayar shi " my boy are you still a virgin?
"Wata irin kunya ta rufe shi ya dukar da kanshi uban ne yayi saurin matsowa kusa da
ita " Tara what are you saying ?
"Ya fada cikin kwantar da murya " You have to understand there is no such a thing
in our religion
"Cikin karaji tafara masifa " I don't bloody care that is your religion you are
talking A bout not mine
"Ta kara matsawa kusa da shi " cikin lallashi tafara yimai magana " why my son me
yasa kaki sauraran Linda kafin ka samu yarinyar da kakeso ?
"Yanzu gashi kana neman kashe kanka bayan kana da right ka huta kaji dad'in rayuwar
ka " meye matsalar ka ? Kanada kudi muntara maka nida Dadyn ka " ka bini Mu koma
America kawai kafin kaga dream girl dinka kaji,
"Wani irin bakin ciki ya turnike shi data hada shi da wata Linda cike da bacin rai
ya kalle ta " Momy I just want my dream girl I love only her and I want to be with
her forever,
"Were is she?
" please Momy leave her I can handle my situation please "'" yafara rokon ta
" uban ma ya kara rike shi yana mai nasiha cikin harshen hausa "ka kula my boy A
nan kasar ba kamar America bane da zakayi duk Abinda kaga dama nan Akwai doka
" kuma a kullum ina fada maka kabi hanyar Gaskiya karka Aikata irin *KUSKUREN NA*
" A ranar aka basu Sallama domin uban yace dole ya kaishi international hospital
Abuja y'anda za a duba mai shi da kyau " yaso ganin Ruman a yau Amma ba hali
"Ya kebe da Ak ya bashi umarnin zuwa wurin partyn domin su kula mai da ita yanaso
yayi ta daukar mai Hoton ta har vedio ya rika turomai
" Duk da yaji Sauki sosai Abinka da gata saida suka kuma bashi gado Aka shiga yimai
checkup Wanda Ann suka gano cewar yana shan kwayoyin kashe sha'awa wa inda zasu iya
illata shi,
"Ran Momyn shi ya baci sosai a take ta kira wayar Linda ta fada mata tabiyo plight
gobe tazo Nigeria '
" Shi kuwa gaba daya hankalin shi naga wayar shi yana jiran kiran Ak Domin sun
barshi A Zaria ta private jet din su suka zo Abuja ba body guard sai w'anda
shugaban kasa ya aiko sukula da lafiyar su
"Yana kwance Akan gadon dukan su suna gefe kowa kamar ya mayar dashi ciki saboda
tsabar so ya matsu yaji kiran Ak,
" Ruman kuwa sunata faman hidima tun da Safe suke G.R.A sunyi k'unshi sun zuba
gyaran gashi sumar nan na sheki sun fito cikin code less dinsu blue ga head fari da
takalmin su da jaka a ranar bama zancen gyale bare hijabi
"Fadin irin kyan dasu kayi bata bakine mu samman Ruman " hip's din nan kamar yayi
magana ita kanta tasan kayan ya kamata dam A jikinta
"Taro yayi taro bako ya iso da tawagar Abokanshi masu yimai sannu da zuwa "
"Suna gefe sun kame sai hirar su sukeyi suna Kwasar dariya " Hajara tace Queen gaba
daya gayun nan idanun su na kanki"
"Sumy tace ai har ya Nasir ida nun shi na kanta " cikeda jin dadi Hajara tace " wow
da naji dadi idan kika Auri yayana zaki hai famana fine girls kamar ki"
"Kai kuma bature fa our young crush kai Gaskiya gayen nan karshe ne " Sumy ma ta
cabe "ai wallahi ba yaroba ko jariri ne idan ya taya da gudu zan bada kai bori ya
hau"
"" Domin kana nan yara Akwai iya love gasu danyen jini ka more kuruciyar ka
"Fada mata dai Sumy tafison ragowar majina ko kuma ragowar wata ba ga danyen jini
da zakiwa training'
" ku dai wallahi sai A hankali Ana zaman lafiya meye na zancen wannan Babyn yau she
aka yimai kaciya bare har ya kosa inba rashin kunya ba ina shi ina babbar yarinya
kamata.
"Suka sanya shewa harda tafawa " Wallahi Queen kibi A hankali namiji baya kadan ki
bar raina Allura karfe ce'
"Ya Amsata yana mai zuba ma Ruman ido kamar ya lasheta " Sannu fine girl ya kike?
"Kafin ta bude bakinta Nasir ya karaso wurin cikin sauri tareda janyo daya daga
cikin kujerun ya zauna gab da ita kamar zai shige cikin jikinta
" Abokina this is my property ka canja sheka na Riga ka malam yafada cikin raha
Wanda dukan su sukasa dariya banda Ruman data hade rai "
"Umar yace shi kenan Amma kamun shigar sauri wallahi. Ya kalli su Hajara " sister
please excuse us I wants to talk to your friend
"Suka mike suna kunshe dariya domin sun San Akwai rikici tsakanin su yau'
"Duk Abinda sukeyi idanun Ak na Kansu yakasa d'auka domin gudun Abinda zai iya
faruwa "
"Kiran wayar shi ya katse mai tunanin mafita da saurin shi yayi picking " cikin
fada yafara magana " nace maka ina bukatar ganin ta so I wants to see her rights
now.
"Bashi da choice dole yayi connecting ya haska mai ita a dai dai lokacin da ta
danyi murmushin ta mai kayatar wa har gefen kuma tunta ya loba
" Domin nasir mutum ne mai tsananin raha da ba mutum dariya shi kanshi dimple dinta
ya matukar burge shi har yakai hannu yana kokarin tabawa saida taja baya
"Baby A Gaskiya Aure nakeso"" ya fada cikin wata irin siga yana mai kwantar da
muryar shi kamar mai rad'a
"Baby ban taba tunanin yin Aure yanzu ba Amma ina dora idanu akan ki planing dina
ya ruguje ki taima kawa tsohon tuzurun nan please
" kallon shi tayi a kaikaice tana mai kare mai kallo " ba laifi shima ya hadu ga
ilimi ga kuma wayewa daga nin shi zai iya soyayya
"Ak na haska mai Saida ya kusa sume wa tsabar bakin ciki da kuma kishi nan take
kirjin shi ya fara halbawa idanun shi suka juya wasu irin hawaye masu Azabar zafi
suka fara Ambaliya a kuma tun shi jijiyoyin kanshi tuni sunfito sunyi rudu rudu'
" Saida ya saki wayar ya dade yana jin yar zuciyar shi yasha kuka ma ishi inda Abin
yazo mai da sauki ya lallaba iyayen sunje suyi wanka Sudan huta domin kawai yaga
rabin ranshi gashi tana neman karasa sauran rabin ran da ke tare da shi'
"Ya samu dakyar ya saita kanshi ya kuma dialing number Ak " go and give her the
phone.
'Cikin bada Umar ni " batareda bata lokaci ba ya karasa gabanta lokacin nasir ya
mike domin Ana neman shi "
"Kawai ganin shi tayi a gabanta kuma bazata taba mantashi ba don tana yawan ganin
shi a gidan su ta kuma San yana tare da bature " ta kuma tanke fuska " lafiya'
"Yi hakuri ma'am my Oga wants to talk " ta balla mai harara cikeda tsiwa " to hell
with you and your stupid Oga
"Ranshi yayi mugun baci kuma shima yana jinta " cikin dauriya ya ce yasa a hands
free " ya danna cikin taushin murya ya ce ,
"Roman kinaso kisa mutane a matsala ko? Ki kiyaye kula wasu mazan " cikin masifa
tace idan naki jifa ubana? " kaga banason rainin wayo kuma ganina da kayi jiya
Allah ya isa karamin yaro dakai sai jaraba"
"Wata irin dariya yayi mai sauti duk da yana cikin damuwa " baby""'"" ya fada
cikin wani irin salo
"Kema fa jara babbiyar ce tunda tare muke ciwon kin San me ? Sai jiya nakara y'arda
da cewar nine dai dai dake saboda jarabar mu daya
" Gashi kin janyo min zuwa Asibiti nima A Gaskiya baby idan nazo dole ki barni in
rage damuwa kin dauki Alhaki na sosai fa
"Ya fada cike da tsokana " saurin barin wurin tayi tare da balla wa Ak harara "
"Shikan shi dariya ta bashi yana mai mamakin Megidan nashi da fitina ina shi ina
wannan babbar yarin ya?
" Ya katse kiran tare da runtse idanun shi shi kadai yasan irin zafin da zuciyar
shi keyi idan ya tuna da ganin wani namiji a kusa da ita har ma yana kokarin taba
ta,
"Hawaye ne ke zarya akan fuskar shi bi yake kamar yayi tsuntsu ya ganshi a gaban ta
'
" A haka iyayen shi suka same shi yayi kokarin saita kanshi domin yasan yanzu
hankalin Momyn shi zai tashi,
"Duk da haka sun fuskanci yana cikin damuwa Amma tanbayar duniya yaki basu Amsa
daga baya ma juya musu baya yayi kamar mai yin bacci'
" Har taron ya watse bata kuma yadda ta hadu da kowane namijin ba daga kar she
komawa tayi dakin Hajara tayi Kwan ciyar ta domin bata son damuwa'
"Sai karfe shida na yamma ta shirya zuwa gida "_Sumy ce ta dauke tareda sha tara ta
Arziki daga maman su hajara tana ta yi musu godiya domin duk sune suka yi Aikin
komai na partyn'
" Iya gajiya ta gaji ko da ta koma gida bata wani tsaya hira ba kasan cewar tana up
kawai wanka tayi ta dan mike Abinta'
"Hajiya ta sameta " Ummu " yaron nan tun jiya ban kuma ganin shiba dazu na tanbayi
yaron shi yace min wai baida lafiya yana Asibiti a kwance "
"Saida k'irjin ta ya buga ' tayi shiru tana tunanin dazu da ya ce Abata waya wato
da gaske yakeyi yana Asibiti'
" Amma mai yasa zai ce ita ce sanadin zuwan shi Asibiti? tayi saurin kawar da
zancen domin bata so tunanin shi yayi tasiri a zuciyar ta
"Ya yi iya kokarin shi naganin Momyn shi ya barshi ya dawo Zaria amma fafur taki
Daga karshe ma gida ta saya mai dan karere akan ya zauna Aciki idan har zaman
Nigeria yakeso to gwara ya zauna a Abuja "
"Bakomai yasa tayi hakan ba " domin tasa Anyi mata bincike akan Ruman ta gano cewar
musulma ce don haka ta dauki Alwashin bazata taba y'ar da d'anta ya Aure ta ba
"Ga badaya fushi yakeyi da uwar ko magana baya son yimata " Yau ma yana kwance a
gefen sweming fool dake cikin katon gidan su ba abinda yakeyi sai tuna nin ta "
"Abu daya ke kwantar mai da hankali Ak dake bashi information akan komai dake
tafiya
Iya dauriya yayi ta ga shi Momyn shi ta kasa ta tsare taki koda barin shi ya fita
kamar wani jariri " jin shi yakeyi idan har bai gan taba yau Akwai matsala "
"Cikin minti goma ya shirya cikin kana nan kaya " yafito kamar ka sace shi ka gudu
ga sumar nan ta kwanta tana sheki saboda gyara da kuma irin halittar gashin
_*Bye Dady*
" Uban yana kwance a gefen maman ya ji karan Shigowar msg yana dubawa yayi dariya
tareda nunawa uwar "
"Tayi wata uwar zabura tafita da sauri Shikuwa tuni yayi nisa domin baiko tsaya bin
private jet din su ba kawai filin jirgi ya tafi ya biya Sai KD
" Ruman kuwa tafara damuwa da rashin dawowar shi ko banza ya taimake ta gashi tun
ranar nan bai kuma neman ta ba
"Ko a makaranta kawayen ta sai faman tanbayar ta sukeyi Amma shiru ba Amsa bata
San mai yasa take damuwa ba?
" Karfe kusan daya suka tashi yau bata tsaya jiran kowa daga cikin suba ta kamo
hanyar ta domin yau Sam bata jin hawa mashin cikin natsuwar ta take takawa "
Ganin mota tasha gabanta Abin ya mugun bata tsoro Sai dai ganin w'anda yake cikin
motar yasa ta shan mur ta kara tanke fuskar ta tamau
"Doctor Sulaiman ne ya fito da sauri " Haba gimbiya ba girman ki bane ki zo in
sauke ki gida don Allah badon ni ba.
"Batason dogon magana shiyasa kawai ta shiga tareda kulle kofar " cikin jin dad'i
yace " nagode gimbiya '
"Kasan cewar rana ce mafi yawancin jama'a sun Adana Kansu domin irin mugun zafin
ranar da Akeyi "
"Bakowa a cikin unguwar har ma da kofar gidan nasu Taji dad'in hakan yana tsaya wa
" yace " Don ALLAH Gimbiya Ruman kiyimin Alfarma in turo iyaye na Wallahi Aure
nakeso Muyi ina sonki tsakani da ALLAH ki taimaka ki Amshi kokon barata"
"Cikin kosa wa tace zanyi tunani akai ' bashida zabi dole ya ce toh Domin ko jiya
nasir ya zo mata da zancen turowa Amma ita Sam bata shirya Aure yanzu ba duk da
sun kai irin mazan da take muradin Aure .
" Duk Abinda ya faru akan idanun shi komawa yayi gefe tana karaso wa ya fisigota
kafin ta Ankara har ya bude mota ya jefa ta "
"Ya fad'a ciki idanun shi sunyi jawur kafin tace wani Abu ya fisgi motar " jikinta
narawa tace " wai meye haka " meye zaka wani fisgoni kamar kaya nifa banason rainin
ka "
"Bai saurareta ba sai da ya isa da ita cikin " GRA dai dai gate din gidan shi yayi
horn mai gadi ya wangale mai sai bala'i takeyi bai saurareta ba yana kashe motar ya
fito ya zagayo gefen ta "kifito"
"Bazan fitoba kamayar dani gidan mu" kifito ko in dauke ki" ya kuma fada " ta bishi
da wani irin mugun kallon raini batareda yace mata komai ba ya fisgo ta tamike ya
wani dagata cak a saman kafadar shi kamar wata y'ar tsana"
"Tafara kaimai duka ko gezau bai yiba saida ya sadata da katon falon mai cikeda
ni ima " yana Ajiyeta tafara masifa " wallahi banason iskanci karamin yaro dakai
sai rashin kunya ALLAH ya isana"
"Tsawa ya daka mata " he that's enough jikin shi narawa ya matso kusa da ita tafara
ja da baya Yana kara binta har ta fada kan kujera "
"Wani irin murmushi yayi tareda tsuguna wa a gabanta " Roman why? Kinaso ki kasheni
ne um?
"Meyasa kike kula maza ne " na kulasu kayi Abinda zakayi tana fada k'irjin ta na
bugawa har sama da kasa na sha nunta ke yi a cikin hijabi'
"Idanun shi ya sauka a wurin yana kallo " ya daga hannun shi dakyar......✍
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
~Dedicated to~
Ai'sha Salis
_Allah ya sauke ki lafiya uwar gidan dan fillo ina miki fatan Alkhairi Arayuwar
Aurenki da dukkan musulmi baki daya_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*
6 6
➡6⃣
''Meye a nan? Yana kokarin dora hannun shi akan kirjin ta, tayi saurin buge mai
hannu tare da ja baya kamar zata shige cikin kujerar,
"Ida nun shi sun kad'a sosai ya kalleta " Why? Me yasa zaki hana ni ? Bayan jiya
naga y'anda kika fita da wasu irin kaya,ko wannan baki saka ba,
" Cikin dauriya tace " banason rashin kunya ina fada maka,
"Zan nuna miki rashin kunya har ma da yarinta " yasa hannu ya rike hijabin ta
yafara kokarin zare shi"
"Rikewa tayi tamau idon ta a waje " wai meye haka ne ? Tafada ida nunta na cikowa
da hawaye " tuni jikin shi yayi sanyi ya saki hijab din "
"Baby""" Ina cikin damuwa ki tai makeni please " cikin dakewa tace " wai me kake
bukata ne a waje na ka barmin Rayuwata in huta don ALLAH.
"Ke ce da muwata *Mary me please"* wani irin mugun kallo ta aika mai ' ni in Aure
ka ALLAH ya kiyaye,
"Ki bani dama in nuna miki kece dai dai dani Roman, ya furta a hankali,
" Tayi saurin ja da baya " banason iskan cin ka ina fada maka ko.
"Ruman tsabar kiyayya ta baki ko damu kisan suna na ba waye ni ? Duk baki damu ba,
"Mikewa yayi yafara takawa cikin isa ya juya mata baya " Ruman banaso kiyi da na
sani banaso wata matsala ta faru a tsakanin mu ina gudun Aikata laifi Akan ki
kibani goyan baya,
"Idan har ina Raye bazan taba bari ki Auri wani namiji ba " kina kirana jara babbe
""yes I am kuma jaraba ta zata kare akanki ne kece kawai nake kwadayi
" idan zina nakeso da tuni nayi a kasar da na baro saboda ke,
"Saboda ni? Tafada tana mai kallon shi cikin ido tun lokacin da yafara magana take
binshi da kallo tana imaging yaro kamar shi yace wai ita yakeso ya Aura?
" Dawowa yayi da baya ya riko hannun ta duk da tana tirjewa haka ya jata zuwa cikin
wani dakin danake tunanin bedroom ne,
"Tun daga bakin kofar tafara cin karo da hotunan ta na Zane manya manya a kowane
kusurwa dake cikin dakin " ta waro ida nun ta waje tana mai bin fuskar tata da
kallo A hankali take matsawa har zuwa gaban Hoton,
"Fuska tace wannan' a ina Kasamu? Domin iya tunanin ta bata taba daukar hoto irin
haka ba,
" A hankali ya fara takawa zuwa gareta "ta shagala da kallon Hoton taji hucin
numfashin mutum a dai dai wuyan ta,
" Juyowar da zatayi tajita a cikin k'irjin shi " ya mata kyakkawan ma sauki tareda
sauke lafiyayyar Ajiyar zuciya nan da nan idanun shi suka canja kala har wani irin
ruwa suka tara,
"Kar ki kashe musu yaro" ni kadai suka mallaka " Sanadin ki gaba daya family na
basuda natsuwa " yanzu haka sunbaro kasar da suke saboda ni,
"Ni kuma gani nan A kusa da farin cikin zuciya ta' ita kokarin kwace kanta takeyi
domin Abun nashi yafara fin karfin ta,
"Auchhh Baby,,, ya fada yana mai rintse idanun shi domin tayi maganar ne akan
fuskar shi hucin numfashin ta mai hade da dan d'umi ya buge shi yakara kashe mai
duka gabobin jikin shi'
" ko ina na jikin shi sakewa yakeyi " ji yake kamar ya turmushe ta ko zai samu
sassauci yana mai zuba wa jajayen lips dinta da suke sheki idanu ya hadiye wani
mugun miyau,
"Da kyar ta samu ta fisge daga jikin shi " w'anda sai da yaji kamar ta zare mai rai
ne "da baya baya yakarasa bakin tafkeken gadon dake dakin yafada rub da ciki yana
nishi "
"Na tonowa kaina ya fada A hankali " ita kuwa neman hanyar fita tafarayi Amma ta
rasa ta inda ya shigo da ita domin sai yanzu ta lura da ko ina na dakin glass ne,
"Wasu irin hawaye ne na takaici suka fara zubo mata " kazo ka bude ni intafi malam
kar ka tayar min da hankalin tsohuwa ,
"Tasowa yayi yana tangadi har ya iso kusa da ita yasa hannun shi a jikin kofar sai
gashi ta zuge,
" Tana fitowa falon ta fisgi jakar ta yayi saurin riko hannun ta " ina zakije?
" Ni shine kuma yanzu na fara taba ki "now tell idan ban tabaki ba wa zan taba?
" Ba yau bane na fara taba ki baby" saidai Akwai banbanci "A da ina tabaki a
mafarki na yanzu kuma A zahiri ne,
" ya kai hannun shi kan fuskar ta, tayi saurin gocewa " da zafin naman shi ya
fisgota zuwa kirjin shi Wanda yayi nasarar hadewar k'irjin su wuri daya for the
first time yasamu y'anda yakeso'
"Saida ya jingina a jikin kofar glass din saboda wani irin dad'in da ya ziyarci ko
ina na jikin shi'
" wani irin mugun numfashi yake fitarwa jikin shi na rawa ya kara gyara tsayuwar
shi domin ya samu damar more taushin Albarkatun kirjin ta dake mugun dimautashi a
yanzu,
"Ji yake kamar ya dagota ya cire hijabin domin zaifi jin dad'in morewa da kyau inda
halima baiki ace hannun shi yaje Kansu ba'
" Ga badaya ya juya ragamar tuna nin ta " shine namiji na farko da tafara taba
jikin ta harta kai ga runguma gaba daya ya sauya mata kuzarin jikinta tsigar
jikinta duk ta mike ta ko ina,
"Da kyar itama take fitar da numfashi kafin tayi wani yunkuri ya dora lips dinshi a
kan nata,
" Kusan faduwa yaso yayi daga jikinta saboda laushin dake kan lebenta " ita kuwa
jin dumin halshen shi akan lebenta ya dawo da ita daga duniyar shaukin Abinda ya
fara dora ta akai yana kokarin zura harshen shi a cikin bakinta tayi saurin hankade
shi ya zube a wurin'
"Zubewa kawai yayi a kasa ya fara juyi tareda zubo war hawaye masu zafi " cike da
wahala yace " Noo baby,,,,
"Zan iya rasa lafiya ta idan har kika gujeni don ALLAH kibarni Koda ajikin ki ne
zan danji sauki kadan ki taima keni zan iya mutuwa wallahi yafada yana mai sanya
mata kuka mai tsinkar da zuciya,,,
" wallahi bazan yafe maka ba ALLAH ya isa tsakani na dakai "dama nasan me kake
bibiya to kuma ta ALLAH bataka ba
" Mikewa yayi dakyar ya nufeta yana mai zubar da hawaye " say what ever you want
Roman ni nasan soyayyar ki ce take hadda sa min fitinar ki meyasa banajin hakan a
sauran mata?
"Ya fara share hawayen shi " yanzu naji ki y'ar da ki Aure ni please koda Asirri ne
idan har kina gudun Ace kin Auri karamin yaro please''
"Wani irin tsanar shi takejin tana kamata domin ta tsani namijin da zai nuna yana
son jikin ta ,
" I danunta suka kada sosai cikin tsananin bacin rai tace " ka budemin kofa kafin
inyi maka lahani na fada maka''
"Ta fada cikin karaji kallon ta yake yi wani iri " yafara tafiya da baya baya har
ya dangana da center table din dake Ajiye a gefen kujerun mai dauke da kayan
marmari da kuma yar Karamar wuka akai ya daukota yanufo gabanta da wukar,
"Idanun ta a waje ta d'auka zai caka mata itane Amma sai taga sab'anin hakan yana
zuwa ya damki hannun ta ya danka mata wukar'
Ya ja hannun ta dai dai saitin zuciyar shi " ki kashe ni kawai Roman please kill
me' ki la antani kamar yadda kikace I will be happy
"Meye Amfanin Rayuwata idan har bazan yita tareda ke ba? Kece cikon numfashi na
idan bakya cikin duniya ta my life is useless,
"Da inada dama bazan bari ki fita ko ina ba banki mu kasan ce a haka ba daga ni sai
ke,
"Ganin fadan ta bazai yi Amfani ba kawai ta durkushe a wurin tasa kuka mai tsuma
zuciyar masoyi,
" wani irin suya kirjin shi yafara yi yayi saurin durkushe wa a gaban ta jikin shi
na rawa hawayen shi na Ambaliya kamar kogi,
"Ku rufama zuciya ta Asiri kukan ki tamkar digar dalma ne a kahon zuciya ta da inga
kukan ki gwara ni mutu,
" I promised you daga yau bazan kuma takura rayuwar ki ba gidan ku ma nasan bakya
sona a cikin shi daga yau bazan kuma zuwa ba ko Ak bazan bari ya kuma zuwa ba,
" Amma kimin Alfarma ya share hawayen shi cikin dakewa ya mike tareda dakko wani
dan karamin diary ki rike shi a wurin ki please "
"Wayar shi ya daga tareda kiran Ak yana isowa ya bashi umarnin ya mayarda ita gida
shi da kanshi ya mike ya dakko mata wata Leda mai tanbarin inna idea shopping
complex ya mikawa Ak " karike mata,
"Jikin ta yayi mugun sanyi ya bata tausayi sosai Amma taki y'arda ta nuna hakan,
" bai iya fita ba kawai ya haye gado tareda fashe wa da wani irin kuka mai tsuma
zuciyar mai saurare,
"Zuciyar shi suya takeyi shi kanshi yasan yayi karya yace zai hakura da ita " I
can't yafada cikin kuka"
"Jikinta yayi matukar yin sanyi har suka isa kofar gidan su bata iya cewa komai ba
ya miko bata ledar ta karba harda godiya ita kanta bata San dalili ba da takasa
karbar Abinda yafito a hannun shi"
"Hajiya kuwa hankalin ta ya tashi ganin har kusan karfe biyar ba labarin Ruman har
magaji ta kira tafara fadamai ko zai je makaran tar ne ?
"Kaga Amfanin waya ko da Ace tana da ita ai koma meye zamu sani bari ta dawo
dolenta ta rike waya nida ita ne'
" tana rufe baki tana shigowa cikin sanyin jikin ta,bakinta dauke da sallama,
"Tun bata zauna ba Hajiya tafara sababi " Yanzu kekuwa Ummu ina kika tsaya har
karfe biyar duk kin daga min hankali?
"Muna gidan su Hajara ne, tafada kai tsaye batareda ta shirya karyar ba tafito daga
bakinta ita kanta mamakin Abin takeyi da takasa fadawa Hajiya komai akan bature'
" Amma zakije meyasa baki fada min ba kin tayar min da hankali' kiyi hakuri my
kakus tafada cikin karfin hali domin ta matsu ta keb'e kanta ko zata iya sarrafa
tunanin ta'
"Bakida lafiya ne Ummu?
" lafiya ta kalau kawai gajiya ce.
"Toh kije kiyi wanka ki dan huta duk da yamma tayi sosai,
" Dama a kage take mikewa kawai tayi da jakar ta har ma da ledar da ke hannun ta
tayi shigewar ta cikin dakin ta'
"Hijabin ta kawai ta iya cirewa ta fada kan gadon ta tareda runtse idanun ta tana
mai tuna moment ago,
" yarrrr tsigar jikin ta ta kuma mikewa sakamakon tunawa da tayi da irin rungumar
da ya bata " har yanzu tanajin cent din turaren jikin shi atare da ita duk da ta
cire hijabin,
"Wani iri takeji sosai ajikin ta w'anda Sam ta kasa sarrafa kanta ga wani irin
shauki mai wuyar fassara atare da ita duk sakamakon tunawa da lallausan kuma
tsadadden jikin shi da tayi,
." Duk da yana da karan cin shekaru amma jikin shi Sam bai nuna ba zaka d'auka
shekarun shi sunkai irin Ashirin da biyar din nan,
"Ta dade A cikin yanayin kafin ta samu ta mike zaune tareda janyo ledar da ta shigo
da ita ta bude,
" wata irin Arniyar wayace kirar Samsung galaxy grand 9 sabuwar yayi wadda bata
taba ganin ta koda wurin kawayen ta ba Mu samman hajara da duk sabuwar waya tafito
sai ta canja'
"Duk da bata kaunar waya wannan tayi bala in burgeta kuma for the first time taji
zata iya rike waya a hannun ta,
" Kodan shi ne ya bata? Meyasa taki karba a hannun Doctor Sulaiman? Ko nasir ya
bata waya taki karba Amma wannan gashi ta karba batareda tasan ita bace kuma ta
y'arda zata rike'
"Bata gama tunani ba sako ya shigo Sai a lokacin ta San wayar akunne take kuma har
ma da layi a ciki tafara juyata kafin ta bude sakon,
*I may not be the one you love and I may not be the most important person in your
life, . but just hope that one day u will Also love me the way I do*
_hope u will Accept my small gift_
*I love you*
" Duk da sakon ba wani Abu na burgewa bane aciki Amma ta samu kanta da karan tashi
ba Ad'ad'i,
"Ranar da kyar taga waye war gari, wayar ma Sam bataso Hajiya tagani Amma tasan
bazata iya boyon waya ba
" Kafin ta fita ta nunawa Hajiya tareda karyar yayan hajara ne ya bata,
"Ummu" Hajiya ta kirata " ta Amsa tareda zama kusa da ita' Me yasa kike wa Sulaiman
yawo da hankali?
" Ki bi a hankali duk kin daga ma dan mutane hankali kullum yana hanyar gidan nan
gashi ko kallon Arzikin ma yanzu baya wani samu,
"Cikin kosawa ta mike " Sai na dawo mayi maganar " Dawo nan tunda kinyi waya samin
lambar ki kar akuma irin na jiya,
"Hajiya bazan dade ba zan dawo da wuri yau " kuma ba wai na gama sanin kan wayar
bane sai naje ankoya min,
" Da wuri ta isa makaranta ta samu su Sumy basu isoba saida ta dauki lokaci kafin
suka iso da shewar su suka rungume ta "Sai Queen ,
" Idanun hajara yakai kan wayar hannun ta ta waro idanun ta duka waje
" Sumy ma tace ke kyama tanbaya ai kinsan waye " cikin jin dad'i suka dafe ta " our
young crush?
"Kai kawai ta daga musu, wani irin ihu suka saka tareda tafawa " kinsan kudin wayar
nan kuwa two hundred plus fa " wani kaya sai Amale,
"Haka sukayita kururuta wayar kafin su shiga Ajin ita kanta Abin yabata mamaki
wayace za a siya harta sama da dubu Dari?
" to ita ko a mafarkin ta bai wuce ace ta rike yar Nokia torchlight ba sai gata da
Galaxy grand Hmmm""
Bature kuwa tun fitar ta ciwo ya dawo sabo Ak ciki Gaggawa ya kira iyayen ya fada
musu hankalin mahaifan shi ya mugun tashi atake suka biyo jirgi suka iso Zaria,
"Linda kuwa ta iso Nigeria don har da ita suka iso Zaria " taci wani irin takalmi
kamar ta fado kasa ta karye tsabar tsini ga sket dinta kamar ya yaye rigar kuwa iya
kacinta wurin nono cibiyar da ciki duk a waje ga wani kwamemen glass Kamar horror
da ta hadu da Jan gashin kanta da tayi dying,
"Kana ganinta kaga American's din nan da idanun su ke bude sosai wai da sunan waye
wa"
"Tunda suka iso take like da shi a gaban iyayen shi sai faman shafa shi takeyi yana
kwance shi bai Masan tanayi ba yanata kanshi'
." sai kusan karfe dayan dare ya farka daga dogon baccin da yayi na Allurar
da,likita yayi mai'
"Ahankali yakejin numfashin mutum a jikin shi yafara bude idanun shi a hankali yana
mai sauke su saman Fuskata
" Wani irin zabura yayi ya hankade ta a jikin shi w'anda yayi sanadiyyar farkawar
ta " oh darling u hv wake up tafada cikin slang English dinta,
" Tafara kokarin rikoshi zuwa jikinta tareda zame yar ficiciyar rigar da ke jikinta
ta y'ar agefe " ya kalle ta cikeda kyama yana mai kallon wani irin bushashshen
kirjinta,
"Cike da tsana " out of my room, ya fada cikin tsawa " I said get lost'
"Mayyar kokarin rikoshi takeyi " come on Darling u no why am here so just for get
it and let enjoy our night together,
Ya kwanta jinya saboda sha'awa amma yanzu yatashi yanacin karo da mummu nar surarta
gaba daya feelings dinshi ya gudu"
"Tsaki ya buga tareda mikewa ya barmata dakin wani daki dake kusa da nashi ya fada
tareda datse kofar da ki don yasan halinta batada zuciya kokadan,
" Ya janyo system dinshi ya fara research din da ya dauki lokaci yana yin shi kuma
yana kan neman haske akai har yanzu.......✍
*A Gaskiya wannan karon ina fuskantar karan cin comments dinku fan's sanadin hakan
yake hanani yi muku typin kamar y'anda nayi kuduri*
*Matar Soja*
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*
_Written by Fenerh_
7 7
➡7⃣
Tun dawowar ta daga school takejin zazzabi na rufeta ita kadai tasan y'anda takeji
A cikin zuciyar ta,
Ganin Wankin hula zai kaita dare yasa ta nemawa kanta mafita ta,
" Washe gari sun tashi da jimamin rashin lafiyar Magaji don haka kawai ya yanke
jiki ya fadi ' hankalin Hajiya yayi mugun tashi tayi mugun rudewa,
"Gwaggo Amina ce mai kwantar mata da hankali wato Matar magajin " Yaya kiyi hakuri
da izinin ubangiji ba Abinda zai samu baban ja'afar,
"Tana share hawaye tace " Amina shikadai nake gani inji sanyi shikadai ya rage min
"ya'yan namu guda biyu duk sun guje mu saboda mace,
" Kiyi hakuri kidaina zubar da hawayen ki akan su ni kaina na cirewa kaina tunanin
wannan yaron ai duniya ce ta ishi kowa Riga da wando,
"Gashi Muhammadu tun Auren shi da yarin yar nan balkisu baifi sau biyu ya zo gida
ba ko tunanin y'ar marainiyar ALLAH bayayi,
" Daina tunamin Amina ni yanzu zuciya ta tafi kar kata da dawowar ja'afaru ko
hankalin d'an uwa na zai kwanta,
"Nasan komai yakeyi yana yin shine a cikin karfin hali Amma abin na cin shi a
zuciya,
" Ita kanta gwaggo Aminar karace irin ta ba haushe Amma Abun na cimata tuwo A
kwarya'
"Ruman da Shigowar ta kenan taji wannan zancen hankalin ta ya tashi sosai da jin
wannan irin labari,
" tana bukatar Karin haske don haka har matsuwa tayi gwaggo Amina ta tafi taji
Karin bayani,
"Tunda ta gai shesu ta shigewa war ta cikin dakin ta cike da tunani kala kala'
" Kallon ta takeyi cike da sanyin jiki tayi Ajiyar zuciya cikin damuwa tace'
"D'an uwan mahaifiyar ki shima tun lokacin da yatafi karatu kasar turawa ya hadu da
wata baturiya ta mallake mai tunani bai kuma wai wayo mu ba,
" Saboda mun nuna mai KUSKUREN shi na Auren shi da Ahalil kitabi Akwai lada aciki
kuma Addinin mu baiyi hani ba Amma Akwai kalubale da yawa da mutum yake fuskanta ko
akan tarbiyar yaran su,
"Nidai har yanzu kaina na cikin duhu " naji kunce d'an magaji ne," eh shine
mahaifin Aisha wato mahaifiyar ki,
"Amma mai yasa baki taba fadamin kaka na bane? " kaji mun shirme ko da can ba kakan
ki bane shi?
"Aa Hajiya shima bai taba nuna min Akwai kusan ci mai karfi tsakani na dashi ba,
" Ba ma wata shakuwa a tsakanin mu har ma ina nuna mai tsana ban San cewa shi ya
haifi mamana ba'
"Kuma duk hakan tafaru ne sanadiyyar nuna son kudin shi da yakeyi a fili'
" Wani irin murmushi tayi irin na manya " Ummu' takirata da murya mai ma anoni da
dama'
"ALLAH ne gatan mu magaji dan uwana ne gatan mu duk Abinda yakamata a ce mahaifin
ki yayi mana shine duka ya dauke duk da shekarun shi kuwa'
"Duk hidimar makaran tar ki shine da wahalar shi da yakeyi Ruman kin taba tunanin
waye yake tallafa mana kuwa?
" kina tunanin da wannan sana'ar ce kawai nake baki gatan da kike samu?
"Magaji yazame min d'an uwa yazame min kani ya zamemin yaya yakuma zama min uba duk
da yana kanina,
" Duk tsawon shekarun nan Ummu magaji yana cikin rashin babban danshi kuma ga
mahaifiyar ki ita ma ta tafi gashi dagani har shi ba wani zuri'a garemu ba,
"Shi guda dayar ta tafi shi kuma w'anda ya kamata ya kula dashi ya yi nisa bayajin
kira kamar mahaifin ki'
Ta karasa tana mai share hawaye " Ummu Ruman jikinta yayi mugun sanyi sai yanzu ta
gane meyasa Gwaggo Amina ke yawan kallon ta a duk lokacin da zasu hadu gashi duk
y'anda Hajiya kaka zata matsa mata da zancen zuwa gidan su bata y'ar da taje.
"Ta gano cewar Ashe ta tafka babban KUSKURE nakin ba wa innan bayin ALLAH kulawa'
" Ummu ni Kaina ban kyauta wa magaji ba yakamata insanar da ke matsayin shi kodan
ki shiga jikin su suji sauki suma Amma Banyi ma dan uwa na Adalci ba na gane
KUSKURE NA a kan hakan yanzu'
"Tayi saurin rungume ta Bakida laifi my kakus nice mai laifin da naki Sakin jiki
dasu Amma daga yanzu zan basu kulawa sosai kodan in rage musu damuwa,
" Da kanta ranar ta shirya ta Debi Abinci mai dan yawa tasa a kula ta nufi gidan su
" Magajin na shinfide a bakin icen da ke gidanshi Gwaggo Amina na gefe tanata yimai
fifita
Gaba daya taji ba dad'i sunyi mugun bata tausayi ta manta rabonta da takawa taje
gidan tunda tayi wayo"
"Su Kansu sunyi mamakin ganinta " ta gaishe su cike da jin kunyar su" ya mai
jikin ? Ta fada batareda ta kira sunan shi ba kamar y'anda tasaba fada'
"Ya Amsa cike da jin dad'i ina yaya take Ummu? " tana nan zuwa Anjima kadan'
" saboda rashin sabo tarasa y'anda zatayi ganin wanke wanke a gefen rijiya ta mike
cike da jin kunya ta kwabe hijabin ta tafara wankewa duk da gwaggo Amina tace ta
bari Almajiri zaiyi'
"Bayan ta gama ta share gidan tas har ma da dakin gwaggo Amina duka ta gyare gidan
yafito tsab duk da itama Gwaggo Amina ba laifi Akwai tsaftar"
"Sunyi matukar farin ciki ganin gudar jinin su yau a cikin gidan su har tana musu
hidima,
" Haka Hajiya ta sameta ta sake sosai harda y'ar hirar ta suka zauna cikin farin
ciki tareda dauke wa juna kewa,
"Kasan cewar unguwar su daya saidai d'an tazara dake tsakanin su yasa suka kai
karfe goma kafin su dawo gidan su,
" tayi matukar farin cikin kasan cewar ta a cikin kakanin ta a yau jinta takeyi A
cikin ni shad'i,
"Tana dawowa ta janyo wayarta taga miss call ba iyaka daga bature sannan kuma da su
hajara,
" nan take tayi dialing number hajara " tana d'auka ta sa mata ihu" sai Matar
bature """""
"Tayi saurin cire wayar a,kunnen ta " Zaki ciremin dodon kunne" sory Amaryar turawa
dama yaya nasir ne yasani gaba inbashi numbar ki shiyasa nakiraki domin inkarbi
izini
Kuma kinsan ni ina team bature don haka bazamu bada numbar ba ta katse kiran kit"
"Sakin baki tayi kawai tana kallon wayar tare kuma da mamakin halin hajara,
" Tayi ta kallon nubar shi kamar tana son ganin wani Abu a cikin numbar daga baya
ta wurgar da wayar gefe tayi baccin ta"
"Gaba daya hankalin shi a tashe yake ga wannan mayyar da Momyn shi takawo gaba daya
ta hana mai ruwa gudu gashi yau kwana biyu baisa Farin cikin shi a idoba,
" Hajiya da Kanta tayi cigiya wai bataga bature ba kwana biyu ko lafiya?
"Tana jinta sarai ta kyaleta Amma duk lokacin da zata wuce sai ta kalli kofar dakin
nashi,
" Wai da gaske yakeyi bazai kuma dawowa gidan ba? Takewa kanta tanbaya?
Batason tuna nin shi da take faman yi dole ta daukar wa kanta,mataki,
Fitowa yayi cikin gayu irin na samarin da sukejin sunkai kuma sun cika maza yana
sanye cikin farin tree quarter hade da Riga Armless Mara hannu ya sanya tsadaddiyar
facing cap mai dauke da sunan new york Kafar shi ta kalmin da yafi kauna ne wato
canvas farare ga lafceciyar waya itama fara a ta kaice komai na jikin shi fari ne
shi baya kaunar kowace kala idan ba fari ba,
"Takunshi yake cikin isa ya shigo falon da iyayen shi ke zaune harma da Linda "
tana ganin shi ta taso cikeda iya yi tarun gume shi tareda manna mai kiss a kumatu,
"Ya dan ture ta kadan tareda daure fuskar shi tamau ya matsa ya gaida iyayen shi
yace musu zai fita ya dawo,
" oh Tnk goodness u are going out so take Linda with you so that she can do
shopping'
"Tayi wani irin karar jin dad'i " tank you mom in low I love shopping,
"Come on Darling let go" tafada cikin zakuwa "bakin ciki kamar yayi ihu ya kalli
uba nshi da ido ya nunamai yayi hakuri suje,
" Yayi kwafa yayi gaba tana biye dashi batareda ya damu da itaba ya fada motar shi
itama ta shige " escort dinshi suka taso yayi saurin tsayar dasu,.
"Ji yakeyi idan har yau bai sata a idoba Akwai damuwa don haka direct f.c.e ya wuce
bai damu da Linda dake gefen shi ba "
"Yayi sa'a suna zaune a wurin zaman su tunda ya kunna kan motar shi ya hangota tana
zuba dariya ita da kawayen ta ga badaya ya shala da kallon ta har saida yaje gab
dasu ya faka motar kamar wani irin mayen karfe ne ke janshi zuwa gareta,
" ya ma manta da Linda dake cikin motar tana ta zuba kamar kanya hankalin shi naga
tauraruwar zuciyar shi,
"Fitowa yayi cike da takunshi na isa kamar wani sarki " Tunda ya faka motar shi gab
dasu su hajara suka fara murna,
"Lokacin da yafito kuwa ita kanta uwar gayyar ta shagala da kallon shi har ma taji
ya burge ta for the first time,.
" Man in white, Hajara tafada a hankali don ya tafi da tunanin su, Sumy kuwa ai ta
kusa suma Shikuwa ai ya shagala da kallon ruhin shi,
"Linda kuwa taji bala'in kishi ganin shi wurin y'an mata " yanzu saboda wa innan
Black's din yake mata wulakan ci?
"Tafito cikin matukar hasala ta nufoshi " tana zuwa batare da tunaniba ta rungume
shi ta baya,
"Oh baby u keep me waiting please am so tired let go back I wants you to massage my
body ,
" ta fada tana mai kara shigewa jikin shi gaba dayan su suman tsaye sukayi suna
kallon Asalin karuwanci,
"Ruman kuwa wani irin kululun bakin ciki ne ya tok'are mata makogwaro
"Kallonta yakeyi yana nazarin yanayin ta yana kuma mai jin bakin cikin Abinda Linda
tayi mai bayan yafara hasko nasara a idanun ta,
" Mikewa kawai tayi ta zari Jakarta ta wuce batareda tace musu komai ba " wani irin
numfashi yaja tareda hankade Linda
"Ya mata wani irin mugun kallo " find your way before I come back if not u will
gate it from me.
"Ya bita cikin sauri yasha gaban ta " tayi saurin dagowa "idanun ta sunyi mugun ja
cikeda masifa ta dago kanta suka kalli juna cikin ido,
" out of my way"' ta furta cikin hasala " bazan matsaba sai kinfadamin Abinda ya
bata miki rai"
"Wallahi zan maka wulakanci idan baka matsaba " koda yake bakasan mutum Ciba domin
hanyar da mutunci yabi kai baka bishiba,
"Tunda ka nunawa duniya kai tantiri ne har kake yawo da karuwa wadda tafi ka girma
da kuma shekaru,
" yanzu na fahimta wato saboda kana tarayya da manyan mata shiyasa kake tunanin
nima zakayi dani?
"Listing nafi karfinka kai Bakayi kosawar da zaka ce nice dai dai dakai ba Am far
beyond ur imagination,
" kallon kinyi KUSKURE kawai yake yimata cikin murmushin karfin hali " Roman Kinfi
karfina? Haka kika ce?
"Kintaba ganin mace tafi karfin namiji? Eh ni nafi karfin ka karubuta ka Ajiye
hakan'
" Hmmm time will tell Ruman nidai ba ruwana my fan's tana bukatar huduba muje zuwa
yanzu aka fara.......✍
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
~Dedicated to~
All my fan's
_ina mai baku hakuri da rashin jina da kukayi sakamakon rashin wutar da muka samu
Amma yanzu Alhmdulillah komai normal,bawai saboda rashin comments bane yasa kukaji
shiru bazan taba yin hakan ba kamar yadda wasu sukayi tunani har ma sukayi sharhi
akan cewa basu San me zasuyi su burge writers ba a kullum suna complained akan
rashin comments ina so ku fahim ci wani Abu comments dinku yana da Amfani a wajen
writers sosai domin yana kara mana karfin guiwa Sann kuma da comments dinku ne muke
samu yi muku typin har ma da gyaran kura kuran mu don haka ina neman Afuwa ga
w'anda na batawa rai masoya a koda yaushe ina Alfahari daku nagode_
➡7⃣
Tun dawowar ta daga school takejin zazzabi na rufeta ita kadai tasan y'anda takeji
A cikin zuciyar ta,
Ganin Wankin hula zai kaita dare yasa ta nemawa kanta mafita ta,
" Washe gari sun tashi da jimamin rashin lafiyar Magaji don haka kawai ya yanke
jiki ya fadi ' hankalin Hajiya yayi mugun tashi tayi mugun rudewa,
"Gwaggo Amina ce mai kwantar mata da hankali wato Matar magajin " Yaya kiyi hakuri
da izinin ubangiji ba Abinda zai samu baban ja'afar,
"Tana share hawaye tace " Amina shikadai nake gani inji sanyi shikadai ya rage min
"ya'yan namu guda biyu duk sun guje mu saboda mace,
" Kiyi hakuri kidaina zubar da hawayen ki akan su ni kaina na cirewa kaina tunanin
wannan yaron ai duniya ce ta ishi kowa Riga da wando,
"Gashi Muhammadu tun Auren shi da yarin yar nan balkisu baifi sau biyu ya zo gida
ba ko tunanin y'ar marainiyar ALLAH bayayi,
" Daina tunamin Amina ni yanzu zuciya ta tafi kar kata da dawowar ja'afaru ko
hankalin d'an uwa na zai kwanta,
"Nasan komai yakeyi yana yin shine a cikin karfin hali Amma abin na cin shi a
zuciya,
" Ita kanta gwaggo Aminar karace irin ta ba haushe Amma Abun na cimata tuwo A
kwarya'
"Ruman da Shigowar ta kenan taji wannan zancen hankalin ta ya tashi sosai da jin
wannan irin labari,
" tana bukatar Karin haske don haka har matsuwa tayi gwaggo Amina ta tafi taji
Karin bayani,
"Tunda ta gai shesu ta shigewa war ta cikin dakin ta cike da tunani kala kala'
" Kallon ta takeyi cike da sanyin jiki tayi Ajiyar zuciya cikin damuwa tace'
"D'an uwan mahaifiyar ki shima tun lokacin da yatafi karatu kasar turawa ya hadu da
wata baturiya ta mallake mai tunani bai kuma wai wayo mu ba,
" Saboda mun nuna mai KUSKUREN shi na Auren shi da Ahalil kitabi Akwai lada aciki
kuma Addinin mu baiyi hani ba Amma Akwai kalubale da yawa da mutum yake fuskanta ko
akan tarbiyar yaran su,
"Nidai har yanzu kaina na cikin duhu " naji kunce d'an magaji ne," eh shine
mahaifin Aisha wato mahaifiyar ki,
"Amma mai yasa baki taba fadamin kaka na bane? " kaji mun shirme ko da can ba kakan
ki bane shi?
"Aa Hajiya shima bai taba nuna min Akwai kusan ci mai karfi tsakani na dashi ba,
" Ba ma wata shakuwa a tsakanin mu har ma ina nuna mai tsana ban San cewa shi ya
haifi mamana ba'
"Kuma duk hakan tafaru ne sanadiyyar nuna son kudin shi da yakeyi a fili'
" Wani irin murmushi tayi irin na manya " Ummu' takirata da murya mai ma anoni da
dama'
"ALLAH ne gatan mu magaji dan uwana ne gatan mu duk Abinda yakamata a ce mahaifin
ki yayi mana shine duka ya dauke duk da shekarun shi kuwa'
"Duk hidimar makaran tar ki shine da wahalar shi da yakeyi Ruman kin taba tunanin
waye yake tallafa mana kuwa?
" kina tunanin da wannan sana'ar ce kawai nake baki gatan da kike samu?
"Magaji yazame min d'an uwa yazame min kani ya zamemin yaya yakuma zama min uba duk
da yana kanina,
" Duk tsawon shekarun nan Ummu magaji yana cikin rashin babban danshi kuma ga
mahaifiyar ki ita ma ta tafi gashi dagani har shi ba wani zuri'a garemu ba,
"Shi guda dayar ta tafi shi kuma w'anda ya kamata ya kula dashi ya yi nisa bayajin
kira kamar mahaifin ki'
Ta karasa tana mai share hawaye " Ummu Ruman jikinta yayi mugun sanyi sai yanzu ta
gane meyasa Gwaggo Amina ke yawan kallon ta a duk lokacin da zasu hadu gashi duk
y'anda Hajiya kaka zata matsa mata da zancen zuwa gidan su bata y'ar da taje.
"Ta gano cewar Ashe ta tafka babban KUSKURE nakin ba wa innan bayin ALLAH kulawa'
" Ummu ni Kaina ban kyauta wa magaji ba yakamata insanar da ke matsayin shi kodan
ki shiga jikin su suji sauki suma Amma Banyi ma dan uwa na Adalci ba na gane
KUSKURE NA a kan hakan yanzu'
"Tayi saurin rungume ta Bakida laifi my kakus nice mai laifin da naki Sakin jiki
dasu Amma daga yanzu zan basu kulawa sosai kodan in rage musu damuwa,
" Da kanta ranar ta shirya ta Debi Abinci mai dan yawa tasa a kula ta nufi gidan su
" Magajin na shinfide a bakin icen da ke gidanshi Gwaggo Amina na gefe tanata yimai
fifita
Gaba daya taji ba dad'i sunyi mugun bata tausayi ta manta rabonta da takawa taje
gidan tunda tayi wayo"
"Su Kansu sunyi mamakin ganinta " ta gaishe su cike da jin kunyar su" ya mai
jikin ? Ta fada batareda ta kira sunan shi ba kamar y'anda tasaba fada'
"Ya Amsa cike da jin dad'i ina yaya take Ummu? " tana nan zuwa Anjima kadan'
" saboda rashin sabo tarasa y'anda zatayi ganin wanke wanke a gefen rijiya ta mike
cike da jin kunya ta kwabe hijabin ta tafara wankewa duk da gwaggo Amina tace ta
bari Almajiri zaiyi'
"Bayan ta gama ta share gidan tas har ma da dakin gwaggo Amina duka ta gyare gidan
yafito tsab duk da itama Gwaggo Amina ba laifi Akwai tsaftar"
"Sunyi matukar farin ciki ganin gudar jinin su yau a cikin gidan su har tana musu
hidima,
" Haka Hajiya ta sameta ta sake sosai harda y'ar hirar ta suka zauna cikin farin
ciki tareda dauke wa juna kewa,
"Kasan cewar unguwar su daya saidai d'an tazara dake tsakanin su yasa suka kai
karfe goma kafin su dawo gidan su,
" tayi matukar farin cikin kasan cewar ta a cikin kakanin ta a yau jinta takeyi A
cikin ni shad'i,
"Tana dawowa ta janyo wayarta taga miss call ba iyaka daga bature sannan kuma da su
hajara,
" nan take tayi dialing number hajara " tana d'auka ta sa mata ihu" sai Matar
bature """""
"Tayi saurin cire wayar a,kunnen ta " Zaki ciremin dodon kunne" sory Amaryar turawa
dama yaya nasir ne yasani gaba inbashi numbar ki shiyasa nakiraki domin inkarbi
izini
Kuma kinsan ni ina team bature don haka bazamu bada numbar ba ta katse kiran kit"
"Sakin baki tayi kawai tana kallon wayar tare kuma da mamakin halin hajara,
" Tayi ta kallon nubar shi kamar tana son ganin wani Abu a cikin numbar daga baya
ta wurgar da wayar gefe tayi baccin ta"
"Gaba daya hankalin shi a tashe yake ga wannan mayyar da Momyn shi takawo gaba daya
ta hana mai ruwa gudu gashi yau kwana biyu baisa Farin cikin shi a idoba,
" Hajiya da Kanta tayi cigiya wai bataga bature ba kwana biyu ko lafiya?
"Tana jinta sarai ta kyaleta Amma duk lokacin da zata wuce sai ta kalli kofar dakin
nashi,
" Wai da gaske yakeyi bazai kuma dawowa gidan ba? Takewa kanta tanbaya?
Fitowa yayi cikin gayu irin na samarin da sukejin sunkai kuma sun cika maza yana
sanye cikin farin tree quarter hade da Riga Armless Mara hannu ya sanya tsadaddiyar
facing cap mai dauke da sunan new york Kafar shi ta kalmin da yafi kauna ne wato
canvas farare ga lafceciyar waya itama fara a ta kaice komai na jikin shi fari ne
shi baya kaunar kowace kala idan ba fari ba,
"Takunshi yake cikin isa ya shigo falon da iyayen shi ke zaune harma da Linda "
tana ganin shi ta taso cikeda iya yi tarun gume shi tareda manna mai kiss a kumatu,
"Ya dan ture ta kadan tareda daure fuskar shi tamau ya matsa ya gaida iyayen shi
yace musu zai fita ya dawo,
" oh Tnk goodness u are going out so take Linda with you so that she can do
shopping'
"Tayi wani irin karar jin dad'i " tank you mom in low I love shopping,
"Come on Darling let go" tafada cikin zakuwa "bakin ciki kamar yayi ihu ya kalli
uba nshi da ido ya nunamai yayi hakuri suje,
" Yayi kwafa yayi gaba tana biye dashi batareda ya damu da itaba ya fada motar shi
itama ta shige " escort dinshi suka taso yayi saurin tsayar dasu,.
"Ji yakeyi idan har yau bai sata a idoba Akwai damuwa don haka direct f.c.e ya wuce
bai damu da Linda dake gefen shi ba "
"Yayi sa'a suna zaune a wurin zaman su tunda ya kunna kan motar shi ya hangota tana
zuba dariya ita da kawayen ta ga badaya ya shala da kallon ta har saida yaje gab
dasu ya faka motar kamar wani irin mayen karfe ne ke janshi zuwa gareta,
" ya ma manta da Linda dake cikin motar tana ta zuba kamar kanya hankalin shi naga
tauraruwar zuciyar shi,
"Fitowa yayi cike da takunshi na isa kamar wani sarki " Tunda ya faka motar shi gab
dasu su hajara suka fara murna,
"Lokacin da yafito kuwa ita kanta uwar gayyar ta shagala da kallon shi har ma taji
ya burge ta for the first time,.
" Man in white, Hajara tafada a hankali don ya tafi da tunanin su, Sumy kuwa ai ta
kusa suma Shikuwa ai ya shagala da kallon ruhin shi,
"Linda kuwa taji bala'in kishi ganin shi wurin y'an mata " yanzu saboda wa innan
Black's din yake mata wulakan ci?
"Tafito cikin matukar hasala ta nufoshi " tana zuwa batare da tunaniba ta rungume
shi ta baya,
"Oh baby u keep me waiting please am so tired let go back I wants you to massage my
body ,
" ta fada tana mai kara shigewa jikin shi gaba dayan su suman tsaye sukayi suna
kallon Asalin karuwanci,
"Ruman kuwa wani irin kululun bakin ciki ne ya tok'are mata makogwaro
"Kallonta yakeyi yana nazarin yanayin ta yana kuma mai jin bakin cikin Abinda Linda
tayi mai bayan yafara hasko nasara a idanun ta,
" Mikewa kawai tayi ta zari Jakarta ta wuce batareda tace musu komai ba " wani irin
numfashi yaja tareda hankade Linda
"Ya mata wani irin mugun kallo " find your way before I come back if not u will
gate it from me.
"Ya bita cikin sauri yasha gaban ta " tayi saurin dagowa "idanun ta sunyi mugun ja
cikeda masifa ta dago kanta suka kalli juna cikin ido,
" out of my way"' ta furta cikin hasala " bazan matsaba sai kinfadamin Abinda ya
bata miki rai"
"Wallahi zan maka wulakanci idan baka matsaba " koda yake bakasan mutum Ciba domin
hanyar da mutunci yabi kai baka bishiba,
"Tunda ka nunawa duniya kai tantiri ne har kake yawo da karuwa wadda tafi ka girma
da kuma shekaru,
" yanzu na fahimta wato saboda kana tarayya da manyan mata shiyasa kake tunanin
nima zakayi dani?
"Listing nafi karfinka kai Bakayi kosawar da zaka ce nice dai dai dakai ba Am far
beyond ur imagination,
" kallon kinyi KUSKURE kawai yake yimata cikin murmushin karfin hali " Roman Kinfi
karfina? Haka kika ce?
"Kintaba ganin mace tafi karfin namiji? Eh ni nafi karfin ka karubuta ka Ajiye
hakan'
" Hmmm time will tell Ruman nidai ba ruwana my fan's tana bukatar huduba muje zuwa
yanzu aka fara.......✍
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love Destiny_
_Written by Fenerh_
✍✍✍✍✍✍✍
GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION
✍✍✍✍✍✍✍✍
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
~Dedicated to~
All my fan's
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love Destiny_
_Written by Fenerh_
*Allahu Akbar Kullu nafsin za'ikatul maut Allah ya gafar ta miki Aisha Allah yasa
mutuwa ta ka sance Hutu a gareki*
_Masoya littafi na ina godiya da Addu oin ku a gareni da masu yimin magana ta prvt
ba Amsa don Allah Kuyi min uzuri karku ce ina yi muku wula kanci abubuwan ne da
yawa ina neman Afuwa👏_
8 8
➡8⃣
Ta wuce shi cikin sauri yana mai bin bayanta da idanu " y'anda take tafiya cikin
natsuwa amma ko ina na jikin ta na motsawa
"Juya wa yayi cike da bacin ran Linda, ta bata mai shiri "Ya nufi wurin su Hajara
dake tsaya kamar stature Suna kallon drama,
" Hannu ya fara mikawa Sumy "Hlo Sumy how are you?
" Jikin ta na rawa har tayi nisa ta tsaya kallon su "Hy batur......
"Bature? Is that my name? Ya fada cikin murmushin shi mai tsada, su Kansu dariya
suka sa'
" Cikin jin kunyar shi hajara ta ce" we don't no your name that is why we call you
with that name,
"Ya kuma yin murmushin " OK no problems my friend, by the way Am Abdullah"
"Gaba dayan su sunyi shocked da jin sunan don Sam basu zata hakan ba,
" Cikin Sakin baki suka ce " wow Abdullah nice to meet you tareda shaking hannun
shi dukansu'
"Hajara da baki baya shiru ta kalle shi " to meyasa kullum sai inga motocin ka
Anrubuta J Abayan su we thought...... Tafada tana mai son jin kwakwaf,
"Ya d'an yi dariya kadan tareda waigawa wurin da mutu miyar ta tsaya, duk Abinda
sukeyi idanun ta nakan su gaba daya jin ta takeyi a takure har su hajara sun bata
mata rai
" ya ma za ayi su wani rikewa namiji hannu kirjin ta har zafi yakeyi'
"Cikin fushi ta shige warta Aji batareda lokacin shiga daukar lecture yayi ba,
" Har Aka tashi a makaran ta ranar bata kuma sauraran su hajara ba sai wani matse
musu fuska takeyi "suma da yake sun iya sai kawai suka shareta '
" Da mamakin ta yana zaune a saman motar shi koda suka fito direct suka nufe shi,.
"Tana gefe gaba daya hankalin ta na kansu sukuwa sun saki jiki sosai sai hira suke
kwasa daga baya ma motar shi suka shige hajara na gaba kasan cewar yau driver ya
kawota don haka suka wucewar su,
" Saida suka fita ya kalli hajara " Friend kina tunanin hakan shine dai dai?
"Trust me my friend that's is the right idear just watch and see"
"A sanyaye ya kalle ta Am scared banaso inrasa friend dinki idan na rasata
numfashi na zai iya tsaya wa,
" Wai don ALLAH ni yaro ne? Kallon shi tayi cikin tausayi domin tarasa Amsar da
zata bashi'
"Meyasa ita kadai take ganin yarin tata? Meyasa take tunanin tafi karfina? Meyasa
take ganin kamar bazan iya bata kulawa ba?
" Ni nasan nine dai dai da ita ni nasan zan iya mata zan bata gata fiye da tuna nin
ta,
"Ya karasa cike da damuwa " friend u no it's hurt me A lot when I saw her with
another man,
"Inada kishi mai zafi Akanta I can do Anything bcos of your friend"""
"Gaba dayan su tausayin shi ya cika musu zuciya " yaro danye sharaf ALLAH ya
jarabce shi da son mace mai murd'adden ra ayi, mace mai kafiya,
"Sumy harda hawaye ta goge ya juya gefen ta su " ina zamu nufa?
" tace ikon Allah ne yasa tana mai Jim farin ciki har suka sauke Sumy itama ya
kaita nasu gidan tareda nuna mata gidan su cike da mamaki take kallon gidan don
kusan kullum sai sunyi maganar wannan gidan
"Don yafi kowane gida dake unguwar haduwa kuma basu taba kawo cewar Akwai mutane a
ciki ba,
" Ruman kuwa bayan tafiyar su gaba daya ranta ya gama baci " su hajara sun bata
mata rai sosai " yanzu saboda wani banza can daban zasu wuce su barta?
Ko a gida Hajiya takasa gane kanta A ranar daga baya ma shirya wa tayi kawai tayi
wuce warta gidan su magaji,
"Gwaggo Amina saida ta tanbaye ta" Ummu yau lafiyar ki kalau kuwa?
"Tace kalau take kawai kanta ke dan ciwo nan kuwa damuwa ce fal cikin ranta'
" Washe gari kuwa da wuri ta wuce makaranta duk da yau ta tashi cikin mugun yanayin
marar ta har ciwo takeyi kadan kadan saboda rashin baccin da batayi ba sosai da
dare tana ta faman juyi da kuma tunani'
"Abdullah kuwa bayan komawar shi gida ya tarar da fadan Momy sosai " yi yayi kamar
ma baisan mai yafaru ba cike da jin haushin Linda dake zaune tana matsar hawayen
munafurci,
"Yace " Momy please I beg of you tell this girl to stay away from my life I don't
wants her please """ ya fada tareda hade hannun shi'
"Wani irin tasowa tayi zata nufoshi yayi saurin daka mata tsawar da dole ta koma
jikin Momy ta lafe,
" Ya matsa kusa da ita kamar zai fisgota jikin shi har rawa yakeyi'
"Stay away from my life or else you will regret, I don't love you or any of ur
stufidity,
" Momy please tell her to go back from ware she came from we don't needs her hare,
"Oh come on my boy don't say that u no why Linda is here she is hare to help you I
didn't forced you to love her or Mary her she is here to satisfied your needs I
don't wants you......
" oh stop Momy what are you saying ?how many times Dady told you that is prohibited
in our religion,
"Wani irin firgita tayi tare da zabga mai wani irin kyakkyawan mari " Jeff ta fada
jikin karfi sunan da ya dade baiji takira ba,
"Tsawon rayuwar shi " Ruman ce ta fara dora mai hannu tunda yake da iyayen shi basu
taba dukan shi ba har dai Momyn shi da bata son komai ya same shi yau itace da
kanta ta mare shi,
"Wasu irin hawaye ne masu ciwo suka fara bin kuncin shi, ita kanta Linda jikinta
yayi sanyi,
" Jeff are you going to followed your father religion? tafada cikin karyewar
zuciya,
"Cikin dauriya da kuma dakewa yana mai kawar da fuskar shi gefe" yes mom.....
Saurin daga mai hannu tayi " don't call me that,
"I no why, is All bcos of ur stupid dream girl, yayi saurin matsawa kusa da ita
tareda riko hannun ta " Momy noooo"
"U hv to understand" I realized Islam is the true religion I have been research All
that long,
"Just stop I don't won't to listing, "now listing to me carefully I want let you do
that,
" cikin zafin zuciya ya matsa gefe tareda share hawayen shi "u don't have the right
to stop me Momy and I will Mary my dream girl insha ALLAH with you or without y....
" marin da ya kuma ji ne ya dawo dashi cikin hayya cin shi ya dafe kumatun shi
cikin tsananin mamakin w'anda ya mareshin,
"Cikin fushi ya nufi Matar shi tareda fara lallashin ta tayi saurin tureshi tafara
zazzaga mai bala'i da cewar ya zuge mata yaro zai koma Addinin shi bayan ba haka
yayi mata Alkawari ba'
" Kallon mamaki Abdullah yabi uban dashi "Dady u promised her? Hmmm yayi wani irin
murmushi mai ciwo ya goge hawayen fuskar shi zuciyar shi na suya"
"I understand Dady meyasa zakayi haka " har yanzu Ashe baka gane "KUSKUREN ka ba
Dady? Kamar y'anda kake fadamin
" Dady na gane ina wahala ne sakamakon zunibin da ka Aikata yake wahalar dani yana
daya daga cikin dalilin da yasa ni na dawo Nigeria saboda hakan ne kawai zai sa ku
dawo Nigeria Amma hakan Sam bai yimin Amfani ba,
"Kumin Alfarma kai da Momy please ku tattara ku koma inda kuka fito I don't needs
you here you are just increasing my problems,
" uban ya daka mai tsawa shi kuwa ko gezau ya kama hanyar waje batareda ya kuma
cewa komai ba'
"Wani irin kuka uwar tasa mai cin rai Dadyn ya fara lallashin ta ita kanta Linda
kuka takeyi tana mai tausayin wannan familyn ita kam dole ta koma inda tafito don
tasan batada sauran Amfani,
Don tasan bazata taba samun Abinda takeso ba gashi ta saba da harka kwana biyu An
tauyeta,
Shiya gari na wayewa ta hada kayanta tabi mota zuwa Abuja kafin lokacin tashin
jirgi,
" yana fita Ya wuce Zaria hotel ya kama daki a nan ya kwana duk da baya kaunar
zaman hotel,
Da sassafe ya nufi kofar gidan su Hajara lokacin dai dai tafito zata tafi maka
ranta tana ganin shi ta fara'a Amma ganin yanayin da yake ciki jikinta yayi sanyi,
"Ta bude kawai ta shiga ganin baya cikin yanayi mai kyau kawai gai suwa sukayi ya
tuka batareda yace mata komai ba'
"Ruman na zaune Alokacin ciwon nata yafara damunta sosai har wani gumi take
karyowa'
" Tunda ya dora idanun shi akanta yasan batada lafiya cikin sauri ya faka motar shi
yafito batareda ya kulle ba ya nufeta da gudun shi kasan cewar makarantar bawasu
mutane bane suka taru shiyasa ba w'anda ya lura da halinda take ciki,
"Zama yayi A gefen ta jikin shi na rawa ya riko hannun ta Roman " lafiyar ki? Meke
damunki? Duka ba tanbaya sai cije lebe takeyi idanunta sunkada sosai saboda Azaba'
"Hajara ta karaso itama cike da rudewa " Queen "" lafiya? Meke damun ki " Cikina
tana mai kokarin zamewa kasa ya rikota tareda mikewa ya dagata cak kamar y'ar
tsana,
"Bayan motar shi ya ce hajara tabude mai ya sakata Aciki " ya gyara mata kwanciya "
sannan ya kulle "
"Cikin sauri ya shiga tareda karbar jakar ta A hanun Hajara " bai jira komai ba ya
fisgi motar ya fita batareda ya kuma sauraran hajara ba,
"Taso ta bisu taga halinda kawarta ke ciki Amma ina ya wuce Abinshi da ita'
" Bai tsaya da ita ko inaba sai Zaria hotel dakin da ya kama ya kinkimeta saida ya
shinfide ta a kan gadon sannan ya cire dogon hijabin dake jikinta,
"Wani irin harbawa zuciyar shi tayi " Domin ganin zunzurutun shape dinta da ya
bayyana A zahiri kasan cewar tana sanyeni da doguwar rigar Atanfa dinkin zamani ya
kamata dam daga sama har yana hango layin nonuwan ta da suka kunburo rigarta kamar
zasu fasa kirjinta,
"Wani irin numfashi yaja tareda dafe marar shi "za ayi biyu kenan ya furta a
hankali' wata irin kara ta sanya tareda wani irin juyi Wanda saida ya juya da
lamarin tunanin shi gaba daya har ma da zuciyar shi yakarasa cikin karyewar zuciya
ya rungumo ta zuwa kirjin shi,
Atare suka sauke Ajiyar zuciya yakai hannun shi saman wuyanta ya shafo wani irin
hucin zafi jikinta kefitar wa " Oh my god" ya furta hawaye na zubowa a idanun shi ,
"Ajiyeta yayi a hankali yashiga bathroom ya fito dauke da wata yar roba da ruwa
hannun shi rike da karamin towel ya Ajiye akan side drowe din gadon...........✍
*Kuyi hakuri da irin turancin dan koyo my fan's please managed Anyi mana Rasuwa ne
A makota muna baran Addu'ar ku*
_kucigaba da biyo_
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
~Dedicated to~
*My Zinariya*
*ina mugun yinki my Real gold Zinariyar Golden pen jinjina ta mu samman Allah yabar
min ke*
✍✍✍✍✍✍✍
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*
✍✍✍✍✍✍✍
_Written by Fenerh_
9 9
➡9⃣
" W'anda a lokacin ne ta danji saukin lafawar ciwon har tafara yunkurin mikewa
zaune tana mai dafe gefen cikin ta,
" Ta ware idanun ta a dai dai lokacin da ya dora tafin hannun shi mai laushin gaske
a kan fuskar ta yana kokarin goge mata hawayen,
"Nan da nan ta matsa nesa dashi tareda watso mai wani irin kallo, Wai meye haka ne?
Sai Alokacin ta Ankare da inda take tayi saurin dira daga kan gadon har tana
kokarin burgewa,
" Da hanzarin shi ya cafko ta zuwa jikin shi "kin gani ko da yanzu bana kusa irin
wannan mikewar da kikayi sai kifadi,
" Ta fara kici kicin fisge jikinta Amma ina ya riketa tamau har wani Ajiyar zuciya
yake sauke wa jinta a cikin kirjin shi,
"Kuka kawai ta saka mai mai dan karfi ta fara dukan kirjin shi " Wai menene kake yi
haka bana son iskan ci na fada maka " ka daina tabani idan har ka saba taba yan
iskan yan matan ka to ni ba irin su bace,
"Tana fada tana kokarin ture shin" Shshshhh relaxed Princes ki natsu jikin ki ba
karfi ki bari in nema miki saukin zafin jikin nan don ALLAH,
"Ya furta dakyar don shi gaba daya jinta Acikin jikin shi ya gama sauya mai yanayi,
" Ka sake ni ka daina tabani' impossible ke ma kinsan bazai taba yuwu wa ba idan
ban taba ki ba wa zan taba?
"Cikin zafin rai ta furta kawruwan ka, murmushi kawai yayi " Baby a Gaskiya zakiyi
kishi sosai ,
"ALLAH ya kiyaye inyi kishin ka ai sai ka damu da mutum zaka yi kishin shi,
" Yanzu bakya tausayin Rayuwata? Na gaji wallahi nagaji ki tausaya min ki sassauta
ma Rayuwata baby,
"Ya furta yana mai kara matse ta a kirjin shi duk da ta takure jikinta ta tokare
shi bai hana shi matse ta gam ba kamar zata gudu"
"Banki mu dawwama a haka ba " zanso ki taimaki rayuwar mu dukkan mu muna bukatar
juna,
" ke kanki kina bukatar Auren nan princess ki bani goyon baya cikin lokaci kadan
zancire miki wannan ciwon domin ni kadai keda maga nin shi
"Wani irin karfi taji tareda tunkude shi " wai don ALLAH kai wane irin yaro ne
haka? Nace bana sonka bazan Aure ka ba dole na?
"Tuni zuciyar shi ta kunburo shi cikin zafi ya rikota tareda manna ta a jikin ginin
dakin,
'Yana huci " Dole ki soni dole ki Aure ni kuma am warning you kar inkuma kuma ganin
ki tare da wani namiji inba haka ba Wallahi kinji rantsuwa zanyi miki Aikin
yarintar da kike kiramin,
"Ki Aure ni shine maslaha inba haka ba wallahi zakiyi Dana sani na har Abada,
" Tana mutsu mutsu still bakinta bai mutu ba "Nace bazan Aure ka ba do your worst,
" Kuma a gaban idon ka zanyi Aure kana gani watch and se.....
"Carab ya rike lebenta da hakorin shi ya dan ciza da karfi ta saka karar wuya kafin
ta dawo dai dai ya karasa da bakin shi cikin nata yayi sa'ar samun harshen ta mai
laushi ya cafke kamar lolipop ya fara tsotsa yana fitar da wani irin numfashi mai
zafi saboda tsabar kishi dake cinshi kuma ga tsantsar sha'awar ta dake manne da
gangar jikinta,
" jikinta yayi lakwas ta ma kasa kwatar kanta daga jikinshi tsotsar ta yakeyi a hau
kace kamar zai cinye mata bakin,
"Kukan da ta sakane yasa shi sararawa daga dogon zangon da yafara zuwa, jikin shi
ya mutu murus tasamu ture shi ya fadi a gefe tareda dafe kanshi idanun shi jajur,
" Wallahi banyafe maka ba ta watsar da miyan bakinta tareda goge wa ALLAH ya isa
d'an iska kawai ina da na sanin ranar da na fara ganin ka wallahi meyasa kake so ka
shiga Rayuwata?
"Cikin tsananin jin zafin zagin da ta surfa mai yasashi saurin mikewa ya kuma
nufota gadan gadan,
" Ni kike zagi Roman? Nagode, Saboda kawai ina sonki kike yimin wulakan ci? Na
farko kina fadamin zakiyi Aure da wani kato agabn idona ya furta yana runtse idanun
shi saboda jin zafin wannan furucin,
"Nayi kissing dinki ne saboda inkoya wa bakin ki ladabi kar ki kuma kiramin sunan
wani namiji da sunan zaki Aura idan har bani bane'
" Inada matukar kishi akanki ke tawa ce ni kadai Wallahi Roman Duk ranar da kikayi
KUSKUREN Auren wani namiji to saidai kije da Cikina jikin ki
"Gidan kowaye kuma wallahi zamu je gidan tare, ke nifa idan naso zandauke ki inbar
kasar nan dake wallahi ba w'anda zai kuma ganin ki zamuje Muyi rayuwar mu dagani
sai ke sai yarana da zaki haifamin
" Kallon baka isaba kake yimai, shikuwa ya dage sai zuba mata ruwan bala'i yakeyi
karo na farko da ta hasala shi har ma yarasa Abinda zai furta mata yafara zubo mata
shirme"
"Ke ko uwata ce ke tunda ina sonki I don't care kuma dole kisoni,
" Haba don ALLAH so kike ki kasheni kinaso ki samun ciwon zuciya ne na daure na
kusan shekaru ina neman ki kuma bayan na ganki kinaso ki bijirewa zuciyar da ta
taso cikin mafarkin mallakar ki kece kika raini zuciya ta ta yaya kike ganin zan
iya Rayuwa batare dake ba?
"Ya durkushe a gabanta ya samata kuka mai ciwo " Ina cikin damuwa mai dinbin yawa
Ki sasauta min please nagaji""""""
"A zahirin Gaskiya taji tausayin shi Amma batajin zata iya Amince mai ganin Wankin
hula zai kaita dare yasata Sauke Ajiyar zuciya,
" Naji Yanzu ina ka kawoni? " muna Zaria hotel, ya furta a takai ce " kallon shi
tayi ida nunta a waje " Hotel? Innalillahi wa inna ilaihirraju un,
Nan da nan bacin ranta ya dawo sabo " kazo ka mayarda ni inda ka dakko ni mikewa
yayi tareda kallon ta " cikin ya daina ciwo?
"Eh ka mayarda ni, are you sure? Yes please take me back,
" Saina duba lafiyar ki Kayimin wannan Alfarmar inaso inyi checking dinki,
"Mikewa kawai yayi tareda karasa wa kan wani dan karamin table ya janyo brief case
dinshi na aiki wata y'ar Karamar na ura ya dakko ya kunna ta mai kamar computer,
" Kallo kawai take bin shi da shi " ki kwanta, ya furta ko baki y'arda dani ba har
yanzu? Wallet dinshi ya dakko tareda budewa ya Ciro mata I D card dinshi,
ya haska mata shi akan fuskar ta Doctor Jeff J ta gani A rubuce tana kallon shi
cikin mamaki dan wannan yaron?
"Jeff? That's means hasashen ta yazama Gaskiya shi ba musulmi bane kenan
subuhanllah Amma Gaskiya ya cuceta da ya hada jikinta mai tsarki tareda nashi mai
najasa,
" Yanzu ne ma takejin ta kara tsanar shi a cikin zuciyar ta wai gawa tayi tareda
kallon inda hijabin ta yake ta fisgoshi ta sanya ta dauki Jakarta ta rataya ta nufi
hanyar fita
"Dan tsaya wa tayi duk yana tsaye yana binta da idanu " a dacan mamaki nakeyi a duk
lokacin da naga kayi wani Abu w'anda ya sabawa Addini Amma a yau na fahimci dalili,
"Rashin sanin hukun cin Addini na yasa kake mun dabi unku na kafirai kuma ya
hudawa, ta Yama zakayi tunanin bin hanyar da nakebi bayan kai ba ita kake bi ba ,
" Ni musulma ce kuma ba haushiya mai cikakkiyar tarbiya da kuma sanin hakkin Addini
na ina rokon ka dakabi hanyar ka inbi tawa gaba daya tsarin ka ya kauce wa Addini
na,
"Gaba daya ta gama birkita mai lissafi ta hanashi koda motsi yakasa koda furta mata
kalma daya,
" Har ta bude kofar ta fita tana maibin harabar wurin da idanu " ALLAH ya isa ta
furta a cikin ranta yanzu saboda iskanci zai kawota Hotel salon wani ya ganta Ayi
mata kallon y'ar iska,
"Kafin ya ce ya saita tuna nin shi ya dawo cikin hankalin shi tuni tafice
Da gudun shi ya biyo bayanta Amma ko inuwar ta bai hango ba ta bace bat,
" Har fitowa yayi yana wai gawa ta ko ina Amma bai hangota ba haka ya juya zuwa
cikin dakin matsaloli sun sakoshi gaba ga damuwar family ga kuma nata da yafi komai
damun shi a halin yazu'
" isarta kofar gidan ta ga bakuwar mota a fake a gefe Amma bata kawo komai ba ta
shigewar ta cikin gidan,
"Tayi sallama a kofar falon nasu cikin sanyin jiki " Aka Amsa jin muryar kakanta
magaji da kuma wata bakuwar murya yasata daga kanta ta fara binsu da idanu gabanta
yayi muguwar faduwa domin ganin mahaifin ta durkushe a gaban Hajiya kamar yana
neman gafara,
"Ta saki idanu ko gaishe su ta gagara yi maganar Hajiya ya dawo da ita cikin hayya
cinta ,
" Ummu kindawo? Shi kanshi sai Alokacin ya kara ware idanun shi akanta " cikin
tsananin farin ciki ya zuba mata idanu yana fitar damurmushin jin dad'i,
" ka ganmu nan muna nan a inda ka barmu ba Abinda ya same mu " Ai dai duniya ce
Muhammadu ta ishi kowa Riga da wando ai ko baka zo ka sauke hakki na na uwa ba
kazo kaga yar marainiyar ALLAH da tayi rashin uwa tun haihuwar ta,
"Don ALLAH Hajiya kiyi hakuri na tuba ki gafar ce ni nakasa daurewa ne bazan iya
daukar rashin Aisha ba Idan har zan zauna a nan hankali na bazai taba kwanciya ba,
" toh yanzu gujewa yar da ta Haifa ta barmaka shine Abinda kake ganin ya dace Ace
kusan shekara sama da goma rabon daka waiwayo mu
"Kana sane dagani har d'an uwa na muna bukatar ku kodan shekarun mu d'an uwanka
ja'afaru har yau bai wai wayo gidaba
" wallahi kubi a hankali hakkin iyaye ba wasa bane don haka ni na gama magana ta
idan kungyara to idan kunki kuwa duniya ce gatanan w'anda ma bai shigo ta ba jiran
shi takeyi,.
"Aa yaya k'arki yimai baki don ALLAH ki gafar ce shi tunda har yagane KUSKUREN shi,
" ni dai ina tsaye ina mai bin mahaifina da idanu idan nace bana bukatar shi a
taredani nayi karya mu samman Yanzu da nake cikin rudu da kuma damuwar zuciya,
"Zonan Ummu ya furta A hankali' cikin natsuwa nafara takawa na karasa kusa dashi
ina isa na fada jikin shi nasa kuka mai ciwo w'anda na rasa na menene?
" Zuciya ta Sam bata min dadi har zafi take yimin akan Abubuwa da dama,
"Hannun shi ya dora A saman bayana yana bubbugawa " kiyi shiru kinji my doughter ki
yafewa babanki nayi KUSKURE ki gafar ceni zangyara duk tsawon lokacin da na d'auka
bama tare da izinin ubangiji,
"Kukan ta karuwa yakeyi ita tasan tana farin ciki da ganin shi duk da cewar tana
fushi da shi sannan kuma a dayan gefen zuciyar ta ta suya a sakamakon Abinda yake
mugun damun ta a halin yanzu,
" ita kanta tasani( she needs a shoulder to cry) don haka yanzu da tasamu dama take
rusa kukanta mai cin zuciya,
"Ummu Hajiya ta kirata" Meya faru Akwai Abinda yafaru dake ne naga lokaci baiyi ba
kika dawo,
"Banajin dadi ne shiyasa na dawo, subuhanllah dukan su suka furta a lokaci daya'
Badai ciwon cikin bane ko? Inji Hajiya
" shine ta furta tana mai tashi daga jikin mahaifin ta" sannu suka fara jero mata
yace " suje Asibiti Adubata " magaji yace ya kamata kam don tana wahala wancan
karon sai da Aka kaita Asibiti,
"Mikewa tayi cikin dauriya tace " naji sauki sosai ai yanzu,
"Toh kije ki kwanta kidan huta Ai yau kina Azumin ko? Cewar Hajiya, ta Amsa da" eh
sai yanzu ta tuna da zancen wai ta tashi da Azumi domin tunjiya takejin Alamar
damuwa kuma gashi ba aje ko ina ba ya karya mata Azumi,
"Don tanajin Ajikin ta har wasu irin ruwa suka fito mata Alokacin da yake kissing
dinta,
" A haka ta shigewar ta daki tabar su a falon tana shiga ta yi wurgi da jakar ta ta
cire hijabin shima ta Ajiye ta fada kan gadon ta tana mai runtse idanunta,
"Ahankali takai hannun ta saman lips dinta tana shafawa saboda wani irin sululi
suke yimata,
"Saboda irin tsotsar da yayi musu " wani irin Yarr takeji tsigar jikinta na mikewa
"wai meyasa suke yimata haka? Don sunga ALLAH ya jarrabeta da lalura suke Amfani da
wannan damar tata ta yawan shawa'aw shiyasa ta tsani Sulaiman A kullum zancen shi
ta Y'ar da suyi Aure ya nema mata lafiya,
" Kwana biyu ta samu lafiya nasir baya gari tasan yana dawowa zai tada zancen Aure
baisan cewa a halin yanzu ita kanta tafishi matsuwa ba,
"A Gaskiya Auren ta shine kawai mafita, to wazata Aura? Tafara tunani Akan Sulaiman
a Gaskiya yayi mata hundred pacent saidai Sam bai kwanta mata ba sai kuma nasir shi
ma ya hadu kuma yakai ta Aure shi kodan Amincin su da Hajara bazataki jinin ta ba,
" Amma me zuciyar ta bata tare da shi ' to tana wurin wa? Jeff kai tsaye Abinda ya
fara zuwa mata kenan A ranta tayi saurin runtse idanun ta
"Is impossible taya ya zuciyar ta zata fada kan soyayyar karamin yaro? Tayaya zata
fada son Arne baya hude ina?
" tayi saurin girgiza kanta bazai yuwuba A Gaskiya ba Gaskiya bane a take ta kara
yanke ma kanta sha wara dole nema ta fisgeshi a jerin tunanin ta "nasir shine kawai
ya dace dani kuma shima daga ganin shi jarumi ne,
" A Gaskiya Aure take so yanzu yana tanbayar ta zata bada kai a wuce wurin ko zata
samu saukin Abun
"Wani irin bugawa k'irjin ta yayi tunawa da tayi da warnin din shi dazu, tsaki
kawai tayi " shirmen banza ta mike cike da kasala ta zame rigar jikinta tana mai
bin kirjinta da kallo ta dan karamin madubin dake banne da bangon dakinta,
"Ita kanta tasan takeru halittar kirjin ta ita kanta burgeta takeyi bare kuma da
namiji,
" Ta dauki lokaci kafin ta daura zani ta zura katon hijabin ta tafito domin tana
bukatar wanka kafin tayi sallar Azahar da takawo jiki,
"Suna zaune a y'anda ta barsu tunda ta fito idanun su suka zuba mata kowane su na
tanbayar ta jikinta " ta Amsa taji sauki,
"Mahaifin ta har wani Annuri yake fitar wa Afuskar shi na ganin gudan jinin shi mai
matukar kama da mahaifiyar ta, fuskar ta na tuna mai da tsohuwar Matar shi da
yarasa,
" Tana fita ya kalli mahaifiyar shi "Hajiya kiyimin izini inje da Ummu Kaduna ta
saba da yan uwanta koda na sati dayane,
" Hmm wato ita Matar ka tafi karfin tazo gidan ku ko?" har ma da yaranta bazasu
zoba sai ita da take babba itace zata bisu ko?
"Aa yaya k'arki yi haka kibashi dama ya gyara KUSKUREN shi da yafada don haka ki
barshi suje don ALLAH,
" Magaji bazan taba rabashi da yar shiba naga har yanzu bai gama sai tuwa ba gwara
inbari yadawo kan hanya da kyau bazan bashi yarinya ba suje can su cutar min da ita
ba
Tanajin muhawarar su kuma ita kanta zataso tabar wannan garin kodan wannan mayen
yaron dake son dagula lissafin rayuwar ta,
"Shikuwa bature tun bayan komawar shi dakin ya zube Akan gadon ya na kuka mai ciwo
soyayyar ta tafi komai daga mai hankali babban tashin hankalin shi a kullum
soyayyar ta karuwa takeyi a cikin zuciyar shi,.
" yana kwance ya fara tuno surarta a dazu datake kwance yayi Ajiyar zuciya "I truly
love you my heart desire ba gangar jikin nake bukata ba kece gaba dayan ki burin
raina ki ceci Rayuwata,
" shi kadai yake sanbatun shi har zazzabi mai zafi ya fara rufeshi " har zuwa dare
yana kwance ya dukun kune a cikin blanket sai rawar sanyi yakeyi
"Yayi ta kokarin yayiwa kanshi Allurar da ya hada dazu domin yayi mata Abun yaci
tura don haka dole yayi dialing number Ak,
" Shikuwa dama duk sun gama karade garin Zaria suna neman shi Amma shiru duk
hankalin iyayen shi ya gama tashi don suna mugun son dan nasu ,
"Yana d'auka yace " kazo Zaria hotel yanzu" ya furta dakyar ya kife wayar batareda
ya kashe ba don A lokacin numfashin shi dakyar yake iya fitar da shi "
"Yana fada wa iyayen gaba daya suka dunguma zuwa Zaria hotel cikin tsananin tashin
hankali'
" Alokacin da suka isa gaba daya ya gama fita hayya cin shi duk sun gigice A rikice
su ka kwashe shi zuwa Asibiti Momyn shi sai kuka takeyi kamar ranta zai fita,
Tana famar kiran sunan shi " cikin gaggawa suka bashi gado domin bashi taimakon da
ya dace
"Har kusan karfe daya idanun Ruman biyu takasa koda runtswa haka kawai takeson jin
waye shi tana son tasan shi waye ,
" Atake ta mike domin tunawa da dan karamin diary din shi da ya bata ranar ta dakko
jakar ta ta ciroshi tareda zuba mai idanu kyakkyawan diary ne dan karami kamar wani
Po's.. .......✍
*masoya kuci gaba da biyoni domin jin wanene Jeff ko kuma muce Abdullah shin wai
meye gaskiyar lamarin nan Kudai ci gaba da biyo*
*Matar soja"*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
~Dedicated to~
All my fan's
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
*Alkhairi bashi kadan jinjinar ban girma zuwa gareki _HAUWA'U MUHAMMAD USMAN_ wato
(REAL SMERSHER) godiya marar Adadi ALLAH yakara miki d'auka ka*
" Anhaifeni a United kingdome Nataso cikin gata fiye da tunani ba Abinda narasa
najin dad'in Rayuwa domin mahaifan Momy na mutane ne da suka shahara da dukiya
akasar ,
"Nayi karatuna Amakaranta mafi tsada kuma ina shekara goma sha hudu na kammala da
karatuna na mataki na biyu w'anda a take na fada jami'a fitattaciya wato University
dake U.S.A,
" Wanda nakaranta Aikin Likitan ci ta fannin mata wato (gynecology) kasan cewar
kasace da aka samu cigaba ko mai kankantar yaro zaiyi Abinda yake Ra ayi,
"Abu biyu ne tunda na taso yake daure min kai shine " banbanci da nake fuskanta a
tsakanin iyaye na "nafarko banban cin Addini na biyu harshen da Mahaifina yayi
kokarin koyarda ni da kuma gayamin Akan hukun cin Addinin shi,
" Mahaifiya ta kuwa duk ranar Sunday zata jani zuwa church domin Muyi bauta Amma a
gefe daya Akullum Mahaifina na kokarin fahim tar dani Akan Addinin Gaskiya,
"A duk lokacin da naga yayi Salla nakan tsayar da shi da tanbayoyina Amma Alokacin
duk bayanin da yakeyimin Sam bana fahimtar kodaya,
" Domin gani nakeyi Sam ba Addini bane idan na hada damu da muke zuwa church ana
kide kide da kuma Raye Raye kullum muna cikin nishad'i,
"Tunanina ya fara canjawa ne Aranar da nafara haduwa da wani d'an Nigeria mai suna
mukhtar a lokacin ina shekara ta goma sha bakwai wand's shima karatune yakawo shi
mun kulla Amintaka a tsaka nin mu a sakamakon ganin shi cikakken bahaushe " shi
kuwa yayi mamakin jin hausa A bakina bayan gani sak bature,
" Duk da Momy na ba ta cika zama bane kullum tana hanyar yawo zuwa garuruwa domin
bunkasa business dinsu na family
"Mahaifina ma Ya samu daukaka sosai ta hanyar mahaifiyata Wanda har yakai ga samun
matsayin jakadan Nigeria dake can kasar ta America,
" Yakan shigo Nigeria kai da kai sakamakon Aikin shi duk da na lura tun taso wata
Akwai wata tarzoma Atsaka nin iyayen nawa,
"A kullum Mahaifina na fadamin inkiyayi zina inkuma kiyaye shan giya kasan cewar
komai na kasar ba doka zakaga kana nan yara da zuwa club's susha giya suyi ta zina
ce zinace,
" ban taba jin sha'awar yin ko daya daga cikiba duk da ina da Abokai da dama da
suke kokarin Jana zuwa Aikata hakan,
"Mukhtar ne yafara yimin tanbayar da ban taba kokarin sanin Amsar ta ba " Shin ya
Akayi mahaifina ya hadu da Momy na har sukayi Aure bayan ba Addinin su' daya ba?
Abin ya dame ni sosai har ya hana ni sukuni na samu Dady na na tanbaye shi,
"Yayi matukar mamakin irin tanbayar da nayi Amma bai yi kasa Aguiwa ba ya fadamin
komai,
" irin KUSKUREN da yayi na barin kasar shi ta haihuwa tareda barin iyayen shi masu
matukar bukatar taimakon shi kasan cewar shine babba a wurin su kuma soyayyar Momyn
ka itace Silar komai domin nayi mata Alkawarin bazan taba barin taba domin har
matsala tasamu da iyayen ta a sanadin Auren mu,
"Shiyasa kaga duk lokacin da zanje Nigeria muke samun matsala da ita domin tana
tunanin bazan dawo ba,
" Amma nasan ALLAH bazai barni ba tunda na watsar da hakkin iyayena Akan mace "kuma
ba akan komai nayi hakan ba saboda girman Alkawarin da na daukar ma Kaina akan ta
banaso ALLAH ya kamani da karya Alkawari,
" Alokacin kaina ya daure domin banga wata hujja da zaisa yaki nashi iyayen ba
saboda ita tana tare da nata A kullum, A nan take na dauki Alwashin sai na gyara
komai idan har na kammala karatuna ni zan je neman dangin Mahaifina,
"Bayan kwana biyu munje church tareda mahaifiyata bayan gama service na mike nayima
pastor din mu tanbayar da ya kasa bani cikakkiyar Amsar ta
Amsar shi " My son Jesus is god and he is the son of god our god your god and the
god of the whole universe
"Aa Tayaya zai fadamin cewar Jesus ALLAH ne kuma dan ALLAH ne, ciki wanene Gaskiya
" na kuma tanbayar shi ya za ayi a ce shine dan ALLAH kuma yayi mulki?
Tanbayar da kawai nayi mai kenan ya fara kame kame tareda nemamin yafiya a cewar
shi na Aikata mugun sabo ,
"Na dawo batareda samun wata gam shashiyar Amsa ba na samu Dady na shima na tanbaye
shi,
" Dady wanene ALLAH? Cikin jin dad'in tanbayar ya cemin " ALLAH shine w'anda ya
halicci komai da kowa shine ma mallakin sama da kasa shine nake yiwa Sallah A
kullum nake rokon shi yafiya kuma yake yafemin,
"Wanene Jesus? " Annabi Isa A.s. bawan ALLAH ne Kuma Annabin ALLAH ne Wanda kafin
shi Anyi Annabawa da dama kuma bayan shi Anyi Annabin karshe w'anda yafi kowane
Annabi girma da daraja shine 'Annabi (Muhammad s.a.w),
"Amsar tashi ta shige ni sosai har ma na kwana da Abin Araina bayan gari ya waye
naje makaranta muka hadu da mukthar shima nakara yimai tanbayoyin da nama Dady na
ya bani Amsa kamar y'anda Mahaifina ya sanar dani ya hada har ma da hikimar shi
domin y'anda zan kara fahimta,
" Ahankali nafara research akan Karin haske dangane da Addinin mahaifina wato
Addinin musulunci kuma A kullum ina kara samun haske A cikin shi,
"Kaina yana dauremin sosai daga karshe na tuna da Mahaifina ya taba fada min Aduk
lokacin da Abubuwa suka fi karfin ka ka kai kukan ka Wurin ubangiji zai war ware
maka matsalolin ka,
" Ina kwance a katoton gadona dake cikin dakina kawai na kalli sama domin bansan
irin Addu'ar da yakama ce niba " shin zanyi ta church ne ko kuma ta musulmi? To
kuma ban iya Addu'ar musulunci ba
Kawai na furta "Oh god show me the right way bansan hanyar da ta dace dani ba Ance
Kaine mai war ware matsaloli ALLAH ka war ware min nawa matsalolin,
" A ranar na kwanta da wuri na yi bacci mai dad'in gaske har da makarfkin da nakira
da mabudin Rayuwata
"Mafarkin fuska mai Annuri fuska mai cikeda haske " Fuskar da bansan Meya kawota
cikin mafarkina ba koda na farka na dade ina ganin wannan kyakkyawar fuskar a
idanuna,
"Natashi A kasalance gaba daya wunin ranar da tunanin fuskar nayi shi,
" Har ma maifiyata ta damu da yanayin da tagan ni Aciki Banyi kasa a guiwa ba na
fada mata naga wata fuska a mafarkina kuma Abin ya dame ni sosai,
"Wasa wasa komai na Rayuwata ya fara canjawa don kusan kullum sa inayi mafarkin
wannan fuskar kamar ibada Ahankali zuciya ta Afka cikin soyayyar fuskar da nake
gani A mafarki na har ma na fada Abokina ina cikin damuwa kasan cewar mukhtar
kwararre ne a wajen Art nan da nan na kwatan tamai irin yanayin fuskar da nake
gani,
" Tunda nasamu wannan zanen A kullum saina tasa shi gaba ina kallo, kusan duk
w'anda nake tare dashi yasan da dream girl dina wasu har tunanin kwakwal wata ta
tabu sukayi,
"Momy na kuwa har hadani tayi da sychlogy doctor tayi cikin dubara ya dubani ya
fada mata lafiya ta kalau kuma zai iya yuwuwa Abinda nake gani Gaskiya ne,
" Tun daga lokacin suka kara bani kulawa da kuma tattali har na shiga shekarar
karshe a karatuna kuma a shekarar ne damuwa ta ta karu akan dream girl dina,
"Sakamakon mafarkin ta danayi muna making love batareda na gama tantance wacece ita
ba Aranar na wayi gari nagan ni kaca kaca,
" Gaba daya na wuni da matukar baka tuwa da kasan cewata da ita ina mai burin dama
zan kuma kwanciya bacci inkuma samun biyan bukata da ita kuma domin gaba daya Abin
ya ki fita Acikin zuciya ta,
"Dakyar nake bacci saboda nasa Abin Acikin zuciya ta kuma tundaga ranar ban kuma
wannan mafarkin ba sai Abin yazamar min damuwa sosai wani lokaci har kuka nakeyi ga
ciwon Mara da ya sani gaba akan tsantsar sha awa da kuma soyayyar fuskar mafarki na
har ma da daren mu na farko Acikin mafarki na da ita,
" A daddafe na kammala karatuna tareda kwalina na zama cikakken Likitan mata,
Na kammala ina shekara Ashirin Aduniya A lokacin nasan inada yancin kaina shiyasa
na damu iyaye na Akan subani dama infita yawon bude idanu for the first time A
Rayuwata,
"Domin inada kuduri a cikin zuciya ta na neman dangin mahaifina Duk da bai fadamin
cikakken tarihin shiba na fahimci cewar shi d'an Nigeria ne,
" Da neman shawarr mukhtar na samu Dady na nafada mishi cewa inaso in shigo
Nigeria ya fadamin inane garin su yake?
"Dariya kawai yayi irin ta manya ya fada min suna cikin Karamar hukumar Kaduna wato
Zaria ya fadamin ne kawai a tunanin shi shirme kawai nakeyi saboda na taso cikin
gata Sam bazan iya Rayuwa a Nigeria ba
" Lokacin da na fadawa mukhtar ya yi farin ciki ya fadamin cewar shima haifaffen
jahar Kaduna ne don haka idan har nazo inne meshi zai tayani neman yan uwan Dady
na,
"Lokacin da na gama shirina Dady kawai na fada ma kasar da zanje domin nasan idan
Momy na ta sani Sam ba zata y'arda inje ba,
" Ita da kanta tayi min odar motoci har ma da security domin kula dani ta kuma basu
damar A duk inda nake su kula dani da kuma lafiya ta,
"Ak wato Ahmde kabir Asalin dan Nigeria ne yana Aiki tareda Mahaifina kusan tunda
na taso na gansu tare Amatsayin mai taima kamai Akwai Amana mai karfi a tsakanin mu
dashi duk da kasan cewar ya girme ni,
" Yan mata kuwa tun bansan komai ba suka fara bibiya ta kasan cewar a kasar ba wani
Abu bane ,
Na diro kasar Nigeria tareda taimakon Ak da kuma mukhtar kuma tun kafin inzo na
bada umarnin Asiya min gidan da zan zauna,
"Aranar da naga gidan da Ak yasiya a cikin GRA Sam baiyi min ba kasan cewar. Nafi
bukatar zama Acikin mutane nasa Ayimin cigiyar gida a cikin manyan unguwan nin dake
cikin gari,
" Saidai Akayi rashin sa'a bamu samu hakan ba sai dai haya da farko naki Amince wa
da hakan Amma daga baya dole na Amin ce kasan cewa na bako a garin kuma ina bukatar
in binciko dangin mahaifina,
"A ranar da Momy na tasan cewa ina Nigeria tayi fada sosai har ta tashi hankalin
Mahaifina ni da kaina na bata hakuri tareda kwantar mata da hankali,
" ta daga hankalin ta sosai domin Abinda take gudu kenan kuma ya faru bata kaunar
ko Mahaifina ya shigo Nigeria bare kuma ni,
"Shigowa ta Nigeria nasamu Karin haske sosai akan Addini na domin har wani malami
mukhtar ya hadani dashi domin ya kara wayar min da kai Alhmdulillah
" A gefe daya ga muguwar damuwar da ke kara Addabar zuciya ta dangane da fuskar
mafarki na wato my dream girl,
"W'anda Abin har yazamar min jiki kwatsam ban zata ba kawai ranar na ganta A zahiri
batareda nasa ran ganin nata ba tsabar shock da kuma da kuma tsananin tashin
hankali ya hanani koda motsawa har ta bacewa gani na,
" Aranar hauka ne kawai Banyi ba sakamakon samu da rashin da nayi w'anda har ya
janyo min ciwo har iyaye na nakira tareda fada musu naga fuskar mafarkina A
zahiri...............✍
*Da fatan masoya bature suna biye da ni domin yanzu ne wasan zai fara kuci gaba da
biyoni*
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
✍✍✍✍✍✍✍
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*
✍✍✍✍✍✍✍
*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical
Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our
worlds for it cause u np pain~*
*KUSKURE NA🙆*
_love & Destiny_
_Written by Fenerh_
*A Gaskiya d'an Adam mai iya mai sai Allah Ada can idan naji marubuta na complaine
Akan readers sai suyi ta bani mama ki, ince meyasa suke bata ransu Akan wasu
mutanen, Ashe su kadai suka San irin Abubuwan da suke gani, wallahi burina in
nishadan tar inkuma fada kar daku my fan's Amma wasu basa tsaya wa suyi tunani wane
irin lokaci kake kashe wa kake tsaya wa ka tsara musu typin? Munada iyali munada
Aikin yi rubutu ra ayine kawai ba wai dole bane ni Anawa bansan Saura ba idan har
nagama typin nayi posting duk wasu sakonni da suka shigo sai bayan na rufe data
nake karan tasu domin Abubuwan da yawa zakaga mutum kusan goma ta prvt suna neman
ka tura musu littafi bayan ka gama typin kabi grp sama da Ashirin kayi post, A
Gaskiya raina jiya yayi matukar baci Akan wata bai war Allah da ta fada min magan
ganu masu zafi Akan tayi magana ban Amsa taba, don Allah yan uwa shin kuna tunanin
irin datar da muke konawa domin tura muku littafi shin kuna tunanin cajin da muke
cinyewa a wurin typin shin kuna tunanin sauran lokuta da ya kamata mu bawa yayan
mu? Ni dai ina neman Afuwar duk w'anda na batawa rai ya yafe ni dan Adam Ajizine
Allah yasa mudace.*
➡1⃣1⃣ 1⃣1⃣
1⃣1⃣
"Wani irin sanyi jikin Ruman yayi Gaba daya jikin ta ya gama mutuwa murus ba haka
taso labarin ya kareba,
" ALLAH sarki Ashe haduwar su mukaddari ne Ashe haka yake sonta ? lallai ta y'ar da
ALLAH shine mai y'anda yaso,
"Wani irin shauki takeji Acikin jinin jikin ta "Wayyo ALLAH kar ka hukunta ni ta
wannan hanyar,ta furta Ahankali tareda dafe saitin zuciyar ta,
" Yanzu Ashe shi musulmi ne kenan me meyasa taki tsaya wa ta saurare shi ya fada
mata labarin da bakin shi kila bazata tafka irin shirmen da ta tafka mishi ba,
"Ta fara tuno lokacin da tafara ganin shi a bakin Congo da kuma haduwar su Inna
Idear shopping complex da irin ruwan masifar da kullum take zabga mai,
" wani irin runtse ida nun ta tayi ta tuno da irin marin da ta zabga mai A cikin
gidan nan,
"Zunbur ta mike tunawa da irin dramar da suka kwasa dazu wani irin murmushi ne ya
subuce mata"
"Ta samu kanta cikin tsananin farin ciki Ashe haka yake sonta?
" mikewa tayi tareda janyo wayar da ta manta da Sha aninta ta kunna ta "Ganin ba
wani caji tayi saurin plugin dinta ta koma gefe zaune tana kallon wayar tana kuma
Ayyana cewar da ma zai kira ta yanzu,
" Akwai tanbayar da take so tayi mishi " Wacece wannan Yarinyar da ta gansu ranar
har take kokarin rungume shi,
"Wani dogon tsaki taja tareda mikewa ta duba Agogo kusan karfe biyu na dare Amma
gaba daya bacci ya kaurace wa idanun ta burin ta kawai gari yawaye,
" Ganin Sam tunanin shi bazai bari ta runtsa ba yasa ta mikewa ta fita cikin Sand'a
Batareda ta tashi Hajiya ba da take jin munsharin ta har cikin falon su,
"Dakin da ya zauna ta nufa ta dade a kofar dakin tana tunani " Ko dai ya kwashe
kayan shi Aciki ne? Ta tura kofar dakin tayi matukar mamakin ganin kofar Abude
saida ta leka ko ina tar da haske " Kamshin shi din nan mai mugun tsada ya fara
yimata welcome,.
"Ta wani lumshe idanu tare da Jan numfashi ta shaki kamshin har cikin kwakwal war
ta,
" tayi matukar mamakin ganin komai Acikin dakin shin yaushe suka kawo duk wa innan
kayan?
"Ganin system din shi Ajiye a gefe tayi matukar mamaki da saurin ta ta kulle dakin
ta karasa jikinta na rawa ta bude tareda kunna ta,
" Ta kara sakan kancewa da lamarin shi sosai ganin Hoton zanen fuskar ta a fuskar
system din shi,
."a nan ta fara tunani Wato kawai ikon ALLAH ne ya kawo shi gidan su haya batare da
yasan gidan su bane?
"A Gaskiya zataso jin karshen labarin nashi tana so ta sani shin har yanzu yana
kaunar ta kamar da?
" Aranar kwana tayi tana yimai bincike a cikin system har ta isa cikin folder
dinshi ta hotuna
"Masha ALLAH ta furta Alokacin da ta fara karo da wani kyakkyawan Hoton shi yana
zaune Abakin Beach dagashi sai gajeran wando wuyan shi sanye da towel fari sai wani
irin kwamemen sun glass da yayi masifar yimai kyau,
" Hannun ta takai Akan sajen fuskar shi da yasha gyara ta shafo shi A hankali domin
Abin yayi matukar kayata kyakkyawar farar fuskar shi,
"Ahankali ta rika bin hotunan shi da kallo kowane yayi matukar burgeta ta dauki
lokaci tana kallon shi,
" Kiran sallar farko ya dawo da ita hayya cin ta ta yi saurin zabura ta mike da
sauri har da system din ta kulle kofar ta koma cikin dakinta ta yi sa'a Hajiya bata
farka ba,
"Alla Alla takeyi gari ya waye ta isa makaranta saidai kash tuni fuskar ta ta baci
saboda tunawa da tayi yau basuda school kasan cewar Asabar ne,
" Tunda gari ya waye ta rasa ta ina zata fara wayar ta kuwa tana manne da ita ko da
Ace zataga kiranshi gashi ita Gaskiya bazata iya kiran shiba ya Renata,
"Tafiso yanzu idan ya kirata ta daina yimai wulakanci batareda ta nunamai cewa ta
damu da shiba,
" Yau Hajiya kanta taga canji "Ruman da sai tayi da gaske take tashi Abacci yau ita
ce ta tashe ta har ma tayi sharar gida kafin Afara sana'ar Abinci,
" Binta kawai takeyi da idanu" Ummu zonan, ta karaso cikin mutuwar jiki " gani
Hajiya, " meke damun zuciyar ki?
"La Hajiya me kika gani? ba Abinda banganiba y'ar nan kinada damuwa ne? " aa
bakomai " ko dai kinaso kibi ubanki ne?
"Nan da nan nasamu kaina da daga mata kai domin dai banda mafita' ta bata rai "
Yanzu Ummu gudu wa zakiyi kibarni ni kadai?
"Aa ni na isa kawai inaso inje ingansu ne indawo ta karasa kusa da ita ta rungume
ta " haba my kakus ai bazan iya Rayuwa babuke ba,
"Ta ture ta " ni sakemin wuya kin wani shakeni "Idan kinyi Aure fa dani zakije?
" Sosai kuwa idan badake ba ba inda zani' to naji naki shirmen sakeni nidai
"Yauwa kakus Anjima zanje wurin Hajara, baki kawai ta saki tana kallon ta cikin
mamaki" ta fara taba wuyan ta " Ummu Bakida lafiya ne" kaji Hajiya ni kalau nike
"Yo keda kullum take faman rokon ki kije Amma kirikiri Saiki ki zuwa yau ko keda
kanki kike cewa zakije,
Akwai Abinda zan Amso ne nakirata wayar bata zuwa naji ALLAH ya kaimu,
" A gurguje ta ga ma Aikin ta ta shirya cikin doguwar Riga Abaya mai shape baka
harda wasu igiyoyi a gefen ta dake kara tsuke rigar ta dakko wani farin breziya
hijab tasan ya ba wata kwalliya tayi ba Amma tafito kamar wata balarabiya,
"Ta sanya wani farin takalmi mai dan tudu da yar Karamar jakar shi mai doguwar
igiya ta rataya ,
" Wayar ta ta d'auka ta jefa cikin jaka tafito kamar ka saceta ka zura da gudu
"Hajiya sai tasbihi takeyi tare da binta da Addu a ALLAH ta tsare min ke daga
sharrin makiya ya kareki daga mugun ido,
" ko tsakar gidan su masu Abincin Hajiya Kallonta sukeyi wata tsohuwa da suke kira
baito tace "Masha ALLAHU zinariya kinfito das dake tubarkalla,
" Wani irin farin ciki take ji domin tasan shima sai ta burge shi idan har ya
ganta,
"Tana isa kofar gidan su hajara suna fitowa ita da Sumy " Sunyi matukar mamakin
ganinta gashi tafito a ainihin Queen dinta,
"Suka sa shewa da ihun ganinta " tace shegun gari ina zuwa? Hajara ta ya tsuna
fuska "Asibiti, " Waye ba lafiya?
"W'anda kike kokarin kashe wa' wani irin faduwa gabanta yayi " wa kike nufi zan
kashe Hajara?
" what Asibiti? Tuni kirjinta ya buga jikinta ya fara rawa har jakar hannun ta
tazame tana shirin faduwa,
"Su Kansu kallon reaction dinta sukeyi" Sumy tace Wallahi sai Alhakin yaron nan ya
kamaki " hajara tace duba jiya saboda ciwonki duk ya rikice " koda na kirashi daga
baya lafiyalau yake nasan kece sila Wallahi
"Idan kika kashe musu yaro Bazasu yafe miki ba, hawayene masu zafi ke yawo a kan
fuskar ta" Don ALLAH kumeje nidai inganshi inyaso daga baya kwaci gaba da fadan,
"Cikin sauri suka fada motar jikin su na rawa suka nufi Asibiti...........✍
*Kuyi hakuri da kadan zamu hade masoyana na Asali love you All*
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽GOLDEN
✍🏽 ✍🏽 ✍🏽 PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽 ✍🏽 ✍🏽 ✍🏽 ~*
*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical
Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our
worlds for it cause u np pain~*
~Dedicated to~
*Umar Dalha &Nabeela*
_U are the best Among the rest guys, muna Alfahari daku A Gaskiya ku ne cigaban
golden Allah ya kara tsare mana ku ya kuma kara d'auka ka mana forum din mu_
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
1⃣2⃣ 1⃣2⃣
➡1⃣2⃣
Tundaga harabar Asibitin suka fara cin karo da security kamar Wani governor ne Aka
kwantar ga kuma motocin su kowane dauke da harafin J
"Hajara na fakawa ta fito cikin sauri tana ware idanu burin ta kawai ta dora ida
nunta a kan kyakkyawar fuskar shi,
" Ak dake tsaye a gefe ya fara hango ta cikin sauri ya matso kusa da su "Welcome
madam,
" Hajara ce da Sumy suka Amsa shi yayi musu jagora zuwa daki na mu samman da Aka
kwantar da shi,
"Ita gaba daya zuciyar ta tana wurin shi shi kawai take son gani,suna kawai
reception Aka dakatar dasu,
" Tayi saurin waro idanun ta tanabin mutanen dake cikin reception din da idanu "
Gaban ta yayi mugun faduwa ganin fuskar wannan bawan ALLAH duk da tana cikin rudu
Amma taji wani iri Ajikinta,
"Sai kuma wata baturiya dake zaune Agefen shi cikin wasu tsadadden suit na mata
Riga da wando bakake har ma da cover shoe kana ganin ta kasan Hutu da naira sunyi
muhalli ko Akasar turai,
" Cikin rawar jiki suka fara gaishe su cikin harshen turanci " hannu kawai Momy ta
daga musu Dady ne ya Amsa su cikin halshen hausa ",
" Ak ya matsa kusa da Dady yayi mai bayani cewar ita ce yarin yar da Jeff yake so,
"Ya kwabe shi da cewar kar ya bari Tara taji ya tafi kawai domin suna zancen ne
cikin Halshen hausa,
" Kallon ta yakeyi cikin wani irin yanayi tare da jin kaunar ta har cikin jinin
shi'
"Ya kalli Momy da gaba daya hankalin ta nakan system din ta tana tura sako "Yayi
mata bayanin Abokan Jeff ne sunzo gai sheshi "
"Kallo ta watso musu mai cike da tan bayoyi " yayi saurin nuna musu dakin yace suje
yana ciki,
"Itace kan gaba domin duk A k'ag'auce take jikin ta na rawa ta tura kofar dakin,
" Shikadai ne Akwance idanun shi Arufe yana sanye da farin singlet da kuma tree
quarter 'Fuskar shi sai sheki takeyi duk da yana cikin ciwo ga dakin na fitar da
wannan unique kamshin na jikin shi Akoda yaushe,
"Tunda ta shigo dakin yafara motsa idanun shi Hajara ce ta fara karasa wa kusa
dashi cike da tausayin shi Sumayya ma ta bita " suka Ajiye basket din da suka zo da
shi na dubiya,
"Ita kuwa ganin shi a kwance gaba daya jikinta ya gama yin sanyi wani irin tausayin
shi ke ratsa ta,
" Ta ma kasa karasa wa kusa da shi, Shigowar Dady ne ya d'an dawo da ita cikin
natsuwar ta" Ya shigo yana mai bin Ruman da idanu yana jinta har cikin tsokar
jikin shi
"My son ka bude idanun ka Your dream girl is here ya furta Ahankali cikin kwantar
da murya,
" Ahankali ya fara motsawa tareda dafe kanshi da dayan hannun shi ya motsa bakinshi
kadan,
"Saida ya kuma mai maitamai sannan yace " Dady bazata zoba ta tsane ni wai ni yaro
ne, "Dady da gaske ni karamin yaro ne bazan iya rike Aure ba?
" no you are a big boy my son, ka bude idanun ka gata Akusa dakai " Come my
daughter ya fada yana mai kallon ta '
"Jiki A sanyaye tare da matsanan ciyar kunyar shi ta kara matsawa ya janyo hannun
ta ya dora Akan fuskar shi,
" gata Akusa dakai open ur eyes kaji my son, shi kuwa kamar A mafarki ya ji
lallausan hannun ta akan fuskar shi,
"Ya d'ora hanun shi Akan nata ya damke shi tamau batareda ya bude ida nun shi ba
"Ya jikin da hajara ta furta yasa shi bude ida nun shi domin shi duk A tunanin shi
mafarki yakeyi,
" Ya sauke idanun shi atsakiyar nata da suka cicciko da hawayen tausayin shi
"Yakara damke hannun ta kamar zata gudu,
" Ya dauki dogon lokaci yana mai bin fuskar ta da kallo har ya sauko zuwa jikinta
yana kare ma surar ta kallo tayi mai kyau sosai A cikin wannan shigar da bai taba
ganin tayi irin ta ba,
"Ya fara kokarin tashi zaune still hannun shi na damke da nata ' sukuwa su hajara
tuni Dady yayi musu Alama da su fita yarage daga shi sai ita Adakin ,
" Ki gyara min filo zan zauna " kanta na duke ta ce " Sakar min hannu in gyara ma
tom,
"Idanun shi na yawo ako ina na jikinta " ki gyara min A haka, ta dan kalle shi da
gefen ida nu ita gaba daya bata son kallon shi wani irin kwarjini yake yimata sosai
gashi ba wani kaya Ajikin shi ga shi ya yaye bargon da ya rufa da shi
"Wasu irin gargasa ne ta ko ina Ajikin shi sunyi wani irin lub club Alamar suna
samun lafiyayyun mai da kuma kulawa,
" Tsigar jikinta har wani tashi takeyi Abinka da dama...... Um ba ruwana,
"Tayi saurin kallon shi cikin idanun shi yaji kallon har cikin kwakwal war shi nan
take ya fisgo hannun ta ta fado gefen shi har tana dan buge mai gefen cikin shi
yayi saurin dafewa yace Ashhh,
" Jikinta ya fara rawa tayi saurin dora hannun ta saman wurin " Sory ba da gan gan
bane ta fada kamar zatayi kuka,
"Kaji ciwo ne? " ya dan kalleta idan har ba gizo idanun shi ke yimai ba yaga Alamar
damuwa kwance Acikin ida nunta
"eh ciwo wurin yake yimun tun tuni, likita bai duba kaba ne ? Likita baida wannan
maganin " maganin wannan ciwon yana wurin mafarkin zuciya ta,.
"Ya furta yana mai kara murza hannun ta Akan marar shi dake dunkule da wani Abu da
yakeji Awurin
" jin Abinda yakeyi yasa ta saurin janye hannun ta ya kalle ta cikin marai rai
cewa" meyasa kikazo? Nasan bakya sona kin tsane ni saboda ni yaro ne ko?
"Kinga irin ciwon da kika jamun ko ? Meyasa kikazo wurina ? Nasan kinzone kawai ki
karamin ciwo bawai kindamu dani bane nasan my friend ce ta janyo ki,
" Wasu irin hawaye masu zafi suka fara fitowa cikin idanun ta tana mai matukar jin
tausayin shi
"Batareda ta shirya ba ta fada saman faffadan kirjinshi tasa mai kuka, wani iri
yarrrrr yafaraji tun daga kan yatsar kafar shi har zuwa cikin tsokar kwakwal war
kanshi,
" ya dora Hannayen shi saman bayan ta yafara bubbuga mata Ahankali,
"Shshhh kiyi shiru haka please meye na kuka idan har ba so kike inkarasa mutuwa ba,
kinga irin halin da damuwar ki ta sanya ni ko,
" Bata dagoba still tana manne dashi "ya sanya hannun shi ya dago fuskar ta ya dora
halshen shi akan kumatun ta yafara lashe hawayen fuskar ta cikin wani irin salo,
" tuni kukanta ya tsaya cak domin jin irin salon da yake yi mata da halshen shi
akan fuskar ta tayi saurin janyewa cikin sauri tana mai gyara zaman dan karamin
hijabin ta ta mike zunbur daga gefen gadon"
"Jikin shi na rawa ya diro daga kan gadon duk da baya jin karfin jikin shi" riko
hannun ta yayi cikin rawar murya " ina zakije? please don't leav me please ya fada
hawaye na bin kumatun shi,
"Idan tace batajin shi har cikin jinin ta tayi karya Amma zancen Gaskiya ko
soyayyar shi zata kashe ta bazata iya Auren shi ba,
" Ina ita ina dan baturiya tafara kokarin fisge hannun ta" cikin tsananin zafi nshi
ya mannata da jikin kofar har kirjin su na hadewa " numfashin shi na fita da sauri
ya hade fuskar shi da tata,
"Kashe ni kikeso kiyi ko? Dama kinzo ki karasa ni ne ko " jikin shi narawa idan har
kikayi sanadin da iyaye na suka rasani Bazasu taba yafe miki ba domin kece sila,
"Sakin ta yayi ya koma kan gadon yasa kuka tareda kwanciya ya juya,mata baya,
jikinta na rawa ta koma bakin gadon " Karufa min Asiri kaga su Momy na nan kar su
gane komai
"An fada miki basu sani bane? Ba abinda kika zaba ba kenan " go just leav,
"Saurin mikewa tayi domin Sam bazata iya da wannan shagwababben yaron ba a Gaskiya,
" Tana fita ya cigaba da kukan shi yana furta " inkin tafi zan iya rasa hankali na
please come back,,,
"Shigowar Momy cikin dakin yasa shi tashi da saurin shi ya riko hannun ta" Momy
please if you truly love me stop her from going tell her to come back,
"Yana wani irin kuka "tafara lallashin shi jikinta na rawa " relaxed my boy and
tell me who is she?
"She is the one Momy she is the one I love she is my dream girl Momy please do
something,
" Ya karasa da kyar numfashin shi na carkewa ya tafi luuuu zai fadi dakyar ta iya
rikeshi kasan cewar shi namiji ta buga ihun da ya dawo dasu cikin dakin da gudu
"Har da Ruman da ke cikin tsananin Rud'u,
" Suna shigowa Dady ya tallabeshi ya dora shi akan gadon likita ya shigo da gudu
domin bashi taimako ita kuwa sai wasu hawaye ne kebin fuskar ta su Kansu su hajara
ya mugun basu tausayi,
" Ruman ce dafe da kuncinta Momy na huci Akusa da ita tafara zazzaga ruwan masifa
cikin harshenta na nasara,
"" idan har yaro na ya mutu sai kema kin mutu yaro tun tasowar shi kin hana rayuwar
shi wal wala kin hanashi sakewa kullum muna yawon Asibiti yanzu kuma kinbayyana
kinaso ki kashe min shi,
"I will never forgive you for that " Tara Dady ne yadaka mata tsawa "what. are you
doing?
" Cikin fada ta koma kanshi da bala'in tace duk shine Silar faruwan komai tayi data
sanin Auren shi kuma da bata Aure shiba bazata haifi yaron ta dashi ba,
"Shima ranshi ya baci " nine nake Dana sanin Auren ki da kika hana ni zama cikin
yan uwa na kuma kisa Aranki ki Ajiye not Anymore zan nemi dangi na inyaso kiyi duk
Abinda kikaga dama,
"Jeff kuwa komai a kan idanun shi koda likita ya nufoshi ya daga mai hannu domin
ranshi na suya ko motsi kasa yi yayi ya nufota dakyar ya dora hannun shi Akan
fuskar ta " Am sorry """"
"Kawai ya iya furta wa yana taku dakyar ya kalli su Hajara ku wuce da ita gida
please nagode muku jikin su a sanyaye suka fita domin hankalin su yayi matukar
tashi daganin irin wannan tashin hankalin
"Suna shiga motar su Sumy tace A Gaskiya Queen Alhakin wannan bayin ALLAH sai ya
kama ki kin tarwatsa gidan mutane Hajara tace Alhakin Abdullah zai fara kamata,
" ta fashe da kuka " haba mana ku bakwa ganin illar Abin yanzu Ashe gwara da ban
karbi soyayyar shi ba tun farko impact ni bazan iya soyayya da yaroba yaron ma
shagwababben da ya Riga ya lalace da Hutu Abu kadan kuka kamar jariri sannan ku
kalli Arzikin su ina ni ina shi ina yar talaka
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
*ku biyoni bashi zuwa dare my fans managed this one I love you All*
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
✍✍✍✍✍✍✍
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*
✍✍✍✍✍✍✍
~Dedicated to~
All my fan's
*Kuna ina ?yan uwana marubuta wato taurarin mu na Golden pen writers Association*
_Doctor Fati_
_princess_
_Ameshat_
_Maman Mamy_
_Dejer love_
_Ummu noor_
_Maman Ashfat_
_princess mazadu_
_Khadijat Hydar_
_tareda Zinariya ta_
*jin jinar bangirma zuwa gareku yan uwa na Allah ya kara daga darajar forum din mu
Ameen ina matukar yinku*
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
1⃣3⃣ 1⃣3⃣
➡1⃣3⃣
Saida suka mayar da ita gida sannan suka juya batareda sun shiga ciki ba domin suna
fushi da ita sosai,
Ita kadai tasan halin da zuciyar ta take ciki tayi matukar kok'arin ganin ta dai
daita natsuwar ta kafin ta shiga cikin gidan su
Tana shiga ta same su kamar ranar Hajiya baban ta da kuma magaji " tashigo da
sallama ta gaishe su,
"ina ganin ko yayi tafiya ne shiyasa baya zuwa Amma tunda ya biya kudin hayar shi
daki na zaman shi ne,
" Kawu idan babu damuwa ku mayar mai da kudin shi kawai tunda ma ba zama yakeyi ba
inaso in gyara gidan nan gaba daya,
" Don haka kabar min gidana haka nan, Haba Hajiya baki yafe min bane? Ni na yafe
maka tuntuni " ki yimin Alfarma in dauki nauyin da ke kaina don ALLAH,
"Kawu kasa baki, Magaji dake gefe ya kalle ta " Yaya kiyi hakuri kibar shi yayi
Abinda ya kamata,
"Ina daga cikin daki naji kirji na ya buga " me hakan yake nufi? Baba na nason ya
hana kowa zuwa gidan kenan? Ita da take sa ran ba Jeff hakuri ya dawo gidan su duk
da tasan ba Abu ne mai yuwu ba tunda taga iyayen shi a gari bazasu taba bari ya
dawo nan gidan da zama ba,
Abun duniya ya taru yayi mata yawa ga wani Abin tashin hankalin kuma Nasir ya
kirata wai zai dawo ta tarbe shi da yamma
"Ita bashi bane damuwar ta , ita gaba daya hankalin ta na wurin Jeff ko ya jikin
shi ?
Tasha matukar mamakin y'anda su hajara suka dauke mata wuta sai wani shan kamshi
sukeyi suna share ta " Abun ya matukar da munta saboda tana son taji ko ya samu
sauki,
"Lokacin da Aka tashi kuwa suna fitowa suka yi wuce war su batareda sun koma kanta
ba,
" Ta fito tana takowa ta ga mota tasha gabanta " Tasan waye ba kowa bane face
doctor Sulaiman sarkin nacin tsiya,.
"Hajiya Ummu Ruman Ataimaka min don ALLAH Ashigo Ayimin wannan Alfarmar har yana
hade Hannayen shi Alamar roko,
" bata da zabi domin yana yi mata kwarjini sosai shiyasa take kokarin kauce wa
haduwar su Bata so tayimai rashin mutunci,
"Har suka isa kofar gidan bata cemai komai ba shi kadai ke surutun shi ita hankalin
ta yayi nisa sosai,
" Sai da ya tafa hannun shi akan fuskar ta ta dawo hankalin ta " munzo gida
hajiyata me kike tunani haka inata zuba nikadai?
"Ta kalli kofar gidan su ta d'an kalli gefen shi " nagode sosai ta fara kok'arin
fita motar,
"Ummu" ya kirata " ta tsaya tareda Amsa wa " Don ALLAH ki rufa min Asiri ki bari in
turo iyaye na Ayi zancen Auren mu "Wallahi na mugun matsuwa,
" wani irin kallo tayi mishi don ita zancen nashi ta bata kunya Amma shi ko Ajikin
shi " ta dukar da kanta kawai ta kasa cemai komai "ki taimake ni don ALLAH kinji,
" Inaso in gama karatu na banaso in hada karatuna da Aure nafi so ingama karatuna,
Hmm yayi d'an murmushi,
"Bakya tunanin lalurar ki? Ya kamata kiyi wani Abu Akai kuma nima Gaskiya na gaji
da zaman gauran taka " ina bukatar mata Atare dani kinga Azumi ya kusa' inso samu
ne kiyi Azumi A gidan ki,
"Shiru kawai tayi mai don batada Amsar maganar shi " kije kiyi Shawara zuwa gobe
zandawo inji ra ayin ki Akai,
"A k'agau ce ta fita motar dan mugun haushi yake bata A halin yanzu tunda yasan
matsalar ta dole ya dame ta da zancen Aure,
" Tun daga tsakar gidan su ta tsaya cak domin jin kamshin turaren da yafi kowane
turare da take shaka kamshi mai shiga zuciya
"Ta kalli kofar dakin da take tunanin yana ciki zuciyar ta na bugawa kamar An dasa
ta Awurin ko kwakkwaran motsi ta kasa yi,
" Lafiya Ummu ki karaso mana tunanin me kike yi "Tayi saurin kallon gefen da Hajiya
take " ta karasa "Hajiya waye Acikin dakin can?
" Mai daki mana, ta bata Amsa a takai ce " Amma naji baba yace ya tashi ai,
"To ai sai ki Kore shi ko " kuma k'arki ji da wai y'anda zaki zauna Anan gidan
shima yana da yancin zama Acikin shi
"Kanta yayi mugun daure wa ta ce " ban gane me kike nufi ba kakus?
"Ki shigo daga ciki tukun sai kiji koma meye, haka jikinta na rawa tana ta ALLAH ta
ji dalilin dawowar shi bayan ya mata Alkawari bazai kuma zuwa gidan ba,
" Ta tube hijabin ta ta Ajiye jakar ta sannan ta dawo falon ta fada jikin Hajiya ta
rungume ta "
"Kara sani zakiyi y'ar wofi inaji da zufa na dama ya lafiyar kafar take ke Abu ba
kadan ba,
" Ta tuntsire da dariya tareda kara matse ta " ina sonki kakata ki barni in more
don ALLAH nayi kewar hawa kafar ki kwana biyu,
"Eh dole Kice haka mana ni gaba daya ban gane miki bane kwana biyu duk kin janza
daga Ummu da na sani zuwa wata daban,
" Aa Hajiya ni ban canja komai ba nice dai y'ar jikan yar ki Ummu Ruman y'ar lelen
Hajiya kaka mai tuwon yan gayu...
"Sallamar shi ta dawo da ita daga shaki yan cin da take yima Hajiya kamar Andauke
wutar lantar ki ta tayi dif tareda juyowa ta kalle shi,
" ya d'an rame sai dai yayi mugun yi mata kyau cikin shigar shi A kullum wato
fararen kaya sai wani tashin kamshi yakeyi ga wani haske da Annuri dake haska
fuskar shi,
"Aa kar ka wani cuceni kace min mama ni ban haife kuba kaida wannan shakiyiyar ku
nemi iyayen ku, ta fada cikin raha fuskar ta dauke da tsananin farin ciki,
" Wani irin murmushi yake fitar wa a fuskar shi mai ta fiya da tunanin mace ita
kanta ta manta da kanta wajen kallon shi yana lura da yanayin ta,
"Kaka Ashe Aunty ta dawo? Eh gatanan ta sani gaba " Ummu kinga ikon ALLAH ko Ashe
muna tareda gudan jinin mu bamu sani ba,
"Tayi saurin tashi zaune nan take brain dinta ya hasko mata komai " kardai Ace
shine d'an gidan kawunta mai Auren baturiya?
"Impossible kenan Ana nufin shi din Ai nihin jinin ta ne ta kalle shi ya daga mata
gira daya toh ya Akayi suka gano hakan?
" Ummu ga Abdullahi nan dazu suka zo da uban shi nan mahaifin ki ya nemo shi dama
su suna zumun cin su tunda Abin tsiyar iri daya suka kulla,
"Tayi matukar mamaki Ashe ba banza ba taji mutumin ya tsaya mata Azuciya Ashe kawun
ta ne yayan mamar ta,
" Hajiya bakin ta baiyi shiru ba " Ai jafaru da Muhammadu sai dai ince ALLAH ya
kiyaye na baya da fadawa sharrin mace shedaniya
Ikon Allah yanzu dama shi jinin ta ne meyasa bata fuskan ci hakan ba tun a labarin
da ta karan ta kuma haduwar ta Asibiti da babanshi taga tsantsar kamannin kaka
magaji Ashe shine kawunta Allah mai yadda yaso,
" Yana zaune kamar bai Santa ba haka ya nuna bayan hada ido sau daya da sukayi bai
kuma kallon gefen ta ba kanshi na kan wayar shi yana faman danna wa,
"Daga karshe ma mikewa yayi " Kaka bari infita zanje inga super market dina da Ake
aiki a sabon gari sai na dawo'.
"ALLAH ya taimaka yasa kar kayi halin iyayen ka kazama sai y'anda mace tayi dakai,
"Ahab sai dai kar Akuma Hajiya tawa ma har mijin k'an tace sai na zama saboda ita
idan nayi wasa yake aiya nawa a zuciyar shi,
" A fili kuwa , " ina kaka ni bazan dauki mace ta juya niba "Yanzu haka zuwa na nan
garin nasamu wata " yar yarin ya har mun dai dai ta kafin Azumi kila kusha biki,
"Ya furta tareda matsewa " wani irin kallo ta jefeshi da shi kirjin ta na dukan uku
uku bai ko kalle ta ba yayi ficewar shi daga gidan,
"Wannan me yake nufi da hakan? Da gaske ya samu wata macen yana so? Wacece ita?
" haka kawai taji komai ya fice mata Aka duk wal walar ta ta bace mikewa kawai tayi
cike da mutuwar jiki ta shige daki kayan jikin ta tafara tubewa tana jifa da su,
"Saurin hadiye Abinda ya fito ya tokare mata mak'ogoro tayi, me yake da mu na? Idan
ma yasamu wata macen sai me ina ruwana,
" Duk yadda taso Abin ya fita Azuciyar ta Amma Abin yaci tura,
"Bai dawo gidan ba sai kusan karfe goma na dare lokacin tana zaune ta mike kafa A
gefen Hajiya daga ita sai wata yar t shirt da ta kamata dam ta daura zanin Atanfa
kanta ba dankwali sai kalaba kanana da Hajara tayi mata tayi parking dinta da katon
ribbon ta sake shi a gefen wuyan ta
" ta tasa Awara a gabanta tana ta faman ci tareda dangwala yaji " Hajiya kin San
me?
"Ina fa zan sani tunda kinsani gaba kamar mai neman gafara ke idan dai Awara ce
tsab za ai miki Asiri da ita,
" Wata irin dariya tasa har tana kware wa " kai Wallahi kakus kinada Abin dariya
Dariyar ta ta tsaya ne tsab lokacin da ya sawo kai cikin falon tareda sallama yana
sanye cikin farin tree quarter da kuma farar t shirt kamar kullum dai,
"Ta fara gyara zamanta ta dan juya mai baya" ya gaida Hajiya tace " Sai yanzu? Aa
na dade da dawo wa naje can gidan tsofaffin can ne kuma na tsaya jiran Momy na ta
dawo daga Abuja a yau,
"Kuma naje hira wurin budurwa ta" Wani irin kallo ta aika mai yayi murmushin gefen
baki" Sannu Aunty na ya kk?
"Wani irin bakin ciki ya tokare mata makoshi dan rainin hankali itace Aunty shi
yau,
" Um Aunty A taimaka min da laptop dina zan danyi bincike idan kina bukata ne kuma
ki rike duka" ya fada cikin yanayin zolaya
"Wani iri ta kalle shi wannan kamar maye waye ya fada mai ita ta d'auka bayan ba
Wanda ya san ta d'auka
" Wani irin kallo yake aika mata akai kaice domin tayi masifar yimai kyau bai taba
ganin tsawon gashin ta ba sai yau duk da kalaba ce akan Abin ya burge shi har ma ya
dauki hankalin shi sosai,
"Ina ita umman taka take Abdullahi? Tana GRA ban gaya mata komai ba nafiso Dady ya
fada mata to ALLAH ya kyauta,
" Mikewa kawai tayi domin jin ta takeyi A takure tunda ta mike ya kafe ta da idanun
shi kamar ya janyo ta zuwa jikinshi wani irin numfashi yaja dakyar,
" Mikewa yayi dakyar domin ita yazo gani Amma ganin ta Sam ba Alkhairi yana
tangad'i yace kaka saida safe,
"ALLAH ya tashe mu lafiya yana shigewa cikin dakin shi direct bathroom ya fada ya
dauki bokitin ruwa mai sanyi ya sheka a jikin shi,
" ko zai samu natsuwar shi ta dawo ya dauki lokaci a tsaye yana diga kafin ya dan
samu sauki ya tube kayan tareda dauro towel ya fito zubewa kawai yayi akan gado ya
kife tareda fitar da zazzafan numfashi,
"A Gaskiya Dady na dawo wa gobe dole zai San Abinyi don yakai mak'ura he can take
it Anymore,
" Wallahi idan har baso sukeyi ya Aikata mugun aiki ba su Aura mai ita kawai Azauna
lafiya kuma shi baiki A daura gobe ba don ji yake yi kamar yayi mata fyade idan har
ya ganta a kusa da shi,
"Shi Dadyn Kaduna ma kawai zai samu Ayi wadda za ayi kawai, wani irin natsuwa ce ta
kama shi Alokacin da ya tuna da cewa Ruman jinin jikin shi ce y'ar uwa Abin yana
yimai dad'i sosai
Allah ne ya kaddara hakan domin yazama iznah ga Momyn shi hakkin su na iyaye ne
ALLAH ya kwato musu ta karfin Addu'a,
" ALLAH ya sanya soyayyar jinin shi A cikin zuciyar shi tun bai San da ita ba har
ALLAH ya hada su, ALLAH mai girma ALLAH buwayi gagara misali,
"Bai San y'anda zai misalta farin cikin shi ba Alokacin da Dadyn shi ya nuna mai
mahaifin Ruman Amatsayin kawun shi ga dangan taka mai karfin gaske A tsakanin su ta
kowane gefe,
" Yasan yanzu ba Abinda zai hanashi mallakar Ruman saidai ikon ALLAH, tuni Annurin
fuskar shi ya canja lokacin da ya tuna da Momyn shi domin yasan da Akwai sauran
rina A kaba Sannan ga Ita kanta Ruman din kuma,
"Wadda ya sani sarai yanzu ta fara son shi tsabar taurin Kaine kawai ke dawai niya
da ita ,
" Yayi wani irin murmushi da ya tuna da irin kallon hotunan shi da takeyi A kullum
ta system din shi, Abinda bata sani ba system din shi na hade da camerar wayar shi
da zarar aka bude ta sai ta nuna mai Abin da Akeyi da ita kuma shi yake tai maka
mata wajen bude folder din,
"Ya hango tsantsar kishin shi A cikin kwayar idanun ta A lokacin da yace yana da
budurwa,
Ganin tunanin shi zaiyi yawa ya mike tareda dauro Alwala domin yasan idan ba Salla
yayi ba yau bashi ba bacci cikin lafiya,
" Washe gari kuwa tun da ta tashi ta yi Salla tayi sharar ko ina na gidan domin
yanzu duk ba masu Aikin Abin cin babanta ya hana sanaar cikin kwana biyu kacal Abin
yafi komai yi mata dadi yanzu gidan su zai samu lafiya da mutane,
"Sai kusan karfe bakwai ta kammala komai har ruwan shayi ta dafawa Hajiya ta soya
mata kwai tace Hajjaju gashi yanzu ba cin tuwo ko funka sau da safe,
" ta kai mata duka ta gudu " ai ubanki ne duk yaja haka kawai ya hanani Sana'a ta
so yake in zauna ba cas ba as sai dai ya kawo min Abincin da ba gamsar da ni yake
ba,
"Yanzu kakus duk wa innan kayan Abincin da nagani ina zaki kaisu?
" Gidan ku zankai su y'ar kunnen uwa, ita dai ta shirya Abinta tafito fes cikin
Riga da zani na Atanfa ta yafa ta yafa farin gyale tareda takalmin su cikin kayan
da baban ta ya kawo mata ne,
"Kusan karo suka gwabza da Doctor Sulaiman yana sawo kai cikin gidan yayi saurin ja
baya " Tuba nake gimbiya nazo ne inkai ki makaran ta bai kamata kina hawa mashin ba
bayan gani kuma jiya na kasa runtsa wa inaso inzo inji shawarr da kika yanke akan
zancen Auren mu,
"Duk maganar da sukeyi yana tsaye a gefe yana kallon su idanun shi yayi jajur kamar
gauta saboda Azabar kishi..........✍
*Kuyi hakuri ntwk na wahalar dani sosai msges dina na shigowa slowly shiya sa bayi
muku post ba kamar y'anda nayi niya ba ku gafar ce ni komai sai Allah ya y'arda
kuci gaba da biyoni masoyan kwarai*
Ga masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma
hoton domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
✍🏽 ✍🏽 ✍🏽
✍🏽✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽
GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽✍🏽
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
1⃣4⃣ 1⃣4⃣
➡1⃣4⃣
"Wani irin tafasa zuciyar Abdullah takeyi domin tsananin kishi da ya rufe mai idanu
nan take fuskar shi fara ta canja zuwa ja tsabar takaici ya bugo kofar dakin garab
har sai da suka tsorata,
" Tayi saurin kallon kofar baya wurin ya Riga ya shige ciki Abinshi badon taso ba
ta ce suje zasuyi maganar Ahanya,
"Ga badaya hankalin ta baya kanshi tana tunanin haduwar ta da shi domin tasan ya
fada mata baya kaunar ganin ta da kowane namiji,
" Bata San meyasa ba Sam bataji dad'in fushin nashi ba, har ya sauke ta Acikin
makaranta jikinta a matukar sanyaye,
"Ya na tsaya wa ya juyo yana mai fuskan tar ta" Ruman please " ki bani izini Jan
Ajin ya isa haka ina matukar bukatar iyali Atare dani ki taimaka ki bani dama,
"Zuciyar ta tayi nisa cikin tunanin halin da Abdullah ke ciki " shi kenan ba damuwa
ta furta Ahankali,
"Cikin tsananin farin ciki yace " nagode sosai yau zanyi bacci har da minshari tank
you so much,
"Wani irin kallo ta aika mishi dashi w'anda ya kara tsima shi, ita kuwa tunani
takeyi why yake yi mata godiya?
" Sai kace ta ce Zata Aure shi, ta bude motar ta fita shikuwa ya juya cike da farin
ciki,
"Yau ma kamar jiya Su Hajara sai shan kamshi sukeyi cikin dauriya ta samesu,
" Wai me yake faruwa ne haka? Nayi muku wani laifin ne kuke share ni?
"Bako daya.inji hajara " Banajin dad'in yadda kike wahalar da yaron mutane ne,
"Wata Ajiyar zuciya ta sauke" yanzu duk Akan Abdullah ne kuke yimin haka? Amma ku
tuna nice kawar ku bashi ba kafin ku sanshi ni kuka fara sani bai kamata sanadin
wani Ace mun samu matsala ba,
"Kuma Abdullah din nan da kuke gani ba y'anda za ayi na Aure shi yana matsayin
kanina,
" kamar yaya kanin ki ? Eh he is my brother, Ahankali ta war ware musu komai "
sunyi matukar farin ciki da jin wannan labari,
"Sumayya ce ta kalle ta ta d'an daure fuska" Queen " tsakanin ki da ALLAH bakya son
shi ?
"Wani iri tayi sannan ta kalle su fuskar ta tayi matukar sau yawa " idan nace bana
son shi nayi ma kaina karya kuma Banyi wa Kaina Adalci ba,
"Ina son shi sosai " Amma bakwa ganin cewar ba ta y'anda za ayi Muyi Aure bayan har
yanzu Akwai sauran sarkakiya mahaifiyar shi bazata y'ar da ba,
"Kai ni kaina ko son shi zai kashe ni bazan taba y'ar da in Aure shi ba saboda Sam
ba tsari A cikin lamarin Da ma Ace ba mu hada jini ba ba w'anda zai San na girme
shi Amma yanzu ko jama'ar gari sun isa su zage ni
" ku kun sani na tsani Auren karamin yaro shi kanshi bansan lokacin da yayi nasarar
cafke zuciya ta ba ina matukar kaunar shi nasan ina nuna mai hakan ALLAH kadai
yasan mai zai faru A cikin Family,
"Shiru kawai sukayi suna tunani " Amma idan har kun dai daita kanku ina ganin
iyayen ku zasuyi matukar farin ciki mu samman Hajiya ma,
"Ni ko bama zai yuwu ba kawai mu bar zancen, "to soyayyar da kukewa juna fa"
soyayyar da yake nuna min dai ni bazan iya furta mai soyayya ba yana matsayin kani
na,
"Hmm Ummu zaki tafka KUSKURE babba Arayuwar ki idan har baki dai dai ta tunanin ki
ba,
" Ku taya ni Addu'ar ALLAH ya cire min son shi daga cikin zuciya ta kawai my
friends,
"ALLAH ya zaba mana mafi Alkhairi, Guy's ni dai ending of this semester Zanyi Aure
jiya My D ya turo Sumy ta fada cike da farin ciki,
" suka buga tsalle suka Dane ta " Wayyo dadi zamu sha biki " Amma yarin ya kin
shamma ce mu Wallahi " Hajara ta fada tana kai mata dukan wasa,
"Wallahi nima ban yi zaton Abun zai faru da sauri ba na d'auka idan ya turo za a
dauki lokaci Amma suna zuwa baffa na ya tsayar nan da wata daya cif,
" ALLAH ya nuna mana sai Muyi shirin Kwasar shoki Ashe kawa za a shige daga ciki "
idan kin shiga zaki bamu labari ya lamarin yake,
"A ranar sun wuni cikin nishad'i da kuma farin ciki bayan ta shin su saida suka
fara sauke ta sannan suka wuce,
" Tun Shigowar ta take kallon kofar dakin shi har ta shige cikin falon Hajiya ta
sameta Azaune ta kurawa TV ido,
"Da sallama ta karasa tareda gai sheta ta zube akasa tareda cewa washh nagaji,.
" Aikin gona kika je ne? Da kike cewa kin gaji " aa nidai Yunwa nakeji meye Akwai?
"Ga d'an wake nan shi nayiwa babanki da kuma kawunki gashi nan a cikin kula idan
zaki ci" baba ya zone ? Eh suna gidan Magaji tareda kawun ki Amina babu lafiya,
"Me yasa meta kuma? Damuwa ce kawai da take boyewa ta bayyana yanzu ai sayi wa
Kansu karatun ta natsu Alhakin iyaye yawa ne dashi,
" sanin mitar Hajiya yasa ta mike sum sum ta shige saida tayi wanka ta shirya
tareda sanya doguwar Rigar Atanfa ta murza dankwalinta kamar wata sabuwar Amarya
sannan ta zauna cin d'an waken ta,
"Sai kusan magrib baban ta ya shigo tareda mahaifin Abdullah " cikin matukar farin
ciki ya kalle ta " Ummu zo nan A she Yata ce ke ?
"Bai karasa maganar shi ba Hajiya ta tari numfashin shi " ina fa zaku sani tunda
kun watsar da iyayen ku akan mace Wallahi ku kiyayi duniya duk Abinda ka shuka sai
ka girbe shi,
"Ganin Fadan Hajiya bazai kare ba yasa na mike sum sum na fice gaba daya daga cikin
dakin domin in basu wuri su tattauna,
"Tayi matukar farin cikin da kawunta bai yi zancen soyayyar da Abdullah ke yimata
ba kuma bai tona cewa taje har Asibiti hai she shi ba,
Yau ta ji dad'in fadan Hajiya, kujera ta janyo ta zauna tareda kunna wayarta ta
fara bude sakonni kala kala da suka shigo atake wasu daga Nasir wasu kuma na
Abdullah ne,
" Sallamar yaro ne ya katse mata Abin da takeyi " wai Ana sallama da Ummu Ruman,"
waye ke nema na ta tanbaya?
"Wani mutum ne a mota, tayi Jim tana tunani ko sarkin naci ne ya kuma dawowa again'
" kace ina zuwa saida ta dakko hijabin ta ta kalli Hajiya " ina zuwa Hajiya Ana
sallama dani zan je inga ko waye?
"To ba damuwa dama hakan kikeyi da tuni ai munsha buki, ta wuce cike da jin kunyar
baban ta da kuma kawun ta,
" Jafaru idan ka gama shiriritar ka sai ka shirya yar ka Magabatan yaron da ke
neman ta zasu turo cikin satin nan dazu yake fadamin sun dai daita ta kuma Amince "
ina jiran ta zauna in kuma tanbayar ta Anjima in har ta Amsa to sai ku sa buki
kawai ko ya kukace Kaine ubanta,
"Jikin shi yayi sanyi sosai yaso yayi zancen Abdullah Amma tunda har tana da
tsayyaye bazai so kanshi ba dole ne ta taushi dan shi yayi hakuri ko banza ba sa'ar
shi bace,
" Kuma bazai taba yima yar kanwar shi guda daya tal da kasa ta rufewa idanu Auren
dole ba bayan laifukan da ya tafka bayan rasuwar ta iyayen shi na bukatar taimako
ya tsallake su ya barsu cikin wahala
Kuma yanzu da ya kamata ya gyara komai sai yazo ya bata ba don Haka dole Abdullah
ya bar zancen Ruman,
"Yasan shi mai laifuka ne A wurin tilon iyayen da suka rage musu gasu Alhmdulillah
yanzu sunada rufin Asiri sosai da zasu tallafe su don haka dole su gyara KUSKUREN
su,
" Tana fita taci karo da Nasir " tayi matukar mamakin ganin shi A yanzu domin ya
fada mata bazai dawo ba sai karshen sati saboda suna Aiki a Ibadan,
"Kanta a kasa ta nufi wurin motar shi, tun daga nesa ya zuba mata idanu A Gaskiya
idan ya mallake ta ya gama sa'a a rayuwar shi,
" Tayi sallama ya Amsa cikin nishad'i ya bude mata gaban motar ta zauna batareda ta
kulle ba ta gai sheshi cikin ladabi,
"Hmmm sai kika ganni ko? Eh ta fada " tunanin ki ya korani daga wurin kwadago na' "
ni ba ruwana, " ke ko keda ruwa har ma da tsaki " gaba daya kin hanani sukuni
kinsani duk ma fita a hayyaci na shiyasa kawai na dawo ayita takare,
"A Gaskiya zan turo manya kafin inrasa tunani na saboda soyayyar ki gaba daya
nakasa (concentrating) a aiki na,
" ita dai kanta na ga screen din wayarta tana kallo ba tareda tana danna komai ba"
"Tun Fitowar ta yake kallon ta a gefe yana zaune a cikin motar shi zuciyar shi na
turiri kamar zatayi bindiga idanun shi kamar zasuyi Aman wuta,
" Bayan dazu ya ganta da wani kuma yanzu ga wani ya kuma zuwa bayan ta sani sarai
baya so tasan cewa yana cikin fushi saboda ta nunamai cewar shi ba komai bane take
yin Abin da taga dama toh zai ko dauki mataki akai,
"Wani irin mugun reversed yayi ya fisgi motar shi da gudu ya bar unguwar,
GRA ya koma yana shiga ya kira Ak " Kafada wa Dady na ina GRA koda ya tanbaye ni,
ya datse wayar tareda jifa da ita ta tarwatse a jikin bango wata irin kara yasa
tare da dafe kanshi dake matukar sarawa kamar zai rabu kashi biyu,
"Kuka ma Rahama ne Ashe dama zai samu yin kukan ko zai rage jin radadin zafin da
zuciyar shi keyi,
" lokacin da Ak ya fada ma Dadyn shi sakon Hankalin shi yayi matukar tashi sosai'
nan take ya nufi GRA domin yasan Abinda ke damun yaron nashi,
"Saboda ya kira shi da cewar su hadu A gidan Hajiya kuma yasan yazo ganin Ummu
Ruman a waje ne sanadin komawar shi,
" Motar shi na fakawa ya fito ya shiga cikin sauri, yasameshi cikin mugun yanayi "
Son meke faruwa ?
"Dady kirji na zai fashe ya furta dakyar yana mai dafe kirjin " Abdullah "
ina neman Alfarma a wurinka amatsayina na mahaifin ka,
"Ya maida hankalin shi sosai akan Dadyn shi" Dady tell me zanyi maka ai kai
Mahaifina ne " Inaso ka cire son Ummu
Ruman a cikin zuciyar ka,
"Wani irin mikewa yayi tareda yin baya da sauri idanun shi gaba daya a waje " Dady
what????
"Dady kasan me kake fada kuwa? Ahankali ya fara yimai bayani tareda rokon shi yana
girgiza kanshi tare da zubowar wasu Azababbun hawaye da yake jin su kamar
tsiyayowar jini a cikin idon shi,
" Dady kana nufin kamar in dauki bindiga ne in saita kaina da ita kana nufin kamar
zarewar numfashi na ne zanyi da karfin gaske Dady kafi kowa sanin matsayin Roman a
cikin Rayuwa ta,
"Kaine da kanka kake tunanin in hakura da soyayyar ta " Dady How? Tell me.
"Ya durkushe a gaban uban " Dady saboda ka gyara KUSKUREN ka kakeso ka jefani cikin
wani hali? Saboda wani dalili Mara tushe kake so ka jefa Rayuwata cikin had'ari?.
"Mikewa yayi ya share hawayen shi ya kalli uban shi" I thought komai yazo karshe na
d'auka lokaci yayi da zan samu farin Cikina but Am mistaking komai ya kara
lalacewa,
"Dady anything can happened kuma duk Abinda ya faru ba KUSKUREN mu bane kune zakuyi
sanadin jefa mu Acikin mummunan had'ari
"Shigowar Momy tana mai watsa mai mugun kallo cikin harshen ta kamar kullum tafara
zubomai ruwan turanci
_*Hmmm Akwai magana my fan's ya zata kasance ne wai? Ku dai ci gaba da biyoni muji
wane irin KUSKUREN ne za a tafka,*_
Ga masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma
hoton domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love&Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
_Written by Fenerh_
_*Am sory my fan's Akwai uzurori da dama shiyasa bakawa samun post A kullum
Aruwan*_
1⃣5⃣ 1⃣5⃣
➡1⃣5⃣
Tun tafiyar Nasir ta fada tunani domin tayi ta zuba idanu bata ganshi ba tun
dawowar ta tayi matukar shiga damuwar rashin ganin shi,
Wasa wasa har kwana biyu bata saka shi a idanun ta ba duk inda hankalin ta yake ya
gama tashi gashi taga Hajiya ko damuwa batayi wani tunani ne ya shige ta ta mike
zunbur ta fita zuwa gidan kakan nin ta,
"Tayi matukar mamakin y'anda aka buge gefe daya Ana zuba wani ginin dakin gwaggo
Amina ta shiga tsohuwar har tafara murmurewa tayi sallama,
" Aa Ummu yau An tuno mu? Ta gai sheta tareda tanbayar kakanta " Ai malam ya fita
bai yi wurin ku ba? tace " aa ni bangan shi ba,
"D'an uwanki kwana biyu baya gari na tanbayi uban yace min wai tafiya yayi,
" Tafiya kuma? To ina yaje haka ? Take yima kanta tanbayar kodai fushi yayi domin
zuciyar ta na bata ba inda yaje,
"Ta ji ba dad'i a cikin zuciyar ta domin tana matukar son ganin shi sai yanzu ne
take gane cewar ba karamin shiga cikin zuciyar ta yayi ba she really needs him,
" Yanzu ina zata ganshi? Wa yarta ta Ciro ta fara duba numbar shi a karon farko
tayi dialing Amma wayar tashi a kashe zuciyar ta ta fara har bawa da karfi,
"Barin gidan tayi batareda tayi wani kwakkwaran tunani ba takoma gida,
" Ke kuma daga ina haka? Hajiya ta tanbaye ta "Gidan gwaggo Amina, shine baki
fadamin ba? Naga kina Salla ne kuma ba dadewa zanyi ba,
" Wai Ummu kuna waya da Abdullahi kuwa? Cikin sauri ta Amsa "Aa " kila bai dawo
ba dan ko jiya Jafaru ya fadamin yaje wurin Abokin shi a Kaduna,
"Tayi Ajiyar zuciya mai karfi Ta shige cikin dakin ta ta fada kan gadon ta still
tana so ta ji muryar shi ko kuma ta ganshi,
" meyasa zai yi tafiya bai fada mata ba? Ai ko a waya ne ya kirata she is very
worried zuciyar ta ta kasa natsuwa,
" Zuwan mahaifin ta ne ya dan rage mata damuwa domin ya ce ta shirya su shiga
Kaduna tare kasan cewar weekend ne,
"Tunda suka kama hanya babanta sai janta yakeyi da hira " Ummu bakya bukatar komai
dangane da karatu ko wani Abu?
"Ba komai baba, " idan har kina bukatar wani Abun ki fadamin in munje zanyi kokari
in bude miki Account kema idan kina bukatar kudi basai kin jira ba kinji.
"Nagode Baba ALLAH ya kara budi " Ameen Ummu kiyi hakuri kinji da sha anin Rayuwa
komai nada lokaci kuma ko wane bawa da irin tashi jarab tar,
"Sun isa lafiya gidan babanta ba laifi babban gidane har da katoton gate tayi Zuru
tana watsa idanu " yanzu Anan gidan mahaifin ta ke rayuwa ?
"Ya barsu Acan koda yake Alhmdulillah sun gode wa ALLAH basu taba rasa komai ba na
Rayuwa Hajiya da kaka magaji sun tsaya mata,
Tunda motar ta tsaya naga wasu yara sun fito da gudun su guda biyu maza suka
rungume shi,
" Baba oyoyo, ya daga karamin cikin su " Oyoyo Abdul Faisal ina sauran suke? "Suna
ciki " OK ga Auntyn ku nan tazo ku je wurin ta,
"Suka maida kallon su wajen Ummu da gudu suka rungume ta Aunty welcome, ta rungume
su duka domin taji dad'in ganin y'an kannen ta,
" Suka wuce cikin katon falon hamshakiyar na zaune ta dora kafa daya kan daya ga
sauran yaran maza guda biyu a gefen ta ta ci Ado cikin wani irin lafiyayyan less
daurin nan kuwa kamar na magajiyoyin karuwai,
"Ta karasa kusa da ita ta tsuguna " Mama ina wuni " ta d'an kalleta kadan ta dauke
kanta gefe" lafiya. Shine kawai Amsarta sauran yaran ma kallon ta sukeyi wani iri'
"Abin ya Sosa mai rai sosai ya buga musu tsawa " bakwa ganin yayarku ne? Kun tsaya
kuna zuba mata idanu,
"Sukayi saurin gai da ita suna kallon ta itama dai kallon su takeyi tana ganin su
taji sunyi bala'in shiga Ranta abinka da jini
" Amma har cikin zuciyar ta bataji dad'in y'anda ta Amsa ta ba, Baba da kanshi ya
kalli babban "Adam ka shigar mata da jakar ta dakin can na kusa da na maman ku,
" Ina lami ? Ta kawo mata Abinci ya shige cikin dakin shi ranshi nayi mishi suya,
"Ita ma bin bayan Adam din tayi ta shiga dakin da Aka nuna mata " ita kuwa Matar
gidan ta bi mijin ta a baya w'anda tun shigar shi yake zagaye dakin,
"Ta shigo tana ginshira " kallon ta yayi A wulakance" Balkisu Wallahi kin kaini
bango wato rashin kaunar har takai kiga Yata gudan jinina kiyimata wulakanci ko?
"To wai kuma yanzu Muhammad me nayi? Kingani ko Ace yarana shida Amma bazaki iya
boye suna na ba saboda rashin da'a.
" To ni bazan iya ba " Sannan kuma me tazoyi nan gidan kuma? Ya kalleta wani
iri"waye?
"Wadda kukazo tare mana, ta fada cikin rashin damuwa wani irin kallo ya watsa mata
" y'ar tawa ce wata " bilkisu y'ar Cikina Yata ta fari y'ar kanwata jinina mata ta
tafari Matar da nafiso fiye da kowace mace Aduniya bayan uwar da ta haife ni ke
kanki da tana duniya bazan taba Auren ki ba,
"To Aikin gama ya gama nice Matar ka uwar yayan ka maza har guda biyar don ta haifi
mace shine me ko Kanaso ko bakaso ni dai ce uwar yayan ka kuma yayana keda gida ba
ita ba,
" na miki uzuri kwakwal war ki nada matsala Amma ki sani ina son Yata kamar y'anda
nake son sauran don haka ki shiga tai tayin ki kina wulakan ta min ya Wallahi zaki
fuskanci hukunci,
"Tunda ke bakisan mutunci ba kin nuna Sam bakya kaunar kowa nawa ya kusan ceni har
mahaifiyata to baki isa ba kuma Wallahi sai na nuna miki karshen ki ya zo,
" ya wuce Abinshi bathroom ya barta tsaye sheke ke ta wuce da sauri dakinta ta fara
danna wayarta Ana d'auka a dayen gefen tace " hello Mama wai ya kukayi da malamin
nan Muhammad fa gaba daya ya canja yau har y'ar shi ya kawomin,
"Banajin me Ake fada a dayan gefen saidai Amsar ta" yanzu shi kenan bazai kuma
Amfani ba maganin?
" Ummu kuwa tunda Adam ya raka ta dakin ta ta ce ta gode ta nemi gefen gadon ta
zauna tana ware idanu tana kallon ko ina na cikin dakin
Gadone da kuma sif dinshi kawai da mirror ta cire hijabinta ta kalli wata kofa da
take tunanin ban daki ne ta fada tareda dauro Alwala ta tayar da Salla tana idar wa
lami na jero mata lafiyayyan Abinci bata wani jin yunwa ta koma kan gadon ta janyo
hand bag dinta ta Ciro wayar ta
"Number Sumayya ta fara kira ta sanar mata tana Kaduna tana dawowa zasu fara shiri
sun dauki lokaci kafin ta kira Hajara ita ma sun dauki lokaci har Tanayi mata
zancen yayan ta ya fadawa su Abba maganar su,
" gaban ta yayi mugun faduwa tunawa da Abdullah ta ce sai Anjima tana katse wayar
ta fara neman layin shi yau kusan sati daya rabonta da shi,
"Cikin sa'a wayar ta shiga Amma tayi ta ringing bai d'auka ba takira yakai sau
bakwai hankalin ta yayi matukar tashi dabara ta fado mata ta tura mai text msg,
_*A'm in KD*_
Kawai ta tura mai shi kuwa a lokacin ya na kwance a dakin Mukhtar yanajin ringing
din wayar ya shareta yasan ita ce " me zata fada mai duk da yana matukar kewar ta
Amma yana tsananin fushi da ita sosai,
"Shigowar msg din yasa shi janyo wayar ya bude " da sauri ya mike zaune' me tazo yi
kuma?
"Nan yayi dialing back a lokacin har ta cire rai zuciyar ta tayi mugun tsinkewa A
Gaskiya takai makura yanzu kam ta y'arda tana mutuwar son shi,
" ji take kamar tayi tsuntsuwa ta ganta a kusa dashi tayi missing ta bata da yakeyi
tana tunano irin y'an da yake rudewa a duk lokacin da yake tare da ita zuciyar ta
tafara raya mata
"Tasan koda bai gamsar da itaba ta hanyar sex tasan he is very romantic gashi yana
matukar kaunar ta ita ma gashi ta Afka cikin kogin son shi,
" tunanin ta ya katse ne Alokacin da taji karar wayarta jikinta na rawa ta kalla
ganin special numbar shi yasa ta daga kiran cikin kasala da kuma tsananin mutuwar
jiki muryar ta ta koma wata iri domin tariga ta shiga wani yanayi mai wahala,
"Tana picking tace" heloo ta furta akasalan ce yaji muryar ta har cikin kwakwal war
kanshi " hy kawai ya iya furtawa domin shima jin muryar ta duk ya birki ce,
"Tafiya ba sallama, ta furta a kasalance, " eh because you doesn't care , who said
so? You are. When? All the time
"Hmmm " why Roman? What? Kinaso ki samun hauka, ni yaushe? Kinfini sani, meyasa
kike mun haka? Any way na hakura gashi na samu y'ar baby A nan tana mugun sona tace
in kaita wurin Aunty na,
"Wani irin bugawa zuciyar ta tayi ta runtse idanun ta har wasu irin hawaye suka
taru a cikin idanun ta'
"Itama tanada komai da yake burgeni kuma nasan ita batafi karfina ba ni Banyi mata
karami ba ta y'arda da ni tasan zan gamsar da ita fiye da tunanin ta,
" kinsan meye kum..... Kit ta katse kiran kamar ta kurma uban ihu ta rufe bakinta
tana runtse idanun ta " Wayyo najawa Kaina ya juya min baya bayan ya gama cutata ya
cusamin kaunar shi cikin zuciya ta Wayyo ni najawa kaina,
"Tunda ta datse wayar yayi wurgi da ita gefe tareda dafe kanshi
" A haka mukhtar ya same shi ya dafa shi " friend what is wrong?
"Ya dago kanshi tare da girgiza wa " yaya zanyi Mukhtar? Tana guduna yanzu ta
kirani ina ma yi mata maganar nasamu wata macen Amma ko a jikin ta ta katse min
waya,
"Dariya yayi" Abdullah that's means tana son ka kuma kishi ne yasa har ta katse
kiran don haka zan baka shawara ,
"Wace irin Shawara haka kawarta ta fadamin cewar tana sona ni banga Alamar hakan ba
bayan kullum tana kula wasu mazan daban,
" patients my friend ka yi kamar y'anda na fada maka you will see da kanta zata
dawo hanya, kai ni gani nake ma kamar tana sonka ne nima nayi tunanin haka but taki
ta bani hadin kai,
"Yanzu ya zakayi da Dady ko ta y'ar da sannan kuma what About Momy? Just for get,
" Damuwa na kawai insamu hadin kanta dole su daura mana Aure, ALLAH ya y'arda.
"Sai da tayi bacci ta tashi sannan taci Abincin ta dai ci ne kawai ba don tanajin
dad'in shi ba saboda bakinta Sam ba Apatite,
" Saida ta yi wanka ta janyo yar Jakarta ta Ciro doguwar Rigar jallabiya mai dogon
hannu ta dan kamata kadan daga kasa kuma ta bude haka ta fito fuskar ta batareda ta
yi wani make up ba powder kawai ta dan shafa sai wet lip Amma wani irin Annuri da
kuma sihirtaccen kyau take fitar wa,
"Ta samu Mama a falo ta gai sheta ta Amsa kadaran kada ham ta samu gefe ta zauna
tana bin kallon da sukeyi itama gaba daya yaran hudu suna wurin ba w'anda ya kulata
" Sun dauki lokaci a wurin duk da kowa sha anin gabanshi yakeyi Amma ta danji
damuwar ta ta ragu saboda program din yayi matukar burgeta,
"Baban su ya fito yayi matukar murnar ganin su duka A zaune a wuri daya cikin jin
dadi ya kalleta " Ummu kintashi?
"Ai na leko naga kina bacci hope komai lafiya? Ta dan zame tareda gai sheshi yaji
dadi sosai y'anda take bashi girma tafi sauran y'an uwanta da ba w'anda yayi
tunanin gai sheshi,
" Ya zauna yana mai fuskantar ta" Na kira Abdullah ya fadamin yana nan garin yanzu
haka yana hanya ma tareda Abokin shi,
"Wani irin dadi ne ya rufe ta taji wani dadi ya ratsa zuciyar ta,
" Gaba daya ta k'agara ta sashi a idanun ta " sai kallon hanya takeyi,
"Karfe kusan biyar suka iso gidan tun daga harabar gidan kamshin shi ya fara yi
mata iso' tashi kawai tayi ta koma cikin dakinta gaban ta na faduwa,
" Sallamar shi cikin daddan muryar shi yasa ta runtse idanun ta tanajin wani irin
kaunar shi na bin kowace gaba ta jikin ta,
"Suka fara gai da Baba mama bilkisu ma ba laifi ta karbesu' Baba ne ya tura Adam "
kira Auntyn ku yanzu ta shiga ta fito ga d'an uwanta,
"Tun kafin Adam ya iso ta mike tareda daukar wayarta ta fito falon kan ta akasa,.
" Tun da ta sako kafar ta ya zuba mata idanu gaba daya ji yakeyi kamar ya ruga da
gudu ya rungumota cikin jikin shi cikin dakewa ya dauke kanshi ya mayar dayan gefen
tareda fuskewa,
"Ta samu wuri ta zauna mukhtar ne ya fara gai sheta yana mai zuba mata,idanu domin
gasgata Abinda yagani tabbas itace wadda ya zanama Abokin shi fuskar ta saidai A
zahiri tafi haduwa,
" Hmm Ashe dole Abokin shi ya haukace , ta Amsa Ahankali shikuwa ya tsare gida ya
daure fuska gaba daya kamar bai gane taba,
"Babane ya katse mata fargabar ta" Abdullah kana cikin garin nan kaki zuwa saida na
kiraka ko? Wato nan ba gida bane kenan Ace ina nan garin zakaje wani wurin,
"Ya dukar da kanshi kasa" Baba kayi hakuri nayi laifi bazan kuma mai maitawa ba' OK
" yaushe zaka koma Zaria?
"Zan dan kwana biyu Anan Akwai kamfanin da muke ginawa da Dady Anan " eh ya fadamin
munje kuma munga ginin ya na tafiya sosai,
"Ya mike " to ni zanfita " Ummu ki basu wani Abun motsa baki mana saikace wata
bakuwa,
"Ta mike cikin jin kunya ta nufi hanyar da take tunanin kitchen ne ta ga firij ta
bude ta dakko musu drinks da ruwa ta dora a tray ta hado da cups ta kawo musu,
" Ga badaya jikinta rawa yakeyi duk bataji dad'in y'anda yake dauke mata kaiba duk
zuciyar ta ta gama tsinkewa da lamarin,
"Baba na fita mama bilki ta tashi sauran yaran kuwa suna gai sheshi suka fita
yarage daga su sai TV da kuma mukhtar dake kallon wani irin salon so,
" Ya kalli Abokin shi " ni bari infita daga waje idan ka gama ka sameni ko? Nop
muje kawai me zan tsaya yi? Da saurin ta ta kalle shi gaban ta na faduwa jikin ta
na rawa tamike itama
"Mukhtar na gaba shima ya fara takawa zai bishi tabishi da sauri tareda shan gaban
shi ta zuba mai idanu ta marai raice gaba daya tarasa gane mai,
" Cikin kasalalliyar murya ta kalleshi " please Abdul enough ""
"Ya kalleta da kyar tareda watsa mata idanun shi masu daukar hankalin ta ta fara
karema sajen fuskar shi kallo gashi ya fito cikin wani farin yadi mai shara shara
har tana ganin farar singlet din shi
" Yayi mata kyau sosai Agogon shi sai sheki yakeyi " idan kin gama karemin kallon
intafi?
"Tun kafin kuma kiga yarintata zanje tafi ne baby na jira na......
" bata bari ya karasa ba ta daga mai hannu " please stop Abdullah......✍
Ga masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma
hoton domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*"Love you All*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
✍🏽 ✍🏽 ✍🏽
✍🏽✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽
GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATI✍🏽✍🏽✍🏽
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
*_Assalamu Alaikum masoya na ina matukar farin cikin irin kaunar da kuka nunamin
Agaskiya banida bakin da zan iya gode muku da shi sai dai ince Allah ya bar kauna
da soyayya ya muku sakayya da mafificin Alkhairi, kuma ina mai baku hakurin rashin
jina da bakuyi ba kwana biyu saboda tafiyar da na d'an yi Amma Alhmdulillah Allah
ya dawo dani lafiya zanci gaba da suburbudo muku posting,_*
1⃣6⃣ 1⃣6⃣
➡1⃣6⃣
"Idanun shi ya zuba mata domin ganin irin tsananin bacin ran da ya hango a kwance a
kan fuskar ta,
" Aunty me nayi kuma yanzu'? Gaba daya ta ma rasa irin Amsar da zata iya bashi
domin ya d'aure ta da jijiyoyin jikinta da irin kallon da yake jifanta da shi da
ida nun shi masu matukar burgeta,
"Nace ina sonki Kince bakya sona, Kince ni ina yimiki rashin kunya saboda ni
karamin yarone yanzu kuma nazo Banyi miki rashin kunyar ba zantafi kin hana ni, "
_Now tell me what do you wants Again um?_
"Yana mai jifanta da idanun shi da ke kara tun zura zuciyar ta zuwa ga kara kaunar
shi,
" Ta kasa koda motsi ta rasa me zata furta tayi saurin matsawa ta juya tareda nufar
kofar dakin da ta sauka,
"Tunda ta juya baya ya tsaya cak tareda zuba mata idanu ji yake kamar ya bita ya
rungume ta ko zai samu d'an sassaucin Abun da yake damun shi,
" Fita kawai yayi duk ko ina na jikin shi ya saki " Yana fadawa mota ya dora kanshi
a kan sitiyarin motar tareda rintse idanun shi zuciyar shi na matukar suya A shi
kadai yasan irin tarin damuwar dake cin shi A rai,
"Mukhtar ne ya dafa shi "Abokina ya dai? Ya dan dago da kanshi ida nun shi sunyi
jajur kamar wuta,
" Mukhtar nayi wa zuciya ta famu na kara wa Kaina da muwa ganin ta na kara hauka ta
zuciya ta sosai ina ganin soyayyar ta ce Ajalina don ina mai tabbatar maka idan har
ban mallake ta ba to zuciya ta na gab da bugawa in mutu,
"Aa kar ka fadi haka da ikon ALLAH sai ka mallake ta, Yanzu dai muje ko?
" Ya gyara zaman shi " zanje in dakko kayan da zanyi Amfani dasu ina son kasan cewa
tare da ita banaso Muyi nisa da juna ko da kuwa ba zata kula ni ba,
"OK ba damuwa ka fita,kawai me zan kawo maka? System dina da kuma brief case kawai,
ya fada a takai ce,
" fita kawai yayi ya koma gefen wata bu shiya dake harabar wurin ya zauna akan
kujerun robar dake wurin tareda dafe kanshi da hannun shi daya,
Tunda ta shiga dakin ta kasa natsuwa zuciyar ta na bugawa har wasu irin hawaye
masu dumi ke bin kuncin ta " Yanzu ya zatayi ta fahimtar dashi cewa tana matukar
kaunar shi ita ma?
"Ta yaya zai fahimci cewar ita ma soyayyar shi tayi mugun yi mata kamu?
" matsawa tayi ta jikin window din dakin dake harabar gidan tasan sun riga da sun
wuce Amma Abin da ya bata mamaki bai wuce ganin shi da tayi Azaune ba a wurin,
"Wani irin farin ciki ne ya rufe ta taji Kamar ta ruga da gudu ta shige jikin shi
ta shaki wannan kamshin nashi mai shiga zuciya,
"Idanun ta ta zuba Akanshi tana karemai kallo a Gaskiya ya mugun haduwa ya k'eru
iya k'eruwa duk da yanada k'aran cin shekaru jikin shi na da matukar daukar hankali
yanada k'ira irinta zaratan maza
Ga sajen nan nashi irin na gayun yanzu dake kwance Kamar Ana shafa mai relaxer yana
sheki'
" Ta dauki lokaci tana karemai kallo yana mai kara cike sauran dan gurbin da ya
rage A zuciyar ta,
"Shigowar wata yarin ya budurwa ya mugun daga mata hankali domin Yarinyar tana
cikin muguwar shiga ta sanya wasu irin Riga da sket da suka gama bayyana komai na
jikin ta,
" Tunda ta shigo gidan idanun ta ya sauka a kan shi direct ta nufe shi tana mai
cewa wow wannan irin sabon jinin fa kuma gashi bature,
" Hy handsome "Wani irin daure fuska yayi tareda d'an kallon ta kadan irin na reni
sannan ya kawar da kanshi
" hy kawai ya furta " jikinta na rawa ta janyo kujera a gefen shi ta zauna kamar
zata fada jikin shi,
"Nace ba. "don ALLAH Aunty bilki na nan? Wani irin kallon kin rainamin wayau kawai
ya jefeta da shi bai ce mata komai ba,
" Ya d'ukar da kanshi kan wayar shi ya fara danna wa tareda manna ta akan kunnen
shi ya fara magana cikin harshen turancin shi mai tsada ta saki baki kawai tana
kallon shi gaba daya ya tafi da tunanin ta,
"Ruman na hango komai gaba daya ranta ya gama baci Wato budurwar tashi har cikin
gida yake kawo ta lallai,
" Tsananin bacin rai bata San lokacin da ta fita tsakar gidan ba jikin ta na tsuma
ta nufe shi a lokacin yana kan magana kawai ganin ta yayi Akansu tana huci'
"Wani irin murmushi ne ya bayyana akan fuskar shi nan take ya riko hannun yarin yar
dake gefen shi" um baby muje ko inaso in dan sha iska ya furta cikin wani irin salo
tareda kashe mata idanu Wanda ya mugun Jan jinin jikinta
"Ta saki idanu tana mai mamakin bature da hausa rad'au a bakin shi
" Mikewa kawai tayi kamar wata jela Ruman kuwa zuciyar ta kamar zatayi bindiga
tsabar kishin da ya tokare mata kahon zuciya,
"Yayi saurin kallon gefen ta da wutsiyar idanu yana mai hango tsananin kishin shi a
cikin kwayar idanun ta wani irin farin ciki ne ya rufeshi kamar ya taka rawa don
murna,
" Har ya fara takawa ya d'an dawo baya kadan " Aunty na kinga baby ko ? Don ALLAH
ki nunamin guest room mu dan huta kadan,
"Ya fada cikin kunshe dariya " cikin tsananin masifa tace " banason raini da
iskanci koni sa'ar kace da zaka tanbaye ni wani guest room to bansani ba idan kaga
dama ka wuce hotel ku kwana I don't care,
"Yayi saurin taron numfashin ta " really? Amma idanu na sun nunamin you really
care,
"Ta zabga mai harara tareda komawa kan Yarinyar ta watsa mata mugun kallo tareda
Sakin tsaki mai karfi ta wuce fuuuu kamar iska,
" Wani irin nishad'i ke dibar shi gaba daya damuwar dake ranshi cikin kashi goma
yanzu bai wuce kashi daya ta rage ba, tana shigewa yayi saurin Sakin hannun ta'
tareda komawa kan kujerar ya zauna,
"Ta kuma biyoshi " muje in kaika guest room din Nasani " ni yar yayar Aunty bilki
ce sunana safiyya amma anfi kirana da sopy ,
"Ya d'an hade rai kadan tareda kallon ta " Am shekarar ki nawa kuma? Ta ce
Shekarata Ashirin da takwas kaga kuwa zaka samu Abinda duk kake bukata Awurina,
"Hmmm me kikeso dani yanzu'? Ina sonka ne ta fada batareda ko jin kunya ba, to ai
kin girme ni sosai ni banason tsohuwa nafison sweet sixteen,
" Nan take ranta ya baci domin ta fuskan ci tsabar wulakanci ne kawai yayi mata"
banason rainin hankali kace nayi maka tsufa ita wannan budurwar taka data wuce bata
girmeni ba?
"Waye ta girmeki? Ya kalleta sama da kasa duk ta wani k'ode a fuska tsabar bilicin
ga wani gashin dokin da ta sanya har duwawu ita Ala dole ta hadu sai wani irin
mugun dinkin sket dogo ne har kasa Amma yasha tsagu har zuwa cinya wai musulma,
"Ganin irin kallon rainin wayon da yake mata yasa ta wucewa ciki fuuu batareda ta
kuma sauraran shi ba,
Shi kam zuciyar shi na cikin nishad'i sosai da kuma farin ciki'
" Ruman na shigewa dakin ta fada kan gadon tareda Sakin d'an marayan kuka " Ashe
haka take da bala in kishi ? Ita kam bazata iyaba wato haka yake ji a duk lokacin
da ya ganta da wani, Ashe kishi masifa ne kai ita kam Wallahi zuciyar ta zata buga,
Yana zaune a wurin har mukhtar ya dawo ya sameshi A wurin cikin wal wala,
"Abokina ya nagan ka cikin farin ciki ne? Murmushi kawai yake saki tareda shafo
sumar kanshi,
" Shigowar baba ne ya tsayar dasu da hirar da sukeyi, ya iso wurin su cikin fara'a
" Abdullah kana nan ? " eh baba zan d'an yi kwana biyu Anan,
"A to hakan yana da kyau bari inturo yaran nan su kaika dakin ka ko.
" ya wuce cikin tsananin farin ciki, Adam ne ya fito yayi musu jagora mukhtar ya
kwaso mai kayan da yasan duk zai bukata suka shiga daga ciki gefen baki,
"Tunda tazo ta ci Abinci bata kuma marmarin saka komai a bakinta ba tana kwance a
wurin ta kasa ta b'uka komai,
Tsaki taja mai k'arfi domin ganin numbar mai kiran bakowa bane face Doctor
Sulaiman sai da ya kira sau uku kafin ta yi picking tana d'auka ya sauke Ajiyar
zuciya,
" Alhmdulillah farin Cikina ya kike? Ta daure kadan ta gai she shi, hope dai ba na
tashe ki Abacci bane?
"Eh, Ruman ina cikin farin ciki sosai A yau, " Meka samu ? Na samu Abinda yafi
komai muhimman ci A wurina wato burin raina,
"Meye wannan Abun? " kece Ruman iyaye na sunje har An karbi gai suwa na kuma rokesu
banason Auren mu ya dauki lokaci nima A matse nake kamar Amarya ta,
"Tunda kin Amince banason A dauki lokaci gwara A shafa kawai in mallake ki gaba
daya,
" Ai gaba daya jinta dauke wa yayi na wucin gadi har wayar ta kubce a hannun ta
batareda ta shirya ba,
"Gai suwa ita da Doctor Sulaiman? Kirjin ta na mugun duk'a ta sulale ta sauka kasa
zufa ya fara tsiyayo mata Ako ina na jikin ta,
" na shiga uku ni Ummu Ruman ya zanyi da zuciya ta? "Yau she ta y'arda da zancen
Auren shi da har zai tura iyayen shi batareda Antanbaye ta ba zasu k'arbi zancen
Aure,
" Wallahi da sake " kirjinta ya kara bugawa lokacin da ta tuna da Abdullah duk da
ya juya mata baya Amma ita tasan bazai taba daina sonta ba,
"Sopy kuwa tana shiga side din Aunty bilki ta wurgar da jakar ta ta Afka har uwar
daki bako sallama ita kanta ta tsorata da ganin ta kamar guguwa,
" Ke lafiya daga ina haka? Wai sai yaushe zaki yi hankali ki kuma natsu, "sai
ranar da kuma kukayi hankali tunda kuma ai bawai tarbiyyar ce da kuba kuma muma
y'ay'an ku a wurin ku muke koya,
"Nidai Aunty bilki wane yaro ne wannan baturen? Ta yatsune baki " ke ina ke ina
wannan kanin bayan naki kuma?
"Nidai ki fadamin kawai " to d'an uwan baban Adam ne a ina kika ganshi?
"Yana harabar gidan Amma mugun d'an wulakanci ne Amma ban damuba tunda na dora
idona Akanshi to ko sai nasamu biyan bukata ta koda ba zai Aureni ba sai mun hole
na dan lashi sabuwar zuma ,
" ke dai Wallahi bakida, hali kullum kina nan kamar karya akan zancen maza sai sun
hade miki gaba da ta bayanki zaki natsu,
"Aniyar ki ta biki tunda ke bakiyi ba nima bazan taba samun hakan.... Ya isa
fitsararriya tashi ki wuce na gode,
"Bari insa Abaki Abinci kici kinsan baban Adam ma gari don haka kibar gidan nan tun
bai ganki ba,
" mijinki ya cika matsala Wallahi Aunty kawai daga yaga ina shan shisha zai wani
tsane ni don ma bai ganni da mai karfin doki ba,
"Tsaki tayi ta mike da kanta ta wuce tareda kawo mata,Abincin kala kala har da
exotic juice na kwali ta Ajiye Mata,
sai baza idanu takeyi A harabar gidan ko zata ganshi Amma bata ganshi ba A dole ta
wuce ba tareda taso hakan ba,
" Har karfe goman dare Ruman na zaune ga Abinci an Ajiye mata ta kasa cin shi Baban
ta ya leko sau biyu yana tanbayar ko lafiya take?
"Tace lafiya kalau tana karatune bayan gaba daya hankalin ta a tashe yake har ta
matsu gari ya waye ko zata koma Zaria taje taji mai ke faruwa?
" Shi kuwa Abdullah yayi bacci cikin farin ciki domin jin shi yakeyi kamar Anyi mai
bu shara da Auren ta,
"Dakyar taga waye war garin tana idar da Salla ta hada kayanta domin batajin zata
iya kara kwana daya A Kaduna,
Burinta kawai ta ganta gaban Hajiya domin ita ce kawai zata bata Amsar da take
bukata,
" Kicin ta fada da kanta ta hada break fast domin taga Alamar Matar gidan sarauniya
ce, ta gama shirya komai ta Ajiye musu dakyar ta d'an sha ruwan tea duk ta k'osa
baban ta bai fito ba
"Sai karfe takwas suka fito Alokacin tana zaune A falon Baban ta cikin fara'a ya
karaso " Ummu har kin tashi?
"Lafiya kalau, ga Abinci A table na shirya, ya fadada fara'ar shi " To keda kanki
ina lamin take ?
"Ina so inyi ne shiyasa kawai nace ta huta, " OK to kin kaiwa d'an uwanki?
"Ai su ma basu tashi ba, Abdullah nake magana yana guest room ki shirya mai shima,
" Tace to ta mike jikinta A sanyaye tana son ganin shi Amma idan ta tuna da zancen
Sulaiman sai hankalin ta ya tashi ya zatayi da rikicin Abdullah?
"Ta shirya mai komai ta dora a tray ta nufi hanyar da take tunanin yana ciki,
Daddadan kamshin shi ne yayi mata welcome ta ware idanu tana mai duba ta ina zata
ganshi ko ya fita ne?
Ta ajiye tray din kenan ya fito daure da towel a kugun shi sai da gabanta ya fadi
ga wani irin bugawa da kirjinta keyi na ganin shi ba kaya Ajikin shi,
" sumar kirjin shi duk ta wani kwanta saboda ruwa ta fara zare idanu ganin irin
kirar halittar shi a bayyane gargasa ko ta ina har akafar shi da kuma Hannayen shi
wani irin tashi tsigar jikinta ta fara yi,
"Shikuwa yana fitowa idon shi ya sauka akanta tayi mugun tafiya da tunanin shi
cikin shigar zani da Riga ga rigar ta kamata daf a jiki komai ya bayyana ya fara
bin jikinta da kallo tundaga kasa har saman ta,
" idanun shi akan hip's din ta da yafito cikin single zanin da ta daura ga kuma
k'irjin ta fam kamar sa faso Riga,
Ita ta fara dawowa cikin hayya cin ta tayi saurin kallon shi dakyau ganin irin
kallon da yake jifar ta da shi ta kalli jikinta tama manta Sam ba hijabi ajikinta
tsabar damuwar da take ciki,
Tayi saurin juyawa zata fita, dakyar ya janyo numfashi ya nufeta cikin sauri tareda
riko tsintsiyar hannun ta,
Tayi saurin juyowa tareda watsa mai idanun ta da suka kara rikita mai lissafi
jikinshi na rawa ya kara narkar mata da idanun shi A cikin nata
" Tuni jikinta ya mutu murus ta kasa koda motsa dan yatsan ta ga wani irin feelings
dake saukar mata ta hanyar riko hannun ta da yayi da Hannayen shi masu mugun
taushi,
Ya kara matsowa idanun shi a cikin nata dakanshi ya kara turata jikin kofar tareda
riko kugunta da Hannayen shi duka biyun
Ya manne Ajikinta kamar wani magnet, Atare suka sauke Ajiyar zuciya
Wani irin shocked yakeji a cikin jinin shi nan take ya,fara fitar da wani irin
mugun numfashi,
Bakinshi dai dai kunnen ta yafara magana Ahankali yana mai busa mata iskar bakinshi
dake kara zuke ruwan jikinta
"Ta kasa bashi Amsa domin bai fasa Abinda yakeyi ba hannun shi na kan West dinta
still
Wani irin fisge jikinta tayi domin ta tsani kiranta da yakeyi da Aunty
Don't please,
K'arki fara raba gangar jikina da naki idan har sun hadu .
Ya furta cikin rada
"Yadan dawo da fuskar shi akan tata ya fara shakar numfashin ta yayi kasa da idanun
shi zuwa saman rigar ta da yake hango dukiyar fulaninta ya ja mugun numfashi tareda
Addu'ar ALLAH ya mallaka mai su zai more,
" kokarin ture shi take karayi Amma yaki Sakin ta kokarin hada bakin shi kawai yake
yi da nata
"Ka daina kaga kai ba mijina bane mijina na Zaria kuma kaima budurwar ka na nan don
haka ka sakeni,.
Wani irin cafka ya kaiwa bakinta da sauri yayi nasarar cafko harshen ta ai tuni ya
matse ta gam a jikin kofar ya fara tsotsar ta da saurin shi yana Sakin numfar fashi
masu wuya,
Saida ya dauki lokaci yana tsotar lips dinta tuntana mutsu mutsu har jikinta ya
saki ta kasa koda motsa dan yatsanta gaba daya ya gama kashe mata lakar jiki,
Saida yaji numfashin shi na fitowa dakyar ya iya Sara ra mata ya zare bakinshi ya
kara shigewa jikinta tareda janyo hannun ta ya dora akan kugunshi
Idan baki rikeni ba zamu zube akasa kin kashe min kuzarin jiki yau bazan wuni da
lafiya ba Tunda har kika motso min da kwantacciyar damuwa ta
"Ina mafarkin kasan ce war mu A tare a gadon Auren mu bazan iya cire ki a zuciya ta
ba Ruman kin zama jini da ruwan jikina idan baki Acikin duniya ta my life is
useless please don't leav me,
Dakyar take iya tsayuwar ta d'an rungume shi kadan domin ya mugun bata tausayi
domin tasan idan har yaji zancen Sulaiman Akwai matsala ita kanta hankalin ta A
tashe yake
Sai kara shige mata yakeyi Kamar zai shige jikinta yana fitar da Ajiyar zuciya
Ya dan saketa kadan tareda sauke idanun shi akan towel din shi dake kokarin kwance
wa sakamakon Hajiya babba data kunburo tanason yimai tonon silili ya d'an runtse
idanun shi yaja da baya tareda datse kofar ya juya rike da key din,
Ni kiyi zaman ki Anan kawai me zakiyi a Zaria hankali na yafi kwanciya idan ma
Hajiya ce zanje in dakko ta
Karatun ki ne kawai kuma matsalar " tank god kina last year da kin gama zan fadawa
baba ya dawo dake KD
"Ta kalle shi cikin matukar mamakin shi har ya gama fushin kuma ya dawo hanya,
" Fuskar ta ta hade ta kalle shi " akan me zan dawo Kaduna?
"Idanun ki sunfadamin haka harma da gangar jikin ki Akwanakin baya duk lokacin da
jikina ya taba naki bakya karbar hakan Amma ayau naji canji sosai da ni kadai nasan
me naji..........✍
Ga masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma
hoton domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
✍✍✍✍✍✍✍✍
GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION.
✍✍✍✍✍✍✍✍
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
1⃣7⃣ 1⃣7⃣
➡1⃣7⃣
Wani irin kallon da take jifan shi da shi ya kara tun zura zuciyar shi zuwa ga
shaukin ta,
"Kok'arin dawowa yayi shi Sam ya manta da yanayin da yake ciki burin shi kawai ya
jishi A cikin jikinta bayaso su rabu koda na minti daya ne,
Saurin ja baya tayi ta hade rai " ka bude ni infita inaso inje da wuri'
To ubana saboda kana waye da zaka hanani zuwa inda nake so,
"Saboda ina d'an uwanki yayan ki kuma mijinki uban yayan ki watara na da izinin
ubangiji,
" Harara ta kuma jefamai banason rainin wayo ka bude ni nace ko'
Zaro idanun shi yayi waje " Aunty tun yanzu kikeso in budeki?
To aini banida matsala dama mai neman kuka bari kigani ma, ya fara matsowa yana
kokarin kwance towel din dake daure a jikin shi
Wani irin zabura tayi ta runtse idanun ta gam tareda fara masifa
Banason iskanci Abdul ni ba haka nake nufi ba ka budemin kofa nace infita,
Numfashin shi taji gab da fuskar ta " oh come on Aunty na ki bude idanun ki me zaki
gani da zai tada miki hankali ni da ban gama girma ba ma kinfa sani ban gama balaga
ba ai ko?
"Nidai don girman ALLAH Abdul ka bari' wata irin Ajiyar zuciya yayi
Tayi saurin bude idanun ta ta kalleshi gab da ita idanun shi duk sun juye
Ita dai tasan ALLAH ya jarabceta da muguwar soyayyar shi da batasan lokacin da ta
shigeta ba,
Aunty na" ya furta da k'yar ki jirani inshirya muje tare tunda kinason zuwa yanzu
ki bari muci Abinci tare please na manta ranar da na zauna naci Abinci da kyau
kiyimin Alfarma don ALLAH.
Matsawa kawai tayi kusa da tray din ta fara hada mai shayi " kake ka sa kaya tom,
.
Yayi murmushi sannan yace " toh Aunty na,
Banaso" meye bakya so? Bansani ba, ya dan d'ara kadan ya Sosa kanshi domin ya lura
batason yana kiranta da Aunty,
Ya wuce Abinshi ya janyo wata Leda mai dauke da kaya d'inkakku masu shegen tsada da
kuma kyau
"Ya Ciro wani material milk colour dinkin matasan yanzu ta juya mai baya domin
tasan Abinda yake shirin yi
" ya zura wandon shi Sannan ya sanya farin singlet ya dawo kusa da ita ta gama hada
komai a plate ta turamai Irish da kuma kwai gefe ga tea mai kauri da toasted bread
Ya riko kafadun ta ya zaunar da ita a kan daddumar dake shinfide akasan dakin shima
ya zauna kamar zai shige cikin jikinta tana shakar tsadadden kamshin shi da ya gama
wanka da shi,
Ita dai wannan kamshin na mugun tasiri a hancin ta ya sanya fake ya debo Irish da
kuma kwai ya nufi bakin ta dashi,.
Ashe kuwa bakyaso inci kenan ya fada a shagwabe domin yau ya samu damu sosai a
wurin ta,
Ita ma kamar wani sihiri ta biye mishi yau kwata kwata ta kasa sarrafa zuciyar ta ,
Ta karbi fake din ta ci kadan saboda ya debo da yawa sannan ta Ajiye sauran
Saurin d'auka yayi ya cinye sauran tareda lashe fake din ya kuma debo wani ya mika
mata a haka suka danci Abincin sosai kuma duk ta rage sai ya cinye ya kuma lashe
cokalin,
Yana maijin dad'in yanayin sosai ji yake dama su dawwama a hakan Amma ina yasan
halinta ko tayi kamar ta saki jiki Anjima kadan sai ta botsare kuma,
"Sai da suka kusa cinye wa saboda ita kanta Akwai yunwa a cikin ta sosai don jiya
Sam ta kasa cin Abinci sosai,
Wallahi kinaso A wayi gari aganni gawa Roman ke Sam baki damu da damuwa ta ba
kinsan irin damuwar dake cikin zuciya ta kuwa?
Matsaloli sun yi min yawa ga Momy na sannan Dady na yanaso inyi mai Abinda bazan
taba iyawa ba A Rayuwata
Sannan babbar matsala ta yanzu kece" Roman kece babbar damuwa ta kece matsalar
Rayuwata ki tausaya min na gaza hakuri na ya kare
Kokarin matsawa ta farayi domin yau yanaso tayi Abin kunya don yana gab da sata
cikin mugun yanayin da gangar jikinta bazata iya d'auka ba,
Ya kara manne mata Ajiki " please Roman horon ya isa haka bansan wane irin Jan Aji
bane wannan ni nasan kina sona ki y'arda kawai Muyi Aure ko ma samu kwanciyar
hankali gaba daya,
Wallahi Aure nake bukatar Muyi kafin inrasa lafiya ta da kuma Rayuwa ta gaba daya
kwanan nan ni kadai nasan irin wahalar da nake sha saboda ke
Me yasa banajin hakan a sauran mata? Meyasa ke kadai nake son kasan cewa da ita
kece kawai burina kece kawai mafarkina kece kawai nake so ki soni ko da kadan ne
Wallahi ba zancen raini a cikin soyayyar mu ba haramci a ciki
Wani iri takeji a cikin jikinta a hankali ta samu damar mikewa " muje zarian mu
dawo, kawai ta iya furtawa
Kazo muje nidai tom" OK ya furta a kasalance ya dakko rigar shi ya zura ya dauki
key din ya bude ta ya kwashi wayar shi tareda daukar agogon shi ya daura ya zura
takalmin shi ya kara fesa turare sannan ya kalle ta
Kallon shi kawai tayi tayi saurin fita yana biye da ita a baya yana bin jikinta da
kallo tana kara tafiya da ima nin shi,
" ji yake kamar ya turmushe ta ya cire Abinda ya dunkule mai a Mara da dadewa,
"Suna shigowa Baba ya gansu cikin jin dad'i ya kalle su " aa Ummu a she kuna tare
na duba ban ganki ba inaso infita
Abdullah ya fara gai sheshi cikin jin kunya " Abdullah ya Bakunta?
Tace "aa yanzu zamu tafi da Abdul"" yayi saurin kallon ta domin yana son y'anda
take kiran sunan shi
OK toh ba damuwa idan kin tafi weekend zan zo in kuma dakko ki ko?
Ya zaro ATM ya mika mata yace " ga Wannan serving account dina ne ki rike A hannun
ki idan kina bukatar kudi kafin in bude miki naki"
Lallai ma baban Adam wato tun yanzu ka fara nuna banbanci ko to ba komai kuje kaida
ALLAH,
"Wai bilkisu yaushe ne zakiyi hankali ne? Aa a turu aka kwantoni karewar rashin
hankali ka dai shirya Gaskiya malam,
Yanzu shekara nawa kukayi ke da yayan ki kuna cin kudin don kawai na bata dan
wannan zaki nemi ki tayar min da hankali to kije bazan yi Adalcin ba tunda ke
Adalcin kike yiwa kanki,
Abdullah ya kalle shi" Baba ka karba kawai basai kayi wahala ba zan rika bata duk
Abinda take bukata,
"Ran ta yayi mugun baci domin ya y'ar fa ta a gaban wannan shegiyar y'ar tashi,
Ruman dai kayanta kawai ta dakko ta yafa katon gyale akanta ta fito rike da wayar
ta a hannu,
." mama na tafi ta ce ma bilkisu " wani irin harara ta zabga mata batareda ta Amsa
ba ta wuce Abinta, Abun ya kona mata zuciya Amma tasa Aranta sai ta saita Matar nan
kuma duk sati sai tazo gidan taga tsiya ita da gidan ubanta,
Tafito tana takawa Ahankali cikin tafiyar ta mai bala'in daukar hankali saidai tana
fitowa taja tai turus ganin wadda ke tsaye a jikin motar Abdullah, wato sopy,
"Ta sanya wasu Riga da wando da sukayi mugun d'ame ta kamar wata tsohuwar karuwa,
.nan da nan zuciyar ta ta fara turiri ta rataya yar Karamar jakar ta ta nufi hanyar
fita kawai batare da ta kuma kallon su ba yana lura da ita tun Fitowar ta ya zuba
mata idanu ji yake kamar ya ruga da gudu ya sunkuceta batareda tasha wahalar tafiya
ba,
Amma ganin ta nufi hanyar waje da sauri ya fisgi motar shi tareda bade ta da kura
ya bi ta a baya,
Tafiyar ta kawai takeyi batareda ta saurare shi ba yayi saurin shan gaban ta da
motar ya faka ya fito tana tsaye fuskar ta a hade Kamar had'ari,
"My Aunty wannan fushin fa? Kizo mutafi ina zakije da kafa? Bansani ba don ALLAH ka
bani hanya in wuce ka koma wurin karuwar ka gata can tana jiranka,
" na shiga uku ni Abdullah so Ake sai zuciya ta ta buga hankalin ki zai kwanta
nidai ki taimake ni ki saki ranki mu tafi don ALLAH,
Bazan jeba ka matsa min a hanya ka koma kaci gaba da hirar ka kawai nasan dama ka
dade a cikin muguwar harkar shiyasa har kake ganin kayi balagar da zakace ni kake
so,
Ta nunashi da yatsaya " kar ka kuma KUSKUREN cewa wai ni kake so ranka zai baci ni
ba irin waccen bace jikin shi na rawa ya fara kokarin riko hannun ta,
.don ALLAH ki saurare ni Wallahi ba budurwa ta bace impact ranar da kika fara ganin
mu nima Aranar na fara ganin ta Wallahi bansan ta ba ya karasa maganar kamar zaiyi
kuka,
Taji mugun sanyi a cikin zuciyar ta har wata y'ar Karamar Ajiyar zuciya ta sauke ta
dan kauce kadan zata wuce ya rike hannun ta "Aunty please"
Ki shiga mota mutafi, "ka sakar min hannu kaga mutane na kallon mu ko,
Tasan halin shi bawai kunya ce da shi ba yasata yin baya ta bude motar ta shiga
batareda ta rufe ba ta zauna Abinta,
Murmushi kawai yayi ya koma gefen ta ya rufe murfin sannan ya dawo gefen driver ya
zauna " tank's Aunty na,
Tafiya sukeyi batareda sunce wa juna komai ba sai shi dake d'an kallon ta ta gefen
ido time to time yana Sakin murmushi,
Domin jin shi yake cikin nishad'i sosai " sun danyi nisa kadan ta fara lumshe
idanun ta ta kwantar da kanta kadan nan take bacci barawo ya tafi da ita saboda
rashin baccin da batayi ba daren jiya,
Driving yakeyi Amma gaba daya idanun shi na kanta yana kallon kyakkyawar fuskar ta,
Har suka shiga Zaria tana baccin ta saida ya faka motar sannan ya juyo gaba daya
yana fuskantar ta ya dora hannun shi a kan fuskar ta ya fara yawo dashi har kan
lips dinta da ke sheki ta dan motsa bakinta kadan da ya bashi damar ganin dimple
dinta da ya d'an lob'a Ahankali ya matsa da fuskar shi zuwa ga tata
.yayi mata kiss kadan a saman lips dinta sannan ya manna mata wani a gefen chick's
dinta
Ahankali ta fara bude idanun ta domin jin kamar ana shafa mata jiki tayi saurin
zabura ta zauna da kyau tareda watsa mai mugun kallo ta fara gyara zaman mayafinta
Me kakeyi haka?
Ta zaro ido tareda shafa lips dinta Abdul banason rashin kunyar ka fa,
" Hmm Aunty na kenan kema fa kinaso kawai kinki ki bada Kaine Abinda harda kara
riko min baki kikeyi Aduk lokacin da na fara kissing dinki'
Bude motar kawai tayi ta fito batareda ta saurare shi ba domin taga kullum sabon
iskanci yake karowa da kuma rashin kunya,
"Ta kalli kofar gidan su taga irin gyaran da yakesha ko ina ya fito tsaf bakamar
lokacin da Ake turuwar zuwa siyan Abinci ba,
Da gudun ta ta karasa cikin gidan " kakus kakus ina kike nayi ke warki ta fada
falon tareda fadawa saman jikinta,
"Ni yau naga y'a karya ni zakiyi da kika fadomin akan jiki da manyan cinyoyin nan
naki ke ni dagani ta d'an tureta kadan,
" wato Hajiya yanzu bakya sona ko? Bawani nan keda kikabi ubanki kika manta dani,
Hajiya ni na isa in manta dake "to naji ga Angon ji nan tunda kin shigo kamar wata
Yarinyar goye bakya ko jin kunya,.
Sulaiman dake zaune tun Shigowar ta ya zuba mata idanu yana musu dariya,
Ahankali ta saita kanta ta kalle shi sai Alokacin ma ta tuna da maganar shi a waya
tayi saurin daure fuska ta kalli Hajiya,
" kuje can dakin Abdullahi toh tunda ta zo ke kuma ki shirya ma Angon naki Abinsha
dama bai dade da zuwa ba kika iso,
Da saurin shi ya mike ya fita domin ya kagara su d'an kebe domin ya nuna mata irin
farin cikin da yakeyi a zahiri,
Yana fita ta kalli Hajiya " Wai ni Bangane ba Hajiya waye Angon nawa?
Sulaiman mana' ai kina tafiya saiga iyayen shi sunzo ya fadamin kin Riga kin Amince
shiyasa kawai na kira Jafaru yazo ya karbesu shida Abokin shi mahaifin ki ma sai
bayan sun wuce nayi mai bayani,
Amma Hajiya ni nafada miki ina sonshi tsakani da ALLAH? Baza ku tanbaye ni ba kuji
ta bakina? Sai kace wata kaza daga ganin mutane zaku Amshi gai suwa to ni Wallahi
banason shi'
Wasa kikeyi yarinya kuma bazaki mayarda mu kananan mutane ba tun farko saida na yi
miki magana idan bakyason shi ki sallame shi sai yanzu zaki kawomin zancen banza to
idan har bakyason shi sai kije kisamu babanki Jafaru bani ba ehem,
Ta janyo wata yar Karamar Leda ta kunce ta zaro kudi wa inda Akalla zasuyi dubu
hamsin " gasu kudin gaisuwar ki ne ki gani'
Ga kwalayen biskit dasu sweet can ta nunamata wasu irin kwalaye a gefe da sunkai
kusan biyar,.
Wasu irin hawaye ne suka wanke mata fuska ta kalli Hajiya " Yanzu saboda ALLAH
neman kai kikeyi dani Hajiya? Dazaki yi saurin yanke min hukunci?
Jikin Hajiya yayi sanyi domin sai yanzu ita kanta ta fara data sanin karbar kudin
gaisuwar Abinka da jika da kaka nan da nan ta janyo ta zuwa jikinta ta fara
lallashin ta,.
'Kiyi hakuri Ummu kiyi Addu'ar ALLAH yasa shine mafi Alkhairi agareki kinji ki
kwantar da hankalin ki kinji?
Hawaye kawai takeyi domin tama rasa wane irin tunani zatayi ta mike kawai ta fada
dakin ta tareda sa kuka mai tsuma zuciya sai yanzu take gane cewa ta cutar da
zuciyar ta da ta Amince tun farko ta y'ar da da Abdullah da ba haka ba wai shin
menene illar Auren karamin yaron?
"Ummu kifito kinbar shi a waje yanata jiranki. Taji Hajiya na magana'
" Tayi kok'arin share hawayen ta ta mike tareda daukar katon hijabi ta saka ta fito
domin dole ne ma ta sanar da shi Gaskiya domin ita Sam bazata iya Auren shi ba,
Abdullah kuwa ya dade Azaune a cikin motar yana faman murmushi kiran wayar shi da
Dadyn shi yayi ne ya sakashi dawowa cikin hayya cin shi ,
Yana d'auka yace " kasa meni a GRA yanzu nasan ka shigo garin,
.tundaga harabar gidan yakejin hargagin Momyn shi ga security ta ko ins ya faka ya
fito Ak ne ya fara ganin shi ya taso da sauri " welcome sir'
Tank you Ak, ya bude kofar ya shiga tana ganin shi ta karaso da sauri ta tareshi,
Abdullah ka fada ma Momyn ka inda kaje tunda ka tafi kullum sai ta karanta min
hauka a gidan nan akan cewar ni ne na boye ka
Kuma ina son yin magana dakai yanzu " ya dan rungume ta kadan ya bata fake a kunci
sannan ya kalleta
Momy am fine stop worrying your self am not a small kid any more
"Why shouldn't I worried Jeff u are not picking up my call ta fada cike da damuwa
Abinka da uwa nan da nan yaji tausayin ta ya d'an kara rungume ta tareda bata baki
da kuma yi mata bayanin cewar aiki sukeyi na company a KD karta damu ,
Ya d'an raba jikinshi da nata ya nufi Dadyn shi ya zauna gab dashi,
Abdullah"
Yes Dady" inaso kamar yadda na fada maka a baya inaso inkara mai maita maka' ka
dauki kaddarar ka ka hakura da Ummu Ruman nariga na tsayar mata da miji har mun
karbi gaisuwa kuma baza a dauki lokaci ba za ayi zancen Auren,
Inaso ka natsu yanzu da Angama Gina companin ka zan Gina ma Asibitin ka a duk inda
kake bukata zan nemo maka kwararrun likitoci da zakuyi aiki tare kaji ko?
Gaba daya Jinshi daukewa yayi har ma da ganin shi atake batareda yasan me Dadyn shi
yake fada ma tun lokacin da ya furta zancen Auren Ummu Ruman saidai kawai ganin shi
yayi ya sulale ya zube akasan Capet sharab kamar gawa,
Wani irin ihu Momyn shi ta sanya tareda nufoshi da gudu tana kururuwa........✍
*_Akwai matsala fa fan's anya wannan hukun cin zai haifar da da mai ido kuwa ? Muje
dai zuwa my fan's_*
Ga masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma
hoton domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_love & Destiny_
_Written by Fenerh_
✍✍✍✍✍✍✍✍
GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION.
✍✍✍✍✍✍✍✍
_All the praises and thanks be to ALLAH who has sent down to his slave (Muhammad)
S.A.W the book (Qur'an)and not has not placed there in any crookedness._
*(Suratul Al khaf)*
1⃣9⃣ 1⃣9⃣
➡1⃣9⃣
Sun gama shiga tashin hankali ganin gudan jinin su akwance kamar gawa ,
Ihun Momy ne ya janyo hankalin su Ak suka shigo da gudu domin ganin meke faruwa?
Ak ne yayi gaggawar neman Likitan dake kula da shi suka ciccibe shi zuwa dakin shi,
Likita na zuwa ya fara bashi taimako gaba daya iyayen sun shiga tashin hankali,
Dakyar Likitan ya samu numfashin shi ya dai daita Amma yana bude idanun shi ya
sanya musu kuka mai mugun ciwo da kuma taba zuciya,
Ba Abinda yake fada sai " please Dady ka taimake ni kar in rasa farin Cikina da
kuma Rayuwa ta ina son Ruman kunsani kar Kuyi gangan cin raba mu itama tana sona,
Momy tayi saurin rike shi domin ita Sam bata San kukan me yakeyi ba ta kalli uban'
Kifita acikin wannan maganar Tara sannan ki gargadi d'an ki ya kiyayeni this time
Around bazan dauki abinda zai bata wa iyaye na rai ba bazan kuma Aikata KUSKUREN da
na Aikata a farko ba
Na fada mishi ya hakura da Umma Ruman don haka koda Ace zan rasa shi bazan taba bin
son zuciya ta ba,
Ummu jini na ce y'ar kanwata uwa daya uba daya yar d'an uwana da muke d'an wa da
d'an k'ani don haka dole abi umarnina,
" Ina so in gyara KUSKURE NA na kin yima iyayena biyayya banaso ya Aikata irin
laifin da na Aikata Abaya na sabawa umarnin iyaye,
Na samu ci gaba na Auri Matar da nakeso Amma kullum banida kwanciyar hankali sai
yanzu da na nemi yafiyar iyaye na suka hakura zaizo ya bata min komai to bai iyasa
ba,
Sannan Ummu da su Hajiya zasu dawo nan gidan domin inaso Agyara gidan gaba daya don
haka idan kinsan bazaki iya yima iyayena biyayya ba to kibar min gidana ki koma
Abuja ko ki bar kasar gaba daya ki koma taku couse this is my country,
Ya koma kan Abdullah da yayi shiru dole da kukan da yakeyi ya kalle shi " a baya
rokon ka nakeyi Abdullah Amma yanzu umarni zanbaka ka fita hanyar Ruman Aure zanyi
mata da w'anda takeso kuma idan har ka kuskura iyaye na suka San da wannan maganar
Wallahi bazan yafe maka ba,
"Idan ka kuma furtawa koda wani kanason Ummu zaka hadu da fushi na Ummu Ruman bata
sonka tanada w'anda takeso ka barta ta Auri zabin ranta na fada maka,
Ya wuce fuu ya fice cikin fushi yana fita security dinshi suka taso ya fada mota ya
bar gidan,
Momyn shi tayi saurin karasa wa ta rungume shi tasanya kuka " Am sory my son is All
my faults please forgive me,
Kukan ma ya ki fitowa yanzu sai zuciyar shi da ke mishi suya kamar ana soyata yau
Dady ne keson rabashi da numfashin shi domin yanaji Ajikin shi Ummu itace rayuwar
shi yana rasata numfashin shi zai tsaya,
Shiyasan duk laifin Ruman ne don da Ace ta Amince mai ba Wanda zai raba su Amma ina
tasa taurin kai,
Bakomai ya barwa ALLAH duk da yasan rayuwar shi bazata taba yin kyau ba idan har
bata tare dashi,
Ruman kuwa tunda tafito tafara baza idanu tana mai neman shi domin ko motar shi
bata gani ba a wajen,
"Toh ina yaje kuma gaba daya hankalin ta yaki kwanciya tama manta da wani Doctor
Sulaiman dake tsaye yana binta da kallo kamar wani maye,
Ya karaso kusa da ita " Hajiya ta ai gani nan a gabanki ko me kike nema?
Tayi saurin kallon shi ta dan ya tsine fuska " kani na da muka zo dashi yanzu nake
dubawa ko ka ganshi ?
Aa banga kowa ba koda na fito nan, OK ta dan matsa kusa dashi ta kalle shi tanaso
ta hango aibun shi amma bata ga komai ba domin Sulaiman ya cika cikakken namijin da
duk wata mace zataso kasan cewa da shi amma kash zuciyar ta na wurin karamin yaron
da take rainawa da farko,
Har yayi surutun shi ya gama hankalin baya tare dashi da kanshi ya Ankare " Hajiya
Ummu da gani Agajiye kike don haka bari inbarki kije ki huta nima Kaduna nakeso in
shiga domin inaso infara shiri da wuri akan maganar Auren mu,
Gabanta ta mugun bugawa tayi saurin kallon shi so takeyi ta bude baki ta fada mai
ita bazata Aure shi ba Amma bakinta ya mata nauyi takasa furta koda kalma daya,
Tana shiga cikin gidan dakin shi ta tura ta shiga " ko ina nan kamar y'an da ta
barshi don tun kafin taje Kaduna kullum sai ta gyara shi da Alama ma ko shigowa
baiyiba,
Kan katifar shi ta nufa ta fada tareda sanya kuka mai karfi saboda tasan ba w'anda
zai jita
Najama kaina waini Jan Aji gashi nan Jan Ajina zai kaini ya baro zan tafka mugun
KUSKUREN da zai kaini da kushe wata haka tayi ta kukanta har ta gode ALLAH,
Ganin ba wata mafita kawai ta fito ta daura Alwala ta nufi dakinta domin sauke
farayi
Ko Abinci kasa ci tayi tana Alla Alla gari yawaye taje school ta samu kawayen ta ko
zata samu sassaucin Abinda ke da munta A zuciya,
Zuwan kawunta ya sanya taji mugun dad'i a zuciyar ta mu samman da ya fada musu zai
kwashe su A yau ya mayar dasu can gidan har ma dasu magaji ya tanadar musu inda
zasu zauna kafin a gama gyaran gidajen su gaba daya
Tafi kowa farin ciki domin tana saran ganin shi a koda yaushe idan har tana cikin
gidan su Hajiya ce dai take so ta kwafsa musu
Jafaru da ka barmu kawai idan an gama gyaran gefe daya mukoma dayan basai mun
takura muku ba kasan idan har ni na y'ar da matarka fa baturiya kuma suma su
magajin ba y'arda zasuyi ba,
"Inna don ALLAH ki sa baki nasan da kinyi wa baba magana zai Amince innan mu kuwa
kinsan bazata ki bin umarnin shi ba kiyi hakuri ki Amince don ALLAH,
Toh shi kenan kaje idan mun gama magana Anjima sai kasa driver yazo ya kwashe mu
kafin nan ma mun d'an tattara Abubuwan mu masu Amfani,
" Inna basai kun kwashi wasu kayaba na tanadar muku komai a can,
"Au kace sai da ka gama tsarin ka sannan ka fada mana ko? Dariya kawai yayi ya
shafa kanshi sannan ya ce Amma idan ba damuwa inaso muje tareda Ummu Ruman yanzu,
Aa ni na isa in hanaka daukar y'ar ka ai gata nan kuje ALLAH yayi Albarka ya kuma
shirya ku da dukkan zuriar ku baki daya, ya Amsa da Ameen,
Ummu kuwa jakar ta kawai ta d'auka d ta dawo da ita batareda ta nemi komai ba sai
kuma system din shi dake dakinta ta saka ta cikin hijabin ta ta bishi tareda
Sallamar Hajiya,
A sauka lafiya tunda kinzama ta maula kowa ya gara shi wancan ya kwasa shi kuma
wannan ya dawo ya kwasa aje ALLAH ya rabaki da sharrin baturiya,
Dariya kawai tayi don tasan halin Hajiya da mita ta wuce domin ita damuwar ta ma
kawai ta isheta,
Tunda suka fito security duk suka taso ya karbi makullin mota daya a hannun Ak,
Abinda kawai ya fada kenan cikin bada umarni sannan ya ce" Ummu shiga mota mutafi
Saida suka d'an yi tafiya sannan ya faka motar shi a gefen titi ya kalle ta "Ummu"
ta Amsa cike da jin kunya tareda dukar da kanta kasa kadan,
Nasan tun zuwan Abdullah Nigeria yake takura miki duk da nasan cewa soyayyar da
yake miki kaddara ce da ta Afka mai tun yana karami tunma bai sanki ba bai taba
ganin ki ba tun baisan cewa ke jinin shi bace, nasani Abdullah yana miki mugun so
nasan komai nida mahaifiyar shi Amma hakan ba zai sa intauye miki y'an ci ba na
hanaki zabin ranki shiyasa nayi gaggawar karbar masu neman Auren ki,
Ki kwantar da hankalin ki Abdullah indai ni na haife shi ba zai kuma damun Rayuwar
ki ba har ki yi Auren ki da w'anda kikeso, yanzu haka na baro shi ba lafiya don
haka kar wani Abu ya daga miki hankali ALLAH yayi miki Albarka,
"Wayyo ALLAH na shine abinda ya fara fitowa a cikin zuciyar ta " Yanzu me Dady yake
nufi?
Ya datse soyayyar da Abdullah yake mun a daidai lokacin da nafi bukatar kulawar shi
a dai dai lokacin da nakejin bazan iya Rayuwa babu shi ba nashiga uku na,
Wani irin zufa ne ke tsiyaya ta cikin hijabin ta har zuwa tafin kafarta har suka
isa kofar gidan hankalin ta baya jikinta saida ya ce Ummu kifito munzo gidan,
Tayi saurin kallon tafkeken gidan kamar A kasar turawa tundaga kofar gate din da
suka shiga har zuwa harabar gidan da kuma gefen lambun mai dauke da kayan itatuwan
marmari kala kala kamar wani gidan gona,
Ya yi gaba tareda cewa muje" bata kara tsinkewa ba saida suka isa bakin kofar glass
din da saida ya sa hannun shi ta bude sannan suka shiga,
Badon tana cikin damuwa ba ba Abinda zai hanata kauyanci Ace irin wannan gida kamar
baza a mutu ba kai jama'a
Tun shigar ta take baza idanu ko ina tana karewa Aljannar duniya kallo a Gaskiya
sai yanzu ne ma ta kara sakan kan cewa da Al amarin soyayyar da Abdullah yake nuna
mata w'anda ke cikin irin wannan daular Amma ya hakura ya zauna a irin gidan su
saboda kawai so"
Ita kuwa wane irin shirme ne ta tafka da ta kasa fahimtar hakan tunfarko
Soyayya Gaskiya ce idan ba don so ba ita tasan cewa Abdullah yayi mata nisa duk da
kasan cewar shi d'an uwanta na jini,
Dady ne da kanshi ya nuna mata wani daki dake cikin katon falon,
Ga dakin ki nan Ummu idan Akwai Abinda kike bukata kiyi magana Ak na nan Akwai kuma
mata masu kula da Aikin gidan,
Ta Amsa da toh sannan ta shiga ciki tareda tunanin me zai faru da su a cikin wannan
gidan..........✍
_Allah yasa muji Alkhairi y'an uwa fatan kowa yana cikin koshin lfy Allah ya sada
mu da Alkhairi n dake cikin wannan rana ta jumu'a Ameen_
a masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma
hoton domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
✍✍✍✍
GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION.
✍✍✍✍
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
*_Aslm yan uwa Kuyi min Afuwa da KUSKUREN number da nayi a last post dina instead
of insa 18 nasa 19 Don haka zancigaba da hakan kawai na gode_*
2➡2⃣0⃣
0 20
2⃣0⃣
Tunda ta shiga cikin dakin zuciyar ta taki natsuwa, shi kawai take murad'in gani A
idanun ta,
Nan take wata zuciyar ta Bata shawarr fitowa ta d'an duba ko zata ganshi,
Ta fito falon Amma ta rasa wace kofa zatabi saboda kofofi ne birjik a cikin falon
kar taje ta shiga inda bai kamata ba,
Ganin Shigowar wata y'ar budurwa dauke da tray da ya sanya ta saurin yimata magana'
Cikin halshen turance ta gai sheda Ruman tareda girma mawa "Ma'am do you need
something?
budurwar tayi saurin cewa" Ok Am coming let me take this to the young master....
Cewa kawai tayi ta tafi ta samu kujera A falon ta zauna tareda bin bayan yarin yar
da kallo har ta shige cikin wani daki,
Har ta dawo ta na nan a zaune tarasa meke mata dad'i A zuciyar ta,
Su Hajiya ma sun zo an basu wasu dakuna can ta baya domin sunki y'arda Sam su zauna
ta cikin gidan " tunda Akwai dakuna ba dole mu zo kuma mu takura kuba
Ruman ma taso ta zauna da su Dady ya hana yace ita ta zauna Abinta a cikin,
Ya wadata su da kaya na more Rayuwa Abinci kala kala suturu Alhmdulillah domin sun
gama tsara komai da d'an uwan shi ko wannen su kok'arin faranta wa iyayen su rai
kawai sukuyi kuma sunyi matukar farin ciki da hakan
Ruman kuwa har wayewar gari bata sashi a ida nun ta ba shi ma kanshi bai San mai
yake faruwa ba duk da jikin shi yayi sauki Amma Akwai ciwo mai girma a cikin
zuciyar shi
"Shiya sa Sam baya kaunar fitowa sallar ma a cikin dakin yake yinta
Sai da ta gama shirin zuwa makaranta ta tuna da cewa ta na kusa da Kawarta yanzu
ita jiya Sam ta manta da cewa tana kusa da Hajara,
Wayar ta ta nema ta fara kiranta tana d'auka tace mata" kina ina ne?
School din fa? Yanzu zantafi, kibiyo ki dauke ni ina unguwar ku tunjiya,
Wani irin ihu ta sanya domin tasan inda zatazo har ta kwana " Wayyo dad'i gani nan
zuwa yanzu kuwa kawata,
Ta datse kiran tana mai dariyar Haukar hajara, break fast din ma da aka kawo mata
kasa ci tayi domin ita kadai tasan irin halin da zuciyar ta take ciki,
Saida ta fito sannan ta shiga wurin su Hajiya ta samesu Zaune har da Dady cikin
farin ciki sai hirar su sukeyi ta durkusa har kasa ta gaida kakan nin ta,
Tareda Dady "Ummu zaki wuce ? "Eh Dady " ok nayiwa driver magana da zai rika kaiki
don haka yana jiranki a waje idan kinfita tace to nagode Dady"
"Hajiya ta kalle shi " Jafaru wai ni ina Matar taka take ne? Munzo tunjiya amma ko
tazo ta gai shemu idan taki zuwa gidan mu na talaka to mu gamu a gidan ta sai tazo
mugaisa ko,
Duk'ar da kanshi yayi cike da jin kunya " Inna bata gari ne tana Abuja'
Tana fitowa Driver ya taso da sauri " Hajiya muje ko? Kafin ma tayi magana hajara
ta iso "kabari kawai zamu tafi da kawa ta'
Ya ce " Adawo lafiya ta Amsa da Ameen tareda shigewa motar suka tafi,
"Kawata ya banga young crush dinki ba? Ta kalle ta cikin damuwa tareda war ware
mata dukkan matsalar da take ciki'
" kuma tunjiya da nazo ban ganshi ba " Wallahi ina cikin damuwa kirji na har zafi
yake mun tsabar tunani da kuma tulin damuwar dake cikin rai na,
Hajara ta matukar tausaya wa kawarta " a Gaskiya Queen tun farko ke kika ja koma
meye da kin bashi hadin kai da duk haka bai faru ba,
Toh yanzu ki fadawa Hajiya mana, " kinsan y'an da Hajiya ke son Doctor kuwa?
Ni yanzu menene mafita ki fadamin gaba daya na kasa sarrafa kwakwal wata, nidai
mafita daya ce kawai ki fadawa Hajiya,
Bazan iyaba Abin da nauyi ince mata wai kanina nakeso Wallahi banaso ta sani nafiso
shi ya fada da kanshi idan sun tanbaye ni sai ince na y'arda Amma haka kawai bazan
iya furtawa ba,
Lallai kuwa zaki tafka KUSKURE babba Queen, nidai ki tayani Addu'a,
"ALLAH ya sa mudace gashi kin haukata min yaya na ko jiya ya kirani wai bakya daga
mai waya,
Kibari kawai ni tashin hankalin da nake ciki baya bari na ko kallon wayar inyi ,
Toh ya shirin Auren Sumy ? Ke muke jira ai ya kamata mu San Abinyi lokaci na
tafiya,
Karfe biyu ta shigo gida lokacin tayi mugun gajiya ga kuma wata uwar yunwar dake
Azal zalar ta ko gefen su Hajiya bata kalla ba ta shigo falon tareda tube Hijabin
jikinta burin ta kawai ta sakar wa kanta ruwa ko zataji sanyi Ajikinta,
Tun Shigowar ta cikin falon idanun shi suka sauka akanta jikin tsananin mamakin me
yakawo ta nan kuma saboda ko kofar falon bai fita ba bai kuma San da zuwan su gidan
ba,
A jikinta taji a lamar ana kallon ta tayi saurin daga kanta tareda kallon tsakiyar
falon,
Tsaya wa taki cak har tana Sakin hijabin dake hannun ta domin ganin shine zaune
hannun shi rike da wani dan karamin glass cup yana shan ruwa daga shi sai short
nicer da kuma singlet,
Yayi y'ar rama kadan ga fuskar shi ta kara fayau da ita kyan shi ya kara fitowa ga
sumar kanshi na sheki kallon shi takeyi kamar ta hadiye shi tsabar sonshi da ke
kara huda jinin jikin ta,
Tunda suka hada ido sau daya ya dauke kanshi tareda maida hankalin shi a kan TV
dake kunne a bangon falon,
Jikinta yayi mugun sanyi da irin halin ko inkula da ya nuna mata kaddai ya hakura
da ita?
Ko dai har Dady yayi mai iyaka da itan ne? Tayi saurin dafe kirjin ta saboda mugun
bugawar da yayi,
Dukawa kawai tayi ta dauki hijabin ta ta nufi hanyar dakinta tana tafiya tana
waiwayen shi Amma ya dauke kanshi ko kallon ta baiyi ba,
Tana shigewa ya ajiye cup din hannun shi tareda runtse idanun shi ya kai ma iska
naushi wasu irin hawaye ne da baisan ranar daina zubar suba suka rinka Ambaliya a
kumatun shi,
Dady ya shiga tsakanin su kuma yanzu ya dakko ta ya kawota har cikin gidan bayan
yasan cewa zuciyar shi bazata taba hakura da ita ba idan har zai rika ganin ta a
kusa dashi,
Ahankali ya Mike ya na tangadi kamar yasha wani Abu ya nufi dakin shi yana tafe
yana kallon kofar dakin da take ciki'
"Tun shigar ta dakin ta fada kan gadon tareda dafe k'irjin ta " wani irin sonshi ne
ke kara fisgar ta ga kuma wani irin mugun feelings akan shi da take ji don tana
tuna irin yanayin da ta ganshi lokacin da ta shigo'
Tasan ALLAH yayi mai kira irin ta zaratan maza kamar ba karamin yaroba ba Abinda
yake mugun burgeta a jikinshi irin wannan sumar dake kwance ako ina ajikin shi,
Nan da nan taji tsigar jikinta na mikewa wa har wani irin yam takeji a jikinta don
zuciya da sake sake har ta hangota kwance a cikin wannan kyakkyawan kirjin nashi
mai fad'i
Ta Dade tana sanya wa zuciyar ta Abinda Sam bazai taba yuwuwa ba sannan ta mike
dakyar ta fada bathroom ta watsa ruwa tareda dauro Alwala saboda la'asar ta kusa ta
yi Salla tareda Addu'ar ALLAH ya kawo mata mafita sannan ta shirya cikin wata
doguwar rigar shadda blue wadda tasha stone work kamar wata sabuwar Amarya ta daura
dankwalin kayan sannan ta feshe jikin ta da turaruka masu sanyin kamshi ta kalli
Kanta a mirror ita kanta tana mamakin irin wannan kwalliyar da tayi a dai dai
wannan lokacin,
Ta fito hannun ta rike da wayar ta sai baza kamshi takeyi kanta a kan wayar tana
duba sakon da Nasir ya aiko mata,
Kamshin turaren shi da kuma zazzakar muryar shi mai tsaya wa arai tayi mata
welcome,
Tayi saurin daga kanta tareda kallon shi yana sanye cikin kana nan kaya farare
kamar koda yaushe ya fito kamar ka sace shi ka gudu,
Yana tafiya cikin natsuwa waya yakeyi akan Aikin ginin su na company kawai ji yayi
yayi karo da mutum wayar dake hannun shi da tata gaba daya suka tarwatse
Tundaga kasa ya fara kare mata kallo tayi masifar tafiya da shi
Har ya dire akan fuskar ta da d'an yi ma make up kadan zuciyar shi na har bawa
cikin sauri yayi saurin saita kanshi ya duka tareda kwashe wayar shi da ta watse ya
mike batareda yace mata komai ba,
"Abdul' yaja ya tsaya kamar an dasa shi tareda dunkule hannun shi yana mai jin
bugun zuciyar shi na karuwa,
Ta matso cikin karfin hali har zuwa gaban shi ta kalle shi cikin ido,
" Abdul nayi maka laifine? Ya dan kalle ta shima idanun shi duk sun juya " me
yafaru?
"Abdul don't play innocent " tunjiya nazo gidan nan ka ganni kuma Amma ka nuna baka
ma damu dani ba bayan ba haka muka rabu ba
"Meye ya canja? " komai ma ya canja kalli y'an da kake share ni Abdul bayan ba haka
kakeyi mun ba ta furta kamar zatayi kuka,
"Yaya nake miki a da da banayi yanzu? Ta ya mutse fuska kamar zatayi kuka" haba
Abdul ka fa canja sosai Abdul din da nasani A kullum yana son kula dani yana damuwa
da Al amurana Amma yanzu ko kallo na ma bakason yi,
"" Hmm meye Amfanin kulawar bayan bakya so Kince Kinfi karfina har ma kin iya bawa
wani namijin dama ya turo to kuma yanzu me kikeso inyi?
Gashi Dady ya ce infita hanyar ki don haka mu yi zumunci kawai dama kin girme ni
don haka I a continue calling you my Aunty ko ba haka kikeso ba?
Ya fada yana kallon yanayin ta" kanta ta fara girgiza wa " no Abdul ta furta dakyar
idanun ta na fitar da ruwan hawaye'
Yayi saurin dora hannun shi akan fuskar ta yana mai share mata hawaye " ya isa haka
please ya furta muryar shi na rawa" horon zaiyi min yawa kibarni kawai da Abinda
yake damuna don't furnished me with your tears please,
"Ruman koda ace ina sonki meye Amfanin shi yanzu bayan Dady ya shiga tsakanin mu
kuma kema bakya son.....
Tayi saurin rufe mai baki batareda ta shirya ba ta furta" I love you too Abdul I
really do, bazan iya Rayuwa da kowane namiji ba bayan kai Kaine farin Cikina ina
sonki kamar y'anda kake so na Abdul,
Jikin shi na rawa ya riko kafadunta " said it a gain please Ruman tayi saurin dai
daita Tunanin ta domin ta d'auka a zuciya take zancen batasan ya fito fili ba tayi
saurin zare idanu zata waske ya riketa tamau tareda riko hannun ta ya nufi dakin
shi da ita,
Yana shiga ya kulle kofar tareda zaunar da ita akan kujera irin ta hutawar nan dake
cikin dakin ya zauna a kasa fuskar shi na bayyanar da Annuri
Ita kuwa duk kunya ta gama rufeta wai itace ta furtawa kanin ta cewar tana sonshi
"Ruman look at me please"" ya furta Ahankali " ta dago kanta kadan cikin jin kunya
ta kalle shi " da gaske kinason Abdullah? yaushe kika fara sona don ALLAH? Meya sa
kika ki nunamin hakan kiketa wahalar da Rayuwa ta ?
Ta kalle shi cikeda jin tausayin shi dake kara ratsa jijiyoyin jikinta "Abdul Am
sory kasan dalili na tun farko ta yaya zan iya nunawa duniya cewar kanina nakeso"
Ya hade rai " kinga matsalar ki ko songirma "gashi taurin kanki yanaso ya jefa mu
cikin matsala wai ma da shekara nawa kika girme ni ? Da kullum zakiyi zancen
shekaru
Ya mike tsaye tunawa da yayi da kashedin Dadyn shi" ya girgiza kai " is to late
now Kinriga kinja mana Ruman don haka yanzu bamuda wata mafita saidai kawai mu
hakura tunda har kin fitar da mijin da kikeso ya juya zai fita tayi saurin riko
hannun shi hawaye na bin kuncin ta,
Tana girgiza mai kai" Abdul yanzu zaka iya hakura da ni? Yanzu kana nufin zaka
barni in Auri wani bayan gaka ?
Ya kuma juyowa zuwa gareta " haka kika zaba tun farko shiyasa kika yita nuna taurin
kai " yanzu ya kikeso inyi Dady ya fadamin idan har na furtawa wani a cikin family
ina sonki bai yafe mun ba,
Don haka yanzu kece kawai zaki nema mana mafita ki fadawa Hajiya kawai ko Baba
Muhammad sune kawai zasu iya tsaya mana,
"Bazan iya ba Wallahi inajin kunya" ya matse fuska yafara kokarin cire hannun ta
Acikin nashi ta kara rikeshi tamau ,
Ki sa kemun hannu intafi Ruman fada kawai kikeyi Kice wai kina sona idan har kina
sona mai zai hana ki fada wa magabatan mu ,
Jikinta na rawa ta fada kan kirjin shi tareda rungume shi kamar zasu fadi ta sanya
kuka mai ratsa zuciya,
"Wallahi bani nace Sulaiman ya turo ba ni bana sonshi Amma bazan iya kallon idon
Dady infada mai hakan ba bayan yana ganin ya isa dani " please Abdul do something,
Wani iri yakeji tun daga kan babban yatsar kafarshi har zuwa kwakwal war kanshi ya
sanya Hannayen shi duka biyu ya zagaye ta kamar zasu maida juna ciki,.
Sun dauki lokaci yana manne da ita Ajikinshi saida yaga suna shirin zubewa sannan
ya dan fara sassauta rikon da yayi mata,
Ya dan dagota kadan tareda yin murmushi " my Aunty ki dan sassauta min haka mana
wannan irin matsa ai Saiki sa tsohuwar damuwa ta tashi kinsan dani dake s....saurin
rufe mai baki tayi tana dariyar jin kunya
Kibar ni infada mana " ina sonki fiye da kaina my Dream kar ki Auri wannan gayen
zuciya ta zata buga ke ko ganin ku a tare banason yi don ALLAH ki daina kulashi
kafin mu samu mafita,
Ta yi saurin share hawayen ta " tareda kada mai kanta kadan yace " tank you Amma
yanzu za arika bani kulawa ko? Inaso soyayyar mu ta zama sirri kafin mu nemi
mafita kinji don ALLAH k'arki kuma juya min baya I can't bear to loose you
Ta yi murmushin da ya kusa tafiya da numfashin shi domin dimple dinta yayi mugun
lobawa " please my dream ki d'an rage yimin irin wannan murmushin idan kikayi wata
rana zai janyo inyi aika aika,
Koda yake Am still a small kid har yanzu ban kosa ba ko tayi saurin bude baki
tajuya da dan guduna domin tasan tsokanar ta yakeyi yayi dariya mai dan karfi kadan
yabi bayanta yayi saurin riketa,
" muje ki rakani mu siya waya tunda kinfasa mana garin kallon masoyin ki ta kalle
shi tareda dukar da kanta cikin jin kunya,
"Muje kaga su Hajiya kafin mu tafi " ya waro ido sannan ya riketa cikeda jin dad'i
da kuma nishad'i ji yake kamar karsu fita suyi ta zama a cikin dakin suna shan
soyayyar su Amma ina yasan zaman Sam bazai haifarda da mai idoba,
Tana gaba yana biye da ita cikin jin dad'i har suka isa gefen da su Hajiya suke
suna zaune sai hirar su sukesha da ka gansu kasan suna cikin kwanciyar hankali,
Da sallama suka shiga " Aa kaga turawa dama kana garin ? Inji Hajiya tafara
tsokanar shi" eh Granny ina nan bansan da zuwanku ba sai yanzu my d... Tayi saurin
taron numfashin shi " yanzu nake fada mai kuna nan kuma,
Yayi dariya domin dama da gangan yaso fadar my dream din sundan dade a wurin su
suna d'an hira har saida ya matsu da kanshi yake mata signal akan sutafi,
"Hajiya zamuje shopping yanzu zamu dawo nida Abdul' ta fada cikin dakewa kamar ba
komai a tsakanin su,
" to kudawo lafiya kardai Kuyi dare ta mike tare da cewa to tayi gaba shima ya bi
bayanta dakinta ta koma yana biye da ita kamar bindi har ta bude world rob batasan
yana biye da itaba saida ta Ciro gyalen da zata yafa taji yace " ki canja kisa
hijab,
Tayi saurin kallon shi yana tsaye a bakin kofar ya harde hannu a kirjin shi yana
mai binta da kallon so da kuma birgewa ,
Dariya kawai tayi tareda Ciro katon hijabi ta sanya ta kalle shi " Wannan yayi? "
saida ya kare mata kallo sannan ya daga mata Hannu Alamar yayi ta sanya takalmin
ta Mara tudu,
"Muje ko ta furta bayan ta karaso kusa dashi ya sauke Ajiyar zuciya yana mai kallon
ta kamar zai hadiye ta,
Hannun shi ya sanya tareda fisgota zuwa kirjin shi saida ta d'an ji tsoro " Abdul
""
Ta fada da d'an karfi shikuwa ai tuni ya fara shinshina dai dai wuyan ta tana d'an
ture shi "Abdul muje mana dare zaiyi man...
Kasa karasawa tayi sakamakon kiss din da ya manna mata a kumatun ta kafin ta kara
motsawa ya kuma manna mata a goshi gaba daya ya kashe mata jiki da zafafan kisses
dinshi dake tasiri a jinin jikinta nan take jikinta ya fara rawa,
" Abdul stop" ya furta dakyar tana nokewa " ya d'an girgiza kanshi kadan yana kara
cacumar ta dakyau ,
Kar kiyi kokarin raba jikina da naki don ALLAH yana maganar still fuskar shi na kan
yawo akan tata ya hade goshin su wuri daya,
Tana dan zamewa saboda irin tasirin Abinda yake mata Ajiki "Abdul please ta kira
sunan shi da ya kuma tsuma zuciyar shi batareda ta shirya ba ya manne bakinshi akan
nata,
Ya fara tsotar lebenta na kasa a hankali yana d'an hura mata iskan hancin shi dake
fita dakyar cikin gwama numfashi batasan lokacin da ta kara tallafo keyar shi ba ta
fara tsotar leben shi na sama,
Ai tuni ya manne ta gam ya fara tsotar bakinta kamar zai cire mata shi a hau kace
kafin ya samu damar cafko halshen ta yana mishi lafiyayyan tsotar da ke shirin
dauke numfashin su ba Abinda sukeyi sai gwama numfashi mu samman shi da Sam ya kasa
control din kanshi ji yakeyi idan ya tsaya numfashin shima tsaya wa zaiyi,
Jin yana kokarin daga hijabin jikinta yasa tayi saurin saita natsuwar ta tareda
kwace lips dinta daga nashi dakyar yaja numfashi tareda Sakin ta ya fada kan sofa
yana gwama numfashi mai wuya,
Ita ma dakyar ta iya tsaya wa da kafafunta kafin ta fita daga cikin dakin da sauri
tana fita ta zauna akan kujera tana runtse idanun ta tareda matse cikinta ita kadai
tasan irin namijin kokarin da tayi wajen hana zuciyar ta biye mishi,
Tana haka ya fito har ya canja kayan jikinshi zuwa wasu daban ta d'an kalle shi
kadan ta dauke kanta " idanun shi gaba daya sunbirkice kamar wani Masha yi,
"Muje ya furta a kasalance mikewa kawai tayi ta wuce gaba yana mai binta a baya sai
famar cije lips dinsa kawai yakeyi,
Shi ya bude mata kyakkyawar sabuwar motar shi suka shiga ya tayar da ita saida
suka hau titi ya d'an kalle ta
" Ruman zuciya ta bazata iya jure wa ba nagaji Na matsu kizama matata kiyi wani Abu
akai don ALLAH kafin in fada halaka ya fada tareda riko hannun ta daya yafara murza
wa a cikin nashi,
Wallahi dakyar nake samun bacci inada karfin sha'awa mu samman akanki saboda kece
muradin zuciya ta
Wai shin kinajin irin y'anda nakeji kuwa ? Ya janyo hannun ta zuwa kirjin shi ki
taba kirjina kiji y'anda yake bugawa da karfi
Ruman ki tallafi Rayuwa ta ina cikin garari kulawar ki kawai nake bukata ke kinsan
soyayyar mu mukaddari ce ALLAH ne ya sanya min soyayyar ki Acikin zuciya ta ba yin
Kaina bane,
A hankali ta zame hannun ta tareda dukar da kanta kasa " yanzu' ya kake so inyi
Abdul bayan na fada maka nima ina...
_"Say it please I wants to hear it a gain from your mouth "Ruman say u love me
please "_
Kallon shi tayi " muna kan titi ne fa ka kalli gaban ka ya ki juyawa still yana
kallon ta " tsoron me kike ji? K'arki mutu to ai idan ma mutuwar ce tare zamu tafi
don bana fatan in mutu inbarki saboda zaki zama rabon wani nafiso mutafi tare
"I love you" ta furta da sauri saida ya kusa Sakin kan motar saboda y'an da Kalmar
ta shige shi
"Yayi saurin tsaya wa tareda juyowa dakyau yana fuskan tar ta" woo My dream tank
you yana Sakin murmushi mai kayatar wa _I love you more and more my dream_
"Abdul muje magrib nayi fa" ai ni to idan har zakiyita kiran sunana a haka bakya so
mutafi kenan don kina jefani cikin yanayi,
"Meyasa Bakajin kunya ta ne wai? Hhhh yayi dariya " ina namijin zan tsaya jin
kunyar wadda wa tarana da kanta zatayi min wanka,
Nima ko ALLAH idan mukayi Aure zaisha shagwaba don narkewa zanrikayi komai sai
kinyi mun da kanki har shafa mai da sa kaya,
Ta zaro ido waje " da girman ka zanyi ma wanka? " kai Aunty na ni yaushe na wani
girma nifa ko yanzu zan iya tube wa a gabanki bayan ni har yanzu karamin
yarone..........✍
masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
2⃣1⃣ 2⃣1⃣
➡2⃣1⃣
Tafiya sukeyi kamar karsu isa wurin da zasuje saboda farin cikin da suke ciki
Abdullah kuwa baya minti biyu saiya kalleta fuskar shi dauke da wani irin
kayataccen murmushi da kuma Annuri na farin ciki,
Pz sukaje ya zabo masu wayoyi masu kyau da kuma tsada har saida taso tayi gaddama
akai ganin uban kudin da ya fitar domin siyan waya kawai,
"Kinfi karfin komai a wurina my dream banaso inkuma baki Abu kiyi kaddama a kai,
ko bakya sona ne kamar yadda kika fada?
Ta kalle shi " meyasa zakace haka gani nayi kawai wayar tayi tsada da yawa,
Daga nan ya wuce da ita Inna I dear shopping complex tunda ya faka ya juyo tareda
riko hannun ta daya " Baby na kin tuna Abinda yafaru Anan?
Tayi dariya kadan tareda kawar da kanta gefe , shima dariyar yayi sannan ya fito ya
bude mata kofa " muje my Queen "
Ta kalle shi " kaima zaka fara kirana da wannan sunan ko?
"Uhm ai Gaskiya ne you are a Queen ya d'an matso kusa da ita kamar zai rungume ta
" and you the Queen of my heart
"Ina sonki sosai Ruman' tayi saurin wai gawa saboda idanun mutane dake kallon su"
muje Abdul kaga ana kallon mu'
"To shine me? Ni dai muje mema zakayi Anan daka kawo mu?
" Muje kiga me zanyi ya riko hannun ta ta fisge tana dariya ALLAH Bakada kunya
Abdul,
Tayi gaba yabi bayanta yana mai Bata Amsa " idan naji kunyar ki na fada miki nizan
sha wuya shiyasa nake cire kunyar don zata cuce ni nan gaba,
Sun shiga gefen kayan kwalliya ya riko hannun ta tareda matsowa gab da ita ya rada
mata "My dream ki dauki Abinda kike bukata anan ,
"Ta kalle shi " ni banason komai Anan mu tafi kawai" ban y'arda ba ya wuceta
tareda fara Kwasar kayan kwalliya kala kala da turaruka masu tsada da kuma kamshi
saida ya cika dan karamin Kwan don dake Ajiye domin irin hakan,
Sannan ya jata zuwa gefen kaya ya fara zaba kamar zai bude wani d'an karamin shago
saida ta riko hannun shi" Abdul ya isa haka mana ya zanyi da wa innan kayan bayan
wa inda Dady ya siyomin,
"Idan Inayin Abu ki kalle ni kawai banason magana ya fada yana d'an bata fuska,
" kayi hakuri tom nayi shiru " uhm that's better ya cigaba yakoma kwaso mata jakun
kuna da kuma takalma designers,
Haka takoma gefe kawai tana kallon shi har ya kwasa iya kar y'anda yakeso sannan
ya biya aka kwashe musu zuwa mota,
Saida ya cika seat din bayan motar shi tab da kaya sai binshi takeyi da ido don
Abin yaso bata tsoro saika ce hauka,
Suka nufi gida bayan ya tsaya ya siya musu gasassun kaji suna isa ana kiran Salla
ya bude mata motar ta fito,..
"Kishiga ciki zanje masallaci indawo kisa Mary ta hada min coffee yunwa nakeji ina
dawo wa zanci Abinci'
Saida ya shigo da kayan ma ta kara ganin yawansu tana mamakin irin dukiyar da ya
narkar a banza yanzu'
Bathroom ta fada saida ta watso ruwa sannan ta nemi wani Riga da wandon Pakistan
pencil ne wandon ya kamata dam sai rigar da tasha tsagu tundaga kasa har zuwa kusan
hips dinta daga sama ma ta kamata dam komai ya bayyana tayi kyau sosai ga sumar ta
datasha gyara ta kameshi a gefen wuyanta da ribon tareda kitse bakin shi,
Sai baza kamshi takeyi kamar wata sabuwar Amarya sannan ta sanya hijabin ta ta
tayar da Salla, saida ta idar ta tuna sakon shi na coffee da kanta ta mike ta nufi
kitchen din,
Tundaga farkon kitchen din ta fara tasbihi tana ganin exactly irin wa inda ake
nunawa a TV Abin ya mugun burgeta da kyar ta gano wurin da gas cooker din yake tana
tunanin y'anda zata kunna Mary ta shigo,
"Can I help you ma'am? " yeah please come and on this gas for me I want to make
coffee'
Da taimakon Mary ta hada mai lafiyayyan coffee ta sanya a dan karamin flask mai
kamar jug saboda kar ya huce ta dora shi a wani madai daicin tray ta dora cup da
kuma spoon guda daya ta d'auka tareda nufar falon da shi w'anda yayi daidai da
dawowar shi daga masallaci,
Tun Fitowar ta ya zuba mata ido yana Sakin kayataccen murmushi saida yaga zata nufi
dining sannan yayi gyaran murya "
" Coffee din ne Anan ? " eh "muje dakina muci Abinci I keep something for us,
Ta dan kalle shi irin rashin yardar nan " inaso inje wurin Hajiya ni banajin yunwa
kaga batasan mundawo ba karsuyi tunanin ko muna waje ga dare yayi".
"OK muje mu gansu mudawo yanzu I need your time gobe inaso inje Kaduna induba
Aikin mu,
Ta wuce gaba yana mai bin bayanta da kallo tareda jin wani irin sauyin yanayi dake
ratsa jinin jikinshi"
"Yayi saurin matsawa kusa da ita " my Queen irin wannan Adon zaki dauki Alhakin dan
karamin yaro fa tayi saurin kallon jikinta " wane ado nayi Anan ?
"Kayan bacci ne fa" kai wallahi bazan y'arda ba idan munyi Aure kirika sanya wannan
kayan ba ai zaki wahalar dani sosai ni Nafisan ganin ki dagake sai y'ar sexy
sleeping dressed,
Ai da sauri ta wuce don batason jin rashin kunyar shi Sam baida kunya kokadan
wallahi " dariya ya sanya na yadda ta sanya sauri tayi gaba batareda ta jira ta
karasa jin sauran zancen
"Da Sallamar ta ta shiga ta samu gwaggo Amina da Hajiya kawai suna hira ta sanya
dariya cikin shaki yan ci" Hajiya kaka mai Abinci ta zama y'ar fursuna yanzu bakuda
aiki saidai kuci kuyita zabga hira ko kuma kallo ,
"Ai dole kiyi dariya tunda iyayenki sun kunshe mu a cikin wannan gida kota ina
gilashi saikace wasu gasassun kaji'
Dariya kawai suka sanya har da Abdullah dake shigowa" ALLAH ya taimaki ran tsofaffi
"kaima ALLAH ya taimake ka shaki yai kawai idan kuka maza iyayen ku zaku jama wa
don yanzu sai mu tada balli muje gidajen mu zamuje'
Hmm gidajen da duk an siyar ai dama Plan su Dady suka hada muku bazaku koma ko ina
ba,
Kabari d'an manzo d'an nan? Ya kyal kyale da dariya ganin irin zaro idanun da
Gwaggo Amina tayi ' to wallahi yaya bazan y'arda ba haka kawai Ai d'an ki na zuwa
yau ki fada mai na gama zaman gidan nan mutum ba cas ba as ina zan iya,
Kedai bari Amina ko shara saidai kullum wa innan masu guntayen sket din kullum keyi
wai ni Abdullahi bazaku yi musu fada ba surika sa suturar Arziki?
" koda yake kuma ai turawan ne uwar... Hajiya mun dawo fa dama mun shigo ne mu fada
miki k'arki yi tunanin muna waje'
Ruman tayi saurin kwabar Hajiya don tasan sarai me zata fada akan mahaifiyar shi
bayan yana wurin kuma uwa uwa ce,
Yayi murmushi kawai don shima yasan kwanan zancen sannan ya mike " ni dai zanje in
kwanta "Aunty let's go'
" Aa ba wani Aunty ka zauna Muyi hira kafin magaji ya shigo shima tunda ya samu ya
fita yaki dawowa'
Ita ma mikewar tayi " Nina tafi kakus inada Abin da zanyi kafin inje school gobe in
kwashi zero,
"Ku sauka lafiya" ta fita domin shi ya dade ya ficewa " ta fito cikin takunta
Anatse kawai ji tayi ya rungume ta tsam har ta danji tsoro kamshin turaren shine ya
sanar da ita waye'
Ya manna mata kiss a gefen wuyan ta saida tsigar jikinta duka ta mike " muryar ta a
dakile "baka shiga cikiba?
Ya kuma manna bakinshi akan chicks dinta yana kara narkar mata da duk wani sauran
kuzarin da yayi Saura a jikinta" ya zan tafi bayan baki fitoba ai kona shiga ciki
zan kasa sukuni ne kawai muje kibani Abinci ko zan iya ci na dade banci wani
Abincin kirki ba'
Ta d'an kwace jikinta kadan jikinta a matukar mace a zuciyar ta take fadin " wannan
yaron ya faya son jiki'
Rike hannun ta yayi ya nufi hanyar dakinshi da ita " dan ja ta tsaya " mu zauna a
falo mana bai dace ba mu shiga cikin daki,
"Ya kalleta wani iri " kinaso Dady ya gan mu ne atare? Tayi saurin girgiza kai " OK
muje tom,
A kasan dakin ya sanya dadduma tareda jera plate da kuma ledar da ya shigo daita
dazu ya kuma bude fridge din dake cikin dakin ya dakko fresh milk ya ajiye musu,
"Ya riko hannun ta ya zaunar da ita a kan Capet din sannan ya cire rigar dake
jikinshi ya rage dagashi sai dogon wando da kuma singlet kawai,
Ta kuma Harar shi ' nice baby? " na shigesu to ya kikeso in kiraki?
"Kace Ruman ko Ummu kamar y'anda Hajiya kefada,
"Da kanshi ya Ciro musu naman a cikin poilpepper yana nan da zafin shi ya juye akan
katon plate din tangaran ga gashin ya gasu harda wani source din cabbage da Albasa
da kuma kayan miya a gefe wow"
Ya sanya fake ya dibo tsokar tareda nufar bakinta da shi' tayi saurin kawar da kai
" zanci da kaina kaima kaci naka'
Hmm ki cigaba da mun wayau da munyi Aure bazan y'arda ba don kiji,
Saida sukaci suka koshi sannan ta zuba mai coffee ya fara sha ita kuwa ta tsiyaya
fresh milk kadan a cup ta fara sha a Gaskiya ta dade bataci Abinci irin na yau ba,
Yana seeping coffee A hankali yana binta da kallon soyayya da kuma imaging inama
ace Andaura musu Aure ne A yau da Gaskiya bazai bar wannan daren ya tafi a banza
ba,
"Don idan ALLAH ya mallaka mai ita to burinshi na duniya ya gama cika,
Ta Ajiye cup din tareda kallon shi ganin ga badaya ya Ajiye cup din hannun shi ya
zuba ta gumi yana Kallonta'
" Abdul lafiya ? Me kake tunani haka? Ke nake tunani " bayan gani a zaune akusa da
kai,.
"Ina mafarkin ranar da zan mallake gaba dayan ki ranar zan iya bacci kuwa saboda
tsananin farin ciki?
Me zai hanaka bacci? Murna da farin ciki na mallaki Matar da nake so " ai ko yanzu
ka mallaki ni'
"Da Saura tunda bamuyi Aure ba " I want to see you as my wife Ruman shine
mafarkina,
Mikewa tayi " zanje inkwanta bacci nakeji ta duka tareda kwashe plate din da suka
bata " saurin karba yayi ya Ajiye '
"Wa yace ki wahalar min da kanki ? Kibarshi Mary zata kwashe su,
" ta juya zata fita domin taga irin kallon da yake mata kamar zai lasheta,
"Yayi saurin rikota " ta runtse idanun ta domin tasan za arina "Abdul ka barni in
wuce bacci nakeji'
" k'arki tafi don ALLAH bangaji da ganin kiba " dare yayi, " ki kwanta Anan ga gado
please " ya dora habar shi akan kafadarta ya hade Kansu wuri daya,
"Idanun ta ta zaro duka waje tareda kokarin raba jikinsu ya kara damke ta ta
hanyar sanya Hannayen shi duka biyu a west dinta yana lumshe idanun shi domin jin
dad'in yanayin da yakeji"
Numfashin da yake saukewa awuyan ta bakaramin daga mata hankali yake yiba ta fara
kokarin kwace jikinta domin yayi sanadiyyar jefata cikin mugun yanayin da ta dauki
lokaci bata shiga ba'
"Please Abdul ka daina" ta fisgo maganar da kyar "menayi ? Shima ya bata Amsa
dakyar still yana nan manne da ita kamar chewingum,
" Ruman stay hare with me please " banaso kije ko ina inaso inkwanta a kan jikin ki
mai laushi kamar y'anda nake gani a mafarki na idan kin barni yau bazan iya bacci
ba bayan yanzu zuciya ta ta gama yadda da cewar kinaso na,.
Ko Aldarmu bai dace ba bare kuma A addinan ce, ta fada cikin karfin hali tareda
cire hannun shi a jikinta ta nufi dakinta da sauri tana jin wani iri a cikin
jikinta,
Bathroom kawai ta fada batareda ta tsaya tubewa ba ta sakarwa kanta ruwan sanyi har
saida tayi Ajiyar zuciya,
Saida ta dade a hakan kafin ta fito ta tube kayan da suka jike sannan tayi wanka
mai kyau tareda dauro Alwala,
Tunda ta fita ya koma gefe kawai ya dafe kanshi bayaso tayi nisa dashi koda na
minti daya ne burinshi kawai su kasance tare har Abada,
A ranar dakyar bacci barawo ya daukeshi ita kuwa kwana tayi tana saka da war wara,
Har cikin zuciyar ta tana kaunar shi Amma Sam batason yawan taba jikinta da yakeyi
tasan sai tafi cutuwa saboda irin lalurar da take damun ta ta wani gefen kuwa tana
ganin laifin kanta da kuma jin kunyar Abinda ke faruwa a tsakanin su wane irin Abin
kunya ne zuciyar ta takeson ta jefata a cikin shi?
Son kanin ta kuma har takai ga furta mishi hakan kuma shine dalilin da yasa yake
kara shige mata tareda kokarin jefata cikin mugun yanayi,
A Gaskiya da zuciyar ta zata yimata Adalci da ta cire mata soyayyar shi ko zata
samu ta tsira da d'an sauran mutumcin ta, Amma kuma Abdullah fa?
Taga irin farin cikin da ya shiga sakamakon bayyana mai irin soyayyar da take mai
sai Alokacin ta tuna da wayar da ya siyo mata takuma kalli gefen kayan da ya tilo
mata tsabar farin ciki,
Wani irin tausayin shine ya kuma ratsata tasan duk ranar da aka daura mata Aure da
wani sai ya fita shiga tashin hankali,
Ranar bacci kaurace mata yayi ta tashi tareda shirya kayan A cikin Waldrop tayi
plugin wayarta a caji sannan ta fara jero nafilfili tareda neman zabin ubangiji,
"Saida tayi sallar Asuba ta mike domin Sam batajin bacci ta gyara dakinda take tsab
ta baza kamshi kota ina sannan ta nufi kitchen ta samu Mary harta fara aiki ta fara
taimaka mata suka hada lafiyayyun dishes karfe bakwai sungama komai tafito tana
mai bin kofar dakinshi da kallo,
" Wannan Ajebon ko yatashi ? Take Ayyana wa a zuciyar ta ' kawai ganin shi tayi
Agaban ta yana numfashi sama sama ga zufa na tsiya ya a jikinshi yana rikeda gorar
ruwa jikinshi sanye da y'ar Karamar riga Armless da kuma tree quarter kafar shi
sanye da canvas ta waro ido waje " daga ina haka?
Bakya ganine daga jugging morning exercise ta d'an tabe baki ta kauce ya d'an bata
fuska ki tsaya mu gaisa to ko kinaso inrungumo kine kowa ya gani'
Tayi saurin tsaya wa tareda kallon shi " ya marai raice fuska " nidai Gaskiya banga
Alamar na shiga cikin zuciyar ki ba irin wannan rashin kulawar banason shi ya
kamata yanzu da kika ganni kidan rungumo ni inji dumin jikinki Amma now look ko
gaisuwa bamuyi ba kike kokarin guduwa,
"Shigowar Dady ne ya hanata bashi Amsa tayi saurin yin gaba " Dady ina kwana "
lafiya kalau Ummu ya bakunta hope bakya samun matsala da hause help din ko?
Ba komai Dady, ya karaso shima tareda gaida Dadyn " Good morning Dady ya furta
cikin daure fuska Alamar yana fushi da uban ,
Morning ina fatan ka shirya tafiya Kadunan ko? Yes wanka zanyi inyi break fast sai
in wuce " OK that'good.
Ya wuce ciki ya waiga ko zai ganta Amma tuni ta gudu abinta ya girgiza kai kawai
tareda yin kyakkyawan murmushi ya wuce shima nashi dakin cikin sauri yake shirya
wa,
Masha ALLAH shine Abinda na fara furtawa lokacin da ya fito cikin wata irin sky
blue din shadda sabuwa dal tana sheki Anyi mata dinki na yayi da yaji aiki mai kyau
kafar shi cikin takalmi mai kyau baki ga Agogon Rolex sai sheki yakeyi yatsun shi
kuwa wasu irin Azurfa ne manya na maza masu tsadar gaske sumar kanshi ta kwanta
tana sheki ya fito kamar yaune za a daura musu Aure'
Falon yatsa ya yana karewa kofar dakinta kallo tareda kallon Agogon hannun shi
karfe kusan takwas,
Dakin ta ya nufa kai tsaye ya shiga batareda ya jira komai ba " subuhanllah. Shine
abinda ya furta yayi saurin jingina da bango,
A tsaye take gaban mirror tana shafa mai a jikinta towel ne iya kar shi guiwar ta
ta dora kafarta daya akan stool gaba daya cinyoyin ta a waje suna zuba sheki gasu
masha ALLAH,
Sulalewa kawai yayi ya nufi falo ko karyawa bai tsaya yiba ya kira driver yace yayi
driven dinshi don bayajin zai iya tuki a halin da yake ciki domin idanunshi sunyi
mugun ja tsabar fitina irin ta yaran zamani'
Sai bayan fitar shi taji kamar motsin Shigowar mutum tayi saurin wai gawa bataga
kowaba ta cigaba da shirin ta,
Yarin yar baban su Faisal ne da uwarta ta mutu ta barmin damuwa gashi nan tun ba
aje ko inaba tafara zamar min matsala,
Shikuma handsome fa" Saunawa Zanfada miki dangan takar su ? Don ALLAH ki barni da
tawa damuwar da nayi nasarar rabasu da shegiyar uwarsu yanzu komai ya lalace mun
gashi malam yace Asiri bazai kuma aiki a jikinshi ba,
"Ga Shawara Aunty inada wani boka ki bude Aljihun ki kiga aiki da cikawa tayi
saurin rikota " da gaske? ALLAH Aunty " to yanzu' kamar nawa zam bayar ?
Ko dubu Dari ki bayar zuwan farkone idan naje sai Muyi jinga dashi,
"Har dubu Dari Aikin da tsada Gaskiya bazan iya ba " ta mike tareda kakkabe rigar
ta " to ke kika sani ni ina ruwana kinganni nan aiki zanje amun muna nan zakiga
bature na yadawo kisa idanu kisha kallo ke kuma bakin ciki ya kashe ki.........✍
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
_*Matar Soja*_
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
✍✍✍✍✍✍✍
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*
✍✍✍✍✍✍✍
_Written by Fenerh_
✍✍✍✍
GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION.
✍✍✍✍
*_My fan's ako ina ina matukar godiya da kuma irin kaunar da kuke yimin inajin
dad'in Addu oin ku Allah yasaka muku da Alkhairi ya kuma sadamu da Alkhairi na
duniya da lahira baki daya I love you All_*
2⃣2⃣ 2⃣2⃣
➡2⃣2⃣
Tunda ta fito take baza idanu tana duba ta ina zata ganshi Amma har tabar gidan
bata sashi a idoba daga bayane zuciyar ta take bata may be ya wuce batareda ya
nemeta ba,
Taji haushi sosai tareda kallon jikinta domin kwalliya tayimai ta musam man daga
cikin dogayen rigunan da ya siyamata masu kyau da,kuma tsada,
Haka ta shiga ta sallami su Hajiya suna yimata tsiya driver ya kaita school
batareda ta jira hajara ba,
Abdullah kuwa tunda suka dauki hanya ya kishin gid'a a bayan mota yana mai cije
lips d'inshi shikadai yasan yanayin da yake jin kanshi har ALLAH ya kaisu lafiya,
"Bayan suntashi school gidansu suka dawo harda su Sumayya domin sunfara shirye
shiryen Auren sumyn a gefen su Hajiya suka baje sunata tsokanar ta " Hajjaju mai
tuwon yan gayu a Gaskiya munyi missing sosai Su Dady basu kyauta mana ba da suka
hana business,
"To ja'rai kutashi kubamu wuri muhuta tunda kuka shigo Kaina yafara ciwo " Amina ke
ko basu isheki ba?
"Ai ni yaya tashi zanyi inje inkwanta tunda haka akeson ganin mu ba cas ba as,
Kai kuzo muje mudan ci wani Abu yunwa nakeji bazanci Abincin tsofin nan ba, eh
lallai Ruman wato iyayen ki sun rabamu da karfi da yaji tun bakiyi Auren ba ko?
"ALLAH ya tsare ni da mugun gani ni da nayi nawa Auren tareda ke mukaje ko wani ya
rakani?
" Mu za a fara akanmu "to mutuwar ma muyita tare " tayi saurin Sakin ta haba haba
Hajiya " keda kinkusa tafiya nida yanzu na fara zaki wani jani muje tare idan kinje
ina gaida mazajenki da kuma Umma na sai bayan ta furta jikinta yayi mugun sanyi nan
take Annurin fuskar ta ya kauce,
Wuce wa kawai tayi kawayen ta suka bita domin sukansu sunsan maraici na damun
kawarsu domin wani Abun sai uwa idan karasa ta karasa babban bango,
Duk da Hajiya tayi kokari sosai Amma soyayyar uwa daban ce ita kanta gwaggo Amina
saida ta dan share hawaye tunowa da gudaliyar yarta mace ALLAH ya gafarta miki
Aisha' ta furta Ahankali Hajiya ta Amsa Amin don nabiyyun Rahmati
"Dakinta ta nufa dasu tundaga falon suka fara zuba santin haduwa har zuwa cikin
dakin da take zama " Wow Queen a Gaskiya kina morewa irin wannan daular kekuwa mai
zai Bata miki rai?
Kuna zagina ne kawai ku bakwa ganin wadda kuke ciki? Ina aikema kinsan yanzu kinyi
mana nisa muna bayanki gimbiyar bature'
Ke wai ma ina yake ne kwana biyu meye labari? Tayi murmushi sannan ta labarta musu
Abinda ke faruwa tareda gaya musu A yaune ya wuce Kaduna basu ma samu haduwa ba ta
nuna musu sabuwar wayarta har ma da shopping din da yayo mata'
Sunata zuba shewar su irinta kawaye tareda tayata murnar samun masoyin Asali tayi
saurin kwabar su " Hajara kinsan Akwai matsala nafada miki komai'
"Mtseew ke Wallahi kinada Abin haushi wannan mayen Sulaiman din kifada mishi bakya
sonshi kawai ni kibarni da Hajiya wallahi zan fada mata,
Ki rufamin Asiri Mana wane irin Abin kunya ne wannan ALLAH kunya nakeji kubar
zancen kawai muga y'an da ALLAH zaiyi damu'
Mudai ba ruwan mu idan komai ya kwabe ni gashi nasa Dadyn mu ya takawa ya Nasir
birki na fada mai Anfitar miki da miji yanzu Dady yace idan har bai fito da mata ba
zai hadashi da duk wadda yaga dama kuma nima my Mr right ya shirya ta fada tareda
rufe idanu irin najin kunyar nan, duk suka cafke tareda sa dariya
Kedai bari Ajere zamu shige ALLAH dai yakai mu y'an mata muma muji Abinda kowa
keji'
Ruman ta zaro ido " me akeji y'ar iska da kikeso kije kiji? dad'i mana soyayya'
Suka sanya dariya tareda kai mata duka " ke jarababbiya ce Wallahi " to idan an
kaiku kar ku more kutsaya kunya kuga kunya wallahi,
Har ma dai ke Queen " waike mai kawaici idan bature yasameki ko hmmm"
Ki fada mana wannan yaron mezai iyayi saidai mu wahalar da juna, shewa suka kara
sawa,
Har karfe hudu suna gidan tare sukayi girki suka koma gefen su Hajiya suka
sallamesu sannan suka wuce,
Karfe takwas na dare wayarta tayi kara ta d'auka da sauri a lokacin dama tana
kwance Adakin ta tana faman tunanin shi,
Wata irin Ajiyar zuciya suka sauke baki dayan su " My dream" ya furta deep down
saida taji muryar har cikin kwakwal war ta " ya kake?
Danayi me? Nashigo naganki ba kaya gaba daya kintayar min da hankali tunda nazo ban
iya yin komai ba gashi gobe zanje Abuja Momy na nason gani na,
Tunda ya fara maganar gabanta ya harba " ya ganta dazu? Ashe shine ya shigo taji
kamar motsin mutum'
"Meyasa ka shigomin daki ba sallama " Am sory baby ai yanzu kinga na janyo ma Kaina
damuwa Wallahi jinake kamar indawo indan rage mugun zafin da kika hadamin ina cikin
wani hali'
Muryar da yake Amfani da ita kawai itama daga mata hankali takeyi kamar dama dagan
gan shima yakeyi don ya sata itama cikin wani yanayin,
Wani irin mugun nishi yake fitar wa tare da numfashi mai tafiya da bargon jikinta "
baby''' ki daure a daura mana Aure kar infada halaka bazan iya ba Wallahi na gaza
nafada miki nikadai nasan irin karfin sha'awa ta'
Katse wayar kawai tayi domin ita kama batasan yazata yi dashi ba gashi ya jefa ta
mugun yanayin itama,
Aranar Shikam bai samu bacci ba yasha magani har ya gaji Amma baiyi mai aiki ba,
Da safe kuwa jirgi yabi zuwa Abuja domin Momyn shi tasa shi gaba da fitina a cikin
yanayin ya isa Abuja"
Can din ma rigimar ta tasa shi gaba akan sai yabita sun koma American ya dai
lallaba ta akan ta bari ya kammala ginin da sukeyi bawai don ya y'arda da tafiyar
ba,
Tunda ta katse kiranshi bai kuma kiranta ba har kusan sati daya da tafiyar shi
Wanda yayi kwana uku a Abuja ya dawo Kaduna yana dirowa ya wuce gidan baffan
shiwato baban Ruman,
Yaji dad'in y'anda ya dawo gidan da zama duk da ba ruwa nshi da shiga cikin gidan
Abincin shi kuwa a restaurant yake ci domin ya lura Matar gidan sai A hankali,
Sopy tayi nasarar karbar kudi a wurin Aunty bilki tana fita wurin bokanta ta nufa
akan yayi mata nata Aikin da kudin dama wayo tayi mata kawai'
"Yayi surkullen shi kar sannan ya kalle ta" meye sunan yaron? Tama rasa mezata fada
don maganar Gaskiya bata sani ba'
"Bansan sunan shiba " kajimin shashashar banza to ungo wannan turaren idan har
biyan bukata kikeso dazaran yashaki kamshin koda kadan ne zai biya miki bukatar ki
jeki tsinanniya Anan ta tule mai kudin Aunty bilki tayi gaba,
Tana farin cikin zata D'ana sabon jini ta nufo gidan Aunty bilki tareda zabga mata
karya boka yace zai fara aiki a yau zataga canji'
Tanata sintirin zuwa gidan Amma har kusan sati biyu basu haduba,.
Ganin sati biyu tun ranar da ya kirata ta katse bai kuma kiranta ba gashi zuciyar
shi na wahala sosai akan tunanin ta don haka dakyar yaga wayewar Garin na jumu'a ko
Aikin bai duba ba ya buga mota sai zazzau,
_birnin shehu gari mai tarin y'an mata garin Ilimi garin manoma garin Albarka_
"Saidai yayi mugun gani daga isowar shi ya hangota a zaune a gaban motar Doctor
Sulaiman suna magana " wani irin uban cin birki yayi tareda buga kanshi da
sitiyarin motar shi,
Kasan cewar motar a bude take da sauri ta waigo gabanta na bugawa taga shine ya
dawo bayan Sam batayi expecting dinshi ba saboda ya daina kiranta,
Tayi matukar damuwa da rashin ganin shi da kuma kin kiranta da yayi,
Dago da kanshi yayi idanun shi sunyi mugun ja tsabar kishin da yake cin zuciyar
shi,
Doctor Sulaiman ya kalle ta " Amarya ta ko kanin namune yazo? Tayi karfin halin
daga mai kai ta saki fara'a domin Hajiya tayimai bayanin komai yanzu yasan dangan
takar dake tsakanin su da shi'
Ranshi a matukar bace ya fito daga cikin motar wato duk kashedin da yayi mata
bataji ba shiyasa ta ki ko neman shi a waya wato tanason wannan jakin saurayin
nata ta nunamai cewa batason shi wato yaudarar zuciyar shi kawai takeyi ko lallai
yau zai nuna mata KUSKUREN ta,
Ya fito cikin takunshi na natsuwa da daukar hankali gashi yasha wanka kamar kasace
shi ka gudu tunda ya fito ta zuba mai idanu domin ya masifar tafiya da ita kyanshi
kullum karuwa yakeyi a idanunta,
Yana isowa ya sanya Hannayen shi duka biyu a Aljihun wandon shaddar shi ya watsawa
doctor Sulaiman mugun kallo kafin ya maida jajayen idanun shi akanta gashi ya matsa
gab da ita gabanta na faduwa'
"Kanin mu sannu da zuwa ya hanya? Juyowa yayi cikin kallon wulakanci ya ce " ita
tafada maka ni kanin ta ne ? Shikuwa doctor cikin rashin fahimta yace " eh
"Bata fada maka Akwai wata Alaka ta daban ba bayan kanin ta? Aa meye Alakar taku?
Ya kara matsawa gab da fuskar ta " Har numfashin su na haduwa " baby na why kika
kasa fada mai matsayina "Alright now bari in nunama waye ni, cikin zafin nama ya
fisgota tareda manne bakinshi akan nata idanun ta a waje gaba daya shock ya kamata
domin bata taba tunanin Abdullah zaiyi mata irin wannan wulakancin ba,
Shikuwa doctor Sulaiman ai kusan mutuwar tsaye yayi " macen da zai Aura? Itace wani
ke kissing a gabanshi Yarinyar da yake ganin ta kamila Ashe tantiriyar y'ar iska ce
no Wonder ta daina damuwa Ashe ta nema wa kanta mafita zuciyar shi kamar ta fito
haka yakeji,
Saida ya tsotse bakinta na kusan minti takwas sannan ya saki yayi wucewar shi cikin
gidan yana Sakin mugun murmushi,
Ita kuwa yana sakinta tsabar bakin ciki ta sanya kuka kawai domin ya mugun wulakan
ta ta a gaban doctor Sulaiman,
Juyowa yayi idanun shi jawur " nagode Ummu da irin mugun wulakancin da kika yimin
ba laifin ki bane laifina ne da nakasa gane wa tun farko na nace A tunani na kece
macen da ta dace da Rayuwa ta but Am mistaken kema Bakida banbanci da sauran mata
Amma kinban kunya tur da muguwar dabi'ar ki kirasa da wazaki yi lalatar saida
kanin bayanki "I hate you,
Ya buga motar shi da karfi ya fita a d'ari ba Abinda takeyi sai kuka tareda jin
wata irin tsanar Abdullah a cikin zuciyar ta ta dauki lokaci tana kuka kafin ta
wuce cikin gidan cikin jin zafin Abinda ya aika ta mata,
Shi kuwa yana hangota ta window tun Shigowar shi har tafiyar Sulaiman sannan ya
juya zuwa dakinshi wasu hawaye na zarya akan fuskar shi na tsananin kishi da kuma
bakin ciki'
A fusace ta nufo falon ko zata ganshi taga wayam tsabar zuciya ta nufi dakinshi kai
tsaye domin jitake Ayau idan bata ci mai mutunci ba hankalin ta bazai kwanta
ba.........✍
_*Matar Soja*_
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
✍✍✍✍
GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION.
✍✍✍✍
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~So magical~*
✍🏽
*~Be hold our words will cause you no pain .~*
_*Rawa da girgiza zanyi gabanku in jujjuya.... wow wannan rangadediyar wakar domin
kune kawai Fenerh fan's group Wallahi comments dinku ya sani nishad'i sosai fiyeda
tunanin ku Allah ya bar kauna*_
*Mrs khamis kina burgeni kuma naji sakon ki Allah ya bar kauna ina yinki*
*Mai daddawa ki taimaka min da daddawa tawa takare Hhhh just jocking sister ina
mugun yinki comments dinki nasani rawa harda girgiza Allah ya kiyayemin ke*
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
2⃣3⃣ 2⃣3⃣
➡2⃣3⃣
Tun shigar shi ya fara tube kayan jikinshi zufa na wanke mai ko ina na jikinshi
kamar Ac baya aiki a cikin dakin,ya rage dagashi sai short ga wata uwar fitina dake
Azal zalar zuciyar shi,
Shigowar ta yasanyashi fadawa kan gadon tareda kifewa domin gudun karta yi mugun
gani Yana Ajiyar numfashi tamatso kusa dashi cikeda masifa,
"Abdullah saboda na baka fuska shine dalilin rainin da kake nunamin ko? To kayi
nasara ka kori Sulaiman tareda wula kanta ni a idonshi ka zubar min da mutuncin da
yake gani na dashi'
To ka saurareni" daga yau bani bakai kar ka kuma shiga sabga ta idan ko baka jiba
to ka gwada wallahi wulakancin da nayima afarko bakomai bane'
Tunda take maganar bai juyoba saida takai Aya ya juyo da karfi tareda zuba mata
idanunshi da ke cikeda fitina mai tsanani'
A uzubillahi shine Kalmar da tafito bakinta domin taga zahirin balagar shi yau,
tayi saurin Jan baya tareda zaro idanu tana mai jinjina karfin rashin kunyar
Abdullah ta fita da gudu batareda ta kuma cewa komai ba,
Wata irin dariya ya saki tareda yin mika mai karfi ya mike yana mai dafe saman
wandon shi domin gyara packing🙈
Still yana Sakin dariya kasa kasa " Aunty na tun yanzu kinji tsoro Hmmm, ya furta
yana dariya shi kadai,
"Dakinta ta fada sai kan gadon ta tana mai jujjuya kai " Wallahi wannan yaron d'an
iska ne na gaske "yanzu haka yake da daske kodai wani salon iskancin shine na
daban?
Dakyar tasamu ta mike tareda fadawa bathroom saida ta sheka ruwa a jikinta sannan
ta fito ta sauya kaya zuwa doguwar rigar material baki mai play rigar tayi mata
kyau sosai ta yafa d'an karamin mayafi ta fito domin shiga gefen su Hajiya,
Tafito daidai da shima ya fito sanye da farar jallabiya mai guntun hannu, saida
gabanta ya fad'i saboda tunawa da iskan cin shi da tayi tayi saurin juyawa tana
shirin fita,
Taku biyu ya isa gabanta ya tsura mata idanu tareda marai raice fuska " Haba mana
my Queen' wai me yasa kike mun haka ne ? "Saboda ke ne fa nazo nan garin Amma ina
isowa na tarar da bacin rai'
" kallon shi tayi cikeda masifa " Amma na fada maka kafita hanya na ko? Kayi
nasarar korar Sulaiman ka barni inji da fargabar Abinda zai biyo baya kuma na fada
maka bazan taba Auren ka ba soyayyar da na y'arda da ita yanzu' na janye kuma koda
Sulaiman ya fasa inada w'anda zan Aura,
Wani irin murmushi yayi mai ciwo " lallai Ruman zaki tafka babban KUSKURE "Wallahi
na rantse daga yau idan An tanbaye ki kawai kifada musu ni zan Aureki kuma ni banki
a daura mana Aure a yau din nan ba,
Na matsu Wallahi nayi iya kokari na na tsare miki kaina banaso inyimiki shearing
Kaina da wata Ruman ki cire taurin kai ki fada musu muna son juna,
Kece kika han tun farko komai ya tafi y'anda ya kamata da ba haka ba kece kika
tsaya Jan Aji har Dady yamun iyaka dake Ruman ina tsoron bakin Mahaifina ya kamani,
Yayi Ajiyar zuciya idanun shi na cika da kwalla " yayi mun ALLAH ya isa idan har na
furtawa wani cewar ina sonki saboda kawai gudun kar ya bata wa iyayen shi domin
gyaran KUSKUREN da ya tafka "ki bari Muyi Auren mu mai tsafta Ruman don ALLAH
Wallahi zan iya mutuwa'
Wani irin harara ta zabga mai bawai bai bata tausayi bane aa Amma tasa a ranta sai
ta saita mai hankali kafin su shirya,
" Ka matsa min A hanya in wuce. Share hawayen shi yayi sannan ya kuma kallon ta
tundaga kasa har sama a haka zaki fita waje? Kinsan fa Akwai masu aiki maza a
wajen,
"Wallahi ka matsa ko in zabga maka mari Ajiye ni kayi ko kuma Aure na kakeyi ?
" Aa me kikewa sauri nidai na fada miki dole ki Aure ni kuma Wallahi last warning
bake ba wani namiji in ba haka ba in nakuma ganin ki da wani Abinda zanyi muku ke
dashi bazaki ji dad'in shi ba,
Yana gama furtawa ya juya cikin dakinshi Aranar ya juya Kaduna saboda tsabar bakin
cikin da ta k'unsa mai,
Ita kuwa duk hankalin ta Atashe yake tana fargabar Abinda Sulaiman zaiyyi'
Bayan kwana biyu ya aiko manyan shi da maganar cewa sunfasa Aure domin dama sunyi
mishi mata shi yaki Amincewa yanzu kuwa ya dawo yace zai Auri waccan din muzo mu
baku hakuri,
Dady yayi bakin cikin faruwar wannan Abu ya samu su Hajiya ya fada musu aikuwa tace
saboda wulakanci saida yarinya ta sanya rai to ai shi kenan ALLAH yasa hakan shi
yafi Alkhairi Gwaggo Amina tace Amin sai hakuri haka ALLAH yaso'
Har babanta da Aka fadamai yaji ba dad'i domin Aunty Balki ma saida ta gane yana
cikin bacin rai ta tanbaye shi?
Yana fada mata taji kamar ta taka rawa don murna tareda Ayyana wa a zuciyar ta
lallai wannan bokan yana aiki murna kamar ta zuba ruwa akasa tasha Amma saboda
makirci ta marai raice murya'
"Ayya Baban Faisal kar ka damu kanka ALLAH zai kawo mata wani kila wannan ba
Alkhairi bane a gareta,
Ya ce " nagode Balki' Amma da kinshirya keda yaran nan muje kuga y'an uwa na gobe
Hajiya tayi fada harta gaji banaso su tsane ki da yawa,
Bakomai yasa ta y'arda ba sai don taje taga halin bakin cikin da suke ciki na fasa
Auren y'ar gaban goshin jikar su'
Ruman bata San ma ya wuce ba har saida taga Ankwana an wuni bata koga motsin shiba
tasan cewa komawa yayi ta share tareda ci gaba da shirye shiryen bikin Sumy da
kullum suna kan hanya a wannan tsakanin har mota ta fara koya wurin Hajara,
Kuma dayake tanada kai har tafara driven saikace mai motar kanta'
Biki sai kara matsowa yakeyi w'anda da,Kansu suke zuwa gyaran jiki kasan cewar y'an
matan yanzu sun San komai basa jiran iyaye kullum suna hanyar beauty palace,
Ita kanta tasan gyaran da suke kwasa ya canja fatar ta ga kuma hutun da suke ciki
gida Ac mota Ac ga shi kudi kota ina Dady ya bata Baban ta ya bata,
Ita kanta tasan ta wuce raini ko a wurin kawayenta yanzu tafisu komai,
Ankon da suka dinka ma na garari har kusan kala goma su biyu da Hajara Amarya ba
asata a ciki,
Aunty bilki ta iso Zaria tana sa ran taga Ankaita wata unguwa ta daban ta ganta a
GRA kuma a bakin tanfatse tsen gida,
Ta saki baki tana bin gidan glass da kallo, Baban Faisal " nan gidan waye? Abokinka
ne keda wannan gidan Amma ka cuceni da baka taba kawoni ba,
Wani irin kallon ke Bakida hankali ya jefa mata sannan yace " ina nace zankai ki?
Ya bude motar ya ce Kufito yaran duk suka fito ita kuwa har yanzu jikinta rawa
yakeyi'
Har suka shiga daga ciki sai baza idanu sukeyi suna Kwasar kallo,
Bata tsinke ba saida tasamu tsofaffin zaune cikin shiga ta Alfarma ga kuma kayan
ciye ciye ajiye a gaban su sunfito shar dasu kana ganinsu kasan Hutu ya ratsa gefe
kuwa magaji ne ya dau wanka harda babbar Riga sai hirar su sukeyi'
"Ta shigo jikinta a sanyaye ta samu gefe tana mai saka mugun kulli a zuciyar ta,
" Maraba da mutanen Kaduna " kai iso mazajena inji Gwaggo Amina " Suka karasa kusa
da ita " bakwa gaisuwa ne y'an samari?
"Suka gaishe su itama murya cikeda hassada da bakin ciki ta gaishe su'
"Ya waiga " ina Ummu take? Ai Ummu kam kaida ganinta yanzu ai sai Anjima domin suna
shirin bikin kawarsu gashi suna jara bawar karshe da suntashi sai su wuce sha'anin
su,
"Ya girgiza kai kawai' ita kuwa Hajiya Balki cewa take " shegiyar yarinya mayya,
Mary ta shigo daukeda tray da kayan ciye ciye kala kala 'Hajiya tace " maryam
shiga da yaran nan ciki suyi kallo zamuyi magana,
Tace to duk suka mike tareda binta cikin gidan " itama uwar ta mike tabi bayansu ba
w'anda yace mata komai
"Tun shigar ta cikin main falon ta saki baki " Ashe da sauran kallo ai kuwa ALLAH
ya isa tsakanin ta da Muhammad da ya kaita Kaduna ya dire bayan ga gida hadadde a
nan ya zuba tsohuwar uwar shi ciki,
Ba inda bata leka ba sudai yaran da suka samu kallo a katon cinema sai shiru kawai
Mary ta hado musu kayan lashe lashe kala kala sunaci suna kallo,
Karfe hudu suka shigo cikin gidan ita ke tuka motar gashi ta sanya wata irin
jallabiya mai kyau taji stones ta yafa mayafinta gaba dayansu sunyi masifar kyau
saboda gyaran da suke d'auka,
Suna tafe suna faman yiwa juna shakiyanci "Queen irin wannan kwalliyar ai Saiki
hauka ta bature " Sumy tace ko kuma ya tsotse janbakin ba suka tun tsere da dariya
domin ta basu labari,
A haka suka shiga cikin gidan suka gaida su Hajiya batareda sun zauna ba hajara
tace kai muje ciki yunwa nakeji yasin ta juya da gudu suna mata dariya sannan suka
bi bayanta
"turus sukaja suka tsaya itada Sumy domin Hajara tuni ta fada kitchen Ruman tayi
mamakin ganin su ta rage murya Ahankali her Highness Matar babana, Sumy ta d'an
zaro ido,
" me ya kawota ? Gulma, suka matsa gab da ita suka gaisheta ita Sam bataga Shigowar
su ba ,
Gabanta yayi mugun faduwa ganin y'an da Hutu ya kara ratsata tayi mugun kyau da
cika fatar ta tana sheki dakyar ta iya Amsa su yaran suka gaishe su sannan taja
Hannun Sumy suka shige dakin,
Hajara kuwa saida ta dafo indomie ta yanka dafaffen kwai ta dauko katuwar gorar
juice sannan ta shigo dakin ta Ajiye tana turiri,
Ta kwabe rigar jikinta ta janyo towel din Ruman ta daura' mun shiga uku wata zatayi
hauka saboda yunwa,
Ko sauraran su batayiba ta fara kai loma Mary ta shigo musu da tray dauke da tuwon
shinka fa da miyar Ogun taji namomi ,
Sukasa dariya "Mary kindafa enemy na Hajara yau tayi murmushi. tama ta fita domin
tanajin dad'in y'anda sukeyi mata Sam basa kyamar ta duk da tana Christian,
Saida sukayi nak hajara ta fara yin wanka sannan ta bude Waldrop din Ruman ta janyo
wata Riga zata sanya tayi wani irin tsalle ta Amshe,
Ki sanya wata wannan my young crush ya siya mun suka samata dariya " muna fuka
kinason Abunki kina cutar kanki,
Tace " eh din ya cika rashin kunya ne ni kuma Kunsan banason raini,
Dawowar Baban ta suka fito tareda gaishe shi ya Amsa cikeda farin ciki,
"Yau shene zaku gama zana exam ? Tace cikin satin nan " ALLAH ya kaimu ya kuma bada
sa'a ku maida hankali sosai kunji'
Suka Amsa da toh Baba ya kalli Balki " muje ko? Tayi saurin kallon shi "ina zamuje?
Ruman tajasu suka fice Abinsu,
Muhammad a Gaskiya baka Adalci kalli irin gidan da ka ginawa mahaifiyar ka da kuma
y'ar ka kwaya daya tal kabar y'ay'an ka maza Wallahi sai Allah ya saka mana idan
har ka cucemu ehem,
Lallai yau ya y'arda da rashin hankalin bilkisu " yanzu saboda Allah bilkisu ni ina
naga kudin Gina wannan gidan gidan Jafaru nefa muna musu gyaran gida shiyasa ya
kwaso su nan Amma Bakida godiyar Allah Duk. Daular da kike ciki baki godewa Allah
ba ki na hango na wani ko
Wannan daular da kike ciki ko kwatan ta matata bata samuba kuma a haka muka rayu
batareda ta taba hango wani kyale kyalen duniya ba,
Don haka Saiki fito musu a gida idan kinaji da rashin da'a ne Matar gidan tafiki,
"Dole taja doguwar kafarta ta fita tana waigen falon " shegiyar Yarinyar nan wato a
nan ma take Rayuwa ta ya mutse fuska cikeda bakin ciki,
Kusan sati uku Ruman bata sa Abdullah a idoba tun tana boyewa har damuwar ta tafito
fili,
Gashi sunata fama da zirga zirgar biki yarage Saura sati daya cikin ikon Allah sun
kammala jarabawar su gaba daya sun maida hankalin su akan biki,
"Abdullah kuwa suna can suna fama da Momyn shi dake fama da rashin lafiya har ma
suna shirya mayarda ita kasarta domin ganin likita duk da halin rudun da yake ciki
baisa ya manta da rabin ranshi ba,
" Gaba daya zuciyar shi na gareta, duk da kuwa yana cikin fushi da ita saboda magan
ganun da ta fadamai ranar da yazo,
Hajiya ce zaune tareda su magaji gefe guda daya kuwa Jafaru ne wato Dady sunyi
jugum jugum dasu cikin jimamin Abinda yafada musu na ciwon Tara,
"Yanzu Jafaru sai Anyanke nonon kenan? Aa Inna za a iya samun lafiya kasance war
kasar tasu Akwai cigaba sunada kwararrun likitoci,
To Allah ya bata lafiya suka Amsa da Ameen baki daya Abinka da zuciyar musulunci "
Hajiya ta nemi da suje su dubata kafin su wuce da ita wajen,
"Sun shirya su uku ya wuce dasu Abuja domin dubata, tayi farin ciki tareda jin
tsananin kunyar su domin bature baya raina Abin Alkhairi komai kan kan tar shi duk
da tana cikin halin ciwo Abun ya matukar faranta mata kuma daga ranar tayi matukar
girma ma zuciyar musulmi a Gaskiya sunada mutumci sosai har ma taji Addinin ya
matukar burge ta Amma ta barwa zuciyar ta idan har Allah ya bata lafiya,
A yaune suka fara gudanar da program din Auren Sumy sun fara da Arabian night
w'anda suka shirya cikin dogayen riguna masu kyau da matukar tsada,
Ruman ta fito cikin nata shigar doguwar rigar sai farin mayafin da ta nade kanta
dashi kamar wata balarabiya ga takalmin ta ma fari da kuma yar Karamar designer
Po's tasha heavy make up tafito kamar ka saceta ka gudu,
Hajara ma ba baya ba Sumy ma data gansu cewa tayi " Agaskiya bazan y'arda ba Queen
kunfini haduwa sukayi dariya,
Shagalinku tread fear dake laliko suka nufa domin gudanar da taron nasu A yau motar
gidan Ruman ta tuka da kanta tareda Kwasar wasu daga cikin kawayen su dake school
ga wani tabarau data maka irin na classic ladies din nan tayi ba karya,
Sunyi taro lafiya sun watse lafiya washe gari kuma sisters day da yayyun ta suka
shirya shi a shagalinku hotel ranar ma sunfito cikin tsadadden material less dinsu
taron ya matukar kayatar dani sosai domin nima nadan leka kuma nayo guzuri don
saida nayo rabin Leda'
"Ana gobe daurin Aure suka gudanar da luncheon w'anda ya samu halartar Ango da
tawagar Abokan sa domin Angon yace da Andaura Aure ba w'anda zai fito mai da mata
wai dasu nan bidi'a
" Masha Allah y'an matan yau sun taba ruwa fiyeda sauran ranakun Ruman da Hajara
sunfito cikin Atanfar su blue taji fulawoyi masu ban sha awa gashi dinkin Riga da
sket ten PCs ya matukar budewa rigar kuwa have play dinkin yayi matukar zaunawa a
jikinsu musam man Ruman da hip's din nan ya fito kamar yayi magana gashi ta yafa
dan karamin bakin mayafi tayi daurin zamani ta zubo sumar ta ta tsakiyar dankwalin
yana reto sai sheki yake zubawa Alamar yaji gyara,
Suna ta kaiwa da kawowa gaba daya idanun gayun nakan su aka fara gudanar da program
din aka fara kiran mutane zuwa kan kujerun da aka tanada domin manyan baki masu
muhimnci,
Ruman Aka fara kira tahau kan hytable ts waro idanu hajara ta sanya dariya " daman
nasan idan kinsani bazaki taba hawaba shiyasa naki fada miki don haka Hajiyar
bature bismillah,
Ta riko hannun ta tareda marai raice fuska " don Allah kawata ki je ki hau ni bazan
iya ba,
"Aa ni zan bada tarihin Amarya don nasan bazaki iya tsaya wa a gaban jama'a ba
batada zabi dole ta wuce ana tafa mata har ta nemi wuri ta zauna a gefen Amarya,
An fara gudanar wa gashi Ansaki kidan Ali jita wakar indo kamar hotel din zai rushe
Ango da Amarya suka Mike domin shiga fili tareda best Friend's ta mike tareda
kokarin bude y'ar Karamar Po's dinta tana kokarin janyo kudin liki taji Anriko mata
kugu ta waro ido waje gaba daya lokacin da ta dago kanta domin mamakin da ya
kamata naganin shi a wannan wurin batareda ta shirya ba,
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
_Daga Alkalamin_
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
✍✍✍✍
GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION.
✍✍✍✍
*Domin farin cikin ku shine nawa my fan's ku Shana ina yinku buhu buhu*
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
2⃣4⃣ 2⃣4⃣
➡2⃣4⃣
Kallo ta fara karemai cikin wani irin tsadadden farin yadi dinkin tazarce yau harda
hula yana zubo kamshi Kamar wani Ango,
Fisgo ta yayi zuwa jikinshi gaba daya kallo ya koma Kansu y'an mata dayawa sunk'ya
sa
Ya fara rada mata magana " my madam wa yabaki izinin fitowa a cikin wannan shigar
kuma ba mayafi?
Ta d'an harare shi da style " bansani ba kaga ka daina y'ar fani cikin mutane duba
y'anda kowa ya zubo mana idanu, ya kuma wai gawa ya ga wurin yayi tsit rawar ma da
aka fara ta tsaya kallo ya koma sama y'an mata sunga bature'
"Da me kike shirin yi? liki. Ta bashi Amsa " to aikema kin cancanci liki domin kema
Amarya ce " ya saki west din ta ya riko hannun ta Suka tsaya tsakiyar filin kusa da
Ango da Amarya,
Ya d'an kalli Security dinshi dake can gefe ya mai Alama da ido w'anda bakowa zai
luraba,
Kawai ji Akayi kida ya canja daga Ali jita zuwa African Queen na 2face Hannu ya
sanya a gefen Aljihun shi ya zaro bandir na dollars ya fara lika mata yanayi yana
kallon cikin idanunta,
Ita kuwa ina kasa ta bude ta shige kunya kamar ta zama invisible "Abdullah kadaina
ta furta a hankali Amma yana hango bacin ran dake kwance a fuskar ta " banason
rainin hankalin ki da raini,
"Madam raini ai ba ayi komai ba sai ma naga Abinda ake kirama girman ya fada tareda
dage mata gira sama still kuma yana kan watsa mata kudin,
Hajara ce ta iso da gudu kusa dashi tayi magana kasa kasa a kunnen shi ya daga
babban yatsar shi Alamar jinjina,
" Sumy ma ta matso kusa dasu ta d'an harari bature _" friend this is not fear u
ruin my party_
Ya kama kunne tareda cewa " sory friend we are leaving ita gaba daya bata fahimce
suba yau she suka yi wannan sabon ita fa bata gane ba mema duk suke nufi da irin wa
innan Abubuwan koda yake ta tuna sun saba tun farkon haduwar su,
"Ta waske tana shirin juyawa ta bar wurin ga shewar y'an mata na tashi yayi saurin
rikota zuwa jikinshi " hy wait Angon Sumy ya matso kusa da shi " Abokina ina tayaka
murna: ya washe baki cike da farin ciki " tnks friend umm bari mu bar muku partyn
ku,
Ya bashi hannu ita kuwa idanun ta na Kansu Hajara dake ta faman kunshe dariya kafin
tayi wani tunani " tuni ya cirata sama cak kamar y'ar tsana ai kuwa wuri ya dauki
shewa harda tafi ga security n shi ta ko ina Ashe suna zagaye da wurin
"Har hotuna wasu suka rika daukar wa innan love birds din ya fice da ita daga cikin
hotel din ga badaya ya gama bada ita tama rasa Abinda zatayi bai Ajiyata ba saida
suka fito waje wajen jerin motocin shi yau convoy ne ga wata fitinanniyar Hummer
jeep
Yana Ajiye ta ya matse fuska tareda juya bayan shi" meyasa kika fito haka ya furta
tareda juyowa ya riko gyalen dake rataye a kafadar ta " kinsan irin fitinar da zaki
hadawa mutane a irin wannan shigar?
Ta nuna shi da yatsa tare da fara kwararo mai ruwan bala'i har hawaye na zubowa a
idanun ta ya waiga ya kalli security dinshi suka bude mai Hummer jeep din ya
sunkuce ta tana kan masifar saida suka shiga ya ajiyeta suka rufe mai ga sauran
motocin a Jere a bayan shi kamar wani president,
"Wallahi natsaneka Abdullah wa Inna halayen naka na tsanesu na rashin kunya wane
irin iskanci ne wannan? Kullum kai burinka ka bani kunya a gaban mutanen dake ganin
mutumci na to Wallahi zan hadaka da Dady yau ince kaki fita daga harka ta ta karasa
tareda mur guda mai baki,
" gaba daya juyowa yayi ya lankwashe kafa daya ya zuba mata idanu'
Batareda ta Ankareba taji hannun shi akife a saman kirjinta😳 dif maganar ta tsaya
tsabar tsoro don bata taba tunanin zai Aikata hakan ba domin ko da ya rutsata
iyakar shi kiss Amma yau iskan cin nashi harda ticket,
"Ga iskanci nan my Aunty kalli dukiyar dad'i na duk a waje don wulakanci yana fada
yana shafawa,
Wani irin mari tayi niyyar zabga mai yayi carab ya riko hannun ta ya fisgota zuwa
jikinshi ya d'an zame kadan ya dora fuskar shi a saman kirjinta yafara goga mata
sajen fuskar shi yana magana A hankali:
" idan da kin mareni ba Abinda ya faru yanzu' inkika fara hannunki zai kone A wuta
domin kin mari..... Sai kuma yayi shiru tareda dago kanshi yasa hannun shi ya zame
daurin dankwalin ta ya cire ribon din ya Ajiye tareda baza sumar yafara yawo da
hannun shi a cikin sumar,
Ai tuni ita bakin masifar ya mutu domin mugun dan romance ne yasan hanyar kassara
mata kuzarin jiki,
"Kici gaba ina jinki Anty na' ya fada Ahankali kamar mai rada'
Still hannun shi na yawo a jikinta' halshen shi ya dora a saman fuskar ta ya fara
lasa tareda Sakin numfashi mai wuyar fassara har ya gangaro saman leben ta " zan
shanye miki janbaki batareda tace wani Abuba ya fara tsotar lebenta saida ya shanye
tas sannan ya jefa bakinshi gaba daya ya fara tsotar halshen ta cikin iyawa ai tuni
jikinsu ya fara rawa sai wani irin numfashi yake fitar wa'
Ya dora hannun shi akan zip din rigarta ya zugeshi batareda ta iya motsawa ba domin
ita kanta taji dad'in wasan bata ko kaunar ya daina
Kara tallabo keyarshi takeyi tana kara hauka tashi da nata salon kiss din duk sun
fita a hayya cin su
Hannu yasa ya zame rigar ta sama farar breziyar ta ta bayyana ga shi sun wani irin
cikowa ta sama ai tuni ya zuba Hannayen shi duka biyun akansu yafara shafawa
Wani irin Abu taji ya ratsa tundaga cikin kwakwal war kanta har zuwa hanjinta a
lokacin da ya dora lebenshi a saman kirjinta yafara yi mata wani irin fittinannen
salo da yakusa zautar da ita,
Wasu irin hawayen dad'i ke zubowa a idanuwansu baki daya ga badaya ya gama
haukacewa a jikinta wani irin gurnani yake fitarwa,
Hankalin ta bai dawo jikinta ba saida taji zafin hakorin shi akan nononta tayi
saurin bude idanunta da suke rufe tana karbar sakonni masu wuyar fassara,
Ganin yana kokarin zame mata sket tayi wuf ta saita kanta tareda tuna halinda suke
ciki wani irin bakin ciki ne ya rufeta ta fashe da kuka Alokacin da tayi Arba da
rigar nonon ta a gefe a yashe ga rigar ta ma a gefe
Tayi saurin rufe k'irjin ta da hannu biyu "Wallahi ban yafe maka ba d'an iskan yaro
kawai'
Shikuwa da yake nan yanata juyi sakamakon halinda yake ciki ai a zabure ya dago
domin jin irin zagin da ta surfa mai ya kalle ta da idanun shi da sukayi jawur
cikin bacin rai ya zuba mata idanun shi masu kwarjini ,
Ruman nine d'an iska? " eh dama fa Wallahi sai Allah ya saka min irin Abubuwan da
kake mun kana Amfani da raunin jikina kana famar tattaba ni,
Gyara zaman shi yayi dakyau duk jijiyoyin kanshi sunyi ja ya janyo wayarshi yayi
dialing number,
"Ak take me to Airport ya furta ranshi a matukar bace sannan ya kuma dialing number
Dady,
" Dady mun wuce UK sai ka zo, banji mai yace ba sai ji nayi yace eh Dady harda ita
zuwa safe mun isa insha Allah,
Ya katse kiran tareda dafe kanshi, ta janyo rigarta ta sanya tareda dukun kune
jikinta domin sanyin dake shigarta na A c tana kallon ikon Allah,
Saida motocin suka tsaya ya bude gefe nshi ya fita sannan ya zagaya gefen ta ya
bude mata " fito kawai ya furta tareda daure fuska,
Ta gyara zama " bazan fitoba ka kaini gida malam, " Malama kifito idan kinki kuwa
daukar ki zanyi kinsan hakan ba gagara zaiyi ba,
Ita gaba daya yau tsoro ya fara bata' dole ta fito tareda kara kudundune jikinta "
ina yake shirin kaita da yakawota filin jirgi?
Bude motar yayi ya janyo cout dinshi ya mika mata batareda ya kalleta ba 'Ak ya
matso da sauri " sir d jet is ready'
"OK tank you Ak Hannun ta ya riko batareda yace komai ba yafara janta " ka sakar
min hannu ina zaka kaini " oh kidnapping dina zakayi ? To Wallahi kaina da karfi
ganin tana bata mai lokaci yasa ya sunkuce ta sai cikin privt jet din su yana
shigar da ita ya danna mata seat belt tana kallon ikon Allah,
Ya zauna shima ya daura nashi sannan jirgi ya fara tafiya " ai jitayi kamar ta saki
fitsari domin ita da ko filin jirgi bata taba zuwa ba yau gata a cikin jirgi gaba
daya,
Runtse idanu tayi tanata jero salati, "tun Anan zan mutu ba saima mun isaba Wayyo,
dariya yayi ya basar kamar baya ganin ta lokacin da jirgi ya dai daita a sama ta
kalle shi " wai ina zakaje dani? Kasan fa hankalin iyayen mu zai tashi musam man
Hajiya,
"Siyar dake zanyi' ya fada tareda janyo plate din da ke cike da pepper chicken ga
drinks an Ajiye musu'
" kici Abinci domin ki kara maiko inji dad'in yanke kanki' " Wallahi Kaina ba zai
yanku ba ehem' " zamu gani kuwa,
Ya bata Amsa tareda ci gaba da cin naman shi" kifa ci Abincin domin tafiya nan da
America is long journey zakiji yunwa da yawa,
Zancen Gaskiya tanajin yunwa gashi d'an tsakanin nan bata wani cin Abinci saboda
tunani da kuma hada hada,
Dole ta fara aikawa domin tana jin yunwa sosai don rabonta da Abinci tun kazar
Amaren da Momyn hajara tabasu suduka A jiya suka cinye ta tas duk da ba dad'i,
"Sai kuma wani irin tsumi mai dadi da suke sha kwana biyu kamar tea,
Taci sosai ta kora da drink ta sanya wifer ta goge bakinta sannan ta gyara zama ta
rufe idanun ta duk yana kallon ta,
" wani irin murmushi yayi Alokacin da yaga bacci ya dauketa matsowa yayi tareda
rungumota zuwa jikinshi yana sauke Ajiyar zuciya,
"I love you Ruman" ya furta can kasan makoshi shima baccin ne ya kwashe shi,
"Ruman taji ya kira sunan ta A hankali ta bude idanunta' ki tashi mun iso " welcome
to United kingdome ta waro ido tareda mikewa ya riko hannunta suka fito ,
Sakin bakinta tayi domin ganin ta A cikin kasar da bata taba mafarkin shiga ba wasu
motoci ne masu dauke da harafin J a Jere kusan guda shida saidai ta tsakiyar tafita
daban ya rikota zuwa wajen motocin,
"Welcome bos turawan keta fada suka bude masu mota suka shiga gaba daya lamarin ya
fara bata tsoro d'an wannan yaron suke yiwa irin wannan girma mawar ,
"Sai a wani tafkeken upstairs sukayi landing gidane zagaye da furanni ta ko ina a
jikinshi kai kiyasta kyawon gidan zai bata lokaci saidai ince ku kwatan ta,
" Welcome to my home we're I grow up Ruman this is my home, yayi murmushi tareda
tuna lokacin kuruciyar shi a cikin shi har zuwa lokacin da yabar kasar,
Janta kawai yayi tana binshi kamar jela domin tama daina yimai gaddama,
Wani irin tafkeken falo ne maidauke da kujeru akalla kusan set uku ga hanyar step a
gefe saman ya nufa da ita tana biye kamar wata sokuwa,
Ya kaita wani daki na mu samman tasaki baki tareda kallon kowane bangon dakin mai
dauke da zanen fuskokinta a kowane bango ga katon Royal bed a tsakiyar dakin kai
komai Abin kallo ne ga hotunan shi na kuruciya a tsakiyar nata,
Zuba mai idanu kawai tayi tana kallon shi domin harde Hannayen shi kawai yayi ya
zuba mata na Mu jiya " kije kiyi wanka ki rama sallolin da Ake binki kafin ki dora
daga inda kika tsaya a masifar.....✍
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery,
Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from
our blog.
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa
novel ko kuma post.
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search
na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
2⃣5⃣ 2⃣5⃣
➡2⃣5⃣
Har ya juya zai fita ta tsayar dashi, "meyasa ka kawoni wannan kasar meye nufin ka?
Murmushi yayi sannan yace "Nufina shine inkawo ki nan kema inkoya miki rayuwar
iskancin da kika ce ina dashi,
"Ni dai ka fadamin meye manufar ka akaina? Soyayya ce nace banayi Aure ne nace
bazan Aureka ba dole ne ?
"Yanzu wane irin hali kakeso iyayen mu su shiga kasan cewa hankalin Hajiya sai yafi
na kowa tashi?
" Idan baki sani ba insanar miki "mahaifiyata na nan tana jinya yakama ta inzo kuma
bazan iya barma kuraye ke ba shiyasa na dakko kayana don haka ki shirya zama da
d'an iska daga yau har zuwa lokacin da naga damar mayar dake kuma by then..... Yayi
murmushi sannan ya juya zai shiga wata kofar,
Wani irin bugawa kirjin ta yayi me yake nufi? Zama dashi Anan gidan? Ta hadiye wani
irin mugun miyau da karfi'
" tana tsaye Awurin har yafito daure da towel Ajikin shi ya karaso gab da ita ya
y'ar fa mata ruwan wankan dake jikin shi,
Ta wani zabura tareda yin baya da sauri domin ya mugun shigo mata,
Ya kalli k'irjin ta yayi murmushi " Baby kije kiyi wanka kiyi Salla kafin inje
insiyo miki wata rigar Abin nan tunda wancan ta yage ya furta cikeda tsokana sannan
ya daga mata gira daya,
"Wani irin bakin ciki ne ya turnike ta ta zabga mai harara sannan ta wuce hanyar da
taga ya fito,
Ya bita da dariyar keta, masha Allah ta furta Alokacin da ta shiga cikin lafiyayyan
bathroom dinshi kamar baza a mutu ba duniya,
Tayi wankan ta cikin nishad'i saboda tsarin wurin ko ta ina mirror ne ta gama
tareda dauro Alwala ta matso jikin mirror din ta tsurawa kirjinta idanu saboda
sululin da Kansu yakeyi,
Wata irin kunya ce ta rufeta wai Ace d'an Abdul din nan har yasan takan rudewa mace
lafiyar jiki ya fitar da ita daga duniyar da take zuwa wata ta daban,
" Wani irin y'arrr take ji a cikin jikinta saboda tunawa da tayi da irin halin da
kanin nata ya jefa ta'
Saida ra sake yin Arwala sannan ta fito ta samu baya cikin dakin saidai ga dadduma
da kuma dogon himar ta janyo ta zura batareda ta mayar da kayanta ba domin ta gaji
dasu,
Ta jero sallolin da Ake binta tana zaune Akan daddumar tayi tagumi domin gaba daya
zuciyar ta na wurin Hajiya tasan sai tafisu damuwa,
Turo kofar da Akayine yasa ta dago wa ta zubawa wata baturiya idanu da ta turo wata
yar keken Abinci mai dauke da Abinci,
"Good morning ma'am' ta furta da muryar ta ta turawa tareda yimata bayani cewar
itace cook dinsu tayi mata godiya ta fita ta mike tareda kallon d'an karamin keken
da saidai ta ganshi a TV yau gashi Ankawo mata Abinci akai,
" Saidai bataji zata iya cin komai a ciki ba domin Abinci ne irin nacan daga ganye
sai ketchup dasu danyen tumatiri,
_"Aini danaga garin gulma yunwa zata kar ni ai tuni na Ciro burodi na fara korawa
da ruwa fan's Anya zan iya daurewa kuwa wurin dauko gulma?_
"Ta yatsune fuska ta ture keken gefe ta koma kan kujerar hutawar dake dakin ta
zauna tareda zubawa Aljannar duniya kallo,
" tana haka ya shigo dauke da ledoji manya manya ya Ajiye sannan ya kuma fita ya
kwaso wasu ya dawo,
Dauke kanta tayi kamar Bata ganshi ba' ya zauna gab da ita kamar zai shige
jikinta,
"Madam ba sannu Kefa najewa shopping, " Ai ban aikeka ba ko?' To aini dole na inje
saboda madam dina batada kaya,
Ya fara bude ledojin daya dogayen riguna ne irin na turawa wa inda dasu da babu duk
daya sai kuma daya Riga da kmguntayen sket ne sai kuma takalma da jakun kuna sai
ta karshen da ya zazzago su breziya da kuma panties kusan dozen dozen,
Idanu ta zaro tareda jinjina rashin kunyar Abdullah ya dago wata tareda cewa" ki
cire hijabin nan ki gwada ingani ko zatayi na manta ne ban tanbaye ki ba so kuma
sai na tuna ai dazu naga girman su kuma na d'an taba shiyasa na gwada da hannu na,
Yana fada yana kara cacumar kokon nonon breziyar " matsawa kawai ta fara yi domin
yanzu lamarin yaron ya fara bata tsoro,
Rikota yayi da hannu daya "ki cire hijab din nan ko in cire miki kuma ingwada miki
da Kaina kinsan zan iya ko'
Rike hijab din tayi ga gam tareda girgiza kai" please Abdul kadaina kasan haramun
ne ko kai ba muharrami na bane Wallahi wuta kake tabawa,
"Uhm a tunaninki ko? Ni halalina nake tabawa don haka kima saki ranki don ni morewa
zanyi Wallahi ai ke kika ja koma meye kibari Muyi Auren mu mai mutunci kinki waike
kinajin kunya ko kar,Ace kina soyayya da kaninki to kisani karamin yaro zai baki
ciki inyaso Saiki San y'anda zakiyi tun yanzu,
Ya fada tareda mikewa " ni zanje wurin Momy kici Abinci bazan dawo da,wuriba,
Bayan fitar shi batada zabi illah ta nemi kaya masu d'an mutunci ta saka Acikin
wa'inda ya siyo mata,
Ta sanya wata riga da wando dogo pencil rigar kuwa side shoulder tayi matukar yin
kyau A cikin shigar gasu sun kamata dam komai ya fito,
Ta kalli kanta A jikin mirror tayi tsaki jin irin karar da cikinta keyi ya sanya
ta fitowa dole ta fara neman hanyar kitchen,
Ta ci karo da Matar da takawo mata Abinci dazu ta tanbaye ta " ware is the kitchen?
"If you need something tell me ma'm I will get it for you'
" no tanks I will do it my self. OK, da jagoran cin ta taimaka mata ta dafa indomie
domin shine mai sauki ta zuba kifin gwangwani tareda soya kwai ko fita batayi ba a
cikin kitchen din ta janyo kujera saida ta koshi sannan hankalin ta ya dawo
jikinta,
Sai Alokacin ta tuna da wayar ta ta laluba ko ina bata ganta ba dole ta hakura
tajira shi ya dawo,
"Har kusan karfe biyar na yamma a kasar ta UK bai dawo ba har bacci tayi ta tashi,
Hankalin ta ya fara tashi domin dai ita girman gidan tsoro yake bata daga baya ma
kasa ta sakko domin tafi jin motsin masu Aikin gidan,
TV ta kurawa idanu bawai don shirin nasu na burgeta ba aa said an zaman kadai cin
da take ciki,
Sai da ta duba Agogo taga karfe bakwai ta mike tsaye cikin sauri tareda buga tsaki
" Allah tsine kasar da baza kaji kiran Salla ba ta Ayyana a ranta,
Tana idar wa ya shigo cikin gidan A matukar gajiye Alokacin ta mike ke nan tana
linke hijabin jikinta yaja ya tsaya cak tareda kare mata kallo yana jin wani irin
har cikin jikinshi ai tuni yaji duk gajiyar shi ta war ware,.
Batasan Shigowar shi ba kawai jin tayi ya rungume ta tabaya ya sauke wata irin
Ajiyar zuciya,
Ita kuwa ta dan tsorata daga farko Amma shakar kamshin turaren shi datayi yasanya
ta fahimtar shine,
Tureshi tafarayi" kadaina banason iskanci Abdul nafada maka ko wannan irin rainin
wayon naka ya fara kaini bango na farko ka satoni daga kasata ka kawoni wannan
muguwar kasar sannan kazo kana laluba ta kamar wata Matar ka Wallahi kuma ka
kawomin wayata zankira Hajiya ehm,
Saida takai karshe ya birkito da ita ta ga banshi ya saki wani irin murmushi
"kidaina wahalar da kanki Ruman domin wayar ki bazarayi miki Amfani ba sannan kuma
lalubar ji kuwa yanzu nafara bakiga komai ba domin Abinda nakawo ki inyi kenan
kafin ki karasa min y'ar sauran lafiyar da ta ragemun,
'Fisge jikinta tayi da sauri " wallahi kasha giyar karya Abdul kuma ko dazu ma
dakayi Allah sai yasa kamun
"Banzan yaro kawai Mara kunya kuma muzuba nida kai sai naga mai cin riba ta buga
tsaki ta fita a dakin yana binta da kallo,
Girgiza kanshi kawai yayi sannan ya fada bathroom yayi wanka ya fito daure da
Alwala ya sameta ta na kokarin shinfida dadduma Alamar zata sallaci isha,
Ko kallon shi batayi ba har ya wuce gaban mirror yafara shafe shafe yana mai kallon
movement dinta ta madubin har ta idar ta kuma fita shima ya sanya short ya zura
jallabiya fara mai guntun hannu ya tada Salla,
Tana zaune a falon kasa ya sakko ya zuba mata idanu y'anda ta zauna a cikin falon
wani irin farin ciki ne ke rufeshi ,
Helen mai aikinsu ya kira tareda tanbayar ta ko taci Abinci tayi mai bayanin
indomie kawai taci ya dafe goshin shi domin shi Sam ya manta bazata iya cin cimar
su ba,
Ya bata umarnin ta gasa mishi kifi da kuma kaza tace OK ya fito falon tareda nufota
ta kauda fuskar ta gefe ya nufi saitin fuskar ta ya zauna a hannun kujerar da take'
" Hmm finally, ya furta Ahankali tareda dora Hannun shi akan fuskar ta' Am sory my
Queen,
Nayi KUSKURE a yimin Afuwa, ai dole kace haka ta fada cikin masifa,
Tunda ka satoni ai dole ka bani hakuri, "nop ni ba hakurin da nake baki kenan ba
hakurin rashin baki Abinci nake nufi kuma ni ba sato ki nayi ba ko ba komai ai gida
kikazo don haka kisaki ranki kawai,
" Am sory naje na duba Momy na ne A yau Akayi mata aiki kuma Alhmdulillah Anyi
nasara so please kitayani Addu'ar Allah ya bata lafiya,
"Jikinta yayi sanyi sosai kuma sai yanzu taji kunyar shi domin tanada labarin komai
amma Bata iya cewa komai ba ta mike tareda komawa sama ta yi zaune akan sofa tareda
zabga tagumi,
Shigowa yayi da y'ar keken Abinci dakanshi ya janyo d'an karamin table gaban ta
yafara sauke naman kazar dake kan plate din tangaran nannade da poilpeper,
Sai kuma plate din gasshen kifi da kuma jug mai dauke da dafaffiyar madara da cups
ya jera tareda kauda keken gefe ya cire jallabiyar tareda zama kusa da ita tayi
saurin matsawa,
" meye haka don Allah meyasa kai Bakada kunya ne? Ya kalleta cikin ido tareda
lankwasar da kanshi, " don Allah menayi?
"Ta zabga mai harara bansani ba don Allah kasa Riga haba mana,
" wai na cirene saboda kiraba ganin da nayi miki ba Riga ne dazu ya furta tareda
daga mata gira,
"Ya janyota tana tirjewa " ki natsu Abinci kawai zamuci yanzu ba Abinda zanyi miki,
"To sai ka rikeni? " eh inba hakaba bazan iya cin Abincin ba'
Dole ta natsu ya sanya ta a tsakiyar shi ya fara war ware naman wani irin kamshi
yayi mata maraba ya kuma bude kifin ai tuni miyanta ya tsinke ya sanya fake yafara
duka a ko ina,
"Madam wanne zakici? Tayi mai banza ya debo kifin ya nufi bakinta da shi sai ga
Ummu an karbe saida tadanci sosai sannan ya fara bata kazar ta danci kadan ta
kawarda kai,
" Am OK, yayi murmushi sannan ya tsiyayo mata madara ya mika mata ta girgiza kanta
" kisha it will help you,
Batason naci dole ta karba ta mike daga jikinshi ta koma gefe ta zauna yana
Kallonta sannan yafara cin kazar shi saida yayi nak ya kora da madarar shima,
Mikewa tayi ta shiga bathroom tayi wanka tareda daukar sabon brush ta wanke bakinta
sannan ta ga wani mouth wash mai sanya kanshin baki ta kuskure bakinta dashi saboda
k'arnin kifin da taci,
Ta daura babban towel tareda yafo wani a kanta saboda tana tunanin yana ciki domin
bazata iya mayarda kayanda ta cire ba,
"Tana fitowa ta nufi kayanda ya kawo mata ta yi saurin daukar wata doguwar Riga mai
hannun shimi mai shaka shaka ta koma bayin ta canja sannan ta dawo dakin ta zura
hijab dinda tayi Salla ta koma gaban mirror ta shafa mai sama sama ta feshe jikinta
da turaruka masu kamshi sannan ta koma kan sofa ta kwanta idanun ta tar tana jiran
taga y'anda yau zata yi bacci a wannan dakin,
Shigowa yayi cikin dakin ya kalleta " hhh Aunty wannan hijabin fa ? Tayi banza
dashi ya janyo towel akan wata hanga da akajera su da yawa ya dora akan short nicer
dinshi ya nufi bathroom saida yayi wanka shima ya kuma dauro Alwala tana kallo nshi
ya kuma zura jallabiya ya tada Salla raka'a biyu ya shafa tareda mikewa ya cireta
ya Ajiye agefe,
"Madam a ina zaki kwanta?Badai sofar ba? " no Kizo mu kwanta tare bayan ni banko
balaga ba ai ba Abinda na iya,
Ta juya mai baya kawai tareda Ayyana wa aranta " Amma ka iya lalubar mutum ai d'an
iskan yaro'
Kyale ta kawai yayi batareda ya kuma cewa komai ba ya haye saman gadon ya kwanta
dai dai yana dariyar mugun ta " yarinya zaki kawo kanki ne'
Wayar shi ya janyo tareda shiga y'anar gizo yanata faman danne danne ba da dadewa
ba bacci mai dad'i ya kwashe ta saidai batakai ko minti talatin ba tafarajin sauyin
yanayi'
Zunbur ta mike zaune domin jin wani irin Abu tundaga tsakiyar kanta har zuwa
kasanta ga wani irin sanyi dake kada ta kuma taciki ba Abinda takeyi sai had'a
gumi kamar ta hadiyi kunama,
"Ta kalli inda yake kwance yana nan y'an da yake tun dazu yana faman danna waya,
ta d'an koma ta kwanta tareda dukun kune jikinta duk yana kallon ta ta wutsiyar
idanu' A hankali ya mur musa tareda fara counting daga 10 9 8. 7 6 5 4. 3. 2
" kawai ganinta yayi ta mike domin wani irin mugun feelings takeji w'anda bata taba
jin irinshi ba tsawon rayuwar ta,
Hijabin ta wurgar a gefe ta fara zagaye dakin gashi yayi mata banza kamar bai ganta
ba ganin zata halaka a banza ta matsa jikin gadon,
"Abdul" uhm inajinki' banda lafiya' Allah ya baki lafiya ya furta batareda ya dago
kanshi ba still yana kwance Abinsha dai dai,
"Wasu irin hawayen wuya ta fara zubowa tareda matse cinyar ta ta zauna a gefen
gadon tareda fasa kukan wahala,
Riko ta yayi jikinshi na rawa " meye na kuka don Allah inba so kike kijamun hawan n
jini ba,
"Ai Kaine na fada maka banida lafiya ka kyale ni " yayo murmushi domin ta mugun
burgeshi y'anda take maganar cikin shagwaba
"Sory ina ke miki ciwo? Ya dora hannu akan fuskar ta' ai tuni taji yanayin ta ya
kara canja wa tayi saurin juyawa tareda fadawa jikin shi ta kuma sanya kuka tareda
fara lalubar shi,
" tuni ta fara dorashi akan network jikinshi yafara rawa sosai' baby me kikeyi
haka?
Ya furta dakyar ta riko hannu nshi tareda dorawa akan k'irjin ta,
"Da kanta ta mike tayi wurgi da yar rigar jikinta ta fada kan jikinshi tareda hade
bakinsu wuri daya '
Suka fara aikawa juna da mugun romance w'anda ita kanta daza a tanbaye ta batasan a
ina ta koyoba,
Sun hauka cewa juna sosai ya ke juya ta da hannun shi ya kwantar da ita akan gadon
tareda kife kanshi akan Abubuwa masu daukar hankalin lafiyyun maza ya fara aika
musu da mugun tsotsa da kuma massage da tafin hannun shi Aranar tajita a wata
duniya mai shegen dad'in shiga shikuwa ai tuni ya Fara tsiyayo da hawayen dad'i
tunma bai jishi a duniyar sama ba,
" ba Abinda kakeji a dakin sai gurnanin su wani irin lasar ta yakeyi tundaga fuskar
ta har zuwa tafin kafar ta ba inda bai lashe ya kuma tsotse ba A wannan daren a
lokacin da ya isa da harshen shi ..........ai sai ta fara samai ihu domin ba
karamin dad'i yake jiyar da itaba ta wannan hanyar har tasamu Abinda ya taso mata
ya kwanta don saida tayi released taji natsuwa ta dawo mata
Wani irin zabura tayi A lokacin da ta kalli yanayin da suke ciki ta dan hasken
fitilar dake dakin,
Rikota yayi yana nishi domin shi yanzu' yake bukatar kasance war su tare idanunshi
a juye,
"K'arki tafi kibarni a haka please I needs you right now tafara tureshi " kabari
Abdul hakan bai dace ba Kasani'
"Ai cikin wani irin mugun karfin da yakeji ya kwantar da ita tareda dora mata
k'irjin shi" ki barni Ruman kar inji miki " yazaki barni cikin mugun yanayi bayan
ni na taimake ki a Gaskiya bazan y'ar da ba,
"Ihu tasa mai " Abdul fyad'e zaka yimun ne? " eh Ruman Wallahi I will reaped you
idan har baki tsaya nayi da Arziki ba haba don Allah kasheni kikeso kiyi?
Cikin zafi zafi ya fara aika mata da sabbin sakonni ya kuma dora bakinshi akan
dukiyar fulaninta ai tuni tayi lakwas tareda barwa Allah ikonshi domin tasan wannan
yaron yau sai ya cimma burinshi,
A kidime ya fara neman hanyar shi saidai gam yajita kamar ba kofa ita kuwa a
lokacin da taji katon Abu a jikinta yana neman fasa ta ai tuni ta fara tureshi tana
waro idanu "d'an yaron da ta raina ne haka tab shikuwa Jinshi a bakin tekun maliya
ai sai ya kara himma wurin kokarin ganin ya samu tsallake shi'
" Gam ya riketa domin jin irin kokarin guduwar da takeyi' yayi fusing kanshi da
karfin gaske domin dai Shikam tuni yabar UK
Wani uban ihun data buga tareda kaimai cizo a wuya Amma ina yayi nisa domin shi
kara danna kanshi kawai yakeyi a jikinta,
Yana mai zuba sanbatu da surkulle kala kala " ihu takeyi tareda kaimai duka yakushi
harda su cizo Amma shi kan ai ya dade da rasa kunne,
"Don Allah ya Abdul ka barni zanmutu ka kyale ni karka jimun ciwo nashiga uku Wayyo
Hajiya Dady Gwaggo Aunty Fenerh😜
Ai da gudu na fito daga bayan labule Amma mugun ganin da nayi yasani juyawa da gudu
nayi kitchen domin karasa sauran naman da aka rage,
Koda na dawo nasamu Ruman a sume amma yana kan Aiki dafarko dana fita Ruman ke kuka
Amma yanzu da nadawo Abdullah ne ke rusa kukan dadi tareda zabga mata kalaman da
mom Sayyed ta hana ni fadar su wai bakyau fadin sirrin mata da miji,
Amma Abdullah mugun jarababbe ne kusan hour uku ya d'auka akan Hajiya Ruman har
saida ta kuma farfadowa ta sanya kukan wahala gashi ko yatsar ta bata iya motsawa
muryar ta gaba daya ta dishe saboda kukan wuya,
" kiyi hakuri my dream " I will never leav you I love you so much please don't leav
me Ruman ki taimaki Rayuwata bazan iya babuke ba'
Shine kawai Abinda zan iya fada sai kuma uban kukan da yake rusa wa jikinshi na
rawa ga wani sabon suna da ya lika mata "Honey'
Bature yaji Zuma saida ya danji ya rage zafi ya d'an tsagaita mata tareda komawa
gefe yana sauke numfashi tareda kokarin janyota zuwa jikinshi Amma ya kasa saboda
jikinshi ya mace'
Wani irin mugun dad'i yakeji na shiga har cikin jininshi " Wayyo garin dad'i na
nesa Ashe shiyasa maza masu mata ke daga kai suna ma samari kallon mai bisa ruwa
sun San lagwadar da suke kwasa hmm
Shikam wlh ba a koma cutar shi irin wannan harka still kuka yakeyi ya juyo tareda
fuskantar ta dakyar take fitar da numfashi'
Ya janyota zuwa kusa dashi " wani irin shaukin ta ke kuma shigar shi ya kalli
k'irjin ta dake muje suna kara tsokale mai idanu gashi dama bawai ya koshi bane Ai
tuni ya fara lalubo ta
Kuka ta kuma sanya wa domin tanajin Abinda yake shirin yi " Wayyo Allah wallahi
bazan kuma cema yaroba daga yau kai yayana ne in kanawa iyayenka Abdul ka bari,
Don girman Allah kabarni na y'arda zan Aureka wallahi ina sonka ka barni haka zaka
cutar dani wallahi kafi karfina ko yanzu na y'arda
Wayyo Allah na gane KUSKURE NA bazan kara rainaka ba ka taimake ni shine kawai take
iya furtawa dakyar muryar ta ke fita susuukar ta kawai yakeyi kamar gero
Tareda rokonta " Wallahi bazan iya hakuri da zumarki ba my Honey kibarni inji
dad'in ki don Allah yana kuka tana kuka nima ina tayasu.........✍
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
💃💃💃💃💃💃💃
Masoya Fenerh godiya Mara iyaka Fenerh Love's you All💋💋💋💋
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
✍✍✍✍
GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION.
✍✍✍✍
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
✍✍✍✍
2⃣6⃣ 2⃣6⃣
➡2⃣6⃣
Saida ya gurjeta son ranshi sannan ya kyaleta suma kuwa idan tayi da kanta take
farfadowa,
Shi kanshi yasan ya wahalar da ita sosai Amma ya zaiyi zumar tace Akwai d'an dano
kamar karya bari'
Ko yanzu badon ta gaji ba da saiya kuma yi duk da shi kanshi yaji ciwon Amma dad'in
yaki barin kanshi'
Shigewa yayi cikin jikinta tareda rungume ta ga gam yana mai reramata kuka " please
Aunty na k'arki kuji Rayuwata idan babu ke numfashi na zai tsaya,
Kuka ma ta daina yin shi saboda irin Azabar da Abdul ya gana mata gashi wani irin
zafi da HQ ta ke mata kamar ta cire ta yar ga wani d'an shi dake bin kafarta tanaji
Amma ta kasa koda motsi'
Bacci takeso tayi ko zataji sauki Amma ina ta kasa gashi ya cukuikuyeta kamar zai
ballata numfashi ma dakyar take fitar wa,
Ya d'an tsagaita da kuksnshi ya fara manna mata a kumatun ta " I love you Ruman I
love you "
"Please say you still love me' inaso inji wannan Kalmar again daga bakin ki,
Ta kasa cewa komai domin maganar ma ba fita zatayi ba shi kuwa wata irin wutar
kaunar tace ke dad'a ruruwa a cikin zuciyar shi da kuma sabon shaukin ta
Ya juyo da ita tana fuskantar shi ya dora hannun shi akan fuskar ta yafara shafawa
tareda tsurawa kyakkyawan kirjinta idanu'
A Gaskiya shi mai sa'a ne da Allah ya bashi wannan tsaleliyar Yarinyar ga k'irjin
ta a cike fam ga wani kunburi da suka kara yi saboda matsar da sukasha sai wani
sheki sukeyi,
Bai San lokacin da ya dora hannu nshi akansu ba yafara shafasu tareda murza kan
Ahankali wata y'ar kara ta sanya Mara sauti wadda Sam bai jita ba
Mugun zafi kirjin ke mata ya zamar mata kamar gyanbo da saurinshi ya dora bakin shi
akansu ya fara hura mata jikinshi na tsuma domin ji yake dole ya kara idan har
yanaso ya samu natsuwa'
" Am sory baby hawaye na zubowa a idanun shi ya fara tsotsar ta a kidime yana bata
hakuri
Itakam tagama Salla mawa gaba daya tabarwa Allah domin iya wahala ta wahalu gashi
yaki barin jikinta,
Tanaji tana gani yaron nan ya kuma hayeta tareda cigaba da aikinshi kuma yana kan
zuba mata kuka
Itakam daga karshe kuma sume wa ta kumayi a karo na uku w'anda shima a wannan karon
yana samun natsuwa ya sulale akan k'irjin ta ya sume,
Ina gefe ina tausayin Ruman a Gaskiya ta haku fans bature karshe ne🤧
Saida gari ya waye Helen ta shigo cikin dakin tagansu a haka ita Ruman ta farfado
Amma ko motsi bata iyayi sai hawaye dake aikinsu
Saidai jin shiru yasata d'an janye bargon tayi saurin ja baya tareda buga ihu ganin
halinda dukansu suke ciki'
"Ma'm oh my god' ta furta tareda dafe k'irjin ta " ihunta ya farfado da Abdullah ya
bude idanunshi da kyar tareda Kallonta y'anda ta tsaya musu kerere akai'
"Get out ya fada cikin tsawa ta fita a tsorace ya yunkura tareda saurin dirowa daga
kan gadon duk da yanajin zazzabi na shigar shi Ahankali ya dagota ta sanya Kara'
" Am sory Ruman please for give me jikinshi na rawa ya dagata saidai yaji tsoron
ganin jinin dake bin jikinta ya runtse idanun shi ya dauketa cak ba tareda ya tsaya
yin komai ba ya nufi jacuzzi da ita'
Idanunta a rufe cikin tsananin wuyar da tasha A jiya ya sakar musu ruwa masu dumi
sosai A jikinsu da kanshi ya yi mata wanka saidai jinin dake zuba A jikinta ya
fara tsorata shi kardai yayi barna?
Saida ya wanke ta tas sannan ya tara mata ruwan dumi ya danna ta a ciki gaba daya
bata iya koda kwakkwaran motsi sai y'anda yayi da ita
Saida ya bari ruwan sun ratsata sannan ya fito da ita zuwa dakin ya shinfide ta
akan sofa sannan ya canja zanin gadon ya dauke wannan ya jefa a washing dustbin ya
dauke ta ya shinfide ta cikin sauri ya daura towel tareda janyo kayan aikinshi
kware towel din yayi ya ware kafafunta
Saida ya runtse idanunshi gam yaji mugun tausayin ta Ashe ba karamin halaka y'ar
mutane yayi ba da kanshi yayi mata Allurar zazzabi da painkiller sannan yayi mata
dinki a wurin da ta yage Tanaji tana gani'
Ya samu Helen ya bata umarnin dafa mata farfesun kayan ciki sannan ya hado mata tea
mai kauri ya kawo mata dakanshi ya dagata ya fara bata Abaki
Saida ta shanye tas gumi ya fara karyo mata sannan ta sanya kuka domin yanzu ne ta
farajin kuzari a jikinta'
Rungumo ta yayi a kirjinshi jikinshi a matukar sanyaye" Am so sory Honey I real
don't mean to hurt you please for give me
Cikin kuka tafara tureshi " I hate you Abdul I hate you yau ka nunamin rashin
kauna ka keta min haddina ta karfi ka Amshe min pride
Kuma duk Abinda zai faru bazan taba Auren ka ba tunda kai mugune idan har kiran ka
dan akeyi yarone yasa kamun haka ai ba sai kayi haka zan San kai namiji bane'
"Yanzu karabani da budurci na ta hanya mai muni wato hanyar zina Abdul shekara ta
kusan Ashirin ina tattalin Abuna duk da lalurar da na rayu da ita Amma a banza ka
Amshemin shi
" Abinda nakewa mijina tanadi' saurin rufe mata baki yayi'
"Yes Ruman nagode da wannan Alfarma da kika yimin na rike mun mutuncin ki a Gaskiya
na kara ganin kimar ki kuma dama ni nafi kowa cancantar inkarbe shi don Allah kar
kiyi bakin ciki akan hakan'
" Bawani nan mugu kawai Azzalumi Wallahi sai Allah ya sak....
Bakinshi yayi saurin dorawa akan nata saida yayi dogon Zango kafin ya saki bakin
suna maida numfashi itama bakin masifar ya mutu murus'
" Ai dama tuni nagama haduwa da tsinuwar ubangiji tunda nayi zi....
"Hy stop ki daina kiramin zina Anan kinajina ko' ni Banyi zina ba kuma da izinin
ubangiji bazan taba yinta ba,
Ya furta cikin fushi kuma fashe wa tayi da kuka "yanzu me muka Aikata don Allah
Abdul?
"Sunnah Ruman muka aika ta and believe me bazan taba cutar da Abinda nake kauna ba
ki y'arda dani'
"Yanzu' ki y'ar da indan kuma saka ki a cikin ruwan zafi saboda dinkin danayi miki"
"Kuka ta kuma samai " saboda Allah Abdul wace irin mugunta ce wannan harda dinki?
"Am sory aike kika kawomin kanki ina zamana kika fara tabani kinga kuwa ba laifina
bane " kuma nimafa kinji min "Auchh ya furta tareda dafe hantsar wandon shi'
" Allah Aunty na kinji min kingani ya furta tareda Ciro mata....😳
Batasan lokacin da ta wuntsila ba domin ganin Abinda yafi karfin ta tareda gasgata
cewar Abdul a cikin marasa kunya shine na farko'
"Wayyo Allah ta fada tareda runtse idanun ta " subuhanllah ya furta tareda saurin
rikota yana kunshe dariya'
Daga ta yayi cancakar ya nufi bathroom da ita tana tirjewa bai Ajiyeta ba sai A
cikin bayin ya tsayar da ita tsaye ta sanya y'ar kara'
"Ahhh "" Am sory ki daure in hada miki ruwan dakyar ta iya tsaya wa tana kwalla
yayi saurin hada mata ruwa sannan. Yada wo ya riko towel din jikinta yana shirin
kwance wa tayi saurin dafewa tareda girgiza kanta,
"Kabarni zan shiga da Kaina don Allah, shiru kawai yayi ya dan shagwabe fuskar shi'
Ta dade a tsaye kafin ta daure ta shiga ruwan gashi dakyar take tafiya tana tale
kafafu'
"Saida tasa kara kafin ta iya zama A cikin ruwan Amma daga baya tayi mugun jin
dad'in ruwan ta kalli kasanta ya mugun canja kamanni saboda tsabar sassakar da
Abdul yayi mata bata ko kaunar tunawa kada Allah ya kuma mai maita mata irin wannan
daren'
" shikuwa yana fitowa ya nemi painkiller ya sha domin yayi mugun jin ciwo a
jikinshi ga wani zazzabi dakeson rufeshi,
"Ya San cewa is a normal ting saboda irin Abubuwan da ya dade da Tarawa a marar shi
dole yanzu yayi zazzabi tunda ya fitar dashi'
Ta dade a ciki kafin ta fito tana takawa dakyar tana cije lebe'
Yana kwance ta fito ya zuba mata idanu yana maijin zazzafar kaunar ta nakara huda
ranshi"
"Come to me" ya furta Ahankali tareda mika mata hannu yana mai jin tausayin ta"
Harara ta zabga mai tareda matsawa kan sofa ta zauna mikewa yayi cikeda dauriya ya
dakko mai tareda zabo mata kaya masu d'an mutunci Riga da sket ta karba tana
kawarda kanta domin bakaya a jikinshi dagashi sai short nicer'
"Ki shirya kafin Akawo break fast"
Ta ci farfesun sosai ya bata magani tasha ta lallaba ta haye gado ba dadewa bacci
mai shegen dad'i ya dauke ta'
"Idanu ya zuba mata yana kallon ta cikin tsantsar kauna kafin shima ya kwanta a
gefen ta yayi bacci batareda ya taba taba domin yasan tana bukatar hutun,
Basu suka tashi ba sai wajen karfe biyun rana shine ya fara mikewa saida yayi
wanka ya shirya sannan ya tasheta ga wani irin Annuri da kuma haske dake fita A
goshin shi,
" my Queen kitashi ki yi wanka kiyi Salla "and don't for get to enter hurt water ya
furta tareda kanne ido'
" domin ina bukatar kiyi saurin warkewa zuwa dare domin in kuma shanawa don ko
yanzu kawai na daure ne'
Wani irin mugun kallo ta Aika mai ya durkusa tareda manna mata kiss a kumatu "take
care zanje indawo da Momy domin yau zata dawo gida'
Amma kuma tayi farin ciki ta wani gefe ko banza zata tsira da iskan cin shi idan ta
dawo wata kila ma tasa ya mayar da ita kasarta,
Basu isoba sai Karfe tara na daren su A lokacin tana zaune a falon kasa jikinta ya
yi mata sauki sosai saidai kasanta da har yanzu bai dawo mata dai dai ba,
Tayi matukar tsorata da ganin Matar Amma Abin mamaki cikin fara'a ta karaso duk da
bata gama warkewa ba'
"Welcome home my doughter' ta fada tareda rungume ta A jikinta shi kuwa wani irin
dad'i ne ke rufeshi'
Ta gaishe ta cikin ladabi da harshen da takeji sai faman tarai rayarta takeyi ta
riko mata hannu tareda cewa muje dakina kihuta my daughter nasan Jeff ya dameki ko?
Ta furta da harshen ta na nasara ta bita cikin jin dadi domin ta huta da wannan
mayen yaron,
Binsu yayi har cikin hadden dakin Momyn da yaji kayan Alatu fiye da dakin Abdullah'
"Cikin minti kadan ta cika musu daki da kayan ciye ciye kala kala tasa Helen ta
Ajiye musu yana gefe yana kallonsu'
" Momy u don't love me Anymore " ya furta cikin shagwaba tareda dan buga kafa
kamar wani karamin yaro'
Abin yaso yabata dariya ta daure tareda kawarda fuska " to ke Malama ai sai ki taso
muje dakin mu ko'
"Harara ta zabga mai " Momy tell her to come with me "
" what Momy noooo" ya samu wuri daya ya zauna tareda cewa" Wallahi ki zo mutafi ko
kuma mukwana tare A nan mu duka,
*"wooo my fan's a Gaskiya kun nisha d'an tar dani da dubun comments dinku Allah ya
biya ina matukar kaunar ku masoya Abdullah*
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA*
_Love & Destiny_
✍✍✍✍
GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION.
✍✍✍✍
https:/f/www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
Samun wuri yayi a dakin ya zuba mata idanu yana aika mata da sakon roko ta ido'.
"Ta dauke kanta tareda kallon Momy dake ta faman danna laptop kamar ba mai jinya
ba,
Aikuwa bata jira komai ba ta haye saman tafkeken gadon ta yi kwanciyar ta,
" Momy nima fa bacci nakeji" ya furta mata da harshen ta' ta d'an kalleshi " kaje
dakinka ka kwanta mana'
"Ni a gadon ki zan kwanta "ok jeka kwanta gadon zai ishemu ai'
Ita dake kwance kuwa jin wai dukan su zasu kwanta a gadon yasata mikewa zaune tana
ganin ikon Allah,
" Agaskiya musulunci yayi haka Al adar bahaushe ma tayi domin bahaushe mai kunya ne
da sanin ya kamata amma idan kana neman rashin kan gado da rashin tunani ka samu
bature,
"Cikin zumudi ya nufi kan gadon ya kwanta a gefen ta ita kuwa gaba daya shock ya
kamata,
"Abdul meye haka? Wane irin rashin kunya ne wannan Wallahi ba tsari a wannan
Rayuwa,
" ke kikaja koma meye don haka duk Abinda ya faru blame yourself not me,
"Ya janyota ta kwanta " don Allah katafi dakinka " muje tare idan kinaso intafi,
Nifa Badan wannan dinkin ba Wallahi yau... Ya furta yana kwabe fuska, a Gaskiya
Aunty kinfaya raki kalli fa daga fara wa,
Ya zabura tareda dora fuskar shi akan tata ya d'an tsotsa lips dinta kadan,
" I had the best moment of my life last night Ruman kin shayar dani Zuma mai ban
mamaki kin rikitani da dad'in ki Ruman,
"Last night is unforgettable Ruman please don't leave my life stay with me for
ever,
" Ina sonki sosai ina sonki har cikin jini na kece kadai farin cikin zuciya ta idan
baki Rayuwa ta zata shiga garari,
"Kinsan me? Ya furta a hankali yana kallon kwayar idon ta ta kalle shi kawai domin
magan ganun shi sun ratsa ta sosai,
" Na Ajiye miki surprise muje kigani kuma yakama ta ki kuma shiga ruwan dumi saboda
dinkin ki yayi saurin warke wa domin Gaskiya ko yanzu a matse nake'...
Zaro idanu tayi tareda matsawa da sauri "Wallahi ka fita kaban wuri haka kawai zan
bika
Ka kasheni,
" kuma kasan cewa Abinda ka aika ta jiya bai kamata ba ko?
"Ta kawarda kanta " kafini sani kuma don Allah ka sauka bacci zanyi'
"Murmushi yayi tareda matsawa jikinta " zunubin Abin da na aika ta jiya inace
nikadai keda shi?
"Muje inkara akan na jiya ya furta yana daga gira " hara rar shi tayi,
"Kai Wallahi kina kuma juya min ido zan danne ki a nan kuma saina cire rainin dake
tsakanin mu don naga Alamar Akwai Saura,
"Yanzu don Allah wane raini nayi maka A nan? Ta fada kamar tayi kuka, ya tuntsire
da dariyar da har Momy ta juyo tareda kallon d'an nata cikin jin dad'i,
Tasan ya samu farin cikin shi don haka zuciyar shi ta samu natsuwa gashi har wani
haske ya d'an kara da yar kiba ta jin dad'i,
Ganin da gaske yakeyi zai kwanta a wurin yasata mikewa tace " muje' wani irin
tsalle ya buga tareda rungume ta ya sakko ya rikota tareda manna ta a gefen jikin
shi'
"Good night Momy' ta kalle shi yayi saurin hada hannun shi wuri daya Alamar ta
taimake shi tayi shiru karta watsa mai shiri,
Fita kawai sukayi tana kallon farin cikin tilon d'an ta' suna fita ya dagata cak
zuwa dakinshi domin har yanzu dingishi takeyi'
" suna shiga ya Ajiye ta tareda kokarin cire mata kayan jikinta tayi saurin rikewa
" Abdul meye haka nifa ba matarka bace,
"Ko? Hmm bai saurare ta ba ya fara cire mata kayan jikinta tareda rike hannun ta
tamau Tanaji tana gani itadai Allah ya kawota wurin d'an iska,
" runtse idanunta kawai tayi tareda tsiyayowar hawaye domin yayi nasarar cire
mata kaya ya barta daga ita sai bra da pant,
"I love you baby' jikin ki zai hauka tani ya dora hannun shi akan hips dinta ya dan
matsa har zuwa kan....
Sai faman bin jikinta yakeyi yana matsawa daga baya ya dan raba jikin su ya yi baya
idanun shi jawur saboda tsabar fitina ya zuba wa k'irjin ta idanu,
Ya cire rigar jikin shi tareda dogon wando yarage dagashi sai short nicer tayi
saurin juya wa domin ganin sandar girman shi a mike kamar ice gata sharbebiya..
Bathroom ya wuce saida ya hada musu ruwa sannan ya dawo tana nan a tsaye cikin ta
ya d'uri ruwa " A Gaskiya wannan yar.... Au Abdullah ya wuce da sanin ta tab ai
dole ya b'arketa,
Jin kawai tayi yayi sama da ita sai bathroom kafin tayi wani yunkuri ya jefata
cikin ruwan dumin ta sanya mai kukan shagwaba
"Nidai banason Abinda kake mun don Allah kabari Wallahi zan hada ka da Dady,
Dariya ta bashi kawai domin y'an da take yi kamar wata yar sha shida hannun shi
yasa cikin ruwan ya fara kokarin cire mata pant tayi saurin rike mai hannu,.
" don Allah kabari, " ki bari incire miki ruwan zaifi shiga da kyau dinkin ya war
ware, "ya warke kabarni'
Ya zaro idanu " haba Ashe zan Shana yau bari kagani yayi saurin mikewa cikin
tsokana ya kwabe short nicer din shi gaba daya ya shigo ruwan tafarasa ihu'
"Wallahi ban warke ba ciwo yakemun sosai don Allah ya Abdullah kabari''''
" Hhhh wallahi kidaina wani cemun yaya bayan kece Aunty na ai dama kinfada Kinfi
karfina kuma na shaida jiya tunda har kinsani suma da kuka gashi kinji mun ciwo
nima saida nayi gashi dakyar fa nake tafiya nima,
"I don ta rufe tamau ya bi k'irjin ta da kallo tareda sanya hannun shi ya fara zame
breziyar jikinta ta ware idanu tana mai kallon ka rufamin Asiri,
Bai fasa ba saida ya cireta ya wurgar a kasan bayin ya zuba musu idanu yana mai
lumshe su kamar wani dan giya ya dora hannun shi a Kansu ya fara shafawa Ahankali
ya janyota zuwa tsakiyar shi ga ruwa na zubo musu ta sama kuma suna cikin ruwa,
Ya sanya Hannayen shi duka biyu ya fara murza su' tuni ta fara mika a jikinshi
jikinta na sakewa bai fasaba ya ci gaba da rufa mata jiki,
Birkitowa tayi da karfi ta fada kirjinshi domin Abinda yake mata yafi karfin
kwakwal war ta " Ashh ya fada A hankali domin jin wani irin shock da yayi ya
shigeshi,
"Baby play with me please ya furta dakyar yana gwama numfashi ita kuwa takasa
tabashi domin tanajin kunya da kuma tsoron wannan katuwar Abar,
Duk ya gama rudewa gaba daya ya fita a hayya cin shi gurnani kawai yake mata da
kuma nishi ganin Abun bazai fitar da shi ba ya sungumeta sai
Cikin dakin ya shinfide ta a gadon shi ya kashe wutar tareda shigewa cikin jikinta
ya fara aika mata wasanni masu zafin gaske,
tuni ta fara maida Marta ni tana kara rudashi domin bakaramin rikita ta yayi ba
shima yasa gaba daya ta manta da zancen haram cin
Tsotar juna sukeyi a hauka ce ya sanya mata kuka " ki bari inyi don Allah ai
bazaiyi zafiba a hankali zan saka please baby'
Duk da tana cikin mayen baisata d'an tureshi ba" Wallahi bazan y'ar daba kasheni
zakayi nidai aa ta d'an juya mai baya ya fisgota cikin fushi na fada miki banason A
juya min baya,
So hana ganin laifi tuni ta fara bashi taimako ta hanyar yimai wasanni masu zafi'
Yana zuba mata ihu lokacin da ta dora hannunta akan Hajiya babba kuwa kuka yasanya
mata y'anda take murza mai ita tareda matsata tana tura yatsarta cikin ramin har
wani zabura yakeyi kamar zai shide mata,
"Aunty na" ke Aunty na ce ina mutuwar kaunar ki ki cigaba da yimun k'arki bari me
kikeso in baki in Ciro muki Kaina in baki ita gaba daya na mallaka miki Kaina da
komai nawa ki yi y'an da kika ga dama dani Aunty na,
Kuka yake shirga mata sosai kamar ranshi zai fita saida yasamu natsuwa ya shige
jikinta ya matseta gam gam " please don't leave me Ruman still yana kuka,
Wani irin soyayyar shi ke kara shigar ta jita keyi A halin yanzu ba wani namiji da
ya kama kafar Abdullah dinta jin soyayyar shi takeyi har cikin kanta,
Ta dan raba jikinsu " Abdul' ta kira sunan shi" ya kalleta idanun shi na fitar da
ruwa " meyasa kake son yin kuka ne?
Ruman dole inyi kukan dad'i kedince ai kiyimin Alkawarin zama dani Ruman cikin
kowane irin hali,
"Don Allah ki rufamin Asiri gobe Dady zai zo ki fada mai cewa kinasona idan baki
fadamaba zai iya rabamu
Rabani dake kamar An Rabani da numfashi nane kuma zanje England gobe gidan kakanni
na ko zaki bini?
Tayi saurin girgiza kai aa" meyasa? Ruman bakya sona har yanzu kawai kina kula ni
ne saboda tausayi da kuma don ina d'an uwanki,
Ko yanzu Abinda kika yimun nasan tausayi yasa hakan badon kina sona ba,
Kara Jan bargon tayi ta kara rufe jikin ta' da wane lokaci Dady zaizo?
"Zuwan Dady ne damuwar ki ba tafiya ta ba? Aa ni inason ganin shine ko zai hadani
da Hajiya nayi kewarta sosai tun taso wata ban taba yimata nisa ba kuma nabar
wayata a gidan su Sumy,
" Kince mun inkira muki itane naki? Ina rokonki Ruman this is our only chance idan
kikayi shiru Dady zai rabamu don Allah kifada mai kema kinaso na'
Gyada mai kai kawai tayi "kin Amince ? Um ' ya rungume ta " tank you tank you tank
you ya furta cikin jin dad'i,
"Muje Muyi wanka duk kin batamin jiki da... Tayi saurin tashi domin tasan mai zai
fada ta nufi bayin ta kulle don tasan zai fadi Abin da yaso,
Ta dauki lokaci mai tsawo a cikin bayin bayan ta gama wanka tana tunanin y'anda
zata fito domin kuwa daga ita sai towel tana gudun kar ya kuma rikice nata domin ta
kula maye ne yaron,
Ido ya zuba mata y'anda ta rab'e shi ta wuce ya shige yana dariyar ta domin ya lura
da irin tsoron shi da yake hangowa a fuskar ta,
Cikin sauri ta sanya kaya tareda zura dogon hijabin ta ta dukun kune akan sofa'
Koda ya fito tsayawa yayi yana mamakin ta "duk lokacin da ya tabota zata badakai
sai daga baya kuma ta botsare mai kuma girgiza kai yayi ya wuce gaban mirror ya
shafa mayuka da turare masu kamshi sannan ya zura short nicer da singlet kawai ya
haye ga donshi yana hangota har bacci ya dauke ta,
Wayewar gari
Ahankali take bude idanun ta na bacci domin jin Ana shafa mata fuska cikin wani
irin siga,
Tar ta karasa budesu domin ganin ta dukun kune a jikinshi duk ya laulayeta suna
fuskan tar juna tayi saurin wuntsilawa ta sauka tareda kallon jikinta,
Waro idanu tayi duka a waje " ina kayana ? Domin tik yayi mata tayi saurin janyo
hijabin ta dake yashe a kasa ta daura,
"Abdul wai don Allah meyasa kakemun irin wannan Abun ne?
murmushi yayi tareda mika " Ya za ayi inkwana daki daya da matana Amma ta kwanta a
kasa ni a gado bayan ina kallon ta impossible,
"Waye Matar ka? " Ummu Ruman' shirme kakeyi sai dai ko a mafarkin ka kake tunanin
hakan,
"Aa a zahiri ne Amma inbaki y'arda ba ai nasha Amarci na a daren Shekaran jiya
shiyasa nakasa daurewa kina baccin ki mai dad'i na dakko ki,
Saurin shafo jikinta tayi domin taji ko yayi mata wani Abun ta tuna hakan bazai
taba yuwuwa ba batareda tasani ba bayan ma Akwai dinki a jikin ta,
" meyasa ka cire mun kaya? Murmushin shi yayi na tsokana tareda d'an kukan shagwaba
kadan" yunwa naji shiyasa na cire miki kayan domin insha Abinci na,.
"Tayi saurin shafo k'irjin ta sai Alokacin taji yana mata wani irin mugun zugi,
Wucewar ta kawai tayi domin yin wanka domin tasan dole ma tayishi saboda ita ta
d'auka mafarki takeyi Ashe a zahiri ne Abun ya faru'
Tana fitowa ta tayarda Salla Shikuma ya shiga domin Akwai tafiya a gaban shi'
Tana idar wa ta shirya cikin doguwar Riga har kasa saidai ta kamata dam ga kirjin
nan sun kunburo kamar an hurasu sunkara cika fam hip's din ta ma ya fito sosai
kamar rigar zata yage ta taje kanta tareda daure shi cikin ribon ta shafa powder ta
dan murza wet lip tayi matukar yin kyau ta nemi dan karamin gyale mai v ta Yane
kanta dashi ta sanya d'an karamin manne na diamond da ya siyo mata ta dakko farar
boyfriend jacket ta dora sama saboda rigar batada hannu,
Tunda ya fito daga bathroom din yake tsaye yana kare mata kallo ta tafi da brain
dinshi gaba daya ko motsi ya kasayi saida ta fesa turaruka ta juyo zata fita ta
lura dashi a tsaye kamar ya sume,
"Saida tafara takawa zata fita ya janyo numfashi yayi saurin taku zuwa gareta
fisgota yayi ya rungume ta tsam tsam a cikin jikinshi'
" Ina sonki Ruman ina sonki ya fara dora mata kisses a fuska har zuwa kirjinta
kamar ya hadiye ta yakeji'
Ta fara kokarin kwace wa " kabarni mana saika bata min kaya da ruwan jikin ka' "Oh
sory kece ai kika rikita ni " come I forget to gave you your promise,
Jan hannun ta yayi ya nufi gefen gadon da ita saida ya zaunar da ita sannan ya nufi
Waldrop din ya Ciro wata Leda ya dawo gaban ta,
Yaji dad'in y'anda ya sanya ta farin ciki kawai don ya bata y'ar wannan wayar,
Da kanshi ya bude dayan kwalin ya Ciro wata y'ar Karamar akwati tareda budewa,
Wow masha Allah sarka ce d'an kareriya ta zinari Akalla zatakai kusan million daya
harda Agogon ta da kuma a war waro,
Duk da batasan zinari ba Amma tana ganin wannan sarkar ta gane ta zaro idanu waje
domin Abun ya Bata tsoro sosai ina zata kai wannan sarkar tab idan tasa wannan
tafita a nija ai sai yan fashi sun bita,
" Abdul: yayi saurin rufe mata baki " banason godiyar ji nine ya kamata in gode
miki domin kin bani Abinda yafi komai tsada da muhimnci A Rayuwa Ruman nidai Addu'a
ta shine kisoni ki nunamin a bayyane kowa yasani cewar kina sona
" ke mallaki nace nikadai kuma na y'ar da da hakan "jikin ta yayi mugun sanyi taji
matukar tausayin shi tasan yana sonta sosai itama kuma tana sonshi ita tasan Abinda
ya gifta a tsakanin su muguwar kaddara ce kuma tana fatan Allah ya sa ta tsaya
Anan,
" bari in shirya kinsan inada tafiya, ta ce OK a sanya ye, daukar sarkar tayi ta A
dana ta dauki wayar ta tafita zuwa dakin Momy........✍
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
2⃣8⃣ 2⃣8⃣
➡2⃣8⃣
Ya shirya cikin kana nan kaya tareda daukar wayayoyin shi da kuma system din shi
kamar w'anda zaije Aiki,
Ya fito yana zuba kamshi tana zaune a falon tana faman danna wayar ta ya shigo,
dago kanta tayi tareda zuba mai idanu domin ya mugun tafiya da ita,
Karaso wa yayi kusa da ita ya ya d'an duk'a kadan tareda hura mata iskar bakinshi ,
"Hy wannan kallon fa My Queen? Ta dawo daga tunanin da takeyi ta kauda kanta gefe'
" ni ba kallon ka nakeyi ba mema zan kalla? "Abin kallo mana ai nima inada Abin
kallo bake kadai bace kikeda shi,
" ko baki y'ar da ba in nunamiki ta waro idanu tana mamakin halin Abdullah shi
gaba daya sun raba hanya da kunya,
"Ni zan tafi My Queen kiyimin Addu'a ya danyi kissing fuskar ta har zuwa kirjinta
sannan ya mike zuwa dakin Momy,
..
Ya dauki lokaci kafin ya fito yana Rungume a jikinta kamar wani jariri karaso wa
yayi ya riko hannun Ruman ya ce " muje arakani,
Ba halin musu dole ta mike ya rike hannun ta suka fito Amma suna takowa wajen gidan
wata kyakkyawar sabuwar mota budaddiya ta faka ,
A cikin wata yarinya ce baturiya ta dau wanka irin nasu na rashin kunya " yaja
yatsaya tareda Sakin hannun Ruman yana murmushin jin dad'i ya nufi wurin ta,
Tana fitowa ta D'ane shi "Natasha" oh my god longest time ya fada shima tareda bata
fake a fuska,
Saida suka gama shirmen su sannan suka karaso Ruman da ta zuba mai idanu ranta na
tafasa jitake kamar kirjin ta ya fito tsabar bakin ciki,
"Wallahi Allah ya wadaran rayuwar bature Sam ba tsari komai nasu ba Addini,
Wani irin kallo ta jefa mai w'anda ya kada y'an hanjin shi ta juya cikin gidan
cikin sauri,
.
Yayi saurin kiranta" Ruman My Queen wait Amma ina ta shige da gudu ya bita Amma
kafin ya shiga har ta shiga dakin ta kulle ta ciki,
Yayi kiran duniya taki budewa gashi ana jiranshi dole ya tafi,
Ko Sallamar Natasha bai tsaya yiba ya wuce domin itace sanadi gaba daya ta bashi
haushi,
Momy ma kiss kawai ya manna mata ya wuce' Tunda ya shiga mota ya dafe kanshi tareda
runtse idanun shi" oh Allah help me "
"Wayar shi ya bude ya tura mata message " Am sory my Queen she is just a childhood
friend noting else'
"Tana jin tafiyar shi ta fito ta yi zaune a bakin gadon tareda dafe kanta tana mai
jin zafin Abun a cikin zuciyar ta,
Karar Shigowar msg yasa ta saurin dubawa taga sakon shi ta karanta tareda zabga
uban tsaki " kai ka sani'
Nigeria
"Jafaru ban gane ba kayi mun bayani ina kuka kaimun yarin ya?
Hajiya dake zaune tareda su Gwaggo Amina har ma da magaji' gefe daya kuma baban
Ruman ne har da bilkisu tana sauraran gulma,
" Inna kiyi hakuri Ya tafi da ita ne can kasar waje ba Abuja ba sai bayan ya tafi
ya kirani yake fadamin kuma kafin inyi magana ya kashe wayar shi Amma yau dinnan
zanje,
"To mai zaisa ya tafi min da yarinya batareda sanina ba? Gwaggo Amina ta ce" yaya
ai dama damusa tayi gudu d'anta yayi rarrafe? rashin hankalin da suka shuka dole
yayan su suma suyi
" Wallahi ku saurareni idan wani Abun kuka kulla to zaku war ware shi in wani Abu
yasamu jikata duka ranku sai ya baci'
Magaji dake gefe yayi shiru sai yanzu ya dago idanun shi cikin bacin rai" yarinya
daga zuwa wurin bikin kawarta sai kawai muji wai Abdullahi ya dauke ta wannan wane
irin shirme ne?
"Dama kundawo cikin rayuwar mune don ku tayar mana da hankali? To ai da baku dawoba
kuci gaba da zama da wa inda kuka zaba fiye damu ,
." waini dakata kodai wannan dukiyar bata Allah da Annabi bace? Kodai siyar min da
jika zakuyi?
"Haba Inna ya kike fadar haka Kuyi mana zaton Alkhairi kuma inaso ki sa Aranki ba
Abinda zai faru da Ruman yau dinnan zanje UK din zuwa jibi zan dawo miki da Ruman
dinki'
" Mama ki kwantar da hankalin ki don Allah bakomai Abdullah bazai cuci y'ar uwar
shi ba ki kwantar da hankalin ki'
"Muhammad kamun shiru " ai nasan dama ba son Ruman kake yiba don haka komai ya
sameta Bazaka damu ba,
"Haba MAMA kidaina fadar haka Ruman fa gudan jini nace ya Zanki ta? " yo sau nawa
Meka sani akan rayuwar ta,
" Shiru kawai tayi domin Abdullah ya sakashi a uku dama idan har ka sabawa naka
iyayen kaima sai y'ay'an ka sun yi maka fiye dashi'
"Yanzu ta ina zai fara fadawa iyayen shi cewar Aure Aka daurawa Abdullah da Ruman?.
" ya sameshi tareda mukhtar yayi mai bayanin komai dangane da sharadin mahaifin shi
akan cewar in har ya fadawa wani nashi zancen soyayyar shi da Ruman bai yafe ba,
Bayan dogon nazari dattijon ya hanga ya hango cewar barna na iya Afkuwa domin a
wannan zamanin w'anda ma ya rayu a cikin musulunci tun haihuwar shi ya yakare bare
kuma w'anda bai gama sanin haram cin komai ba yasan Al adar bature ba tsari idan
har bai dauki mataki ba za a haifi da Mara ido'
Yasa ya samu wakilai guda biyu ya wakiltasu waliyai ya nemi Abdullah da ya bayar da
sadaki A daura musu Auren jikin shi na rawa ya bada dubu Dari biyar domin baida
wasu kudi da yawa a hannun shi a lokacin,
.Dady yayi matukar firgita da Abinda Abdullah yayi ya kuma kirashi yayi mai fada
sosai kuma ya fada mai ya rubuta mai Sakin Ruman ya turo tun kafin kowa ma ya ji
"Daurin Auren yazo dai dai da ranar sa lallen Sumayya Abdullah da kanshi yayi ma su
hajara bayanin komai ya kuma rokesu da karsu fada mata don Allah shine kuma ya
shirya musu dinner da yaje har ya dauke Ruman a wurin,
Shiyasa hajara ta dage wajen sawa Ayiwa Ruman gyaran jiki sosai,
" kinsan halin kawar ki bazata taba bada hadin kaiba idan har na tsaya wasa inaji
ina gani zata Auri wani bayan tana sona kuma ga Dady na,
Sunji dad'in lamarin saidai sun San Akwai matsala nan gaba a cikin family,
Sai yanzu Dady ke da yasanin rashin fadawa iyayen shi da kuma d'an uwanshi Abinda
ke faruwa gashi yanzu komai ya kwabe,
Hajiya dai ta dage zata UK jama'a Bayan sun fito Dady ya kasa zaune ya kasa tsaye
a dole ya samu d'an uwanshi ya yi mai bayani tareda bashi hakuri'
"Murmushi yayi mai cike da jin dad'i" Alhmdulillah nagode wa Allah " kasan cewa A
kullum tunani na bai wuce waye Ummu zata Aura ya rike mun ita Amana ba,
" Amma banji dad'in y'anda ka hanashi fada ba Yanzu kaga KUSKUREN ka a nan ya nuna
ma zamani
Dariya kawai yayi '
"Bilkisu kuwa wani irin farin ciki takeji don a tunanin ta Asirin ta ne ke aiki
Tunda har aka gudu da Ruman,
Wani gefe kuwa dariya take yiwa sopy " shegiyar yarinya ba kin nace sai kin
sameshi ba to shi ya dauke y'ar uwar shi sun tafi sheke aya a kasar waje " Allah
yasa ta dawo musu da ciki muga karyar soyayya nasan bakin ciki zai kashe tsohuwa,
Dariya kawai takeyi Abunta' Hajiya dai ta shirya tsab su magaji na kara zuga ta,
"Karfe daya jirginsu ya daga zuwa UK' tafiya ta tafo Hajiya za'a UK,
Tun tafiyar Abdullah take zaune a cikin dakin gaba daya jikinta a sanyaye yake Momy
ce ta shirya cikin zuwa Aikin ta ta leko ta ce ta shirya ta bita saboda zaman
kadaici ba dad'i,
" tayi farin ciki sosai kobanza zata rage tunani ta shirya cikin Riga da wandon
Jean's rigar ta sauka har kan guiwarta saidai batada hannu sai ta kuma dora wata
boyfriend jacket din akai ta nemi mayafi ta nade kanta irin na musulman America ta
saka wani takalmi mai d'an tudu ta dauki wayarta ta fito tana baza kamshi,
Momy ma ta yi matukar burge ta ta rungume ta tareda manna mata fake a gefen fuska "
looking great my daughter'
"Tayi dan murmushi " tank you Momy, security ta ko ina suka shiga motar Sun fara
tafiya kenan a cikin lafiyayyar lemoxen din Momy wayar ta tayi kara tasan shine
don ba w'anda zai kirata sai shi,
Kin dagawa tayi ya kuma turo mata da msge Tanaji " Momy kuwa tana aikinta a
laptop,
Wayar Momyn ya kira tayi picking " hy son ya fara zuba mata shagwaba ta d'an kalli
Ummu dake wasa da wayarta tayi connecting da laptop dinta ta haska mai Ruman'
"Muryar shi kawai taji " hy my Queen " please kiyi hakuri fushin ki zai jefani
cikin matsala ki rufamin Asiri'
Murmushi kawai ta aika mai tareda gyada kai tana kallon shi yana kwance a tafkeken
gado lafiyayye dagashi sai boxer'
"Baby Am missing you " dole ce tasa natafi da ba inda zan tafi inbarki. Wallahi
kamar indawo,
Baby ki warke please kafin indawo inba hakaba zan iya hauka cewa kin lasamin Zuma
mai wuyar mantawa pray for us so that everything will be Alright,
"Ajiyar zuciya kawai ta sauke tana mai binshi da kallo ita har mamakin kanta takeyi
wai wannan yaron ne ya gama da ita shine ke Jan ragamar rayuwar ta shine sirrin
ruhin ta A Gaskiya jarumtar shi tasanya ta kara kaunar shi ya nuna mata Asalin
jarumta,
Jinshi take sosai a Gaskiya ita kanta tasan cewa tana matukar kaunar shi Tunda har
ya rabata da pride dinta bataji haushin shiba ya kamata ta kyamaci hakan a
matsayin ta na y'ar musulma " shin wai meke faruwa da itane haka Anya tayiwa Hajiya
Adalci?
"Ruman ya kira sunan ta " what are you thinking? Ta girgiza kai " Momy ta karbi
laptop din ta ce ya barsu sun iso office ya kira Anjima'
Ya zaro ido" office da Ruman Momy Noo please tell driver to take her back '
"Why son ? Yace Akwai maza da yawa bai y'arda ba su kalle mai mata saidai ta koma
gida tanajin rigimar shi '
Haka kuwa driver ya koma da ita gida bayan har sunkai company tana sauka ya kirata
ta d'auka
" Meya sa kake mun haka ? Abdul ka raboni da kasata ka Rabani da pride dina kuma
yanzu katafi Abunka ka barni a nan fitar ma yanzu ka hana inyi saikace wata Matar
kulle,
"A sanyaye take maganar domin yanzu Sam bata iya daga mai murya batasan dalili ba,
" am sory my Queen nayi laifi Amma ki fahimce ni " soyayyar ki ce sanadi ina kishin
ki"
"Banason ko kallon ki wani namiji yayi kiyi mun Alfarma daya Ruman don Allah no
matter what k'arki bari a rabamu zan iya rasa Rayuwa ta,
Wani irin dad'i takeji har cikin zuciyar ta domin Yanzu ta kuma sakan kancewa da
irin soyayyar shi a gareta
Don da jikinta yake so ai yanzu ya samu zai gujeta amma sai karuwa da soyayyar ta
tayi a cikin zuciyar shi
Meyasa batajin bakin cikin Abinda yayi mata? " saboda kinason shi kema wata
zuciyar ta fada mata,
A haka ta wuni daga kwanciya sai Sallah ita kadai a gidan kamar mayya sai kuma su
Helen mai aiki,
Sai washe gari su Hajiya suka iso Uk tayi wujiga wujiga a lokacin ma Momy ta fita
ita kuwa bacci kawai takeyi hankalin ta kwance,
Kamar a mafarki taji muryar Hajiya " Ummu Ummu " ta d'an bude idanun ta domin
gasgatawa
"Aa sakeni ja'ira bayan kintaho kinbarni inashi ja irin yake da ya taho dake?
Dariya tayi cikeda mamaki " Hajiya ta kece a UK ? "Eh y'ar wofi dana nima ya
kawoni,
" kai naji dadi Wallahi domin nayi ke warki sosai "matsa can a ina kikayi kewata
keda ke baccin ki hankali kwance ni kuwa inata fama da tunani " ai dana sani bazan
zoba,
"Yi hakuri my kakus nan ma ai gidane' eh ina baturiya take? Badai tayi miki komai
ba ko? " kai Hajiya don Allah kiyi shiru Wallahi Momy batada matsala kune baku
fahimce taba,
"To naji Yanzu ina Abdullahi yake? " baya gari tunjiya ai" dama dole ya gudu Tunda
baida Gaskiya ina nan ina jiranshi zai dawo ya sameni'
Dariya kawai takeyi domin tayi matukar farin cikin ganin kakar ta mai sonta,
"Kallon dakin kawai takeyi tana ganin Aljannar duniya A ce yayansu ke Rayuwa cikin
wannan daular ' ai dole su manta da iyaye,
Abincin Hajiya kebi da idanu " Ummu ina Abincin yake sai ganye d'anye kawai nake
gani '
"Ai Hajiya shine Abincin " wannan ? Babu tuwo ? "Hajiya tuwo a nan tab ai Wallahi
ko masara basuda ita ta tuwo sai dai ta gwangwani,
" aa da sake kiramin Jafaru "yo ko a makka ai Akwai wurin masu tuwo bare nan,
" shigowa yayi dakin yana dariyar Hajiya domin ya na jinta " Inna sannu ya gajiya?
Ai har yanzu Akwai ta Tunda banci tuwoba,
"Jafaru wannan ai yafi makka nisa ko? " Hhh eh Inna Akwai tazara a tsakani"bari a
kawo miki Abincin da zaki iya ci'
"Ai ni da ka fadamin har kuka ta zan riko mai kyau da kuma garin dawa Amma wannan
ai mutum zai horu ,
"Saida tayi kat da namomi tanaci tana tanbayar Ruman" Amma wake musu yanka kaddai
mushe muke ci?
"Dariya Ruman tayi tace " to kidaina ci kawai Kakus dina nayi ke warki Wallahi
sosai "
"Hajiya tayi matukar mamakin irin tarbar da ta samu a wurin Momy don har Dukawa
tayi wajen gaisheta,
" ke ce ta mike tunda batajin hausata' ta ce ma Ruman dake kallon gaisuwar Hajiya
da Momy kamar ta tuntsire saboda dariyar da ta kunshe,
A gefen Dady kuwa gaba daya masifa ya sauke wa Momy akan cewar ita ke daurewa
Abdullah gindi shiyasa ya aika ta Abinda yayi yanzu' kuma ta fada mai ya dawo ina
jiranshi yabani takardar yarinya don bazan dauki sakar cin shiba.....✍
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
_Domin ki SA'ADATU BINT ABDULLA, Uwar marubuta ina matukar farin cikin y'an da kike
bibiyar wannan littafi nawa Wannan shafi sa daukar wace ga duk wani member na
BOYAYYEN AL AMARI kuma muna neman Alfarma da ki karasa mana wannan labarin kafin
Muyi zanga zanga, masoya ina Alfahari da ruwan comments_
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
2⃣9⃣ 2⃣9⃣
➡2⃣9⃣
Ruman tasamu wal wala sosai da kuma farin ciki zuwan Hajiyar ta, Abdullah kuwa
tunda yasan sunzo bai kirata ba har tsawon kwana biyu ga shi Dady ya je meeting a
Chicago Momy kuwa kullum tana wurin aiki watara na ma sai dare take dawowa,
"Hajiya kaka kullum mita " Wace irin Rayuwa ce wannan mata aiki miji aiki shima
tilon d'an su yawo sunemo su bashi ya kashe '
Yau kusan sati biyu da zuwan su Hajiya Wanda yayi daidai da tafiyar Abdullah A
zaune suke a cikin katon falon Ruman na kwance a langwabe haka kawai batajin dad'in
jikinta wani iri yakeyi mata gashi bakinta Sam baya mata wani dad'i,
Ga muguwar kewar Abdullah dake damun ta yaki bari suyi waya saidai kullum ya turo
mata da text msg fiyeda sau goma a rana a yanzu ne takejin mugun sonshi na kara
shigar ta wani irin kewar shi ke damunta Hajiya kanta taga rashin wal walarta
" Karar wayarta yasa ta duba domin tasan ko waye zai kirata gashi tana cikin
matukar bukatar ganin shi a yanzu,
Mikewa tayi ta nufi daki kafin ta fada gado tayi received " A jiyar zuciya suka
sauke a tare " Baby ina hanya ke warki zata kasheni I can't keep myself away from
you anymore zanzo ayi mai yuwuwa nasan Hajiya na nan,
"Baby ina sonki sosai bazan iya Rayuwa bake ba dakyar nake iya bacci daren jiya
kuwa ban runtsa ba saboda ke warki da kuma tunanin ki
" nasan dinkin mu ya warke ko? Ki shirya mun a yunwa ce zanzofa "aa Abdullah a
Gaskiya bazan kuma y'ar da wani Abu ya shiga tsakanin mu ba kasan fa babban laifine
wannan muka aika ta
" Abdullah ina kiran Kaina babba a she ni nafi kowa kuruciya domin nasan nice
nabaka gudun mawar da har ka aika tamun a binda muka aikatan don haka banason hakan
ya kuma faruwa saida igiyar Aure akan mu,
Murmushi yayi mai kayatar wa "kin yarda zaki yi Rayuwar Aure dani Ruman?
" kin y'arda cewar ni zan Isar miki? Kin Amince nine zan iya baki kulawar da kikafi
bukata?
"Eh Abdul na gane KUSKURE NA nakin Amince maka tun farko da hakan bai faru ba
" Ruman kina sona? "Eh Abdul soyayyar da nake maka ta hanani ganin laifin Abinda
Kayimin ka dawo na shirya fada ma kowa ina sonka,
" wani irin ihun murna ya sanya tareda farin ciki' nagode sosai Ruman bakisan irin
farin cikin da kika jefani ba " I love you so much ki jirani nan da thirty minit
zan shigo UK,
"Wani irin farin ciki ke bayyana a kan fuskar ta ta mike tareda kallon kanta a
madubi domin ita tana mamakin matukar canja war ta
Kullum Hajiya tanbayar ta takeyi " Ummu wannan cika da kikeyi duk zaman wuri daya
ne ya janyo ko ?
Ita bata taba lura da muguwar canjawar da tayi ba sai yau komai nata ya kara cikowa
musamman kirjinta da sukayi fam fam dasu itama tafara y'ar da da canjin muhalli ne
da kuma Hutu da yake ratsata,
Fitowa tayi falon cikin wal wala" aa Albishir aka yimiki da zuwa makka wannan
fara'ar da nake gani a fuskar ki tun safe ban ganta ba sai yanzu,
Bayan minti goma ta tsinci kanta da son yin wanka ta shirya cikin tsantsar ar riyar
kwalliya wata doguwar Riga mai tsagu tundaga kasa har zuwa kwabrin ta ta sanya
tight a ciki mai shara shara ga rigar ta kamata tsam tsam ta d'an yi kwalliya sama
sama kar Hajiya ta tanbaye ta
Ita kanta mamaki takeyi " Yanzu saboda wannan yaron da ta Rena ne take irin wannan
kwalliyar?
"Tayi matukar kyau ga fatar ta ta kara goge wa da kuma sheki ta fesa turaruka ta
fito,
Batafi minti goma ba ya iso gidan sai da kirjinta ya buga domin batasan mai kuma
zai faruba duk da tana matukar kewar shi Amma bai hanata jin tsoron karon su ba
karya kuma rinjayarta
Da Sallamar shi ya shigo murya kasa ba inda idanun shi ya sauka sai Akan hasken
zuciyar shi,
Ajiyar zuciya ya sauke mai karfi tareda zuba mata idanu har ya karaso tsakiyar
falon batareda ya lura da Hajiya ba'
" Au Allah ya dawo dakai sarkin yawo to ina nan dama jiranka nakeyi "ja'iri '
Maganar Hajiyar ne yadawo dashi daga dogon zangon Kallonta da yatafi domin tayi
mugun tafiya dashi ta rikita mai kwakwal wa gaba daya cikin minti daya kacal ya
hango canji a jikinta,
Ya juyo cikin tsokana " haba Hajiya kakar mu "Ai itace babba ita ta nuna zata
biyoni kinga ni karamine dole inbi umarni don haka inzakiyi fada kiyi mata'
Bude baki tayi tana mamakin Abdul da rainin hankali yanzu itace babba ko Tunda zai
hadata da Hajiya,
Dawowa yayi kusa da ita ba tareda ya damu da Hajiya ba ya zauna gab da ita " My
Queen " yana in healing kanshin jikinta ya rage murya,
"Muje ciki don Allah kar inyi Abin kunya don Wallahi inason rungumar ki jikina har
rawa yakeyi baby kin canja muje ciki in dubaki kafin in zauce,
" dago idan uwan ta tayi tareda zuba maisu ta yi mishi wani irin kallon da saida ya
kusa shide wa " kirufamin Asiri muje daga ciki don Allah Wallahi zuciya ta zata
buga idan har banjini cikin jikin kiba,
"Waiku wannan kuskus din da kukeyi na menene? " Hajiya tasan Abinda nakeso Amma
taki kina ganin ko sannu da zuwa Bata yimun saboda banje da itaba
"Au yaushe kuka fara wannan ? In ban manta ba bakwa shiri " Da ne
Wannan yanzu mun shirya "Aunty na zamuje infada miki wani Abu kar Hajiya taji mu'
Ya fada tareda riko hannun ta a dole ta mike domin rikon da yayi mata bawai rikone
ba kawai harda d'an sako yake aika mata
Hajiya dai ita kallon ta kawai takeyi kamar tana fahimtar abinda ake fadar
Janta yayi cikin dubara ya nufi wani dakin dake cikin falon kasa dakin ma ya hadu
sosai kamar na saman '
" Yana shiga ya wurgar da jacket din hannu nshi yayi saurin rungume ta kamar zai
maida ta ciki' I missed you so much my Queen,
Dan fara kokarin raba jikinsu domin gudun Abinda zai iya faruwa
"Abdul stop" yana shinshina wuyan ta ya dora hannun shi ya cire mayafin dake
jikinta k'irjin ya bayyana
Tuni jikinshi ya fara rawa ya dora hannu nshi akan k'irjin ta yana fitar da
mawuyacin numfashi,
"Please Abdul kadaina' idanun shi har kwalla ya tara muryar shi na rawa " ya ce ki
bari in rage damuwa ta don Allah Ruman wallahi zan iya cutuwa idan har kin hanani
haba nafayi kokari yasunkuce ta ya nufi saman gadon da ita
"Cikin zafi zafi ya fara rage kayan jikinshi sannan ya nufeta ya fara kokarin cire
mata Riga kafin tayi wani yunkuri ya zugeta har ya sauke ta tasama ,
" Ruman kin canja ya fada muryar shi a dishe ya zubawa k'irjin ta idanu duk da yana
bu kace da ita ya Ciro daya a cikin brah ya zuba mai idanu'
Tareda riko hannun ta ya zubawa tafin hannunta idanu har zuwa yatsunta sai nan ya
dago kanshi ya zubawa fuskar ta idanu,
"Baby look at me' ta d'an buda idan ta kalle shi" da wani irin kallon da yasashi
manta Abinda yakeyi ya fara romancing dinta da zafi zafi
Ganin yana shirin zarce wa tayi saurin tureshi ta mayarda nonuwan ta a bra da ya
Ciro yake ta faman tsotso kamar na gyatumar shi
"Noo Ruman please k'arki yimun haka idanunshi sun kada sunyi mugun ja har wani
ruwan kwadayi suke fitar wa,
" Rigar ta ta mayar tareda daukar mayafin ta ta yafa " kayi hakuri Abdul banason in
kuma aika ta wani mummu nan Abun bayan w'anda mukayi kabari Muyi Aure,
Dakyar ya iya mikewa yana tangadi ga igiyar K'arin girmanshi na Harbin iska kamar
taci babu gaba daya yaron yanzu tsoro yake bata don ya wuce da saninta,
"Rikota yakuma yi" k'arki horani don Allah kibani dama ko yanzu ne kawai bazan iya
jurewa ba ki taimaka min Ruman ni ko wasa ki yi dani to irin na ranar,
"Abdul banason girma na ya gama faduwa bayan kasan duk Abinda ya faru niza aga
laifina ina gudun Abun kunya,
" saboda nice babba " cikin fushi ya saketa Abin kunya ? To indai shi kike gudu ai
ya faru tunda komai ke kar girman ki ya fadi to gwara ma kibada kai kawai domin
ina hango Alamar Ajiya ta a kwance a mararki........✍
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
3⃣0⃣ 3⃣0⃣
➡3⃣0⃣
"What? Me kake nufi da hakan? Matsowa ya karayi jikinta ya kara rage murya,
" Ruman me yasa bakya tausayi na ne kinfa san nayi kokari da nayi har sati biyu ki
bari insamu natsuwa kafin Muyi maganar Ajiyar,
"Wai ni Bangane Ajiya ba? Ta fada idanun ta a waje " shafo cikinta ya farayi yana
mai kara shige mata,
"May be you are pregnant, ai wani irin zabura tayi tareda tureshi'
" ciki cikifa kace " ina bazai yuwuwa ba ta furta tana girgiza kai cikeda da farga
ba da kuma nadama
"Relaxed ya furta tareda rikota ta buge mai hannu' impossible ya ma za ayi inyi
ciki da Nashiga uku,
A matukar rude ta tureshi " ka matsa kar inyi ma wani lahanin " cikifa Abdul ? "
ban tabbatar ba tukun Amma ki nutsu idan ma cikin ne ni zanfi kowa farin ciki'
"Farin ciki? Da shegen? Mugun hankade ta yayi tareda daure fuska cikin tsananin
fushi tuni fuskar shi ta sauya
" cikin nawa zaki kira da shege? Ruman gudan jinina ne shegen? Dan halak d'an
sunnah?
Ita Sam bata fahimtar magan ganun shi hawaye ne masu zafi ke fitowa a cikin idanun
ta "don Allah ka dubani idan cikin ne ma tun kafin kowa ya sani ka cire mun
" Wayyo Allah na wai nice da cikin she.... Tsawa ya buga mata mai karfi tareda
nunata da yatsar shi kasa cewa komai yayi ya janyo rigar shi ya saka
"Fita kawai Ruman k'arki batamin rai ' ya nuna mata kofa " Wallahi ba inda zani
saika dubani idan shine ka cire shi tun wuri kafin kowa ya sani,
"Kallon ta yakeyi kawai y'an da duk ta rude take zuba mai bori akan Abinda bai
tabbatar ba,
Kwantar da ita yayi tareda dakko wata y'ar Karamar scanner ya daga rigar ta sama ya
goga wani dan Abu kafin ya fara Aikin shi,
" wani irin farin ciki ne ya lullube shi domin ya hango jinin shi a kwance a cikin
mararta
"Ya rufe tareda rungume ta cikin tsananin murna" baby tank you kinbiya ni da irin
wannan kyauta,
Ita kuwa sandarewa tayi cikeda tsoro " Abdul ciki nake dashi da gaske? " eh Ruman
kinada Cikina cikeda murna zan zama baba "Allahu Akbar Allah mai girma,
" Wayyo Allah ta fasa mai kukan da ya dawo dashi daga dogon zangon farin cikin da
ya shiga,
"Wai meye kikeyi haka Ruman ? Ai Bazaka saniba Tunda ka cuceni Hajiya zata kasheni
Banyi wa Hajiya Adalci ba bata cancanci ganin wannan bakin cikin ba
" ni Ruman da ciki cikin ma wai naka? Fisgota yayi cikin fushi zuwa jikinshi " ki
saurare ni Wallahi wallahi wallahi rantsuwa nawa nayi?
"Idan har wani Abu ya samu Cikina Wallahi sai kinyi dana sani A rayuwar ki' ki
kiyaye ya saketa tareda nufar bathroom,
" kuka ta saka mai d'an karfi, Na gata Kaina ni Ummu Ruman ina zani da wannan
babban Abun kunyar?
Shikuwa tun shigar shi bathroom din yakasa sukuni ga koshi ga kwanan yunwa ga farin
ciki ga bukatar shi,
Saida ya sakarwa kanshi ruwa sosai kafin ya fito farin cikine sosai a bayyane akan
fuskar shi " wai shine da cikin kanshi ?
"Wani tsoro da ya shige shi shine kar ta salwantar mai da ciki ta hanyar tunanin ta
na banza,
Zabura yayi ya zura jallabiya ya fito " Hmmm Ajiyar zuciya ya sauke mai karfi ganin
su zaune a falon har da Momy ta dawo,
Da saurin shi ya karasa kusa da su ya zauna gab da Momyn shi ya d'an rungume ta "
welcome my Momy'
Rungume shi shima tayi tareda manna mai kiss a kuncen shi "tnks my son how was your
journey?
Hajiya dai mamaki kasheta yayi har ta kasa daurewa tayi magana " yanzu kai
Abdullahi da girman ka ka haye jikin uwarka? Ikon Allah,
"Dariya suka sanya har Ruman dake gefe cikin tashin hankali batasan lokacin da ta
dara ba domin jin irin shishshigin Hajiya kaka,
Kallon ta yayi ta sakar mai harara tareda daure fuska ta dauke kanta,
Momyn shi ya kalla " Momy come I want to tell you something,
Tana shiga ya rungume ta hawaye nabin kuncin shi ta fara tanbayar shi lafiya?
Natsa kanshi yayi tareda fada mata cewar Ruman nada shigar ciki,
Wani irin farin ciki ne ya lullube ta Rungume shi tayi cikeda farin ciki
Ta janyo wayar ta zata fadawa Dady yayi saurin riko hannun ta " Momy not now
A hankali ya fada mata rigimar shi da Ruman din ta reda rokonta ta kula karta
yimai Asarar ciki domin zata iya cutar dashi,
Ruman kuwa dakin da take zama ta koma cikin tsananin tashin hankali tafara tunanin
Abinda zata sha cikin ya fita domin ta dauki Alwashin zubar da shi tun kafin Asirin
ta ya tonu,ta
A ranar dukansu basu runtsa ba shi sai faman juyi yakeyi domin yana tsananin
bukatar ta gashi tana tareda Hajiya ba halin yaje dakin haka ya kwana a wahal ce,
Gari na wayewa tayi wanka tareda shirya wa cikin irin shigar da yanzu ta zamar mata
jiki wato kana nan kaya ta yi matukar kyau sosai
Kitchen ta nufa domin ganin mai zata sarrafa wa Hajiya domin Bata iya cin girkin su
ita ke kokarin nema mata Abinda zata iydinahsayehsaye take t ana wanke hannun ta a
cikin sink
Kallo daya zaka yimata kasan tana cikin tsananin damuwa "Rungume ta ta ji anyi wata
irin Ajiyar zuciya ya sauke
Sanin shine yasata yi saurin ture shi jikinta tafara ruwan masifa " kasan y'anda
zakayi da shegen cikin ka Wallahi kafin kowa ya sani,
Wani irin kallo ya bita dashi cikin jin haushin Kalmar da ta fada mishi wai shegen
ciki'
Fisgota yayi cikin jin zafi " k'arki kuma sheganta min ciki kinaji "kuma ko ma
Yayane inason Abuna kuma Wallahi ki kiyaye halshen ki kuma ki wuce muje ina
bukatar ki yanzun nan kafin ranki ya baci Wallahi,
Sakin baki tayi kawai tana kallon shi lallai ma wannan yace wani Abu ya dirka mata
cikin kuma ya bita da wani fadan
" ba inda zanje kayi Abinda zakayi kuma daga yau ko hannu na ka kuma tabawa ban
yafe maka ba bare har a wuce hakan,
Kallon ta yakeyi cikeda fushi "Ruman stop ki daina haram tamin Abinda Allah ya
halasta min ke halas dina ce kuma Cikina Wallahi ko kud'a ya taba min shi bazan
y'arda ba don haka ki kiyaye
kuma hakki na yanzu nake bukata ki wuce muje ko kuma a yau din nan Zanfada wa
Hajiya komai dake tsakanin mu harda cikin jikin ki
Tsoro ne ya kama ta wasu hawaye ne masu dumi ke bin kuncin ta kallon shi tayi
hawayen na zuba " Abdul kasan me kake aika tawa kuwa?
"Eh sunnah nake yi da iyali na ganin baya ganewa kawai ta juya tareda kokarin ci
gaba da Aikin ta,
" kallon bayan ta yakeyi yana had'iyar mugun miyau " ki wuce mutafi nace Ruman,
"Hajiya nakewa girki kajira ingama, jikinshi narawa ya kara matsowa kusa da ita "
da gaske zakizo gareni Ruman ?
"Bata Amsa shiba taci gaba da Abinda ta keyi, bari in tayaki so that kiyi sauri '
A haka suka kammala yana kwakume da ita kamar wani magnet ta dauki Abincin tayi
dakin Hajiya tana mai Ayyana wani Abu a zuciyar ta,
Komawa yayi dakin da yake ya zauna yana mai jiranta duk ya kagara ta dawo ganin ta
dauki lokaci ya zura jallabiyar shi ya bi bayanta
.zaune take a gefen Hajiya tanata Kwasar hirar ta tama manta dashi
Tama cire rigar jikinta ta rage daga ita sai shimi da dogon wando ga kirjin ba bra
komai ya bayyana " tun dosowar shi yayi suman tsaye don ta gama gogemai duk d'an
karatun dake cikin kwakwal war shi,
"Shigo mana Abdullahi' inji Hajiya " dakyar ya saita kanshi idanun shi har sun juye
ya karaso a sanyaye,
Ya gaisheta " wai ni yaushe baban ka zai dawo ne nifa nagaji da zaman wannan kasar
da babu tuwo bare miyar kuka,
"Sai zuwa jibi Dady zai dawo idan sun kammala in kuma bai dawoba sai wani satin
"Keda wa Hajiya? " nida Ummu mana dama ai saboda ita nazo " ja iri Kasani biyo
doguwar hanya,
Ai duk kai kaja da ina can garin mu da na saba gaba daya hankalin shi nakan ta tako
ki kallon shi bare ya yi mata magana,
Yasan ba tasan Auntyn nan dama da biyu ya furta, "muje kibani Abincin nima kinsan
fa yunwa nakeji,
Harara ta zabga mai yayi murmushi ya kalli Hajiya" Hajiya yanzu idan Na haifi yaro
ko Ruman meye matsa yin shi a wurin ki?.
"Kinga mu jikokin kine shi kuma fa ? Wani irin zabura ta yi tun kafin Hajiya ta
bashi Amsa ta mike don kar ya tona mata Asiri ta shiga uku
" muje in baka Abincin ta furta cikin sauri' yayi dariyar kyeta " ta janyo rigar ta
zata zura ya girgiza mata kai" don't ware it,
Kallon shi ta yi wani iri dole ta fita a dakin tanufi dakin da yake zama yanzu'
Zaune take cikin zurfin tunani dafa tan da yayi yasata dawowa cikin hayya cin ta,
Zama yayi dab da ita ya rungumo ta cikin jikin shi " Ruman kina sona kuwa yanzu?
"Ka daina maganar nan yanzu ni mafita kawai nake nema kasan y'an da zakayi da
wannan cikin
" shiyasa nace bakya sona yanzu " da kina sona zakiso gudan jinina hannun shi ya
dora akan marar ta ya fara shafawa
"Kinsan irin farin cikin da nakeji kuwa idan har na tuna wai kina dauke da Cikina
sonki karuwa yayi a cikin zuciya ta kin kara girma a idona Ruman I truly love you,
Kece farin cikin Rayuwa ta ina sonki sosai tuni ya fara ruda mata jiki yana mai
kasheta da dadadan kalamai tareda kaiwa jikinta sunba ta ko ina,
" ki Haifa mana cikin mu zamuyi Alfahari da Abun mu wata rana ina son kayana sosai
kar kiyi mun hasa rar shi,
Hawaye kawai take fitar wa " haba Abdul meyasa Bazaka gane Abinda nake guduba "na
tafka babban KUSKURE na y'arda da kai tun farko duk da ta karfi kayi mun bada son
raina bane,
Yanzu idan iyayen mu suka sani me kake tunani nice babbar banza da har na sake maka
jiki ka bani ciki don Allah wane irin KUSKURE ne wannan na tafka
.
Sai yanzu na gane KUSKURE NA,da tun farko na Y'arda munyi Aure duk haka bazata faru
ba yanzu gashi munyi ciki batare da Aure ba ta yaya zan fuskanci Hajiya
" Abdul kabarni bazan taba yima Abinda kake bukata ba don ni ba y'ar iska bace
kabarni inji da Abinda ke damuna
Duk y'anda yaso ta barshi ya samu natsuwa a ranar hanawa tayi komawa yayi gefe ya
dunkule tareda dafe cikin shi ya sa kara'.
"Kasheni kikeso kiyi kinaso ki jefani cikin halaka ne Ruman a Gaskiya yau bazan iya
hakuri ba ki hani hakkina a matsa yinki na matata ko kuma infita in nema a waje
zunibin ya hau kanki ba ruwana
Juyowa tayi ta zuba mai idanu ta na mai binshi da kallon mamaki " Matar ka?........
✍
*"Am sory my fan's da rashin jina kwana biyu saboda rashin tabbas na na urar bature
wayata tasamu matsa la Amma yanzu zaku rika samun post insha Allah*
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
Matar soja
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA*
_Love & Destiny_
_Written by fenerh_
✍✍✍✍✍✍✍
GOLDEN PEN WRITER'S ASSOCIATION.
✍✍✍✍✍✍✍✍
_*Alhmdulillahi Ala kulli halim nagodewa Allah da ya bani ikon dawo wa online Allah
ina kara gode maka da irin baiwar masoyan da nakedasu Albarkacin wannan rubutun
masoya Ina matukar godiya da irin kulawar Ku a gareni A gaskiya banida bakin code
muku Allah ya bar kauna INA matukar yinku sosai wallahi*_
_*daga karshe ina ma daukacin musulmi murnanr ganin sallah lfy Allah ya mai maita
mana Allah ka karbi dukkannin ibadun Mu ya kuma biya mana bukatun mu Na Alkhairi
Ameen*_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
*KUSKURE NA*
_Love & Destiny_
_Written by fenerh_
3⃣1⃣ 3⃣1⃣
➡3⃣1⃣
Mikewa tayi zunbur tana mai watsa mai wani irin kallo "me ka ke nufi da ni Matar ka
CE?
Sai daga lokacin ya San me ya furta mata tuni ya shiga taitayin shi' "ki nutsu
inyi miki bayani A hankali
"Kallon wane irin bayani kawai take jifan shi da shi jikin shi a sanyaye ya dukar
da kanshi kasa'
"Ruman ke mata ta ce Dady Na yasani ki natsu mi shirya yanda zamu shinfida rayuwar
Auren Mu idan har mun shirya kanmu bawanda zaiyi kokarin rabamu
"Auren Mu mai tsarki ne cikin jikin ki halas ne ki daina sheganta min shi please
INA sonshi fiye da komai a yanzu ki tayani tattalin shi'
"Matsowa yayi ya rikota domin takasa koda motsi ya d'an girgizata "Ruman ki dawo
hankalinki ki bani Amsa
Tureshi tayi cikin fushi "karka raina min wayau Abdul nasan wayon ka so kawai
kakeyi in kuma. Sakar maka. Jikina ka kuma yin Abunda kaga dama To bazai yuwuba
"Ina aka taba daura Aure batareda sanin iyaye ba ko yarda ta wallahi rainin hankali
ne wannan
Ta juya cikin fushi zata. Fita ya sha gabanta "Ruman meye haka ne wai?
"Bakya tausayina ko? Kusan duk rayuwata tana tareda ke meyasa bazaki barni
hankalina ya kwanta ba ya furta kwalla Na ciko mai a idanu'
Hankad'e shi ta kumayi cikin zubarda hawaye "wallahi nayi Dana sanin saninka.
Arayuwata ka cutarda ni ka shiga rayuwata da yawa Allah ya isa
"I hate you. Abdul kuma koda da gaske ne Andaura mana Aure wallahi saika sakeni don
ba zan zauna dakaiba kuma cikin jikina saiya bi ruwa idan har akwaishi
Zaro idanu yayi duka a waje yana mai binta da kallon mamaki "cikin nawa zaki zubar?
"Hmmm go Ahead sannan Aurena dake mutu karaba basaki ba yaji
Ya furta tareda matseta a jikinshi ta fara tureshi wallahi ka kyaleni kafin insa
maka ihu,
"Go Ahead shout I will be happy kinga idan Hajiya taji said infada mata komai
Kokuwa sukeyi sosai tana kaimai duka da cizo ta ko ina. Daga karshe ya nunamata
karfin maza ya ciccibeta said kan gado yafara yanda yaga. Dama da ita
Ganin irin kukanda takeyi yasan ya shi dole ya kyaleta tareda tureta gefe ta
dunkule gefe daya tana maida numfashi
Gefe shima ya koma ya rike cikinshi cikin tsananin bukatuwa yana mai juyi kamar
zaiyi hauka wasu irin hawaye yake fitar wa masu zafi
Tana saita kanta ta mike tagudu dakinsu tasamu Hajiya zaune" kekuma tundazu daga
zuwa bashi Abinci shine kikayi zamanki?
"Na tsaya wani aikin ne ta furta tareda samun gefe ta zauna tana mai tunanin
abinda kefaruwa tsakanin ta da Abdullah hankalinta Na kara tashi yanzu ina zatakai
wannan Abin kunyar?
Kallon Hajiya tayi"kakus wai yaushe zamu koma Nigeria? "Ai ni nafi ki matsuwa mutum
kamar yana cikin kurkuku
*************************
Bata kuma waiwayar
Shi ba har gari ya waye bata yarda sunhadu ba har wayewar wani garin da Dady ya
dawo
Hajiya tasashi a gaba. Akan ya maida su gida nan take ya fara shirin koawar su nija
Abdullah kuwa baya ko gidan ya je England. domin ya nisanta kanshi da ita domin.
Yasan bakaramin wahala zaiyiba idan har zairika ganinnta akusa dashi,
Momy ce kadai tasan da tafiyar shi kasan cewar itama ba zama takeyiba Sam batada
labarin tafiyar su
Gabadaya hankalin Ruman yatashi domin taso ganin shi kafin ta wuce don Agaskiya
tana sonshi saidai fitinar da take hango musu musamman idan cikin jikinta ya
bayyana don haka dole yana komawa zata nemi hajara tasan yanda zatayi dashi run
wuri,
A kwance yake a dakinshi dake cikin hotel din da yayi masauki a cikin birnin Na
England ba Abunda yakeyi sai tunani domin gaba daya hankalin shi a tashe yake
Shidai ya shiga ukun shi Wallahi, karar Shigowar kira ya sanya shi mika hannun shi
tareda Kallon screen din wayar ganin Dady ne yasa shi mikewa jikin shi na rawa yayi
picking,
"Idan ka gama guje gujen ka ka sameni a Nigeria domin mun wuce dasu Hajiya da Ummu
Ruman,
Ya katse kiran batareda ya jira Amsar shi ba , wani irin wawan zabura yayi ya diro
akan gadon cikin tsananin tashin hankali
" zata zubar min da ciki idan har ta isa Nigeria don haka dole ya bi bayan ta kafin
ta yi mishi aika aika,
Cikin sauri ya fara shiri ya bi jirgi sai Uk domin daukar kayan Amfanin shi ya
samu har sun tafi bai tsaya jiran komai ba ya nufi Airport domin Dady ya tafi da
private jet din su'
Ruman sun isa lafiya tsohon gidan su suka sauka domin Angama gyara ko ina ya dawo
ginin zamani part biyu aka mayar da gidan Dady da baban ta ba karamin kokari sukayi
ba domin dun sanya musu kayan more Rayuwa ko ina
Sakin baki kawai sukayi suna kallon y'anda gidan su ya dawo kamar ba shi ba runfar
yan gulma kuwa An mayar da shi dan madai daicin gareji
"Hajiya harda kukan Dadi' tana ta sanya musu Albarka ita kanta Ruman ganin yanayin
gidan us d'an rage mata damuwa ,
Komai anzuba musu har kitchen dinsu ya zama na zamani kamar ba gidan kaka mai tuwo
ba dakin Ruman kuwa komai anzuba mata tundaga gado har zuwa suturu sababbi
Suna hutawa ta hada musu lafiyayyan tuwo ta kawo musu miyar kuka domin ita kanta
tana marmarin tuwon kuma sunci sosai saidai tana gamawa taji zuciyar ta na dan
tashi ta mike da sauri ta nufi cikin dakinta dake dauke da bayi a halin yanzu
Kafin kace me ta fara sheka amai duk saida ta Amayar da Abinda ke cikin ta sannan
ta watsa ruwa ta fito bata dawo falon ba gadon ta ta haye
Cikin galabaita ta fara mayar da numfashi
Dole ma tasan Abun yi kafin wannan cikin ya bayyana da sauri ta mike ta dakko wayar
ta ta fara lalebo numbar hajara
Ta kira sau kusan uku bata daga ba ta tura mata msg " _na dawo ina nija I need your
Assistance please_
Baccin gajiya ta yi ba ita ta tashi ba sai wayewar gari Hajiya ma da ta leka taga
tana baccin itama kawai kwanciyar ta tayi domin bakaramin gajiya sukayi ba
Abdullah kuwa sai karfe tara na safe ya iso gidan su dake GRA ya nufa saidai ba
kowa domin Dady ma Kaduna ya wuce domin kula da Aikin da Ake yimai,
"Kayan shi kawai ya Ajiye ya kira Ak tareda tanbayar shi Dady ya mai bayanin suna
KD Hajiya kuwa duk sunkoma gidan su
Cikin sauri ya katse kiran ya nufi gidan su Hajiya, Ruman na tashi ta shirya cikin
Riga da zani single na Atanfar ta super tayi wani irin kyau da kuma jiki na Hutu da
kuma yanayin kasar da ta fito
Sumar nan tasha gyara tayi packing dinta a tsakiyar kanta ta daura dankwalin ta ta
fito kamar wata Matar shugaban kasa
Hajiya ta kalle ta " ke kuwa daga tashi kin shirya ina zuwa haka?
"Zanje GRA ne wurin hajara,
"Ta fita tana murmushi saida ta leka gidan su Gwaggo Amina taga y'anda suma gidan
su yasha gyara kamar nasu ko ina masha Allah ga masu taya ta hidimar gida suna ta
aiki,
Sunyi matukar farin cikin ganin ta " Aa keda muke shirin zuwa yimuku sannu da zuwa
sai kuma gaki kinzo
"Ya hanya mutanen turai ?tayi dariya ai Alhmdulillah mundawo lafiya " yayar ku
nacan ko motsi bata iyawa saboda gajiya
"Ja ira kun wahalar da ita ba dole ta gaji ba " ina shi dan kusun uwar yake da ya
tafi dake?
Sun d'an taba hira sosai kafin ta wuce tana fitowa ta nemi mai mashin ta yi mai
kwatancen inda zai kaita
Mashin din na tsayawa ta biyashi ta juya da nufin shiga cikin gidan su hajara taji
An fisgota
Cikin tsananin jin tsoro ta dago kanta tareda ware idanun ta akan w'anda ya
fisgotan '
"Abdul' ta fada cikin kidima domin batasa ran ganin shi ba a nan " to yaushe yazo?
"Cikin tsananin fushi ya fara ruwan bala'i " Ruman kina matata kike hawa mashin
kika hau bayan wani katon da igiyar Aurena?
"Kin cuceni Ruman " yanzu daga dawowar ki shine kika fito kalli irin Adon da kika
caba Ruman zaki shiga wuta idan har baki nutsu ba horon ya isheni haka da wanne
zanji da borin ko da fadan Dady?
Fisge wa tayi tareda kallon shi cikin masifa "ba ruwana koma meye kuma Auren karyar
dakake fada ko da gaske ne saika sakeni don ba zan zauna dakai ba kamun yaro ehem'
Ta fada tareda mur guda mai baki " kuma cikin nan zubar da shi zanyi Wallahi'
"Ni inason iskanci mu samman ma dake don haka ki shirya karbar iskanci a hannun
karamin yaro,
Bai direta sai tsakiyar dakin shi mai gadin ma kallon tsabar rashin kunyar yakeyi
", lallai bature bashi da kunya
" Abdul ka fita hanya ta banaso "Ruman ba hanyar ki ba har rayuwar ki yanzu na fara
shigar ta kuma ki shirya bani hakki na nagaji Wallahi bazan iya hakuri ba kin Riga
da kin d'an danamin zumar ki bazan iya yi babu ke ba
" fisgota yayi zuwa jikinshi jikinshi na rawa ya fara sauke Ajiyar zuciya "Ruman
kidaina wahalar da rayuwar mu haka ki bari mu more Auren mu
" kinga y'anda kika sani duk na fita hayyaci na "ki barni haka na Azabtu ki y'ar da
dani Auren mu na sunnah ne idan har baki y'ar da ba zankai ki wurin malamin da ya
daura mana Aure ina zuwa ,
Ya juya cikin sauri ya janyo wata drower " kudine bandir guda ya mika mata "ga
sadakin ki tun lokacin da Aka daura Auren na Ajiye miki su
Wani irin kallon ka maida ni y'ar iska kawai take jifanshi dashi
Jakarta kawai ta fisgo tareda gyara mayafin ta ta nufi hanyar fita, yasha gabanta
cikin fushi " Wallahi ba zaki fita ba idan kuwa kikayi KUSKUREN zubar min da ciki
sai mun hadu a kotu na fada miki Cikina ko shege ne inason Abuna
Idanun shi da suka fara k'ankance wa ya zuba mata yana mai bin ko ina na jikinta da
kallo "baby na kinyi kyau sosai sannan ya guntse fuska
" meyasa zaki fito batareda izini na ba? "Anyway daga yau bazaki kuma fita ba sai
tare dani
Kallon karfin halin shi kawai takeyi ta zuba mai idanun ta mayafin ya fisge ya fara
bin kirjinta da kallo dake cike fam fam ga dinkin ya mugun kamata saboda jikin da
ta kara
Tuni yafara Sakin layi matsowa yayi sosai ya shige jikinta yana fitar da nishi my
wife ki dan tausayawa kanin ki kibashi Abinda yake murad'i ina cikin tsananin
begen kuma kasan cewar mu a inuwa daya,
Fuskar shi ya dora saman kafadar ta numfashin shi na yawo a wuyanta tuni ya sakar
mata da wata irin muguwar kasala a hankali jikinta ke macewa yana sakewa ta ko ina
Kafin kace me tuni jakar hannun ta ta sabule shikuwa ganin yasamu nasarar ta tuni
yafara zuge rigar jikinta ya sabule ta daga kafadar ta yana mai bin ko ina da kiss
Tuni tafara karbar darasin tareda bada gagarumar gudun mawa wajen kara mai kaimi
Ba abinda ke tashi sai nishin su cak ya dagata sai kan gadon shi ya sanya hannu
tareda warware zanin da ta daura ta rage daga ita sai bra da under Wear
Gurnanin shi kawai ke fita tuni ya fita hayya cin shi jikin shi sai rawa yakeyi
tuni yafara sarrafa ta ko ina yana Sakin mata zafafan sakonni
Bakin shi ya jefa cikin nata ta cafko tareda fara bashi wani irin sunba mai tafiya
da numfashi
Tuni yayi fatali da kayan jikinshi ganin haka najanyo legedis Benz dina na fito kar
inyi mugun gani
Falon na fito na zabga tagumi ina mamakin halin Ruman anaso ana kai kasuwa ihun ta
yasani komawa domin ya samu isa birnin maji dad'in ya kure iyakar gudun shi neman
agaji takeyi domin bakaramin gudu yakeyiba
"Wayyo Allah na Wallahi Abdul Bakada tausayi wane irin Abune wannan kai mugune ka
barni karka kasheni Wayyo Hajiya zai kasheni
" don girman Allah Abdul kabari Wallahi Akwai zafi Marana ciwo takeyi Wayyo Cikina
jin irin kukan da takeyi yasa shi tsagai tawa ya dan rungume ta yana buga mata baya
a hankali ko magana yakasa yi domin yana cikin jirgin sama
Dakyar ya fisgo magana "Sorry baby ai kece kikaja da tuntuni kinbar ni da ba haka
ba don haka kibarni in fitar da Abinda kika sani natara
" don Allah kabarni zaka cutar da cikin ka nima zan cutu' dagowa yayi da jajayen
idanun shi ya kalle ta kadan,
"Ba Abinda zai samu Cikina karfi kawai zan karamai " kuma ma yau she kika fara son
Cikina da har kike gudun wani Abu ya sameshi?
Shiru kawai tayi tafara kokarin tureshi domin ya mugun sakar mata nauyin kirjin shi
akan nata
Bai saurareta ba saida yayi son ranshi tun tana kuka har tayi shiru saida ya gamsu
dan kanshi ya koma gefe yana maida numfashin satisfaction
Ita ma dunkule wa tayi ta dafe ciki tana numfashi domin bakaramin zungurota yayi ba
ga kasanta kamar an watsa mata barkono
Kuka ta sanya ya mirgino tareda rungume ta "sorry my wife " bazan kuma yi miki haka
ba ke dince Akwai sirrin dad'i ko yanzu da zaki y'ar da zan kara Wallahi babyna
nima da da halin kuka zanyi kinji y'anda joy stick dina ke zafi dakyar fa na samu
na shiga kamar wata budurwa najiki baby Gaskiya nayi sa'a ke ta daban ce
Ga wani dadi da naji kin kara Zuma zakwai hannu ya dora akan cikinta yana shafawa a
hankali "marar na zafi ne?
" kai kawai ta iya dagawa domin tunda yafara magana tayi tsit domin Sam Abdullah
baida kunya Wallahi
"Sorry my dear sweet wife hannun shi na yawo akan cikakkun nonuwan ta yana murza wa
" Auch ta furta tareda ture hannun shi " kadaina Akwai zafi fa , ta fada cikin
salon shagwaba
Shikuwa tuni yafara bin wata hanyar ai jin Abinda yake kokarin yi tuni ta zabura ta
mike tareda janyo zanin ta ta daura dakyar take takawa saboda Azabar zafin da
takeji ta nufi bathroom ta barshi yana juyi a gado,
Ruwa mai zafin gaske ta hada saida ta gasa jikinta kafin ta tara wani mai zafin ta
shiga ciki tana runtse idanun ta,
" Wallahi Abdul karshen Mara kunya ne jin Shigowar shi cikin ruwan yasata bude
idanun ta "kirjinta yakebi da kallo da ke shekin ruwa tuni ya dora bakinshi akansu
yafara tsotsa kamar yasamu sweet
Tana ture kanshi yana girgiza mata kai Alamar ta barshi a haka ya rika mutsutsuka
ta a cikin ruwan saida ya kuma rage zafi a zuciyar ta ta furta,
"Eh ni maye ne kuma mayen Ruman da da hali ma hadiye ta zanyi gaba daya kowa
yadaina ganin ta saini kadai
Kokarin mikewa tayi domin bazata iya da rashin kunyar shi ba janyota ta ya kuma yi"
ki tsaya Muyi wankan tsarki ko ke baki zubar da ruwan dad'in bane?
"Kallon shi tayi tareda kauda fuska " Abdul wai meyasa Bakada kunya ne? "Inji
kunyar matata? Ni ki tsaya ki gasani kinji min ciwo nima hannunta ya janyo ya dora
tasa kara Wayyo Allah na,
Zaro ido yayi " saikace wadda taga Abin tsoro? "Eh kai ma Abin tsoron ne ai, dariya
yayi sannan ya sakar musu ruwa saida sukayi wanka ya kinki mota ya dawo da ita
dakin ya ajiyeta " ki shirya muje wani wuri yanzu,
Ta harare shi " ni gida zankoma yanzu tunda ka hanani zuwa inda nai niyya,
Shirin shi yayi cikin kananan kaya kamar koda yaushe farare Riga da wando ya fito
kamar Justin bieber mawakin baturen nan kuruciyar shi a bayyane
Magani ya Ciro ya mika mata kisha zakiji karfin jikin ki karba tayi domin tana
bukatar maganin kayanta ta mayar ta dan shafa mai da powder
Shi ya dauki Jakarta tareda wayoyin shi da kuma makullin mota yace " muje ko
Kallon shi takeyi y'anda yake fitar da wani irin Annurin kyau da sheki ga wani irin
Annurin dake fita a fuskar shi
Yana gaba tana binshi a baya suna fita harabar gidan ta kalle shi " ni zanje wurin
da nayi niyya
Daure fuska yayi tamau ki wuce muje kafin inyi wani Abun a gaban mai gadi
"Dole ta bishi don tanajin kunyar tsohon wata sabuwar mota dalleliya kirar benzer
new mothern 2019 golden colour ya bude mata tashiga motar ta tafi da ita gashi tana
tashin kamshin turaren mota mai tsada ya tayar cikin kwarewa
Tun tafiyar bata je ko inaba bacci ya dauke ta shikuwa titin Kaduna ya d'auka cike
da farin ciki yana mai binta da kallo
Jifa jifa tareda shafo fuskar ta har zuwa tafin hannun ta Yarike ta mau yana tuki
da hannu daya saida ya kai jaji ya dauki wayar shi tareda kiran numbar magaji
" kaga baturen turai kashigo garin ne? Dariya yayi "eh kaka ka fadawa rikitacciyar
yayar ka na kuma dauke mata jika idan ta huta ta biyomu wannan karon ba nisa mukayi
ba muna Kaduna,
" Shiru kawai magaji yayi ya kalli Gwaggo Amina "kinji ja irin yaron nan wai ya
kuma tafiya da Ummu " ni malam meke tsakanin su ne haka?
Wannan Abun ba banza ba" Hmmm Ajiyar zuciya ya sauke tareda goge gumi" uban shi ya
mun bayani ina batun zuwa insamu Yaya gashi ya kuma yin wani shirmen
"Amma wannan yaro Akwai sha kiyi koda yake barewa tayi gudu d'an ta yayi rarrafe?
" bari inkira ubanshi yanzu "shi kuwa yana gama fada ya kashe wayar shi wata ya
janyo da yasanya sabon layi ya kira mukhtar
" Abokina nakusa isowa hope everything is ready ? "Yeah till you come friend,
Hankalin Dady ya tashi domin yasan Abinda zai iya faruwa Hajiya zatayi kara'i idan
har taji Abinda ke faruwa numbar Abdullah ya fara nema Amma Akashe,
Wani tafkeken gidan ya nufa cikin shahararriyar unguwar masu hannu da shunin nan
dake malali gidane nagani a buga a jarida ya danna horn aka bude mai ya shiga
Bayan mai gadi harda security ta ko ina saida ya faka sannan fara shafo fuskar ta
idanun ta ta bude ta zuba su akan fuskar shi,
Tayi saurin zama da kyau " hy sleeping beauty welcome to our palace,
"Abdul kuma satoni kayi? Eh gidan ki na kawoki na gaji daga yau kin tare a gidana
Sakin baki tayi tana mai mamakin shi" Abdul haka ake Aure? Bayan fyaden daka yimun
sai kuma ka satoni ka kawoni wata kasar
"Matse fuska yayi " wane fyade kece fa kika fara batani ina dan yarona dani kin
lalatani don haka bazan iya hakura ba ki shirya bani gidan dad'i na a kullum.......
✍
*Kuyimin uzuri my fan's ina kula da Soja na ni bazan iya sakacin Ruman ba kubarni
inji dashi inya koma aci gaba dayi kullum🙈🙈*
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
*ke d'ince dai sharifiya ta Allah ya kara miki d'auka ka wato SADIYA SIDI SA'ID
SIDIYA matukar jidake sosai Allah ya bar kauna*
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
➡3⃣2⃣ 3⃣2⃣
3⃣2⃣
Fitowa kawai yayi daga cikin motar ya zagayo gefen ta ya bude mata murfin motar
"Fito Amaryar Abdullah " welcome to my world, fitowa kawai tayi tana baza idanu
domin Abun yafi karfin magana,
Ginin gidan kawai take kallo Aljannar duniya gidan ya k'eru yanzu ana nufin wannan
katon gidan mallakin d'an yaron nan ne ?
"Numfashin shi taji gab da wuyan ta " gidan ki ne mallakin ki my Queen "Momyn na ta
gina min shi domin tasan ina burin zama a kasar nan shiyasa ta saki kudi aka
keramin son raina domin nida matata,
Ajiyar zuciya kawai ta iya saukewa " Abdullah meye hakan kataba ganin Anyi Aure a
haka ? Nan fa ba turai bane da kowa keyin Abinda yaga dama,
A nan ana Aure cikin y'ar dar iyaye komai nan anayin shi cikin Al'ada da tsarin
Addini bawai irin wannan da kayi ba gaba daya ba tsarin bahaushe bane wannan,
"Kallon ta kawai yakeyi tunda ta fara magana saida takai Aya ya ce" waye yaja ?
"Duk Abin da ya faru KUSKUREN ki ne Ruman kinki kibani had in kai kinki ki y'ar da
Muyi komai akan tsarin da ya dace don haka blame your self,
" OK na gane KUSKURE NA ne yanzu ka mayarda ni gida Muyi musu bayani " murmushi
yayi tareda girgiza kai "no Ruman I can't take you back sau nawa kike cewa zakiyi
magana daga baya ki botsare ni dai kawai ki wuce mu shiga ciki yunwa ma nakeji muje
ki yi mun girki yau inci Abincin matata
Kallon kafi kowa karfin hali kawai take yimai da kuma rashin hankali yayi gaba
tareda cewa muje kawai'
Tama kasa furta komai shike nan yanason yaja musu Abun fada itace ma za afi Zagi ba
shiba don duk Abinda da namiji yayi Adone
Dole ta lallaba shi ya mayar da ita don taga Alamar Jan ido bazai yi aiki ba a
wurin wannan yaron,
Bin bayan shi tayi har zuwa cikin tafkeken falon gidan da yaji komai na more duniya
Tsaya wa fadan tsaruwar falon bata bakine kawai saidai ku k'iyasta readers
Juyowa yayi ya sakar mata murmushi mai tsayawa a zuciya " madam kinga gidan ki ko ?
Nine na zabi komai dake cikin gidan domin nasan zaiyi dai dai da tsarin my Queen
Ya matso cikin shauki da kaunar ta dake kara ratsa shi " baby ki barmu mu rayu mu
reni cikin mu kinga ko Dady na bai San da wannan gidan ba ki bari musha dad'in
rayuwar mu mu more '
Riko hannun ta yayi ya jata cikin wani daki mai dauke da wani irin Dubai bed irin
na larabawa mai sanduna harda labule kamar wani gadon sarauta,
Ga sif dinshi wall to wall ya matsa da ita har gaban shi ya sanya hannu ya zuge
suturu ne birjik masu tsada da kuma kyau gefen atanfofi daban lacess daban dogayen
riguna ma daban ga kuma kasa ta kalma ne kala kala suma kowace da jakar ta ga kuma
su designer Po's na zamani suma
Ya sanya hannun shi ya janyo wata y'ar Karamar save sarkoki ne da su agogo gasu war
waraye na gold da Azurfa har ma da zobuna
"Baby kinga dakin baccin mu duk wa innan kayan nakine ya furta tareda sak'alo
hannun shi ta k'uibinta tareda dora habar shi akan kafadar ta
Ya fara sauke Ajiyar zuciya " stay with me for ever my life please ya furta cikin
kashe murya
Wani irin tausayi ya bata domin tasan yana matukar sonta sosai hannun shi ya dora
akan marar ta yana shafawa
"Kinsan me ? Ta girgiza kai " ina son wannan cikin fiyeda raina kinsan saboda me?
Ta kuma girgiza mai kai,
" zoki gani ya kuma Jan hannun ta zuwa wani dakin na daban da Aka shirya kayan
wasan yara har mada gadajen su kusan uku ga bangon ko ina An lika wall peper ta
cartoon din yara irin su Barbie dasu dora tom&Jerry ,
Ga su balls toy's kala kala gefe ga yar Karamar computer ta roba da gado irin na
Asibiti d'an karami gwanin sha'awa
"Abinda duk zan Haifa zai zama likita kamar ni insha Allah
Tsuguna wa yayi agabanta tareda riko hannun ta duka biyu ita kuwa sai dai ido "
"Ruman please don't leave me ' idan kin fita Rayuwata zata zama useless
Wasu hawayen tausayin shi suka fara zubowa cikin idanu na ya taso tareda tarewa da
hannun shi " please don't break my heart with your tears please "
"Muje ki huta kafin ki hada mana girki zansa akawo miki house help banaso ki
wahala,
" wane irin Rayuwa ce wannan ni Ruman take aiya nawa a cikin zuciyar ta ga koshi ga
kwanan yunwa,
Dady kuwa kiran Momy Tara yayi ya fara rufeta da masifa akan ta fadama d'anta ya
dawo mai da yarin yar shi kafin ranshi ya baci'
"Ita kanta batada labarin Abinda yayin saidai ta kira managern ta da ya kula da
Aikin ginin ya fada mata cewar ai yana cikin gidan tareda madam,
Ita kanta ta jinjina karfin halin yaron nata ai ko su idan har Auren kwarai zakuyi
dole sai An gayyaci relatives bare Nigeria dake da Al adu
Dole Dady ya bar Kaduna ya nufi Zaria domin samun Hajiya saida ya gayyaci baban
Ruman ya fada mai komai
Dariya kawai yayi " ai wannan ba wani Abu bane tunda Matar shi ce ta sunnah kawai
muje muyiwa Hajiya bayani kawai nasan zata fahimta,
Kana ganin abin zaizo da sauki kuwa ? "To bamuda wani zabi saidai kawai mu barwa
Allah,
A haka suka kama hanya cikeda fargaba Hajiya dai tana zaune har kusan karfe biyu
ba labarin Ruman
Magaji ma dayazo yimata sannu da zuwa ya kasa furta mata komai sai tad'i kawai
take bashi na Uk da irin Abincin su har da yimai tanbayar " dama magaji Akwai
garin da babu kuka da daddawa ?
Dariya ya sanya mata " kai yaya kuka a kasar turai? Ai kuka sai Nigeria " to Allah
ya Rabani da zuwa irin wannan garin Amma kaga makka Akwai tuwo da miyar kuka
lokacin da mukaje Aikin haji lokacin da riyal dinka kaci kayi kat Amma wannan
shegiyar kasa tunda naje banga idon tuwo ba,
"Shidai dariya kawai yakeyi Abun shi har zuwa lokacin zuwan su Dady
Gaisuwa suka fara mikawa tafara sanya musu Albarka tareda godiyar hidimar su sannan
suka tankwashe kafafu domin koro bayani,
" Mama magana ce ta kawo mu akan yaran nan' "to Allah yasa muji Alkhairi wasu yaran
daga farko?
" Ruman da Abdullah, " to inaji wani Abune ya faru? "Eh Mama a hankali suka koro
mata bayanin komai cikin natsuwa tareda zancen Auren ga badaya,
" tsit kakeji bayan sun gama koro bayanin tace "tirk'ashi lallai An yi mun Aikin
rainin hankali a gidan nan wato tun lokacin da ya dauke mun ita daga farko zuwa
yayi ya sa Aka daura ma yarinya Auren rashin gata to Allah shine gatan mu nida Ummu
kuma ku saurare ni magaji ka zamo sheda idan har yarinya ta Bata dawo gidan nan ba
daga yau zuwa gobe ban yafe muku ba
" Ashha yaya kiyi hakuri kece fa ke mun fadan inrika daukar Abu da sauki gashi ke
kuma kina zafafa Abun,
"To ko da hadin bakin ka aka cutar min yarinya saboda ita diyar mace ce a wurinka
uwarta bata Raye to nice gatan Ummu ni na isa in tsaya mata duk kutashi kubani
wuri,
" Subuhanllahi haba yaya "ya'ya basu hadamu ba jikoki ne zasu hadamu? Don Allah ki
bar wannan zancen mu nemi maslaha kawai,
" maslaha daya ce ku dawo min da jikata yanzu ehem yarinya na da w'anda takeso aka
shiga tsakani Allah kadai yasan Gaskiya ,
"Taja gefen zani tareda goge hawayen ta da kuma sharbe majina,
Ran Dady yayi matukar baci domin Abdullah yanaso ya shigo musu da matsala a cikin
zuri'a lallai zai hadu da shi
Ga ba daya Momy ya kira ya sauke mata buhu buhun masifa sannan yaji d'an sauki'
Sai yanzu yake kara daya sanin Abinda ya aika ta shi kanshi gashi d'an cikin shi
yayi fiye da nashi,
Baban Ruman ke kwantar mai da hankali " Muhammad ka duba fa duk wannan wahalar
Inayin ta ne saboda jin dad'in wannan yaron gashi yanzu haka Asibitin shi Angama
ginawa shi kawai ake jira har ma aikata an tanada da kayan aiki ga J company ma ya
kammala Amma wannan yaron so yake ya kaini ga kunya,
"Yanzu inba zamani ba guda nawa yake ko mu da mukayi Aure Ai sai da muka shekara
Ashirin da takwas zuwa talatin Amma shi yanzu ne yake shiga Ashirin da daya me ma
yasani akan Auren?
" ni kuwa nace um um Dady yaran yanzu sun gama sanin komai bare w'anda ya rayu a
turai,
Momy ba Arziki ta biyo jirgi zuwa nija, Ruman kuwa tana zaune ne kawai zuciyar ta
tayi nisa wurin hango Abun da zai faru wannan karon don tasan dole Hajiya tasan
komai
"A Gaskiya duk KUSKUREN ta ne da tun farko ta fada wa Hajiya da bataji kunyar
Abinda yake shirin faruwa da ita ba a halin yanzu, Tayaya zata fuskan ci Hajiya
yanzu ga ciki a jikinta?A haka yafito cikin falon ya kalle ta ya dade a tsaye yana
kallon y'an da ta fada dogon tunani,
Matsawa yayi kusa da ita tareda zauna wa gab da ita har laps dinshi na gugan nata
yafara magana A hankali,
" Ruman' tayi saurin dawo wa cikin hayya cin ta " Ruman bazaki saki jikin ki dani
ba?
"Ki saki jikin ki don girman Allah ki bani kulawar da nake bukata daga gareki
please ko zan samu natsuwar zuciya ta,
" kallon shi tayi wani iri "Haba Abdul a haka kakeso in natsu? Bayan ni nasan
zuciya ta bata ta taba natsuwa ba muddin zamu zauna a haka wane irin Rayuwa kakeso
mu shin fida?
" Rayuwar Aure mai cike da so da kuma kauna tareda Abinda zaki Haifa min ,
"OK naji yanzu Aure na kayi ' Amma yardar iyayen mu fa? Albar kar Auren da muke
nema dole saida sa Albar kar su "ka mayar dani gida na y'ar da zanyiwa Hajiya
bayani a gaban ka don Allah,
" kallon ta yayi cikin jin dad'i ya rungume ta "tnks my wife gobe zamu je in Allah
ya tashe mu kinji inason farin cikin ki my Queen,
Mikewa yayi tareda dagota cak zuwa cikin dakin " muje kiyi wanka ki kwanta nasan
har yanzu Akwai gajiyar tafiya a jikin ki kuma ga wadda kika tara mana dazu'
"Hararar shi tayi cikin wasa " Bakada kunya Allah' daga gira yayi tareda cewa "
muje ki nuna min inda kunyar take ta fara zulle wa ya riketa gam,
Sai bathroom din da yagaji da haduwa ya direta tareda zame tree quarter din jikin
shi ya jefar ya kuma cire singlet din jikin shi ya tsaya mata zur'
Ja baya tayi tareda rufe idanun ta domin ta fara sabawa da rashin kunyar shi yanzu'
Shi ya kuma matsowa tareda zuge zif din rigar ta yafara kok'arin kwance zanin tayi
saurin bude idanun ta tareda rike hannun shi " meye haka?
"Wanka kawai zamuyi ba komai ba ya furta tareda dage gira daya" OK to ka fita in
farayi kobari in fita inka gama zanyi nawa,
Duk y'anda yaso suyi tare ki tayi saida ya fito daure da towel ta koma bathroom din
tayi nata
"Mai kawai ya shafa tareda fesa turaruka ya koma kan gadon tareda janyo bargo ya
rufe rabin jikin shi domin bai sanya kaya ba,
Ita kuwa zanin ta ta daura tareda goge jikinta da towel tun a cikin bathroom din
saida ta war ware d'an kwalin ta ta fito ta dan shafa mai tareda roll-on kawai
domin bata cika son turare ba a jiki yanzu Sam batason kamshi da yawa,
Komawa gefe tayi bayan ta gama tayi tsaye domin ita dai bata fatan ya kuma taba ta
a halin yanzu koda da Aure bare ita tasan mugun zunubi take aikatawa,
"Ki zo ki kwanta baby ya furta tareda nuna mata kusa dashi bata da zabi domin ta
gaji da maganar ma yanzu
Matsowa yayi tareda shigewa cikin jikinta kamar zai huda ta ya shiga duk ya
cukuikuye ta
." Abdul please " ta fada can kasan makoshi, "me ya faru my Queen?
" bacci nakeji' "to kiyi mana, " a hakan ne zanyi bacci nafa gaji sosai I needs
some rest "kiyi baccin ki ki barni a hakan bazan iya nesa dake ba while you are
close to me,
A haka bacci barawo ya saceta shikuwa shugaban jara babbun sai jagwal gwala ta
yakeyi duk tsumin shi ya tashi Amma yasan da wuya Abashi don haka a wahalce gari
ya waye mai tareda dana sanin hada shinfida da ita domin yaga mugun dare,
Shi yafara tashi saida yayi wanka kafin yayi Alwala ya fito daure da towel sannan
ya tashe ta zanin jikinta ta gani a gefe gashi taji wani iri a kirjin ta domin ba
karamin wuya sukasha ba,
" to wai ita wane irin bacci tayi a daren jiya? Lallai ciki ya canja ta don tasan
shi yasata bacci kamar gawa,
Kallon bayan shi kawai tayi domin mamakin karamin. Yaro da shegiyar jaraba takeyi
Saida tayi wanka itama kafin ta dauro Alwala batada zabi dole ta nemi kaya a cikin
Waldrop don ta gaji dana jikinta
Tsayawa tayi cak domin ta kasa zaben kayan da zata iya sawa duk sunfi karfin ta
take gani dakyar ta Ciro wata English wax ta war ware zanin ta daura tareda sanya
hijab ta tada Salla,
Tana kan daddumar har kusan karfe bakwai na safe sannan ya shigo dauke da tray da
kayan kari kala kala ,
"Ga breakfast my Queen' ta kalli tray din tareda kallon shi sai fara'a yake zabga
wa
Gyara zama tayi domin tana matukar jin yunwa ya hada mata tea mai kauri tareda mika
mata kwai da kuma farfesun naman kaza a gefe tayi luguf
Saida suka koshi ya mike tareda zabo mata wani material less fari kall tareda inner
wears ya mika mata" baby kisa wannan
Kallon kayan kawai tayi domin akalla zaikai kusan fourty thousands kudin shi ya
zabo mata takalmi da jaka bakake tareda labcecen hijabi Navy blue har kasa
Ta fito kamar wata Amaryar Gaskiya da kanshi ya fesa mata turare ya zubawa halittar
Allah ido yana tasbihi a zuciya,
Sannan shima ya shirya cikin farin shadda guntun dinki da kuma bakin cover shoe na
maza ya fito yana sheki da kuma tashin kamshi sun fito gwanin burgewa yana rike da
jakar ta tareda fito da wayar ta ya kunna tareda jefawa jaka
*_to ku biyoni muje Zaria my fan's muji me zaa toya a can Hajiya dai na jira_*
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
3⃣3⃣ 3⃣3⃣
➡3⃣3⃣
Sun fito kamar ka sace su ka gudu saboda haduwar da sukayi ga shi sunyi mugun
dacewa da juna duk da kana kallon fuskar Abdullah zaka hango tsantsar kuruciyar
shi,
Matsowa yayi gab da ita tare da rungume ta a gefen shi ya sauke numfashi " My Queen
kin hadu da yawa fa ji nake kamar kar in barki ki fita don banaso ana kallar min
mata,
Driver yasa ya tuka shi cikin lafiyayyar motarshi shi kuwa yana manne da ita a
bayan mota zuciyar shi wasai sai wani shige mata yakeyi kamar zai koma cikin ta,
"Abdul stop bamu kadai bane fa, ta furta a hankali domin ita Sam batasan wannan
kwakumar da yake mata ga fargaba fal cikeda zuciyar ta batasan me zasu tarar ba'
" Ya d'an sassauta rikon tareda zamewa ya kwanta saman cinyar ta tareda juya fuskar
shi gefen cikin ta ya d'an daga rigar ta kadan tareda kissing din cikinta a
hankali,
Saida ta d'an rintse idanun ta domin ya fara kunna ta da irin salon da yake yimata,
Yakara yin sama da rigar dama suna shiga ciki ya cire mata hijabin rike mai hannu
tayi " Abdul meye haka?
"Na fada maka Akwai driver fa, and so? Ki barni please " kayi hakuri ka daina tunda
bamu kadai bane' yana nishi ya d'an juya tareda riko hannun ta zuwa gaban seat din
su kinji ko Akwai glass baya ganin mu kuma baya jin komai,
"Ina zuwa ma ya d'an na wani Abu wani labule yayi musu katan ga da driver domin
yarufe su gaba daya
" ya kuma juyawa tareda ci gaba da Abinda yakeyi ita kuwa mamakin wannan motar
takeyi don ko a TV bata taba ganin irin ta ba lallai kudi kare zance ne,
Tuni ya birki ce mata sai ya mutsata yakeyi yana birkita mata lissafi hannun shi
ya sanya tareda balle mata bra tana kallo domin ya gama kashe mata jiki ya d'an
rankwafo da ita tareda dora bakin shi akan kirjin yafara tsotsar su kamar zai
cinyesu tuni sun fara mantawa da Kansu ita kanta taima kamai takeyi don harda kara
danna mai kirjin takeyi kamar wani jariri,
Yana fitar da numfashi dakyar ya fara sassauta ta zugen shi ya janyo hannun ta zuwa
kan marar shi Alamar ta yi mai wani Abun ita kuwa gabanta saida ya buga jin irin
y'anda ya koma tsabar jara ba ta fisgo hannun ta
"Kece ai da kin barni jiya daba haka ba, ya furta cikin fisgo Kalmar a haka ya
cigaba saida ya fitar da damuwar shi sannan ya rungume ta gagam yana fisgar
numfashi
Kafin bacci yayi Awon gaba da shi " idanu kawai ta zuba mai tareda gyara jikinta da
duk ya gama ya mutsawa ta mayarda bra dinta tareda gyara zaman rigar ta
Saida suka shiga kofar doka ya farka tareda zama yana kallon tsakiyar idanun ta ya
yi murmushin tsokana " baby kin lalatani fa duk kin samun jaraba,
Hararar shi tayi tareda tureshi kusa da ita " banason rainin wayon ka fa"OK bari
muje ma na fasa zaman Auren zanje in nemi doctor Sulai....
Saurin hade fuska yayi tareda rufe mata baki " Wallahi kika kuma kiran sunan wani
namiji a gabana zanyi miki Allah ya isa,
Saurin kallon shi tayi " mu wuce gidan mu please banza ya mata bai ce mata tak ba
suka isa GRA ya fito tareda zagayowa ya bude mata sannan yayi gaba batareda ya ce
mata tak ba,
"To yau kuma fushi? Hmmm dole ta bishi ciki ruwa ya fara watsawa tareda canja kaya
ya fito ita kuwa tana zaune a falon tana jiran shi
" bakya bukatar wankan ne? "Jaraba ta batakai can ba ta furta a hankali sannan ta
girgiza kai'
" kallon ta yayi domin yaji ta sarai yace muje zaki samu Ansa very soon,
Gidan Hajiya suka nufa yanata kunburi tareda Ayyana irin dibar Albar kar da ya
shirya yi idan har Akayi kok'arin rabashi da Matar shi,
Ba Abinda kirjinta keyi sai bugawa batasan ta yaya zata fuskanci iyayen ta da kuma
kakannin ta ba,
Motar na tsayawa ya fito tareda bude mata gefen ta ta fito ga unguwar a cike da
jama'a daga ganin yanayin unguwar kasan munafukai sun karu tunda ba,kofar gidan
Hajiya can gefen wani d'an karamin shago suka koma da gulmar su ,
Gaba daya kallo ya koma sama lokacin da Abdullah ya bude mata motar ta fito ya
dakko mata jakar ta tareda riko mata hannu,
"Abdul ka sakar min hannu ana kallon mu' dan hararar ta yayi tareda cewa" ko Akwai
saurayin ki a ciki ne bakyaso ya gan mu shiyasa kike pretending?
Fisge hannun ta kawai tayi ta wuce gaba ya biyota batareda ya kula da motocin su
Dady ba dake fake a wurin ba,
Y'an gulma suka d'auka " kai kagani ko baba ai dama na fada maka yarin yar nan
bakaramar y'ar iska bace wato karuwanci tajeyi
"Ai kai b'ab'a infada ma a karuwan cin ne saurayin ya zo ya tare a gidan su har ya
sakar musu kudi ya dauke ta sukaje kasar waje
" kai bakaga bature bane yaron jifa y'anda yake rungumo ta
Kaini Wallahi har ciki na hango Alamar shi a jikin ta "hhhhh kuth bariki tayi riba
Hajiya kaka dole a daina tuwo dasu Alkubus giwa ta fadi
" ni kuwa nace Allah ya tsaida Ku ranar sheda? Mutane basa tsoron Allah sai su rika
maganar da bata shafesu ba Allah ya shirya,
Tun shigar su gaban shi ya buga domin jin muryar Hajiya na balbala fada
"Muhammad idan baku dawon da yarin ya ba duk sai na bata muku rai ku duka,
Gaba daya falon d'an kam yake da jama'a duk sun hadu har ma dasu mama balkisu da
y'ar koranta tazo ganin gulma, wato sopy domin baban ta ya fada mata zancen Auren
Ruman din da Abdullah
Tasan irin yaudarar da,sopyn tayi mata shiyasa ta debota ta kawota don ta bata mata
rai itama don har gobe tana hauka akan Abdullah, har uwarta takewa dibar Albarka,
Cikin karfin hali yayi sallama gaba daya suka dago Kansu harsu magaji da Gwaggo
Amina duk suna falon,
Cikin mutuwar jiki ta wuce ciki tama kasa gaida kowa tafara ziraro hawaye masu zafi
dakuma jin kunya,
" zonan Ummu nasan halinki tunkina karama nasan ba y'anda zaki y'arda da Auren
wannan yaron don haka k'arki damu kanki nasan wannan fitsararren ne mai jajayen
kunnuwan,
Matsawa tayi gab da ita ta samu ta gaishe su shi kuwa dukar da kanshi yayi kawai
tareda samun gefe ya zauna,
"Isashshe ka dawo? Cewar Dady " kaga irin matsalar da kakeso ka haifar mana a
family ko" Abdullah tun muna mu biyu na rokeka kabar wannan Abun ka nunamin kai sai
kayi y'an da kakeso tareda goyon bayan uwarka to ka shirya da ta iso zan bata
takardar ta kuma kaima yanzun nan ka rubuta takar dar Sakin Ruman kabani
Wani irin zabura yayi tareda kallon Dadyn shi jikin shi ya fara rawa'
"Aa karka fara Jafaru dama ita Rayuwa haka take muddin Bakayi biyayya ga nagaban ka
ba to tabbas kaima na bayanka bazasu maka biyayya ba
Kun bakanta mana kuma kunyi y'anda kukeso to suma yayan da kuka Haifa sun fara nuna
muku kaga sakayya kenan
Cewar kaka magaji dake gefe Gwaggo Amina tace hakkun Hajiya kuwa ta yi carab
" nidai Ruman bazata taba y'ar da tayi Abinda zai batamin raiba don haka ka bata
takardar ta yanzun nan
"Kai kuma Jafaru muddin naji koda wasa kasaki Matar ka nidakai ne koba komai kun
hada zuri'a
Isowar Momy yayi daidai da zuwan malam Abubakar wato madaurin Auren su Ruman,
Sun tarbeshi cikin mutunci da karramawa domin malamine mai mutunci a idon jama'a
Hajiya tana ganin girman dattijon domin Abokin mijinta ne tunda kuruciya,
Addu'a yafara korowa tareda bayani hade da nasihohi tareda hadisai da kuma fadakar
dasu illar rashin Auren
" Hajiya Salamatu ba daka nayi komai ba saida na yi istikhara naga Alkhairin Abun
kafin in daura na hango rabo kusa w'anda idan ba Auren aka daura ba barna zata iya
wanzuwa a cikin zuri'a
Abdullah dai na gefen Momyn shi tun Isowar ta da malam ya koma gefen ta don zaifi
jin dad'i don yaga Alamar ba w'anda zaibi bayanshi sai ita,
Bayan malam ya gama bayani Momy ta kalli Dady tareda fara magana cikin turancin
"Ina fatan zaka daina fushi dani jefar ba laifi na bane bansan zaiyi ba sai
zuwanshi America shine yamun bayani
Bayan nan ne na fara yimai gida a Kaduna saboda farin cikin ku gaba daya nasan
kafison kasarka kuma kana bukatar yaronka akusa dakai shiyasa nayimai gida a Kaduna
sannan,
Naji dad'in irin kulawar da y'an uwanka sukayi min lokacin da na fara ciwo duk da
ban kula dasuba sun nunamin muhimncin mutum w'anda ko a Addini na ba akarantar dani
ba
Naji sha'awar kasan cewa a cikin wannan Addini zaman da nayi da Ruman ya karamin
son Addinin domin naga irin dabi'ar da take nunawa tana bani girma duk da da farko
ban nuna mata kauna ba
Al adar ku ta burgeni Jafar tsawon zaman mu dakai baka taba wula kanta niba ka
nunamin kauna wadda sanadiyyar sonda kakemun kabar iyayenka da y'an uwanka ka zabi
zama dani
To ni me zai hana in zauna dakai tare kuma da karbar wannan Addini mai tsarki da
kuma daukaka
Duk wannan bayanin dake faruwa baban Ruman na fassara musu gaba daya jikinsu yayi
mugun sanyi mu samman Hajiya,
Har inda ta tsaya da cewa " Allah is great saboda soyayyar Ruman ga Jeff duk mun
dawo kan hanyar Gaskiya ta kuma kamar y'anda malam yafada tabbas Akwai rabo domin
kuwa Ruman nada shigar ciki a jikinta,
"Ina kasa ta bude Ruman ta shige takeji tsawon rayuwarta bata tabajin kunya ba
irin ta yau tuni ta cure cikin hijabin ta shikuwa wani irin rawar kai yakeyi tareda
farin cikin Momyn shi ta hau hanyar Gaskiya duk sanadiyyar soyayyar Ruman dinshi
yake samun wannan farin ciki,
Malam yayi kabbara tareda cewa " Alhmdulillahi Ala kulli halim to nayi farin cikin
wannan lamari sakamakon wannan lamari munsamu karuwa a cikin Addini don haka ba
Abinda zamuce saidai godiya ga Allah S.W.A
nan take Momy ta karbi Kalmar shahada Dady farin cikin shi yafi na kowa domin ya
Dade yana kwadayin matarshi ta karbi musulunci,
Mama balkisu kuwa jikinta yayi mugun sanyi domin taga masu duniyar ma a hannun su
sundawo hanya bare kuma ita dake takama da Arzikin miji,
Sopy kuwa ai gaba daya tayi saranda tunda taji labarin soyayyar Ruman da Abdullah
Malam ya canjawa Momy suna zuwa Khadija wato suna mai girma da daraja
Dady suka raka shi tareda Alheri mai tsoka duk da yana kin karba saida suka tilasta
shi
Abdullah kuwa ya shigewa Momyn shi Hajiya kuwa mamaki da farin cikine fal cikin ta
"wai Ruman da Aure har ma da guzurin ciki?
Kafin kace me mama balkisu ta mike cikeda sanyin jiki ta shiga kitchen din Hajiya
ta dora girki tareda taimakon Sopy da tasamu natsuwa,
Ita ta shirya lafiyayyun dishes gaba daya ta shiga taitayin ta domin taga karamcin
iyayen mijin nata a fili,
Don ta tabbata badon suba Muhammad da ya saketa sai yanzu ta gane cewa Asiri Aikin
banza ne,
Shi kuwa Abdullah idanu kawai ya kafe ginbiyar shi dasu ganin irin curewar da tayi
saboda kunya yasashi mikewa tareda matsawa kusa da ita,
"Matar Abdullah' ki bude idanun ki haka mana duk su Dady sunfita dagani sai Momy
sai kuma Hajiya domin su Gwaggo Amina ma sunbar falon suna waje suna zance itada
tsohon mijinta,
" yau taga ta kanta wannan yaron ya gama kashe ta ina zata fara kallon idanun
iyayen ta bare kuma Hajiya,
"Munafuka bakyason karamin yaro Amma gashi ya Aure ki a sirri ya saceki kunje can
kinsa kar mai jiki ya d'irka miki ciki bakiji kunya ba sai yanzu ni kutashi a
kusadani,
Wasu hawaye suka fara gangaro mata ta share tareda bude fuskar ta ta kalli Hajiya"
"Wallahi Hajiy.... "Aa Ummu banson jin komai yanzu Amma nayi matukar mamaki da
kika kasa sanar dani Alakar ki da Abdullahi tun farko wato badon malam ba saidai ku
kawo mana shege cikin zuri'a,
Girgiza kai kawai takeyi domin hankalin ta ya tashi da fushin Hajiya "
Shikuwa ko Ajikinshi "Hajiya k'arki fa rikita min mata batada laifi kodaya nine
naja KUSKURE NA ne ba na Ruman ba
Natsuwa ya karayi tareda zama sosai ya fuskanci Hajiya " Kakar mu ki gafarce mu
dukkan mu munyi KUSKURE tun farko yakama ta musanar dake Alakar mu
"Sannan nayi iya kokari na akan Ruman ta bari mu shirya kanmu taki Hajiya inason
Ruman kamar raina A hankali ya war ware mata komai tun farkon zuwanshi Zaria da
gwagwar mayar da yasha da Ruman
" Hajiya tanada taurin kai nayi ta fama saitace wai nayi mata karami to yanzu waye
babba?
Ya fada tareda dage mata gira daya domin tuni ta gama cika da halin Abdullah Saura
kiris ta fashe,
Cikin fushi ta mike tayi dakinta dafe kai yayi "oh ni nashiga uku zan zama mijin
Hajiya
" hhhhh yanzu ma zaka zama Badai kace kaji kagani ba ai w'anda duk yasai rariya
yasan zata zubar da ruwa,
"Wai ni a wane gefe kike ne Hajiya ni ko Ruman? " tashi a kusa dani Abdullahi bana
bayan kowa a cikin ku,
Momy dake gefe tuni ta fara musu dariya domin ta fahimci daukar magana yaron nata
keyi
Mikewa yayi tareda bin bayan ta falon ya zama shiru saidai idanu bamai jin yaren
wani ,
.itadai Momy sai ido sai Shigowar mama balkisu tana dauke da tray da kuma plates ta
fara jerawa cikeda ladabi,
" mama ga Abinci "ita Hajiya Abin ya bata mamaki Matar danta ce ke mata aiki yau?
Allah mai iko,
"Sannu balkisu to kin zubawa mazanku ko? " eh nakai musu can gefen harda baba ma
Gwaggo Amina ma tayi mamaki haka suka hadu suka kwashi garar Abinci har Momy shi
kuwa yana ciki yana famar lallashin ta ta botsare mai.
Fitowa ta kumayi ya biyo bayanta kamar bindi "oh Allah ya kawomu wannan bita zai
zai to kuzo ga Abinci ko kun koshi da soyayya?
Zama tayi gefen Hajiya ta kalli lafiyayyan tuwon shinkafa miyar Agushi yaji namomi
tayi zauna ta diba domin tanason miyar agushin ya sanya hannu cikin plate din ta ba
ruwanshi da kowa
" banza tayi mai taci tuwon ta sosai saidai tana gamaci zuciyar ta tafara tashi don
haka ba shiri tayi waje saida ta Amayar da komai ta wanke bakinta sannan ta dawo
falon jikinta ya mutu duk ta galabaita
Shikuwa ya matukar rudewa gashi ba kayan aiki a tare dashi ga wani zazzabi da ya
rufeta nan take tafara rawar sanyi
Hajiya Kanta ta rude tuni ta jefar da makaman yakin fushinta ta fara tarayrayar yar
jikallen ta
Ba shiri yayi waya tareda bada umarnin akawomai kayan aiki cikin mintuna kadan ya
bata taimako tareda sanya mata drip domin taji karfin jikinta
A ranar dai dukansu basu koma gida ba har Momy gidan kaka magaji ta kwana su kuwa
su mama balkisu suna gidan Hajiya
Abdullah kuwa dakyar ya koma side din da ya zauna tareda baban Ruman donshi yaso
Abarsu su kwana tare
Hajiya ta kwana da ita su kuwa mama balkisu suka kwanta dakin Hajiya ita da sopy,
Washe gari ta tashi wasai saidai tana tashi da Amai tafara saida tayi kamar zata
amaye yan cikin ta kowa ya tausaya mata har iyayen su mazan
Abdullah kuwa duk ya gama rudewa domin daga gani yasan Matar shi zatayi mugun
laulayi kenan,
Kallon Hajiya yayi tareda marai raice fuska "Kaka ku bari mukoma gidan mu zankula
da ita dakyau har zuwa lokacin da lau layin zai d'an ragu,
" saboda gamu mahaukata ko sai mu baka yarinya da lalura kai kuruciya ita kuruciya
kuje can kuta zuba shirme ko,
To ai ma ni yanzu ta dawo kenan sai Allah ya sauketa lafiya ayi bikin tarewar Ku
gaba daya.......✍
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
3⃣4⃣ 3⃣4⃣
➡3⃣4⃣
Wani irin kallo yake jifar Hajiya dashi "Kice muna nan sai mun haihu kenan ?
" ko kuma kubani matata mu koma GRA kinga unguwar ku Akwai zafi kinga ni zan iya
zama Ruman ma haka Amma banaso a haifamin yaro ko amun renon ciki a nan'
"To tatacce ubanka ma a nan aka haifeshi bare Abinda zaka haifa, " kai idan baka
fita idona ba saina ci mutuncin ka,
Mara kunyar banza Mara kunyar wofi, itadai tana kwance kamar ruwa tanajin su ita
yanzu ta kanta kawai takeyi,
Dariya yasa ya fita domin yana da bukatar zuwa gidan su baban Ruman yayi farin
cikin sauyawar Matar shi domin yaso su koma Kaduna da kanta tanemi ya tafi ya barta
idan zai dawo yazo da yaran kawai zata dan tsaya ta kwana biyu a nan,
A cikin kwana kin ba Abinda yake faruwa sai Abubuwan farin ciki domin kan zuri'a r
ya hadu Ruman na samun gata ta ko ina duk da tana cikin laulayi ita kanta tanajin
dad'in ganin irin y'anda y'an uwanta suke kulawa da ita'
Abdullah kuwa yana cikin wani hali domin tun zuwan su bai samu kebewa y'anda yake
so da ita ba iya kacin su falo domin yanzu data shiga dakin zata kulle
Duk ya susuce ya fita hayyacin shi yau kusan satin su daya da dawowa Zaria mama
balkisu ta koma kd gidan yarage daga su sai Hajiya
Da sallama ya shigo cikin falon lokacin tana zaune da ga ita sai daurin kirji domin
wani irin zafi takeji zanin ma jitake kamar ta wurgar dashi
Hajiya na gefe tana mata zuba ya samu wuri guda ya zauna batareda ya iya ko gaida
Hajiya ba ya zabga uban tagumi idanun shi duk sun k'ank'an ce har wani shigewa
sukeyi
Ya zuba mata ida nu gashi da Alama yau jikinta da sauki tunda har take iya zaman
hira
K'irjin ta ya zubawa idanu dasuka kara kunburo wa saboda cikin gashi daurin zanin
yadan zame ta sama yana hango tudun su
Tuni ya kara birki ce wa ya kalli wayar ta dake gefen ta sannan ya tura mata msg
_My Queen please help me Kizo muje can dakin wallahi na mugun matsuwa Kizo ki
taimake ni kar in samu matsala wallahi jiya ban yi bacci ba_
Kallon shi kawai tayi bayan ta karanta ta d'an harare shi tareda kawar da kanta ya
kalle ta tareda marai raice fuska da Alamar roko
Hajiya ta fara magana "yau ko gaisuwar ma bansamu ko hakimi kazo ka tasamu gaba ka
wani zabga tagumi saikace wani ne ya mutu,
" to wa yasani ko magaji ne zai tafi ya bata Amsa cikin gatse " Aniyar ka ta bika
d'an nema saidai Muhammadu ya tafi da Jafaru Amma d'an uwana nanan ba inda zaije ya
barni,
"To naji Kice mata ta taso zamuyi magana, " kaida Matar ka ai gaka gata ke tashi
kije ko ya barmin daki,
Mikewa yayi cikeda farin ciki ya juya jikinshi na b'ari ita kuwa saida ta d'an
bata lokaci kafin ta mike ta sanya katon hijab sannan ta fita zuwa dayan gefen
Sai sintiri yakeyi a cikin dakin har ya tube kayan shi yarage daga shi sai boxer da
sallama ta shiga
Dan tureshi tayi " ni kabarni jikina ba karfi kuma wane sadaki zaka Mora ni naci ma
sadakine nida Sakin jiki sai ka hada komai da Al ada ta gindaya
Don haka kama cire ranka akan zaka samu wani Abu ta juya zata fita yayi carab ya
riketa
"Wai so kike in sumar miki ne don Allah ki Ajiye komai ki Samar min natsuwa wallahi
a mike nake ko fita bazan iya yiba ki kalla fa,
Ta kalleshi tareda kawarda kanta domin inda sabo yaci ta saba da halin shi na
rashin kunya domin ta lura Sam baya jin kunya'
Juya wa tayi tana shirin fita yayi saurin shan gabanta tareda datse kofar ya cire
key din ya wurga cikin dakin ya riko hannun ta
Idanun shi kamar wuta ya zame wandon da hannu daya ya tsaya mata haka tareda cire
mata hijabin ya cillar yasanya hannun shi yana kokarin kwance zanin tayi saurin
rikewa
Fincike shi yayi ya barta haka tayi saurin dunkule wa tareda rufe jikinta da hannu
domin daga ita sai pant kawai'
" wai meye haka Abdul? "Ke kinsan me nakeso don haka ki bani kawai a zauna lafiya,
Dagota yayi cak zuwa gado yafara aika mata da sakonni cikin rawar jiki da zakuwa ya
mugun kamuwa har wani hawaye ke taruwa a idanun shi
Ita kuwa lakwas tayi domin yanzu Sam bata da kuzari a jikinta ko magana wahala take
bata
Juya ta yake yi kamar baby duk ya gama birkicewa ita saidai ido domin batada karfin
tayashi bare kuma hanashi
Cikin minti kasan yasamu isa inda yakeson zuwa saida wani irin Azabar zafine ya
ziyarce kasanta kamar ana sanya mata barkono wata irin Azabar zafi ya ziyar ci
marar ta tuni ta dunkule tareda kokarin tureshi
" Wayyo marata ta furta tana nishi dakyar "Abdul ka bari marata, ta furta cikin a
zaba don ita kadai tasan me taji
Yana fara trusting tayi kara tareda hankade shi cikin d'an saurin karfin da takeda
shi tasanya mai kuka
Wani irin b'ari jikinshi yafarayi don har yafara shawagi a sararin sama niya ta
sakko dashi kasa
" meye haka Ruman kinason kika sheni ne ? Ya furta dakyar tareda kokarin dawowa
jikinta,
"Don Allah ka daina zafi nakeji sosai zaka jimin Wallahi bazan iya daukar ka ba,
" ji yayi kamar yasa ihu " me kike nufi da bazaki iyaba ? Ya kikeso inyi yanzu
kinaso ki cutar dani ne ko me
Shigewa yayi jikinta cikin rawar jiki "k'arki yimin haka Ruman kinsani ina son
kasan cewa dake bazan iya Rayuwa batareda kulawar ki ba Ruman har yanzu ban samu
y'anda nakeso daga gareki ba ki taimaka ki saki jikin ki mu tafiyar da rayuwar
Auren mu cikin kulawa da nunawa juna kauna,
Wasu irin hawaye ne na tsananin bukatuwa ke fitowa daga idanun shi sai rokonta
yakeyi tun yana lallashi har yafara jin haushin ta
Cikin fushi yafara aika mata da sakonni tana tureshi " Wallahi banaso ni ka bari
shikuwa karfi yake kok'arin sa mata
Kiran Hajiya ya tsayar dashi "Ummu kifito kinje kinyi zamanki bayan kinsani ba wai
lafiya ce dake ba to Kizo kinada baki,
Zabura tayi cikin sauri tareda wawurar zanin ta ta daura ta zari key cikin sauri
tareda hijabin ta ta tsere dama tana neman dauki
Tasani sarai yau idan ta bari yayi sai taji jiki bakadan don ita Wallahi tsoro yake
bata yaro karami sai manyan kayan aiki a Gaskiya ita yafi karfin ta,
Dunkule wa yayi yanata faman juyi da dunkule wa a Gaskiya wannan wulakanci ne tayi
mai saida ta fara yafara lasar zumar ta zata fisge mai cokali
Dakyar ya iya mikewa ya sheko ruwa sannan ya nemi magani yasha Amma a banza shi dai
kawai harka yake so yau idan har yanaso ya zauna lafiya,
Driver yakira ya kaishi gida GRA domin yasan Momyn shi na can bai ko tsaya ganin
waye yazo ba ya fita Abinshi
Ita kuwa sai da ta natsu sannan ta shiga cikin falon Hajiya cikin sauri ta karasa
ciki domin jin muryar su hajara suna hira da Hajiya,
" ihu suka sanya kamar zasu fasa falon suka rungume juna Hajiya ta janye y'an
kafafun ta domin gudun karsu take mata y'an kafafun girman,
" Hajiya ai dole Muyi murna wata nawa ba a hadu ba, "to ku wuce ciki duk kun cikan
kunne,
Aikuwa suka kule k'uryan daki suna tayiwa juna tsiya, " kaga Amaryar bature kardai
yaro yayi mugun aiki?
"Kema saikin tanbaya ai dagani babu tanbaya " a Gaskiya yaro yayi Aikin manya wow
bature,
Ai kedai young crush yayi aiki irin wannan d'uri haka ta zabga musu harara
"Ai wallahi duk bakwa kauna ta wai daku aka hada baki aka cuceni wato duk Kunsan da
komai kuka barni cikin duhu ai Nayita tsine muku,
Dariya suka sanya harda tafawa " yo bake kin cika taurin kaiba wai bakya son yaro
bayan kinason abinki gulma ce kawai irin taki
Shiru kawai tayi domin ita kadai tasan y'an da takeji a jikinta
Sun dauki lokaci a gidan saida samy t kira mijinta yazo ya tafi da ita hajara kuwa
sai da tadan kara zama Anan take fada mata ai nasir yayi Aure da cousin dinsu bayan
tafiyar ta itama Auren ta Saura wata biyu,
" to shakiyiya ai sai kuci bayan iyayenku sun hana saika ce sune masu yimin hidimar
da farko,
Har bakin mota ta raka ta a dai dai yana isowa parking kawai yayi ya zuba mata
idanu batareda ya fito ba domin bayason ya fito hajara ta ganshi domin bayan
cikin yanayi mai dad'i,
Itama ta hangoshi sarai batason ya fito don haka cikin sauri ta sallami hajara ta
juya cikin sauri,
Binta kawai yayi da idanu "wato gata sarai da ita Amma da zai zo yanzu Zatace
batajin dad'i
" A Gaskiya yau bazai y'ar da ba don bazai y'ar da ba haka kawai yana da mata
yayita wahala ba bari ya shiga gidan ayi wadda za'ayi yau ko tazo ko shi yaje har
dakin ya kwana sai yaga w'anda zai hanashi......✍
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
➡3⃣5⃣ 3⃣5⃣
3⃣5⃣ A fusace ya shiga cikin gidan , ita kuwa bata
tsaya ko ina ba sai cikin dakinta ta kulle domin tasan sai ya shigo mu samman da ta
San irin rabuwar da sukayi dazu
Tasan halin nacin shi yanzu zai zo ya cigaba daga inda ya tsaya jara babben yaro
kawai'
Wanka kawai tayi ta janyo Agwalimar da ta sa Aka siyo mata dazu domin batajin
dad'in bakinta kwata kwata duk yau bataci wani Abun kirki ba a cikin ta,
Falon ya shigo dauke da sallama Hajiya ta Amsa shi ya zauna "Wai yau Ruman taci
wani Abu kuwa ?
" ina fa tun safe da taci dumamen tuwo kadan tayi amai sai agwalimar da taketa
gabza,
"Meye haka kuma Hajiya? " inafa zaka sanshi wannan Abincin bahaushe ne bana masu
jajayen kunne ba,
"Nidai ta fito inbata Abinci taci kar yarona ya fito a rame " Abdullahi tashi ka
bar dakin nan banson rashin ta ido'
."meye kuma rashin ta ido ? Bakinta taja ta tsuke don tasan hausar sai a hankali,
"Ai gwara kai da uwarka da sai dai mutum yayi zaman kurame da ita ita ba eh ni kuma
ba yes,
Ruman najin dramar su sai dariya takeyi domin ta lura tun a UK ya tsiri zolayar
Hajiya yanzu rainin ma karuwa yake yi,
Mikewa yayi ya tura kofar yaji ta gam ya Kwan kwasa Tanaji tayi mukus,
Wayar shi ya fito da ita daga pocket din wandon shi ya fara dialing number ta,
Tana kallon wayar shima yanajin ringing din daga inda yake tayi biris dashi,
" ka wuce kabar yarinya Tanaji da kanta kazo kana damun ta,
"Kaji Hajiya idan ban dame ta ba wa zan dama? To rasai nayi shiru mai mata,
Komawa yayi kan kujera ya tura mata text msg " ki fito ko in kwana a falon nan,
"Inka fasa Mara kunya ai ga kujera nan bisimillah ko gadona zaka hau ?
" wai meyasa baza kaje gidan su magaji ba saika zo nan ka dame ni can ma ai gidan
kakan ka ne don Allah ka wuce'
"Naji idan har kinaso inbar gidan nan to kiban matata yanzu ba sai gobe ba zan bar
miki gida kai har garin ma idan kasar ma kikace zamu iya bari'
Baki kawai ta tsuke domin ta fara sabawa da halin shi kuma yanzu ma ta fara ganewa
fin karfi da son zuciya da kuma kudi yayi Amfani dashi ya Aure mata jika to ko zata
yi maganin shi,
" kai nama gane Ummu bata sonka fin karfi kayi mata don haka ka kyaleta tunda ba a
Aure dole'
"Hajiya can kika bulla tab Wallahi zakiyi kisan kai kuwa muddin kika raba mana Aure
don a gaban ki zan mutu'
Jin fadan nasu bai karewa yasata dole ta fito tana sanye cikin doguwar Rigar bacci
mai kyau wadda batada tsiraici ta sanyo karamin hijab fari iya wuya ta fito,
Harar shi tayi tareda cewa " Hajiya bakiyi bacci ba ? "Ina ni ina bacci ina tareda
jikokin mayu'
Tuntsirewa tayi da dariya ta kalleshi domin tasan baisan me hakan yake nufi ba
kafin ta matse
Shikuwa shagala yayi tun lokacin Fitowar ta ya zuba mata idanu tareda mantawa da
kanshi da komai
Idanu ya zubawa kumatun ta dake daukar hankalin shi idan tayi dariya
Mikewa Hajiya tayi " ni dai zanje in kwanta saida Hajiya ta shige sannan ta kalle
shi "wai me kake jira har yanzu?
Mikewa yayi tareda nufo ta yana matsowa bai tsaya komai ba ya sunkuce ta zuwa
bangaren da yake zama,
"Ka sauke ni don Allah meye haka? Idan Hajiya ta fito fa? " sai ta ganki a hannun
mijinki dama hakan takeson gani shiyasa ta ajiye ki a nan,
"Wai me yasa Bakada kunya Abdul? " kece sanadi ke kika lasa min zumar da tasa ni
manta meye kunya kuma yanzu dole ki bani inba haka ba tom.
"Tsayar da ita yayi ya zuba mata ido " my Queen me yasa kika canja ?
"Wane irin canji nayi? " ina feelings din ki ya je? Nasan Ruman dina lafiyayyar
mace ce why the sudden change?
"I don't like you like this inason Ruman dina ta ainihi ciki na ne ya cire miki
sha'awa ?
Idan shine bai min Adalci ba Gaskiya, Dukawa yayi tare da dora bakinshi akan cikin
ta
" baby me yasa zaka mun haka ya zaka hana akula da Dadyn ka kayi hakuri Dady na
cikin wani hali
"Bari inje in kwanta bacci nakeji " ni kuma fa ya zakiyi dani ? Haba Ruman wai ke
kina tunanin makomar Rayuwa ta idan har kinci gaba da haka ina gab da gazawa
Wallahi k'arki jefani a halaka,
"As my Age kinsani ina cikin lokaci na I needs you mothern anything right now
please don't punished me by keeping your self a way from me I really wants you,
Duk ya wani marai rai ce mata duk dad'in bakin shi a ranar haka ya kwana batareda
ya samu Abinda yakeso ba yayi kuka har ya gama juyin shi tana gefe domin itadai a
Gaskiya bataso ya rabeta Sam
Gaba daya batajin feelings idan har yace zai tabata haushi takeji,
Yanzu ma saboda batada kunya zata wani kwana tare dashi da safe da wane idon zata
kalli Hajiya'
" tun da daren t gudu dakin ta ta gark'ame yana tashi da safe shirya wa kawai yayi
Ya bar gidan cikin fushi'
Ruman kuwa ta tashi agala baice domin Amai ta kwanayi ba kakkautawa shiyasa ta
tashi duk jikin ta ya mutu dakyar ta iya gabatar da Sallar Asuba,
Ga wata yunwa da ke Azal zalar ta A hakan ta mike zuwa kitchen ta dora indomie
guda daya tareda zuba mata Alayyaho y'anda zata iya ci'
Tun A kitchen din ta fara ci saidai batakai ko ina ba Amai ya taso mata kafin ta
mike ta fara kyaro shi kakarin Amanta Hajiya taji ta fito ta sameta tsamo tsamo
"Subuhanllahi Ummu Amai dai ? Ta sa hannu ta daga ta saida ta raka ta ban daki ta
dawo ta gyare wurin sannan ta koma ta sameta tana nishi sama sama tsabar gala
baitar da tayi,
Cikin sauri ta nufi dakin domin kiran Abdullah Amma wayam baya ciki ta dawo " ke
ina mijin ki? Yazo ya dubaki
Ta girgiza kai Alamar bata sani ba waya ta d'auka ta nemi numbar Dady yana d'auka
ko Amsa gaisuwar shi batayi ba tafara magana'
"Jafaru ka kira danka ya zo Ummu ba lafiya idan baya kusa kuma mu wuce Asibiti'
." Ashsha aa bari yanzu zaizo ina zuwa, yana datse kiran ya kirashi saida tayi
ringing sau kusan uku kafin ya daga domin yana ta fama da kanshi'
Yana dagawa Dady yafara fada' kana ina ne? Dady gani a dakina, "wane dakin ? GRA "
baro Ummun kayi kai kadawo nan bayan kasan tana bukatar ka akoda yaushe? To ka
shirya ka tafi Hajiya ta kira jikin ya motsa'
"Zabura yayi tareda dirowa daga gadon shi ya zura Riga tareda zarar key
Yana tafe yana tunanin maganar Dady" wai tana bukatar shi Hmm shidai ke bukatar ta
Kasan cewar safiya ce hanyar ba wani cinkoso cikin karamin lokaci ya iso banaden
Kayan Aikin shi ya dakko tareda nufar cikin gidan da taimakon Hajiya ta watsa ruwa
mai zafi ta koma kan gadon ta kwanta tana daure da towel ta kife tana maida
numfashi,
"Ki tashi ki saka kayan to kafin ya iso' Hajiya ke mata magana " zan saka Hajiya ba
yanzu ba, bata kara wata kalma ba ya shigo bakin shi dauke da sallama,
"Wato kai tafiya kayi kabar min yarinya da jinya bayan ka hadata da jinya ko wama
yasan me ka mata da ta tashi a hakan don jiya lafiya kalau na barta,
Ta fita tana kan mita kallo kawai ya bita da ido domin bayajin magana yau tana
fita ya kulle kofar tareda Ajiye yar akwatin Aikin shi ,
Ya juyo zuwa gareta ya zuba ma bayan ta ido har yana Ajiyar zuciya " ga kayan
hutawa Amma ba halin mutum ya Mora ya furta a zuciyar shi"
"Ruman ki daina kwanciya a haka zaki jima yarona juyowa tayi a hankali w'anda
dakyar idan bata juya da kwakwal war shi ba domin towel din har zamewa yayi ta sama
har yana hango bakin kansu ,
Jan kafar shi yayi zuwa gadon ya zauna saida yadan natsa sannan ya riko hannun ta
ya rike yaji yanayin ta yana rintse idon shi'
Dakyar yake iya cire hannun shi a duk inda ya taba a jikin ta
" kinyi Amai ne ? Kai ta daga mai "ki bude min baki' harara ta zabga mai tareda
zubowar hawaye tace" ka daina mun fada malam bayan ka cuceni ka hadani da aiki
tunjiya Amai nakeyi Wallahi duk jikina ciwo yakeyi ta karasa tana sharbe,
Tausayi dariya sha'awa gaba daya suka bayyana akan fuskar shi domin koma mai tayi
kamar y'ar shekara goma sha shida y'an da tayi maganar cikin shagwaba,
Bude kayan Aikin shi yayi y fara duba ta " mikewa yayi ya dakko karamin towel ya
jikoshi da ruwa sannan ya dawo ya janyota zuwa jikinshi ya dora saman goshin ta
saboda jikin yayi mugun zafi
Ya fara goge mata har zuwa saman kirjin ta ya zame towel din zuwa kasa tana kallon
shi yafara goge mata ko ina mu samman kirjinta da yafi goge wa har yana gwama
numfashi
"Ya juya ta ya fara goge mata bayan ta yana mai zubawa As dimple dinta ido idanun
shi yana lumshe wa
Saida ya daure ya kai zuciyar shi nesa badon haka ba zai iya reping dinta kuma
yanajin tausayin ta saida ya yi mata Allura tana jikin shi duk ta wani shige mai
ta cukurkude a jikin shi
Koda ya mata Allura zai cire ta kin y'ar da tayi domin kamshin jikinshi ya mata
dad'in shaka bata son ya cireta domin har wani bacci ke daukar ta '
" baby ki bari intashi k'arki ja inyi mugun aiki ki bari in nemo miki Abinda zakici
kinga cikin ki ba komai shiya sa kika galabaita
"Your body is weak Ajiye ta yayi yadan lullubeta ya fito ya sami Hajiya " Akwai
Abinda zata iya ci mai ruwa ruwa ?
"Saidai kunun tsamiya gashi nasan tana son shi' yanzu na dama karba yayi ya d'an
kurba kadan. Yaji tsami'
" Hajiya wannan Abun zai iya cutar da baby na Abinci ne a haka ?
"Uwarka ce ai gwara mu muna da Abincin Arziki ku da ko tuwo babu garinku bani wuri
ni in wuce'
Dariya yayi domin tsokana ce kawai ya wuce ya Ajiye jug din ya dagota " tashi kisha
kallon shi tayi "meye wannan ? Oho Abincin ku ne ta karba tayi murmushi domin taji
dadi ko zataji dad'in bakinta ta kafa kai ta sha sosai yana Kallonta cikeda
tausayi,
Saida tasha sosai ta mika mai takoma zata kwanta ya riketa " nop ki bari ya sauka
kafin ki kwanta,
Kwabe fuska tayi " ni kabarni inkwanta, OK ya matsa kan gadon da kyau ya rungume ta
a jikin shi ki kwanta a nan to
Dama tanaso ta shige kuwa ta kwakume shi "my Queen wannan irin shige mun da kike yi
kinaso mu rabu lafiya kuwa?
"Bacci mai dad'i yayi Awon gaba da ita a kan jikinshi ya kwantar da ita ta kara
rikeshi gam domin tanajin dad'in kamshin,
Haka ya kwanta ya zubawa jikin ta ido yana had'iyar mugun miyau saida ta sakeshi
da Kanta sannan ya mike ya sauko yana hada hanya,
Fita kawai yayi ya bar gidan batareda ya tsaya Sallamar Hajiya ba ya koma GRA
Ya samu Dady na shirin fita ya tsayar dashi " ka shirya muje KD ginin Asibitin ka
ya kammala nama yi ma Abokin ka maganar neman ma Aikata har ya nemo kwararraru
cikin wa inda kukayi karatu a uk wa inda ke nan nija
Yayi matukar farin ciki tareda rungume Dadyn shi yana godiya "Dady tank you so much
Allah ya kara Arziki,..
Shi ma yaji dad'in ganin farin ciki akan fuskar tilon dan nashi " Umm Momyn ka ta
fada min ta gama maka gini har ma ka tare jiya naje nagani tsarin yayi tunda tayi
min shigar sauri na sa An kawo muku sababbin motoci guda biyu kaida Ummu yau zasu
iso
Gaba daya ji yayi damuwar shi ta yaye Jinshi yake kamar ya Goya iyayen nashi sun
gama mai komai a duniya gashi yana tareda farin cikin rayuwar shi har ma tana batun
haifa mai da to shi yanzu me ya rage mai a duniya saidai yayi fatan gamawa lafiya,
Sun shirya cikin sauri suka kama hanyar Kaduna har da Momy domin tanaso taje gidan
mama balkisu don sabo yashiga a tsakanin su
Suna cikin lafiyayyar Hummer jeep din Dady Ak ne ke driving su kuma suna baya sun
sashi a tsakiya tafiya suke yi cikin jin dad'i da kuma farin cikin kasan cewar su
tare,
Gidan baban Ruman suka isa saida suka ci Abinci mama balkisu An canja ta tarbesu
cikin mutunci da girma mawa
Baban Ruman ma yaji dad'i sosai na ganin d'an uwanshi da iyalin shi Abdullah kuwa
yana isowa ya kira numbar Ruman w'anda tashin ta kenan ta ji ringing din wayar tayi
picking,
Murya can kasa yace " my Queen ya kike? Ta Amsa da lafiya "kinji sauki? " eh "to ni
naje KD da Dady kila sai gobe Amma idan Akwai damuwa ki kirani zan dawo a yau komai
dare'
" kin kuma yin Aman? Tace aa OK nasan baza kiyi ba saboda Allurar da na miki tana
tsayar da,Amai kici Abinci please kodan kiji karfin jikin ki baby na ya samu lafiya
shima'
" me kajeyi a can? Murmushi yayi can kasan makoshi "naje neman Aure ne'
Gaban ta ya buga " Aure kuma ? "Eh saboda matata na guduna shiyasa zan kara Auren
ko zan samu kulawa domin nasan bata sona,
" waye yace maka Matar ka bata sonka? Ta fada cikin fushi kamar yana ganin ta " ita
ta fadamin tafi karfi na ni yarone shiyasa zan nemi sweet sixteen a nan KD kuma
gashi ina zuwa na samu
Kinga y'anda take sona Inaga Auren ba zai dauki lokaci ba domin na fada mata inada
bukata sosai don haka ta shirya....
Kit ta katse kiran domin so yake yayi sanadin dora mata hawan jini
Tana zaman ta lafiya jitayi gaba daya ranta ya jagule takasa sukuni kardai da gaske
yakeyi tab ,
Shikuwa dariya yasa har saida Momy dake zaune ta tanbaye shi lfy ? Yace bakomai
Jingina yayi jikin kujera wani irin nishad'i ke ziyar tarshi Ashe haka take sonshi
Amma take jamai Aji
A Gaskiya wurin ya tsaru Dady ya kashe mai kudi sosai an zuba kayan aiki na zamani
Akwai komai na bukata Saura budewa
A Gaskiya ba Abinda zai cewa iyaye nshi sai dai ya bisu da Addu'a,
A ranar a Kaduna suka kwana domin basu kammala da wuri ba don saida sukaje wajen
ginin company Dady
Ruman dai taci ka fam ganin bai dawo ba Aranar wato da gaske wurin mace yaje,
Tun dare take neman wayar shi bata shiga ba lokacin shi yana can tareda mukhtar
suna tattauna y'anda Aikin su zaifara domin har mukhtar yafara tallar Asibitin
trough internet kuma Akwai Alamar nasara akan abinda sukeson gudanar wa,
Shiyasa ya kashe wayar gaba daya bai kunna ba sai kusan karfe goma sha daya yasan
tayi bacci kuma bayason ya tashe ta musammn yanayin da take ciki ba ason tashin
mace mai ciki,
Tun da safe ta fara kiranshi domin duk hankalin ta ya tashi Amma tanata ringing bai
dagaba lokacin yana wanka,
_*Matar Soja najin dad'in comments dinku my fan's keep it up Allah ya bar kauna ina
mugun yinku*_
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
3⃣6⃣ 3⃣6⃣
➡3⃣6⃣
_*kuna cikin aikina inajin dad'in Addu'ar ku a gareni masoyan Asali Alkhairin Allah
ya kai muku da dukkan musulmi a duk inda kuke wato Hafsat Haruna muh'd tareda
takwarata Fenerh dake bango Abin jingina ta wato mom Sayyed ina matukar godiya
comments dinku na sani nishad'i*_
Saida ya fito ya shirya sannan ya dauki wayar domin kiranta Amma yaga miss calls
harda text msg Abin ya bashi dariya sosai saida ya d'an dara sannan ya jefa wayar
cikin pocket ya fito domin zai je ya sami mukhtar,
Su Momy su ba yau zasu koma ba gaba ma zasu yi don commitment dinsu nada yawa
saida yaje gidanshi ya dauki motar da Aka kawo musu sabuwa
Karamar ya hau somin yasan itace ta Ruman motar kirar Prado tayi matukar haduwa shi
kanshi ta burgeshi sosai yasan zata dace da Queen din shi gata fara dal
Yana yin packing mukhtar na fitowa tareda kanwar sa mubena zasu fita ganin
Shigowar sabuwar motar yasashi tsayawa domin ganin waye,
Ganin Abokin shi ne yasa shi cewa kaga d'an gatan Momy da Dady ya fito cikin
shigar shi ta kananan kaya farare kamar kullum wandon shi tree quarter da kuma T-
shirt wadda Akayi ma rubutu da golden An rubuta proud da manyan harafi a bayanta
da kuma gaba
Ga facing cap dinshi da sumar shi ta fito tana sheki ta baya glass din idon shi
kuwa ya mugun kara mai kyau da kuma class kana hangoshi zakasan Akwai duk abinda
ake bukata Arayuwa
Hutu kudu kyau da kuma kwanciyar hankali kuma Bazaka taba tunanin ya Ajiye mace ba
couse yana cikin lokacin shi saboda yanzu ya ke cikin shekara ta Ashirin da biyu
Idanu mubena ta zuba mai tun Fitowar shi ya tafi da ima nin ta "wow he is dam
handsome, ta furta a zuciyar ta
" yaya waye wannan? ta tanbaye yayan ta " Abdullah J da kikaji ina fada Abokina
dake UK
Isowar shi yasa shi yin shiru tareda rungume shi suka tafa kuma
Yi yayi kamar bai gan ta ba domin ya lura da irin kurutai datayi mai shi kuma ya
tsani mace ta rika kallon shi
"J ga cousin' sister na da nake fada maka mubena d'an kallon ta kawai yayi ya
mata na bature " hy y kk? Tace "Am fine harda kashe murya,
Ya basar " nifa zan tafi inada uzuri Kasani yafada cikin sigar dariya "eh nasani A
sauka lfy ni daga nan idan na Ajiye ta zan koma Asibiti inga meke going domin na
fada musu mun bude namu su shirya rasa ni a nasu " to sai munyi waya '
"Karka rainan hankali sai yaushe zaka dawo? " sai ka ganni kasan bazan iya nisa ba
da kusa da gida ana bukata ta a kusa dole in tsaya,
"Amma karenan hankali " OK nima dai zanyi lamarin nan inji me kk ji ya fada tareda
kallon mubena ya sakar mata murmushi ita kuwa ta wani tsuke fuska tareda zubawa
Abdullah ido
Juyawa yayi domin ji yayi Yama fasa Abinda ya kawoshi dole ya nufi zazzau yanzu ga
kuma wannan mai kalar kazar mayun ta zubamai na mujiya,
Motar ya fada sannan yace "sai munyi waya ya fisgeta yayi waje Abinshi ita kuwa
cikin salon ta don dagani an waye ta ce " baby muga wayar ka mana,
Mika mata yayi tareda d'an matsowa "ai ko Kaina kikeso zan baki bare wayata ta
karba tareda waskewa ta fara duba numbar Abdullah,
Saida ta kwashe sannan ta mika mai gashi na fasa shi dai gaulan ya shagala yana
kallon kyakkyawar yarinya domin yana matukar son ta sosai Amma ita a ganin ta tafi
karfin shi sai kuma gashi taga Abokin shi taji duk duniya shi take da muradi kuma
insha Allahu sai ta mallake shi'
Karfe goma tayi mai a kofar gidan Hajiya ya fito cikin takun shi ita kuwa lokacin
har wani zazzabi ya rufeta tsabar sama zuciyar ta damuwa da kishi
Jin kamshin turaren shi tareda sallama yasata Ajiyar zuciya da kuma zirarowar wasu
hawaye masu zafi na kishi ta kara dunkule wa a gadon ta,.
" Hajiya ce kawai a falon tanajin redio ya gaishe ta ta Amsa tareda korafi
Kaidai ka zama kudi ko ina Akwai ka idan Katashi tafiya baka sallama to naji Abin
Alkhairi Allah yasa Albarka ya sa ku fara a
Yace Ameen tareda gyara zama batareda ya tanbaye ta ba wayar shi tayi kara,
Ganin makuwar number kuma ga shi yaga sunan mubena true caller ya fara mamaki wace
ce haka? Saboda shidai baida numbar wata mace bahaushiya bayan Matar shi '
Kin d'auka yayi saida ta kuma kira kusan sau biyar kafin yayi tsaki ya daga "hello
ta kashe murya a can dayan gefen
" hy handsome, "who please? Mubena, " mubena? Ya tanbaya cikin rashin ganewa
"Kanwar Abokinka mukhtar na karbi numbar ka saboda murika gaisawa ina fatan ba
damuwa?.
Har zai bude baki yayi magana yaganta a tsaye akan shi tana mazurai wai gawa yayi
yaga Hajiya ta tashi yayi murmushi tareda basarwa
Yaci gaba da wayar shi " nop ba damuwa nagode mubena sai nadawo KD ko ? Bye, ya
kashe wayar tareda mikewa yayi waje tabishi a baya domin batason Hajiya taji su,
Dakin da yake sauka ya shige yasan zata biyoshi yana mai Sakin murmushin kyeta
yana shiga ya zame wandon jikinshi ya cire wando ya rage daga shi sai singlet da
short nicer yayi kwanciyar shi tareda daukar waya
Shigowa tayi cikin fushi tareda kulle kofar ta matso gab dashi ta tsaya tana cika
yayi kamar bai ganta ba,
"Abdul wane irin Abune haka ka tafi na fada maka banda lafiya kadawo ko kadamu ka
nemeni duk haduwar da kukayi bai ishe ku ba shine har a cikin gida kana daukar
wayar ta,
Ta furta cikin kuka saurin tashi yayi zaune " yanzu me nayi miki kuma ? In kula ki
Kice nayi miki rashin kunya ita da ta damu dani har kirana takeyi
Rai ma nason mai kyauta ta mai don haka na kyale ki ki huta bazan kuma damun kiba
zanje in Auri macen da zata bani kulawa
Fadawa kawai tayi kan jikinshi tareda sa mai kuka ta rukun kume shi yayi saurin
riketa "meye haka Ruman zaki jamun Asara ne ? So kike kijima kanki kijima yarona
please ki kiyaye ki daina faduwa irin haka,
" to ai Kaine kaja wacece ta kiraka ? Itace kaje wurin ta ko? Dariya taso bashi
domin batada wayo tunda ta kasa boye kishin ta " eh tana tanbaya ta ne ya na iso ?
Zabura tayi ta tashi zaune ta zuba mai idanun ta da sukayi ja saboda kuka "kana
sonta?
" uhm ai dole zanso ta tunda tana bani girma kuma tayi min Alkawari zata bani
kulawar da nake....
Hade bakin su tayi cikin sauri domin taji zuciyar ta na shirin faso kirjin ta
tafito tsabar kishi tafara bashi kiss mai ban mamaki harda mugunta take tsotsar
bakin da ke kiran sunan wata macen shi kuwa tuni yayi suman wucin gadi domin irin
cafkar da take kaiwa harshen shi tuni notukan kanshi sun kwance
Ya zama kamar gawa tuni ta birkita shi da mu gayen kisses dinta hannun ta tasa ta
zame rigar shi sama tana shafo kirjinshi mai fadi tareda laushi kamar na mace
Cikin salon ta ta dora hannun ta akan nonon shi tana shafawa cikin wani irin salon
da ya dimautar dashi tuni ya fara Sakin nishi
Sama sama ya riko kugunta tareda zame hijabin jikinta yaganta daga ita sai pant da
bra kawai
Zuba mata idanu yayi cikin Alamar tanbaya " ba haka kakeson gani ba shiyasa na zo
maka a hakan ta fada cikin dukar da kanta,
Dago habar ta yayi cikin murmushin shi domin yasan duk me ya janyo hakan
Ya zubawa kirjinta idanu tareda zame hannun bra din duka biyu suka bayyana awaje
saida ya kusa shidewa ganin y'anda suka mike yasanya hannun shi zuwa kasanta ya
zame pant din ma gaba daya tareda dora bakinshi zuwa kunnen ta " haka nakeson ganin
ki necked
Kwantar da ita yayi ya fara aika mata da sakonni masu wuyar fassara wa tuni suka
birkicewa juna duk da bataso Amma yakaita limit din da bazata iya gaddama ba
Lokacin da Alkalamin shi ya hau Allo kuwa dif ta dauke domin taji shi har cikin
kwakwal war kanta tuni marar ta ta d'auka shi kuwa har wani daukewa numfashin shi
keyi tsabar Jinshi da yayi a cikin kogin Zuma har ma da mad'i yana linkaya
Wani ihun dadi kawai yake saki ita kuma tana ihun wuya "please my Queen don't
punished me again k'arki kuma hanani kanki don Allah zan iya mutuwa nasha wuya
sosai ki daina guduna kinji'
" ita ina bata jin shi kuka ma takeyi domin bata jin dad'in sex din sai Azaba
haka yake ta murza ta son ranshi kamar injin yana kukan dad'i tana na wuya saida ya
galabai tar da ita sannan ya saurara badon ya koshi da ni imar ta ba '
Ya mata wata irin wa wuyar runguma tareda jin kamar ya mayarda ita cikin ciki
Ita kuwa dunkule wa tayi domin marar ta tayi mugun rike mata saida natsuwar shi ta
dawo ya lura da yanayin da take ciki cikin tsananin tashin hankali ya mike zaune
tareda rungumo ta
"My Queen lafiya ? ta na dafe da cikin ta hawaye na zubowa a idanun ta yayi saurin
dirowa ya janyo towel ya daura
Ya kwashe ta saida ya kaita bathroom ya lura da irin jinin dake fitowa ta kasan ta
ya mugun firgita
Cikin sauri ya shirya tareda janyo kayan aiki yafara dubata Amma Abin ya ci tura
tuni yafara tsorata da lamarin don haka bai tsaya bata lokaci ba ya fito ya nufi
dakinta batareda ya kula Hajiya ba ya dakko mata kaya
" lafiya nagan ka a ujule ina ita Ummu n take ? Ko sauraran ta bai tsaya yi ba ya
koma ta sanya mata kaya sannan ya nufi Asibiti da ita
Domin dole sai An duba ta don baida kayan aiki a gida da a KD ne sai ya kaita
Asibitin shi har ya dagata tace ya Ajiye ta zata iya tafiya cikin dauriya ta ke
maganar domin marar ta na mugun murda mata
Suna fitowa Hajiya na fitowa "lafiya Ummu ? marata ke ciwo ' wani irin kallo ta
jefeshi da shi " me yasame ta? Lafiya lau take
Shidai baida lokacin ta kawai sunkutar ta yayi ganin surutun Hajiya zai iya jamai
hasara
Saida ya shigar da ita mota sannan ya shiga ya fisgeta batareda ya saurare ta ba
Wani private hospital ya nufa da ita mafi kusa bai jira komai ba ya shigar da ita
Likitan ya karbesu cikin sauri ya fara tanbayar shi kayan dayake bukata yabishi
shi da ido
Saida ya nunamai I d dinshi sannan ya basu daki tareda nunamai kayan Aikin da yake
bukata cikin lokaci kadan yayi nasarar tsayar mata da jinin tareda bata Allurar
Hutu Likitan na kallon kwarewa
Karamin yaro da irin wannan baiwa domin Anan Nigeria da wuya mace mai ciki karami
ta fara zubar jini kaga likitoci sunyi kok'arin tsayar dashi sai dai suyi kok'arin
wankeshi
Kuma gashi suna da kayan aikin Amma rashin goge wa akan Aikin yasa basu San Amfanin
shi ba
Sunyi matukar jinjina mai sannan sun nemeshi da ya taimake su akan Aikin da ya
shige musu duhu ya kuma Amince domin suntai makeshi
Amma ya fada musu su bari Matar shi ta farfado yaga yanayin ta kafin ya iya
taimakon su domin hankalin shi ba ya jikinshi
Sai da ta dauki hour biyu kafin ta farfado ta bude idanun ta ta zubasu akanshi yana
zaune ya zuba mata ido kamar za a sace ta,
Saurin matsawa yayi tareda rike ta ya dagota "sannu my Queen ya jikin marar ta
daina? Kai kawai ta daga mai tareda tanbayar shi ruwa,
No bazaki sha ruwaba sai kingama shan na Leda, sai da ya fada ta kalli hannun ta
tagan shi daure da ledar ruwa ya kusa karewa,
" sorry baby nine naja ko ? Gashi har Natashi jama Kaina Asara
Saida ruwan ya kare sannan ya cire mata tareda cewa bari in mayarda ke gida indawo
zanyi wani Aikin ,
Yana rike da ita ya fito har wajen motar ya bude mata tashiga tareda mamakin shi
kullum cikin canja mota yake kamar mai K'era su ga wannan tayi masifar yi mata
kyau
"Kinga motar ki naso in miki surprise sai gashi kinganta Dady ne ya siya mana shine
nazo miki da taki,
" ta kalli cikin motar ma Abin burgewa ne ta d'an cije domin tana d'an jin zafi
kadan a marar ta tace nagode Sosai Amma tayi kyau
Ya riko hannun ta daya yana murzawa "ai bata kaiki kyau da haduwa ba you are the
best my Queen kin hadu ciki da waje Saura kadan ki hauka tani dazu kinsani ina
sanbatu mema nake fada ne wai?
Saida ta d'an dara kadan sannan tace " bansani ba nidai bayan kajimin har kaja mun
zuwa Asibiti kissing hannun ta yayi tareda cewa sory my Queen kece Akwai Zuma,
Hajiya sai sintiri takeyi tun fitar su takasa zaune saida suka shigo tace " wai
meke faruwa ne ? Kun ajiyeni kamar zan samu hawan jini kuntafi kunbar ni,
Toh gamu mundawo kije ki kwanta kar kiyi wani aiki domin kina bukatar bed rest idan
kinyi wani Abu mai wuya zaki iya mun Asara ko Alwala zakiyi ki fadawa Hajiya ta kai
miki buta
Yana fada ya juya cikeda dariya ya fita kafin ta fara ai kuwa tafara balbala mai
bala'i
"Ai fa ba dole ba kazo ka zunguro yarinya tana fama da kanta shine zakazo ka kafa
min dokar iya shege zaka dawo kasa meni shakiyin banza
Itadai sum sum ta wuce dakin ta domin wani irin bacci takeji shikuwa Asibitin ya
koma domin cika Alkawari n da ya d'auka
Ya samu Ankawo wata emergency tana lebour gata tana bleeding cikin sauri yafara
bata taimakon gaggawa saida ya samu nasarar fito mata da yaron kafin ya fara
kokarin tsayarda jinin cikin ikon Allah ya samu nasara Likitan yayi matukar
jinjina mai a haka ya taimaka ma mata da dama a Asibitin
Sai kusan magrib ya dawo gida bayan ya biya ya musu odar kaji da kuma Abinci mai
dad'i daga shagalinku restaurant
Ya nufo gida ya same su suna hira ya Ajiye tareda kallon ta y'anda tayi dai dai a
gaban Hajiya tana faman cin zogale
" meye wannan Abun kuma ? "Ai fa to Abincin mune na malam bahaushe sai ka kalla
kawai
Janye kwanan yayi sannan ya tura mata ledar da ya shigo da ita " ga Abincin da ya
kamata kirika ci domin lafiyar baby na
"Kaji min iyayi da can kai kake bata Abincin da takeci sai yanzu zaka kawomin
sanabe kai tashi kaje ma magaji na neman ka yace yakiraka yafi sau goma bata shiga
ba,
" oh na kashe wayar ne ina aiki' aiki ka fara? Aa a nan ya mata bayanin Abinda ya
faru taji dad'in jikan ta yayi taimako tayi ta sa mai Albarka tareda janshi da
hira
Dakyar ya kwaci kanshi domin yana bukatar wanka kallon ta yayi cikin wani irin
yanayi domin ta tafi da tunanin shi'
Tasan me yake nufi don haka ta fara mikewa ta nufi hanyar waje yabi bayanta da
kallo tana sanye da Riga da sket na Atanfa tayi matukar yin kyau,
Tashi yayi tareda cewa Hajiya " bari inyi wanka kakar mu, zandawo hira domin inaji
dake sosai,
"Kaji dashi gulmamme ko ince gulmammu kaida munafukar matarka dariya kawai yasa ya
fita domin Hajiya batasan meyasa take Sakin jiki da shiba yanzu,
Da sallama ya isa cikin dakin Ya Ajiye ledar da ya dakko ya kalleta wani iri " bari
in watsa ruwa sannan ya wuce yana shiga wayar shi tayi kara
Ta kalli screen din wayar domin tana kan table dinda ke gabanta
Daga bathroom yace "waye? Tayi mai banza tareda mikewa ta fita dakin koda ya fito
yaga wayam
Wayar ya d'auka ganin wadda ya takira yasa shi buga tsaki tareda cewa headache
domin tafara damunshi sosai
Bai kaiga Ajiye wayar ba ta kuma kira dagawa yayi tareda tsuke fuska kamar tana
ganin shi
" hello " hy "y kk ? " lfy kawai yace "ya dai kinkirani kuma?
" Wallahi inason ganin Kane shiyasa nakira domin inji yaushe zaka shigo KD?
"Ba rana ' OK to zan shigo Zaria ni gobe idan ba damuwa kit kawai ya kashe wayar
shi domin ya lura ta samu tabin hankali haka kawai me zata yimai takeso tazo wajen
shi?.....✍
Masu neman Complete din Littafin sai su taba bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton
domin sauke cikakken Littafin a cikin wayoyinku na hannu 👇👇👇
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
3⃣7⃣ 3⃣7⃣
➡3⃣7⃣
Yayita zuba ido yaga dawowar Ruman Amma shiru, a dole ya mike ya koma zuwa dakin
falon ya samu tsit Alamar Hajiya ta shura ya tura dakin ya sameta a kwance ta kife
ciki tana shashshekar kuka,
Saurin karasa wa yayi "subuhanllah Ruman meke faruwa yazaki kwanta a haka k'arki
cutar da Babyn dake cikin ki fa,
Ya matso tareda dagota ta zuba mai idanun ta " waye mubena? Kallon ta yayi tare da
murmushi domin yagano dalilin kukan
"My wife to be' ya bata Amsa atakai ce, " oh itace Karamar Yarinyar ko? Shiyasa ka
juya min baya saboda zaka Auri under sixteen ko,
Allah sai ya saka min tun farko wayace ka shigo Rayuwa ta idan kasan cewa ni nayi
maka girma meyasa zaka cutar dani meyasa baka barni na Auri dai dai dani ..
Saurin rufe mata baki yayi tareda hade rai ya matsa gab da ita " k'arki kuma furta
Kalmar Auren wani " zuciya ta zatayi bindiga kinji y'anda naji kuwa,
"Ruman dama tun Asali ke tawace nine zan mallake ki ina sonki fiye da kaina ina
matukar kishin ki Ruman ni kadai na can canci zumar ki
Ki duba irin wurin da nayi Rayuwa bai sa na lalace ba ban taba kusan tar wata ya
mace ba sai akanki kece zumar da na fara d'an dana banajin zan iya yin nisa dake
koda na minti daya ne sai dole,
Ruman yakama ta Ace Yanzu ina bakin aiki kinsan cewa Dady ya gama gina min Asibiti
na inaso kisamu karfin jikin ki ne dole in koma Kaduna infara aiki na kodan iyali
na,
" ko kinaso in zauna akoda yaushe iyaye na namin hidima kinga zanfara ajiye yara
dole in dage in nema musu da zufa na y'an da zasuyi Alfahari dani kamar y'anda nake
Alfahari da iyayena,
Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta kuma kallon shi " yaushe zaka koma KD ? Sai naga
yanayin jikin ki kinga Hajiya ta dage sai kin haihu zaki tare gidana
"A Gaskiya tayi min shiga hanci Hajiyar nan ni kibini kawai mutafi tunda ai kowa ya
shaida ke matata ce yanzu'
" aa sai lokaci yayi sai kayi komai da Akeyi a al ada "meye shi da akeyi Banyi ba
ya fada tareda Jan hancin ta 'na Riga na cika aiki har ma result ya fito to me ya
rage ?
" lefe biki "kin manta da irin kayan da natanadar miki me zakiyi da suturu kuma ?
OK k'arki damu duk Abinda kikeso za ayi Amma ki bari idan za ayi na mubena sai ayi
biyu harda naki
.yana karasa fada ya diro yana guntse dariya filo ta jefeshi dashi ya fita da
gudu yana mata dariya sakko wa tayi domin binshi don tana muradin cin wani Abu
domin yunwa take ji,
Saida ta watsa ruwa sannan ta nufi dakin sanye da Riga da wando na bacci rigar mai
siririn hannu ta sameshi ya baje yana cin Abinci zama tayi a gefen shi
Zuba mata idanu yayi tareda janyo ta zuwa jikinshi " ya fara bata naman kadan kadan
ta danci ba laifi sannan ta tashi ta wanke bakinta ta janyo Agwalimar ta tafara
tsotsa gudun tashin zuciya,
Saida ya gama sannan ya kwashe sauran ya zuba a mini firij din dake dakin sannan
ya wanko bakin shi ya dawo ya janyo ledar magani ya ballo ya mika mata
"Ki rika shan magani akan lokaci na lura bakyason magani kodaya baku sha ba nagani
Ya mutse fuska tayi " zanyi amai idan nasha banason warin shi,
Baza kiyi amai ba yanzu na tsayar dashi ko kinji tashin zuciya bazai zoba
Karba tayi ya bude mata gorar ruwa Mara sanyi ta sha sannan ya ce kwanta inga
lafiyar Ajiya ta,
Harar shi tayi ta mike ni zanje inkwanta dama yunwa nakeji "oh kina nufin tafiya
zakiyi kibarni?
" kije to bari inkira mubena Muyi hira saida safe ya furta tareda daukar wayar shi
ya juya mata baya,
Zama tayi a kusa da kafafun shi har saida ya mur musa "to me zanyi maka kasan fa
banda lafiya,
." Niko nasani ya zabura tareda cire singlet din jikin shi ya jefar tareda janyo ta
" ke sai kitafi haka kawai kibar ni bayan nayi ido biyu da kayan dad'i na kalli
y'anda suke min kwale le,
Ya furta tareda dora fuskar shi akan kirjin ta da rabin su ke waje ya fara lasa
har saida tsigar jikinta ya fara mikewa
Ta d'an zame "banfa warke ba, dagowa yayi tareda kallon cikin idon ta " jinin bai
daina zubowa bane ? "Eh
Zaro ido yayi tareda kwantar da ita " mugani saurin rike mai hannu tayi ta waro ido
me zaka gani?
"Wurin da jinin ke zubowa zanyi yanzu inyi maganin Abun " don Allah ka bari "dariya
yasa matsoraciya kawai sai cika baki da son girma bayan ke din ma yarinya ce d'an
ya sharab,
" naji na y'ar da ni dai kabar ni intafi kar Hajiya ta gane ina nan, to sai me
mutum da Matar shi
Cire mata rigar yayi ya cillar dama rigar ce kawai a jikin ta ya zubawa na shanun
ta ido "wow kullum kara kyau sukeyi baby na na gyara min kayan dad'i na,
Ture hannun shi tayi " ni kabar ni intafi'
"Zaki iya tafiya kibarni haka ? kinsan fa hakuri kawai nakeyi nake kwanciya nikadai
Amma a Gaskiya yau bazan iyaba ki kwana a nan ko muje dakin ki, kallon shi tayi "
zaka iya kwanciya a dakina? Mezai hana muje kigani "
"To ni inada kunya har yanzu " ni naji banda ita kuma yanzu zan nuna miki "
Bakin shi yasa akan k'irjin ta yafara yi masu wani irin tsotsa, tuni ntwk dinta ya
tsaya cak saboda jin irin salon da yake binta dashi,
Ganin yana kok'arin kauce wa tayi saurin dakatar dashi " Abdul banda lafiya fa' "I
no bazan wuce hakan ba kibarni insamu natsuwa kawai,
A haka ya gama jarabar shi ya kyaleta domin taki bashi gudun mawa don kar yace zai
zarce hakan saida ya mike ya shiga bathroom ta sulale ta gudu itama saida ta fada
ta watso ruwa tareda zubawa kirjin ta idanu ta dan karamin madubin dake bathroom
din,
A Gaskiya Abdul karshe ne wajen fitina kalli y'anda ya sa k'irjin ta yayi jajur
tsabar matsar da suka sha,
Saida ta dauro Alwala sannan ta dauro towel ta fito idanun ta a waje ta zuba mai
ido domin ganin shi yayi dai dai akan gadon ta
" me kakeyi Anan Abdul? "Me kika ga inayi a nan? " Don Allah ka tafi Abdul kar
Hajiya ta ganka,
"Ai sai kiyi Kizo kawai mu kwanta ni bazan kwanta nikadai ba bayan inada mata muna
gida daya saboda ke fa nake nan gidan Amma kina korata to bazan fita ba,
Batada zabi dole haka ta hakura ta yi Salla sannan ta sha maganin ta ta haye gadon
gefe ta kwanta ya mirgino tareda rungume ta gam cikin jikin shi
Baccin su sukasha mai dad'in gaske basu San lokacin da gari ya waye ba jin kiran
Hajiya yasa ta bude idanu ta ware su akan fuskar shi bai ko San tanayi ba baccin
shi yakeyi hankali kwance,
" zabura tayi ta d'an bugeshi kadan ya bude ido "Abdul kagani ko yanzu ya zamuyi
gashi munyi lattin tashi har Hajiya ta fito '
Duk tayi tsuru tsuru kamar wadda tayi karya " tashi kawai yayi tareda dirowa ya
sanya rigar shi da ya cire ya nufi hanyar fita tayi saurin shan gaban shi
"Fita zakayi ta ganka? " eh to kwarto ne ni da zan tsaya labe labe bakin ta sake ta
ke kallon shi ya fita Hajiya na kishin gide tana lazimi
"Barka da Asuba Hajiyar mu' tsayawa tayi cak da Abinda takeyi tana mamakin wai a
nan ya kwanar musu ko me,
Yana kokarin fita falon ta tsayar dashi " Abdullahi ya dawo "na am hajjo " rasa
kunya Badai a nan ka kwana ba?
"A nan ne mana Akwai laifine? " babu d'an ubanka Mara kunya yanzu ko kunyar idona
bakaji ba zaka kwana a nan,
"Kiyi fushi kawai ki bani matata yanzu mubar miki gidan ki ba bata lokaci
" ai kuwa duk rashin kunyar ka bazan baka itaba kuma yau sai ka bar gidan nan sai
famar taku rawa yarinya kakeyi ina Ankare jiya har kusan barar da cikin kayi tsabar
fitinar ka,
"Wai ke Hajiya meyasa kike cewa nine mai laifi itafa tace inzo intaya ta bacci
tsoro takeji"
"Carbin hannun ta ta jefa mai tafi d'an nema oh ni salame ' yau naga zamani'
dariya yasa ya fita Abin shi saida ya yi wanka sannan yayi Salla domin lokaci ya
tafi
Itadai tama kasa fitowa saboda tsabar kunyar da Abdul ya sanya ta tunda tayi Salla
ta shirya komawa tayi tayi kwanciya r ta duk da tanajin yunwa,
Saida Hajiya ta shiga tace " oh ni Ummu wannan marar kunyar yaron duk ya canja min
ke yanzu ni kike jin kunya lallai,
"To fito ga dumamen da kikace zakici yau na dumama miki ga kuma kunun tsamiyar nan
duka,
Ba tada zabi dole ta fito domin yunwar na azal zalar ta ta murje ta kwashi Abinci
Cikin shirin shi ya shigo falon yan zuba kamshi cikin wani milk colour material na
maza mai kyau da kuma tsada ya mugun haduwa ya zauna kusa da ita,
" toh Hajiya ni zan tafi KD zamu fara aiki an fara kawo patients sati mai zuwa zaku
zo bikin budewa ku duka kafin in tafi zan biya gidan wa incan tsoffin
"Toh Allah yasa afara a sa'a , Ameen " kallon Ruman yayi "madam zantafi ga makullin
motar ki bance kije yawo ba idan zakuzo zanyi ma Ak magana ya hadaku da driver ya
tuka ku
Yasa hannun shi ya shafo cikin ta tareda dora mata kiss a,goshi ya mike ya zaro ATM
ya Ajiye mata idan kina bukatar wani Abu Akwai kudi a ciki sai kunzo,
Zuba mai ido kawai tayi domin ya matukar burgeta har tanajin kishin fitar da zaiyi
a haka
Kamar ta tsayar da shi takeji key din motar ta nuna wa Hajiya tasanya Albarka "
Mahakurci mawadaci Ummu Allah yasa Albarka,
Sai mun shiga d'ani "ai ko yanzu ki shirya muje gidan su kaka magaji, to sai Anjima
yanzu ki gama cinye Abincin ko,
Matar likita gashi laulayi ya tsaya cak Abinka da masu Abu, dariya kawai tayi domin
ita Kanta ta y'arda domin irin magun gunan da ya ke dirka mata,
_"I Always tink of you,but I always fail to know the reasons why.is there something
else I should know about you? But there is one thing that I know is true. That life
will always be sad without you._
_" caring for someone is easy but making someone care for you is hard. now I keep
wandering how did you make it so easy for me to care for you' I love you so much_
Text msg din ya matukar tafiya da ita har batasan lokacin da t aika mai da simple
reply ba,
Murmushi yayi kawai domin ganin reply dinta yana tuna moment dinsu da ita a
hankali ya furta,
https://aihausanovels.com.ng/novel-document/kuskure-na-complete-novel-by-fenerh
👆👆👆👆👆
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
3⃣8⃣ 3⃣8⃣
➡3⃣8⃣
Ya isa Kaduna lafiya gudan shi ya fara wucewa ya sameshi tsab domin Akwai ma Aikata
masu kula da gidan akoda yaushe
Bedroom dinsu ya fara shiga ya zubawa gadon su ido domin tuno da ranar da suka
kwana a kanshi duk da bawai wani morewa yayi ba Aranar Amma bazai manta da moment
din ba how he wish a ce yanzu ma tana zaune a cikin gidan shi da yafi kowa farin
ciki
Ya matsu Matar shi ta tare tare dashi ya gansu dagashi sai ita tana bashi kulawa
irin ta mata da miji Hmmm Allah ya sauke mai ita lafiya,
Hutawa ya farayi saida ya kwanta tareda janyo filon da ta kwanta akai ya rungume
gam bacci mai dad'i ya daukeshi mai cike da mafarkin yana raya sunna da Abar sonshi
karar wayar shi ya katse shi batareda yakai ga cimma burin shi ba tsaki ya buga
tareda danna wayar ya sa a kunne batare da ya duba ba,
Saurin tashi yayi zaune domin jin muryar wadda ke kiran shi wato mubena,
"Ka fada min inda zan sameka a Zaria yanzu zan zo domin na kasa daurewa'
Shiru yayi kawai domin bai taba ganin mayyar yarinya irin wannan ba kofa sa'ar
Matar shi batayi ba Amma sai rashin kunya,
" mema sunan ki ? "Mubena kardai har ka manta sunan ? " to ai ni sunan mace daya ne
kacal bana manta wa dashi bayan na mahaifiyata wato my one and only wife,
"Wife? wasa kakeyi nasan Bakada mata As your Age don kana tsakiyar lokacin ka
Bazaka taba bata rayuwar ka ba,
A matsayin ki na musulma a wane hadisin ne ya fadi cewar ni ban isa Aure ba?
" aa ba wannan bane ni ina maganar zamani da kuma wayewa da tazo , OK yanzu meyasa
kika kirani?
"Inason mu hadu ne, " ina mukhtar ki fada mishi ya kawoki "no banaso yasani please
OK ni ina Kaduna yanzu haka kuma ina cikin gidana so idan na fito zan nemeki
" Kafada min unguwar inzo "aa gidan matata ne nan banason kowace mace a ciki
Wani iri taji domin taji Alamar wulakanci a cikin zancen shi Amma mai nema baya
fushi,
A haka Abubuwa keta tafiya akalla yayi kusan kwana biyar a Kaduna batareda ya bari
sun hadu ba sunata faman shirye shiryen bude Asibitin shi da kuma company Dady,
A kullum suna kan waya da Matar shi ya matsu ta zo KD yayi matukar kewar ta
ita,kanta tayi missing din shi sosai sai dai basar war da takeyi
Sarkin naci kuwa Yanzu har kuka takeyi idan ta kirashi akan ya bata izinin zuwa
wurin shi,
Har ya gaji ya daina daukar wayar ta sai dai msg idan ya karan ta ya share da ita
" yau Saura kwana daya a yi taron bude Asibitin yana zaune a cikin falon shi yana
kurbar coffee wayar shi na kunnen shi yana waya da Abar kaunar shi '
"Baby na meyasa bazaki zo yau ba nafa daure sosai kusan sati daya ban saki a idoba
ki zo yau gobe ina busy sosai bazamu samu sakewa ba,
" ai zaka ganni ko "bakya ganewa ne nafayi missing sosai Kizo mukasan ce tare a
daren yau aiki ne ya rikeni kinsan da tuni na zo Zaria
" my Queen ya furta cikin kashe murya "um Kizo please " Hajiya tace sai gobe zamu
shigo da wuri dasu Gwaggo Amina Amma Su Dady na zuwa yau,
Ki biyosu to "saidai munzo bye ta katse kiran " murmushi kawai yayi ya shafo sumar
kanshi mai santsi da sheki "my wife ya furta can kasa
Su Momy sun iso KD sun hadu da mama balkisu suka fara aiwatar da shirin tarbon
mutane domin y'an uwan Momy ma zasu zo daga UK
Mukhtar sun kayatar da wurin da sauran Abokan Aikin su wurin ya kayatar domin sun
gayyato manyan mutane irin minister lafiya tareda sarkin zazzau da kuma mai gayya
mai aiki wato gwamna daya tamkar da dubu malam nasir el rufa'i domin bude wannan
Asibitin da zai bada gudun mawar shi a garin na Kaduna,
Bakin turawan sun iso nija An saukesu a gidajen da aka kayata domin ma aikatan
Asibitin sun yaba da kasar ta mu da kuma garin na gwamna wato KD garin ilimi
Shidai ya matsu farin cikin shi ta iso yaga lafiyar Babyn shi kuma
Da wuri suka shirya ta yi wani haske na ban mamaki domin cikin ya shiga wata biyu
yanzu tayi matukar kyau cikin dinkin ta na Senegal doguwar Riga shadda mai tsada
ruwan goro taji design blue kamar wata Matar gwamna ta fito tana sheki
Ta sanya farin mayafi da kuma takalmi da jaka farare Hajiya tace nasha Allah uwar
gidan baturen marasa kunya,
Saida ta dara sannan suka fito tana rikeda makullin motar ta suka rufe gidan su
suka nufi gidan su Gwaggo Amina domin daukar ta don magaji shi a can ya kwana domin
Dady ya Ajiye mai driver na kanshi ,
"Wai ni ina driver da zai kaimu naga kin tukomu zuwa nan " ni zankai ku ku dauro
Alwala kawai'
"Wane ni Wallahi da sake kira driver da yace ko in kirashi kinsan halin shi ai
bazaki kaimu lahira ba bamu shirya ba,
Dariya kawai tasa saida Gwaggo Amina ta fito cikin shirin ta itama tsoffin sun fito
shar kana ganin su kasan suna da gata haihuwa tayi rana,
Driver ta kira ya zo suka wuce sunata zuba hirar su har suka isa Kaduna lafiya,
Kiran wayar shi tayi " mun iso ina zamu isa ? "Ku je gidan baba su Momy na can idan
kin Ajiyesu zan iso in dauke ki yanzu'.
Surukan nasu sun tarbesu cikin girma suka basu wuri na mu samman tare da Abin motsa
baki
Ita ma ta zauna domin ta matsu bata ga mijin nata ba Sallamar shi taji cikin
daddadan muryar shi ta dago kanta akan wayar da take danna wa ta dora su akan
nashi,
Idanun shi ya zuba mata tayi mugun tafiya dashi saida ya yi Ajiyar zuciya sannan ya
tako zuwa tsakiyar falon
Batareda ya lura da duk mutanen dake zaune a falon ba ya fara kokarin nufota,
" Saurin mikewa tayi ta nufi dakin mama balkisu gudun kar ya bata kunya ya waske
tare da zama kusa dasu Hajiya
"Tsoffi sannun ku da zuwa " yanzu ka ganmu shiryayye to sannu kaima ya shirye
shirye,
Alhmdulillah ya d'an taba hira dasu kadan sannan ya mike ya fita waje wurin motar
shi ya kira ta" kifito kafin in shigo cikin dakin ina waje,
Ya katse kiran ya zubawa hanya ido wata wawuyar Ajiyar zuciya ya sauke tareda zuba
mata ido tun daga sama har kasa ji yake kamar ya ruga ya rungume ta yakeji,
Ta karaso idan ta akasa cikin takunta na burgewa har saida ta iso sannan yayi
Ajiyar zuciya ya zagaya tareda bude mata mota ta shiga sannan ya zagayo tana kallon
shi ta glass ya zauna,
"Muje gidan mu in rage zafi kar inkasa zuwa taron nan kin dagamin hankali da irin
haduwar ki madam ya kalle ta da idanun shi dasuka canja launi
" kallon shi tayi itama ta dukar da kai "ba kace sai nayi wata biyu ba ina hutawa "
riko hannun ta mai laushi yayi ya dora a saman jikin shi kinji y'anda ma koma daga
ganin ki so dole ki taimaka in baso kike in kasa yin komai ba,
Zaro hannun ta kawai tayi daga ganin sarkin fawa sai miya tayi zaki Abdul ya
shiga uku da jaraba ta fada afili batare da tasan zancen ya fito ba,
"Naji ni nacika jaraba Amma nagode wa Allah jaraba ta ta tsaya akan Matar Aure na
ita kadai nakejin sha'awa,
Hannun shi ya dora saman cikin ta " ya baby na? shiru kawai tayi yanata lalubar ta
har suka isa gidan su ya shiga tareda bude mata tafito ya riko mata jakar suka
shiga daga ciki'
Tun daga falon ya Ajiye jakar ya cire mata gyalen ya sunkuce ta sai cikin dakin bai
direta ko inaba sai gado yafara binta da kallo ta ko ina jikinta,
"Baby lau layin ya tsaya ko naga yanzu lafiya lau " eh sai lokaci lokaci nake d'an
zazzabi Amma inacin komai "god ya ce kinyi kyau sosai my madam,
Murmushi kawai tayi ya rungumo ta tsam tareda Ajiyar zuciya " baby I really miss
you '
Tuni ya fara dora mata kiss a ko ina na jikin ta yafara kok'arin cire mata Riga
kenan wayar shi tayi kara tsaki kawai yayi yaci gaba da Abinda yakeyi
Kallon jikin ta kawai yakeyi domin ko ina nata burgeshi yakeyi fatar ta sai sheki
takeyi tana santsi hannun shi kawai ke yawo akan jikin ta
Saida wayar ta kuma kara ya daga yana tsaki " wai kai meyasa kake haka ne banfada
maka iyali na sun iso ba inason time tare da ita please "
"To d'an iska ai saika fito An fara taruwa kai kadai Ake jira ga su salis sun iso
ma Amma kai kana can kana fitina don Allah ka fito malam yanzu,
" kai Wallahi Allah ya isa tsakani na dakai mugu kawai ka hana ruwa gudu 'dole ya
diro ya nufi bathroom ya sheko ruwa cikin sauri ya fito tareda janyo kaya ya fara
sakawa"
Madam ga kayan ki kitashi ki canja ba time mun tara manyan mutane kar mu barsu suna
jira
Ta mike ita ma ya fito mata da wasu kayan less ne blue Riga da zani mai kyau da
kuma tsada har tafi haduwa yanzu ya dakko mata pos da takalmi shi kuwa ya shirya
cikin suit blue ya fito yayi kyau sosai ita kanta ya burge ta
Sun fito fes dasu kamar taurari ya riko hannun ta kana ganin ta kaga Matar d'an
gata suna fitowa motoci tagani Jere kusan guda biyar ta tsakiyar aka bude musu
security suka shiga sauran sai kace wani gwamna haka suka nufi Asibiti
Sun isa wurin taron jama'a sun hallara ga runfuna ta ko ina motocin na isowa
wurin Kallo ya koma Kansu security suka bude mai motar ya fito tareda zagaya wa
dayan gefen ya budewa Matar shi ta fito,
Sunyi matukar burge mutane mu samman kasan cewar shi karamin yaro Amma ya mallaki
Abubuwa da dama na ci gaba
A gurguje taron ya kayatar sosai duk mutanen da suka gayyata sun samu damar hallara
Anbude Asibitin cikin nasara
Iyayen sunyi matukar Alfahari da yaron nasu ita kanta ya matukar burgeta A wurin
duk da ranta ya baci da ganin wata Yarinya da take mai shishshigi a wurin duk da
tagan shi a tare da Matar shi Amma bai sa ta fasa shige mai ba ranta ya baci sosai
shiyasa duk da gundura a wurin
"Su Hajiya sun yi matukar farin ciki da ganin cigaban gudan jinin su gashi An zuba
kayan Aiki sosai na zamani a Asibitin Domin sauka kawa mata wajen haihuwa
Domin sun kwashi kwararrun likitoci ta fannin mata wato Gynecologist domin bama
mata taimako dangane da matsalolin haihuwa sannan Akwai gefen yara suma Annemi
likitoci da zasu bada tasu gudun mawar ,
Sun shirya nufo gida domin gudanar da walimar da suka shirya su Momy nata kaiwa da
kawowa domin kayata Abun kasan cewar harabar gidan nada girma aka zuba kujeru da
runfuna gaba daya a harabar gidan ga security tako ina
Suna isowa suka shiga daga ciki shida Matar shi domin shirya wa
Gaba daya zuciyar ta a jagule take domin ganin irin y'anda y'an mata ke shigewa
mijin ta a Gaskiya hankalin ta ya tashi sosai,
Har batason ta tafi ta bar shi a yanzu gwara ta zauna da kayan ta tabashi kulawa,
" yana lura da yanayin ta duk jikinta yayi sanyi suna shiga cikin dakin su ya
rungume ta
A hankali ya dora habar shi akan Kafada r ta
"Miss Abdullah Jafar what is wrong? batasan lokacin da hawaye suka fara zirarowa
daga idanun ta ba tsabar kishin da ke cin zuciyar ta,
" naga y'an mata sunata shige maka ne ni dai Wallahi banyar da ba kawai ni....
Dariya yasa tareda zuba mata idanun shi masu dauke da tsantsar soyayyar ta
"Madam haka kike kishina " wow Gaskiya naji dad'i don haka zan kara Aure kodan inga
kishin ki"
Duka takai mai cikeda shagwaba "nidai Wallahi banyar da ba tasan ya mai kuka, wani
irin farin ciki ne ya kara rufe shi wato tana sonshi sosai har haka itama,
Juyo da ita yayi ya rungume yana Ajiyar zuciya cikeda tsantsar farin ciki " madam
relaxed ya kamata ki duba tarihin soyayyar mu the you tink Akwai sauran space a
zuciyar Abdullah akan wata mace?
Nop ke kadai nakeso Ruman banso wata mace ba tun farko sai Yanzu da na sami mafarki
na bazan iya Rayuwa da kowace mace ba idan ba ke bace,
"Am only yours and you are mine for ever insha Allah don haka ni ki cire damuwa a
zuciyar ki
Sannan y'an mata da kike gani duk cousin's dina ne turawa y'an uwan Momy na me
zanyi dasu nifa jinin zage Zagi ne ki gane ina Alfahari da Asalina da kuma kasar
mahaifina,
Sannan Mubena a hankali ya war ware mata komai don haka kisa a ranki ni nakine
Rungume shi tayi gam tareda dago bakinta ta hade da nashi ta aika mai da wani salon
sunba w'anda saida ya kasa tsayawa da kafar shi'
Sannan ta zare bakin ta dakyar numfashin shi ya tsaya " wow baby zaki kashe ni da
salon ki Gaskiya ina bukatar irin shi Anjima don haka ki shirya min OK'
Dage mai gira tayi cikin salon ta tareda murmushi "karka damu my one I promise "
zaro ido yayi cikin zumudi "da gaske ? " uhm zanyi sake ne kadangaru suyimin
wawaso,
Kyalkyalewa yayi cikin jin dad'i "suwaye kadan garun? " suna nan da yawa irin su
mubena "to wannan Mubena ta kiyaye ki k'arki mata rotse
" ai kuwa gwara ta fitar min hanyar miji tun ban karta ba, rungume ta yayi yana mai
jin wani irin nishad'i Mara iyaka a yau Ruman din shi tana nunamai kulawa
Kiran wayar shi da Akayi yasashi mikewa "oh my god mun manta da mutane baby tashi
mu shirya we have the whole night today
Kaya ya kuma bata wata doguwar Riga kamar wedding gown pink hade da d'an mayafin ta
ta shirya ciki rigar tayi masifar daukar ta
Wayar ta tayi kara ta duba ganin sunan hajara yasa ta saurin dagawa
" yanzu kun manta dani Besty " ba wani nan kece dai kika manta damu yanzu dai idan
kun gama shanya jama'ar kufito muna jiranku,
Wani irin ihun murna ta sanya Aminan ta sunzo tayi saurin sanya bakin takalmin ta
mai tsini gashi tayi simple makeup ta Yane fuskar ta da d'an karamin mayafin rigar
mai dogon hannu ce gashi ta fito kamar Amaryar balarabiya
Da y'ar Karamar Po's dinta mai kyalli masha Allah shima ya kuma shirya wa cikin
farin suit da fararen takalmin ga Agogon shi na Gucci mai tsada
Kallon junan su kawai sukeyi cikin burgewa kowa na kyasa haduwar d'an uwan shi,
Haka suka fito yana rungume da hannun ta irin na turawa.....✍
"Acan na hango y'an kuskure na fan's cike y'an gayyar sodi Niko nace waya basu
invitation? Ina jiran Amsarku
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
3⃣9⃣ 3⃣9⃣
➡3⃣9⃣
Sunyi matukar daukar hankalin jama'ar dake wurin duk y'an uwa na wurin har ma da
kakan nin su Hajiya bakin ta har kunne ganin irin hutun da Allah ya kawo ma yar
jikar ta
Mikewa Akayi ana musu tafi mukhtar na gefe shida mubena 'wani irin kishi ne ya
turnike ta yanzu saboda Matar shi ne yake mata wulakanci
Me Matar tashi ta fita da zai wulanta ta har haka, harara kawai take zubawa Ruman,
ita dai tana nan like da mijin ta har suka isa wurin da Aka tanadar musu
Aka fara gudanar da taron inda mukhtar ya mike ya fara bayanin sanadiyyar taruwar
su a wurin "
Daga nesa ta hango Aminan ta sun kame a kujeru sunata zuba hira dasu Hajiya su
MOMY ma duk suna gefe tareda y'an uwanta da sukazo
Dana duba wani gefen kuwa iyayen su ne maza tareda Abokan su suma sunata faman
tattaunawa atsaka nin su
Cikin natsuwa mukhtar yafara jawabi kamar haka, "Assalamu Akaikum jama'a munayi
muku barka da zuwa wannan d'an karamin taro da muka hada domin cigaban Abokin mu
d'an uwan mu da kuma mu kan mu baki daya,
Akwai dalili da dama da ya tara mu a nan na farko domin murnar bude Asibitin mu
sannan na biyu domin taya shi murnar Auren shi da ba mu samu yi ba tun farko don
haka muka ga ya dace yanzu mu d'an hada mai d'an kwarya kwaryar taro
Kafin zuwa lokacin da Matar tashi zata sauka mu hada gagarumin fati yanzu ma mun
sassauta ne saboda Akwai iyayen mu Anan,
" mahaifan mu Alhaji Jafar Ahmed da Alhaji Muhammad zubair muna matukar godiya
agareku
Sai kuma iyayen mu mata "our mother MOMY Khadija you are highly welcome thank you
so much m'am
" mama balkisu muna miki barka da zuwa sauran baki da suka zo daga nesa dana kusa
duk muna muku bar ka da zuwa ,
"An nayi suya na manta da Albasa kakar mu Hajiya kaka barka da zuwa manyan kawayen
uwar gida kuma muna yi muku barka da zuwa,
" nidai ina gefe na kure a daka bakina har wuya ina zura wuya ina jiran Akira suna
na Amma har ya gama introduction dinshi bai kirani ba don ya rai nan wayau Asha
wuya tare dani Amma ko barka da zuwa Anki yimin kuth,
Ya bada takai taccen tarihin Abdullah da irin nasarar da ya samu a karatun shi
tundaga farko har zuwa kammalawa r shi,
"Sai tarihin Asalin soyayyar shi da Ruman yana fada cikin raha" kowa na dariya
banda ni na zabga uban tagumi saboda haushi
Saida yakai Aya sannan ya zauna Aka kira Hajara tazo ta d'an bada tarihin Ruman har
zuwa yanzu a takaice cikin harshen turanci da irin son girman ta sai gashi Allah ya
hada ta Aure da yaro karami kuma Allah ya sanya mata soyayyar shi sosai a cikin
zuciyar ta don haka muna musu fatan Alkhairi Allah basu zaman lafiya kuma Allah ya
kaimu nan da wata bakwai mu dawo suna,
Ta zauna aka tafa mata kafin A fara fito da Abubuwan motsa baki ma Aikata ne na mu
samman na gani Ankwaso daga hotel suke rabon Abin cin,.
Nida na shirya rabo inayi ina zubawa a burgame Amma MOMY tayi mun bakin ciki
yaseen,
A can gefe na hango y'an gayyar sodi su hauwa'u u Sulaiman da su Momyn suhaila sun
zuba tagumi ga manyan jakun kunan su
Maman uku da ta kafa kafa dani kuwa tana gefe muna mazurai KUSKURE NA fan's kuwa ba
show domin taron ba gayyar sodi duk haka muka kwashe muka nemi gudu saboda ba waku,
Meenat sarkin gulma ta maidoni ai wallahi ita gulmar bata isheta ba mu koma sai na
gama kwaso musu labari,
A haka aka yi ta ciye ciye ni ko plate din kuli kuli ban samu ba gwara meena da
mukhtar ya rage ta sud'e plate din shi,
Bayan Anfara mika musu gift Ruman ta mike zuwa wurin kawayen ta suka rungume juna
"Agaskiya Queen Bakida kirki Badan bature ba bazamu San komai ba yanzu Aminci
yace haka?
" don Allah Kuyi hakuri bansan taron yakai har haka ba saboda ni Ance kawai za a
bude Asibiti ne Ashe su bidi'a suka shirya har haka'
"An bature ya fita Abakin ku kuce Abdullah,ta fada tana zuba dariya " aa kifada ai
mungani ya yi winning zuciyar ki kiyi lokacin ki ne
Young crush ya burge ni ya sace zuciyar Queen karamin yaro ya zama babba " banson
wulakanci mijin nawa ne karamin yaro to Yama fi manyan mutane in fada muku,
Dariya suka sanya mata Sumy tace Wallahi kedai bari gashi ina Kwasar takaici kinsan
inada uwar gida kullum cikin raba miji ni Abin yana damu na,
Hajara takai mata duka "kedai anyi jara batu Wallahi kin shige su " Ruman tasa
dariya Ashe Akwai aiki kenan,
Isowar su mukhtar ne da Abdullah yasa su yin shiru "hy my friend's " hello our
husband hajara ta fada cikin tsokana
Mukhtar ya zuba mata idanu sai kallon ta yakeyi tun da ya ganta yaji shima fa
babbar yarinya yake muradi tunda ya lura Sam mubena bata yin shi,
"Thanks for coming " you are welcome Allah yasa Alkhairi suka furta baki dayan su"
"Abdullah' mubena ta fada cikin wani irin salo tana tafe tana kara'i raya gaba
dayan su suka juyo domin zuba ma sarautar Allah ido,
" please inason Muyi magana minti biyu, idanun shi ya zuba Akan Ruman data saki
baki har hanci tana kallon sarautar ubangiji,
"Ke baki ganshi tare da iyalin shi bane kike cewa ya zo Kuyi magana? Mukhtar ya
fada cikin hasala " and so malam ban kasa dakai ba badakai nake yiba,
Wani irin turirin bakin ciki ne ya turnike ta kamar zatayi ihu hajara ce ta ja
hannun ta "Queen muje daga ciki muga yanayin gidan namu,
Dama ta k'agu don haka da sauri ta bisu sukayi cikin gidan batareda ta koma kan
kowa ba,
Suna shiga falon ta fisge hannun ta ta nufi kujera ta zauna kamar tayi bindiga
" Sumy ce ta matso gab da ita ta zauna " Queen wacece wannan ? Wasu irin hawaye ne
suka zubo mata kamar wuta,..
"Wace ce kuwa bayan sonshi takeyi kuma kuna ganin ina zaiki ta bayan Karamar
yarinya ce tafini kuruciya sannan gata fara irin shi
Da na shirya zama Amma yanzu kam tafiya ta zanyi don bakin ciki kashe ni zaiyi
inada mugun kishi akan Abdullah is better inyi nisa dashi before I do some thing
stupid,
" Ashe Bakida wayo Ruman matan bariki zaki tafi kibar wa mijin ki saboda mugun
kishin da baida ma ana ya ce miki yana sonta ne?
"Aa " kinsan cewa mijin ki na matukar kaunar ki me yasa kikeso ki wahalar dashi
Ruman please ki barshi haka yaji da Aikin da zaifara ki kama mijin ki gam ki janyo
Abinki a jiki Wallahi sai kin bani mamaki Amma idan kikayi sake
Wallahi duk soyayyar da yake miki zaki fita Azuciyar shi yanzu ma na janyo ki ne
don k'arki kwafsa kijawa kanki raini domin nasan wannan Yarinyar rashin kunya ne
kawai bata wuce eighteen,
"Sun dauki lokaci suna mata hira har saida Hajiya suka shigo sannan ta yi kokarin
saita kanta suka zauna suka fara zuba hira,
" yanzu Ummu wannan gida saika ce mutum hamsin zasu zauna kuma duk na mutum daya
lallai hadiza ta daure muku maciji Kuyi wasa da kai wannan gini kamar baza a mutu
ba,
Gwaggo Amina tayi dariya cikeda jin dad'in jikokin ta cikin jin dad'i saidai su
tayasu Addu'ar Allah ya basu zaman lafiya,
Yakuma sa da jinkiri suka Amsa da Ameen "ina Momyn da mama suke hajjo " Ruman ta
tanbaya "suna can tareda y'an uwanta daga gani ta fada musu maganar musulun tar ta
naga sunata fada duk da banajin ko bihin ai nasan fada,
" dariya suka sanya tare kuma da Addu'ar Allah yasa kar ta bi ra'ayin su ta koma
ruwa,
Wayar ta ta fara danna wa tana neman layin shi Amma tanata ringing bai daga ba ita
kuwa tuni ta kuma hawa wato suna can suna hira,
Sukuwa tun wucewar su Ruman ya kalle ta " ki fadawa mukhtar koma meye zai fada min
he is my best friend sannan ya wuce wurin su Dady ya rungume shi "
I love you Dad " Abdullah kafa girma you are going to be a father in a next seven
months
Am still your child Dady may Allah S.W.A bless you for me Tnk you so much ya fada
yana hawaye,
"Baban Ruman na gefe yana maijin farin ciki ba Abinda yafi mai Dady irin Ace y'ar
shi ta samu kwanciyar hankali a hankali ya furta Allah ya jikan ki Aisha,
Dakina Raye zakiyi Alfahari da yarki na Auren yaron yayanki da ke sonki fiye da
kanshi
Matsowa yayi ya gaida baba yasa mai Albarka " Abdullah Allah yasa ku fara a sa'a ya
kuma baka hakurin zama da iyalin ka'
Suka Amsa da Ameen "to mu zamu shiga gari munada sauran Abin yi kaga ma a samu
bude company ba saboda rashin kammaluwar shigowa da sauran kayan Aiki '
" OK Dady, wayar shi na silent baiji kiran da take yimai ba ita kuwa duk hankalin
ta ya tashi tana tunanin cewar suna can tare da Mubena'
Ita kuwa mubena wani irin bakin ciki ne ya turnike ta "Wayar ta ta bude ta fara
rubuta mai massage " _Abdullah naso Muyi magana face to face kaki sai gudu na
kakeyi to Wallahi yanzu na fara binka and I don't care About your wife "ina sonka
Abdullah please give me a chance I will proved my love to you_
Haka ta bar gidan cike da zullumi idan ya ki ta ta shiga uku domin tana mutuwar
sonshi kamar ranta,
Mukhtar ya biyoshi " please malam muje kamun rakiya inga Queen of heart dina
Wallahi na Afka kafin inyi sake amun sakiya,
"Kai wai tsaya ina zaka kaita tafa fi karfin ka Kasani " Amma kaci uwar rainin wayo
j dan ubanka ita wadda ka Aura sa arka ce?
To nima babbar yarin yar ta shiga zuciya ta zanshiga daga ciki inji waye babba ni
ko ita "to wai ma intanbaye ka kodai da gaske Ruman tafi karfin naka ne?
Duka ya kaimai " kana hauka ni ai ko mace hudu zan iya da ita bare mace daya "to ka
shiga uku jara babbe naji ni ba RAGGON MIJI bane,
" nidai muje da Sallamar su suka shiga cikin falon lokacin Ruman ta shiga cikin
dakin ta zama sukayi Mukhtar ya zubawa hajara ido da kanta ke kan wayarta tana
chart
"Sannun ku Hajiya suka gaida Tsoffin sannan Abdullah yace "friend My friend want to
talk to you
Kallon su tayi taga irin kallon da Mukhtar ke mata tayi murmushi domin ta lura da
shi tun dazu a wurin taron " OK bani numbar ka zamuyi magana a waya domin tafiya
zamuyi yanzu muna jiran Queen ne,
"Abdullah yayi saurin kallon ta ina take ? Ta shiga ciki " mikewa yayi yabi bayanta
ya bar mukhtar da zubawa babbar yarinya ido ya kasa cewa tak saboda tayi mugun
yimai kwarjini,
A tsaye take ta sauke rigar da ke jikinta daga ita sai tight iya guiwa sai bra ga
shape dinta ya fito tsayuwar kawai yayi daga kofar dakin ya zuba mata ido cikeda
jin dad'in ganin Matar shi a cikin gidan shi yau kuma har tana nuna mai so,
Kayan da ta cire dazu ta janyo tana shirin sawa ya karaso tareda rungume ta ta baya
tareda sauke Ajiyar zuciya,
"My wife ya furta har iskar bakinshi mai dad'in kamshi ta bugi hancin ta gaba daya
jikin ta ya gama mutuwa,
Kizo wai zasu tafi yanzu su Hajiya ma na kira driver zai mayar dasu' cire hannun
shi tayi tareda da daure fuska ta matsa tareda mayar da rigar ta,
Kallon ta yayi cikin kidima" my Queen me ya faru kuma? Cikin masifa ta juyo batare
da ta saka rigar ba kuma bata damu da yanayin da take ciki ba '
"Ka gama hirar da Mubena yanzu kakeda lokaci na? " wace mubena muke hira? Karka
rainan wayo Abdul'
Dafe goshin shi yayi domin shi ya ma manta da wata mubena " Ruman please ki daina
maganar ta inace nayi miki bayanin ta kuma kina gani ita take biyoni ko'
"To can ya rage maku inna tafi sai ta ci gaba da shige maka I can't take it,
Me kike nufi ya furta yana mai zubawa kirjinta dake cike fam da ido,.
" zan koma Zaria yanzu don haka kaje wurin ta kuji dadin hira har ni zankiraka
kusan sau uku baka daga min ba
Wayar shi ya Ciro cikin rawar jiki " oh my god Wallahi nasa wayar a silent ne tun
dazu shiyasa banjiba,
Fisgo wayar tayi domin jin wayar tayi karar Shigowar msge ta bude ganin sakon da ya
shigo kawai hawaye ne suka zubo mata zurzur tsabar kishi tayi firo da wayar ta
tarwatse
Bin wayar yayi da kallo y'anda tayi dai dai kafin ya maida idon shi akanta kuka
tasa wiwi yayi saurin Jan baya ya rufe kofar sannan ya dawo kusa da ita cikin rawar
jiki " haba Ruman wai meye haka please k'arki daga min hankali mana ina cikin farin
ciki
Matsawa ya karayi ya shige jikinta " please matana ki daina damun kanki akan wata
can'
Juyo ta yayi ya dora fuskar shi a tsakiyar kirjinta yana mai shakar kamshin humrar
ta tuni komai ya fara canja mai
Nan da nan yayi connecting din duk wasu igiyoyin wutar dake hade da nata tayi
saurin matsawa tareda kuma janyo rigar ta zata mayar ya rike
"My madam me kikeyi haka? Please ki bari mana na gaji kibar ni in samu Hutu a jikin
ki kinsan na kwadaitu da ni'imar ki ya furta yana mai kuma shige mata
Bakinshi ya dora akan lips dinta yafara kokarin jefa harshen shi cikin nata tayi
saurin janye wa domin wani irin turirin kishi ke dibar ta rigar ta kawai ta sanya
taja mayafin ta dankwalin ta ma a hannu ta d'auka ta fita,
" dama ke muke jira zamu tafi kin shige ciki da miji kin manta damu'
Murmushi kawai tayi "muje to na shirya kallon ta sukeyi gaba daya suna mamakin wai
su tafi " ke ai kina nan ko? Cewar Gwaggo Amina,
"Aa Amina kafata kafar ta sai ta haihu " kar ki tafi min da mata tazo kenan idan
kuma kika tafi da ita Allah zamu bata '
"Ka dade baka bata dani ba dama shiru mukeyi dakai d'an kusun uwa kallon ta kawai
yakeyi ta dauke kai "
"Ina dreva mutafi na matsu ingan ni a garin mu Amina muje " Ummu kira dreva mutafi
yamma nayi'
"Amma sai munje gidan baba ko? Me zanyi mai muje gida kawai ai mun gaisa,
" tashi kawai sukayi gaba daya ran hajara ya baci domin Ruman nada taurin kai da
zai iya cutar da ita zata tafka KUSKURE........✍
_*Kuyi mun Afuwa NEPA na tsiya sunki bamu wuta y'anda yakamata don Allah Kuyi
managed"*_
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
4⃣0⃣ 4⃣0⃣
➡4⃣0⃣
Sunfito yana biye da ita suna shigowa motar baba na sawo kai cikin gidan tare da
Dady,
Cikin sauri sukayi parking suka fito "Mama Dama ku zamu d'auka don baba ya tafi shi
tun dazu,
" ai gwara da kuka zo domin wannan marar kunyar so yake ya rike min yarin ya kamar
bata da gata'
"Haba mama kibar mai Matar shi mana ku zo muje kinga aiki zasu fara kar ku kasa mai
hankali kuma Kunsan Aikin shi na bukatar natsuwa,
" to ubana tunda yarinya bata ra'ayi sai inyi mata dole ? "Duk tsawon rayuwar da
mukayi mukadai me yasa memu sai yanzu a rika kawo mana salo akan banzar dukiyar ta
ku " ke wuce muje kinji'
"Sumy muje ko hajara ta fada cikin fushi ta nufi motar ta batareda ta kalli Ruman
ba Sumy ce tayi karfin halin cewa " Hajiya sai kunzo'
Matsawa tayi kusa da su "Wucewa zakuyi kubar ni ? Nifa tare nakeso mutafi daku
" sai kibi su Hajiyar dake daure miki bamu ba ko ki hau taki motar ki kai kanki
Amma ba a tamu motar ba "bazan kuma cewa komai ba Ruman ki kalli mijin ki don Allah
yana bukatar ki a kusa dashi Amma kina so kitafi ki barshi " duk Abinda ya biyo
baya kiyi kuka da kanki '
Fisgar motar ta kawai tayi ta wuce batare da ta kula ta ba bin bayan motar tasu
tayi da kallo tareda mamakin irin daukar zafin na su,
Baban ta dai tunda Hajiya ta fara sababi yayi tsit Dady dai cewa kawai yayi "innar
mu muje to Gwaggo Amina ta shiga tareda tausaya wa jikan nata saidai kawaici irin
nata ta kasa cewa uffan ,
Baba ya kalli driver dake gefe " ita ka kawo ta ya furta tareda kallon Abdullah da
kallon tausayi suka shiga mota,
"To Kefa ? Zan shiga tawa Hajiya ai zamu hadu a gidan baba naji yace sai munje can
tace to '
Suna wucewa ta nufi motar ta tareda cewa driver muje' " saurin matsowa yayi cikin
fushi ya riko ta cikin sauri tare da hade rai " Ruman k'arki bar gidan nan idan har
inada hakki Akanki idan kuma kintafi ban yafe miki ba kuma Wallahi zaki gane
KUSKUREN ki haba so hauka ne ina binki kina botsarewa sai gara ni kike kamar wani
yaronki Wallahi nagaji kuma k'arki sake kibar gidan nan,
Sakin ta kawai yayi ya fita a gidan bayan ya gargadi mai gadin da kar ya sake ya
bude mai kofar gate sai da izinin shi tareda Sallamar driver,
Kallo kawai ta bishi da shi cikin mamakin irin birki cewar da yayi domin bata taba
ganin fushin shi ba ba tada zabi dole ta koma cikin fushi,
Dakin ta shige tareda kulle wa ta koma kan gadon ta kwanta kawai tana tunanin irin
rayuwar da zata gudanar a cikin wannan gidan
Cikin ta ta shafo domin jin yana kugi don Bata wani ci Abin cin kirki ba duk yau
dole ta mike ta nufi kitchen dinta da ya gaji da haduwa da kuma kayan Amfani na
zamani ,
Store din ta bude kayan Abinci ne birjik komai Akwai ta kalli buhun flour ta fasa
ta debo ta dawo firij ta debo kwai ta fasa domin taji tana ra'ayin
Cin wainar fulawa
Ta danyi grinding su tarugu da Albasa sannan ta nemi frying fan ta fara suya bayan
ta zuba kayan d'an dano,
Tana suya tana ci saida tayi nak sannan ta wanke Abinda ta wanke duk Abinda ta bata
ta gyara wurin tas sannan ta koma dakin domin watsa ruwa tana fitowa ko mai bata
shafa ba ta bingire'
Sai bacci,
Abdullah kuwa shima gidan baban ya koma domin Sallamar bakin su y'an uwan momy
domin zasu wuce suma,
"Akwai yar kanwar momy mai suna Madonna da ita kawai ta rage domin tace ita zata
d'an tsaya kwana biyu domin tana son ganin Jeff a cewar ta don ta dade tana sonshi
tun suna UK Amma yaki bata fuska don haka zatayi Amfani da wannan damar ta samu
cikar burinta,
Hajiya na ganin shi tace " kai wai ina take nufa zamu tafi? "Bazata jeba ku tafi
Abinku ai ni keda umarnin da zan bata ba keba,
" Abdullah" uban ya buga Mai tsawa "kana hauka ne ko uwar mu sa'ar kace da kake
fada mata Abinda kaga dama'
" barni da shi d'an wofi ai gashi ga ummun jiki magayi ba yace yaji ya gani ba,
Shidai wucewar shi yayi tareda su mukhtar zuwa Asibiti domin ya fadamai Ankawo wata
emagency kuma ana bukatar shi a wurin don haka ya wuce Abin shi,.
Bai dawo gidan shi ba sai dare ya shigo a matukar gajiye bai kai ga hutawa ba momy
ta kira shi yazo ya dauki Madonna ta dameta ita gidan shi zatazo
Tsaki yayi kawai ya ce tasa driver ya kawota shi ya gaji kuma yasan Akwai matsala
tsakanin shi da Ruman saboda rawar kan Madonna ga Ruman da d'an banzan kishi,
Kallon falon yakeyi batareda jin motsin komai ba kamar ba mai rai a cikin gidan ya
mike cike da gajiya ya nufi cikin dakin,
Dai dai lokacin da ta fito daga wanka tana daure da towel iya guiwa sumar ta a
jike hannun ta rike da karamin towel tana tsane gashin kanta
Kamewa yayi ya zuba mata ido gaba daya ji yayi gajiyar da ya kwaso ta ware matsawa
yayi cikin tafiya a hankali
Ji kawai tayi Anrungume ta ta baya, zabura tayi domin ta tsorata don batasan ya
dawo gidan ba,
"Relaxed gimbiyar Abdullah nine mijin ki' Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta
b'anb'are hannun shi akan k'ugunta
Binta yake da wani irin kallon kauna da tsantsar sha'awar ta dake cikin jinin shi
akoda yaushe,
Juyawa tayi ta nufi Waldrop domin neman kayan da zata sa Mara nauyi, ya zubawa
bayanta ido duk ta motsa kafa sai ta motsa da jinin jikin shi domin ta matukar
kunno wutar sha'awar shi nan da nan idanun shi suka juya kala,
Wata rigar bacci ta Ciro doguwa mai rubi biyu rigar ta matukar karbar surar jikinta
malam Abdullah na tsaye gaba daya ta gama kone mai ruwan kai,
Matsawa yayi kusa da ita" madam fushi kike dani saboda na hanaki tafiya ko? "Ruman
kina sona kuwa kamar y'anda kika fada da farko?
Yakamata ki bar duk wani shirme mu rungumi rayuwar dake gaban mu, ya matse ta gam a
jikin shi tareda shafo cikin ta " kin ki bari mu natsu bare har inbaki kulawa dake
da my unborn child,
Shiru kawai tayi ya juyo da ita suna fuskan tar juna, ta zuba mai ido tana kallon
cikin kwayar idon shi'
"Bakada lafiya ne? Shine maganar da ta fara yimai' " eh mana ' Meke damun ka? "Kece
damuwa ta Ruman kin sani idan har kin mun sassauci komai zaizo min da sauki"
"Girgiza kai tayi kawai " bari in hada ma ruwa kayi wanka' ta fada still fuskar ta
a daure ya saketa cikin jin dad'i yace tanks my wife,
Saida ta hada mai ruwan ta fito tasame shi ya tube ta kawar da kanta ya wuce yana
kallon ta, gaban mirror ta matsa ta d'an shafa mai tareda humrar ta mai d'an
taushin kamshi sannan ta samu wuri guda ta zauna tareda daukar wayarta ta kirasu
hajara,
Har lokacin fushi hajara keyi da ita cikin kwantar da kai ta fara nusar da
ita"Queen naso infada miki cewar Anfasa Aure na da sadeq saboda mahaifiyar shi taki
y'arda wai na bude ido da yawa sunfi son ya Auri yar secondary'
"Ruman a lokacin nan duk macen da ta samu ta shiga daga ciki ta godewa Allah ni
yanzu da ni nasamu irin mijin ki Wallahi ko fita zaiyi sai kabi kaya na Amma ke kin
samu dama kina tsula tsiya
Wallahi kiyima kanki fada' Abin ya matukar daga hankalin ta domin ta tausaya wa
Amini yar tata don tasan irin son da suke yiwa juna
Fitowar shi yasata yin sallama da hajara tace zasu yi magana da safe , dariya tayi
" oh mijin na kusa ne?
Kedai sai da safe "Allah ya zaba miki mafi Alkhairi Besty' tace Ameen,
Tashi tayi ta nufi wurin shi ta karbi towel ta fara goge mai jiki yana binta da
kallo kamar zai cinye ta " na canja maka ne?
Ajiyar zuciya ya sauke "aike kullum cikin canji kike wai meke damunki ne ? Yau ki
hau hanya gobe ki kauce,
Dariya kawai tayi ya fisgota zuwa kirjinshi yafara kokarin neman bakinta" nidai Aji
dani Jan Ajin ya isa ko'
Ya na shirin sa bakin shi Madonna ta fado cikin dakin cikin karad'i "brother"
sukayi saurin kallon ta ya hade girar sama da ta kasa'
"Madonna what is this ? Can't you nock before enter ? " oh sorry bro "hy sis in
low'
Ta fada tana dagawa Ruman hannu irin na turawa, ita dai ta sankare tana mamakin mai
zaisa ta fado musu daki haka kuma ma ba suntafi ba me ta tsaya yi ita ?
Yana rungume da Matar shi still" ya kalleta tareda bata umarnin komawa falo zaizo
ya nuna mata guest room,
Sai bayan ta fita ya kalli Ummu "my Queen kiyi hakuri Madonna cousin sister dina ce
zata yi kwana biyu a nan kafin ta koma UK,
Shiru kawai tayi domin tasan Akwai matsala zama da wannan dangin yahudawan,
" idan Akwai matsala kifada kawai yanzu insa a mayar da ita wurin Momy?
Saurin girgiza kawai tayi kafin tace "ba wani matsala ita da gidan d'an uwanta' "
aa gidan ki ne kinfini mulki dashi my Queen it's your palace'
Da kanta ta nuna mata daki sannan ta bata Abin motsa baki domin Akwai komai na
bukata a cikin gidan
Yaji dad'in ganin y'anda ta sake har karfe goma sha daya suna zaune a falon suna
kallo tareda hira tsakanin Abdullah da Madonna ita dai tana kallon su
Matsowa yayi kusa da ita "my Queen muje mu kwanta dare yayi mikewa yayi tareda riko
hannun ta, ta zuba musu ido tanajin wani iri ace akan wannan mai duhun kan ce ya
baro kasar su ya dawo nan gashi batada ko wayewa '
Kallon ta takeyi cikeda hassada har ta mike suka shige ciki jikin shi na rawa,
suna shiga ya fara koro zalamar shi a fili cikin rawar jiki ya fara aiwatar da son
ranshi,
Kallon shi takeyi cike da mamakin shi y'anda yake aika mata sako kamar zai cinye ta
gaba daya yanayin da ya shiga ya tsoratar da ita '
Rike hannun shi tayi dake yawo a jikinta " Abdul " dakyar ya iya Amsata da um'
please kabini a hankali mana kana tsorata ni fa'
"To ai kece kullum kafin in samu sai na wahala ya furta cikin rawar murya tuni ta
fara bashi taimako ta birkita mai tunani kafin kace mai ya fara shawagi a sararin
samaniya ,
Ranar sun murji juna domin tayi na mijin kokari wajen ganin ta gamsar da shi kuma
ya gamsun d'ari bisa d'ari wani irin runguma ya yi mata hawaye na zuba mai a idanu
tareda rokon ta,
" please my wife k'arki ce zaki tafi ki barni again bazan iya hakuri ba ina bukatar
kulawar ki idan kika barni zan iya fadawa halaka don Allah ki cigaba da bani irin
wannan kulawar dama haka kika iya birkita mutum amma kike wahalar dani?
Rungume shi tayi itama cike da so domin ji take kaunar shi ta lunku a cikin zuciyar
ta
Ranar sunyi kwanan farin ciki w'anda har saida suka makara wurin tashi
Ita da kanta ta hada musu breakfast irin w'anda tasan bakuwar su zata iya ci kafin
ta feso wanka ta dauki kwalliyar ta kafin su fito cin Abinci yana like da ita kamar
cingam,
"Abdul wannan mannewar fa? " ai bazaki gane bane ni ji nake kamar kar in je aiki mu
kasance tare kibani irin kulawar daren jiya, ya fada tareda dage mata gira daya,
Murmushi tayi kawai ta hada mai Abincin itama Madonna ta hada mata ta kalle ta taga
ta hade rai sai mazurai takeyi '
Ta fahimci Yarinyar sarai don haka ta fita hanyar ta suka ci Abincin su cikin jin
dadi da kuma kulawa suna ciyar da juna tareda shafo cikinta har zuwa saman kirjinta
ya matso da bakinshi kusa da kunnen ta,
"Baby kinsan me? Ta ce " aa, "na matsu banga kin haihu ba, " kinsan saboda me?
"Saika fada' " saboda inga y'anda zaki rika bawa yarona ko yarinya ta wannan
nonuwan naki, kinga a lokacin zanrika ganin su y'anda nakeso tunda yanzu rowar su
kike mun bakya so ina ganin su'
Saurin matsawa tayi tareda kallon Madonna tana mamakin halin Abdullah shi Sam kunya
bata cikin list dinshi
"Zakayi latti fa ka tashi ka tafi kasan ana bukatar ka a wurin' " Hmmm bakyason
Muyi maganar ko? Please ki gane irin Abinda nakeso da irin rayuwar da nake burin
shinfida wa da matana,
"Bari dai idan na dawo zan fada miki komai, ya duka tareda manna mata kiss daga
goshin ta har zuwa k'irjin ta sannan ya ce" I love you'
Ya fita da Akwatin Aikin shi "tuni Madonna ta shiga dakin da suka bata ta fara
tattara kayan ta domin Sam bazata ji dad'in zama a gidan ba don kishi zai iya,kashe
ta saida ta hada kayan ta tsab sannan ta kira Abdullah cewar ita zata je wurin Momy
yasa driver ya kaita,
Yaji dadin tafiyar tata domin ji yake tayi matukar takura mai sosai shida yake son
gidan shi yazama love garden tazo zata takura shi ta sauka lafiya,
Yana zaune a office nashi dake cikin Asibitin hannun shi rikeda Biro yana kallon
p.o.p fuskar shi kunshe da murmushi mai kayatar wa yana tuna Abar kaunar shi tareda
tuno moment din su na jiya a Gaskiya ta rikita shi fiye da tunani ya matsu bai
kammala Aikin shi ba ya nufi gida yana mai kwadayin kasan cewa tareda ita again,
Turo kofar da Akayi yasashi saurin kallon me Shigowar batareda izinin shi ba,
Zuba mata ido yayi yana mamakin nacin ta ba kowa bace face mubena, " karaso wa tayi
ta zauna a kujerar da ke fesin dinshi,
"Me kuma kikazoyi har office dina? Kinsan nan dai wurin aikina ne ko
"Abdullah ka taimaka ka saurare ni please
" Wallahi na wahalu ka taimake ni ina matukar sonka fiye da Kaina' "kallon ta yayi
cikin mamaki
" Mubena kina so ki haddasa was kanki damuwa ki kuma haddasa min' kinsani inason
matata fiye da Kaina Tayaya kike tunanin zan iya son wata mace?
"Ni ko a mafarki banason inganni da wata Matar bayan matata bare kuma a zahiri don
haka k'arki batawa kanki lokaci,
Gyalen dake jikinta ta Ajiye tareda tsayawa a gaban shi " Abdullah ka kalle ni da
me Matar ka tafini da Bazaka bani matsuguni a zuciyar ka ba?
Kallon ta yayi tareda dauke kanshi don yasan yana cikin wani yanayi baison kallon
ta ko kadan don baya jin sha'awar kallon ko wace mace inba Ruman dinshi ba,
"Matsawa tayi gab dashi kamar zata rungume shi hawaye na zuba daga idanunta' "
Abdullah don Allah ka rufa min Asiri ni na y'arda ka Aure ni a hankali zaka soni
watara na,
Ta fada tareda fadawa kan kirjinshi, wani irin fisgota yayi ya yarfa mata mari
kyawawa guda uku tareda hankade ta,
"Kina hauka ne to idan Bakida hankali zan nemo miki shi uban wa ya fada miki jikina
zai iya haduwa da na wata macen bayan matata ? "
Wai ke kin manta da irin son da Abokina ke yimiki ne da har kike sona kinaso ki
hada ni da Amini na ne?
"aa Abdullah ba macen da zata hadamu na dade da fahimtar ta don haka na nemi wadda
zata tallabi Rayuwata don haka karka damu da ni,
Mukhtar ya fada w'anda tun Shigowar ta ya biyota ya kuma ga komai " harara ta zabga
mai tareda cewa" mukhtar nace bana sonka ga w'anda nakeso ra ayi na ne zuciya ta
shi take za'ayi bakai ba don haka ka fita a maganar mu nida shi'
Daga hannun shi yayi sama "be my guest ya kalli Abdullah Abokina godluck idan ta
tafi zan dawo ya fita Abinshi domin yasan is impossible Abdullah yaso wata mace
Arayuwa,
Domin yafi kowa sanin tarihin soyayyar da yake yiwa Ruman don haka ya tafiyar shi
don yasan Abdullah zai saita mata tunani,
Kallon shi tayi cikin murmushi " Abdullah dole ka Aure ni ni ban damu ba kasoni ko
karka soni nidai inganni a matsayin matarka,
"OK Aure na zakiyi dole kenan ? OK god luk with that " Amma ki sani ni mijin mace
daya ne a Rayuwa wato my Ruman my wife she is the only woman I love and she will be
the last insha Allah
Gyalen ta ta d'auka ta kalle shi wani iri " me kake tunani ? Wannan wulakanci zaisa
in hakura Wallahi ina sonka sosai Abdullah kuma yakin da zanyi A duniya shine yakin
ganin na mallake ka koda shine karshen numfashi na.......✍
"Hmmmmmmmmm🤐
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
4⃣1⃣ 4⃣1⃣
➡4⃣1⃣
Har ya dawo gida yana mamakin karfin halin mubena, ana so dole ne ? Amma yaji
tausayin ta domin ya lura tana yimai mugun so don ya hango a cikin idanun ta sai
dai kash shi bazai iya budewa kowace mace zuciyar shi ba bayan Matar shi Abar
kaunar shi da yafi so a duk duniyar nan'
Yau ma a gajiye ya dawo gidan tana zaune a falon cikin kwalliyar wani farin yadi na
mata Riga da sket tayi matukar yin kyau ga kanta ba dankwali tana rike da plate din
wainar flour da miyar tarugu a gefe tana ci tana Jan yaji,..
Har ya karaso bata kula dashi ba, ya zubawa plate din ido tareda zaro ido" Ruman
meye haka kike durawa yarona?
Sai a lokacin tasan da tsayuwar shi tayi saurin dago kai tareda marai rai cewa "
Wainar fulawa ce' "meye kuma hakan ?
Ya zauna tareda ajiye jakar hannun shi ya debo zai kai bakinshi tayi saurin rikewa
" Bazaka iya Ciba Akwai yaji'
"Oh shine ke kike ci k'arki sa yarona yazo da ciwon ido fa don haka k'arki kuma cin
irin wannan Abun,.
" kallon shi tayi Kalan tausayi "Abdul fa ni ita nake bukata r ci yanzu don Allah
ka barni inci Wallahi ji nake kamar zanyi hauka in banci ba'
Kallon yanayin ta kawai yakeyi tareda mika mata plate din " OK Amma ki gama in duba
lafiyar Ajiya ta bari inyi wanka in fito,
Wucewa yayi tabi bayanshi da kallo tana mamakin halin yaron kamar d'an shekara
talatin yasan kan Rayuwa fiye da tunanin ta ga ilimi ga daukaka shiyasa yanzu take
ganin girman shi sosai,
Saida ya dauki minti kusan talatin ya fito sanye da guntun wando da kuma yar T-
shirt karama saidai bata falon ya nufi hanyar kitchen don yaji karar plate,
Tsaye take tana wanke hannun ta ya karasa dauke da murmushi a fuskar shi ya rungume
ta tareda cirata sama cak kamar baby,
Bai direta ko inaba sai tsakiyar falon akan doguwar kujera ya dago rigar ta tayi
saurin rike mai hannu " meye haka?
Kallon ta yayi wani iri" baby kinfasan halak dina ne ki daina hana ni ganin su
please kibarni ina rika ganin Abuna ina sonsu da yawa
Ke kuma kina min rowar su' "muje kaci Abinci to ' ni banajin yunwar Abinci yunwar
su nakeji idan kinbani nasha ya isheni,
Kallon shi takeyi kawai sai ta bude mai nonon ta ya kama sha tab Wallahi itadai aa'
Mikewa tayi kawai ta nufi dining ta debo mai Abinci a tray ta jero drinks din da ta
hada na gargajiya sannan ta dawo wurin shi ta dora akan karamin center table,
Duk yana kallon ta " ga Abinci kaci' nifa bazan ci Abinci ba' to saboda me? Saboda
baki yimin Abinda nakeso ba,
"Me kakeso? Ki cire rigar jikinki tayi miki girma da yawa ki zauna a haka,
Ta kalli rigar jikinta fited ce ta kamata dam Amma zaice tayi mata yawa, " yanzu
wannan rigar ce tayi min yawa?
"Eh ni dai ki cire har ma sket din ki tsaya inrika ganin kayana, a zuciyar ta tace
tab ita ina zata iya " to ai wani zai iya shigowa ' ba w'anda zai shigo mana nan ko
masu aiki nayi musu iyaka da fslona saboda ina bukatar sakewa da iyalina,
"To kaci Abincin first' " zaki cire to? Eh ka ci idan ka gama zan cire, cikin sauri
ya fara danna Abincin saida ya kusan cinyewa sannan ya ture plate din ta zuba mai
lemon da ta hada natural ba na kwali ba yasha sosai tareda yabawa sannan ya ce "OK
my promised tunda kin sani cin Abincin da ban taba cin mai yawan shiba kuma kinsan
inason insha wata madarar,
Ya furta cikin sigar tsokana, kwashe kayan tayi tas ta mayar kitchen saida ta wanke
w'anda ta bata sannan ta dawo ta tsaya daga nesan shi yana kishin gide ya zuba mata
ido,
" am waiting fa madam ' murmushi tayi irin na mugun ta sannan ta sanya hannun ta ta
zuge zif din rigar ta ya yi saurin tashi zaune yanason ganin kayan kallon shi,
Tafara sauke ta daga sama cikin salo kuma gashi ba ko bra a ciki daga ita sai rigar
domin tanada breast coup
Tuni idanun shi sun fara taro ruwan jaraba don Saura kiris ta gama cire rigar daga
Kansu taja ta tsaya cak tareda dafe kirjin ta da hannu ta dage mai gira cike da
tsokana,
"Opps wanka zanje inyi bye' ta juya da gudu cikin daki " Saura kiris ya sume a
zaune domin ta bala'in kunno shi
Tana shigewa ta kwabe kayan tas tareda dariyar yanayin da ta faro jarababben yaron
a ciki sannan ta shige bathroom din tareda b'ame kofar don tasan hali,
Yana shigowa ya tube tik ya nufi hanyar bathroom din saidai yaji ta bam ya fara
bugawa "Ruman please open for me tana jin shi saida ta gama wankan ta ta tsaya ta
goge jikinta tas sannan ta feshe ko ina da turare ta dauro d'an towel dinta sannan
ta bude kofar,
Saurin ja da baya tayi domin ganin shi kwance kamar mayunwacin zaki a kan gadon ta
yayi tik yana kallon sama
Come to me baby ya furta yana mika mata hannu " cikin takun ta da kuma yanga ta
fara takawa zuwa gareshi saida takai gab dashi ta cire kunyar ta saki towel din ya
fadi kasa,
Wani irin dogon numfashi yaja tareda Jan yaji ya fisgota ta fado saman kirjinshi
saida tace "Ash
Yayi saurin dagota sory baby tareda shafo cikin ta hope banjima Ajiya ta ba zaune
ya tashi sannan ya tayar da ita ya zubawa Abin kaunar shi ido kafin ya kai hannun
shi samansu ya fara shafawa cikin salo yana lumshe ido,
Daga baya ya dora bakin shi akan su yafara tsotar su kamar sweet ita kuwa tana "
Ashh Abdul Akwai zafi kabari haka please "
Girgiza kanshi kawai yayi saida yasha ma ishin shi kafin ya barsu ya koma ya kwanta
rigingine ya kalleta cikin dage gira nima a tsotse ni yau hot romance nake so
muyi ,
"Kai Wallahi bature baiyi ba wata irin kunya ta rufe ta yaron nan kunyar ma basu
hada hanya ba ta kalli dakin Tass da haske sannan ta koma ra kwanta tareda dunkule
wa,
" Ruman meye kikeyi haka kitashi mana' to ka kashe wuta " cikin rawar jiki ya diro
ya kashe wutar sannan ya koma gadon ya hade bakinsu ta cafko harshen shi ta fara
bashi wani irin kiss na ban mamaki har numfashin su na daukewa romancing juna suke
kamar zasu cinye junan su ita har taso tafishi zakewa yanzu domin ta birkita mai
kwakwal war shi sosai,
Lokacin da ta dira kasan shi kuwa ai wani ihun dad'i yasa mata tafara tsotsar shi
cikin irin salon ta da ya kusan haukatar dashi ya riko kanta yana kara danna wa
"Baby tank you I love you my Queen no one but you my life,
Sambatu kala kala a haka tasashi ya kawo ya rungume ta gam gam yana zubar da hawaye
" baby ni nasan kece dai dai dani nasani zaki bani kulawa nagode sosai my wife I
love you so much,
" don't leave leave me no matter what please if u do I will sourly die my Queen,
Saurin rufe mai baki tayi itama ta hanyar manne bakinta da nashi domin jinta takeyi
a sama gaba daya feelings din ta na baya sundawo a yau
Ta kuma gode wa Allah da ya kaddare ta da yin Auren kuma ya bata gwarzon na miji
w'anda zai iya mata
Dama Abinka da mai nema tuni yabada kai borin ya hau suka fara kashe junan su da
zazzafar kauna,
Kusan kwana sukayi suna kulla jarabar su har saida taji marar ta ta kulle tana mata
zafi sannan ya sarara mata yayi saurin bata taimako ya yi mata wanka tareda bata
magani sannan bacci ya kwashe ta,
"Asubar farko ma tana farkawa tayi ido biyu dashi tuni ta fara neman kari yayi
saurin tashi zaune ya rungumo ta " my Queen sorry nima inaso Amma kinsan ina son
cikin nan shima sosai fiyeda jin dad'i na kinga jiya mun wahalar dashi to ki bari
zuwa jibi saboda kina bukatar Hutu
Marai marai tayi da ido domin ji take kamar ta yimai fyade wannan Abin tasan duk
sharrin ciki ne da farko bataso kuma yanzu ba Abinda tafi kauna sama da sex itadai
ta boni,
Saida ya mata dabaru ta samu natsuwa sannan sukayi wanka sukayi Salla
Sai karfe takwas na safe ya bar gidan shi domin Jinshi yake cikin wani irin farin
cikin da bai taba tsintar kanshi a ciki ba
Ita ta rakashi har bakin motar shi yana makale da ita dakyar ya y'arda ya tafi ya
barta ta koma cikin gidan cike da jin kewar shi,
Ya isa office cike da kewar ta ya kasan ce cikin nishad'i w'anda har ma aikatan shi
sunga canji a yau
Yana samun sarari ya daga wayar shi somin kiran ruhin shi a lokacin tana kitchen
tana hada musu lafiyayyun dishes mai Aikin da ya nemo mata na gefe kawai tana
kallon ta
Wayar ta yi kara murmushi tayi tareda daukar wayar ta fita domin Amsa kiran mijin
nata da ke kara shiga cikin birnin zuciyar ta,
"Hlooo 'ya furta cikin kashe murya da kwantar da kai " hy, ta mayar mai da Amsa
itama kamar mai rad'a.
"Come to me baby Am missing you here' murmushin tayi w'anda har yaji sautin shi a
kunnen shi,
" yaushe kabar gida da har kake missing dina? "Ai Wallahi ji nake kamar inzo gida
yanzu' saidai nasan idan nadawo zanyi barna domin baby na nason hutu,
"Tsokana ko? To idan ka dawo ba ruwana dakai ' na shige su a rufa min Asiri don
Allah kar inyi hauka Wallahi na tuba nine jarababben ke ai taimako na kikeyi,
" kinsan me my Queen "aa " inaso mu kasance a haka har abada please don't change
again,
Ina cikin shaukin irin rayuwar da kika shayar dani jiya badon baby na ba ko da zan
huta fiye da tunani domin na samu irin damar da nake neman samu daga wurin ki tun
farko ban samu ba,
Sun dauki lokaci yana fada mata damuwar shi har ta tausaya mai tare da faranta mai
rai sosai domin karamai karfin guiwa domin maida hankali akan Aikin shi,
Matsuwa yayi lokaci baiyi ba, ganin lokacin bai tafiya ya gudo tareda Tarawa
mukhtar aiki
"Ka karasa ni madam tayi kira zangudu gida don ina kara minti biyu a nan zan iya
sume maku " Amma Wallahi Abdullah ka raina ni OK karka damu nima zanyi Auren inji,
"Kaki ka taimake ni muje wurin tawan ma a Zaria Karka damu zanje ni kadai " ni da
nawa Kaina yaki ka tayani ? To kowa ya iya Allon shi ya wanke,
A kagauce ya isa gidan shi tana shirye cikin kwalliyar zani da rigar Atanfa koriya
tayi kyau sosai tanajin tsayuwar motar ta fito kofar falon ta tsaya tareda zuba
mai ido har ya kashe motar ya fito,
Kamshin ta ya mai maraba idonshi ya dago ya sauke su akan ta, wani irin sanyi yaji
har cikin zuciyar shi ya sakar mata wani irin kyakkyawan murmushi mai shiga zuciya,
Hannun shi ya sanya a cikin Aljihun wandon suit dinshi ya fara takowa cikin salon
tafiyar shi na matashi mai ji da lokacin shi
Saida ya kawo gab da ita ta juya ciki da gudu cikeda tsokana tana kada mai ukun ta
yabita da saurin shi " Ruman please kitsaya k'arki mun Asara irin wannan gudun,
Dakyar ya cin mata ya rungume ta tsaka " kidaina irin gudun nan k'arki jima baby
na' ya shafo cikin ta " ya kikeji a jikin ki yanzu?
"Banajin komai sai kasala sai kuma..... Tayi shiru ta kasa karasa wa domin wani
irin mugun jin feelings cikin keson saka mata daga jiya zuwa yau,
Shiyasa duk ta matsu ya dawo, kallon ta yakeyi yana murmushi domin ya dagota: "
fadamin matar likita,
Ta girgiza kai " muje food is ready' "hmm na lura kinason inyi tunbi ko? " uhm
inaso kayi kiba sosai asan ina kulawa dakai sosai,
"Ko yanzu haka kina kulawa dani muje inyi wanka saboda ke nadawo ko tashi ba Muyi
ba kuma duk saboda ke'
" baruwa na nidai ka rika tsayawa Aikin ka, da ruwan ki kuwa don kece sanadi,
"A hankali ya matsa da kunnen shi dai dai kunnen ta ya mata rada " aa banyar daba
ka cika wayo,
"To shi kenan bazanci Abincin ba idan har baza a bani madarar peak dina ba in kora
da ita,
" muje to zakasha kadan "wayo ko? Ya fada kamar wani karamin yaro
*************************
A cikin kwanakin soyayyar su suke gudanar wa kamar ba gobe kana ganin su kasan suna
kula da junan su Abdullah hankalin shi ya kwanta
Kusan kullum sai sun kira Hajiya da sauran kakannin su Hajiya ta hakura dole ta
kyale su tare don ta hadu da y'an zamani,
Takan je gidan baban ta time to time idan yaje aiki kannin ta ma nazuwa domin mama
balkisu ta yi matukar canjawa harsu Hajiya na jin dad'in ta yanzu'
Yau kusan watan ta biyu a Kaduna kana ganin ta kasan tana cikin jin dad'i domin
tayi matukar canjawa
A kwance suke a kan gadon su da dare ya zuba mata ido kamar maraya, " my Queen a
Gaskiya wannan Babyn yana jamun rai idan yaso Abani kulawa idan baisoba a fita
hanya ta dubi fa kinbarni kamar wani maraya bayan kinsan na kwana biyu bansha
madara ta ba
Nidai Gaskiya Abani insha yau, kallon shi tayi wani iri" wai kai baka koshi ne?
"Yazanyi in koshi bayan ba ruwa jira nake ma ki haihu lokacin zamu sha ai nihin
madara ,
Ido ta waro" ruwan nonon zaka sha? To meye ba na matata bane nadaisha .... tayi
saurin rufe mai baki "kadaiyi shiru Akwai y'an gulma karsu ji
Kara labewa nayi domin nasan da mu Ake nida meenah wato tana Ankare damu Amma duk
dishes dinta saidai muji kamshi kuth
After two months
A zaune yake a office dinshi ta turo kofa tana sanye cikin wasu matsattsun kaya
kamar diyar Arna, kanshi a duke yana Aikin shi
Fadawa tayi kan jikinshi yana dago kai ta hade bakinshi da nata tareda kai hannun
ta akan jijiyar shi " kafin yayi wani yunkuri ta gama kashe mai jikin shi,
Wani irin salo take mai w'anda ya kasa kwatar kanshi a hannun ta'
"My Queen"" ya furta cikin mutuwar jiki "yes my dear sweet Abdullah, da saurin shi
ya dago kanshi domin yayi zaton matar shi ce ta kawo mai ziyara sai Alokacin yaji
wani irin karnin mai tareda warin turaren ta mai tayar da zuciya
Wani irin hankada ta yayi tareda fara gyara rigar shi ya zuba mata idanun shi cikin
tsananin bacin rai zuciyar shi na tafasa kamar wani kumurcin zaki ya matsa kusa da
ita
Ita kuwa wani irin kallo take mai mai cike da tsantsar burgewa " wow my Abdullah
ni nasan kai cikakken namiji ne a Gaskiya ka kara burgeni ka kara shiga zuciya ta
nasan zaka jiyar da mace .....
Wani irin Aranan mari ya tsunka mata har guda hudu a Jere saida bakinta ya
fashe,cikin fushi yafara zazzaga mata rashin mutunci
"Jakar banza akuya Karamar karuwa wallahi tir da haihuwar mace irin ki ya ma Akayi
kika fito cikin family masu mutunci ? Wallahi kinyi kyan banza'
" ni nasan nayi sa'ar Auren mace tagari mai rike mutuncin ta ba Abinda zanyi da
karuwa irinki kuma wannan marukan da nayi miki kadan ne idan har kika kara shiga
gona ta wallahi sai na baki mugun mamaki,
Ni zaki kawo wa iskanci, sannan mazan takata da kikewa wallahi ba a halicce ta d'an
wata mace ba sai don mace daya
Idan ba Ruman a Rayuwa bazan taba Auren wata macen ba don haka ki kama gaban ki
kije ki nemi y'an iskan maza irinki ni nafi karfin ki
"Ke har zaki iya d'auka ta karyar jaraba kikeyi Karamar y'ar iska...
Matsowa tayi tareda share jinin da ke fitowa daga bakin ta " ya isa Abdullah saboda
kawai nace ina sonka shine kake min irin wa innan zagin'
"Wallahi Abdullah ni ba y'ar iska bace impact ban taba aika ta irin haka da kowane
namiji ba sai kai kuma inason Kane Abdullah fiye da Kaina,
Ka y'arda ka Aureni don girman Allah ni na kasance mace mai matukar bukata Amma ban
taba bawa wani Kaina ba iyakata idan na matsu inyi fingering Kaina Amma Wallahi ni
ba y'ar iska bace please Abdullah ka taimaki Rayuwa ta,
" ni kadai ne namiji a duniya da zaki nace min? Nafada miki ni bana sonki bana
sonki ke ni ko kaunar jin sunan ki banayi ki fita a hanya ta na rokeki
Kije nasan kinada masoya da yawa masu sonki ni ko Tsirara zakiyi a gabana bazan ji
komai ba ko Shigowar ki a farko kinci sa'ar zuciya ta tana tunanin Abar sona ne har
kikayi nasarar aika ta abinda kikayi niyya Amma Wallahi kin cuceni mubena kin cuci
matata na taba mata halalin ta next time you cross my way I swear I gonna kill you
just stay away,
Ya fada idanun shi jawur cikin tsananin bacin rai "I hate you ya furta cikin watsa
mata miyau ya kama hanyar fita" and if you like you can spend the whole night here
I don't give a dam'n ya fita cikin fushi,
Yanada patients da dama da zai gana dasu Amma tsabar bacin ran da yake ciki ko
mukhtar bai nema ba yayi gida,
Yana fita tayi dariya tareda shafo lips dinta "Abdullah idan baka Aureni ba zaka
dawo ka neme ni dolen ka sannan wannan matar taka da kake kirarin Kanaso, hammm,
wani irin murmushi tayi ta shaki kamshin turaren shi ta lumshe ido, what a man, ta
furta ta fita cikin karairayar cin nasara ta yi waje,
A zaune take cikin ta ya fito tana rike da plate din cucumber ta yayanka tana
dangwalowa da yaji daga ita sai zani da kuma shimi
Tayi wani irin kyau da cika irin na masu ciki domin cikin ya matukar fitowa kamar
d'an wata takwas,
Bataji tsayuwar motar shi ba ya shigo cikin falon bai ko lura da ita ba ya wuce
cikin dakin
Ita kuwa tun turo kofar falon ta zuba mai ido cike da mamakin dawowar shi gida a
irin wannan lokacin,
Sannan har ya shigo bai lura da ita ba mai ya bata mai rai har haka? Ko kuma wani
sabon salo ne yau ya canja,
Ajiye plate din tayi ta mike ta nufi dakin ga kafafun ta sun d'an kunbura kadan
karar ruwa taji a bathroom,
Zama tayi a bakin gadon su tana jiran Fitowar shi, ko kayan shi bai cire ba ya bude
shower ruwa na zubomai saida ya danji sanyi sannan ya tuna irin Shigowar dayayi
dafe goshin shi yayi,
" oh my God yanzu wane irin tunani Ruman zatayi ya shigo gidan ba kamar y'anda ya
saba ba kuma sai yanzu ya tuna ya ganta a falon cikin sauri ya tube ya janyo brush
ya wanke bakinshi tareda jin kyamar kanshi da kuma jikin shi da ya taba na wannan
jakar yarin yar,
Yayi kokarin saita kanshi sannan ya fito daure da towel, tsayawa yayi a bakin kofar
yana zuba mata murmushi " ba oyoyo my Queen,
D'an matse fuska tayi "Abdullah lafiya kake kuwa ka shigo ko gani na Bakayi ba? "
dariya yayi cikin dauriya
"Am sory my wife ke ce kikasa ni dawowa ai ya furta cikin dage gira domin ya kawar
mata da tunani
Ya yi saurin hade bakinsu yafara kissing jikinshi na rawa tareda wasu hawaye da
suka d'an tari a idan shi domin yana gudun ace Ruman ta gano abinda ya faru dashi a
yau bazata taba Y'arda da duk Abinda zai fada mata ba,
Rungume ta yayi tsam " I love you so much my wife don Allah k'arki kuje ni no
matter what ina sonki my Queen dagoshi tayi daga jikin ta ta zuba mai ido cikin
Alamun tuhuma,
"Abdul me ya faru? Girgiza kai yayi " noting I always said that kin San irin son da
nake miki Ruman bazan taba yin Abinda zai bata miki ba
"Waini na fada maka zanguje ka ne? Kafada min me ya faru? " ba komai ya kuma
rungume ta ki bani Abinci na ki kuma hada min da peak dina,
*"Zan yi Amfani da wannan damar in Tunatar da y'an uwa na mata akan KUSKUREN da
muke tafkawa a duk lokacin da mijin ki ya fita wallahi Akwai idon wata macen a
kanshi komai munin shi wata zataga ya mata, ba muda dabara sai dai mu kasan ce
masu yi musu Addu'ar Allah ya shiga tsakanin su da mugayen mata irin su mubena, mu
rage kishi wata rana A sanadin kishin mu wani Abun da muke gudu yake faruwa damu
mu rika yaki da zukatan mu, _kukan k'urciya jawabi ne_......*
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
➡4⃣2⃣ 4⃣2⃣
4⃣2⃣
Washe gari bai fita da wuri ba suna like da juna kamar kar su rabu ji yake kamar ya
zauna a gida kawai yana tarai rayar matar shi da Abinda ke cikin ta gashi yanzu
cikin ya fito sosai baya gajiya da kallon ta,
''Dakyar ta samu ya tafi aiki koshi saida akayita kiran shi ana bukatar shi kafin
ya tafi,
"A zaune a kasan falon nata tana shan magwaro ta mimmike kafa irin na masu ciki,
'takun ta kawai taji batareda tayi sallama ba, saurin daga kanta tayi cike da
mamakin wacece ta shigo mata gida ba da izini ba kuma har cikin falon ta?
" tuni Annurin fuskar ta ya dauke domin tozali da fuskar Mubena cikin dinkin zamani
Kafada a waje ga gashin kanta a waje bako dankwali saidai wani dan karamin mayafi
mai shara shara,
Zama tayi a kan kujerar tareda d'ora kafa daya kan daya " barka dai uwargida' ta
fada cikin salon rainin hankali,
"Kinsan yaka mata inzo mu saba tun kafin Nashigo daga ciki' "oh my Abdullah bai
fada miki tsaka nin mu ba?
" OK don worry I will tell you now" opps bari ma kika deal, ta bude tafkekiyar
wayar dake hannun ta ta kunna video din da ta d'auka ta haska mata dai dai lokacin
da bakin ta ke cikin na Abdullah hannun ta ke cikin wandon shi,
Wani irin bugawa kirjin ta yayi tuni zufa ya fara wanke ta tundaga saman kanta har
zuwa kafar ta,
Wani irin kululun bakin ciki ne ya turnike ta "Abdul dinta ke kissing wata mace?
Dama cin Amanar ta kawai ya keyi?
Tuni ta gama shiga mugun yanayi mikewa tayi cikin tsananin dauriya ta kakaro
murmushi,
" Mubena kike ko wa? Ki saurareni da kyau "Abdullah mijin mace hudu ne idan kina
tunanin akan d'an wannan Abun zaisa raina ya baci so you are mistaken,
Sannan inaso tun muna shedar juna ki barmin gidana ki jira har lokacin da zaki
shigo da sunan matar gidan,
Kuma daga yau kar inkuma ganin ki ko a gate din gidana " now get out of my house"
ta furta cikin k'araji tare da dafe cikin ta,
Saurin mikewa tayi domin taji tsoron irin zaburowar da tayi ta kama hanyar fita" to
ni na tafi uwar gida sai na shigo bye"
Ta fada tareda fita tana Aiya nawa A zuciyar ta Abinda zai faru domin ta gano
karfin hali kawai Ruman din keyi,
Tana ficewa ta ruga dakin ta dafe da baki domin Saura kiris ta saki ihu tun tana
nan,
Kuka takeyi sosai kamar ranta zai fita zuciyar ta na tafar fasa
Saida kanta ya dauki ciwo mikewa tayi dakyar ta ja kafa zuwa bathroom ta watso ruwa
tareda sa kaya marasa nauyi sannan ta janyo wayar ta ta tura mai sako kamar haka,
"Na tafi kuma bazan dawo ba ka zauna da karuwar ka Mubena Abdul ka cuceni, kasan
inda zanje dama ba son zama na akeyi a nan ba sannan idan har ka y'arda kafar ka ta
tako Zaria zan tona ma Asiri a gaban family gaba daya,
Sannan cikin ka ina haife shi kazo ka dauki Abinka don bazan shayar dashi ba ka
kaiwa karuwar ka da kuke lalata da ita ta rainar maka shi,
" ciki ne ya Riga ya shiga banida y'anda zanyi dashi Amma Abdullah kaji tsoron
Allah ka tuna kai musulmi ne,
Ta kama hanyar Zaria " yaune karo na farko da ta taba tuki mai tsawo tsabar bakin
ciki da kishin da ke damun ta ya hanata ganin Nisan hanyar,
Abdullah na fama da Aikin shi domin sunada tiyata wayar shi ma kasheta yayi bai
bude ba saida suka kammala ya janyo wayar ya kunna yafara tunanin kiran sweet wife
dinshi"
Sakon ta ya fara cin karo dashi ' wani irin firgita yayi da ganin sakon tuni
jijiyoyin kanshi suka bayyana idanun shi sukayi jawur,
Har jiri ya fara daukar shi zai fadi dakyar ya iya tsaya wa da kafafun shi ya kife
kanshi a kan table din shi wasu irin mu gayen hawaye ne na tsananin bacin rai da
bakin ciki suka fito mai,
"Mubena I will never for give you' ya furta cikin bacin rai tareda dukan table din
da karfi har saida takardun suka watse,
Mukhtar ne ya shigo ya same shi a cikin mugun yanayin, cikin sauri ya karaso tare
da rike shi domin sai watsi yake da da kayan dake kan table din,
" Subuhanllah meye haka Abdullah? Wani irin karaji yasa hade da kuka'
"Mukhtar Mubena ta cuceni tayi sanadin tarwatsa min gida ta korar min farin
Cikina,
" please kamun bayani y'anda zan fahimta Kasani a duhu, "cikin kukan ya mai bayani
" Wallahi ina raga mata ne cos she is your sister amma wannan karon she crossed
All the line ,
Mukhtar ma yayi bakin cikin lamarin sosai tuni ranshi ya baci ya fita batareda ya
tsaya lallashin Abokin nashi ba,
Gidan su ya nufa, dai dai ta fito daga kitchen dinsu tana rike da cup me dauke da
ruwan zafi bai ko tsaya sallama ba ya dauke ta da mari lafiyayye,
Saida ruwan ya zuba Allah ma ya so su bai zubo musu a jiki ba, maman shi dake zaune
tun Shigowar shi tayi saurin tasowa domin jin ba asin marin,
"Mukhtar meye haka me tayi maka ? " MAMA kibar ni in jima yarin yar nan na ce ina
sonta taki ta je tana so ta kashe Auren da bata San mafarin shiba,
"Ni kamun magana a natse kana min hargagi ' a dole ya saita kanshi ya mata bayani,
maman ma taji ba dad'i ta kalle ta,
" kai Mubena Amma baki kyauta ba ya zaki shiga soyayyar da bakisan Asalin ta ba' ke
kin San tarihin wannan Auren kuwa a Gaskiya kin tafka babban KUSKURE kina ya mace
kike cushe ga na miji,
Matar cushe bata daraja ba k'imar ya mace bace ba waye wa bace, saurin gyara
tsayuwar ta tayi ta kalli MAMA'
"Yanzu Mama me kike nufi? wato bakyason farin Cikina? Kinfi so in mutu da ki tai
make ni?
Kuka ta sanya " Wallahi yau dole inyi kukan rashin uwa da tana nan dole ta Goya min
baya Amma yanzu yazo ya dake ni a kan gaskiyar zuciya ta to Allah ya isa,
"Kuma wallahi idan Allah yayi ba w'anda ya isa ya hana domin rabo zai iya k'isa ,
Tajuya fuuu zata wuce yayi wuf zai cafko ta mama ta rikoshi,
"Mukhtar kyale ta dibar Albarka take ji kanajin magan ganun marar kunyar? Oh ni
wannan zamani ina zaka damu?
" ka duba irin gatan da naba y'ar nan a yau ta k,e k'ashe kasa take furta min wai
tayi rashin uwa,
"Mama da kin barni yau na saita mata tunani, " aa ba za ayi haka ba, "yarinya
marainiyar Allah barta duniya ce ai Wanda bai zoba ma jiran shi take
" nidai ki mata iyaka da Abokina kuma Wallahi duk Abinda yayi mata ita taja baruwa
na,
Ikon Allah ne kawai yakai ta Zaria lafiya, domin ba a hayya cin ta take ba, a kofar
gidan su ta faka bata tsaya bata lokaci ba ta shiga,
Ko sallama kasayi tayi domin sai yanzu wani mugun kuka ke shirin zuwa mata,
A zaune Hajiya take tareda wata y'ar dattijuwa dake taya ta zama a yanzu saboda
zaman kadaici ta kawo ta cikin dangin ta don tsohuwar batada wani gata itama tazo
ta d'an gwali arziki,
Shigowar ta yasa Hajiya tashi zaune da kyau " Allah ka hada ni da Alheri ni salame
"ke lafiya ? Da yamma cin nan?
" ina mijin ki? Wucewa kawai tayi cikin dakin ta batareda ta iya cewa komai ba,
"Tana shiga tasa kuka, " kande ki tai makeni ni salame Allah kasa muji Alheri, "to
yaya kitashi kiji bamusan sanadin zuwan ta ba,
Yunkura wa tayi ta shiga ta tsaya a kanta" Ummu irin wannan shigowa ai Saiki samin
hawan jini "me ya faru?
Ganin hankali n tsohuwar ya tashi dole ta natsu ta share hawaye ta fara magana,
" ni ba komai bazan zauna a Kaduna ba, "toh babbar magana, " fada kukayi? "Aa nidai
bazan zauna da shi ba ai tun farko ba sonshi nake yiba dole yayi mun kema kin sani,
" toh koda naji "yanzu saboda kuma ina tsohuwar banza sai in zo in Ajiye ki a nan
bayan kina da,dakin ki'
" Ummu na d'auka kina da,hankali Ashe baki da shi kindauka ni mahau kaciya ce ni
toh Wallahi badani ba wannan haukar "dama gani ake banason hadin yanzu in daure
miki ki zauna min a gida to badani ba ko dai ki koma ko ki tafi gidan ubanki bazan
zama tsohuwar banza ba,
Sakin baki tayi kawai tana kallon Hajiyar " Hajiya ni kike kora? "Yo ko ubanki ban
kora bare ke inace da farko lafewa kikayi gidan mijinki saida hatsaniya ta tashi
tsaka nin ku shine zaki kwaso kafa Kizo min to badani ba,
" wai ni Hajiya wace Alkibila kike bi? "Tashi ki koma gidan mijin ki yanzu tun muna
shedar juna "
"Wai da gaske kikeyi ko wasa Hajiya ? " Wallahi kinji rantsuwa bazaki kwana nan ba,
"matan zamani kuna da abin mamaki idan dad'i yazo ku cinye a gidan miji Kuyi lukus
idan akasin hakan ku dawo gida to da sake kije ki cinye matsalar ki ke kadai kamar
y'anda kika cinye dad'in.......✍
*Allah yasa iyayen mu sugane, dama mata su gane cewa ba komai a cikin yaji sai
bacin rai ko ince zubar da mutunci Allah yasa mu gane ya kuma bamu hakuri da
mazajen mu, don zamanin nan duk macen da tace batada matsala a gidan Auren ta tayi
karya saidai muce Allah kabamu ikon iya hakuri,*
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
4⃣3⃣
Bata taba ganin Hajiya tayi mata haka ba tsawon tasowar ta, tasan fushi takeyi
tunda tun lokacin da tace ta biyo ta taki,
A haka taja kafafun ta cike da fushi tayi waje hawaye na zuba, batajin zata iya
fadawa kowa wannan damuwar ko da kuwa su Hajara ne'
Gidan kakan nin ta ta nufa Gwaggo Amina ce a zaune tana kad'i maganin zaman banza,
itama tayi mamakin Shigowar ta a yanzu,
"Ummu yau kece a gidan mu lafiya? " Hajiya ta koro ni, "Bangane yaya ta koroki ba
ina gidan mijin ki ko ince ina mijin ki?
" yana can Kaduna, "to ke me kikazoyi? " na gama zama dashi ni nadawo nan shi ne
Hajiya ke korata,
"Ture Abin kadin tayi gefe ta zuba mata ido' kafin ta fara magana'
" Ummu anya? Yanzu da girman ki da kike kira ma kanki zaki yiwo wa kanin bayanki
yaji inba Abin kunya ba sannan da wannan katon cikin naki
"Aa yaya tayi dai dai koni ba barinki zanyi ba saidai in yi Abu daya tunda yamma
yayi gobe da safe zaki koma dakin ki,
" a Gaskiya bakiyi wayo ba Ummu ba haka mahaifiyar ki take ba "ita mai hakuri ce
har tabar gidan duniya ban taba jin kanta da Muhammadu ba " to kema ki dauki wannan
halin ki rika hakuri duk da bansan me ya hada ku ba Amma ki yiwa kanki fada,
Tayi mata nasiha sosai har jikin ta yayi sanyi tareda da na sanin tahowar ta gashi
tun Fitowar ta bai kirata ba,
Har zuwa dare tana ta duba wayar ta kozai kirata Amma shiru ko dai baiga sakon ta
bane' kila bai gani ba don da yanzu ya biyo ta,
Abdullah dai a ranar kwanan bakin ciki yayi domin Ummu ta bata mai rai duk irin
rokon da yake mata Amma saida ta bar gidan shi bayan tasan bazai iya daurewa rashin
taba a Gaskiya dole ya nuna mata KUSKUREN ta wannan karon koda shi kanshi zai cutu,
A haka yaga wayewar gari da wuri ya isa Asibiti yau yana zuwa ya fara duba patients
dinshi cikin dauriya,
Bayan ya koma office din shi ya kunna wayar shi tareda zubawa Hoton su ido w'anda
suka d'auka shida ita suna zuba dariya sunyi matukar yin kyau,
Hannun shi ya dora saman kuncin ta wurin dimple dinta shima yayi murmushi kafin ya
d'an hada rai ya furta "why Ruman?
" kinsan bazan iya jurewa ba kika tafi kika barni harda baby na Am not Happy with
your Action,
Shigowar kiran Mubena yasashi kara hade rai yayi saurin dagawa domin yana neman ta
wanted yasan kuma zata kawo kanta,
'Hello" ya furta a hankali , jin irin Amsawar da ya yi mata yasa ta jin dad'i ta
yi saurin Amsawa,
" Hy sweetheart ya kake? "Lafiya, Kefa? " kalau nake saidai ina kewar ka don Allah
inaso ingan ka,
"Ba damuwa u can come, Wani irin zabura tayi Wayyo dad'i da gaske ka y'arda inzo? "
uhm Am All yours,
"OK ina zanzo ta fada jikin ta na rawa "ina kike so ? Office din ka " nop saidai
gida "OK yanzu zanzo,
Wani irin murmushin mugunta yayi ya mike ya dauki key din motar shi ya fita "
Hajiya Mubena tuni ta shirya ta nufi gidan shi cikin kwalliyar ta ta daukar
hankali,
Ta riga shi isowa ba bata lokaci mai gadi ya bude mata gate ta shiga cikin jin
dad'i. Kanta na rawa ita a la dole tazo wurin masoyi,
A bude ta samu falon kai tsaye ta shige kamar na tshoho tana kara'i raya ta samu
kujera ta dora kafa daya kan daya,
Kallon falon take tana Ayyana y'anda zata yi Rayuwa a cikin wannan tamfatsetsen
gidan, ya shigo cikin shigar kana nan kaya farare hannun shi daya sanye cikin
Aljihun wandon shi dayan na rike da wayar hannun shi,
Saurin tashi tayi ta zuba mai ido tana kallon tsantsar haduwar shi ta nufeshi da
gudu tareda rungume shi, tsayawa kawai yayi tana kwakume dashi sai daga baya ya
dago ta da hannun shi daya
Fuskar shi a daure yace kinyi wanka kuwa? Saurin kallon jikinta tayi domin tasan
tayi karshen wanka don ko mama saida ta yaba da Adon ta
"Banyi kyau bane? " nop naji kamar wari ne kuma kyau ai ni na mace daya nake iya
ganewa,
"Murmushin yak'e tayi ta ce idan bai yiba zan iya yin wani wankan, tabe baki yayi
ya nufi kujera ya zauna ya zuba mata ido shi bayan gashin dokin da ta zuba da kuma
farin da yana gani yasan bilicin ne ga wasu fingers da ya tsani gani a jikin mace
sai wani kirji da kana gani kasan har da ciko kai idan ba karya yayi ba ko hips
dinta ciko ne,
Tayi bala'in tsarguwa da irin kallon da yake mata ta kalli jikinta " seat ya bata
umarni tayi saurin matsowa jikinshi zata zauna yace " nop seat there ya nuna mata
kujera mai facing dinshi,
Magana zamuyi' zama tayi tace ina jinka' gyara zama yayi ya kalleta " ki fadamin
Abinda kika fada ma matata ta bar gidana sannan Muyi maganar Abinda kikeso A
wurina,
Wani dadi taji "zaka y'arda ka Aureni? " ki fadamin Abinda nakeson ji first, jakar
tuni ta yimai bayanin video da ta d'auka a office din shi ta kuma fadamai zuwan ta
har gidan shi ta nuna ma Ruman,
Wani murmushin takaici yayi irin w'anda yafi kuka ciwo, "OK yanzu me kikeso? " ka
Aureni please,
"Meyasa kikeso in Aureki? " inaso inganni a matsayin matar ka saboda ina sonka
sosai zanyi ma biyayya,
"OK Amma ni inason budurwa ne ba bazawara ba " kallon shi tayi wani iri "ni ai
budurwa ce' yazan San hakan?
Bayan kinfadamin kina fingering kanki that means you dis virge your self, girgiza
kai tayi " Wallahi ba Gaskiya bane kawai inaso inja hankalin Kane Muyi Rayuwa nasan
dole ka Aureni idan har kasan cewa ni budurwa ce kuma na d'auka kai ma kana neman
matane ganin ka bature,
"Hmmm ya furta tareda murmushin takaici, " OK yanzu idan nace ki bani kanki zakiyi?
Cikin rawar jiki ta mike Wallahi zan y'arda idan har zaka Aureni,
Kallon zakici ubanki yayi mata sannan ya mike yace follow me, binshi tayi cikeda
rawar kai ya shiga cikin wani daki na daban na tarban baki
Nuna mata bathroom yayi " kije kiyi wanka ina jiranki' ta a jiye Jakarta tareda
ajiye mayafin ta nufi bathroom din,
Zama yayi yana danna wayar hannun shi, cikeda basarwa fitowa tayi sanye da kayan ta
ya dago kanshi "umm ki cire wannan gashin ya nuna mata Almakashin dake a jiye akan
mirror,
" Bangane ba, "banason suma inaso ki aske shi yanzu for me" ya furta yana mata
killer smile,
Ganin murmushin shi yasata d'auka ta yanke shi tas sannan ya dago kai "hmmm ki cire
kayan jikin ki inaso inganki necked
Kallon shi tayi cike da tsoro domin baza taso ya ganta Tsirara ba don iskan cin
nata abakine kawai duk karyar iskanci ne
" to ka kashe haske ta fada muryar ta na cracking' "no sweety inaso inga Abin
burgewar da akeson Jan hankali na da su a zahiri idan sunyi min sai in Aureki,
" anayin Hakane ta fada tanaja baya domin matsota yakeyi "kinga ranar kin taba min
kayan aiki banshirya ba yanzu kuwa na shirya kingani,
Ya nuna mata jikinshi da yayi wani irin mikewa " ai wani irin uban tsalle ta buga
taja baya, domin bata taba gani irin tashin ba
Amma saboda duniyan ci ta basar "to to ni bana cire k.... Caraf ya rikota tareda
fisgo ta zuwa jikin bango ya fincike rigar ya yageta tayi saurin dafe kirjinta,
Riko Hannayen yayi tareda fisge breziyar da tayi a cuci da ita bakin shi ya tabe
domin yana ganin kirjin ta kamar na Bera tuni yakara raina mata wayo ga kan dama ta
aske
Gaba daya ta gama kaiwa bango da salon wulakan cinshi baya ya tun kuda ta ya danne
ta kamar kaza ya fincike wandon mai hade da ciko ganin ta yayi kamar wata one
runtse idanun ta kawai tayi,
Wasu hawayen bakin ciki suka zubo mata baya ya koma ya Ciro hand gloves ya sanya
tareda matsowa kusa da ita ya tale kafar ta kamar Wanda zai karbi haihuwa hannu
kawai yasa ya yage pant din jikin ta,
Wani irin ihu tasa ta matse kafar ta tareda kokarin tashi zaune'
"Enough Abdullah ya isa wulakancin saboda kawai nace ina sonka shine zaka wulakan
ta ni to na hakura Allah ya bani mai sona,
Tafara kokarin saukowa yayi dariya irin ta mugunta" tun yanzu kin karaya ina ai da
Saura ni ban hakura ba sai naga wurin da zan shiga idan zai iya d'auka na,
"Danne ta yayi ya sa mata hannu tana ihu ya ware kafafun ta ya tura hannun shi
kasan ta,
Akuya kawai bunsura Wallahi baniba ko wane namiji ya rabeki takaici zai kwasa
kinada illoli da dama a tareda ke
Kin korar min mata saboda son kanki me kikeda shi da zai dauki hankali na ke ba
macen da zanji sha'awar ta bayan Ruman kalli nan,
Ya nuna mata gabanshi kinga da farko ta tashi Amma ganin mummunan surar ki ta
kwanta kamar batada lafiya,
Kinyi nasarar shiga tsakani na da farin Cikina Amma kisani Wallahi next time Abinda
zanyi miki ko kare bazai Ciba,
Ya juya zai fita ya tsaya ya d'an juyo "uhm kije kiga likita yayi miki dinki domin
rijiya ma tafiki matsewa duk namijin da ya shige ki sweeming kawai zaiyi a ciki,
Domin kina nan kamar kwale kwale, ya kuma darawa zai wuce ya juyo " please pack
your attachment I hate it,
Fita yayi kawai tabi bayanshi da kallo ta fasa kuka mai ciwo yau taga tantagaryar
wulakanci lallai ta koyi hankali Abdullah ya nuna mata KUSKUREN ta cikin ruwan
sanyi ba duka ba Zagi,
"Yana fitowa tana shigowa kallon ta yayi tareda jin farin cikin dawowar ta Amma ya
basar ya wuce dakinta batareda ya kalleta ba,
Kallo tabishi dashi na irin share tan da yayi " kaya ya dakko a cikin Waldrop din
ta riga da zani ya fito ya koma dakin tana wuri daya ta kasa matsawa
Komawa yayi ya wurga mata "ki shirya kifito matar gidan da kika kora ta dawo kafin
ta fasa miki kai kibar mata gida,
Jikin ta na rawa ta fara zura kayan tana kukan bakin ciki domin wulakanci n shi
kawai ya isheta a yau kafin zuwan na matar gidan,
Jiranta yayi ta yafa mayafi ta taso kanta a duke domin batako son kallon shi ta
kwashe sumar da ta Yanke ta zuba a handbag dinta sannan ta fito yana murmushi n
mugunta,
Kallon kananan kayanta yayi wato bra dasu pant din ta ya kwaso su tareda fitowa
yabiyo ta
Ruman na tsaye a wurin ta kalle ta gaban ta yayi mugun faduwa wato fili ta basu
suyi iskancin su
Saurin matsowa yayi gab da Mubena " my bena ga wa innan ki saka a jaka kin manta
dasu,
"Karba tayi cikeda kunya ta saka a Jakarta ta fita tana hardewa ta nufi waje binta
yayi da wani irin kallo tareda cewa " sweet idan jikin yaki ki kirani zanzo inyi
Miki dinki nasan kinji jiki,
Ita kuwa tuni tayi waje, Ruman dake tsaye cikin tsananin shock wani jiri ya
kwashe ta tayi baya zata zube cikin sauri ya isa ya rikota
"Please idan bakyason kanki ni inason Cikina ki kula domin bazan dauki Asarar
Abuna ba nasan wahalar da nasha kafin insamu Abuna domin haka ki kula zan iya
daukar mataki akanshi idan har kikamun ganganci dashi
Ya saketa ya juya ya fita ta bishi da kallon mamaki Abdullah ne ya mata irin wannan
wulakanci bayan Abinda idon ta ya gane mata ?
Wani irin kuka tasanya tareda dafe kanta saboda jirin dake. Kan daukar ta dakyar ta
lallaba ta zauna tana mai kukan dana sanin tafiyar ta domin ita taba mijinta kafar
da ya kawo wata mace har cikin gidan ta....✍
*Matar Soja*
[10/8, 4:34 PM] Offἶეἶმl 🐅 (Oum Janan)💕: 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
*Aslm my fan's ina matukar godiya da irin kaunar ku a gareni a Gaskiya naga kauna
daga masoyan Fenerh na Asali I really appreciate ur love and concern Allah ya saka
muku da Alkhairi*
4⃣4⃣ 4⃣4⃣
➡4⃣4⃣
Dakyar taja kafar ta ta isa cikin dakin ta ta fada gado ta sanya kuka mai cin rai
yanzu ita Abdul zaiyi wa cin fuska?
"Lallai zata nuna mai ita din macece da bazata taba daukar rainin hankali ba sai ta
gasa mai aya a hannu sai ta,nuna mai Asalin Ruman,
A ranar haka ta kwana cikin damuwa shikuwa dauriya kawai yayi domin dakyar yaga
safiya, wai
Shi zaiyi mata horo gashi horon ya dawo kanshi domin a wahal ce ya kwana a ranar,
ya matsu safiya bata waye ba,
Ita kuwa tana tashi ta shirya cikin wani skintight tree quarter na mata ya kamata
dam ta hada da singlet din shi pink tayi packing sumar kanta a gefe da ribon kalar
kayan ga cikin ta ya fito das tayi matukar kyau,
Ta fito dakin rike da emtyn goran fresh milk din da tazamo Abincin ta yanzu,
hankalin ta a kwance ta nufi hanyar kitchen din ta,
Suman zaune yayi domin yana zaune a kujerar falon yana tunanin y'anda zai tunkareta
don Gaskiya yafara gasuwa cikin kwana biyun da kawai yayi batareda ita ba,
Gashi karon farko ta yimai mugun harbi da kyakkyawar surar jikinta mai hauka tashi
har wani irin dogon nishi yaja tuni idanun shi suka kad'a,
Ya kasa koda motsi har ta fito dauke da plate din gasasshen naman ta da ta gasa a
oven da ruwa ruwan shi yaji kayan kamshi da su kori yana tururi,
Ta na dosowa idanun ta ya sauka a kanshi yana zaune kamar ya zunduma ihu tsabar
damuwa, a Gaskiya ya kashe kanshi garin horata,
Kallon shi tayi cikin minti kadan ta karanci yanayin shi ta hango damuwar shi a
zahiri don haka ta kara daura damara ta canja taku da gayya ta nufo tsakiyar falon
tana juyi kamar tarwada Wanda ya kusa tafiya da sauran numfashin da yake d'an
hurawa,
Saida tayi kamar zata nufoshi ta kauce gefe ta zauna tareda lankwashe kafar ta ta
ajiye naman ta a gefe ta fara yankowa da y'ar karamar wukar ta tana lumawa a
kyakkyawan bakinta,
Bakin yabi da kallo tareda Jan dogon numfashi ya yunkura ya sa guiwar shi a kasa ya
matsa wurin ta idanun shi sun ciko taf da hawayen fitina,
"My one" ya kira sunan ta can kasan makoshi dakyar ma Kalmar ta fito daga bakin
shi,
"Tayi mai biris kamar bada ita yake ba a hankali ya riko hannun ta jikin shi na
rawa " please my life forgive me.
Fisge hannun ta tayi ta kalle shi cikin basar wa "Abdul nace kamun wani Abu ne? "
aa ni nasan nayi miki laifi don Allah ki yafe min ba Abinda kike tunani bane ya
faru,
"Ke kinsani ina sonki sosai bazan taba iya hada soyayyar ki da ko wace irin mace ba
believe me my wife.
Wai gawa tayi sannan ta dawo da fuskar ta a kanshi, " ba Mubena a nan fa Abdul nice
Ummu Ruman,
Kaje wurin ta ni yanzu ina zaman Cikina ne ina haife shi zan kara gaba don bazan
kaiwa kowa wahala ba kaida kayi shi kai zaka yi d'awai niyar kayan ka,
"Ruman ciki na ne wahala? Babyn nawa ne wahala? Gudan jini na ne kike kira da
wahala? " OK naji ni dai yanzu Kice duk abinda kikaga dama nidai bazan iya irin
wannan zaman ba ki San y'anda zakiyi dani nidai ina bukatar kulawar ki,
Ya mike tareda mikewa ya zauna gefen ta ya rungume ta yana Ajiyar zuciya "please
stop All this I can't take any of it ya isa haka,
" kokarin tureshi tayi ta na magana " ni dai kaga ka barni bana bukatar ka ba na
son damuwa kayi rayuwar ka inyi tawa.
"Bazan iya Rayuwa bake ba Ruman, " amma na tafi baka damu da halin da nake ciki ba
ka dakko macen da kake so har cikin gidana don wulakanci,.
Ta furta idanun ta sun cicciko da hawaye yayi saurin rike mata fuska yana girgiza
kanshi "trust me my wife noting happened I can proved that to you,
Me zaka fadamin bayan naga komai? OK ina zuwa, ya mike cikin sauri ya dakko laptop
dinshi ya kunna mata
Tun Shigowar Mubena gidan har Abinda ya faru a tsakanin su duka yayi recording,
Abin ya bata dariya sosai amma ta matse tareda kallon shi,
" me yasa ka yi mata haka kuma kasan cewa abinda kayi ya sabawa Addini?
Me yasa zaka sawa macen da ba halalin ka ba hannu? Ta furta cikin daure fuska tare
da ture hannun shi da yake kokarin tabata,
"Don't touch me with your hand, ido ya zaro " why ? Ya zaka taba wata mace kazo
kace zaka taba ni. Kanshi ya dafe idanun shi sunyi ja ,
"Na shiga uku ni Abdullah " Ruman yanzu me kikeso inyi w'anda zan faranta miki ?
"Ni dai ina rokon ki da ki yafemin please,
Ya furta muryar shi na rawa ido ta zubamai domin tasan yana matukar kaunar ta itama
kuma tana son mijin nata sosai,
Amma dole ta d'an kara hora shi kadan kafin ta bada kai don haka ta mike tayi
kitchen da plate din ta da ta cinye naman ta ya bita da idanu kamar ya zunduma ihu,
" nidai na shiga uku da matar nan tawa ya furta a hankali, tana fitowa ta nufi
dakin ta ta garkame idanun shi a waje,
Yanzu kofa take rufewa saboda shi "a Gaskiya da sake bazai yuwuba, karar wayar shi
ya dawo dashi cikin natsuwar shi,
Mukhtar yagani a kan screen din wayar shi yayi picking tareda yin tsaki,
" friend ka fazo Asibiti ni nayi Zaria farin Cikina nason gani na don haka ni
natafi , waini ban gane ba? Har kun shirya ne?
"To ka tsaya wasa ai baza a dauki lokaci ba nima zan shiga daga ciki in rama
wulakanci n ka,
Adawo lafiya, yawwa please meye yafaru tsakanin ka da,Mubena naga ta samu natsuwa ?
Har ya gama shirin shi yabar gidan bata fito ba, saida taji tafiyar shi ta fito
tayi Aikin da ya dace da tayi tare da daura damarar soya mai aya a tsakiyar hannu a
ruwan sanyi,
Ya dawo a matukar gajiye, ya zube a kan kujerar ya zubawa kofar ta ido yana burin
dora idanun shi akan ta,
Fitowa tayi cikin shiga mai matukar daukar hankali cikin shigar ta ta bahaushiya
Amma dinkin ya bayyana komai nata gwanin burgewa da kuma daukar hankalin mai kallon
ta
Gaba daya kuzarin shi ya dawo jikin shi ganin ta cikeda kissa da kuma wayewa ta
matso tareda rankwafowa ta saman kujera y'anda zai hango kayan kallon dakyau,
Tuni idanun shi sukayi masauki akanta jikin shi yayi lakwas saboda kasalar da ta
mamaye shi lokaci daya,
"Welcome" ta furta a hankali, dakyar ya iya Amsa ta da tank's idanun shi kamar su
fada jikin ts tsabar kallon da yake aika mata da shi,
Ta juya tare da cewa" wanka zakayi ko Abinci zaka fara ci? "Dakyar ya iya furta
wanka tareda Jan numfashi ya mike ya nufe ta,
Wata irin wa wuyar runguma ya aika mata dashi tareda kwakume ta yana Ajiyar zuciya,
Murmushi tayi kawai domin tasan ta mugun kunna fitinannen yaron don data irin
yanayin da ta shiga,
Please" forgive me my wife I need you very badly please help your husband,
Korarin b'anb'are hannun shi a kugun ta "kayi wanka ka gaji ta furta a hankali, "
nop bazan iya yi ba ki barni a haka,
"Muje in taya ka ko bakaso? Wani irin dad'i yaji ya zabura ya juyo da ita " inaso
mana muje my wife ya fada cike da jin dadi ya rungumo ta,
Saida suka isa cikin dakin ya saketa ya fara tubewa ta shiga bathroom din ta hada
mishi ruwa mai dumi Wanda,zaiji dad'in shi domin ta lura yayi matukar gajiya,
Shigowa yayi haka ba komai a jikin shi ta waro ido ta zuba mai tana mamakin halin
shi na rashin ta ido,
Kallon ta yayi tareda nuna mata towel din cikin salon shagwaba "yaki dauruwa towel
din aike ce kikaja kinsa yana ta kwance wa,
Kawar da Kanta tayi kawai domin ta gano shi sarai tace kazo kayi wankan kafin
lokacin Salla yayi,
Da tai makon ta yayi wanka sai binta yake da ido kamar ya cinye ta,
Cikin sauri ya shirya domin karatowar lokacin sallar magrib bai ci Abinci ba saida
suka gabatar da Salla ta zube musu Abinci a Capet ya baje ya kwashi gara tareda
zuba mata santi
" baby Abincin Nigeria Akwai dadi mu samman tuwo miyar taushi, tuni ta tuntsire da
dariya ta janyo d'an karamin filo ta jingina mai
Wani irin farin ciki ya lullube shi ganin dariyar ta harda k'yak'yatawa, miyar
taushe akace malam ba taushi ba'
"Kallon ta yake cike da so ya dora yatsan shi akan dimple dinta a hankali ya furta"
I love you so much Ruman,
"Be Happy Always I want to see you smiling All the time I love this ya fada yana
kara shafa fuskar tata
Ya dauki lokaci yana shafo fuskar ta saida aka kira isha suka mike tayi dakin ta
tayi wanka ta yi Salla tareda canja shigar ta zuwa nighty pink iya guiwa batareda
ta sanya komai ba ta fito domin dakko fresh milk din ta da ta zamo jiki,
Sukaci karo yayi saurin rikota " ina zuwa madam ki rika kula kodan Babyn mu ina
zakije ma yanzu ?
"Fresh milk zan dakko a kitchen, babu a frij dinki ne? 'Ya kare " OK ina zuwa ki
koma,
Da kanshi ya je store ya dakko carton na fresh milk din ya zuba a frij dinta sannan
ya koma ya kawo mata mai d'an sanyi kadan,
Kallon shi kawai takeyi yana bata tausayi tasan ba karamin so yake mata ba don haka
ma ta daura aniyar tallafawa rayuwar su,
Ta hanyar bashi kulawar da yake bukata, matsowa yayi bayan ya gama ya hauro kan
gadon madam zan duba baby na nayi missing dinshi kwana biyu'
D'an matsawa tayi tareda d'an Jan Aji " lafiyar shi kalau basai ka duba ba'
"Nop muje ma inyi scarning inga yanayin lafiyar kayana, kintashi tayi ya diro
tareda sunkuto ta kamar baby ya nufi dakin da ke dauke da kayan na urorin baturen
na aikin shi,
Shinfide ta yayi ya hada kayan Aikin tana binshi da kallon burgewa domin dole ma ta
y'arda Allah ya bata miji na tserewa sa'a
Kallon ta yayi bayan ya gama hada kayan Aikin " madam irin wannan kallon fa ai
Saiki hana ni aikin,
"Murmushi tayi ta d'an tashi " ka bani zani to ba komai a jiki na kuma kaga rigar
ba girma,
Kallon jikinta yakeyi ya dora hannun shi a kan rigar ya fara dagawa' "ai dama dole
ki cire rigar gaba daya domin bana bukatar ta,
" saurin riko hannun shi tayi tareda girgiza kai "no Abdul bazan iya ba ina jin
kunya, wani irin kallo ya aika mata,
" meye wannan ? Ya furta tareda shafo cikin ta " Tayaya kika sameshi ? Ki ajiye duk
wata kunya da son girma mu shakata my baby inason Rayuwa da matata,
Da wayo ya samu ya zame rigar duka yayi wurgi da ita ai tuni notukan kanshi suka
warware cikin tsananin jarumta yafara Aikin shi batare da ya gano me ya Aikata ba,
Duk ya rude da halittar jikin ta ya fita hayya cin shi, ganin irin yanayin da ya
shiga yasata mikewa ta dauki rigar ta ta sanya ta nufi dakinta domin tanaso ta d'an
ja mai Aji kafin ta sallama domin ita kanta tana cikin yanayin,
Ya dade a wurin kafin ya iya mikewa ya nufe dakin ta tun a bakin kofar ya yi wurgi
da sauran kayan shi ga badaya idanun shi sun rufe ita kawai yake bukata a halin
yanzu ji yake idan har bai samu ba zai iya samun matsala a yau,
Yakai makura wajen bukatuwa, yana isowa ya fara magana kamar zaiyi kuka" please
Ruman ki tausaya min mana horon yayi mun tsauri me kike so inyi miki ki taimaka
min?
Juyowa tayi cikin sauri ta janyo shi zuwa jikinta dama tuni ta gama shirya mai ta
jefa bakinta cikin nashi batareda ta bari ya karasa maganar shi ba,
Ai tuni na bar dakin domin naga Alamar yau wasan babbane na dawo falo na zabga
tagumi tareda tausayin Babyn don da Alama yau zaiji jiki, kafin inbi taushi in fara
Jan minshari
Asuba tagari,
Bude idanun ta tayi ta sauke su a fuskar shi ya tsare ta da ido kamar zai cinye ta
ga wani murmushi mai tsayawa a zuciya wani irin Annurin farin ciki ke fita a fuskar
shi,
"Good morning my wife" ya furta yana shafo fuskar ta " wani irin murmushi tayi ta
dan kauda fuska cike da kunya yayi saurin dawo da fuskar ta' no banason wannan
kunyar bayan kin gama hauka tani daren jiya kuma yanzu Kice wata kunya to banaso,
D'an kallon shi tayi cikin kulawa" Bakayi bacci bane wai kai? "Ina farin ciki zai
barni inyi bacci a yau bayan irin farin cikin da kika sanyani,
That is my real Ruman " ina feelings dinki yaje a da ? Yanzu Ruman dina da nake
mafarki ta dawo " tashi tayi saida ta sauka a gadon ta ce" ai sai ma na haihu zaka
gane ni ba ta wasa bace, ta furta tareda rugawa bathroom,
Ido ya zuba mata cike da jin dad'i " da gaske Kice inshirya zan more kenan wow"" ya
furta tana Jinshi sai dariya take mai saida tayi wanka ta fito daure da towel ta
samu baya dakin ta wuce gaban mirror ta dan shafa mai sama sama saboda yanayin
cikin batason wani kamshi sosai,
Ta fito fess da ita cikin wata doguwar Riga fubu ta material blue mai stones tayi
matukar karbar ta ta sanya d'an karamin hijab iya wuya sannan ta juyo yana tsaye a
jikin kofar ya harde hannu ya zuba mata ido,
Matsowa tayi gab dashi ta hura mai iska "my crush wannan kallon fa? Zaro ido yayi
tareda rungumo ta zuwa jikin shi" say it again wow,
"Me ne ? ta fada cikin basar wa" sunan da kika kirani yanzu I like it please" d'an
juya mai ido tayi tareda tsokanar shi " my young crush "
Murmushi yayi mai tsada " yeah I agree "ni karami ne a duk lokacin da nake tareda
ke domin kina sani inajina kamar wani jariri,
Harar shi tayi cikin wasa" Kaine yaron bayan abinda kake mun ko babba bazaiyi ba"
dariya yasanya mata me nakeyi miki my lovely wife"?
"Kafini sani " ni yunwa nakeji muje in nema mana Abinci sannan kuma ka canja wannan
shigar kayi kyau da yawa ' dariya ya sanya cikeda jin dad'in ta nuna kishin ta a
fili,
"Oh come on wa ma zata ga kyauna ni ai ba nida wani kyau' hmm a haka bayan nasan
kuraye na nan kai ni tare ma zamuje Asibitin yau kafata kafar ka"
"Wani irin dadi yau yakeji wai shine Ummu Ruman ke tarai raya haka,?
Abinci ta samu a shirye a table ta zuba mai ido da Alamar tanbaya? " uhm ni na
hada miki banaso ki wahala bayan nasan kin gaji da yawa jiya so ki huta,
Murmushin jin dadi tayi zaunar da ita yayi kusa dashi ya hada mata tea mai kauri
tareda zuba mata farfesun kayan ciki da kuma soyayyan kwai da ya soya mata sama
sama kamar source domin yafi Amfani a jikin mutum,
Bajewa tayi ta kwashi garar da. Mijinta ya shirya mata sun ciyar da juna cike da so
da kuma tattali,
Da taimakon shi suka kimtsa wurin sannan ta koma dakinta ta dakko jakar ta fara
tareda takalmin ta ta dakko wayar ta
.ido ya zuba mata domin ganin iya gaskiyar ta kenan binshi zatayi' "muje ko? "
waike da gaske kikeyi Asibitin zakije?
"To ka tsaya a nan ta karbi key din hannun shi tayi waje yabi ta cikeda mamaki da
kuma jin dad'i,
" ita ta bude katuwar motar ta zauna a mazaunin driver ta tayar ya zagayo gefen da
take" Hajiya ta ni zama zanyi ki tukani kamar wani mijin Hajiya?
"Kaifa kace Hajiyar ka to ka zauna kawai mijin Hajiya intuka ka, " dariya yayi yana
maijin dad'in yanayin da suke ciki ya zagaya ya shiga ta harba motar suka fita,
Kallon ta kawai yakeyi motar tayi matukar dacewa da ita ya dora hannun shi akan
cikin ta "baby na yau mun zama y'an gatan momy ko?
" dama ai ku y'an gata ne tuntuni' "an dai fara sonmu sosai yanzu shiyasa hannun
shi nakan yawo akan cikin ta har suka isa Asibitin,
Ta faka a gefen da aka tanada domin ajiye motoci sannan ta kalle shi" mun iso
malam"
Saurin juyawa yayi yaga har sun iso" ya bata fuska " har mun zo? "Uhm " bangaji da
kallon ki ba nidai'
"Fita kawai tayi ta zagaya tareda bude mai motar ta riko hannun shi " yana fitowa
ya rungume ta batareda ya kula da mutanen dake kai kawo ba a harabar Asibitin,
Mukhtar na gefe tun Shigowar su yake kallon ikon Allah " yau abin haka ya dawo kuma
toh?"
"Karbar jakar ta yayi ya rataya tareda rungume ta a gefen shi suka nufi cikin
Asibitin duk inda suka wuce kallon su akeyi'
Nurses din dake aiki a wurin tuni suka kama Kansu " lallai dole yaki kallon su a
she lafiyayyan fure ya. Ajiye a gidan shi yana tsunka,
Suna shiga office dinshi ya kwakume ta Hmmm " murmushi tayi ta dafe Hannayen shi
dake k'uibinta, .
"My crush" um" ya Amsa cike da kasala' kaje kayi Aikin ka zan jiraka anan.
"I can't" saurin juyoshi tayi ta fuskan ce shi da Alamar tuhuma "why?
" ya zaki biyoni ki kumayi expecting in iya yin aiki bayan kina tare dani'
"OK to kayi Aikin ka ni bari intafi' ta k'arbi jakar ta saurin riketa yayi "
please don't go" bari induba patients dina sai muje gida yau Amarci zamuyi"
"Wane irin Amarci da wannan. Ta fada tareda nuna mai cikin ta, shafawa yayi tareda
Dukawa ya bata fake a saman cikin sannan ya rungume cikin,
Kinsan cewa wannan Babyn yana kara mana Armashi a wajen hutawa koda yake inaso ki
haihu inga ai nihin jarumtar babyna,
Shafo sumar kanshi tayi yayi saurin lumshe ido tareda Jan numfashi domin Abin yayi
mai tasiri sosai,
"Kasan ko yanzu ni jaruma ce". Dagowa yayi tareda zuba mata idanun shi dake dauke
da ma'anoni da dama " ya dago habar ta tareda manne bakinshi akan nata tuni ta fara
karbar sakon shi tareda maida martani'
"Turo kofar yayi saida ya kusa bugewa domin ganin abinda sukeyi kamar mayu' har ya
juya zai koma ya ja ya buga kofar,
A firguce ta cire bakinta a nashi yayi saurin rikota tareda kallon kofar " harde
Hannayen shi yayi ya zuba mai ido,
"Malam yanzu saboda Allah Aikin da zamuyi kenan a yau? " Kaifa d'an sa idone ya
zaka dakatar da mutum yana morewa koda yake rashin mata ne ke damunka,
"Eh ba laifin ka bane amma karka damu nima nakusa kuma saina rama duk wulakanci n
ka agareni,
Ita dai kunya duk ta rufe ta tama kasa hada ido da mukhtar din,
" Amaryar mu barka dai " ya furta cike da tsokana' wace irin Amarya kana ganin
maman twins Abdullah ya fada cike da tsokana,
To naji kaga duk kasata jin kunya nidai kazo munada c.s a yau,
.OK ku shirya ina zuwa yanzu" yana tafiya ta tureshi tareda Hararar shi nice maman
twins ko? Uhm my baby ki jirani bari ingani '
Zama tayi akan kujerar zaman shi ta zubawa office din shi ido ba wani tarkace daga
gado sai table da kuma firij din shi dake gefe ga kuma coffee machine a samanshi
hade da cups,
A kan gadon ta koma ta kwanta tareda kunna wayarta ta fara kiran hajara,
"Yar gari kinboye ' ta furta cike da fara'a akan fuskar ta' " kedai bari abubuwan
ne ya Oga ? Lafiyar shi kalau muna tare da shi a office,
Wani irin ihun shakiyanci ta sanya "Kice kin hau hanya Queen" ah ba dole ba kuraye
nakai hari'
Da kitsaya kallon ruwa kwado ya miki kafa, wai ina labarin mutumin ki ba a daidai
ta bane?" Ai ni tuni na shafe shi da mukhtar nakeyi nima zan shiga inji kalar
soyayyar yaran,
Na gabatar dashi a wurin Dady Saura a shafa fatiha kawai na matsu nima inbi
sahunku,
,ga Sumy ma ta kwashe tana nan tafara lau layi "kai haba ? Dariya suka sa ta ce
bari inkira ta inji inkuma rama tsiyar da tamun '
Ta dauki lokaci tana waya da kawayen ta kafin ta kira Hajiya kaka suka d'an taba
dramar su tana ta Kwasar dariya a haka ya same ta ido ya zuba mata cikeda so har ta
katse ta diro "
My crush "zanje gidan Baba kafin ka gama Aikin kar intakuraka " matse fuska yayi
"banyar da ba ki jirani ingama muje tare.
Dariya tayi " OK as you wish my crush, shafo fuskar ta ya shafo that's my wife,
A haka suke tafiyar da rayuwar su cikeda so da kuma tattali a haka har cikin ta ya
kai wata tara lokacin yayi girma sosai ga Hajiya tasa tsiya Adawo mata da jikar ta
ta haihu a gabanta,
Shikuwa shugaba yace atafau ba inda matar shi zataje momy da Dady duk sunyi Jan ido
yaki baba dai cewa yayi Abar mai matar shi kawai,
Kaka magaji ya ce ita ta shirya ta koma gidan har a haihu don duk hankali ba Isar
su yayi ba daga ummun har Abdullah......✍
"Nikuma nace Zako kisha kallo Hajiya domin ni Kaina ba karamin mugun gani nakeyi ba
don sun fara kashe min karfin ido,
*" godiya Mara iyaka my fan's wlh banida bakin gode muku Allah yasaka muku da
mafificin Alkhairi naga kauna naga kulawa Allah ya bar kauna I really heart you*
Takun ce dai
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
*I dedicated this page to you uwar gida kuma Amarya a gidan baban jiddah dake nake
kawar rufin Asiri ina Alfahari dake Hajiyata Allah ya bar kauna*
*The whole page is urs Hajiya sa'a datu Allah yayi miki minister of education*
➡4⃣5⃣ 4⃣5⃣
4⃣5⃣
Ina labarin Mubena ? "Tun ranar da Abdullah yayi mata wulakanci ta shiga natsuwar
ta tuni ta saita kanta mama kanta tayi mamakin canjawar ta don har ladabin dole ta
koya,
Mukhtar harda godiya yayi wa Abdullah" friend duk da bansan mai ya hadaku da Mubena
ba ina matukar godiya domin ka saita mana rawar kanta,
Ya d'an ji kunya kodan mukhtar yasan ya yi crossing limit dinshi duk da ita taja
dole ya bata hakuri idan ya ganta,
Hajiya dai ta shirya tsab zuwa zaman jego ta tanadi komai nata na jego har da
itacen ta na jiko a gidan bature tab,
Tayi kira har ta gaji yazo ya tafi da ita yaki. Ai tuni ta tadawa Dady balli yau ta
ce ita sai KD dole ya Ajiye commitment dinshi ya kwashe ta sai KD,
"Suna tsaka da jin dad'in su a falon su dagasu sai tree quarter da kuma singlet s
yana matsa mata kafafun ta da suka kunbura tareda yi mata complain " baby ina
hanaki cin salt shi ke kawo wannan kumburin wurin me ciki Amma bakya ji'
Ya fada yana kallon ta " nifa maggi kawai nake ci Kasani bana girki da gishiri'
"So meye a species din ai rabi gishiri ne a ciki so zan fara dafa miki duk abinda
zakici da Kaina yanzu and then ki daina shan wannan yajin kar ki haifomin yaro da
ciwon ido,
Kallon shi tayi cike da shagwabar ta" hmm kullum warning daya nidai in haifo cikin
nan in huta da ka ida ni matar likita,
Dariya yayi yana rungume ta "uhm kinaso in sa idone a cutar min da baby bayan ina
fadawa wasu ni kuma insa ido a nawa,?
" hmm masu baby"' "eh sai ma yafito zaki gani ' " ni nafika matsuwa kaga kirjina
har nauyi yake mun yanzu saboda cikowa,
Kallon kirjin yayi ya sanya hannun shi ya daga rigar ya zuba musu ido" hmmm inason
su a haka ina hutawa da kayana kuma da Alama yarona zai samu wada taccen Abinci ba
sai mun nema mai na gwangwani ba,
Zai sha har ya ragewa baban shi' ya furta tareda dora bakinshi akansu.....
Karar karar rawar kofar Shigowar ce tasashi tsayawa tareda buga tsaki who is that?
Ya mike cike da jin haushin an hanashi shakata wa ,
Dariya ta sanya mai " my crush baka koshi ne ? Ya zan koshi kullum kara ni ima
kikeyi.....
Maganar tsayawa tayi a makoshin shi lokacin da yayi ido biyu da Hajiya kaka da ku
ma Dady rike da katuwar Jakarta '
Turus kawai yayi yakasa koda motsi " kauce mun kar in tureka ka tsaya min a hanya
to nazo tunda kaki dawomin da ita tunda ni ban isa ba ai nasa w'anda nake iko
dashi ya kawoni,
Matsawa yayi ya gaida Dady tareda cewa Dady ka shigo daga ciki "
Ina sauri ne Amma bari inga doughter na Momyn ka na gaishe ka tunda ka guje mu
yanzu ko?
Shiga sukayi yana Sosa keya tareda dariya "zamuzo Dady aiki ne yanzu yayi yawa ga
kuma bab.. Um Ruman shiyasa na ke zama gudun kar haihuwar tazo bana kusa,
" yayi kyau sosai hakan ka kara kulawa son' ita kanta tayi mamakin ganin Hajiya
kaka ta yunkura tareda daura zanin ta ta gyara mayafin dake kanta domin tsaro dama
ta Ajiye su,
"Aa zauna Allah sarki Ummu sannu kin hadu da miji Mara hankali yanzu haka kika
tsufa amma ya ajiye ki ke kadai a nan?
Ta gaida Dady cike da kunyar ganin ta da katon ciki sannan ta wuce domin kawo mai
abin motsa baki,
" dawo Ummu nasan me zakiyi k'arki damu bana bukatar komai innan mu kawai na kawo
so zantafi inada meeting,
Kudi ya Ajiye mata rafer guda yan dubu dubu sannan ya wuce Abdullah ne ya rakashi
har mota "Dady kai ka tuko?.
" so kake in hada uwata da driver? Nop Dady a sauka lafiya ya koma cike da jin
haushin tauraru wa mai wutsiya wato Hajiya kakus,
Tana kan fada ga Abinci tasa An shirya mata domin yanzu tanada masu mata Aikin
komai saboda ciki
Tanaci tana masifa " na kira nakira yaki kawoki ke kuma Mara hankali kinzauna ko a
jikin ki?
"Itadai tayi tsit ba tacewa don tasan halin kayar ta " idan ankai miki ita me zaki
mata kinzo sai damun mutane kike da fitina wai ma me zaki mana?
"Uwarka hadiza zanyi da ubanka Jafaru da Muhammadu zanyi Mara kunya yanzu d'an
magun gunan da muke ba mai juna biyu na saukin guiwa tun wata takwas ko daya bata
shaba waiku turawa to na jiko mata kuma shi zai zama ruwan shanta har randa zata
haihu,
" ta janyo wata katuwar gora a cikin jakar ta "kinganshi ki fara tun yanzu ms"
saurin fisge gorar yayi ya bude tareda sawa a hanci wani irin gafi yaji ya zaro
ido,
.Hajiya wannan Abin zata sha? Eh "ubanka ma Ansha a cikin shi " tsb to wallahi ba
mai durawa ciki na wannan abin
"Zamu gani nidakai d'an halak ka fasa muna nan " ai zubarwa zanyi" ka zubar min da
magani sai ranka ya baci kuma sai ubanka ya dawo tunda shi na isa da shi shi idan
ya fada zakaji ko,
Allah ya baki hakuri ni bari infita tunda kinzo' "wata irin dariya ke cinta domin
dramar na burgeta Hajiya masifa Abdullah daukar magana Akwai zama kenan tab,
A haka ta kwana biyu suna zuba drama sai in ya fita aiki ake zama lafiya yau ma
zaune suke a falon suna kallon tashar MBC 2 sunayin the Martian film din ya dauki
hankalin ta
Hajiya nata sababi" waiku bakuda nta ne na hausa mutum yaga labarin kasar shi sai
na turawa kukan gidan ku da gyara,
"Kallon ta tayi " Hajiya bakya gajiya da korafi? "Nayi y'ar nema ke da mijin ki duk
kun raina ni to mu zuba nidaku ne,
" dariya tayi haba kakus din mu mai tuwon y'an gayu " ke kika sani dai "matse ido
tayi domin jin wani Abu da ya soke ta a Mara,
Yunkurawa tayi tace " Washh" saurin kallon ta tayi "lafiya dai " Marana"
subuhanllahi ko Abun ne ta furta tareda mikewa ta nufota
Wasa wasa Abun ya fara karuwa tuni Hajiya ta rude ta kasa koda taimaka mata a
hakan Abdullah ya iso gidan domin yana zaune a office yaji kawai yanaso yazo ya
ganta domin tunda EDD dinta ya cika ya kasa sukuni duk inda yake hankalin shi na
kanta,
Samunta yayi a cikin yanayin duk ta hada gumi ga Hajiya sai juyi take ta rasa maka
ma'
Cikin kidima ya kinkime ta zuwa dakin da ya tanada domin iyalin shi a cikin gidan "
Taimakon da ya kamata ya fara bata Hajiya na gefe tana kallon ikon Allah,
Ganin irin wahalar da jikar ta kesha yasa ta fita domin tsananin tausayi shi kuwa
ya yi iya dauriyar shi wajen ganin ya bata kulawa duk da wuyar da yaga tana sha,
Cikin ikon Allah da taimakon jarumin Likitan mijin ta ta sullubo mai katon bouncing
baby boy kyakkyawan gaske kamar ubanshi,
Kukan jaririn yasa Hajiya shigowa da gudunta tans hamdala "Alhmdulillahi Allah
nagode maka ni salamatu sannu Ruman kinga duk na rude bansamu ko hannu na jika miki
ba,
Harar ta yayi tareda Ciro hang loves din hannun shi ya canja wani saida ya yanke
cibin ya d'an kalle ta " baby kiyi hakuri in kwashe jinin saboda ciwon ciki ya fada
cike da tausayin ta domin ta galabaita sosai saboda girman yaron,
A hankali ya kwashe mata jinin ya mata Allura domin yaga Alamar sai yayi stitches a
wurin.
Ya dinke abarshi tsab sannan ya shirya ta saida yaga ta dawo tsab sannan ya koma
kan yaron shi yana mai hamdala da kuma farin cikin ganin gudan jinin shi,
Ai tuni kanshi ya fara girma wai yau shine ya zama Dady da d'an cikin shi, "
"Tuni ya fara yadawa y'an uwa da Abokan Arziki Hajiya ta wanke kayan jinin tsab
ta baza turaren wuta a burner,
Shi kuwa gogan yana nan kwakume da kyakkyawan danshi ita kuwa bacci takeyi sosai
saboda Allurar hutun da ya mata,
Yau miji ya kawoni " Hajiya tace ai Gaki ga shi nan yaro ya biyo ubanshi tsab Allah
ya kiyaye hali"
Dariya tasa tace" kai mama ai dana halin shi mai kyau ne, nidai ina wannan Auren
naga farar fata,
Ita ta hada mata lafiyayyan tuwo miyar kuka da kuma farfesun kayan ciki gefe ga
kunun sabara irin na y'an kebbi yana tashin kamshi saboda ruwan nono,
Su Dady kuwa farin ciki kamar me anyi jika momy tuni ta gama siyayyar ta a kasar
waje tuni ta hanasu ko siyan safa duk da uban ya yi nashi shima,
Abdullah sai rawar kai yakeyi ya zama Dady' tuni ya kara zuba kayan Alatu a dakin
yaran da ya shirya tun farko,
Ya kasa ya tsare ko nisa baya iyayi da cikin gidan zuwan mama bilki ne yasa shi
d'an fitowa don ya na dan jin kunyar ta Amma yanajin kukan yaron ya koma dakin da
gudu har suna cin karo da Hajiya,
"Oh ni salame yanzu ina zaka? " bakyajin yarona na kuka shi zan lallasa kuma ya
kamata yasha nono kafin komai,
"Toh Abu yazo inda akeyi ni bani wuri ta fada tana mai fita abinta mama na dariyar
su"
Ganin ta ya d'an tsaya kadan ta tashi "shigo Abinka Abdullah kyale mama kaji tayi
waje tana dariya,
Matsawa yayi bakin gadon ya zuba mata ido baccin ta takeyi hankali kwance
Wani irin murmushi yayi mai cike da tsantsar kauna da kuma farin ciki ya mike ya
garkame kofar sannan ya janyo spirit da Auduga,
Saida ya zuge zip din rigar ta sannan ya zameta ya zubawa kirjinta ido dake sheki
kamar ya kai bakin shi yakeji,
Ya dangwalo spirit din ya kama kan nonon ya fara gogewa domin cire bakin fatar dake
rufe wurin Fitowar nonon da kuma fitar da datti,
Zafin gogowar ne yasata bude idanun ta ya d'an tsaya kadan " sorry baby natashe ki
ko "my boy is crying Yanajin yunwa shiyasa nake wanke mai yasha,
" har zai fara sha? Ta fada tana bata fuska kamar zatayi kuka' "uhm yakamata domin
shiyafi komai Amfani a wurin jariri ya fara shan nonon uwa kafin komai farkon
Shigowar shi duniya yanada Amfani sosai yellow nonon uwa na farko ga jariri,
" daure ki d'an bashi kinji "shi ya taimaka mata ta zauna ya dauko yaron ya dorashi
saman cinyar ta da kanshi ya dago nonon ya sama yaron tuni ya cafke kamar ya saba
ya fara tsotsa,
Ita kuwa saida tasa karar zafi ta runtse ido tareda riko hannun shi gam" Akwai zafi
wallahi ".
" sorry zai daina ya fara shafa mata hankali y'anda zata rage jin radadin,
Saida yasha sannan ya karbeshi yasa a Kafada ya d'an jijjigashi kadan kafin ya
sanya shi cikin kyakkyawan gadon dake gefe na jarirai,
Dawowa yayi ya zuge mata zip din tareda rungume ta tsam" tank you baby kin bani
Abinda yafi komai a duniyar nan Allah yayi miki Albarka I love you so much
Bakin ta ya tsotsa kadan ya kuma manna mata a kumatu da goshi fadan Hajiya ya sashi
shiga taitayin shi ya mike a guje ya bude kofa "
"Na shiga uku da wannan zamani yanzu yarinya ta haihu yau ka shige mata harda kulle
kofa? Me nake shirin gani nu salame,
" rabeta kawai yayi ya wuce yana magana kasa kasa" ai bakiga komai ba tunda kin
nace sai kin zo ma mutane gida,
Najika sarai Mara kunya toko zamu sa kafar wando daya nidakai mu zuba ta shiga
itama ta hauta,
Ai Saiki tashi kiyi wanka tunda mijin naki ya fita kuma wallahi idan kikayi wasa
wata tara na dawo gidan nan ehe ki biyemai,
Ruwa mai d'an banzan zafi ta hada mata yana tururi har ta shiga bayin ta fito" wai
Hajiya wa zaiyi wanka da ruwan can?
"Ni zanyi na haifi ubanki ai a yau dole inyi wankan jego " tube ki wuce ingasa ki'
Tace ina wallahi ba mai mata wankan Azaba a haka ya dawo ya samesu shima ya tayata
karshe dai shi ya hada mata ruwan wankan ma hardashi a bayin Hajiya tayi fadan har
ta fito ta barshi,
Shi ya cudeta tsab ya hada mata ruwa da d'an gishiri ta zauna saboda dinki sannan
ya fito ya hada wa baby nashi gaba daya y'an kallo suka koma namiji da yiwa jariri
wanka "
Tsab ya wanke kayanshi ya shafeshi da mayukan jarirai masu kyau da tsada da kuma
inganci
Kayan ma da yasamai gwanin sha'awa ita kanta Hajiya ta yaba mai domin komai nashi
akan tsari da kuma kwarewa yakeyi,
"Kekam Ummu kin more miji irin wannan hidima inji mama bilki " more miji ko rashin
kunya duk gamu ya hana wai shike wankan jego har da jariri,
Shidai saida ya gama ya fice Abinshi domin duba Asibiti, domin yana da patients
dama ya gudo gida,
Kafin dare tuni gida yacika har momy ta iso da Gwaggo Amina kannin ta ma duk suna
falon sai game suke bugawa cike da jin dad'in ganin su gidan yayar su a yau,
Dakin baki dole ya bude shida mukhtar da wasu Abokan shi da sukazo taya shi murna,
Sha tara ta Arziki tun farkon zuwan baby duniya domin Dady tuni ya dallo mata
sabuwar mota ga takardun companin da ya bude a KD ya mallaka wa baby gaba daya,
Duk yadda yaso ganin ta dole ya hakura domin su Gwaggo Amina sun kasa suntsare momy
dai gidan baba tabi mama balkisu saida safe zasu dawo,
Haka ya kwana juyi dakyar yaga wayewar garin domin ya matsu bai ganta ba da kuma
Babyn shi,
Hajiya ta zake sai labarin y'anda Akayi haihuwa take ba Gwaggo Amina ita dai baccin
ta takeyi sosai irin na gajiyar nan ta haihuwa,
"
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
_*Godiya cikin sokoto Aunty ZAINAB MAKAWA Allah yakara miki daukaka da fik'ira
wannan shafin sadaukar wace gareki Allah yabar kauna*_
4⃣6⃣ 4⃣6⃣
➡4⃣6⃣
Shigowa yayi dakin A kunbure domin bayason maganar Hajiya, tun Shigowar shi idanun
ta akanshi wata irin dariya ta kunshe domin tasan halin kayanta,
Ci gaba tayi da shan kunun ta kamar bata ganshi ba domin itadai tasan kunya,
Gaida su Hajiya yayi dakyar sannan ya kalleta "ke idan kin gama ki kawomin yaro
induba lafiyar shi.
" toh ina ruwan masu yaro zo ka dauki abinka ka tafi dashi basai tazo ba ai, "wai
meyasa kike shiga tsakanin miji da mata ?
" Gwaggo Amina ke baruwanki da sa ido Amma su mai tuwo harda baki sawa sukeyi'
Dariya tasa kawai Hajiya ta ce har kafa sai nasa maka kai kam" ya dauki danshi tare
da zuba mata ido da Alamar magana "Am waiting. Ya furta ya fita Abinshi,
Dakin shi ya koma ya zubawa yaron shi ido cike da tsantsar so da shiga rai wani
irin dad'i yakeji a cikin zuciyar shi,
Saida ya tura mata text msg " idan bakizo ba zandawo kinsan sauran Hajiya Bata isa
ta hanani ba,
Zaro ido tayi domin tasan zai aika don haka tana gama sha ta mike tanufi hanyar
fita'
"Ina zaki? Hajiya ta furta" Abdul ya kirani yaron na kuka' Hmm wai kinibibi bashi
ya daukeshi ba? Jeki kekika sani ni ina Zaria,
Tafiyar ta tayi domin maganar Hajiya bata karewa, tura kofar tayi yana kwance a
rigingine, idanun shi ya juyo ya zuba mata ido Alamar tausayi,
Ahankali ta karaso yana mai bin Adon ta da kallo domin tayi wani irin fresh irin
na masu jego ga wani kyau da ta karayi
Tashi yayi da sauri tana zuwa ya janyota cikin jikinshi yana Ajiyar zuciya' saida
tace Ashh Abdul dinkina,
"Oh sorry baby nayi ke warki ne sosai ' tunyanzu? Yaufa kwana daya kawai har kafara
gajiya to kuma sai nayi Arba'in zamu fara kwana tare'
Saurin dagota yayi " mene? Arba'in a ina akeyi? "A nan Al adarmu ce " tab Wallahi
da sake ai ko sati biyu bazan iya ba bare wani Arba'in
"Kallon shi takeyi cike da mamaki " Ashe Akwai aiki' "ni fa ki d'an yi wani Abu
atakure nake " aa wasa kakeyi "
"Wasa ko? Bari kigani saurin hade bakinsu yayi yafara tsotsa a kagauce tuni ya fara
lalubar ta tans d'an tureshi domin bata manta ba'
" kukan yaron yasashi saurin sakinta ya janyoshi jikin shi na rawa ga idanun shi
kamar Jan gauta ita kanta jikinta ya mutu da taimakon shi ya zuge mata rigar gaba
daya ya Ajiye a gefe tana mai kallon tsantsar fitina a fili,
Nono ta fara bashi tana runtse ido ta dafe dayan domin zubowar da ya farayi yayi
saurin rike mata hannu cike da kallon why kika rufemin shi?
"Zai zuba ne ' janye hannun yayi ya zuba musu ido a hankali ruwan ke fita bakinshi
ya dora yafara lasar ta a hankali ta zaro ido,
" me kakeyi haka? Dagowa yayi cikeda bukatuwa ya ce "kisa ido ai nafada miki tare
zamu rika sha "
Ido tasami shi har ya gama fitinar shi ya dan rage damuwa kadan tana mai matukar
mamakin halin wannan yaron yasan takan jaraba ciki da waje,
Dakyar ya barta ta fita shikuwa ya fada bathroom ya sheko ruwa domin tsab tace
kanshi,
Asibiti ya wuce, kafin kace me gidan yacika tab da mutane domin y'an uwansu na
Zaria duk sunzo barka ga hajara ma tazo sai hira suke zabgawa wani Abin farin ciki
tana nan har suna,
Kusan kullum gidan a cike yake da jama'a ga iyayen su mata ga kuma kakannin su
Abdullah dai ya zama Abin tausayi domin dakyar yake samu ya ganta a gurguje,
Mukhtar kuwa kullum yana gidan suna soyewa da hajara,
A gurguje
Yau suna zaune a guest room suna shan soyayyar su ya shigo a kunbure ya kalle su "
kun mayar min da gida lambun soyayya bayan ni tawa matar ma sai naci sa'a nake
ganin ta,
Dariya mukhtar yasa " haba new Dady kayi hakuri mana "naki inyi malam,
Dariya tayi " yi hakuri friend bari inzo yanzu, gidan tashiga ta sameta zaune cikin
y'an uwa da dubara ta fito da ita saida sukazo falon tace'
Zaki kashe rai Kizo kiyi ceto "megida ya na cikin wani hali" bata rai tayi " bafa
banason ganin shi bane shidin ne rigima Wallahi gashi ko sati banyiba ya ballo min
aiki,
"Me kike nufi ? Bazaki gane ba saikin yi Aure muje' dariya tasa mata domin ta gano
ta "
Tana shiga mukhtar ya fito tareda yimata tsiya "maman Babyn mu ya hakuri da
Abokina?
" aa mukhtar yadai soyayya wane irin hakuri kana ganin masoya' wani irin dadi yaji
ya taso da sauri ya rungume ta tsam"
"Tank you my wife kinbiya ni.tuni su hajara suka fice kar a yi a gabansu suna fita
ya kalleta " haba baby yazaki mun haka na horu da yawa kinsani sarai kike biyewa
Hajiya,
"Sorry my dear mutane ne suke hanani fitowa " Hmm mutane sunfini? Aa kayi hakuri
daga gobe shi kenan"
"OK Allah ya kaimu Anjima ki zo dakina Akwai kayan da zan nuna miki'
Momy har y'an uwanta sunzo domin sunan jikanta Anshirya walima sosai domin sunyi
odar komai daga shagalinku restaurant
Dady tsabar farin ciki tuni ya yi rabon kujerun makka Wanda zasu halarta bayan suna
Wanda gabadaya family zasu keta hazo banda masu jego sai badi idan da rabo,
Su mama bilki baki har wuya tsabar farin ciki su Hajiya kaka kuwa ba a magana za
akara keta hazo
Fadin irin hidimar da Akayi bata bakine domin Ankar kudi don akwaisu shi kuwa uban
gayya sarkokine na diamond da kuma gold masu matukar tsada ya mallaka wa uwar gidan
tashi a matsayin gift domin duk abinda yaso yimata Anyi mata shiyasa ya bata wannan
kyautar,
Anyi suna lafiya domin mu kanmu wannan karon mun Debi Angara y'an Fenerh fan's
group harda guzuri sunyi' yaro yaci sunan kakan shi Ja'afar amma sunayi mai Al
kunya da haneef,
"Bayan suna daki guda suka zuba kayan Arziki da yaro ya samu da kuma uwarshi fadar
irin farin cikin da taje ciki bata bakine domin a yau tana Alfahari da Auren
karamin yaro,
An watse kowa ya koma gidan shi Saura Hajiya kaka suna ci gaba da dramar su da
Abdullah,
Yau kusan sati biyu da yin suna ya shigo gidan Agajiye domin halartar wani meeting
da sukayi na likitoci da zasuje su wakilci Nigeria a kasar waje kuma yana daya daga
cikin wa inda zasu je taron duk da bayason zuwa,
Tanajin Shigowar shi ta nufi dakin da yake zama dole, tana cikin Adon ta na matar
d'an gata tayi matukar kyau,
" zuba mata ido yayi cike da so " welcome d'an gata na" tank you matar d'an gata ya
mayar mata cikin murmushi,
"Ina yarona? " yana bacci "OK bari inyi wanka nagaji sosai ita ta hada mai ruwa a
bathroom din ya sameta tana shirin fitowa yayi saurin riketa tareda shafo kasan ta,
Saurin zaro ido tayi ya d'an tabe fuska" Gaskiya na kosa wai jinin nan bai kareba?
"Jinin haihuwa ba kamar haila bane fa " ba wani nidai kila wayo akemun mugani kawai
, ya fara kokarin sanya hannun shi cikin zanin ta dakyar ta samu ta zille tana mai
dariya,
Kayan da taga ya dace ta fitomai dashi sannan ta jira Fitowar shi da taimakon ta
ya shirya sannan suka nufi dakin ta
Yau hira sukeyi ba fada da Hajiya saidai duk rabin hankalin shi na wurin matar shi
yaronshi na kan kafar shi yana mai wasa kadan kadan,
A nan yake fada musu tafiyar shi waje nan da sati daya domin wakiltar kasar shi
domin irin hazakar da aka ga yanada ita
Cikin y'an watanni Asibitin su ba karamin suna yayi ba sun samu nasara sosai da ci
gaba ,
A gurguje
A kwance yake yaron shi na saman kirjin shi sai wuntsul 2yake yi tunanin Rayuwa
yakeyi yau shine da yaron shi da Ruman yana tunanin irin gwagwar mayar da sukasha
kafin zuwa yanzu,
Kayan tafiyar shi take hada mai saida ta shirya sannan ta dawo kan gadon " d'an
gata yadai? "Ajiyar zuciya yayi " tunanin matar d'an gata nakeyi,
.
Tashi yayi ya Ajiye yaron sannan ya janyo ta "zantafi gobe Amma har yanzu ba wani
motsi saidai in rage zafi Gaskiya Akwai matsala kuma kinga sai munyi kusan wata
daya kafin mu dawo,
" kayi hakuri kana dawowa zaka samu tarba ta mu samman "bata fuska yayi " Amma
kinsan nayi kokari ko?
"Sati uku ne kayi kokarin? " uhm ke bakiga hakurina ba ko to shi kenan zaki biya
bashi duk ranar da na dawo sai nayi miki dinki na uku".
"Wayyo sorry baby na wasa ne aikafi kowa hakuri nasani ta fada tareda manna mai
fake a chick din shi " Bawani nan wayo kikeso kimun Nagano ki,
Washe gari suka daga zuwa England shida Abokan Aikin shi iyayen su sunyi matukar
farin cikin samun cigaban d'an nasu a kananan shekarun shi,.
Sunyi kewar juna sosai tun tafiyar shi mama bilki ta dage ta fara bata gyara na mu
samman itama tana nata dabarun domin gyara wa d'an gatan ta
Bikin su hajara ya karato suma komai ya kam kama lokaci kawai suke jira Sumy an
kusa juyewa ,
Cikin wata daya sunfito shar dasu yaronta yayi bul bul gwanin sha'awa daka ganshi
kaga jinin bature
Sai shirin dawowar mijin nata takeyi domin tayi matukar kewar abinta tun tafiyar
shi baida wani ishashshen lokaci sai dare sometimes yake samu ya kirata shiyasa
duk ya k'agara ya dawo gida,
A yau ne zai zai cika shekara Ashirin da uku a duniya kuma a yaune zai iso Nigeria
cike da cin nasara kuma a ranar ne su Hajiya zasu daga zuwa kasa mai tsarki domin
Aikin hajji gaba dayan su sungama hallara har da momy khadija su mama bilki magaji
da kuma Gwaggo Amina
Taso ace da ita za ayi tafiyar Amma ba hali saboda jaririn ta Amma zata roki Abdul
ko umara ne suje kafin lokacin Aikin hajji,bad'i,
Suna tafiya ta fara gyara gidan tareda da taimakon y'ar Aikin ta domin tarbon
mijin ta da zai iso,
Kawata gidan tayi da kwalliya mai tsari da kuma ban sha'awa ga wasu balloons data
jejjera ta ko ina na welcome back da kuma happy birthday ,
"Sai bayan ta gama gyara gidan ta shiga kitchen ta hada mai lafiyayyan cake tayi
mai simple decoration da happy birthday d'an gata na,
Ta shirya mai dishes masu dad'i sannan ta dawo kan Babyn ta ta shirya shi tsab tayi
mai ado da wata T-shirt da aka bugo mai na mu samman da sunan shi a baya haneef
gaban kuma J ne da golden ga d'an Jean's dinshi ta sanya mai socks da canvass fari
na yara yaron kamar ka sace shi ka gudu'
Ta mikawa mai taimakon ta kafin ta shiga ta sheko nata wankan ta shirya cikin farar
doguwar Riga kamar wedding gown mai net ta sama ta gyara sumar ta ta feshe da hair
freshener kafin ta bi ko ina na jikinta da kamshi kala daban daban,
Tayi matukar kyau kamar sabuwar Amarya jin karar tsayuwar mota yasata fitowa da
turaren haneef ta kara feshe shi kafin ta Rungume shi ta fita kofar falon domin
tarban mai gidan ta,
" kallon shi takeyi cikeda so ga wani kwarjini da ya karayi yana sanye da wani
tsadadden eyeglass na matasan yanzu jikin shi sanye da fararen suit wani irin farin
ciki ne ya lullube ta ganin farin cikin ta ya dawo
Saida ya janyo briefcase dinshi sannan ya nufo cikin gidan cike da jin dadin yau ya
dawo gidan shi bayan wata daya da yakwashe a England,
."tsayawa yayi turus domin hango tauraru wa mai haska zuciyar shi tsaye tareda
bouncing baby dinshi cikin shiga ta Alfarma ga wani kyau da ta kara kana ganin ta
kasan tana cikin kwanciyar hankali,
"Ajiyar zuciya ya sauke ya cire glass din ya nufota cikin kasala da kuma so'
Hannu yasa ya dauki yaron shi kafin ya rungumo ta gefe daya yana mai binta da ido
gaba daya murna ta hanashi koda furta kalma daya,
" welcome home d'an gata na" ta furta wani cikin wani irin salo' kara matse ta yayi
a gefen shi "tank you matar dangata
" ya kuke? "Alhmdulillah ta furta kafin ta bude kofar suka shiga ta kunna bouncing
light dake rubuta welcome back and happy birthday to you d'an gata'
Ta jikin katon screen din TV ma haka ga wasu decoration da suka matukar burge shi "
tuni gajiyar shi ta ware ya fara bin dakin da kallo ga katon cake din da ta shirya
a tsakiyar falon a gefe da kwalbar tsadadden wine da kuma glass cup,
"Zuba mata ido yayi cike da Ma anoni da dama tare kuma da tanbaya,
" baby All this?
"Yeah my husband happy birthday , janyo d'an gadon yaron yayi dake falon ya
shinfide shi kafin ya rungume ta tsam
" tank you my wife "kinsan ni na manta cewar yau na kara girma who told you?
Dagowa tayi " nataba jin momy ta fada shiyasa na rike date din how can I for get
something special?
"I love you baby.. Saurin rufe mai baki tayi da hannun ta " nop not now muje kayi
wanka kafito Muyi celebrating,
"Za a tayani ko domin kinsan dai a matse nake ko? Eh shiyasa bazan tayaka ba zaka
hana mu celebrating, kaje inka shirya kafito,
Ta samu ya shiga dakin 'nan ma wani surprise din ya tarar gadon ma a tsakiyar shi
ta Dan gata na aka rubuta da fulawa gefe kuma wani kyakkyawan kati ne da rose ja
akai wani irin murmushi yayi ya d'auka,
*_may this day be the beginning of Another beautiful year for you. May there be
pleasant surprise, Lot's of joy and infinite happiness wish you a very happy
birthday D'AN GATA NA_*
" wow ya furta a zahiri bazai iya furta irin farin cikin da ya tsinci kanshi ba
tubewa kawai yayi domin yayi saurin shirya wa ya koma falon yakuma ganin farin
cikin shi,
Towel ya daura ya nufi bathroom a nan ma ruwan kanshi fulawowi ne a ciki ko ina
decoration ne a jikin kofar yaci karo da wani katin
*_wishing an. Amazing day and many great thing to come to a wonderful person in my
life, happy birthday D'an gata"_*
Dariya yayi irin ta jin dad'in nan ya juyo kawai domin farin ciki bazai barshi ba
ya nufo falon domin ya kuma ganin ta don bazai iya nisa da itaba a y'anda yakejin
shi a halin yanzu she drive's him crazy.......✍
"U too my fan's u are driving me crazy with ur comment I love you wujiga wujiga
mun kusa kai karshen labarin Ruman da Abdullah da izinin ubangiji
*Matar Soja*
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KUSKURE NA🙆*
_Love & Destiny_
_Written by Fenerh_
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽
✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 ✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
4⃣7⃣ 4⃣7⃣
➡4⃣7⃣
Dubawa ya rikayi bai ganta ba ya duba ko ina har kitchen kafin ya koma dakin wayar
shi ya d'auka ya kirata'.
"Wai kina ina ne? Dariya tasa " sai ka shirya zaka ganni kayi sauri ina jiranka'
saurin wurgi yayi da wayar ya nufi bathroom cikin sauri ya yi wanka ya fito ya samu
kaya a jiye a gefen gadon
D'auka yayi ya duba rigar t-shirt ce mai guntun hannu polo an rubuta Happy birthday
d'an gata a gabanta da bayan ta ya girgiza kai lallai na zama d'an gatan daga gani
A gurguje ya zura tree quarter din fari shima sannan yasa rigar ya feshe jikin shi
da turarukan shi masu kamshi da tsada,
Yana fitowa ya sameta cikin shiga irin tashi saidai ita dogon wando tasa skintight
ya kamata dam tata Rigar Armles ta dan kulle ta kadan a gefe,
Tana ganin shi ta juya mai bayan rigar ta "Matar d'an gata yagani da manyan harafi
sannan ta dago mai yaron shi shima cikin irin shigar " d'an gata son a tashi
rigar ,
Bazai iya musalta farin cikin shiba a yau karaso wa yayi cike da kauna ya rungume
ta tsam wasu hawaye masu dumi suka fara zubowa a idanun shi,
"I love you so much my life kin gama bani duk farin ciki a Rayuwa murmushi tayi ta
dago shi ta girgiza mai kai ta na goge mai idanun shi,
" kafa girma yanzu ga shekaru ga kuma yaron ka u are now a Dady so stop shedding
tears ,
"Kece kike sani kuka baby kin maidani d'an gatan da gaske domin ba gatan da nake
nema a duniya fiye da naki a yanzu,
" am sory my husband nayi wauta a baya banason in kuma tafka KUSKUREN da nayi ina
kokarin gyara Rayuwa ta data iyali na ina Alfahari da Auren miji daya tamkar da
dubu,
"Am very proud of you' ts furta tareda manna mai fake' Harar wasa ya mata " bansan
irin wannan kiss din wayon Abani baki insha son raina'
"Saika ce ka koshi baby karka damu yanzu dai muje mu karasa celebration din mu,
Ya dauki d'an shi yana mai fake " baby me kike ba yaron d'an gata yayi irin wannan
kibar?
"Abincin dan gata yakeci Shiyasa yayi jiki ta fada tana nunamai kirjin ta tareda
dage mai gira da kuma kashe ido daya,
" zuba masu ido yayi zai kai hannu tayi saurin rikeshi ' not here baby come let me
feed you first,
Sun ciyar da juna cikeda so da tattali sun yanka cake suka ba juna a baki kafin ta
kira mai kula da yaron ta ta bata sauran suje su raba suma,
Kafin suka tattara sai bedroom domin akara sa babban celebration a can,
Tsit kakeji da daren nan sai ihun Abdullah kawai da nake jiyowa daga falo domin kin
binsu nayi na tsaya lashe ragowar makulashen kar ayi bani,
Har kusan karfe ukun Asuba ina jiyo su kwana sukayi suna jaraba sai haneef yayi
kuka suke tsayawa su lallashe shi
Tayi matukar kokari domin duk jarabar ta bata isa ta kamo Abdullah ba saidai tayi
dauriya domin tadauki Al washin bashi kulawar da duk yake nema A Rayuwa,
Sai karfe goma safe suka fito cikin shiga ta Alfarma a gurguje ta shirya musu break
fast sukayi cikeda tattalin juna ga d'an su a gefen su,
Tsaraba ya kawo musu kala kala ita da yaron shi na suturu da kuma sarkoki da
takalma ga wata waya sabuwar yayi mai matukar tsada da ya kawo mata,
Shima yaron harda ke kunan hawa da kuma na zama dana kwanciya kala kala,
"Baby duk mu kadai wannan tsarabar ? " uhm ai bangama ba Anjima zamuje kika wani
Abu ,
"Rungume shi tayi tana godiya sosai kamar zata Goya abin ta shikuwa Jinshi yake
kamar bashi ba a yau ya gama samun Ummu Ruman ciki da waje y'anda yake bukata,
Karfe hudu na yamma suka fita cikin shigar Alfarma cikin katuwar motar shi tana
rungume da yaron ta Asibiti ta fara rakashi ya d'an duba sannan suka nufi gidan su
mukhtar,
Tarike musu tsaraba mai yawa a nan taci karo da Mubena suna tsayawa ita,kuma tana
tsaye sa wani saurayi ga hijabi har kasa daga ganin ta tasamu natsuwa a Rayuwa,
Ido ta zuba musu gwanin burgewa " what a family ita kanta tasan Ruman tayi sa'a a
rayuwar ta ta dukar da kai tana maijin kunyar rayuwar ta ta baya ,
Cikin gidan suka nufa batareda sun kula ta ba mama ta tarbesu cikin mutunci suka
gaisa tayi ma Ummu maraba,
Yau Yata tazo bani mai gidan ingani haka tayi ta haba haba ya tanbayi mukhtar tace
yana ciki ka shiga,
Barin ta yayi da momy ya nufi sashen mukhtar "sun tari juna cikin farin ciki, 'ai
nasan kana bukatar time jiya kar inyi mugun gani yasa naki zuwa gidan ku,
" ka kuwa kyauta domin da kazo bazan kalle ka ba, nasani nima dai Saura sati biyu
Kasani ko,?
Eh amma dai munrigaku ai" nidai ya zancen Abun an kammala? "Eh bari in shirya muje
ko? 'No zan mata surprise ne
" fitowa yayi bayan sun gama maganar su da ta shafesu sukayi sallama da mama tareda
Ajiye mata tsarabar da sukazo mata da ita,
Suna fitowa zata shigo ta dukar da kai cike da kunya "ina wuni yaya Abdullah ta
fada cikin ladabi"
"Dariya taso bashi ya Amsa ita kuwa Ruman tuni tayi mota don ta tsani Yarinyar
sosai,
Saida ya tsaya ya bata hakuri tace ba komai itace zata bashi hakuri sannan ya nufo
motar tayi tab tacika
" zama yayi yana dariya "wannan fuskar fa matar d'an gata?
" banza tayi mai shima bai kuma cewa komai ba saida suka isa na sarawa bakin wani
katon super market ya faka a gefe ya fito kafin ya bude mata ya karbi yaron shi
yasa a Kafada,
"Ya riko hannun ta ta fito ta zubawa rubutun wurin ido cike da mamaki ganin rubutun
dake jiki DAN GATA SON super market gefe kuma wani katon saloon ne da aka rubuta
DAN GATA WIFE saloon sai a dayan gefen kuma wani katon kamfani ne da idan bata
manta ba a wurin ne kamfanin da aka mallaka wa Haneef wato kyauta r haihuwar da
Dady ya mata,
Gaba daya duk girman wurin ya zama mallakin su kenan? Wasu hawaye ne masu zafi suka
biyo kumatun ta tayi saurin rungume shi ,
" ya dagota yana dariya "meye na kuka matar d'an gata? Muje daga ciki kigani' ki
ajiye hawayen nan sai munje gida kinayi ina tsotse wa ta d'an bugi kirjin shi kadan
yace " Auch sai na rama,
Da sauri tayi gaba domin zai Aikata suka shiga ciki, wurin ya kayatar da ita komai
Akwai a wurin ta kasa bakin magana sai hawaye kawai take maida wa,
Bayan y'an satuka Alhazai sun dawo su Dady sun shirya wa su Hajiya tsantsa reren
gida a Kaduna domin yace hidimomin su yafi yawa a Kaduna gida guda ya gina musu
saidai kowa na gefen shi ya zuba musu y'an aiki ta ko ina basa cas basa as,
Momy na Aikin ta hade da business dinta na kasar ta "magaji w'anda ya zama Alhaji a
yanzu ya yi wata irin kibar jin dad'i,
Haneef yayi wayau sosai yaro d'an wata uku yayi kamar dan wata shida saboda jin
dadi, kullum yana wurin kakan nin shi mu samman Dady zaizo ya dauke shi yaje dashi
gida idan yana free haka ma momy yaro mai gata,
Anyi bikin su hajara itama tana nan a Kaduna suna soyewar su da mukhtar Sumy ma ta
haifi y'ar ta
..
Haneef yayi wayau yanada kusan shekara Ruman ta samu hutu da jin dadi na duniya ga
miji mai sonta suna shirin tafiya umara daga can zasuyi Aikin haji kafin su dawo
kasan cewar Azumi ya karato,
Haneef dai anyaye shi tuni momy ta d'auka sukuma suka dunguma sai kasa mai tsarki
domin sauke farali tare dasu hajara
" ibada suke gabatar wa cikin natsuwa domin tayi matukar farin cikin ganin ta a
gaban ka'aba da take mafarkin zuwa gashi Allah ya kawota dole ta dage da gode wa
ubangiji da yamata baiwa,
" suna kasa mai tsarki har suka yi Azumin su suka yi umara tareda Aikin hajin su
kafin su tattara su wuce us wurin y'an uwan momy su mukhtar su sun juya nija domin
Asibiti ba Abdul shima baya nan,
"Suna kwance a kan gadon su ya rungume ta bayan sun gama hutawar su" baby kin tuna
Meya faru a wannan gadon'
"Juyowa tayi tana mai kallon idon shi " ya zan manta da wannan gadon bayan a kanshi
aka barkeni a kai aka nunamin KUSKURE NA
Dariya yasa ya rungume ta tsam ya ce "yau ma sai na nuna miki KUSKUREN ki domin
kinki bani dama in baki twins to yau sai kin bani Abdullah da Ruman,
Wutar ya kashe tareda shigewa cikin bargo bayan ya wurgoni da Biro na da ya tona
min Asiri domin faduwar da yayi
" toh shugaban munafukai sai a barmu haka ko? Jawo kafafuna nayi cike da sanyi wato
Abdullah duk tsawon rayuwar su da Ruman yana Ankare dani Amma ko na burodi bai bani
ba,
To my fan's ku taimako dana jirgi don dagani a us za abaroni tunda Asiri ya tonu,
"A nan nakawo karshen wannan lbr masoya Abdullah da Ruman har ma da Fenerh fan's
ina matukar godiya agareku,
********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery,
Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from
our blog.
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa
novel ko kuma post.
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search
na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************
Godiya Mara iyaka ga..✍
eedatu
Fareedaty
Dr fati sabitu
Lipton girl
Prince's
Etc
Ina jin jina gareku y'an golden Allah yakara hazaka da kuma hada kanmu,
My precious groups
KUSKURE Na fans ✍
KUSKURE NA fan's 2
KUSKURE Na
Fenerh fan's
Kuna sani nishad'i kunada yawa bazan iya fadar kuba Amma kusani duk ina sanedaku
ina kuma Alfahari da ku kune ke bani karfin guiwa da bazar Ku nake taka rawa
Alherin Allah ya kai muku masoyan Asali.