Kazamar Gida Complete-1
Kazamar Gida Complete-1
*****38
Ta dafe kai don alal hakika kan nata ya soma sarawa
dagaske. Ji takeyi Jafar duk ya takura mata,so takeyi yabar
d'akin ta nemo mafitan wannan matsalar dake son wargaza
rayuwar aurenta.
"Bakya jina ne?"
Ta ja karamin tsaki
"Don Allah ka rabu dani,nikam na sha shayi kaje ku nemi
abunda zakuci kaina ya dameni."
Ta mike tabar falon,yayi kwafa ya dauki Faruk dake wasa a
falon babu alamar tayi mishi wanka lura da yanda rigarsa
take da datti sannan tun na safe ne.
Siyama tayi makwas akan gadonta tana cike da tunane
tunane,a ina Bash ya samu lambarta ne? A saninta ko Nana
hafsah bata da lambarta toh waye ya bashi? Da azama ta
fito ta dauki wayar ta kunna,karar alert na shigowar sak'o
ya dauki hankalinta. Cikin gigita ta mike ganin anyo mata
transfer na kud'i har dubu d'ari biyu. Ta duba dakyau taga
daga lambar account din Hajiyarta ne. Hankalinta bai
kwanta ba saida ta danna mata kira........!
*****
"Ya akayi Siyama?"
Cikin rawar murya ta jefeta da tambaya
"Hajiya naga sak'o daga banki dake...."
Dariyarta ce ta katseta
"Kinyi mamaki ko autana? Naki ne mallakinki. Kyauta ce
daga d'an hakimi saboda yace bai nan akayi bikinki ya baki
wannan a matsayin gudunmuwarsa."
Siyama ta zaro ido,kwalla suka cika mata ido. A tsorace
tace
"Hajiya meyasa zakiyi haka? Akan wane dalili za'a karb'i
kud'insa? Yanzu..."
"Ke mahaukaciyar banza kiyimin shiru nace ko?!!! Wai ke
meyasa kodayaushe ana baki kina k'in karb'a? Meye laifi
idan yaron nan yayi maki kyauta?"
Ta hau sintiri a d'akin,ga fanka na juyawa saidai gumi da
hawaye sun gaza tsaya mata. Ta dafe kanta kafin ta yarfe
hannunta
"Bakisan waye Bash ba Hajiya,yana da naci kamar tsufa.
D'an akuya ne wallahi! Kirana yayi da zantukan banza
Hajiya! Ina ya samu lambata?!!"
Hajiya ta daka mata tsawa wacce ta gigita ta
"Idan kika k'ara zaginsa sai nayi mummunan furuci gareki!!
Wawuyar banza da wofi! Wallahi kika sake kika sanarwa
Jafar maganar kud'i ko wayar da yayi maki sai na sab'a
maki!"
Hajiya ta kashe wayar,wannan ya sanya Siyama rud'ewa
sosai,ta zube a kasan kafet ta soma risgar kuka. Wannan
wace irin masifa ce? Anya Hajiya tasan abunda takeyi
kuwa? Lallai ta yarda akan kud'i babu abunda Hajiya bazata
aikata ba koda ace ya sab'awa shari'a ne.
*****
Acan kuwa,Jafar ya kawo ruwan zafi suka had'a shayi
abinsu sukaci. Hadiyya dai sai mamaki takeyi,a kwanakin
nan taga abubuwa da yawa a wajen Siyama,ciki kuwa harda
shanyan undies dinta da taga Dauda yana yi mata. Bayan
lura da tayi kusan rabin hidindimun gidan shine mai daukar
nauyinsu. A yanzu kuwa jin da tayi Jafar yace kanta ne
yake ciwo ya sanyata kokwanto. Tasan Jafar bai samu
dawowa da rana ba jiya toh wannan ma duk ciwon kan ne
ya hanata girki? Ita kam ba don Jafar yana hanata ba da
tuni ta soma d'ora tukunyarta. Amma lallai yau da daddare
ita zatayi girkinta babu ruwanta da jiran Siyama.
"Tunanin me kikeyi?"
Jafar ya katseta,tayi azamar girgiza kanta
"Ko d'aya."
Ta wayance da mikewa ta fita da kofuna da cokulan da
suka b'ata. Saida ta wankesu tas ta shigo ta tattara inda
sukayi karinsu kafin daga bisani ta d'auki Faruk tayi hanyar
waje. Jafar wanda ke kishingid'e saman kujera yana
kallonta cikin tsananin burgewa da sha'awa yace
"Ina zaku gudu ku barni?"
Tayi murmushi ta dubeshi kad'an
"Wanka zamuyi gwara ka amso mana kaya."
Ya maida mata martanin murmushin yana mai cigaba da
jifanta da salon kallon nan dake rud'a tunaninta. Tayi
azamar dauke kanta ta fice zuwa band'akinsu
Ya lumshe ido yana mai jin wani dad'i yana ratsashi,yau
shine da wannan sa'ar? A kyautata mishi,a tsaftace
muhallinsa? Kai babu abunda zaice ga Ubangijinsa sai
hamdala. Ya gama biya mishi bukatarshi ta duniya,samun
mace irin Hadiyya a wannan rayuwar abu ne mai wahala.
Gashi wai har yau shine abokansa ke cewa yayi
k'iba,hakanan ma antinsa d'azu daya lek'a mata tayi ta
mamakin sauyawarsa. Hajjah kuwa banda albarka babu
abunda take sanyawa Hadiyya ko babu komai tana kula da
d'anta,ya samu nutsuwar zuciya.
Cikin nishad'i ya mike ya fito ya nufi d'akin Siyama. Tana
zaune cikin d'akinta tana kuka,saidai jin sallamar Jafar ya
sanyata mikewa da saurin fad'awa band'aki ta b'ame. Ya
karaso d'akin,a zatonta zai nemeta saidai ba hakan bane
don shima fushi yake da ita. Dakyar ya samo mahad'in
rigar daya zakulowa Faruk,sannan ya fice bai ko damu da
yasan halin da Siyama ke ciki ba. Abunda ya bawa kansa
shine dai ta zagaya bandaki. Saida ta daina jin motsinsa
sannan ta fito a gurguje ta leka ta tagar falonta. Daidai
lokacin Hadiyya ta fito rike da Faruk tayi mishi wanka ta
sanya,Jafar ya bita d'akin rike da kayan a hannunsa.
Ta saki labulen ta zauna gami da yin tagumi,hawayen bakin
ciki suka zubo mata. Wannan fa shine zafi biyu. Da me
zataji ne? Ta ina zata b'ullowa Bashir? Wallahi tana son
Jafar,batajin koda da sakan zata iya barinshi. Bata k'i
rayuwar jin dad'i ba saidai bazata iya kiyasta adadin kaunar
da take yiwa mijinta ba. Jafar fa na daban ne,duk macen
data sameshi ba shakka taji dad'inta. Har ta kammala bata
sami mafita ba,karshe ta bar abun a zuwan idan ta kaiwa
anti rumaisa ziyara gobe saita nema mata mafita..!
******
"Akan me? Me akeyi a gidan Antin da zaki fita?"
Cewar Jafar fuska a daure tamau,ji tayi kamar ta d'ora
hannu aka tayi kuka. Cikin marairaicewa
"Domin Allah ka barni naje Jafar,bata da lafiya yau kwanaki
uku kenan."
Ya tab'e baki ba don ya yarda da hakan ba saidai kawai
ganin damarsa yace
"Saikin dawo."
Ta sauke sassanyar ajiyar zuciya wanda har saida ya
kalleta,saita wayance ta hanyar yin murmushi
"Nagode."
Ya gyada kai daman ya sallameta da kudin cefane ya mike
cike da mamakin yanda a yau Siyama tayi sanyi, babu
wannan tsiwar ko rashin kunyar,a haka ya fice ya bar gidan.
*****39
Tafi minti uku rike da kanta bayan kammala
dogon bayanan anti rumaisa,ta rasa kalar tunanin
da zatayi. Banda innalillahi wa inna ilaihirraji'un
babu abunda take nanatawa a zuciyarta. Anti
rumaisa ta katseta ta hanyar dafa cinyarta
"Bud'e kunnuwanki ki saurareni kanwata,yanzu
soyayya ba shine rayuwar aure mai dadi ba. Idan
miji yana da kud'i toh babu sauran wani bayani.
Don haka ki kauda wani batun shirme na soyayya
a ranki, wallahi ina mai tabbatar maki matukar
kika yarda kika rabu da Jafar kika auri Bashir toh
hakikanin gaskiya kina da sa'a. Aikin
banza,wallahi da ina da babbar 'ya budurwa babu
abunda zai hana na sharewa Bashir hawaye na
aura mishi ita. Ke irinsu Bashir ba mazan yar wa
bane kinji ko? Shima don dai yana da naci kamar
kuturu amma Allah na tuba me zaiyi dake?
Malama ki saki jikinki babu abunda Bashir bazaiyi
maki ba ko menene shi. Bakiso ki ganmu muna
watayawa ne?"
Siyama da bakin ciki ke nukurkusa ta dubi Anti
rumaisa cikin tsabar takaicin maganganunta
"Wai anti kunsan menene so kuwa? Meyasa
kodayaushe kuke yunkurin rabani da Jafar?
Meyasa bakwa kaunar farin ciki na? Wallahi ni
kud'in bash baya gabana,ko a baya bai rufemin
ido ba ballantana kuma yanzu. Nikam kome
za'ayimin bazan rabu dashi ba saidai..."
Bakinta taji ta buge,anti cikin fushi da fad'a tace
"Toh wacce bata gaji arziki ba. Ai ke kam na lura
ko kina kwance aka kawo maki dukiya tashi
zakiyi ki gudu. Shashasha kawai!"
Siyama dai kuka takeyi,karshe anti ta koma
lallab'awa
"Haba kanwata,baki ganin dad'in da muke hango
maki ne? Zan baki lokaci nan zuwa sati kiyi
tunani sosai ki nutsu. Ga dai Jafar nan da kike
ikrarin kina sonshi son da bazaki iya rabuwa
dashi ba,gashinan ya k'ara aurensa ya share
lamuranki. Ke kuma bazaki iya cireshi daga
rayuwarki ba,ko wannan ya isa nuna maki cewar
ke kad'ai ke son Jafar bakya gabansa a yanzu.
Tunda yayi aure na tabbata idan kikayi nazari
zaki fahimci ya chanja maki. Allah dai Yasa ya
nemi ma wani hakkinsa a wajenki da kike wani
rawar jikin karb'ar girki yanzu."
Ta mike tayi d'akinta,Siyama ta zuba uban
tagumi tana mai nazarin jawaban antin....!
*******
Misalin takwas na dare ya tarasu a falon Siyama.
Saida ya soma da nasiha akan hakuri da
girmama junansu kafin ya gangaro batun girki. Ya
dubi Siyama
"Madam kwana nawa kika ganin ya dace ku
dungayi?"
Siyama ta yamutse fuska
"Kwana bibbiyu yayi."
Yayi murmushi,a ransa baiso hakan ba ya
tabbatar zai dunga kewar amaryarsa hakanan dai
don ba yanda zaiyi ya hakura
Ya dubi Hadiyya
"Hakan yayi maki?"
Tayi murmushi ta gyada kanta
"Komai antina ta yanke yayimin."
Tsakin siyama ya fisgi hankulansu,suka dubeta.
Ta kauda kanta zuciyarta cike fal da kishin
Hadiyya tamkar ta shak'ota takeji. Ga wani uban
kwalliya da taci, Siyama kuwa a yau banda hoda
ba abunda ta shafawa fuskarta don har lokacin
bata cikin nutsuwarta. Jafar ya girgiza kanshi
cike da takaicin wannan hali na tsaki da Siyama
take yawan yinsa.
Fuu ya mike ta shige d'aki ta barsu anan
zaune,ganin haka Hadiyya ta mike a sanyaye zata
fita.
"Muje na rakaki."
Suka fita tare,Siyama bakin ciki tamkar ya
kasheta. Tabbas ta soma amincewa Jafar ya
daina sonta. Bai damu da ita ba yanzun tamkar
babu wata soyayya data gifta tsakaninsu.
Hawaye suka taho mata,wayarta tayi k'ara
alamar shigowar sak'o. Ta dauko ta bud'e
"I wish to spend all the rest of my life with you.
Leave everything and come to me my sweet
angel,I promise to always keep you happy. I can't
stop myself from loving you. Please help me!
Save my life! From Bash."
Ta mike a firgice,ta karanta yafi sau biyar,ta
kama kanta
"Na shiga uku,wannan wace irin kaddara ce?"
Ta fad'a a fili,jin taku ya sanyata kashe wayar
gaba d'ayanta. Tayi azamar ajiyeta cikin dirowa
ta fito falon. Daidai lokacin Jafar ya shigo ya
dubeta cike da zargi
"Lafiya ke kuma? Me ya biyoki kika fito daga
d'akin kamar wata marar gaskiya?"
Ta basar ta hanyar harararsa da kauda kai
"Kace haka mana tunda ka tafi d'akin matarka
sai kaje can ka kwana ina ruwana."
Yayi murmushi sanin da yayi kishi ke damunta.
Ya rufe kofar sannan ya bita cikin d'akin bayan
ta kinkimi Faruk da yayi bacci saman kujera.
A daren Siyama bata iya runtsawa ba,bata damu
da yanda Jafar ya shareta ba bai nemi tayi mishi
komai ba,hankalinta ya karkata ga Bashir,ta rasa
ina zata sanya kanta. Tunani ya dabaibayeta,me
Bash ke nufi da ita? Wannan bala'in da me yayi
kama?
"Wai lafiyarki kalau kuwa Siyama?"
Ta d'an firgita domin kwata kwata batasan
idonsa biyu ba,ta wayance da juya mishi baya
"Ina ruwanka ne? Banjin baccin ne."
Ya juya bayansa
"Ai shikenan sai kiyita istigfari da salati."
Tana jinsa ta shareshi,ita kam batasan ma me ya
dace tayi ba,karshe sai tabi shawararsa wajen yin
abunda yace dakyar bacci ya d'auketa.
Washegari Jafar yana fita,Siyama ta dannawa
Bashir kira.
Yana zaune a bakin ruwa(swimming pool) anan
farfajiyar gidansa yana busar sigari yana fesar da
hayakin a sama. Wani irin sanyin dadi yakeji a
k'asan ransa,tabbas burinsa na mallakar abunda
ya jima yana muradi ya kusa cika. Karar da
wayarshi ta soma ya katseshi,ya d'ago a nutse
ya duba,murmushi ya saki kafin ya d'aga wayar.
"Hello my sweet lady."
Cikin bacin rai Siyama ta soma magana
"Bash ka fita hanyata,ka rabu da rayuwata don
Allah. Inason mijina,kada ka k'ara gangancin
kirana a waya. Kud'i kuwa yanzun nan zan fita
zan maido maka kayanka banaso! Bana
ra'ayinka! Just leave me alone please!!"
"Calm down My sweet,menene abun daukar zafi
haka? Naji zan fita a rayuwarki muddin zakiyimin
wani taimako guda d'aya!"
Da hanzari tace
"Fad'i ina sauraronka."
"Ki yarda ki fito na aureki."
"Naga alama jahilci yana d'awainiya dakai
Bash,ya kamata ka koma makaranta domin ka
koyo tarbiyya da ilimi irin na addinin musulinci.
Kaidai kam na kula bazaka taba daina akuyanci
ba. Toh ka sani cewar babu abunda zai rabani da
auren jafar sai mutuwa. Wallahi ko kafi kuda naci
ni Siyama nafi karfinka har abada!"
****40
Ta kashe wayar a fusace ta wurgata kan kujera.
Zaman dirshan tayi a tsakar falon,taja tsaki yafi
sau nawa. Yanzu shawarar wa zata nema ne?"
Nan da nan aminanta suka fad'o mata. Ta janyo
wayarta tayi kiran Fatima sanin da tayi duk
cikinsu ta fisu nutsuwa . Cikin rashin sa'a
wayar Fatima a kashe saboda fama da matsalar
rashin wuta da sukeyi a kwanakin nan,wannan
yasa ta nemi Shukra ba don ta so ba .
Ko ringing daya bata cika ba Shukra ta dauka.
"Ya akayi uwargidan Jafar,ko amaryar ta fara
gasaki?"
Shukra ta fad'a cikin wasa,Siyama ta rufe ido ta
bude
"Wannan da sauki akan matsalar dake tunkaroni
Shukra,ina bukatar taimakonki don Allah."
Nan ta zayyane mata halin da take ciki,shukra
hankalinta ya tashi.
"Subhanallahi,wannan wace irin masifa ce? Toh
ke kuwa ki chanja layinki mana idan yaso ki
maida mishi kud'insa. Abu na gaba kuma kada ki
sake ki dauki dukkan wasu shawarwari na Hajiya
ko anti rumaisa. Wannan abune daya shafi
rayuwarki. Kada kiyi wasa da hakkokin dake
kanki na addininki Siyama. Aure fa ba abun wasa
bane."
Shukra tayita bata shawarwari har ta
gamsu,karshe sukayi sallama.
******
Da gudu gudu Hadiyya ta shiga gidansu. Tana cin
karo da Mama ta rukunkumeta cikin
matsananciyar murna. Mama tana murmushin
farin ciki ta tureta
"Nikam zaki fad'ar dani."
Sallamar Jafar ta katse mama, mama tayi saurin
gyara zaman dankwalinta
"A'a ashe tare kuke shine kika barshi a waje?
Sannu da zuwa d'ana."
Jafar fuska a sake ya karasa yana mai durkusa a
ladabce ya gaida mama. Ta amsa itama cikin jin
dadin ganin yanda duk sukayi kyau. A karshe
bayan sun taba hira kad'an ya mike yace zai tafi
sai zuwa la'asar zai dawo daukarta. Ta mike tayi
mishi rakiya har zaure sannan ta dawo wajen
mamanta.....!
"Ya zamanki da Siyama,ina fatan dai babu wata
matsala ko?"
Hadiyya ta girgiza kanta
"Babu ko d'aya mama,saidai abu d'aya ne ke
tayarmin da hankalina."
Mama ta fuskanceta sosai
"Me kenan?"
Cikin damuwa Hadiyya ta d'an yamutsa fuskarta
"A sati biyun nan da nayi a gidan na kula anti
siyama tana da karancin tsafta ga son jiki.
Babban abunda ke damuna bai wuce yanda koda
na tsaftace tsakar gida da madafar girkinmu ba
toh wallahi mama sai ki rantse ba'ayi gyaran
komai ba muddin zata shiga tayi dahuwa toh ba
shakka sai komai ya lalace. Kuma fannin girki
ma..."
"Ya isa Ladi,kiyi hakuri domin Allah. Taje ta
k'araci kazantarta da rashin iya girkinta. Kedai ki
zage damtse wajen kula da mijinki shine
wajibinki. Koda zata b'ata sau goma,kiyi hakuri ki
gyara tunda a yau kukayi bak'o yazo yaga ko'ina
kaca kaca tkanta bazai kira Siyama kad'ai
kazama ba,kema baza'a cireki ciki ba. Saidai ma
ayi maku jam'u,a kiraku KAZAMAN GIDA."
Hadiyya ta jinjina kanta
"Hakane Mamana,Allah Ya barmin ke. Wallahi duk
sa'ilin da abu ya shigemin duhu matukar zan
nemi shawararki ko kuma ta Basma sai naji wani
sanyin dad'i."
Mama tayi murmushi ita kanta tana kaunar
d'iyarta sosai. Haka sukayita hira,suna cikin yi
Sarah itama ta shigo da yaranta maza su uku
kowannensu da kayan makaranta sai Najwa
itama yarinya mai shekaru goma ta shigo. Gaba
daya tare suke zuwa makaranta. Ihun murna suka
hau ganin Hadiyya amarya. Haka aka had'u
akayita hira har Jafar ya iso. Nan ma suka gaisa
da Sarah yake tambayarta kwana biyu
kasancewar yanzu mama ta chanja sana'a na yin
wainar siyarwa anan zauren gidanta,ita kuwa
Sarah mai mik'awa mutane. A haka suke rufawa
junansu asiri,Sarah kullum cikin fatan alheri da
addua takeyi ga Mama domin yanzu ta dauketa
matsayin uwarta tunda Sarah kwata kwata koda
zata girmi Hadiyya toh baifi da shekara d'aya ba.
A karshe dai sukayi sallama Hadiyya kamar tayi
kuka haka ta baro mamanta.
******
Har kawo wannan lokacin,Siyama bata bar samun
barazanar raba aurenta da Jafar ba daga Hajiya.
Ga anti rumaisa zuwanta wajen sau uku gidan da
nata kalar masifun. Gashi duk da ta chanja layin
wayarta bata tsira daga Bashir ba don tuni ya
samu lambarta na yanzun. A wannan lokacin
Siyama bata tantama cewar wajen Hajiya yake
samu. Gaba daya bata cikin nutsuwarta.
Watarana da magriba tana tsaye gefen titi tana
jiran abun hawa saidai abun bakin cikin ta gaza
samun wanda zai kaita can unguwarsu. Faruk
yana goye a bayanta yayi bacci,ga wani tashin
hankalin na hadari da iska mai karfi da akeyi. Ya
dubi hanyar layinsu Fatima,akwai nisa sosai
domin kuwa acan karshen layin suke kafin ta
koma ma wani aikin ne. Hankalinta a tashe tana
ji inama batazo sunan jaririn da Fatima ta haifa
ba yanzu gashinan ruwa yana neman sauka. Bata
ankara ba taga mota ta tsaya a gabanta. Tayi
duba ga motar,ba'a ganin wanda ke ciki tayi
azamar yin gaba tana jan tsaki. Yayi saurin tarar
gabanta. Gabanta ya bada dam! Saboda wanda
ta gani,yana sanye da bak'ar t-shirt sai wandon
jeans blue, ga wani d'an iskan aski a
kansa,hannunsa time da karan sigari ya yar ya
murjeshi da k'afa. Ya zuba mata ido yana
murmushi,fari ne dogo saidai siriri ne sosai bashi
da jiki.
Siyama wacce cida na ruwa ya k'ara rikirkitata
tayi azamar kauce masa zata wuce,yayi azamar
k'ara shan gabanta
"Har yaushe my sweet zata dunga gudu na? Ki
taimaka ko ba don ni ba ki shigo na kaiki kinga fa
an soma yayyafi. Please Siyama."
Ta bishi da wani malalacin kallo ta nunashi da
yatsa
"Wallahi Bash ina mai gargadinka ka fita a
harkata. Kai jahilin ina ne da baisan..."
Karfin da ruwan saman ya k'ara ne ya hanata
k'arasa jawabinta,yayi daidai da canyara kukan
Faruk dake nuni ruwa ya soma tab'ashi. Da sauri
Bash yace
"Oh no! Siyama please shiga mu tafi ko saboda
yaron nan!"
Dole tayi azamar shiga ta kunto Faruk daga
bayanta. Sanyin Ac ya ratsasu,da azama shima
ya shigo motar ya rufe. Hankalin Siyama ya
tashi,gaba daya ta rasa nutsuwarta. Tsoro da
fargaba suka mamayeta,kwallah ta cika idonta.
"Anya banyi kuskuren shiga motar Bash ba?"
Ta fad'i a ranta,daidai lokacin daya harba motar
titi yana wani murmushi.........!!!*****41
"Siyama!"
Ta runtse idonta saboda wata irin tsanarsa daya mamaye
zuciyarta. Ta juyo a fusace
"Look Bash,ban hau motarka ba domin ka jani da maganar
banza ba. Zaifi yi maka kyau ka kame bakinka."
Bashir yayi wata dariya irin ta 'yan duniya kafin ya dubeta
"Kiyi hakuri Siyama,saidai bazan fasa sanar maki abunda ke
raina ba. Siyama har yanzu da kuruciyarki,babu wanda zai
ganki yace kin haifi wannan bebin ba. Siyama ban taba son
Amal ba,hakimi yayimin auren huci haushi akan hanani
aurenki da Abbanki yayi ne. Ke kanki shaida ce akan babu
macen data tsaremin gabana saike. Amal batasan yanda
zata kula da miji ba ko kadan,a komai bata gwanance ba ke
na takaice maki......"
"Ya isa Bash! Na gaji da sauraron wadannan shirmen
zantukan da kakeyi! Ka tsaya na sauka bana bukatar
taimakonka."
Kafin ta kara magana wayarta tayi k'ara,a firgice ta zarota
daga (purse) d'inta,ta zaro ido ganin da tayi Jafar ne.
Bash ya dubi wayar kafin ya maida kansa ga titi yana
murmushi
"Ki d'aga mana,nasan rival dina ne ko?"
Ta harareshi kafin tace
"Don girman Allah kayi shiru."
Ya tabe baki kawai,ta d'aga murya na rawa.
"He..hel..lo."
"Siyama kina ina ne? Bakya ganin ruwan da akeyi?"
Ta had'iyi miyau ta saci kallon Bash,hankalinsa yana gareta
saidai idanuwansa suna ga titi. A sannu ta maida kanta ga
kallon hanya,sun kusa unguwarsu.
"Ganinan taxi na hau,ina nan tafe."
Dariyar da bash yayi ce ta sanyata zaro ido jikinta ya soma
kad'uwa,wannan yasa Jafar yin tsai yana sauraro.
Hadiyya tana gefenshi zaune tana zuba mishi abinci ta
tsaya cak tana duban Jafar a tsorace ganin yanda nan take
ya daure fuska,ya mike tsaye rike da waya a hannunshi.
Baya zaton zai taba mance mai muryar nan ko don bakar
wahalar daya sha akanshi a yayin neman aurensa na fari.
Cikin kakkausar murya yace
"Siyama muryar wa nakeji? Ki gayamin gaskiya kina ina?"
Cikin sa'a suka tsaya a danja,tayi azamar bud'e kofar ta fita
da sauri daga motar
"Gani a hanya,akwai fasinjoji ka bari na iso Jafar bansan
amsa waya a waje."
Tayi azamar kashe wayar ta tsallaka,lokacin yayyafi akeyi
ruwan ya ragu. Bash ya sauke gilashin motarsa kafin yakai
ga wani yunkuri tuni ya fad'a wata adaidaita ba tare data
fad'i takamaiman inda zatayi ba. Allah Ya bata sa'a tana
hawa aka basu hannu.
Ta dunga sauke ajiyar zuciya cike da tsabar rud'u,ta k'ara
kudundune Faruk cikin zaninsa saboda sanyin da gari yayi.
"Hajiya bansan fa inda kika nufa ba."
Ta waiga bayanta,ranta yayi sanyi ganin bash baya biye
dasu. Ta sanarwa direban unguwarsu,tayi sa'a nan hanyar
ya nufa. Wayarta ta hau k'ara,ta ja tsaki ganin Bash ne. Ta
kashe wayar gaba d'ayanta.
Acan kuwa Jafar ya rasa nutsuwarsa,wani azababben kishi
ke cin zuciyarsa na iyalinsa. Hadiyya ta ajiye (serving
spoon) dake hannunta tana kallonshi
"Lafiya kuwa? Fatan anti siyama suna lafiya?"
Ya gyada kansa,sai lokacin ya tuna bashi kadai bane a
d'akin. Ya kakalo murmushi
"Lafiya Deeyana,suna hanyar gida. Cigaba da zubamin."
Ta sauke ajiyar zuciya.a sanyaye ta cigaba da zuba mishi
sannan ta ajiye a gabanshi. Tare suka ci abinsu,hankalinsa
ya kasu gida biyu. Meke shirin faruwa? Meyasa yaji murya
irin ta Bash? Meya had'ashi da matarsa yanzu?
Siyama kuwa mai adaidaita yana tsayawa a kofar gidan,ta
soma laluben (purse) dinta
"Nawa ne kud'in..."
Sauran maganarta ta mak'ale sakamakon tashin hankalin
daya rufar mata. Babu (purse) dinta babu dalilinsa......!
"Hajiya dari zaki bani."
Ya maimaita a karo na biyu ganin da yayi kamar bata jishi
ba. Yayi daidai da fitowar Jafar daga gida. Wannan ya
sanya Siyama d'ago kanta tana dubanshi. Shima ita yake
kallo cike da zargi,tunda yaji k'arar tsayuwar mota ne yasa
ya fito don ganin wanda ke dauke da ita. Tayi azamar
fitowa ta karasa wajensa
"Kaga na yarda fos d'ina,don Allah sallameshi. Bari na
shiga ruwa yana tab'a Faruk."
Tayi wuf ta shige,ya k'arasa wajen mai adaidaita sahu ya
dubeshi
"Nawa ne kud'inka?"
"Dari ne."
Jafar yayi tsai yana dubanshi,
"Daga ina ja daukota?"
Mai adaidaita wanda tuni ya tayar da mashin d'insa yace
"Daga nan wajejan gadon k'aya,kaga zuwa nan rijiyar zaki
kuma ita kad'ai ai sai d'arin."
Jafar ya zura hannu aljihu ya dauko d'ari biyu ya mik'a
mishi,
"Bani chanji,amma wa kaga ya sauketa ne?"
Cikin gundura da wannan tambayoyin mai adaidaita sahun
ya mik'a mishi chanji
"Malam ta yaya zan sani ne? Anan junction na ganta ko?
Kawai ta fad'o adaidaita sahuna tace min rijiyar zaki zan
kaita."
Jafar yayi murmushin takaici
"Shikenan abokina kana iya tafiya nagode."
Da karfi ya ja ya tafi,Jafar ya juya ya koma ciki ya kulle. Kai
tsaye ya nufi d'akin Siyama. Tana zaune da daure kirji tana
cirewa Faruk kayan jikinsa da suka jik'e. Ya dubeta ta
dubeshi saidai zuciyarta na bugu da sauri da sauri.
"Kika cemin taxi kika shiga?"
Ta maida dubanta ga abunda takeyi tana mai hade gira
"Eh mana,anan gadon kaya na sauka na hau adaidaita sahu
saboda daman ragemin sukayi ganin ana ruwa kuma ba nan
suka nufo ba."
Ya jinjina kansa,
"A garin yaya kika yarda fos dinki?"
Ta soma yarfa hannu cikin jin zafi
"Don Allah ka rabu dani,ni kaina bansan inda ta fad'i ba."
Bayason zuciyarsa ta cika zarginta. Yaso ya tambayeta
akan muryar bash da yaso yaji saidai kuma yabar abun a
ransa. Bata kara yarda ta dago sun hada ido ba domin gani
takeyi kamar rashin gaskiyarta zai fito a zahiri. Tana jin
sadda ya juya ya fita daga d'akin. Kawai saita zuba uban
tagumi. Fatanta ya kasance a titi ta yarda fos d'inta ba a
motar Bashir ba. Ta kunna wayarta sak'o ya shigo.
Gabanta ya fad'i
"Kin manta (purse) dinki anan motata. Zuwa da safe zan
shigo na kawo maki my sweet. Hope kin isa gida lafiya?"
Cikinta ya bada wani sauti,ta runtse ido cikin tsabar bakin
ciki. Tayi azamar aika mishi sako
"Ka barshi banaso! Ka rufamin asiri ka fita daga rayuwata.
Dan iska kawai."
Ta aika mishi,nan take ya maido martani
"Hahaha! Sarkin tsoro. Shikenan amma tabbas ganinki a
yau ya k'ara kid'imani ya dace ki gaggauta samar mana
mafita."
Taja tsaki ta kashe wayar gaba d'ayanta. Wannan shine
babban tashin hankalin da Siyama bata tab'a cin karo da
irinsa ba tunda take a rayuwarta. Ga azalzalar da Hajiya
keyi mata,ga anti rumaisa. Abun bakin cikin daidai da
sauran yayyunta sun goyi bayan Hajiya,Hanif ne dai take
zargin baida masaniya akan halin da ake ciki.
******41
Hanif ne dai take zargin baida masaniya akan halin da ake
ciki.
***
Hajiya ta dubi aminiyarta
"Hajiya shema'u ya dace musan abunyi,wannan
kinibabbiyar yarinyar bazata taba taimakamana burinmu ya
cika ba. Dole ne sai mun hada da malamai."
Hajiya shemau cikin mamaki matuka tace
"A'a,wai anya kuwa Jafar haka yabar Siyama? A wannan
zamanin banga macen da za'a nuna mata arziki ba ta
gujeshi. Yanzu fisabilillahi da gaske ta mayar mishi da
kud'in nan?"
Hajiya tayi kwafa cikin fushi
"Bar yar iska,hanata nayi shine ta maidoshi asusuna. Ai
wallahi nikam na tsani zuri'ar Hajiya Binta. Gaba d'ayansu
matsiyata ne kuma matsafa. Banda tsafi,ya za'ayi Siyama
zata guji tarin arziki ta nanik'ewa matalauci? Hajiya
shema'u ki taimakeni da wannan aikin ki kaini wajen
kowane malami matukar bukata zata biya toh fa shikenan
zamu biyashi ko nawa ne."
Hajiya shemau ta jinjina kanta tana taunar cingam
"Kada ki samu damuwa yar uwa, komai zai daidaita. Yanzu
zanyi waya da Malam yahuza duk yanda mukayi zakijini."
Ran Hajiya yayi sanyi kad'an,
"Yauwa yar uwa,a rabasu. A sanya mata tsanar Jafar a
ranta. Soyayyar da take yi mishi ya koma kan Bashir."
Haka sukayita kulle kullen su kafin su rabu.
Sunyi magana da Malam inda yace zai musu aiki amma a
aikomishi kud'i ta asusunsa. Nan ya bayar da lambar
asusunsa na banki a karshe yayi musu alk'awarin zai musu
aiki.
*******
Misalin karfe tara na safe,Jafar yayi shirin kasuwa saidai
hankalinsa yana ga Hadiyya wacce gaba daya batajin dadi
tun jiya. Ya isa gareta ya janyota jikinsa,cikin muryar
tausayi yace
"Anya zan iya tafiya na barki a wannan yanayin Deeya?
Tashi ki shirya muje asibiti idan yaso daga nan sai na wuce
ke kuma ki dawo."
Ta kara kwanciya a kirjinsa tana kukan shagwaba
"A'a nidai Yaya j...."
"No Deeya,har zuwa yaushe ne zakiyita zama haka? Tun
jiya nake lallab'aki muje kin k'i yau dai dole ki shirya mu
tafi."
Ya soma kokarin cire mata kaya kafin ya kaudata ya bude
kwaba ya ciro mata doguwar rigar abaya. Ya taimaka mata
ta zura sannan suka fito yana rike da hannunta. Siyama ta
fito daga kicin ta gansu,wani kallo ta watsa musu batace
komai ba tayi hanyar d'aki.
"Zan kaita asibiti ne yanzu zamu dawo."
Kishi ya mamaye zuciyarta,kada dai cikine da ita? Ta tabe
baki ta juya zuwa d'akinta. Jafar ya girgiza kansa, Hadiyya
kam zuwa yanzu bata damun kanta da sai sun zauna lafiya
da Siyama tunda ta kula halinta ne bazata sauya ba. Bata
kaunarta batason ko kadan ta dunga shiga harkarta
wannan yasa ta watsar da ita.
Jafar ya rufe kofofin dakunan Hadiyyah sannan ya fidda
mashin d'insa yaja suka bar gida. Yana zaune cikin motarsa
yana hangensu,murmushi ya saki.Motarsa ya bud'e ya
fito,kai tsaye ya nufi cikin gidan.
****
Sun kai titi kenan Jafar ya laluba aljihunansa,
"Subhanallah,kinga garin sauri na mance wallet d'ina ko?"
Hadiyya cikin jin ciwo ta dubeshi
"Ai da sauki tunda bamuyi nisa ba. Ka koma ka dauko Yaya
j."
Ya juya kan mashin d'insa..........
Ta juya baya tana kokarin juye indomin data girka a faranti
babu zato taji hannuwa akan kugunta. Cikin tsabar firgita ta
juyo ta tsorata ainun da ganinsa har numfashinta yana
barazanar daukewa. Da karfin tsiya ta tureshi,bakinta yana
rawa tace
"Ba..sshhh....menene ya kawo ka gidana? Fitar min tun
banyi maka ihun b'arawo ba wallahi! Ka fita!!!"
Ko kusa bai gigita ba,ya kara marairaicewa
"Ki taimakeni Siyama. Wallahi na k'ara d'imautuwa da
bukatarki a tun lokacin da muka rabu wallahi ban k'ara
baccin kirki ba. Siyama save my life,ki bani abunda nakeso
I promise to...."
"Ka fitar min daga gidan aure! Kai dan..."
Bakinta ya kafe sa'ilin daya rungumota. Ta hau kiciniyar
kwacewa,daidai lokacin taji sallamar Jafar. Hankalinta yayi
mummunan tashi,shi kansa Bash sai yayi azamar sakinta.
Da gudu ta fito daga kicin d'in har tana firgita Jafar dake
kokarin bude kofar dakin Hadiyya. Haki takeyi kamar wacce
tayi tseran gudu,ga gumi da take fitarwa. Shima bash yayi
saurin sanyo kai yana haramar fita saidai ina! Tuni sukayi
ido hudu da Jafar. Ya dake iya dakewa yana shafar
sumarsa. Jafar ya dubi Siyama kafin ya dubi Bashir. Jikinsa
ya hau rawa,idanuwansa suka sauya launi. Cikin mugun
zafin nama ya shak'i wuyan Bashir,murya a d'age ya soma
magana
"Meya kawoka gidana don ubanka?!!! Me kake nema a
wajen matata? Daman kai kwartonta ne? Ka gayamin!!!"
Tuni Bashir ya soma kakari,siyama ta dora hannu akanta
tana ihun kuka. Da gudu Hadiyya ta shigo,tayi matukar
kaduwar ganin Jafar ya shak'i wuyan mutumin da bata taba
ganinshi ba. Nan tayi kan Jafar tana ihu
"Wayyo Allah,Yaya j ka sakeshi kada ka kasheshi. Wayyo
Allah!"
Duk iyakar yinta amma ina Jafar bai saki bash ba,tuni Bash
ya soma zaro idanuwa. Ganin babu sarki sai Allah tayi wuf
ta fita tana ihun neman taimakon jama'a. Nan aka shigo
gidan,wasu matasa uku sukayi nasarar janye Jafar dakyar.
Yana ihun fad'in
"Ku barni na kasheshi! Ku rabu dani nace!! Dan iskan karya!
Shege wanda baisan mutuncin aure ba!!"
Siyama ta shige dakinta ta rufe ruf sakamakon firgita da
tayi. Dakyar mutane suka janye Bash daga gidan,cikin
matukar jin kunya yabi layin ya shiga motarsa sai nunashi
akeyi ana gulmarsa. Matan cikin gida harda lek'e. A fusace
ya bar unguwar.
Hadiyya ta kori yaran da suka rage ta rufe gidan da mukulli
saboda masu tururuwar zuwa kallo. Jafar ya hau bugun
kofar Siyama yana kukan bakin ciki
"Kin cuceni Siyama! Ki fito ki tafi na sakeki bazan iya zama
da kwartuwa ba! Mai yawon bariki! Har cikin gidanki na
sunnah saikin kawo kwartonki.! Allah Ya isa tsakanina dake
Siyama! Na tsaneki! Ki fito tunda ba gidan ubanki bane.."
Hadiyya tayi azamar rufe mishi baki cikin matsanancin
kuka,Jafar baya cikin hayyacinsa. Ya buge hannunta yana
mai daka mata tsawa
"Ki rabu dani Deeya! Ki kyaleni na kori wannan 'yar iskar
daga gidana!"
Hadiyya tana kuka ta kara matsawa ta jashi
"Don Allah Yaya j kazo muje. Don Allah kabar yanke hukunci
cikin fushi."
Dakyar Jafar yabi Hadiyya zuwa d'akinta yana fad'a ji
yakeyi tamkar zai mutu don tsananin kishi da bakin cikin
Siyama.
"Da me na rageta Deeya?! Menene bana mata?!! Me wani
zai fini?!! Deeya mata macuta ne! Maha'inta ne!!!"
Hadiyya cike da matsanancin mamaki take kuka,amma
Siyama ta b'ata wayonta. Taji bata ganin girmanta.
*****
Siyama tunda Jafar yayi furucin saki gareta taji hawayenta
sun tsaya cak!
"YA KASHEMIN AURE!!!"
Itace kalmar da take ta nanatawa! Gaba daya ta kasa
katabus,Faruk sai kuka yakeyi saidai ko kusa hankalinta
baya tare da ita.......!****43
Saida Jafar ya fice daga gidan sannan Hadiyya ta isa ga
kofar Siyama ta hau bugu.
"Anti Siyama! Anti Siyama!!"
Siyama ta dawo hayyacinta daga dogon tunanin data shiga.
Sai lokacin taji kukan Faruk wanda shine dalilin daya sanya
Hadiyya kwankwasa mata. Siyama tayi azamar mikewa ta
lek'o ta tagar d'akin. Sukayi ido hud'u da Hadiyya. Cikin
dauriya daga ciwon kan da takeji ta cize lebbanta
"Ki bud'e Yaya j yabar gidan nan."
Siyama tayi azamar bude kofarta,ta janyo hannun Hadiyya
zuwa falon sannan ta rufe kofar gam saboda tsananin tsoro
da fargaba. Hadiyya ta dauki Faruk ta soma jijjigawa,Siyam
a ta zauna cikin tagumi sunkai mintuna uku a haka kafin
Siyama ta soma magana cikin sanyin murya.
"Wallahi Hadiyya ban aikata laifin da Jafar ke zargina ba
akai. Nasan kema ba lallai ki yarda da zancena ba amma
ga wannan ki karanta."
Siyama cikin hawaye ta janyo wayarta ta bud'o sak'onnin
da Bash ke aiko mata ta mikawa Hadiyya wayar. Hadiyya a
sanyaye ta karb'a ta soma karantawa d'aya bayan d'aya
yayinda hawaye suke kara ambaliya akan fuskarta. Ta
mik'awa Siyama faruk sannan tayi zaman dirshan akan
kafet ta zuba uban tagumi.......
"Nasan cewar nayi babban kuskure da ban sanar da Jafar
ba Hadiyya,saidai rashin sanin ta inda zan soma ne ya
hanani cewa komai gareshi. Jafar bai tambayeni dalilin
chanja layin wayata ba,da ace ya nemi sani watakila a
lokacin na iya sanar mishi wannan bibiyata da Bash
yakeyi."
Siyama ta d'an tsagaita da maganarta tana mai share
hawaye,Hadiyya wacce ta jingina kanta jikin kujera saboda
sarawar da yakeyi ga zazzab'in dake jikinta. Tayi shiru tana
sauraron Siyama. Nan Siyama ta fayyace mata tun lokacin
da Bash ke bibiyarta har zuwa yau d'innan,saidai bata
sanar da ita da sanya hannun mahaifiyarta ba ko yayarta.
Saida ta gama sannan ta share hawayenta
"Nayi imanin Allah zai min sakayya tsakanina da bash. Na
barwa Allah komai."
"Kiyi hakuri anti siyama,Allah bazai bar bash ba zai maki
sakayya. Gaskiya ne baki kyauta ba da tun farko baki sanar
da Yaya j ba. Na tabbata zai fahimceki,yanzun ma lokaci
bai kure ba anti Siyama. Idan Yaya j ya dawo ki nemi
gafararshi kiyi mishi bayani wannan sak'onnin ma sun
isheki shaida. Allah Yana tare da duk mai gaskiya. Ki yiwa
Yaya j uzuri yanzu,yana cike da bacin rai da kishi ne. Duk
abunda ya fad'a cikin fushi ne,duk da bansan takamaiman
abunda ya faru ba amma ina da tabbacin yaya j abun kona
mishi rai yayi."
Siyama tayi murmushi mai ciwo tana girgiza kanta saidai
batace komai ba,karshe dai Hadiyya ta mike ta nufi dakinta.
Allah Ya taimaketa tana da maganin ciwon kai ta dauka ta
sha. Asibitin da ba'aje ba kenan,ta jawo wayarta tana kiran
layukan jafar saidai duk a kashe suke. Hankalinta ya tashi
ga azababben zazzabin da takeji,ga kuma tausayin anti
siyama sannan rashin sanin inda mijinta yake. Haka ta
kwanta ta kudundune cikin bargo tun tana gwada kiran
wayarsa har dai batasan sa'ilin da bacci ya dauketa ba
saboda zafin ciwon da jikinta keyi.
Ta yafa mayafinta bayan ta goye Faruk,tana hawaye ta
tsayar da idanuwanta akan hotunansu na aurenta da Jafar
wanda suke manne har uku a bangon falon. Hawayenta ya
k'aru,Allah kad'ai ne zai shaideta akan son da take yiwa
mijinta,yau gashinan ta rabu dashi bisa sharrin da
shaidanin nan yayi gareta.
Ta goge hawayenta ta fita daga gidan. Kanta yana kasa
saboda tsabagen kunyar yanda mutane suke nunota suna
surutai duk da batasan me suke fad'i ba amma nan da nan
ta tsargu. Da sauri saurinta har tana tuntub'e tabar
layin,bataci wuyar samun adaidaita sahu ba. Ko cinikin kirki
bata tsaya sunyi ba ya shige,kuka sosai takeyi har suka isa
unguwarsu. Tayi ta kwatanta mishi gidansu har bakin kofa
ya kaita.
Gabanta ya hau bugu ganin Abba zaune yana karatun jarida
anan kofar gidan. Ya tsaya yana dubanta harda cire gilashin
idanunsa,ji tayi kamar ta saki fitsari......!
Ta dauke idonta daga gareshi tayi azamar biyan mai
adaidaita sahu yabar wajen. Gari yayi luf luf babu rana
tamkar lokacin ba karfe sha daya na safe ba. Ya kasance
asabar.
Kanta a kasa tazo ta gaban Abba zata wuce,a sanyaye ta
durkusa ta gaisheshi. Abba ya amsa har lokacin bai bar
kallonta da mamaki ba. Ya rufe jaridar hannunshi
"Ke kuma lafiya na ganki a hargitse hakanan?"
Ta kakalo murmushi
"Lafiya Abba."
Ya jinjina kanshi yayi shiru,can kuma ya tabe baki kadan
"Allah Ya sauwake toh,shige ciki."
Ta mike tayi ciki,sai lokacin ya lura da kayan jikinta. T-shirt
ne sai zanin data d'aura ga mayafi marar kauri. Mamaki ya
rufeshi,tabbas Siyama ba lafiya take ba,daman yayi
mamakin fitowarta da wuri haka. Maganar Alhaji ce ta
katseshi
"Yaya mu tafi ko?"
Abba ya mike yana ajiyar zuciya,daman daurin aure zasuje.
Suka hau mota sukayi gaba.
*****
Hajiya tana sashen Abba acan Siyama ta isketa. Kallo d'aya
ta yiwa Siyama taji sanyi a ranta
"Ke kuma lafiyarki kuwa? Wannan wace irin shiga ce? Kodai
bakyajin dadi ne?"
Siyama wacce kiris take jira,kawai saita zube a k'asa ta
fashe da kuka.
"Ke! Ki gayamin me Jafar d'in yayi maki ne? Kukan nan na
menene?"
Cikin sheshsheka Siyama tace
"Ya sakeni Hajiya,Bash ya kashemin aurena."
"Alhamdulillah."
Hajiya ta fad'i a ranta,a fili kuwa taja tsaki
"Toh menene abun kuka? Shi kadai yake namiji ne? Kedai
wallahi kina da matsala babba ma a rayuwa,menene ciki
don kin rabu da tsiya? Ai wannan abune na farin ciki.
Daman nasha sanar dake baki kamaci Jafar ba,yau
gashinan keda kika amince dashi ga abunda yayi maki.
Daman kiris yake jira kiyi mishi laifin da baikai ya kawo ba
ya koraki gidanku. Tunda dai a yanzu ya auri wata ai dole
ne ya wulakantaki. Ki share hawayenki ki watsar da
batunshi,bari uban naki ya dawo saina sanar mishi."
Da sauri sauri Siyama ta mike tabar d'akin zuwa falon
hajiya sakamakon jin da tayi zuciyarta bazata iya daukar
wadannan kalaman na hajiyarta ba. Bakin ciki ya turnuke
zuciyarta,tabbas batasan a matan ma me zata kirawo
hajiyarta ba,abun nata kuma yayi yawa sai du'a'i. Ta lura bil
hakki dagaske takeyi bata bakin cikin mutuwar aurenta da
Jafar. Wannan wace irin uwa ce da zata iya zab'ar abun
duniya akan farin cikin 'yarta? Haka Siyama tayi ta tunane
tunane har dai daga karshe ta mike domin gabatar da nafila
don kaiwa Ubangiji kukanta.
*******
Haris ya zubawa Jafar ido wanda ya dafe kansa da
hannuwansa yana mai cike da tunani. Sai zufa yake
had'awa. Ganin haka ya tsiyaya mishi ruwan sanyin daya
kawo mishi
"Karb'i kasha Jafar."
Ba musu ya karb'a ya shanye ruwan tas yayinda sanyin ke
ratsa zuciyarsa. Sunfi minituna uku saidai Jafar bashi da
niyyar cewa komai har Haris ya gaji yace
"Wai Jafar menene ya faru? Tunda kazo bakayimin furucin
kalma koda guda d'aya bane wanda zai fahimtar dani
matsalarka ba,ka daure ka kwantar da hankalinka ka
samarwa kanka nutsuwa Jafar. Meya faru?"
Ya d'ago kod'ad'd'un idanuwansa ya dubeshi cikin
kakkausar murya yace
"Na saki Siyama."
Haris ya zaro ido a tsorace
"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! Kasan abunda kake fadi
kuwa Jafar?"
Jafar ya dauke dubansa daga kallon Haris,yayi murmushi
mai k'ona zuciya
"Babu k'arya Haris,na saketa."
Haris cikin fad'a yace
"For what reason Jafar?!!! Me tayi maka? Bata da
magabatana da bazaka kai k'ararta ba? Baka gudun
abunda mutane zasu ce akan wannan d'anyen aikin da
kayi?"
Jafar a fusace ya dubeshi
"Kabar saurin yankewa mutum hukunci batare daka saurari
uzurinsa ba! Siyama yaudarata takeyi,kwarto ta kawomin
har gidana....
******44
"Kwarto fa kace?!!! Anya Siyama zata aikata wannan laifin?"
Jafar ya girgiza kanshi
"Daman ba lallai ka yarda ba sai idan kaji wanda na tarar a
gidan. Ba kowa bane illa bash."
Haris yayi tsai yana duban Jafar a mamakince, yana
nanata sunan a ransa. Tabbas yasan waye bash. Tsohon
saurayin Siyama ne wanda akan shi Hajiya ta tsani auren
Jafar da Siyama. Akanshi ne kuma akayita rikice rikice.
Saidai anya zai amince Siyama ce ta kawoshi gidan?"
Ya girgiza kai cikin shakku
"A yaya ka tarar dasu?"
Jafar ya labarta masa komai. Haris yayi murmushin takaici
"Ka bani mamaki daka iya yankewa matarka hukunci babu
wani kwakkwaran bincike Jafar. Ya kamata ka nutsu ka
bincika gaskiyan al'amari. Ka zaunar da Siyama ka
tambayeta menene.."
"Kaga Haris, bash bazai san hanyar gidana ba sai ta
wajenta hakanan bash bazai iya shigomin gidana ba saida
izninta. Kada kaso kaga yanda suka rud'e da tsabar
kad'uwa a ganina da sukayi. Gaba daya basu so hakan ba.
Saidai Allah Yayi niyyar tona musu asiri ne kawai. Hum,ashe
wannan ne dalilin da yasa bata nemana a matsayinta na
mijinta? Bata bani hakkina aduk lokacin dana nema? Daman
tana da wanda ta ajiye a gefe take yiwa biyayya? Ni kuma
ta daukeni shashashanta a gefe? No haris, duk da
matsanancin son da nake yiwa Siyama na hakura da ita
Haris. Bazan iya cigaba da zama da ita. Na jima ina hakuri
da ita kai kanka ka sani kuma ba don komai ba sai saboda
son da nakeyi mata. Amma yanzu kam na hakura."
Haris ya kula Jafar kishi ke damunshi bazai fahimci komai
ba yanzu. Can kuma kamar wanda aka tsikara ya mike
"Oh kaga na manta fa ashe deeya batajin dadi zan kaita
asibiti,shikenan sai munyi waya."
Ya kama hanyar fita Haris ya dakatar dashi
"Jafar."
Wannan yasa ya juyo
"Kayi tunani sannan inaso ka bincika al'amarin nan. Idan da
hali ka boyewa su Abba maganar ka rufa mata asiri ko ba
don halinta ba."
Jafar ya gyada kansa
"Zanyi amfani da shawararka,nagode."
Daganan sukayi sallama.
*******
Shi kuwa Bash bayan fitowarsa daga gidan Jafar. Yana
sharara mahaukacin gudu na jin zafin cin mutuncin da Jafar
yayi mishi har bai ankara da babban motar data sanyo kai
ba kawai sai jin sautin k'arar buguwa mutane sukayi. Saiga
motar Bash a karkashin babbar motar nan. Nan mutane
suka fasa salati. Mata masu raunin zuciya a wajen tuni sun
soma fidda kwallar tausayin ganin yanda mai rai ya koma.
Bash yayi kaca kaca dashi,kafarsa d'aya ta fita, ga kayan
cikinsa a waje. Ko shurawa baiyi ba a wajen nan. Take
anan akayi kokarin janyeshi. Mai motar cikin ikon Ubangiji
babu abunda ya sameshi saidai na gefenshi daya samu
raunuka a goshi saboda buguwar da sukayi bata wasa ba.
Dakyar aka iya janye babban motar. Yan sanda suka laluba
cikin motar duk da ta talitse har Allah Ya basu ikon fiddo
wani id card dake motar. Anan fa sukayi gaggawar tafiya
dashi kamfanin da yake aiki bayan sunbi kwatancen dake
jikin idcard din
Acan kuwa sukayi nasarar samun babban yayansa Nabil.
Yayi matukar kaduwar ganin yanda kaninsa ya koma har
kuka saida yayi. Dakyar suka lallab'ashi ya tashi suka nufi
gidansu Bash.
Jimawa kadan labarin mutuwarsa har a rediyo. Hankalin
kowa a gidan hakimi ya tashi. Bakajin komai sai koke koke.
Amal sumanta yakai uku saboda ba karamin so take yiwa
mijinta ba duk da irin cin kashin da yakeyi gareta.
Rayuwar kenan! Shiyasa mutum ya shuka nagari don
baisan ranar mutuwarsa ba!!!!!
******
"Meke faruwa ne Siyama?"
Siyama dake durkushe gaban mahaifinta ta kasa cewa
komai sai kuka. Hajiya tayi wuf tace
"Ai ga irinta nan,shiyasa tun farko banso auren nan ba
saboda rashin mutuncin yaron nan. Yanzu gashinan ya
sako mana ita bayan daya auri wacce yakeso."
Cikin mamaki abba ya dubeta sannan ya dubi Siyama
"Sakinki yayi? Me kikayi mishi?"
"Yo me..."
"Hajiya maimuna rufemin baki! Tashi ki fita! Bake na
tambaya ba!"
Tsawar da yayi ya rud'asu gaba daya,sum sum Hajiya ta
mike a fusace tabar falon. Ya maido dubansa ga
Siyama....!
In sha Allah yau zamu kammala...IN SHA ALLAH!!!!
Ya maida dubansa ga Siyama bayan fitar Hajiya.
"Ke nake sauraro. Menene ya hadaku da mijinki har ya
fusatashi ya yanke wannan hukunci?"
😪Siyama kanta a k'asa ta kasa cewa komai. Tsoro
ne ya mamayeta. Toh wai me zata cewa Abban ma? Bayan
ta riga tasan ko za'a yanka naman jikinta da wuk'a bazata
iya furtawa Abba komai dangane da lamarinta da Bash ba.
"Da alamu dai baki da gaskiya Siyama. Saidai ki
sani,matukar na gane kece mai laifi ba shakka hukuncinki
mai tsauri ne tunda kin nuna baki da tawakkali. Kin kasa
tsaida hankalinki ki zauna da abokiyar zamanki lafiya ko?
Shikenan tafi zanji komai daga bakin Jafar d'in."
Ta mike tana kuka mai karfi ta fice. Lokacin data shiga
falon Hajiya kukanta ne ya tsaya cak ganin yanda Hajiyar
ke doka salati hannunta d'aya rike da waya d'ayan kuwa
rike da kanta. Wannan ne yayi dalilin daukewar kukanta sai
faman numfarfashi,ido a waje take duban Hajiya cikin jan
k'afa ta k'arasa gareta.
"Menene ya faru Hajiya?"
Ai kawai saita yarda wayar ta hau dukan siyama iyakar
karfinta tana kuka.
"Shegiya kawai,kin kashemin d'an 'yar uwata! Kedai wallahi
ina mai takaicin haihuwarki Siyama. Wallahi.."
"Maimuna!!"
A firgice tabar dukan Siyama ta dubeshi,Siyama wacce take
ihun kuka wanda a dalilin hakan ne ta jawo hankalin Abban
nata zuwa falon. Ya karasa shigowa ciki
"Menene haka wai? Meya faru? Akan wane dalili zaki
dokarmin d'iyata?!!"
Cikin kuka hajiya tace
"Akan soyayyarta gashinan ya mutu yabar duniyar."
Wani irin faduwar gaba ya dirarwa Siyama. Ta zaro ido tana
dafe kirji. Bash ya mutu?!!! Allahu Akbar. Ai saita kara
fashewa da kuka,lallai Allah abun tsoro ne.
Abba yayi salati gami da yi mishi addu'ar samun rahmar
Allah. Ya dubi Hajiya cike da takaici
"Shine akace maki Siyama ce ta kasheshi? Kedai bansan
lokacin da zaki dawo hankalinki ba. Ke kuma tashi kiyi d'aki
muddin ta kika k'ara dukanta zan dauki mataki. Maganinki
kenan kin kaso aurenki yanzu wace riba kika samarwa
kanki a gidan? Kadan kika soma gani."
Abba ya fada sannan ya fita a fusace. Hajiya tayi zaman
dirshan tana zage zage da ihun kuka kafin ta mike ta koma
d'akinta.
******
Jafar akan hanyar zuwa gidansu bayan ya mik'a Hadiyya
asibiti ya dawo an sanar musu tana dauke da juna biyu.
Farin ciki ya danne masa kaso hamsin na bakin cikin da
Siyama ta d'urma mishi a jiya da safe. Duk yanda Hadiyya
taso tayi mishi zancen siyamar ma ya gujewa hakan,ya
gargadeta akan kada ta kuskura tayi mishi maganar baya
bukatarta.
Gabansa ya fad'i da ya iske Abba a sashen Alhajinsa. Ya
daure ya k'arasa cikin falon yana ji inama sashen Hajja ya
soma nufa,kila ya kaucewa tambayoyin Abban Siyama. Ya
gaishesu a ladabce,Alhaji ya daure fuska murtuk kamar bai
tab'a dariya ba wannan yasa Jafar shan jinin jikinsa.
"Baba yaushe ka soma yanke hukunci ba tare..."
"Ya isa Rilwanu,wannan magana ce tsakanin nida d'ana."
Abba ne ya katse alhaji daya soma magana,kafin ya maida
dubansa ga Jafar yana murmushi irin na manya*****45
"Jafar menene ya had'aka da matarka har ka yanke mata
wannan hukuncin?"
Cikin jin nauyi Jafar yayi k'asa da kanshi,har abada bazai
taba iya sanarwa su Abba abunda ya faru ba. Bayason
tozarta Siyama.
"Jafar yi magana mana."
Ya rikice ya rasa mafita,nan take kuma ya chanja laifin
nata. Zuwa ga halayenta daya tsana wanda ya nuna sune
silar daukar matakin.
Nan ya kwararo musu halin kazanta da rashin ganin
girmansa da Siyama keyi. Ya kammala jawabinsa harda
k'ararta daya kawo wajen anti.
Ba zato Alhaji ya daukeshi da mari,
"Kaga d'an iskan yaro nan,ace don ka raina mutane saboda
wannan d'an laifin da bai taka kara....."
"Rilwanu ban hanaka magana bane?"
Alhaji yana huci ya koma ya zauna,Abba wanda ya gama
tunzura da wannan d'abi'un na Siyama ya dubi Jafar
"Amma jafar meya hana kazo ka sanarmin? Wannan ai
shiririta ne. Kana zaune da mace tana yin abunda taga
dama gareka amma ka kasa magana? Sai kace ta d'aure
maka bakinka?"
Abba yayi ta fada cikin tsananin bakin ciki,Jafar yasha jinin
jikinsa. Wannan inda ace Abba zaiji ainahin abunda ya
janyo sakin ya zaiji ne?
Karshe Abba ya umarci Jafar da tafiya,Alhaji yayi saurin
katseshi
"Bafa zai bar nan wurin ba sai ya mayarda matarsa."
Abba ya harareshi kafin ya k'ara kallon Jafar
"Tafi Jafar."
Sai bayan fitar Jafar, Abba suka tattauna magana da Alhaji
wanda yasa zuciyar alhajin yin sanyi.
*****
A fusace Abba ya shiga gidansa.
"Maimuna! Maimuna!! Siyama!!"
Da gudu gudu suka fito. Abba baiyi wata wata ba ya
kwashe Siyama da mari wanda tsananin gigita saida ta
zube k'asa. Zuwa yanzu hawayenta sun gaji da zuba sai
kukan zuci. Abba ya nuna Siyama
"Wannan yarinyar shaidaniyar kanta ce ashe ban sani ba?
Tarbiyyar dana baki kenan? Ashe zaki iya koyi da jahilan
mata a harkar aurenki? Tabbas Maimuna kin cuceni kwarai
da har kika bari na mik'a Siyama gidan aure bata iya komai
ba a fannin kula da miji. Yanzu da ace Jafar bare ne da tuni
auren nan ya jima da mutuwa. Toh wallahi sai na hukuntaki
daidai da laifinki."
Tun daga ranar Abba ya sallami mata yan aiki a cewarsa ya
basu hutun watanni uku. Hankalin Siyama ya tashi sa'ilin
da Abba ya sanar da ita rankatakaf aikin gidan nan ya koma
hannunta. Ya k'ara fa cewa
"Wallahi na iske kuskure daga ko'ina saina ci mutuncinki a
gidan nan!"
Fuu! Ya fice yana bar musu fuka fukin babbar rigarsa dake
tashi a sama.
*********
Jafar jin labarin mutuwar Bash a wajen Hajja ya kad'ashi.
Ya rike kai yana jinjina al'amarin,tabbas hatsarin ya afku
bayan barinsa daga gidansa. Lallai mutum ba komai bane
sai fatan cikawa da imani kawai.
"Ya dai na ganka haka?"
"Dole ki ganshi haka tunda ya aikata abunda yayi niyya bisa
son zuciyarsa."
Hajja ta dubi Alhaji wanda ya shigo cikin rashin fahimta
"Menene ya faru?"
Alhaji ya zayyane mata halin da ake ciki. Shiru tayi kafin
tayi salati.
"Babana ya akayi ka aikata wannan d'anyen aikin? Meyasa
baka sanarmin ba?"
Jafar dai shiru yayi,Alhaji yayi kwafa
"Ina zai sanar damu? Ai bamu isa dashi bane."
Jin haka Jafar ya soma basu hakuri har da durkusawa
k'asa.
"Ai baba na fad'a maka abunda zaisa na yafe maka kawai
shine ka janye sakin nan ba idan kuwa ba haka ba wallahi
babu ni...."
"Alhaji kayimin afuwa domin Allah,maida auren Siyama
tashin hankaline agareni. Ku fahimceni..."
"Toh shikenan! Naji,tunda ka zab'i rabuwarka dani kaje.
Kada na k'ara ganin keyarka a gidana!!"
Jafar da Hajja suka dubeshi a razane,shakka babu da
gaske yake. Wannan yasa Jafar ya daure yace
"Shikenan na janye sakin,na maidata. Allah Ya huci
zuciyarku."
Yana kaiwa nan ya fice da saurinsa yana jin tamkar ya
kashe kansa don bakin cikin mayarda Siyama da aka
sanyashi yayi.
Tun daga lokacin rayuwa ta chanjawa Jafar. Baida wani
babbar matsalar data sha kanshi irin na aurensa da Siyama
da Alhaji ke matsa mishi akan ta komo d'akinta. Saida Abba
ya bud'ewa Alhaji wuta yace ya barshi sai nan da wata uku
zata koma d'akinta sannan ne Alhaji ya daina cewa komai
akan maganar.
Yana tsaye yana sharce gashin kansa da (comb) yana
kallon matarsa ta madubi sai turo baki takeyi ita a lallai tana
fushi. Murmushi yayi ya ajiye ya karasa wajenta. Tayi
azamar kauda fuskarta. Ya sanya hannunsa a hab'anta ya
juyo da ita, tayi saurin rufe idonta ita ala dole bazata
kalleshi ba
Jafar yayi dariya
"Oh kallon nawa ma baza'ayi ba? Shikenan nayi niyyar nace
maki ki shirya muje na saukeki amma tunda hakane.."
Da sauri ta rukunkumeshi tana dariya
"A'a kayi hakuri Yaya j zan kalleka har ma abunda yafi
kallon zan aikata maka in har zanje kamun Basma."
Ya janyeta yayi mata wani irin kallo ta kauda kanta tana
murmushi
"A'a ban yarda ba,kince zaki iya kallona menene abun
d'auke kai? Kinsan ina burin ganin ranar da zakiyi ta kallona
har tsawon kamar minti uku ma."
Tayi kokarin mikewa ya janyota cinyarsa
"Ai ba haka mukayi dake ba yar budurwata. Saikin kalleni
ko kuma ki..."
"Nayi me? Ni inagaa shi zaifi min sauki fad'amin."
Ya tallafo fuskarta yayi mata rad'a a kunne. Tayi wuf ta hau
zille zille suna dariya
"Aa Yaya j,barni na saka kayana kaga lokaci fa yana
tafiya."
Dakyar Jafar ya bar Hadiyya. Ta shirya tsaf kai idan ja
ganta bakace tana dauke da d'an mutum a cikinta ba. Wani
ma sai yayi mata kallon wacce bata da aure. Ta yafa
mayafi wadatacce ta sanya komatsanta a 'yar jakar hannu
sannan ta fito ta kulle kofar. Anan d'an soron gidan ya
iskeshi yana goge mashin d'insa. Ko kallonta baiyi ba ya
cigaba wai a dole fushi yakeyi. Ta danne dariyar dake cinta.
Ta karasa ta rungumoshi ta baya, tana jin sanda ya sauke
ajiyar zuciya. Cikin lankwasar fa murya tace
"Haba mijina,mahad'in rayuwata kasan fa komai da nakeyi
duk saboda kai ne. Yanzu idan ba yau asabar ba sai lahadi
fa gareni na hutu. Kaima shaida ne tunda na koma karatuna
komai na rayuwa ya chanjamin amma haka nake kokari
saboda son da nake yiwa karatun. Bikin Basma fa?"
Ya juyo ya sumbaci goshinta yana murmushi
"Na huce ai deeyana. Saidai kwalliyar nan tayi yawa. Ina
fatan ba haka kike yinta ba kije makarantar?"
Tayi murmushi
"Ni kuma a suwa da zan tsallake umarnin mai house?"
Ya jinjina kai sannan ya fita da mashin d'in...
*****46
Wajen hud'u na yamma an soma sha'anin biki,Basma an
fito anyi shar. Hadiyya ma sai binta akeyi da kallo cike da
sha'awar yanda tayi kyau ta chanja. Suna zaune suna hira
da Mamanta inda mama ke tambayarta ko Siyama ta dawo.
Hadiyya tace batasan ma halin da suke ciki ba amma
kwarai har a zuciya tana son dawowarta. Mama ta jinjina
kanta
"Ai da tausayi. Allah Yasa ya maidota."
"Amin dai,na lura bayason nayi mishi maganar ma kwata
kwata."
Mama zatayi magana wata budurwa 'yar makociyarta tazo
"Maman Hadiyya wai kinyi bak'i daga nijar suna nan tsaye a
kofar gidanki tare da Kawu nuhu shine yace nazo..."
Kafin takai karshe Hadiyya da mama sun mike a razane. Da
azama mama ta zura takalmanta tayi gaba. Hadiyya wuf ta
fad'a d'aki ta dauki mayafinta jiki yana rawa tayi saurin bin
bayan mama wacce tayi mata nisa. Tana kaiwa daidai
kofar gidan,taga mamanta ta runtuma a guje ta fad'a jikin
wani mutum dogo fari tas kana ganinshi kasan bafulatani
ne. Kuka sosai ta sanya, shima kukan yakeyi yana fad'in
"Allah Sarki Inno ashe da rabon muga juna?"
Ita kanta Hadiyya kukan farin ciki takeyi tana k'are musu
kallo. Su hud'u ne,maza uku sai mace d'aya. Kana ganinsu
kasan jinin mamanta ne saboda dukkansu suna d'iban
kama da ita. Dakyar aka shiga ciki aka zauna. Nan aka
kara gaisawa. Mama ta rasa inda zata sanya ranta don
dadi. Sai bayan an nutsu,dogon nan da mama tayi kira da
Hamma ya soma magana.
"Munsha wuya sosai kafin mu gane inda kake Inno. Baffa
tana shan kwanshe ba lafiya ita ta tilasta akan lallai ko
nawa zamuyi asararsu sai mun nemo mata inda kake. Toh
da farko Surajo muka soma nemowa dakyar muka samu
kwatanshen gidanta. Ashe tayi k'aura daga birnin Tawa ta
koma Arlit da zama. Karka so kaga wuyar da munkashi
Inno. Karshe dai munka isa munyi sa'ar ganota. Ita ta bamu
labarin mutuwar Muntari munyi kuka aradun Allah. Karshe
ta bamu adireshin inda kake a nijeriya. Koda munkazo kano
munka bawa wata a tasha ya karanta mana abunda ita
Surajo ta rubuta mana a takarda sai ta gane unguwar itace
tayi mana alfarma daman direba ce ta kawomu har nan
gidan wanga dan uwan na muntari. Anan munka taho nan
gidanka."
Mama tana kukam farin ciki saida hankalinta ya tashi da
taji mahaifinta ba lafiya. Nan ta rikice tace su wuce
yanzu,Kawu nuhu ya dakatar da ita
"Tafiya yanzu bazai yiwu ba Hajiya,baki ganin sun kwaso
gajiya? A bari zuwa gobe sai ayi tafiyar. Bari zan wuce gida
zansa a kawo musu abinci."
Mama tayi godiya bayan tafiyarsa suka juye yare zuwa
fillanci sai hirar yan uwa akeyi. Hadiyya kallon mamanta
takeyi tana mai jin wani dadi a ranta yau kukan dare ya
k'are tunda an samu biyan bukata sai godiyar Allah. Suna
hirarsi taga suna kallota. Mama tayi dariya tana gayamusu
diyarta ce ita kadai gareta tayi aure ma. Hamma ya mik'a
mata hannu
"Yakinan yarona."
Hadiyya na murmushi ta mika hannunta ta zauna a gefensa
tana gaishesu. Hamma ya dafa kanta
"Kayi hakuri kaji? Bakasanmu ba. Ka yafemuna."
Saiga hawaye a fuskarsa. Mama ta dakewa zuciyarta,
"Hadiyya,hamma shine babban yayana a wajen mamanmu.
Wannan da kike gani ta nuna d'an tsamurmurin bak'i,d'an
kanin baffa nane sunansa Haladu. Wancan kuma,(ta nuna
gajeran cikinsu) baffanmu d'aya dashi sunansa Saminou.
Itama wannan sunanta Amina muna ce mata Amindago.
D'iyar yayan Baffana ce. Hadiyya sai kallonsu takeyi cike da
kauna. Babu mai jin Hausa cikinsu sai Hamma da surajo.
Ganin suna hira itama hadiyya ta shiga daki ta kira Jafar ta
sanar dashi abunda ke faruwa. Yaji dadi sosai ya tayasu
murna yace zai biyo anjima. Kan kace me,yan uwan
mahaifin hadiyya sun cika gidan kowanne da d'an
kwanonsa na abinci. Basma ma bayan gama kamunta ta
kira Hadiyya taji tana ina sai take sanar mata nan da nan ta
suka taho da 'yan gidansu harma da wasu yan uwanta da
sukazo biki. Gidan Mama ya cika. Sarah sai hidimar aiki
takeyi ita kanta ta taya mama murna. Surajo sai binta
yakeyi da kallo har ya kasa hakura cikin fulatanci ya
tambayi mama ko wacece.
Nan tayi mishi bayani ai kuwa yace yaga matar aure a
Kano. Mamaki ya kama yan uwan saida suka gane da
gaske yakeyi sannan mama tayi murmushi cikin yaren
Hausa ta yiwa sarah maganar. Ta kara da cewa
"Na tabbata babu wanda zai barki ki tafi nijar aure."
"Haba me zai hana mama? Ai nikam bani da yan uwan da
suka fiku. Wallahi ina kaunarku fiye dasu tunda suka kasa
taimakona a halin da nake ciki. Ai babu inda bazan iya zuwa
ba saidai zanyi shawara da kakata naji abunda zatace."
"Yauwa Saratu,ko idan mun dawo ne ko kuma ta waya saiki
sanar dani."
Sarah taji dadi sosai don har fita tayi suka d'anyi hira.
Shima surajo matarsa sun rabu saboda takura masa da
takeyi. Tabarshi da 'ya'yansa shida.
Jafar kuwa harda iyayensa yazo,itama anti habiba jin da
tayi washegari zasu tafi tazo. Kowa ya taya mama farin ciki
karshe har hadiyya suka tattara suka tafi.
*******
Duk wanda zaiga Siyama sai ya tausayawa rayuwarta.
Gaba d'aya bazakace itace wannan Siyamar ba kyakkyawa
kodayaushe cikin wahala take a gidan. Tayi bak'i ta lalace
tamkar ba gidan ubanta ba. Ko yanzu ta kammala aiki Abba
ya dawo yaga sashensa bai gyaru ba yanzu zai kamata ya
lafta sannan ya sanyata ta k'ara yi. Hajiya bata magana
kasancewar sau d'aya ta gwada yin magana ya kusan
dukanta sannan ya tsawatar akan kada ta sake tasa mishi
baki a lamarinsa da d'iyarsa. Siyama bata damu sosai da
abunda Abba keyi mata ba. Sai lokacin ta soma fahimtar
kuskuren data tafka a gidan Jafar. Tausayi da matsanan
son mijinta ya shigeta. Tana ji inama ya maidata ta
gwammace tayi aikin da take kad'an da batason yi na
gyaran gidanta akan wannan na gidan. Ko babu komai acan
bata wanki. Amma anan gashi har nata dana hajiyarta da
faruk ita keda alhakin yinsa. A wata biyu tuni ya kware a
kowane aiki. Har ta saba,ga wani uban ladabi da ta koya
kullum ta tashi saita durkusa ta gaishe da hajiyarta abunda
koda wasa batayi a baya. Ga Abba kuwa,yafi kowa jin dadin
wannan chanji na Siyama. Kullum idan ta kammala zaka
tsinceta zaune tana karatun alkur'ani tana yi tana hawaye
da jin takaicin wannan sakin da Bash ya janyo mata. A gefe
daya ba wanda ta tsana yanzu kamar hajiyarta da rumaisa
wadanda sun bada nasu kwamashon wajen lalacewar
aurenta. Wata rana da yammaci anti rumaisa tazo saidai
bata iske hajiyarsu ba ta d'an fita. Kasancewar Lahadi
Abba yana gidan,ta zauna ta soma bawa Siyama labarin
abunda ke damunta akan mijinta wanda a yanzu ya juya
mata baya aure zaiyi bata ko kalleta ba balle ta tofa ta
cigaba da linke kayan shanyar data wanke,Faruk yana
gefenta yana wasa abunda. Har hakan ya bawa anti
rumaisa mamaki. Ta dubeta
"Siyama ni kika share haka?"
Siyama ta dubeta tayi murmushin takaici
"Me zance anti rumaisa? Laifine idan Yaya nura yayi aure?
Ki godewa Allah tunda bai rabaki da gidansa ba kamar ya
da kuka janyomin mutuwar aure."
Idanunta suka cika da kwalla
"Kun cuceni anti. Ina zaune gidan mijina kun tayarmin da
hankali kun rabani da aurena mutuncina. Kuna tunanin Allah
bazaimin sakayya ba? Kuna zaton zaku cigaba da rayuwar
farin ciki bayan kun kassara nawa rayuwar?"
Siyama tayi murmushi mai ciwo kafin ta k'ara cewa komai
tuni Anti ta rufeta da duka. Bata damu data kare kanta
ba,saidai ganin da tayi ta samu Faruk ya runtuma ihu
wanda ya janyo hankalin Abba yasa Siyama mikewa ta
janye d'anta tana kuka. Abba ya shigo sosai fuskarsa daure
wannan yasa anti rumaisa nutsuwa. Ya dubi Siyama
"Menene ya had'aku?"
Daidai lokacin Hajiya wacce ta dawo daga unguwa ta
shigo,Siyama wacce ta gama kaiwa bango tana kuka mai
karfi tace
"Wallahi yau zan tona duk abunda ya faru. Abba inaso yau
ku bani damar magana. A kirawo Yaya jafar😝(
Sabon salo) yau sai kowa yaji warin rub'abb'an kwan nan.
Abba abunda Yaya jafar yace maka shine ya had'amu
wallahi ba shi bane ya janyo sakin wani lamarin ne daban
saidai bance wannan d'in ma bana aikatawa ba. (Kazanta).
Abba ka yafemin,don Allah ka bani damar magana."*****46
Wajen hud'u na yamma an soma sha'anin biki,Basma an
fito anyi shar. Hadiyya ma sai binta akeyi da kallo cike da
sha'awar yanda tayi kyau ta chanja. Suna zaune suna hira
da Mamanta inda mama ke tambayarta ko Siyama ta dawo.
Hadiyya tace batasan ma halin da suke ciki ba amma
kwarai har a zuciya tana son dawowarta. Mama ta jinjina
kanta
"Ai da tausayi. Allah Yasa ya maidota."
"Amin dai,na lura bayason nayi mishi maganar ma kwata
kwata."
Mama zatayi magana wata budurwa 'yar makociyarta tazo
"Maman Hadiyya wai kinyi bak'i daga nijar suna nan tsaye a
kofar gidanki tare da Kawu nuhu shine yace nazo..."
Kafin takai karshe Hadiyya da mama sun mike a razane. Da
azama mama ta zura takalmanta tayi gaba. Hadiyya wuf ta
fad'a d'aki ta dauki mayafinta jiki yana rawa tayi saurin bin
bayan mama wacce tayi mata nisa. Tana kaiwa daidai
kofar gidan,taga mamanta ta runtuma a guje ta fad'a jikin
wani mutum dogo fari tas kana ganinshi kasan bafulatani
ne. Kuka sosai ta sanya, shima kukan yakeyi yana fad'in
"Allah Sarki Inno ashe da rabon muga juna?"
Ita kanta Hadiyya kukan farin ciki takeyi tana k'are musu
kallo. Su hud'u ne,maza uku sai mace d'aya. Kana ganinsu
kasan jinin mamanta ne saboda dukkansu suna d'iban
kama da ita. Dakyar aka shiga ciki aka zauna. Nan aka
kara gaisawa. Mama ta rasa inda zata sanya ranta don
dadi. Sai bayan an nutsu,dogon nan da mama tayi kira da
Hamma ya soma magana.
"Munsha wuya sosai kafin mu gane inda kake Inno. Baffa
tana shan kwanshe ba lafiya ita ta tilasta akan lallai ko
nawa zamuyi asararsu sai mun nemo mata inda kake. Toh
da farko Surajo muka soma nemowa dakyar muka samu
kwatanshen gidanta. Ashe tayi k'aura daga birnin Tawa ta
koma Arlit da zama. Karka so kaga wuyar da munkashi
Inno. Karshe dai munka isa munyi sa'ar ganota. Ita ta bamu
labarin mutuwar Muntari munyi kuka aradun Allah. Karshe
ta bamu adireshin inda kake a nijeriya. Koda munkazo kano
munka bawa wata a tasha ya karanta mana abunda ita
Surajo ta rubuta mana a takarda sai ta gane unguwar itace
tayi mana alfarma daman direba ce ta kawomu har nan
gidan wanga dan uwan na muntari. Anan munka taho nan
gidanka."
Mama tana kukam farin ciki saida hankalinta ya tashi da
taji mahaifinta ba lafiya. Nan ta rikice tace su wuce
yanzu,Kawu nuhu ya dakatar da ita
"Tafiya yanzu bazai yiwu ba Hajiya,baki ganin sun kwaso
gajiya? A bari zuwa gobe sai ayi tafiyar. Bari zan wuce gida
zansa a kawo musu abinci."
Mama tayi godiya bayan tafiyarsa suka juye yare zuwa
fillanci sai hirar yan uwa akeyi. Hadiyya kallon mamanta
takeyi tana mai jin wani dadi a ranta yau kukan dare ya
k'are tunda an samu biyan bukata sai godiyar Allah. Suna
hirarsi taga suna kallota. Mama tayi dariya tana gayamusu
diyarta ce ita kadai gareta tayi aure ma. Hamma ya mik'a
mata hannu
"Yakinan yarona."
Hadiyya na murmushi ta mika hannunta ta zauna a gefensa
tana gaishesu. Hamma ya dafa kanta
"Kayi hakuri kaji? Bakasanmu ba. Ka yafemuna."
Saiga hawaye a fuskarsa. Mama ta dakewa zuciyarta,
"Hadiyya,hamma shine babban yayana a wajen mamanmu.
Wannan da kike gani ta nuna d'an tsamurmurin bak'i,d'an
kanin baffa nane sunansa Haladu. Wancan kuma,(ta nuna
gajeran cikinsu) baffanmu d'aya dashi sunansa Saminou.
Itama wannan sunanta Amina muna ce mata Amindago.
D'iyar yayan Baffana ce. Hadiyya sai kallonsu takeyi cike da
kauna. Babu mai jin Hausa cikinsu sai Hamma da surajo.
Ganin suna hira itama hadiyya ta shiga daki ta kira Jafar ta
sanar dashi abunda ke faruwa. Yaji dadi sosai ya tayasu
murna yace zai biyo anjima. Kan kace me,yan uwan
mahaifin hadiyya sun cika gidan kowanne da d'an
kwanonsa na abinci. Basma ma bayan gama kamunta ta
kira Hadiyya taji tana ina sai take sanar mata nan da nan ta
suka taho da 'yan gidansu harma da wasu yan uwanta da
sukazo biki. Gidan Mama ya cika. Sarah sai hidimar aiki
takeyi ita kanta ta taya mama murna. Surajo sai binta
yakeyi da kallo har ya kasa hakura cikin fulatanci ya
tambayi mama ko wacece.
Nan tayi mishi bayani ai kuwa yace yaga matar aure a
Kano. Mamaki ya kama yan uwan saida suka gane da
gaske yakeyi sannan mama tayi murmushi cikin yaren
Hausa ta yiwa sarah maganar. Ta kara da cewa
"Na tabbata babu wanda zai barki ki tafi nijar aure."
"Haba me zai hana mama? Ai nikam bani da yan uwan da
suka fiku. Wallahi ina kaunarku fiye dasu tunda suka kasa
taimakona a halin da nake ciki. Ai babu inda bazan iya zuwa
ba saidai zanyi shawara da kakata naji abunda zatace."
"Yauwa Saratu,ko idan mun dawo ne ko kuma ta waya saiki
sanar dani."
Sarah taji dadi sosai don har fita tayi suka d'anyi hira.
Shima surajo matarsa sun rabu saboda takura masa da
takeyi. Tabarshi da 'ya'yansa shida.
Jafar kuwa harda iyayensa yazo,itama anti habiba jin da
tayi washegari zasu tafi tazo. Kowa ya taya mama farin ciki
karshe har hadiyya suka tattara suka tafi.
*******
Duk wanda zaiga Siyama sai ya tausayawa rayuwarta.
Gaba d'aya bazakace itace wannan Siyamar ba kyakkyawa
kodayaushe cikin wahala take a gidan. Tayi bak'i ta lalace
tamkar ba gidan ubanta ba. Ko yanzu ta kammala aiki Abba
ya dawo yaga sashensa bai gyaru ba yanzu zai kamata ya
lafta sannan ya sanyata ta k'ara yi. Hajiya bata magana
kasancewar sau d'aya ta gwada yin magana ya kusan
dukanta sannan ya tsawatar akan kada ta sake tasa mishi
baki a lamarinsa da d'iyarsa. Siyama bata damu sosai da
abunda Abba keyi mata ba. Sai lokacin ta soma fahimtar
kuskuren data tafka a gidan Jafar. Tausayi da matsanan
son mijinta ya shigeta. Tana ji inama ya maidata ta
gwammace tayi aikin da take kad'an da batason yi na
gyaran gidanta akan wannan na gidan. Ko babu komai acan
bata wanki. Amma anan gashi har nata dana hajiyarta da
faruk ita keda alhakin yinsa. A wata biyu tuni ya kware a
kowane aiki. Har ta saba,ga wani uban ladabi da ta koya
kullum ta tashi saita durkusa ta gaishe da hajiyarta abunda
koda wasa batayi a baya. Ga Abba kuwa,yafi kowa jin dadin
wannan chanji na Siyama. Kullum idan ta kammala zaka
tsinceta zaune tana karatun alkur'ani tana yi tana hawaye
da jin takaicin wannan sakin da Bash ya janyo mata. A gefe
daya ba wanda ta tsana yanzu kamar hajiyarta da rumaisa
wadanda sun bada nasu kwamashon wajen lalacewar
aurenta. Wata rana da yammaci anti rumaisa tazo saidai
bata iske hajiyarsu ba ta d'an fita. Kasancewar Lahadi
Abba yana gidan,ta zauna ta soma bawa Siyama labarin
abunda ke damunta akan mijinta wanda a yanzu ya juya
mata baya aure zaiyi bata ko kalleta ba balle ta tofa ta
cigaba da linke kayan shanyar data wanke,Faruk yana
gefenta yana wasa abunda. Har hakan ya bawa anti
rumaisa mamaki. Ta dubeta
"Siyama ni kika share haka?"
Siyama ta dubeta tayi murmushin takaici
"Me zance anti rumaisa? Laifine idan Yaya nura yayi aure?
Ki godewa Allah tunda bai rabaki da gidansa ba kamar ya
da kuka janyomin mutuwar aure."
Idanunta suka cika da kwalla
"Kun cuceni anti. Ina zaune gidan mijina kun tayarmin da
hankali kun rabani da aurena mutuncina. Kuna tunanin Allah
bazaimin sakayya ba? Kuna zaton zaku cigaba da rayuwar
farin ciki bayan kun kassara nawa rayuwar?"
Siyama tayi murmushi mai ciwo kafin ta k'ara cewa komai
tuni Anti ta rufeta da duka. Bata damu data kare kanta
ba,saidai ganin da tayi ta samu Faruk ya runtuma ihu
wanda ya janyo hankalin Abba yasa Siyama mikewa ta
janye d'anta tana kuka. Abba ya shigo sosai fuskarsa daure
wannan yasa anti rumaisa nutsuwa. Ya dubi Siyama
"Menene ya had'aku?"
Daidai lokacin Hajiya wacce ta dawo daga unguwa ta
shigo,Siyama wacce ta gama kaiwa bango tana kuka mai
karfi tace
"Wallahi yau zan tona duk abunda ya faru. Abba inaso yau
ku bani damar magana. A kirawo Yaya jafar😝(
Sabon salo) yau sai kowa yaji warin rub'abb'an kwan nan.
Abba abunda Yaya jafar yace maka shine ya had'amu
wallahi ba shi bane ya janyo sakin wani lamarin ne daban
saidai bance wannan d'in ma bana aikatawa ba. (Kazanta).
Abba ka yafemin,don Allah ka bani damar magana."
Kazamar Gida*****47
Hajiya ta yarda jakar hannunta hankalinta ya tashi ta zaro
ido tana gumi tana duban Siyama. Rumaisa ji tayi kamar ta
saki fitsari a tsaye,cikinta sai kad'awa yakeyi
Abba cike da mamaki yake duban Siyama,tsananin
tausayinta ya kamashi ya d'agota tsaye
"Tashi Siyama,na baki dama. Bayan magriba zamu had'u
kowa da kowa ayi maganar. Ke kuma ki zauna kada kibar
gidan nan sai an gama."
Rumaisa ta hau rawar murya
"Abba baice nakai dare ba ai
"
Ya watsa mata wani kallo kafin ya jinjina kanshi
"Shikenan zanyi kiran Nuran na gayamishi ni nace ki zauna
zamuyi magana."
Hajiya ta dafe kirji
"Yar iskar yarinya me kike nufi?"
Jin wannan furucin yasa suka san ta shigo. Siyama
hankalinta ya tashi,ta sanarwa Abba bazata iya zama
wajensu ba. Yace ta dauki yaronta ta yafo mayafi ta
biyoshi. Yana tsaye ta dauko mayafi ta ciccibi yaronta suka
fita,jajayen idanun Hajiya yana kanta tamkar ta shak'ota
takeji. Gidansu Jafar ya kaita wajen Hajja sannan ya nufi
sashen Alhaji ya sanar dashi anjima bayan magrib yanason
ganinsu. Daga nan ya bugawa jafar yace yazo shima da
iyalinsa..
Hajiya ta kasa zaune ta kasa tsaye,ta dubi Rumaisa
"Siyama yar kutumar uba ce,(sry) me take nufi? Asiri zata
tonamin? Na shiga uku ni Maimuna."
Kawai sai tayi zaman yan bori a kasa ta rushe da kuka. Anti
rumaisa ma kukan takeyi na danasanin abunda ta aikata,ta
mike da sauri
"Wallahi bazan zauna ba tafiya zanyi."
Daga haka tayi hanyar fita saidai me? Abba ya kulle kofar
gidansa gam saboda yasan halinsu. Dole ta koma ciki tana
fad'a
"Duk kece Ummul aba'isin shigarmu wannan masifa Hajiya.
Da ace munyi hakuri da lamarin auren nan na Siyama an
nema mata maganin mallaka da duk haka bata faru ba
yanzu gashinan ba tsuntsu ba tarko."
Hajiya ta soma balbaleta da fad'a
"Kyace haka mana tunda kin gama lashe kud'ad'en da
yaron nan ya aika maki. Abun kunyar ai bani kadai ya shafa
ba."
Haka sukayita maganganu wannan ta yab'awa
wannan,wannan ta maida martani babu zancen ganin
girma.
*****
Jafar yayi mamakin jin kiran da Abba keyi mishi. Duk da
haka dai yayi kiran Hadiyya yace ta shirya gashinan tafe
zasu fita. Itama dai cikin mamakin ta shirya tana jiransa
koda yazo kawai wucewa sukayi.
*******
MISALIN BAKWAI NA DARE......
"Ke muke sauraro Siyama."
Wannan yasa Jafar satar kallon inda take cike da mamakin
yanda ta kod'e ta chanja. Tabbas alhakin abunda tayimishi
ne ya maisheta haka. Hadiyya ta tausayawa Siyama
matuka ganin yanda gaba daya tayi duhu ta rame sai kace
wacce ba gaban iyayenta take ba koda dai gidan miji yafi
amma lalacewarta tamkar wacce ke a hannun kishiyar uwa.
Ta k'ara rungumar Faruk wanda tun zuwanta ya mak'ale
mata ita kanta tayi kewar yaron. Kowa ya baza kunne yana
sauraron abunda Siyama zata fad'a. Hajiya da rumaisa
gumi suke had'awa,Yaya hanif ma yana zaune cike da
mamaki domin shi d'in baisan dalilin taron ba yazo ne
domin gaida Abbansa akace shima ya samu wuri ya zauna.
Siyama ta soma magana cikin ruwan hawaye. Tiryan tiryan
ta basu labarin abunda ya faru tun daga kiran da Bash yayi
mata da kuma kud'i da uzzurawar dasu Hajiya suka yiwa
rayuwarta akan lallai saita kashe aurenta ta auri Bash
saboda yana da kud'i. Bata boye komai ba ciki kuwa harda
motar Bash data shiga bisa larura.
Salati kawai kakeji da kuka. Abba jikinsa har rawa yakeyi.
Jafar saida yaji hankalinsa ya tashi,ya kad'u sosai da jin
gaskiyar abunda ya faru. Nadama mai tsanani na abunda ya
aikatawa Siyama ya rufeshi,inama yabi shawarar Haris da
Hadiyya yayi bincike a baya. Tsananin tausayin Siyama ya
kamashi. Abba ya kaiwa Rumaisa duka a hanci sai ga jini
yana fitowa. Hajiya tana ihun kuka tace
"Oh ni Maimuna yau Allah Ya hadani da shegiyar yarinya.
Wannan sharrin ki rasa wacce zakiyiwa sai ni?"
Siyama na hawaye bata saurareta ba ta ciro wayarta ta
mik'awa Abbanta.
"Abba ga sakonnin da muke musayarsu ciki kuwa harda na
kud'in da hajiya ta aikomin tace daga Bash ne."
Ta juya ga Hajiya
"Hajiya ke uwata ce, ina sonki. Ina iyakar kokari wajen yin
biyayya agareki saidai baki taba bani shawara na gari ba a
komai na rayuwata. Kodayaushe burinki ki rabani da farin
cikina. Gashi a yanzu kinyi nasara,saidai hajiya ki sani
alhakina bazai barki ki runtsa ba. Allah zai sakamin abunda
kika aikata ga rayuwata. Yaya jafar ka gafarceni,wallahi
ban taba sha'awar aikata zina ba. Ni ba mazinaciya bace,
kaddara ce ta afkamin. Don Allah ku gafartamin."
Siyama ke maganar tana kuka sosai,ta bawa kowa tausayi
musamman ma Jafar wanda boyayyen soyayyar nan nata
dake boye a k'asan zuciyarsa ya dawo sabo fil. Ji yakeyi
inama yana da damar da zai rungumeta ya rarrasheta.
Abba ya dubeta
"Baki da laifi Siyama,saidai kinyi kuskure da tun a farkon
lamarin baki sanar da ko mijinki ba idan mu bazaki iya
sanar damu ba. Na tabbata da abun baikai ga haka ba,koda
dai haka Allah Ya kaddara zai faru toh dole ya kasance."
Ya maida dubansa ga Hajiya
"Hajiya Maimuna ya mukayi dake a baya akan auren Jafar
da Siyama? Inace na fadamaki muddin kikayi nasarar raba
aurensu kema a bakacin aurenki ko? Toh ni Alhaji Mustapha
na sakeki ki tattara komai naki ki barmin gidana. Mugun
halinki nikam bazan iya dashi ba."
Siyama ta runtse ido,har cikin ranta bataso ba. Uwa uwa ce
duk lalacewarta kafiso ka budi ido ka ganta tare da
mahaifinka. Hawaye masu zafi suka zubo mata. Hanif
kuwa baiji ko d'ar da hukuncin Abba ba,saboda shi kanshi
yaji bakin cikin abunda ta aikata. Ai kuwa hajiya ta mike
tana zage zage babu wanda ya kulata karshe ta fice daga
gidan tana tsine tsine.
Abba ya dubi Rumaisa
"Ke kuwa na rabaki da gidana..."
"Haba Yaya,abun yayi yawa. Don Allah kada ka yiwa
yaranka mugun baki. Kaifa mahaifi ne."
Cewar Alhaji. Wannan yasa Abba yiwa anti rumaisa tsawa
"Tashi ki wuce gidan mijinki,aure ne Nura sai yayi babu
fashi. Don uwarki saikin gasu a gidan."
Ta mike tana goge hancinta da mayafi,sum sum ta fita.
Hadiyya dai tana gefe tana hawayen tausayi ganin lamarin
takeyi kamar a fim.
Abba yayi dogon nasiha,karshe Alhaji yayiwa Siyama
albishir akan tun washegarin ranar da sakin ya afku Jafar
ya maidata saidai Abba da yak'i komen. Amma ta shirya
gobe mijinta zaizo su tafi. Ta gefe ta saci kallon Jafar taga
ko yayi na'am da hakan. Illai kuwa haka dinne,murmushi
Jafar yake sakar mata tayi azamar sunkuyar da kanta.
Hawayen farin ciki suka kwaranyo mata.
*******48
Bayan kowa ya watse,Siyama ta rako hadiyya da jafar zasu
koma gida. Hadiyya ta dubeta tana dariya
"Toh antina,sai kuma munzo daukar abarmu ko?"
Siyama tayi dariya ta rungumeta cikin farin ciki. Jafar yana
kallonsu yana jin dadi a ransa. Hadiyya tayi azamar fita
tana cewa
"Bari na shiga na yiwa Hajja sallama."
Abunda Jafar ke jira kenan,ai kuwa da hanzari ya rungume
Siyama jikinsa yana rawa ga wani irin sanyi da yaji a ransa.
Ya dago fuskarta ya hau sumbatar bakinta bata musa mishi
ba har saida ya kammala don kanshi ya saketa. Suka dubi
juna cikin so da kaunar juna,murmushi ya sakar mata ya
shafi gefen kumatunta
"Ki yafemin.."
Da sauri ta rufe bakinshi
"A'a Yaya jafar,ni keda laifi don Allah ka yafemin bazan kara
boye maka komai ba."
Yayi murmushi
"Na yafe maki siyama,komai ya wuce."
Farin ciki ya cika mata zuciya. Ta sauke numfashi. Haka
sukayi sallama cikin kewar juna.
********
Washegari da yamma saida ya kammala komai a kasuwa
sannan ya nufi wajen Haris. Nan ma haris yaji mamakin
yanda lamarin ya faru karshe ya kara nusar dashi
muhimmancin yin bincike kafin yankewa mutum hukunci
gudun shiga hakki. A gurguje yayi mishi godiya da sallama
ya tafi dauko Siyama har Haris yana mishi dariya.
Hadiyya ta gyarawa siyama komai na dakinta da falo. Hatta
bandakunan ta wankesu sunyi kyal dasu. Girki lafiyayye ta
shirya musu ta jera a tsakar falon Siyama. Sai kamshin
turaren wuta ke tashi. Saida ta kammala tayi wankanta tsaf
itama tayi kwalliya. Jim kadan taji shigowar mashin d'in
Jafar tayi azamar bud'e musu gidan ta rungume Siyama ta
amshi Faruk.
Siyama taji dadi matuka ganin irin gyaran da Hadiyya ta
yiwa sashenta.
Bata kara gaskata cewar Hadiyya tana kaunarta ba saida
tayi kwanaki a gidan,anti sama anti k'asa take kiranta
dashi. Ga kula da Faruk duk da itama d'in tana fama da
nata cikin. Wannan yasa Siyama wancakali da kishi ta riki
Hadiyya yar uwa. Yanzu yan jafar suna yawan zuwa
gidan,Hajja na kaunar surukanta kamar me.
Jafar kodayaushe Siyama cikin shayar dashi mamaki
takeyi. Bai taba dauka KAZAMAR GIDA zata koma
TSAFTATACCIYAR GUDA ba. Ba shakka Allahu mai hikima
ne,Mai chanja bayinSa ne. Sai gashi kodayaushe Siyama
cikin aiki take. A wata guda ta murje tayi kyau abinta.
Hadiyya kuwa dakyar Jafar ya barta suka shirya zuwa nijar
wajen yan uwan mamanta da Maman nata. Ganin haka
itama Siyama tace baza'a barta a baya ba. Tare sukaje
abinsu don mota guda Jafar yayi musu haya,daga su sai
direban. Mama tayi mamaki kwarai na ganin Siyama tare
dasu. Taji dadin hakan kwarai. Sunga sarah tayi kyau
abinta da mijinta Surajo. Yaranta suna hannun kakarta tana
kula dasu.
Komai na rayuwa ya chanja. Hajiya dakyar Abba ya
maidota bayan bin da yan uwanta suka dungayi karshe tayi
alkawarin zata gyara halinta. Abun zai baka mamaki idan
kaga Hajiya a falon Hajjah ana hira da dariya.
Lamarin Allah kenan!!
******
Hadiyya zaune tana koyawa Faruk homework,yan biyunta
Na'im da Na'ima suka shigo a guje suka fada jikin Siyama.
Hadiyya ta daka musu tsawa
"Kuyi a hankali mana,baku ganin cikin dake jikinta?"
Siyama dake zaune da tulelan ciki haihuwa yau ko gobe tayi
dariya
"Barsu malama,idan basu zo wajen uwarsu ba wajen wa
zasuje?"
Hadiyya tayi murmushi tana kallon Siyama
"Allah anti ke kike sangarta yaran nan. Basajin magana."
"Kul,karki kara cewa yarana basuji zamu sa k'afar wando
d'aya."
Ta maida dubanta garesu
"Me kuke so?"
Na'ima sarkin surutu tace
"Anti alawa mukeso."
Tayi murmushi ta kama hannunsu suka shiga d'aki
"Ku muje ai akwai sauran wanda na siya maku jiya."
Da murna suka bita d'akin. Hadiyya ta girgiza kanta,ta lura
Siyama bazata daina shagwab'a yaran nan ba.
Da daddare suna zaune suna kallo a falo,Jafar ya dawo.
Yaran suka tafi wajenshi da gudu suna murnar ganinsa. Ya
daukesu daya bayan daya ya cilla sama kamar yanda yake
musu. Sannan ya amsa sannu da zuwan da matansa keyi
mishi.
"Maman twins ya nauyin jiki?"
"Alhamdulilllah baban twins."
Siyama ta amsa,ya dubesu
"Akwai albishir da zan maku amma kowacce saita fad'i
abunda zata bani."
Siyama da Hadiyya suka dubi juna kafin su dubeshi,Siyama
tayi magana
"Kada ka damu,zaka samu abunda yafi kud'i."
Yayi dariya sannan ya ciro takarda ya mik'a musu
"Alhamdulillah,yau na samu aiki a First bank. Sai ku tayani
addu'a Allah Ya dafamin."
Cikin murna matsananci suka rungumeshi a tare suna
hamdala,yaran ma ganin haka suma suka rungume
abbansu ta baya......!
Karshen KAZAMAR GIDA kenan
..inda nayi kuskure pls ayimin gyara kuma a yafemin...d'an
Adam ajizi ne
.wanda duk na b'atawa shima yayi hakuri...
Rufaida Omar Ibraheem!